AUREN TAGWAYE Page 51-60
.
"Yanzu kamar ni ina matsayin mijinki ace ban isa ki gayamin damuwarkiba, to shikenan zan fad'ama Daddy 'kila shi kin gayamashi idan ya tambayeki amma kinsan bazan saka maki ido kina matsayin matataba inje waje innemi matan banza.
.
"Yanzu kamar ni ina matsayin mijinki ace ban isa ki gayamin damuwarkiba, to shikenan zan fad'ama Daddy 'kila shi kin gayamashi idan ya tambayeki amma kinsan bazan saka maki ido kina matsayin matataba inje waje innemi matan banza.
Bayan Hannu Hassana tasa ta share hawayen dake bin kumatunta sannan ta kalli jabeer cikin dasashshiyar murya take magana "Nifa ba wani abu bane ke damuna kawai ina tunanin 6atan "yar'uwatane yau kwana biyu ko labarinta ba'a samuba.
Tana kaiwa nan tafashe da wani sabon kuka, jabeer har cikin ranshi tabashi tausayi sosai janyota yayi jikinsa yana rarrashinta, da dabara tasamu ta kwace kanta tanufi kitchen domin had'a masu breakfast.
** ** **
Daddy zaune daga bakin gado kallo d'aya zakayimai ka tabbatar da tsananin damuwar dake tattare dashi, Momy kuma nakan abin sallah tana lazimi idanunta fall da hawaye ro'kon Allah kawai take Allah bayyanar mata da d'iyarta aduk halin datake ciki,
Wayar daddy dake jone jikin socket tana chaji tahau ruri alamar shigowar kira, ko motsawa beyiba barantana yad'aga haka ta 'karaci ringing d'inta harta tsinke aka kuma kira karo na biyu nanma beyi niyyar d'agawaba, dan ko kallon wurin beyiba, Momy ce ta kalleshi tasa hannu ta goge hawayen dasuka gangaro kan kumatunta tace "Alhj wayarka fa tana ringing, shiru yayi kamar beji maganar datakeba, magana ta'karayimashu lokacin da kiran wayar ya'kara shigowa karo na ukku "Alhj yakamata ka d'aga wayarnan dan da alama kowaye yadamu daya gayama kowace mgana ce saboda wanda yakiraka dai-dai wannan lokacin 'karfe shidda na safiya yakira baka d'agaba yanace yanata kira kasan maganar nada matu'kar muhimmanci, tana rufe bakinta wani kiran yakuma shigowa karo na biyar, Momy bata jira daddy ba tanufi inda wayar take ta d'auko ta danna ok sannan ta mi'kamai ba musu ya kar6a yakara akunnensa batare daya kalli sunan wanda ke kiranba.
"Assalamu Alaikum aka fad'a a d'aya 6angaren, me maganar bejira jin abinda Daddy ze fad'aba yacigaba da magana
"Sunana Ahmad turaki comusioner of police, ina fata dai muna magana da Alhj manair company?
"Eh dashi kake magana daddy yabashi amsa a ta'kaice.
Zaku iya zuwa babbar headquarter mu ta police domin tabbatar da wata gawa da muka tsinta kota d'iyarkace.
"Sunana Ahmad turaki comusioner of police, ina fata dai muna magana da Alhj manair company?
"Eh dashi kake magana daddy yabashi amsa a ta'kaice.
Zaku iya zuwa babbar headquarter mu ta police domin tabbatar da wata gawa da muka tsinta kota d'iyarkace.
Saurin mi'kewa tsaye Daddy yayi yana yana salati "to shikenan ganinan zuwa bekobi takan Momy ba ya suri key d'in motarsa jikinsa dagashi sai jallabiya, silifas yazura a 'kafarsa yana shirin fita, momy tabiyoshi tana tambayarshi "Alhj lafiya? Beko sauraretaba yawuce hankali tashe.
Fad'awa Momy tayi kan gado tafashe da wani irin kuka me ban tausayi "ya Allah ka bayyanamin Hassana Allah sa duk inda take tana cikin aminci da kariyarka ya ubangiji, wani sabon kuka ya kubce mata.
Daddy na isa headquarter police bayan sun gaisa da comusioner nan yahad'a daddy da wasu police guda hud'u suka nufi babban asibitin dake garin kai tsaye matuare (d'akin ajiye gawa) suka nufa nan aka jawo dorowar da gawar Hussaina take, Daddy na ganinta yafashe da kuka kamar 'karamin yaro, nan ya tabbatarma 'yansandan d'iyarsace lokacin duk kamanninta sun canja fuskarta ta kunbura ga jini daya gama wanke mata jiki.
Nan yansandan suka shiga rarrashin Alhj "kayi ha'kuri Alhj inshaAllah zamu tsaurara bincike sai mungano Wanda ya aikata wannan mummunan laifi, dan bincike ya nuna ankashe marigayiyar ne ta hanyar dukan da akayimata aka.
Daddy kasa magana yayi sai kuka kawai dayake, haka aka d'auki gawar Hussaina cikin motar police d'in aka nufi gida da ita.
Love u all my Fan's
[2/2, 9:05 AM] Zee Elkaseem: *AUREN TAGWAYE*
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*
[2/2, 9:05 AM] Zee Elkaseem: *AUREN TAGWAYE*
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*
*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace*
Page......................37
® _TALENTED WRITER'S GROUP_ _(TWG)_
Momy kuwa tun bayan fitar daddy Daga gidan gabanta keta fad'uwa takasa zaune takasa tsaye.
Jin 'karar bud'e get tayi da sauri tatashi tanufi 'kofar fita daga falon zuwan harabar gidan, ganin motar me gidanta tare data police yasa tayi saurin komawa ciki tare da dafe 'kirjinta saboda jitake kamar zuciyarta zata fad'o saboda bala'in fargaba.
Jin annufo falon yasa fad'uwar gabanta ya yawaita, bata ankareba kawai sai gani tayi anshimfid'ar da gawar Hussaina tsakiyar falon, tana kai dubanta gareta taji duk illahirin wasu jijiyoyin jikinta dake aiki sunyi tsaye cak, kafin ayi wata magana sai ganin Momy akayi 'kasa ba alamar numfashi tattare da ita.
Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un Daddy yari'ka furtawa da sauri ya d'auko ruwa ya yayyafa mata, nan akayi nasarar dawowar numfashinta bakinta d'auke da salati.
Nan Daddy yacigaba da yimata nasiha yana rarrashinta da 'kyar yasamu ta nutsu ba abinda take maimaitawa a zuciyarta sai salatin annabi.
Ranar kafin ad'au wani lokaci labarin mutuwar Hussaina ya bad'e gari dandanan gidan Alhj mansir yacika da 'yan'uwa da abokan arzi'ki wasu na zubar da hawaye wasu kuwa sunyi jugum-jugum. Amma duk a tunananin mutane harma da daddy da Momy Hassanace ta mutu.
** ** **
Hassana zaune tana duba wani littafi na addu'oi kad'an-kad'an tayi try number Hussaina wai ko Allah zesa tashiga dan tanaso tagayamata Halin datake ciki, amma kamar kullum dai akashe ake cewa.
Jabeer ne yashigo jikinsa a sanyaye. haka kawai yana shigowa Hassana ta tsinci kanta da wata mummunan fad'uwar gaba.
Kallonta yayi ya matu'kar tausaya mata sannan yace "ki tashi yanzu zamuje gida daddy yana nemanmu, jitayi fad'uwar gabanta ya tsananta lokaci guda hawaye ya wankemata fuska a tunaninta jabeer yakai karartane.
Tasowa tayi jiki a sanyaye ta dur'kusa gaban jabeer "dan Allah kayi ha'kuri indai wannan maganarce nayima Al'kawari wlh zan gyara.
Wani irin tausayinta ya'kara mamaye zuciyarsa "a'a ba wannan maganar bace ban dad'e da isa office ba daddy yakirani yace muzo yanzu nidake nikaina bansan ko miye dalilin kiranba, haba tanajin haka wani sabon tashin hankali ya ziyarceta jikinta yafara kyarma kad'an yarage tasaki fitsari dan bako tantama tasan asirinsune ya tonu kan abinda suka aikata itada 'yar'uwarta nasanya jabeer yin *AUREN TAGWAYE* batare da saninsaba, innalillahi kawai tacigaba da furtawa acikin Zuciyarta, ahaka tanufi bedroom ta bud'e wadrope ta d'auko wata doguwar Riga ta canja kayan jikinta sannan tasaka hijab med'an girma wacce ta tsayamata iya gwiwa, plate shoe tasako sannan tafito falo ta iske jabeer na jiranta, yana ganin fitowarta yayi gaba tana biye dashi har gurin mota yabude gurin driver ya zauna sannan itama yabud'emata gidan gaba ba musu tashiga, amma duk illahirin jikinta kyarma yake dan kallo d'aya zakayimata ka tabbatar da bata cikin nutsuwarta.
Ahaka har suka 'karaso 'kofar gidansu tundaga nesa tahango dandazon Al'umma haka yacanjamata tunanani Zuwa wani daban "to wannan iyayen mutanenfa meke faruwane "innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un.
Hankalinta be'kara tashiba saida tashiga harabar gidan nanma cike yake da jama'a maza suna jiran afito da gawa, cigaba tayi da tafiya dai-dai 'kofar dazata sadata da falon gidan taga wasu gun-gun mata zaune sunyi jugum-jugum sai d'aya daga cikinsu ta nuna Hassana tana cema sauran matan "wannan itace Hussainar marigayiyar, d'ayar tace "oh itace wacce akayima aure kwanakin baya, d'aya tace itacefa Allah sarki mutuwa me yankan 'kauna lalle wannan yarinya tayi rashi Allah bata ha'kuri da dangana.........
Dai-dai wannan lokacin Hassana tanemi numfashinta tarasa sai mutanen dake gurin sukayo kanta anata salati aka kinkimeta akayi ciki da ita.
Dai-dai lokacin kuma aka fito da gawar Hussaina domin kaita makwancinta.
*Anan inso inja hankalin Al'umma akan mutuwa, yanzu abinda aka gane shine da ance wane ya mutu sai mata suje su cika gida wasuma ba dangin iya bare na baba, kuma Alhalin lokacin ana kimtsa gawa irin haka na jawo matsaloli da yawa, da zarar ka mutu 'yan'uwanka da iyayenka sha'kikai ake bu'katar suje ga gawarka bawai mutanen unguwaba, ba'ace kada mutane suje gidan suyi gaisuwaba amma ayi ha'kurin kauda mamacin, mata inajan hankalinku da kunyi gaisuwa ga wad'anda akayima mutuwar kutafi gidajenku shine mafi Alkhairi agareku kada azauna zaman gulma da cin abincin gidan mutuwa. ALLAH SA MUDACE ALLAH KUMA YASA MUCIKA DA IMANI ameen*.
.
Nan fa aka Shiga wani sabon tashin hankali ganin Hassana kwance ba Alamar numfashi tattare da ita, Momy kuka take tama rasa inda zata dosa saboda tsabar rud'ewa.
Sai kusan awa ukku sannan Hassana ta farfad'o lokacin 'Karin ruwane ke shiga jikinta, ahankali tafara bud'e idonta ido biyu sukayi da 'kanwar babanta Haj Uwani tana mata firfita, ganin ta bud'e idonta yasa tafara jeramata sannu.
Bin robar 'karin ruwan dake hannunta tayi da kallo, tunanin 'yar'uwarta tafad'omata arai "yanzu shikenan Hussaina tamutu nashiga ukku, ya zanyi da 'kullallen al'amarin data barni cikinsa, yazanyi in tunkari iyayena da mijin 'yar'uwata da wannan 'kazamin Al'amarin damuka aikata.
Fashewa tayi da wani irin kuka me ban tausayi, tana 'ko'karin tashi daga kan gadon, saurin ri'keta Haj Uwani tayi tare da rarrashinta.
"Kiyi ha'kuri Hussaina dukkan me rai mamacine, addu'a kawai zakibi 'yar'uwarki da ita, dan ita tafi bu'kata akan kome "Allah ji'kan Hassana yakai Haske kabarinta Allah toni asirin wad'anda suka aikata wannan mummunan aiki akanta, Haj Uwani tafad'a tana share hawayen fuskarta.
Hassana kuwa kwance tayi, tayi lamo akan gado tana sauraren yanda Mama Uwani 'Kanwar daddy take kwararo addu'a akanta bayan ita tasan ba itabace ta mutu, amma babu damar tafad'i, hawaye yacigaba da kwarara daga idanunta ba 'kakkautawa. Ahaka Momy tashigo d'akin hannunta d'auke da cup, ganin Hassana na kuka ya 'kara d'aga hankalinta itama kad'an yarage tafashe da kukan da kyar ta rarrashi zuciyarta, ta daure tami'kama Haj Uwani cup d'in hannunta "gashi tunda tatashi 'kara ta daure ko tea tasha kota d'an samu 'karfin jikinta.
Nan Haj Uwani kar6i cup din ta tada Hassana zaune tana 'ko'karin bata tea d'in tana 'kin kar6a da kyar tasamu tasha Rabin cup takoma ta kwanta da tunani barkatai cunkushe a kwalwarta.
*Bayan sati d'aya*
Hankali yad'an kwanta mutane 'yan'uwa na kusa dana nesa kowa ya koma gida, gidan yarage daga Momy sai Hassana wacce tundaga ranar da'akayi rasuwar tazo bata komaba saboda har yanzu jikinnata ba 'karfi duk tabi ta rame ta kod'e.
Washe gari ranar kwana takwas da rasuwar Hussaina Momy da Hassana na zaune, Momy na aikin rarrashinta akan taci abinci dan duk yinin yau batasa kome acikintaba, daddyne yashigo gidan da sallama, Momy ta amsa masa sallamar tare dayimashi sannu da zuwa, kallon Hassana yayi yaga yanda tarame ta kod'e cikin sati d'aya duk ta fita hayyacinta, har cikin ranshi ya tausayamata dan yasan ba karamar sha'kuwa tayi da 'yar'uwar tataba, sai dai al'amarin ubangiji ba ruwanshi da sha'kuwar dake tsakaninka da mutum idan yatashi d'aukar rayuwarsa.
"Hussaina, daddy yakira sunanta.
Gabanta yafad'i sannan ta juyo ta kalleshi tare da amsawa, amma kanta sadde 'kasa dan bata yadda su had'a ido dan gani take idan suka had'a ido da daddy ze iya gane cewa ba Hussaina bace.
Gabanta yafad'i sannan ta juyo ta kalleshi tare da amsawa, amma kanta sadde 'kasa dan bata yadda su had'a ido dan gani take idan suka had'a ido da daddy ze iya gane cewa ba Hussaina bace.
Daddy yacigaba da magana "inaso kitashi ki shirya dan munyi waya da mijinki yanzu haka yana kan hanya zezo ya d'aukeki sai kitashi ki shirya kikoma d'akin mijinki kicigaba da biyayya, kinga dai abinda yafaru da yar'uwarki saboda haka kicigaba dayimata addu'a Allah kai haske kabarinta, yana gama fad'in haka ya wuce d'akinshi, Hassana kau fashewa tayi da wani irin kuka tafad'a jikin Momy tana maida numfashi sama-sama.
Hankalin Momy ya masifar tashi ganin yanda Hussana ke kuka ga numfashinta na fita sama-sama, amma ba yanda zatayi dan tasan tunda Daddy yariga ya furta takoma tofa ba fashi saita koma yau d'in, saboda haka jiki a sanyaye Momy tatashi ta taimaka mata tayi wanka, tana fitowa tad'an shafa mai sama-sama sannan tacanja kayan jikinta zuwa wata doguwar Riga, bata dad'e da gama shirinba suka jiyo tsayawar motar jabeer a harabar gidan, kafin jabeer yashigo ciki daddy yafito ya umarci Hassana data tashi sutafi kada ta 6atamai lokaci.
Haka ta mi'ke jiki ba laka tanufi harabar gidan tana tafiya tana waige jitake kamar takoma tasanar da daddy gaskiyar Al'amari amma data tuno da irin zuciyar daddy sai tsoro yakamata, dan tasan tsaf itama ze iya aikata inda 'yar'uwarta tatafi.
Ahaka ta isa gurin motar jabeer na ganin tahowarta yashige mazaunin driver tare da budemata gidan gaba tashiga ya tayar da mota me gadi ya bud'emasu get suka d'au hanya.
.
.
Tun a mota Hassana ke faman kuka har suka iso gida, jabeer nayin parking tafito tanufi cikin gidan dagudu tana 'kara fashewa da kuka, tana shiga falo tawuce bed room tasa key tarufe 'kofa
tarufene dan bata bu'katar jabeer yabiyota yace ze rarrasheta, fad'awa tayi kan gado tacigaba da rizgar kuka Kamar zata cire ranta.
Tunanin Hussaina yafad'omata arai yanda suke kome tare, ba abunda ke rabasu ko bacci basu yadda yarabasu har tayi aure amma gashi mutuwa tarabasu, zaune tatashi ta d'auko wayarta tana kallon Hotunan dasukayi itada Hussaina lokacin suna gida wasu sabbin hawaye suka kwararo a idanunta, tafara surutai kamar wacce ke magana da wani a kusa da ita tana kallon wani hoto na Hussaina "sister mesa kika tafi kika barni da 'kulallen Al'amarin da bansan yanda zanyi in warwareshiba, Hussaina ina kikaje aka rabaki da rayuwarki, me kikayimasu suka kasheki, ya Allah ka toni asirin kosu waye suka aikata maki wannan abin.
Cillar da wayar tayi gefe takoma kan gadon ta kwanta tacigaba da kukanta,
Bata tashiba sai 'karfe bakwai da rabi na dare lokacin wani matsanancin ciwon kai ke addabarta, a daddafe tatashi tashiga toilet ta d'auro Al'wala ta rama sallolin da'ake binta daga magrib har isha'i tadad'e tana lazimi kafin tashafa takoma kan gado ta kwanta, tunani barkatai takeyi a zuciyarta tace "ni yanzu yazanyi in fidda kaina cikin wannan sar'ka'kiyar......
Bata tashiba sai 'karfe bakwai da rabi na dare lokacin wani matsanancin ciwon kai ke addabarta, a daddafe tatashi tashiga toilet ta d'auro Al'wala ta rama sallolin da'ake binta daga magrib har isha'i tadad'e tana lazimi kafin tashafa takoma kan gado ta kwanta, tunani barkatai takeyi a zuciyarta tace "ni yanzu yazanyi in fidda kaina cikin wannan sar'ka'kiyar......
Bayan kwana goma tunda Hassana tadawo gidan jabeer bayan rasuwar Hussaina bata yadda su had'u da jabeer.
Kalacin safe saitaji fitarshi take fitowa tasamu abinda zata sama cikinta, dukda ba wani abincin kirki takeciba hakanan take tutturwa, da rana zata fito tayi abinci tajera a dining sanan ragyara ko'ina na gidan ta share hadda d'akin jabeer d'in, tana gamawa take ibar wanda tasan ze isheta daga lokacin har dare sannan takoma d'aki bakuma Zata 'kara fitowaba sai gobe idan taji fitar jabeer d'in
Tun jabeer na rarrashinta akan tafito ta daina zaman d'akinnan har yaha'kura ya kyaleta ganin tunda yake magiya ko saurarensa batayi sai dai duk ranar dayayimata magana yajiyo sautin kukanta.
: Bayan sati d'aya tana zaune d'aki kamar yanda tasaba tanajin lokacin da jabeer yafita saboda haka da sauri tafito tahad'a abinda zataci, dankali da kwai tasoya sannan tahad'a tea cikin cup tadawo palo ta zauna tafaraci, bawani dad'insa takejiba dan yau tashi tayi da wata irin kasala ga tashin zuciya dake addabarta, ahaka tasamu ta tuttura dan yunwar jinta takeyi, tana gama cin abincin kuwa yafara tu'karta da gudu tanufi toilet tafara she'ka amai, saida ta amayar da duk abinda taci sannan taji sau'ki-sau'ki
Nan take kuma wani irin zazza6i yarufeta, tafara kyarma kan gado tafad'a sannan tajawo wani 'katon bargo ta kudundune dukda uban zafin da akeyi a lokacin.
.
Jabeer be dawo gidan ba sai bayan sallar azahar kamar yanda yasaba dawowa, da sallama yashigo falon kai tsye d'akinshi ya wuce yafad'a toilet yayi wanka danya kwaso gajiya sosai, bayan yafito daga wankan ne ya murzama jikinshi mai sannan ya canja kaya zuwa 'kanana marassa nauyi, falo yadawo kai tsaye dan yakwaso yunwa sosai yasan ze tarar da abinci kamar yanda yasaba.
Falo yadawo kai tsaye ya doshi dining area amma bisa mamakinsa sai yaga wayam bako cokali gurin barantana yasa ran abinci, cike da mamaki yashiga kitchen nanma ganinsa yayi tas ko ina a share a goge ba alamar andafa wani abinci cikinsa, cike da mamaki yadawo falon sannan yanufi d'akin Hussaina nocking yayi ahankali duk da yasan ba bud'ewa zatayiba, hannu yasa yad'an murd'a handle d'in 'kofar da mamaki kawai sai gani yayi kyauren ya bud'e, ahankali yashiga d'akin yari'ka dubawa inda ze ganta can idanunsa sukayimai tozali da ita tana kwance kan gado ta kudundune a bargo tanata makyarkyata kamar wacce aka she'kama ruwan 'kan'kara, duk zafin da akeyi a garin.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un jabeer yafad'a tare da nufar inda take kwance, zama yayi gefen gadon tare da bud'e bargon yana kallonta sannan yakai hannunsa kan wuyanta, jin wani irin zafi yayi rau ajikin nata, "subhanallah zazza6i Kike amma baki gayaminba sai ki zauna da ciwo ajiki, kitashi mutafi asibi,
: Bejira mezata fad'aba yanufi wadrope ya d'aukomata hijab, da kanshi ya taimaka mata ta sanya hijab d'in sannan suka nufi mota da sauri jabeer yabud'emata gaban mota ba musu ta zauna sannan ya zagaya yashigaazaunin driver suka d'au hanyar asibiti.
Bakin wani private Hospital suka tsaya me suna *Allah Bamu Lafiya* dake cikin garin katsina jabeer da kanshi ya taimakama Hassana tafito daga motar suka nufi cikin asibiti, suna zuwa kai tsaye aka bud'emata file sannan aka turasu gurin likita, bayan yan tambayoyi da likitan yayima Hassana itakuma tayimai bayanin duk abinda takeji, nan take likitan ya danna wata 'yar karaurawa saiga wata nurse tashigo, ta rissina gaban likitan cikin ladabi, ya nunamata Hassana "kije da ita kiyimata wannan gwaje-gwajen yafad'a yana mi'kamata wata takarda, "owk sir tafad'a tare da amsar takardar sannan takama hannun Hasaana suka nufi lab, nan aka ebi jini sannan tanunamata toilet tabata wani d'an konkoni na roba ta umarceta datayo fitsari anan, haka Hassana tayo fitsarin takawo sannan takoma kan wani benci Wanda masu jira ke zama ta kwanta ta kudundune cikin hijab d'inta dan har yanzu wani irin sanyi takeji,
Kusan minti talatin suna jiran result ganin yanda mutane ke 'kara yawa yasa jabeer matsawa kusa da Hassana yace "ko muje inkaiki gidanmu tunda kusane ni sai indawo injira sakamakon dakuma magungunan daza'a rubuta.
'Daga mashi kai kawai tayi, alamar hakan yayimata dan dama ita tamatsu dasubar wannan asibitin ganin yanda mutane suketa zuwa gashi gurin zama ma yana neman gagarar wasu itakuma ga wani irin sanyi datakeji.
Da taimalonshi suka isa gurin mota, bud'emata yayi tafara shiga sannan shima yashiga yatshi motar suka tafi, kasancewar ba nisa tsakanin asibitin da gidansu jabeer ba'a d'au wani lokaciba suka iso, bakin 'kofar gidan sukayi parking sannan suka fito, suka nufi cikin gidan Ahankali Hassana take tafiya tana biye da jebeer, yanayi yana waigenta har suka isa cikin gidan suka kwad'a sallama Umman jabeer daga d'aki ta amsa, dai-dai lokacin 'kanwarsa nusaiba tafito daga wanka ta kai dubanta garesu cike da fara'a "Lah Yaya jabeer ashe tare kuke da aunty Hussaina, jin an ambaci Hussaina yasa Umma Fitowa daga d'aki tana masu sannu da zuwa, takai dubanta ga jabeer baka cemin tare kuke.
"Eh wlh mama daga asibiti muke shine nace bari inkawota nan tad'an huta kafin agama gwaje-gwajen daza'ayi.
"Subhanallah, Umma tafad'a meyasameta? Ta tambaya tana 'karema Hassana kallo wacce ta saddar da kanta ta'ki bari su had'a ido da Umma, amma hakan behana Umma tagano wani Abu tattare da itaba, murmushi tayi me d'auke da farin ciki, sannan takama Hannun Hassana suka nufi d'aki tanata jera mata sannu.
Jabeer ne zaune gaban likita, saida likitan yayi wasu 'yan rubuce-rubuce sannan yafad'a mashi ainafin abinda ke damun Hassana, sannan yabasu shawarar hanyoyin daza'abi domin kare lafiyarta,
Jabeer ne zaune gaban likita, saida likitan yayi wasu 'yan rubuce-rubuce sannan yafad'a mashi ainafin abinda ke damun Hassana, sannan yabasu shawarar hanyoyin daza'abi domin kare lafiyarta,
Nan jabeer yayi godiya sannan ya sayi magungunan da'aka rubuta ya wuce gida.
Da sallama yashigo gidan, zaune ya iske Hassana da kwano a gabanta d'an wake ne Mamanshi tayimata shine takeci dan ba 'karamin dad'i yayimataba, dai-dai lokacin nusaiba tafito daga d'aki cikin kayan islamiyya kalar ruwan 'kasa, cikin ladabi ta isa kusa dashi "yaya harka dawo? "Eh nadawo nusaiba ina mama take ? "Tashiga nan makwabta zata kar6oma Aunty Hussaina kunun aya, tunda kashigo ni bari na wuce islamiyya dama nafara latti baniso inbar aunty ita kad'ai shiyasa nad'an jinkirta.
"To shikenan maza kitafi ga wannan kihau napep dan kiyi saurin zuwa yafad'a yana mi'komata d'ari biyu hannu biyu tasa ta kar6a sannan tayi godiya tawuce.
Kujera jabeer yajawo ya zauna gaban Hassana suna fuskantar juna "sannu ya jikin naki,? "Da sauki, tafad'a tana cire Hannunta daga kwanon d'anwaken, buta ta d'auka tanufi bakin maguji domin wanke hannunta, jabeer yabita da kallo har cikin ranshi yake matu'kar tausayamata ganin yanda tarame sai wani uban fari datakara.
Umma ce tashigo da sallama, dai-dai lokacin Hassana tagama wanke Hannunta zata mi'ke Umma tayi saurin kamata ta mi'ke tana ri'ke da ita har kan tabarma datake ta zaunar da ita, tana jeramata sannu a zuciyarta kuma fall da farin ciki ganin takusa samun jika.
Dai-dai lokacin kuma aka kira sallar la'asar saboda haka jabeer besamu damar yin wata magana da maman tashiba yad'auki buta yayi Al'wala ya wuce masallaci.
Dai-dai lokacin kuma aka kira sallar la'asar saboda haka jabeer besamu damar yin wata magana da maman tashiba yad'auki buta yayi Al'wala ya wuce masallaci.
** ** **
Zaune yake gurin wani sha'katawa, gurin ya 'kawatu da itatuwa da flower's masu kyan gani da dad'in 'kamshi, mutane ne kala-kala a gurin wasu mata da mijine da yayansu, wasu kuma saurayi da budurwa, kowa harkar gabanshi yakeyi babu Wanda yadamu da wani, shikam yakasa zaune yakasa tsaye kad'an-kad'an yaduba agogon hannunsa, dan 'karfe hud'u sukayi da ita zatazo nan suhad'u amma gashi har hud'u da rabi kome kama da ita be ganiba.
Wayarshi ya d'auko yayi 'yan danne-danne sannan yakara a kunne, wani abin takaicin cemasa akayi switch off, wani mugun takaici ya lullu6eshi jiyayi kamar ya kwala wayar da 'kasa dan haushi.
Dai-dai lokacin me napep ya sauketa, sanye take da ba'kin wando pencil da jar riga iyakar cinya, wacce ta d'ameta tafiddo duk wata sura da Allah yayimata, sai wani yala-yalan gyale kalar ba'ki datayi rolling dashi kafarta jan takalmine mai matu'kar tsini, hannunta ri'ke da waya 'kirar iPhone 7 yayinda d'ayan hannun take ri'ke da poss kalar ja, duk illahirin gurin ya buge da 'kamshin tsadadden turarenta, wani 'katon ba'kin glass ne rufe da kwayar idanunta wanda ake kira no respect, cikin takunta na yanga da 'kasaita ta iso inda yake lokacin yayi zurfi cikin tunanin rashin zuwanta besan ta iso gurinba saida taja kujera ta zauna 'kamshin turarenta ya daki hancinta sannan ya maida dubansa gareta.
"Haba zuby saboda me zaki shanyani anan aka gayaki banida aikin yine tun d'azu nake kiran wayarki gaba d'aya a kashe, cikin tsananin 6acin rai da d'aga murya yake mata magana.
Tashi tayi tsaye tare da d'age bakin glass d'inda ya rufe kwayar idanunta ta d'aga mai hannu "dakata Hafiz karfa kace zaka d'agamin murya, kasani da da yanzu ba d'aya bane, sabodame zakari'kamin shouting a kunne banison hayaniya
Hafiz sakin baki yayi yana kallon zuby yanda take gayamashi magana son ranta, wanda a da koda kud'i aka sakata bazata iya gayamai hakaba.
A zuciyarshi yace lallai dole inyi maganinki zuby, amma a zahiri sai yayi murmushi "sorry abin bekai hakaba yanzu dai zauna muyi magana ta fahimta
Komawa tayi ta zauna ta d'ora 'kafa d'aya kan d'aya tana taunar cingam irinnan gogaggin yan duniya.
"Kingane zuby abinda yasa nakiraki nace muhad'u anan kinga yanzu rabona dake kusan wata biyu kenan kuma kinriga kin sabamin da lallausan jikinki, kin shagwa6ani da shan daddad'ar zumarki 'kauracewarki gareni ba 'karamin cutar dani yakeba yakamata mukoma yanda muke da.
"Kingane zuby abinda yasa nakiraki nace muhad'u anan kinga yanzu rabona dake kusan wata biyu kenan kuma kinriga kin sabamin da lallausan jikinki, kin shagwa6ani da shan daddad'ar zumarki 'kauracewarki gareni ba 'karamin cutar dani yakeba yakamata mukoma yanda muke da.
Murmushi zuby tayi me d'auke da rainin wayo, "Hmm Hafiz aini yanzu na wuce ajinka, dan yanzu gaf nake danayi aure, kuma wanda zan aura yafika kyau kud'i wayewa, kai yafika kome wlh.
"Amma waye wannan wanda ze aureki shin besan Halinkiba, ze kwasarma kanshi bala'i "besaniba kuma baze ta6a saniba dan iya sanin da yayimin mutunniyar kirki yasanni kuma ahaka zan bayyanamai soyayyata kuma inada tabbacin ze aureni.
"Kada kaji inata baka labari ban gayama ko wayeba, ba Kowa bane face *JABEER* mijin 'kawata Hussaina wacce tarigamu gidan gaakiya.
Tana gama fad'amai tasa hannu ta d'auki wayarta da poss d'inta dake ajiye kan table d'in tare da gyara zaman glass dinta a fuska tace kaga tafiyata sai anjima ko...
Tafiya take tana karairaya Hafiz kuwa bin bayanta yayi da kallo yanda take juya mazannai, wani miyau ya had'e 'kutt sannan ya kwalamata kira "Zuby....... A yangance tajuyo ta kalleshi tana wani shu'umin murmushi, hannu yasa Aljihu ya ciro wata agogo ya d'aga mata zaki iya sheda wannan agogon da kuma ranar da kika yaddata.
Wani mummunan fad'uwar gaba taji lokacin data tuno da ranar data kashe Hussaina bayan ta dawo gida tanemi agogon tarasa.
.Dawowa tayi ahankali jikinta yayi sanyi, "Hafiz ina kasamu agogona?
.Dawowa tayi ahankali jikinta yayi sanyi, "Hafiz ina kasamu agogona?
"Murmushi Hafiz yayi me cike da samun nasara "Zuby kenan idan ke sammako kikayi wani a hanya ya kwana, kince zaki auri jabeer ko, saboda kinaso zaki aureshi shine kika raba matarshi da duniya, kina tunanin bansan ke kika kashe Hussainaba.
Kyarma Zuby tafara 'kirjinta na dukan tara-tara ta kalli jabeer, sannan ta dake ta nuna ba Alamar tsoro tattare da ita tace "of course, bazan tsaya jayayya dakaiba Nina kashe Hussaina kuma bazan ta6a danasaniba saboda Hussaina tashiga gonatane ta hanyar rabani dakai, Wanda a lokacin banida wanda nakeso bayanka.
Amma yanzu na canja akalata zuwa ga jabeer kuma nasha Al'washin saina aureshi.
Murmushi Hafiz yayi tare da mi'kewa tsaye yayi taku ahankali yazagayo bayan kujerar datake zaune yadafa bayan kujerar sannan yadu'ko saitin kanta yace
Murmushi Hafiz yayi tare da mi'kewa tsaye yayi taku ahankali yazagayo bayan kujerar datake zaune yadafa bayan kujerar sannan yadu'ko saitin kanta yace
"Karya kike Zuby nasan har yanzu kina sona, kuma inada tabbacin babu wani namiji daze maye gurbina a zuciyarki.
Kawai shawarar dazan baki shine :nasan ke mayyar kud'ice kuma nasan badan kome kikeson jabeer ba sai dan kud'insa.
Idan kinajin shawara me zai hana mu had'a kai inrufa maki asiri idan kin auri jabeer shima ki aikashi inda kika aika matarshi ki kwashe mana dukiyarsa muyi aure mucigaba da jin dad'inmu. Yana gama fad'in haka yadawo kan kujera ya zauna yana fuskantarta.
Wani shu'umin murmushi tayi tacigaba da taunar cingam d'inta sannan tayima Hafiz wani sakaran kallo "baka isaba Hafiz bakuma zeta6a yiyuba kura da shan bugu gardi da kwace kud'i.
Ai dukiyar jabeer tawace ni kad'ai tafad'a tana nuna kanta,
Murmushi Hafiz yayi sannan ya d'auki wayarshi yayi yan danne-danne saiga duk magan-ganun da zuby tayi ashe yayi recording _Of course bazan tsaya ina jayayya dakaiba nina kashe Hussaina kuma bazan ta6a danasaniba, saboda tashiga gonata_ latsa wayar yayi ya kashe sannan ya maida Aljihu, zaki iya fansar kanki da shawarar danabaki idan kuma kinyi gardama zan mi'ka wannan recording d'in ga hukuma.
Murmushi Hafiz yayi sannan ya d'auki wayarshi yayi yan danne-danne saiga duk magan-ganun da zuby tayi ashe yayi recording _Of course bazan tsaya ina jayayya dakaiba nina kashe Hussaina kuma bazan ta6a danasaniba, saboda tashiga gonata_ latsa wayar yayi ya kashe sannan ya maida Aljihu, zaki iya fansar kanki da shawarar danabaki idan kuma kinyi gardama zan mi'ka wannan recording d'in ga hukuma.
Take zuby takashi ta duri ruwa ta dad'e da sanin shu'mancin Hafiz tsaf ze kaita a hukuma kuma ya wanke kansa. "Kada ka damu na amince da shawararka amma dan Allah ka goge wannan rocording d'in, tafad'a tana kyarma kamar wacce akayima wanka da ruwan 'kan-'kara.
"Zan goge kada kidamu fatana kawai mucigaba da harka kamar yanda muka saba.
"Indan wannan ne kada kadamu muje koh.
"Indan wannan ne kada kadamu muje koh.
Owk muje kawai yafad'a, mota suka nufa gidan gaba Hafiz yabud'ema zuby tashiga sannan ya zagaya mazaunin driver suka d'au hanya.
Gidan Hafiz suka sauka ranar sun she'ke ayarsu suduka sun nunama juna sunyi missing d'in junansu.
** ** **
Sai bayan sallar isha'i jabeer yadawo lokacin ya iske Hasaana tagama sallah mama ta zubo mata tuwon masara da miyar ku6ewa ga manshanu, nan Mama ta kalleshi "zakaci tuwon ne azuboma "Eh mama ai kinsan tuwo mutuminane, mama da kanta tashiga kitchen ta zuboma jabeer tuwon
Bayan sun kammala ne sukayi haramar tafiya gida, mama ta kalli jabeer "shin ka kar6o sakamakon kuwa a asibitin naji har zaku tafi bakayiman bayanin komeba
"Eh mama na kar6o wallahi ba wani abu bane ke damunta (Malaria) zazza6in cizon sauro, amma ga magun-guna na siyo likitan yace inshaAllah indai tanasha zata samu sauki.
Fara'ar mama tad'an ragu dan ita a tunanunta cikine da Hassana, amma saitaji sa6anin haka "to Allah sauwa'ke Allah maidaku gida lafiya, nan sukayi bankwana suka d'au hanyar gida.
Suna isa sukayi horn megadi yabud'emasu get jabeer nayin parking Hassana tafito da sauri tanufi d'akinta tarufe da key kamar yanda tasaba tayi kwanciyarta, tunanin Hussaina yafad'o mata a rai batasan lokacin data fashe da kukaba,
Shikenan ni yanzu haka zancigaba da zama, gidan yar'uwata ba gidan mijinaba. Ya Allah ka kawomin mafita ina cikin tsaka me wuya.
.
Washe gari da misalin 'karfe goma na safe jabeer ne zaune office d'insa da wasu fayiloli yanata faman wasu rubuce-rubuce, nocking d'in 'kofar akayi ahankali, d'agowa yayi ya kalli 'kofar sannan ya maida hankalinsa ga aikinsa, kara nocking akayi karo na biyu, aje biron hannunsa yayi sannan yabada izinin shigowa.
.
Washe gari da misalin 'karfe goma na safe jabeer ne zaune office d'insa da wasu fayiloli yanata faman wasu rubuce-rubuce, nocking d'in 'kofar akayi ahankali, d'agowa yayi ya kalli 'kofar sannan ya maida hankalinsa ga aikinsa, kara nocking akayi karo na biyu, aje biron hannunsa yayi sannan yabada izinin shigowa.
Da sallama tashigo office d'in sanye take da riga da siket na less, wad'anda suka kame mata jiki, sai wani madaidaicin gyale data yafa har saman kai dan kan nata bako d'an kwali, 'kafarta sanye cikin plate shoe,
Kallonta jabeer yayi daga sama har 'kasa yace "zuby kece tafe da wannan lokacin,
"Nice tafad'a tana murmushi.
"Bissmillah zauna mana yafad'a yana nunamata kujera.
"Nice tafad'a tana murmushi.
"Bissmillah zauna mana yafad'a yana nunamata kujera.
Ba musu ta zauna tana wani sakar mashi wani shu'umin murmushi, bayan sun gaisa tace "dama zowa nayi inyima gaisuwa dan lokacin da'akayi rasuwar bani gari, gaskiya munyi babban rashi tafad'a tana matsar kwallan munafinci, Hussaina 'kawatace banida tamkarta nayi babban rashi.
A mamakance jabeer yake kallonta, kindai manta Ai Hassanace tamutu ba Hussaina ba.
Wani mummunan fad'uwar gaba zuby tayi lokacin data tuno da shawarar databa Hussaina na cewa Hassana ta zauna maimakinta.
Inkau hakane ba shakka Hassana bata gayama jabeer ba itabace Hussaina idan kuwa hakane akwai aiki babba agabanta.
Wani mummunan fad'uwar gaba zuby tayi lokacin data tuno da shawarar databa Hussaina na cewa Hassana ta zauna maimakinta.
Inkau hakane ba shakka Hassana bata gayama jabeer ba itabace Hussaina idan kuwa hakane akwai aiki babba agabanta.
Jabeer ya kalleta "naji kinyi shiru me kike tunani, firgigi tayi kamar wacce tafarka daga bacci, ah bakome, nizan wuce Allah bada ha'kuri. "Ameen kawai jabeer yace sannan yacigaba da aikinsa.
Jiki ba lakka Tabar office d'in, daga nan gida kawai tawuce zuciyarta cike da tunani barkatai.
Zuby a d'akinta sai safa da marwa takeyi, tana sa'ke-sa'ke a zuciyarta "tabbas Hafiz shine babban matsalata idanko hakane dole in d'au mataki kanshi.
Wani mugun murmushi tayi lokacin wanda koni zee bansan ma'anar yinsaba.
Wayarta ta d'auko ta danno sunan Hafiz bugu d'aya ya d'auka "hellow zuby na yadai, akwai labari ne?
Wayarta ta d'auko ta danno sunan Hafiz bugu d'aya ya d'auka "hellow zuby na yadai, akwai labari ne?
"Sosaima kuwa akwai labari me dad'in sauraro, inaso muhad'u a park dinda muka saba had'uwa.
"Owk ba damuwa kamar 'karfe nawa?
"Yanzu-yanzu kome kakeyi ka ajiye kataho dan abari ya huce shike kawo rabon wani.
"Owk ganinan zuwa.
"Owk ba damuwa kamar 'karfe nawa?
"Yanzu-yanzu kome kakeyi ka ajiye kataho dan abari ya huce shike kawo rabon wani.
"Owk ganinan zuwa.
Saurin fad'awa wanka zuby tayi ta she'ka wanka, tana fitowa batare da 6ata lokaciba lotion kawai ta murzama jikinta sannan tasaka irin 'kananun kayan data saba sakawa, tana fitowa bakin titi ta tsaida me napep tagayamai inda ze kaita, cikin mintinan dabasu wuce talatinba ta iso gurin ta sallami me napep, wayarta ta fiddo da niyyar takira Hafiz ta tambayeshi ya isone hangoshi tayi jingine jikin motarsa yana sakar mata murmushi, itama murmushin tayi sannan tanufi gurin wasu kujeru kai tsaye ta zauna, shima Hafiz nan yadawo ya zauna kusa da ita a 'kagare dayaji labarin datazo mai dashi.
Kusan minti biyar da zamansu zuby batayi maganaba, a 'kagauce Hafiz ya kalleta inajinki zuby, na bud'e kunne ina sauraron jin daddad'an labari kinyimin shiru.
Kallonshi tayi daga sama har 'kasa "owk kada ka damu nad'an gajine inaso in huta tukun, bari naje can na kar6o mana drink's mud'ansha konaji sanyi-sanyi,
"A'a kibari in anso mana Hafiz yafad'a yana mi'kewa tsaye,
"A'a kabarshi kawai zan amso saurin yin gaba tayi dan kada Hafiz d'in yacemata a'a.
"A'a kibari in anso mana Hafiz yafad'a yana mi'kewa tsaye,
"A'a kabarshi kawai zan amso saurin yin gaba tayi dan kada Hafiz d'in yacemata a'a.
Haka ta isa gurin siyar da drink's kwalbar lacasera biyu ta kar6o duk idanun Hafiz kanta dan tsakanin gurin dasuke da gurin siyan drink's d'in ba nisa.
Gurin dawowa maimakin tabiyo hanya street saita kauce ta inda be ganinta, tad'an jima sannan tayo zagaye tadawo da lemun guda biyu hannunta.
Zama tayi sannan tabud'e kwalba guda tami'kama Hafiz, itakuma tabud'e guda tanasha suna labari nan takeba Hafiz labarin cewa taje office d'in jabeer kuma ya amince da aurenta, wani dad'i yaratsa zuciyar Hafiz, dai-dai lokacin kuma yagama shan lemun lacasera dake hannunsa ya jefar da robar.
Mi'kewa zuby tayi tsaye tare da kecewa da wata irin dariya tace "anzo gurin kasani Hafiz kwananka ya'kare yau zakayi bankwana da duniya, zuge Jakarta tayi tafito da wata 'yar'karamar kwalba tace "gaga wannan shine ake kira da silent killer, kuma ahine na zubama a lemun dakasha, saboda haka zaka iya zuwa gida karo'ki Umma yafiya kafin ka margaya barzahu, dan baya kisa farat d'aya, ni kaga tafiyata.
Tana gama fad'amashi tami'ke takama hanya tayi tafiyarta.
Hafiz kuwa duk illahirin jikinsa kyarma yake, yasan shu'umancin zuby kome tafad'a zata iya aikatawa, da sauri ya suri makullan motarsa yabar gurin.
'
Hafiz kuwa duk illahirin jikinsa kyarma yake, yasan shu'umancin zuby kome tafad'a zata iya aikatawa, da sauri ya suri makullan motarsa yabar gurin.
'
Cikin tsananin rud'ani da tashin hankali Hafiz ya isa gida, falon mahaifiyarsa ya zube yanata mai-maita istigifari, a zuciyarsa yana cewa "wannan bala'i dame yayi kama, gashi yanzu son zuciya yajamin na jefa kaina ga halaka, 'kanwarsa ce tashigo da sallama ganin yayan nata kwance da alama yayi nisa a tunani ga hawaye kwance a idanunsa dan alamu sun nuna besan da shigowar wani mahalu'ki a d'akinba.
Saida ta matso gaf dashi tadafa kafad'arshi "Yaya lafiya kuwa na ganka haka da Alama kukama kakeyi, saurin tashi yayi ya goge sauran hawayen dasuka ma'kale a idonshi ya 'ka'karo murmushin 'karfin hali yace *Bakome Zee kada ki damu kaina ne kemin ciwo.
"Kuma shine ka zauna a gida, yakamata kaje asibiti, "to 'kanwata zanje jeki shirya saimu tafi tare dan kan yana matsamin sosai bazan iya driving ba, "owk to ba damuwa bari na sanarma Hajiya kafin mutafi, saurin ri'ko hannunta Hafiz yayi kada kije tana bacci kuma kinsan doctor yahana atasheta idan tana bacci, muje kawai idan mundawo mun gaya mata.
A harabar gidan suka bud'e mota suka shiga Zee ke driving Hafiz kuma na zaune gefenta lokacin yaji cikinsa na juyamasa, ahankali ciwon ke gaba, zee kuwa hankalinta ya matu'kar tashi ganin yanda yayan nata ke magowa gashi har wani kumfa yafara fitowa a bakinsa, wani irin mahaukacin tu'ki tari'kayi dan ikon Allah kawai yakaisu asibitin, suna Isa aka kar6eshi Emergency aka nufa dashi, nan lokitoci suka rufa akanshi, yayinda zee ketai kai komo a bakin 'kofar d'akin da aka shiga dashi tanata sharar hawaye dan ganitake kamar za'a fito acemata Hafiz ya mutu dan yanda aka shiga dashi ba alamar rai tattare dashi.
A harabar gidan suka bud'e mota suka shiga Zee ke driving Hafiz kuma na zaune gefenta lokacin yaji cikinsa na juyamasa, ahankali ciwon ke gaba, zee kuwa hankalinta ya matu'kar tashi ganin yanda yayan nata ke magowa gashi har wani kumfa yafara fitowa a bakinsa, wani irin mahaukacin tu'ki tari'kayi dan ikon Allah kawai yakaisu asibitin, suna Isa aka kar6eshi Emergency aka nufa dashi, nan lokitoci suka rufa akanshi, yayinda zee ketai kai komo a bakin 'kofar d'akin da aka shiga dashi tanata sharar hawaye dan ganitake kamar za'a fito acemata Hafiz ya mutu dan yanda aka shiga dashi ba alamar rai tattare dashi.
*washe Gari*
Da misalin 'karfe goma na safe, Zuby na kwance kan gadonta da waya hannunta tana chat a wani tambad'add'en group data bud'e maza da matane aciki ba abinda ake a group d'in sai maganganun batsa da tura blue film da sauransu, tana chat din ta Lula duniya tanayi tana matse 'kafafu dan tsabar jaraba, da kuma sauraron voice message d'inda wani tsagera a group d'in yaturo wanda shima Admin ne a group d'in.
Da misalin 'karfe goma na safe, Zuby na kwance kan gadonta da waya hannunta tana chat a wani tambad'add'en group data bud'e maza da matane aciki ba abinda ake a group d'in sai maganganun batsa da tura blue film da sauransu, tana chat din ta Lula duniya tanayi tana matse 'kafafu dan tsabar jaraba, da kuma sauraron voice message d'inda wani tsagera a group d'in yaturo wanda shima Admin ne a group d'in.
ganin wayarta ta tsaya cak tasan kirane ze shigo, tun kafin kiran yashigo tafara buga uban tsaki dan ganin za'a katse mata jin dad'i, amma da mamakinta sai taga number Hafiz a firgice tami'ke tsaye, sai lokacin tatunafa tasaka mashi guba a lemu kuma yasha tasan ba tantama bekwana da raiba, to amma kuma taya aka kirata da number shi.
Tana cikin wannan tunanin har kiran ya tsinke, batare da 6ata lokaciba aka kuma kira karo ba biyu, jiki a sanyaye ta danna ok sannan takara a kunnenta.
"Hello" Zuby tafad'a cikin muryar fargaba.
A d'aya 6angaren Zee tafashe da kuka tare da cewa "Zuby koh?
Zuby ta amsa da "Eh nice amma wacece ke?
Zee ta'kara fashewa da kuka, sannan tace "ni 'Kanwar Hafiz ce naga kece mutum ta 'karshe da kukayi waya dashi jiya, cuma naga call log d'insa duka sunanki yafi yawa da Alama akwai sha'kuwa tsakaninku shine nakiraki in gayamaki jiya da dare Allah yayima Hafiz rasuwa.
A d'aya 6angaren Zee tafashe da kuka tare da cewa "Zuby koh?
Zuby ta amsa da "Eh nice amma wacece ke?
Zee ta'kara fashewa da kuka, sannan tace "ni 'Kanwar Hafiz ce naga kece mutum ta 'karshe da kukayi waya dashi jiya, cuma naga call log d'insa duka sunanki yafi yawa da Alama akwai sha'kuwa tsakaninku shine nakiraki in gayamaki jiya da dare Allah yayima Hafiz rasuwa.
"What Zuby tafad'a kamar tana cikin irin firgicinnan, sannan tadoka uban salati "Allah Sarki Allah ji'kan Hafiz,
"Ameen" Zee ta amsa kafin ta tsinke kiran.
"Ameen" Zee ta amsa kafin ta tsinke kiran.
Zuby kuwa tana kashe wayar rawa tafara takawa tana rera wa'kar ado gwanja inda yake cewa _Me nemam jini yaje kwata, niko bani zuwa bikin daba mata, mata.....mata....._ ta'karashe wa'kar tana nuna kanta "saini zuby duk wanda yaja dani yajishi kushewa, wata shegiyar dariya tayi sannan tafad'a toilet ta she'ka wanka.
Tana fitowa ta tsaya gaban mirror ta watsa wani matsiyacin make up a fuskarta na marassa mutunci, wasu watsatatsin kaya tasaka dan basuda maraba da shigar arna.
Kai tsaye gidan jabeer tayima tsinke, tana isa me gadi yayimata sannu da zuwa ta wuce dan yasanta kwanaki tana yawan zuwa gidan.
Hassana kuwa ganin tad'anji 'karfin jikinta yasa yau tashiga kitchen tagama girki tana d'aukowa daga kitchen tana jerawa kan dining, tagama jera kome sanan ta tafi da niyyar takoma d'akinta dan tasan jabeer yana gab da dawowa kuma bataso yadawo ya isketa a falo.
Ido hud'u sukayi da zuby wacce ko alama bataji lokacin data shigoba, ba 'karamin fad'uwar gaba Hassana tajiba dan ganin zuby tsaye fuskarta ba fara'a ko kad'an.
0 comments:
Post a Comment