Kaman wacce bata san da hallittu a parlorn ba haka ta nufi stirs zata haura sama dan ko son ganin fuskokin Laila da Aziza batayi, Amma tabita da Kallo yayinda su Laila ma ita suke kallo.
"Nadiya!" Muryan Amma ya dakatar da ita, juyowa tayi da kyar ba tareda ta furta koda kalma guda ba,
"Baki ganin mutane bakisan ki gaishesu ba and kin shigo without even saying salam.
"Nadiya ta dan yatsina fuska kafin tace" Oh come on Amma, nayi sallama fah.... "Amma ta kalleta cike da takaici kafin tace" toh ina kika baro Deejahn, " Daddy yace sun taho gida tare da yaIrfaan, so I guess probably by now sun iso, though banga motarsa a waje ba. Daidai lokacin data watsa wa Laila da Aziza wani muguwar harara, tsaki tayi kafin ta furta "what a fuck"
"Amma kam cike da kunyan abinda Nadiya tayi ta dubi su Laila tace kuyi hakuri pls kunsan ba anan ta tashi ba ta saba da _al'adun wasu_ sam bata saba da al'adunmu ba.
"Dariyan ya'ke Laila tayi, Gamida mikewa tana fadin "ai ma tafiya zamuyi Amma, Amma tace a haba da wuri haka, eh wllhi Amma dama mukace bari muzo mu gaisheki, cewan Laila... Aziza kuwa bata da buri da ya wuce ta zama kawa da Nadiya,
"Har 'kofa Amma ta rakasu kafin ta dawo ta nufi sama dan yin fa'dawa Nadiya....
"Tafiya suke kan yi har suka fice daga cikin gari, jikinta duk ya mace sabida tsaban yunwa da takeji, wani wawan holdup suka ha'du dashi tun daga cijin gari, shi kansa Irfaan saida yaji haushin kansa da ya sani da bai fara ba, but ba yanda ya iya, Ahidjo bashida kowa sai shi.
"Da kyar suka samu suka rabu da holdup din nan, ashe wata tankace ta lalace bisa titi. Ai kuwa kaman jira yake, nan ya dinga falfala gudu, Deejah kuwa gab tace da fashewa sabida tsaban haushi da takaici....
"Su Laila suna dawowa gida da zancen suka soma wa Hajiya Karima. "Hajiya kinsan akwai aiki jazur a gabanmu, wnn 'yar tasa ko ka'dan bata da ta ido, daga ganinta zatayi rashin mutunci, cewar Laila." Hajiya Karima ta sauke ajiyam zuciya kana tace" ni nasan ta yanda zan bulla masu, tinda dai kin samu kar'buwa wajen shi Nazif din da uwarsa 'ya'yansa ai me sau'ki ne. Laila tayi murmushin jin da'di tace shiyasa nake sonki Hajiyata. Juyawa tayi ta kalli Alhj Ma'aruf dake kwance bisa gado yana so yayi magana babu hali, duk wnn tattaunawan da suke a gabansa suke, yanayin maganar nasa kaman na bebaye haka yakeyi baka gane komai baka fahimtar komai.
"Laila ta kwashe da dariya tana kwaikwayan yanda Alhj Ma'aruf ke magana, Hajiya ta murmusa kafin tace" kina kwaikwayan gwalamniyan wnn azabebben tsohon ne, me shegen taurin ran tsiya, da mutuwa kayi da ya fiye maka wnn rayuwan azaban, magani dai bazan fasa baka ba, amma na sani kalamai da zaka rin'ka ji masu zafi su ka'dai sun isa su 'karasaka har lahira. "Laila ta kuma she'kewa da dariya kana tace Kai Hajjaju na baki da dama. Haka sukamci gaba da hiransu, Alhj Ma'aruf kuwa ji yake kaman ya yun'kura ya tashi ya hana Engr auren Laila, amma bashida iko, yayi kudirin cikin ransa ba zai daina addu'a wa Engr ba.
"Tin daga parlor yake ranga'da mata kira cike da farin ciki, Mami! Mami!! Mami na!!!, Ruqayya ce ta fito daga 'dakinta wanda yake a cikin parlorn kana tace" Yaya sannu da dawowa, murmushi ya sakar wa Ruqayya kafin yace yauwa sanu lil sis, Mami fah,
"Inaga tana sallah dan 'dazu na barta a parlor, gyada kansa yayi kafin ya ajiye takardun hanunsa bisa madaidaicin center table din dake parlorn.
"Yaya na kawo maka abinci ne, Ruqayya ta bida,
"Kai lil sis da kin kyauta kuwa dan na kwaso yunwa sosai, cewan Sadiq. Da sauri Ruqayya ta wuce kitchen dan hada wa Sadiq abincinsa.
"Mami ce ta shigo parlorn sanye da hijabi da alamun sallah da ida, Sadiq an dawo, ta fadi sanda take zama bisa sofa... mikewa yayi daga kishingi'dan da yayi yana murmushi yace " eh mami na dawo, nan suka gaisa mami tace Allah sa dai an dace.
"Gyara zamansa yayi sosai kafin yace" mami Allah ya amshi addu'an mu, daga ziwana aka bani mu'kami mai tsoka, Mami ta daga hannu sama tama Allah godiya, kai Alhamdulillah masha Allah, Allah na gode maka, Allah ya wuce maka gaba a wajen aikin ka, inama yau babanka na nan da yafi kowa farin ciki, matsowa Sadiq yayi kusa da mami ya ri'ke hannunta yana girgiza mata kai alamun kar tayi kuka... Daidai lokacin da Ruqayya ta ajiye masa tren abinci a gabansa...." 'Karan da suka jiyo daga 'dakin Dada ne yasa su rugawa duka a guje suka nufi 'dakin,
"Zaune suka sameta ta ta'kure jikin gado tana rungume da 'yar tsananta da tun tsintarta da sukayi da 'yar tsanar suka tsinceta. Da'da rungume 'yar tsanar tayi sanda mami ke 'ko'karin matsowa kusa da ita ta soma fa'din" Kar ku zo nan kar kuzo zasu 'kwace mun 'diyata, ta da'da matse ta cikin jikinta nan ta kwanta rungume da 'yar tsanar ta soma fa'din" sleep sleep my baby, my baby da haka har bacci ya 'dauke ta...." Su mami Ruqayya da Sadiq zukatansu cike da tausayin Dada, Allah sarki jinyar hauka ba 'karamin jarabawa bace, Ruqayya ta 'karasa ta gyara mata kwanciyarta dan jin sanyi ya sau'ka a garin alamun ruwa na zuwa. "Mamie ta dubi Sadiq tace" Sadiq kana ganin bazamu canza mata asibiti ba,
"Sadiq ya jinjina kai yace ba laifi idan muka canza amma ni a ganina mu dage mata da na islama, Mamie tace hakane Allah ubangiji ya bata lafia, Allah sarki ko shekaru nawa tayi cikin jiyar hauka sai Allah.
"A parlor Sadiq ya ha'du da Ruqayya, murmushin da ita ka'dai tasan fassaransa ya sakar mata, sunne kai tayi tana mai mayar masa da murmushin itama, takardun saman center table ya nuna mata ba tareda yace komai ba, kallon takardun take taga anyi approving masa aiki, murna sosai tayi ha'di da jero , asa addu'o'i.
"Wnn kyakkyawan 'dabi'a na Ruqayya na burgesa sosai, hakan nema yake ji bazai iya rayuwa babu ita ba, shi ko ka'dan kyau bai damesa ba, kyawawan 'dabi'u sunfi burgesa.
"Kallonta yake yana jin tsantsan sonta har cikin ransa.
"Sosai hankalin Irfaan ya tashi ganin motan ta shiga danger, besan me ya sami motarsa ba shan mai take sosai kwana biyun nan, a hankali ya furta ya salam, dole ya nemi hefen titi yayi parking.
"Deejah da hawaye suka soma zarya a fuskanta juyowa tayi tana masa mugun kallo kafin tace "Ina ne nan?
"Irfan da ransa ya gama jagilewa gaba 'daya ko kulata beyi ba ya ciro wayansa "unfortunately babu chargi, " Shit" ya fadi gamida buga starry da hannunsa....." Ruwan sama ne ya soma zubowa tamkar da bakin 'kwarya....
👸🏻Queen Samy😍💄💋.........
[8/19, 06:25] Umar Dalha: 🌓🌓🌔🌔 *Mallakin waye*
19
"Kifa kanta tayi kan cinyarta kuka na shirin kufce mata, Irfan ya 'dan kalleta tausayinta ya kamasa, ji yake dama gida ya soma kaita duk da haka bai faru ba, so yake ya lallasheta but besan ta yaya zai soma ba.
"Dekewa ya danyi da kyar ya iya furta" muga wayarki. "Ba tareda ta dago ba tace ai ban fito da waya ba,
"Tsaki ya kumayi a hankali, daidai lokacin da kuka ya kufcewa Deejah, ko kadan Irfaan baison jin kukan nata, it hurts him sosai, cikin 'kulewa yace" will you shut your trap! Kin cika wa mutane kunne. Ko saurarensa bata yi ba balle ta tanka sa,
"Kinsan Allah idan bakiyi shiru ba zaki fice mun daga mota, kaman bada ita yake ba haka tayi, tsaki yayi gamida bude kofar motan ya fice duk da ruwan da ake tsulawa, ya zagayo mazaunin Deejah. To her greatest surprised bu'de marfin motan Irfaan yayi ya fincikota waje yace" idan kin gama kuka let me know, daga haka ya zagaya ya shige cikin motarsaw.
"Banda tsanar Irfan babu abunda Deejah keji, lallai ma yaron nan sai ta koya masa hankali ta yanda gaba ko hanya bazai ha'da da ita ba.
"Kallonta yake ta miro ta takure cikin hijabinta ga ruwa na lugude a kanta, runtse idonsa yayi bazai iya ganinta a haka ba,Oh Shit shit! Ya fadi yana mai dukan starry da hannunsa. Ganin Deejah ta soma tafiya yasa Irfan saurin bude motan yana fadin" My goodness ina kuma zataje, gabanta yasha yana mata mugun kallo yace ina zaki." Zuciyanta na tafarfasa take fadin" wai miye ruwanka dani, me nayi maka da tsanani, idan akan so called project dinka ne, na baka hakuri, let me be pls ka fita harkata pls. Bai saurareta ba ya fizgo hanunta ya bude mota ya jefata ciki.
"Kallonta yake yanda take rawan dari duk sai ta basa tausayi, kauda kansa gefe yayi bai kuma cemata komai ba, dukansu biyu da abunda suke sakawa a zukatansu. Har wajajen karfe shida na yamma kafin ruwan ya tsagaita, da sauri Irfan ya fito ya shiga sawa motoci hannu alamun su tsaya amma babu wanda ya kulasa, sosai hankalinsa ya tashi ga duhu ya soma yi....
"A can gida kuwa hankulansu ya kai kololuwan tashi izuwa yanzu, wayan Irfan baya shiga ga wayan Deejah a gida, Nilam kuwa sai kuka take a kaita Deejah, gaba dayansu hankalinsu ya tashi, Engr kusan wuni yayi a station babu labarin Irfan da Deejah, abu kaman wasa har dare yayi babu su Irfaan.
"Crackers da bottle water dake a back seat din motarsa ya dauko ya mikawa Deejah, babu musu tasa hannu ta karba nan ta dinga rusawa dan kuwa bakin yunwa ne ke azalzalanta, sosai Irfan ya tausaya mata ganin yanda take hadiyan crackers din nan.
"Bayan ta gama ci ne taga yana folding hannun rigarsa, kaman bazata masa magana ba sai kuma tace" me zakayi, ba tareda ya kalleta ba yace zan matsar da motan ne is dangerous barinta nan gefen titi. Fitowa Deejah tayi tasa hannu zata tayasa, ba tareda ya kalleta ba yake murmushi kafin yace" wayasaka ki, " kallon yanda yake murmushi mai class Deejah keyi kafin tace" kawai zanyi ne, toh ni bana son taimakon Irfan yace. " yatsina fuska tayi itama kafin tace" toh ai dama ba tayaka zanyi ba kawai nayi ra'yi ne. Bai kulata ba ya shiga matsar da motan har ta sauka gefen titi, ga wani sabon hadari dake haduwa.
"Bakin titi Irfan ya kuma komawa yana waving wa motoci, cikin sa'a mota daya ta tsaya, da sauri Deejah ta fito daga motan ta karaso wajen Irfan.
"Haka kawai Irfaan yaji bai yarda da mutanen da suka tsaya ba, motan gaba daya maza ne snn dukansu gabza gabza ne...." Deejah zata karasa jikin motan da murnanta tana fadin" Alhamdulillah at last mun samu taimako....." Irfan ne yayi saurin riko hannunta yana ja da baya... daidai lokacin da mutanen nan suka cimmasu.
"lay down! Lay down or I'll shoot, abinda mutanen suke fadi knn. Da sauri Irfan ya 'kan 'kame hannun Deejah yace muyi yanda suka ce, hakan kuwa sukayi. Searching motar Irfaan suka soma yi wasu kuma suka karaso suna fadin" ina cell phones dinku, da sauri Irfaan ya ciro ya mika masu, aljihunsa suka soma searching suka ciro dan canjin kudin dake jikinsa, wallet dinsa suka shiga dubawa sukayi filla filla dashi suka watsa masa ID dinsa da dangin su Atm card dinsa. Cikin motar kuwa sun sami kudi kusan 20k.
"Tsaki Ogan yayi yace" kai wani irin matsiyaci ne, kana tafiya da luxurious car irin wnn snn a samu just 20k a safe din motarka, you must be stupid, zakayi tafiya bazaka ajiye mana namu ba. Irfan bai ce komai ba har lokacin suna kwance a kasa, dayan yace Oga ga matarsa nan ai ita bazamu rasa yankunne na gold a kunnenta ba,
"Oga yace good badguy. KE! ya daka wa Deejah tsawa, dama kadan ya rage bata saki fitsari ba dan tsoro, ina wayarki, da sauri irfan yace bata taho dashi ba, dayan ya buga masa bakin bindiga a keya yace kai aka tambaya shut up.
"Runtse idonta tayi baki na bari tace wllhi banida waya a hida na barta. Fizge hijabib jikinta badguy yayi nan fa jikinta ya bayyana gashi dama ruwa ya jikata. Murmushi suka soma ganin yanayin jikin Deejah gashi kayan barci ne dama a jikinta.
"Oga ne ya matso yace" a baby zaki famshi kanki da jikinki.... bai gama rufe baki ba Irfaan ya mike a zuciye.... yana masu mugun kallo yace" don't you dear mess with my wife, daku ta'bta gwara ku kasheni..... " dariya suka kwashe dashi, suna kallon Irfaan da fuskansa ta koma jazur sabida bakin ciki.
"Oga ya dafa kafadun Irfan yace" relax lover boy, matarka tana da sura me kyau wanda duk lafiyayyen namiji idan ya gani sai yaji sha'awarta, yanzu dai ka za'ba, ko mubaka fuel ka zuba amotarka mu dana matarka, ko mu bar maka matarka mu tafi da ride dinka mu barku a nan in danger.
"Key din motarsa ya ciro ya jefa masu ya fizge hijabin Deejah daga hannun badguy ya rufawa Deejah dake kankanme da jikinta a gefe. Sunaji suna gani am rubbers din nan suka daura igiya wa motar Irfan suka bar wajen.
"Kuka take kanyi a hankali maras sauti, sosai ta basa tausayi, cire suite din jikinsa yayi ya rufa mata, hannunta ya rike suka karasa wajen wani checkpoint dan bukkan securities suka shige, ya dan kalleta yace ki zauna a nan barin fita ko zamu samu wasu, da sauri ta riko hanunsa tana girgiza kai kar ka kuma taro mana 'barayi.
"Murmushi ya dan sakar mata kafin yace karki damu na gari basa 'karewa....
👸🏻Queen Samy😍💄💋......
[8/19, 06:25] Umar Dalha: 🌖🌖🌗🌗 *Mallakin waye*
20
"Irfan yafi minti shabiyar na tsaye na waving wa motoci but babu motan da tayi attempting tsayuwa, zafi yaji hannunsa na masa aiki yana dubawa yaga ashe yankewa yayi, wajen yayi jazur ya tara jini, tunda uwarsa ta haifesa bai ta'ba shan wahala irin ta yau ba, dafe kansa ya 'danyi yana karanto iyakan addu'an da sukazo bakin sa. Karshe dole ya koma yanda ya baro Deejah.
"Zaune ya sameta ta ta'kure kan wani itace har lokacin rawan sanyi take tana faman kuka, ko ka'dan Irfan bai son jin kukan nata, a hankali yayi gajeren tsaki ya furta" what a fuck! Duk ransa ya gama jagulewa, a harzu'ke ya juye yana mata mugun kallo yace" Ke dan Allah kiyimin shiru haka nan.
"Harara Deejah ta galla mai kafin tace" this is all your fault, mugu kawai duk ba kai ka jawo ba,..... shiru tayi sanda ya taso a harzu'ke yayo kanta, mugun kallo ya watsa mata kafin yace" idan da baki 'bata min project dina kika sani bada ha'kuri the worse abinda nafi tsana ba da baki zo nan. Kuma kika dameni da kuka kiyi waje coz this is my palace.
"Harara Deejah ta galla masa gamida kifa kanta bisa cinyoyinta, tunanin Nilam take kan yi 'kilama kuka take kanyi yanzu haka, Allah sarki my little Nilam ta furta a hankali.
"Wasa wasa har wajajen karfe tara, Kallon Irfan take kanyi yana sallah a dan bakin bukkan, fratan 'kafarsa take kallo dogaye dasu farare sol, kai Allah yayi hallita a wajen nan, kana gani zaka san 'dan hutun gaske ne, gashi yau jarabawan waha ta sau'ko masa. Har ya sallame Sallahn sa kafin Deejah ta dena kallonsa.
"Cikinta ne ya fara mata azaban ciwo, ta sani period dinta ne, innalillahi itakam ta shiga uku yau yaya zatayi da wnn rayuwan azaban.....
"Engr sai kai komo yake a parlorn da suka hallara gaba daya ahalin gidan, waya ne a hannunsa sai faman dialing lamabar Irfan yake but baya shiga, wayan colleagues 'dinsu na company ya shiga kira but babu wanda yaji dutiyan Irfan, masu kuka sunayi masu ban hakuri sunayi, gashi Irfan bashi da wani ta'kamemmen aboki a nan balle su kirasa, hankulansu ya kai koluluwa wajen tashi.
"Ammah Irfan bashida hankali ko ka'dan, yanzu idan ya salwantar da rayuwan 'yar mutane yaya zamuyi, could you imagine wai kan ta bata masa project shine ya dauke ya kaita har office tayi defending, tun safe nace ya dawi da ita gida ban san ina ya kaita ba gashi ya kashe wayansa, duk yanda yaje zaizo ya sameni ne a gidan nan..... Ire iren fa'dan da Engr kekanyi kenan.
"Nazif ya isa haka ka daina fa'din maganganu haka, bamu san wani hali suke ciki ba, nasan Irfan bazai abunda zai cutar da ita ba, mudai muyi addu'an Allah bayyana su......
"Nadiya kuwa cike da mamaki take kallon dad din nata, zuciyanta na raya mata wani al'amari daban...
9:32pm
"Mamie gobe insha Allah zanje Garko na kar'bo magani wa Dada, Sadiq ya fa'di sanda yake jefa lipton cikin mug, Mamie ta jinjina kai kana tace amma motar naka zaije kuwa naji kaci ka buga ta,
"Gya'da mata kai Sadiq yayi yace zataje Mamie bamba ne kawai ya dan bugu, Toh Allah ya kaimu ya sa kuma a dace, Mamie ta fadi sanda Ruqayya ta shigo parlorn. Sannu yaya Ruqayya ce. Murmushi ya sakar mata me cike da fassarori kadin yace yauwa sannu lil sis ya shirye shiryen fara jami'a. Murmushi tayi ta dan sunne kanta kana tace ana kai yaya. Toh Allah ya taimaka Sadiq yace. "Ameen suka amsa gaba dayan su.
"Wani takarda Ruqayya ta mika wa Mamie kafin tace" Mamie dama dazu mutanen nan suka kawo maki daga *Nile University* Da sauri Mamie ta kar'ba tana dubawa, murmushi ta soma tana fa'din alhamdulillahi, ku gani sunyi min approving zan fara girka abinci a Cafeteria din Nile University. Gaba daya farin cikinsu ya kasa 'boyiwa, Allah sarki haka Allah kanyi lamarinsa, lokaci guda sai kaga 'kofan samu na bu'de maka. Ga Sadiq ya samu aiki a M&M Builders ga Mamie ta samu sana'a Babban University a Nigeria kaman Nile University.....
"Gani yayi ta takure tana faman cije le'be, ta'be baki ya 'danyi kafin yace " Ke meke damunki. Ba tare da ta kallesa ba tace cikina ke ciwo. Cikin ko in kula yace ciwonku na mata I guess... Kallon mamaki ta bisa dashi yaya akayi ya gane, girgiza kai tayi fuska a tamke tace ni bance ba.
"Ai dama bance kince ba, ya fa'di sanda ya mike ya saka hannu a aljihun wandansa yaji alamun abu, da sauri ya ciro yana kalla, Shortbread biscuits ne guda biyu, baisan sanda murmushi ya kifce masa ba, Allah sarki, Allah maso bayinsa bacin haka, baisan wani dalili bane zaisa sa saka shortbread cikin aljihunsa ba, quiye alright ya sani yana son shortbread shine best biscuit dinsa amma me zai kawo shi cikin aljihun wandonsa, wata zuciya tace wnn shine taimakon Allah, hamdala yayi kafin ya bude biscuit din, daya ya dauka ya mikawa Deejah daya, kasa kar'ba tayi sai juyi take, nan fah Irfan yaga abun nata da gaske ne, nan hankalinsa ya tashi sosai, zama yayi gefenta yana mata sannu, duk ya rasa wanne zaiyi, wani goran faro ya hango can gefe, da sauri ya dauko yaje waje yanda ruwa ke tsiyaya da shike har yanzu ana dan yayyafi, wanke goran yayai kana ya taro ruwa a ciki.
"Gefenta ya zauna yace" tashi kisha ruwa, girgiza masa kai tayi alamun a'a, ya 'danyi shiru yana binta da kallo, bai kuma cewa komai ba ya koma gefe ya rafka uban tagumi, lallai babu nawan da yafi karfin jarabta daga ubangiji, yau shi Irfan shine mota abinci ruwan sha wajen barci duk suka fi karfinsa a 'dan lokaci 'kan'kani lokaci, lallai Allah ya isa bawa yaji tsoronsa, zai iya canza lamarun bawansa a lokacin daya so...... tunaninsa ne ya yanke sanda sukaji karan tafiyan mutane sun doso yanda suke. Da sauri ya mike yana leke leke, itama Deejah mikewa tayi da kyar tana raba idanu.
"Muryan mutanen suka soma jiyowa, kai Oga yaufa bamuyi kamu ba, nifa a bu'kace nake ma, gashi yau Ester bata fito patrol ba, ko wacce irin mace na samu zan sauke bukata na..... " Tashin hankali gobaran gemu, tashin hankalin da Deejah ta shiga ko 'kafan kama na Irfan beyi ba.......
👸🏻Queen Samy😍💋💄........
[8/19, 06:25] Umar Dalha: 🌗🌗🌘🌘 *Mallakin Waye*
22
_I sincerely dedicated this chapter to all my fans, you guyz ave no idea how much you mean to me, ILYSM❤_ *#Always 2geda👌🏼*
"Mamie tayi masu treating duk wani wounds dake a jikinsu, sosai suka tausaya masu da jin wnn labari nasu me cike da al'ajabi da tausayawa, Deejah da Ruqayya suna dakin Ruqayya a can tayi wanka Ruqayya ta bata kaya ta kintsa jikinta ta saka.
"Irfan ya dubi Sadiq yace" wato a gaskiya Sadiq samun mutane irinku a wnn zamani nada matukar wuya, thank you very much.
"Murmushi Sadiq yayi kafin yace" haba Irfan ka daina fadin haka pls ai duk wanda ya taimaki wani kansa ya taimaka. Irfan ya danyi murmushi yace hakane, wayan Sadiq ya amsa ya shiga neman layin Ammah, bugu biyu Ammah ta daga da sallama lokacin suna tsaka da zancen komawa station itada Engr. Jin muryan irfan yasa Ammah mikewa tsaye babu shiri tana fa'din" Irfan me ya faru daku daga ina kake kira, ina Deejah.
"Ammah calm down pls, muna nan lafiya muna kan hayanmu ta dawowa gida. Engr ne yayi saurin amsar wayan ka kara a kunnenesa.
"Ashe bakada hankali Irfan, tinda nake da kai baka taba ganin bacin raina ba koh, toh ina mai tabbatar maka karka kuskura kayi abunda zaisa raina ya baci, duk yanda kuke maza ku taho gida.... daga haka Engr ya katse ko sauraren Irfan baiyi ba. Lallai Ran daddynsa ya baci, bai taba jinsa cikin yanayi irin haka ba.
"Sadiq ne ya shigo dakin dauke da abinci yake fadin "friend bismillah fah kai bakaci komai har yanzu ba.
"Girgiza kai kawai Irfan yayi yace" na gode Sadiq hankalin iyayenmu ya tashi, we need to go, daga haka yasa kai ya fito, dole Sadiq ya biyo bayansa.
"A parlor suka tarar haukan Dada ya tashi sosai sai fama ake da ita, ta kankame Deejah tana fadin babu mai rabasu, Deejah kuwa sai kuka take dan sosai Dada ta kankameta numfashima da kyar take.
"Da mugun mamaki Irfan ke kallon lamarin, Mamie ta karaso wajensu da sauri take fadin" yanzu nakecewa Ruqayya ta kiraku, kuzo ku taimaka ku kwace Deejah hannun Dada. Sadiq ya karasa ya soma lallashin Dada yana mata wasa da en dabaru dan ya samu ya kwaci Deejah, wani tokari takai wa Sadiq saida ya kwanta, " kar ka kwace mun 'diyata, kar kazo kusa dani.... tana huci take fadin haka tana hararan Sadiq, nan fah ta shiga ma'kure wuyan Deejah tana fa'din " sun kashe mun diya sun kasheta...... " Ai a tamanin Irfan yayi wata tsalle dukda dingishin da yakeyi bai hanasa capko Deejah ba, suka shiga kokawa da Dada, ciko yakushi duk bai hana Irfan kwacen Deejah ba, Deejah kam bata san sanda ta rungume Irfan ta 'kan'kanmesa cikin jikinta, Ya Salam wani shokin ne kawai ya dirar wa irfan, sun jima a haka, a hankali ya zameta daga jikinsa, ya mata masauki kan kujera,Mamie ta dubi Ruqayya tace maza kawo mata ruwa ta sha, da sauri Ruqayya ta kawo mata cup din ruwa ta mikawa Irfan dake zaune gefenta, hannu Irfan yasa ya kar'ba ya dubi Deejah da har lokacin jikinta na 'bari sabida tsoron ma'kurin Dada data sha, in a soft voice yace" have some water, dago ido tayi tana kallonsa sai ta samu kanta da kasa masa musu, a hankali tasa hannu ta karba ta soma sha, Sadiq kuma tuni yayi ta maza ya shige da Dada 'daki ya kelleta.
"Sosai lamarin yabawa Deejah tsoro, haka kawai taji mahaukaciyar ta shiga ranta, haka nan dukda zafin makura datasha bata so aka raba ysakaninsu ba. Jikinta duk ya mace sabida shauki.
"Har waje su Mamie da Ruqayya suka raka su yayinda Sadiq yaja su zuwa gida......
"Safwan ne zaune gaban Yakumbo mahaifiyarsa nasiha take masa gameda da duniya," Safwan kaga ku biyu rak Allah ya bani daga kai sainmarigayi yayanka, gashi shima yau baya nan saura kai kadai, Safwan ina so kabi duniya a sannu sann idan ka tashi aure ka auri matar kirki, abu na gaba bance karka rinka zuwa duba Aziza ba 'yarka ce tinda 'yar wanka ne, amma ko kadan bana so kana alaka da wadann mutane dan basu da mutunci basu san mutunci ba.
"Ta'be baki Safwan yayi ya mike yana fadin, Yakumbo Aziza dai jikarki ne kuma yar yaya nane dan haka babu yanda za'ace mu rabu da ita ni kinga fita na ma can na nufa..... baki sake Yakumbo ke bin Safwan da kallo har ya fice tama rasa kalma guda a bakinta balle ta masa magana.
"Tunda suka karyo kwanan LifeCamp zuciyan Sadiq ta kuma jaddada masa anya Irfan ba 'dan Engr Nazif Mumtaz bane President na M&M Builders, wata zuciya tace ka dakata dai kaga yanda kuka nufa, da wnn tunani har suka iso makeken gate din gidan Engr Nazif Mumtaz.
"Sadiw ya dubi Irfan yace" dama kai dan gidan nan ne, murmushi Irfan yayi yace kasan Dad dina ne sanda ake hangame masu first gate.
"Nasansa jiya jiya yayi employing dina a company dinsa, mutumi mai mutunci da sanin darajan dan adam, murmishi kawai Irfan yayi ba tareda yace komai ba, Deejah kuwa cewa tayi a ranta tabbas kayi gaskiya Sadiq, Engr akwai sanin darajan 'dan Adam daidai lokacin da second gate ta gama zugewa ta bude dan da sensor na jikin mota take amfani.......
_Kuyi hakuri da mistake da ya faru a page 21, instead sai nayi numbering dinshi page 20, my mind was somewhere else😀 you guys should bear with me pls. Labarin bai canza ba daidai yake tafiya👌🏼_
👸🏻Queen Samy😍💄💋...........
[8/19, 06:25] Umar Dalha: 🌗🌗🌘🌘 *Mallakin Waye*
23
"Sallaman su a kofar parlorn yayi daidai da jan hankalin illahirin mutanen dake parlorn, Irfan ne ya soma sako kafarsa da niyyan shigowa, Cikin tsantsan 'bacin rai wanda ya rufe idon Engr ko kula da yanayin Irfan beyi ba ya mike ya nufe sa, baiyi wata wata ba ya sau'ke wa Irfan lafiyayyar mari ji kake tasss 'karan marin da Engr yayiwa Irfan.
"Ba Irfan kawai ba harta su Ammah da Nadiya dake zaune cikin parlorn saida sukaji shock da wnn al'amari, Deejah da Sadiq dake 'ko'karin shigowa ai tuni suka kafe 'kafarsu ta kasa 'karasawa ciki.
"Da mugun mamaki Irfan ya dago yana duban mahaifin nasa sanda yake dafe da 'kuncinsa, abune da bai ta'ba shiga tsakaninsa da yaransa ba, lallai ran maza ya 'baci.
"Rai 'bace Ammah ta taso tana fa'din" meyasa zaka maresa Nazif, baka ganin yanayinsa ne, ka bari muji ta bakinsa.
"Engr na huci yake fadin" me zamuji me zaice mana, bansan rashin hankalin Irfan har yakai haka ba, au wato zamanka a turai har yakai ka dauki budurwa sukutum ka gudu da ita....." Ya isa haka! Ammah ta fadi cikin kakkausar murya hannu tasa ta ei'ko Irfan wanda har lokacin yake nan kaman mutum mutumi, je just couldn't believe it wai daddy ne ya maresa yau.
"Kasa zama Irfan yayi dan kuwa tuni fuskansa tayi jazur zuciyansa na tafarfasa, shi ba zafin marin bane ya damesa, no zargin da daddy ke masa ne, me yake nufi kenan, yana nufin shi din 'dan iska ne ko me. Rai 'bace Irfan ya juya ya fice daga parlorn gaba daya..... Kallo daya yayi wa Deejah ya dauke kansa zai wuce, itakam kasa kallonsa tayi, Sadiq ya soma binsa yana kiransa ko saurarensa beyi ba, sashemsa ya shige ya kulle kansa.
"Ammah ta riko hannun Deejah suka shige parlorn yayinda Sadiq ya take masu baya, Ko kadan Deejah ta kasa daga ido ta kalli Engr bata sani ba amma kullum girmansa a idonta karuwa yake, saidai yau abunda yayiwa Irfan sosai ya ta'ba zuciyarta.
"Sadiq! Engr ya kira sunan Sadiq yana mai kallonsa cike da mamaki, Sadiq ya 'karaso yana mai rusunawa yake gaida Engr. Nan Sadiq ya kwashe komai ya fa'da masu, nan fah Engr ya dada harzu'ka yana fa'din" banda rashin hankali irin na Irfan yanzu da wani abun ya samesu fa, snn ya kama ya dauki yarinya ya tafi da ita tayi kwanan daji fisabilillahi......Deejah kam tune ta sulele ta gudu daki dan kuwa kirjinta barazanr tarwatsewa take sabida bugawa da take da sauri da sauri dama har yanzu zuciyanta bata daina tunanin mahaukaciyar nan datayi ba, snn sai yanzu mafarkinta da takeyi da wata mahaukaciya ya dawo mata kwanyanta.
" Nan fah Sadiq ya shiga bawa Engr baki yana nuna masa faruwan hakan mu'kaddari ne daga Allah.
"Daga karshe Engr da Ammah sukayi godiya wa Sadiq kafin ya mike da niyyan tafiya, Amma tace a'a baka tafi haka nan ba baka sha ko ruwa ba... ta juya ko zataga daya daga cikin ma'aikata idonta ya sauka kan Nadiya dake bin Sadiq da wani asirteccen kallo dan kuwa sarai ta ganesa. Ehen yawwa Nadiya kawo masa abin ta'bawa Ammah tace tana mai kallon Nadiya, sai sann idon Sadiq ya sauka kan Nadiya for sure ya ganeta, maras kunyan yarinyar nan sunan da zuciyansa ta lakabawa Nadiya.
"A'a wllhi ba komai yanzu zan tafi ma ai, Sadiq yace yana dan shafa kansa. Engr yace no Sadiq ka zauna ka huta ka dan taba wani abu bazan ji dadi kazo har gidana ka tafi hakan nan ba, feel at home kaji.
"Babu yanda Sadiq ya iya dan kuwa Ogan nasa ya gama dauresa dole ya zauna ba don yaso ba, Ammah da Engr mikewa sukayi suka nufi garden din dake cikin gidan dan tattaunawa..
"Yatsina fuska Nadiya tayi sanda taga Sadiq ya daure fuska tamau kamar bai ta'ba dariya ba, Zama tayi ta mike fararen sawayenta ta saka earpiece a kunnenta ta shiga kwalawa Zulai kira... babu shiri Zulai ta bayyana a gabanta, a dakile ta kalli zulai kafin tace ki serving wnn, ta fadi tana mai nuni da Sadiq...
"Kutt, kaman ya mi'ke ya kai mata naushi haka yaji dan takaici, daba don kar ya fice Engr ya gansa ba da tuni yayi tafiyarsa.
"Cikeda ladabi zulai ta amsa kafin ta wuce kitchen dan aiwatar da umarnin Nadiya.
"Cikinsu babi me cewa kowa cikanka haka suke zaune a parlorn, banda sanyin ac da karar tv dake tashi a hankali bakajin komai sai kamshin gidan 'yan gayu dake wanzuwa cikin makeken parlorn.
"Zulai ta jere gaban Sadiq da kayan makulashe da tande tande da kuma shaye shaye... ko kalla Sadiq beyi ba balle yayi tunanin ci ko sha, jiran lokacin da ya diba yake ya cika ya tashi ya cika ma rigarsa iska.
"Wayansa ne tayi ringing take kyakyawan fuskansa ta cika da annuri ganin 'kanwarsa ce kuma sahibarsa me kira.
"Hello my little ya akayi ne, kinji shiru ko, kar ki damu na kusa dawowa.... yayi wata smile da zan iya kira killing smiling kafin yace I luv you..... Nadiya da earpiece ke manne kunnenta ashe gaba daya hankalinta naga Sadiq😂, yatsina fuska ta danyi tace ko ma waye wann zai gwada yanga oho. Haka kawai ta tsinci kanta da jin haushin wayan da yayi, a fusace ta mike ta tsaya a gabansa.
"Ko kallo bata isheshi ba balle ya tankata." Malam kaci abinda aka kawo maka ka tashi ka tafi pls dan nasan abunda ka zauna ci kenan, coz your presence irritates me.
"Sai snn Sadiq ya dago ido yana watsa mata mugun kallo cikeda tsana kafin yace" and who ordered anything da zakice naci abinda ya zaunar dani. Mind you karki nemi raina min hankali, karamar yarinya dake sai rashin kunya... ya girgiza kai kafin yace tir da hali irin naki, daga haka ya mike yasa kai ya fice daga parlorn... kallo ta bisa dashi gamida jan tsaki tana maijin haushin kanta meyasa ta masa shiru ya gaggaya mata maganganu yana yaron babanta. Rai bace ta nufi stirs.....
"Aziza ce zaune saman mota a parking lot ta fa'da kogin tunanin abin kaunarta da baisan tana existing ba wato Irfan, har Safwan ya gama parking motarsa a gefe Aziza bata sani ba, murmushi yayi ya karaso yanda take yana fa'din "Azee baby, tsalle tayi ta diro daga saman mota sanda ta jiyo muryansa taga ya nufo yanda take, da gudu ta tafi ta rungumesa tana fa'din" oyoyo Uncle Safff, hannunta ya riko suka nufi cikin gidan yana fadin" tunanin me kike ke kadai a waje.
"Juya ido ta waniyi kafin tace" Uncle Safff am in love..... Dariya Safwan yayi yace iyye ashe daughter na ta girma, who is the lucky guy.... Tayi wani murmushi tana juya ido kafin ta soma masa hiran Irfan...
"Hajiya nifa gani nake kamar aikin bokan nan bayayi ki duba ki gani har yanzu shiru, yace Engr da kansa zai nemeni gashi babu labari, anya kuwa bazamu canza boka ba, Laila ta fadi haka cike da damuwa.
"Dariya Hajiya Karima tayi kafin tace" kai dadina dake bakida ha'kuri kamar zawo, yo ba shekaran jiya jiya aka soma aikin ba, ki jira ki gani harta uwarsa sai mun basa izini ya gaisheta balle 'ya'yansa dasuke hanasa aure.
"Laila ta sau'ke ajiyan zuciya tace hakane Hajiya ai na yarda dake.... daidai nan Safwan da Aziza sukayi sallama suka shigo.....
👸🏻Queen Samy😍💄💋.......
[8/19, 06:25] Umar Dalha: 🌘🌘🌗🌗 *Mallakin Waye*
24
"Yana nan har kusan 'karfe 5:pm a sashensa, zaune yake cikin lallausan sofa da ya 'karawa parlorn kyau da annuri, yana sanye cikin 'bakar riga maras hannu gaban rigan an rubuta _Armany_ wandon jikinsa kuwa three quater ne me ruwan toka, kallon tashan ball yake amma da alama hankalinsa gaba daya baya wajen. "Sai yanzu yake da'da jin tsanar mata a ransa, tsakaninsu da mutane babu komai sai sharri, bacin haka meyasa daddy zai masa mummunan zargi gameda Deejah, for goodness sake har ya gama zamansa a States bai ta'ba bin mace ba saida ya dawo nan, why on earth zaiyi haka a rayuwansa, tun tasowarsa tun yana 'karami daddynsa bai ta'ba 'daura koda 'dan yatsa a jikinsa da sunan duka ba sai gashi yau har marinsa yayi, and the most annoying thing din shine akan mace ya maresa. Hiss yayi gamida mikewa ya nufi yanda yake motsa jiki a cikin sashen nasa, ya jima akan keken motsa jikin har yanzu fuskan Deejah yake gani akanta daddy ya maresa har yake zarginsa. Tsaki ya kuma ganin bazai bar tunanin ba yasa sa daukan car key ya nufo waje...
"Deejah Nilam Amir da kuma Aiman ne zaune a farfajiyan gidan suna wasa kaman yanda suka saba mussaman dashike jiya sunyi missing dinta, ita kuwa hankalinta gaba daya naga sashen Irfan ko Allah zaisa ta gansa, dan ta 'kagu tasan halin da yake ciki.
"Aiko yana fitowa sukayi ido hu'du, yayi matukar yin kyau shigar ya kar'besa tamkar balarabe zalla babu surki haka ya fito. Kallo daya ya mata ya dauke kansa ko takan 'kannensa dake wajen bebi ba ya nufi parking lot.
"Nilam ce ta fara hangosa ta tafi da gudu ta rungumesa nan su Amir da Aiman ma suka mara mata baya.
"Ko kadan Irfan bai wani sake da 'kannen nasa kaman yanda ya saba ba, fuska a daure ya hamasu karasowa yanda yake, wann al'amari ne da basu ta'ba gani ba, dukda yayan nasu miskili ne amma ko ka'dan baya hantaran 'kannensa snn yana jansu a jiki yana tsananin sonsu, dan haka gaba daya sai suka sha jinin jikinsu harta Nilam 'yar gaban goshin nasa. Ita kanta Deejah saida abun ya mata wani iri dan bata ta'ba ganin yayi hakan wa 'kannensa ba.
"Ammah dake zaune kan resting chair a balcony sosai abin ya bata mamaki lallai ran Irfan ya 'baci, amma fushinsa bai kamata ya shafi 'kannensa ba.
"Cikin tsanaki yake tu'kin motar 'kirar _Camryy Anaconda_, bai tsaya ko ina ba sai Amigo, koda ya shiga zama yayi ya kasa ordering komai, kaman daga sama Ahidjo ya hangosa shima shigowansa kenan.
"Tun daga nesa Ahidjo yake fa'din" what a coincidence!
"Kallonsa kawai irfan yayi gamida yin kasalcecciyan murmushi wanda take dabi'ansa ne, Ahidjo ya saba da miskilancin Irfan tu a US dan haka baiji komai ba da ya masa haka.
"Guy what's up, Irfan ya fa'di sanda Ahidjo ke zama seat next to him. "Kallonsa Ahidjo yayi yana murmushi kafin yace" you will never change Irfan, will you?, na dauka Nigeria zai canza ka ashe nothing has changed. Kai na tunama ashe fada mukeyi da kai, I was waiting for you jiya zaka zo ka dauke ni, babu kai babu labarinka and your phone baya shiga, bakaga wuyan danasha ba, kai yesterday was awful..
"Har yanzu Irfan bai ce masa komai ba sai wasa da car keys dinsa da yakeyi, Ahidjo ya kura masa ido sai yanzu ya kalli alamun ciwo a jikin Irfan.
"Guy me ya same ka haka, why are you wounded.
"Au sai yanzu zaka tambayeni bayan ka gama zubannaka, Alright fine now that you asked zan fada maka, wadan nan ciwo daka gani is all because of you, zaro ido Ahidjo yayi kafin yace " ni kuma, ban gane ba Irfan pls spell it out.
"Kaman bazaice komai ba sai kuma ya labarta wa Ahidjo yanda lamarin ya kasance, saidai bai fada masa yanda sukayi da Engr ba, Sosai Ahidjo ya tausaya masa..." Kai friend am so sorrry, danasan haka zata kansance wllhi da ban kiraka ba.
"Kallonsa Irfan yayi a kaikaice kafin yayi murmushi yace" just look at your self, jibi yanda kake wani apologizing as if you were at fault. Allah ya kaddara hakan zai faru koda kai ko babu kai.
"Ahidjo yayi murmushi yace, Dude da'dina da kai akwai tawakkali da matso da Allah kusa, Irfan yayi murmushi ba tareda yace komai ba.
"Sun jima suna fira kafin suka mike suka nufi gidansu Ahidjo dake Asokoro....
"Misalin 'karfe 8:pm Engr yayi kiran Deejah dan tin dawowansu magana bata shiga tsakaninsu ba, sosai ta tsinci kanta da mugun fa'duwan gaba, zaune ta samesa a garden hasken fitulu ya gauraye ko ina yana sanye da fara kal din jallabiya haka nan idonsa manne da medicated glass hannusa dauke da news paper yana dubawa.
" 'Kirjinta ya tsananta fa'duwa sanda taga ya dago kai sukayi ido hudu, yau kam fuskansa a 'dure tamkar bashi ba, muryansa me cike da 'kwarjini taji ya mabato sunanta yace bismillah,
"A hankali ta soma taka 'kafarta tana sanye cikin doguwar riga ta atampa da hijabi daidai gwiwarta, tsugunawa tayi ta soma gaishesa, a dake Engr ya amsa kafin yace tashi ki zauna, 'kirjinta na ci gaba da bugawa da sauri da sauri haka ta mi'ke da kyar ta zauna a 'daya daga cikin kujerun.
"Shi kansa Engr ya lura da yanayin Deejah bata sake yanda ta saba sakewa dashi a da ba, zuciyansa ta shiga tambayansa wai me kake ji gameda Deejah ne, wata 'bangare na zuciyansa tana son kallon Deejah a matsayin uwa gasu Nilam, amma 'bagare mafi rinjaye 'kasan zuciyansa tafi kallon Deejah a maysayin 'yar uwa gasu Nilam. Sun jima kaman babu wanda zai yi magana cikinsu, sai jiyi sautin rufe jarida taji alamun yana rufe news papers din, ajiyewa yayi bisa table din dake gabansa kafin yayi gyaran murya. Dai dai lokacin da motar Irfan ta sako hancinta cikin farfajiyan gidan........
👸🏻Queen Samy😍💄💋.....
[8/19, 06:26] Umar Dalha: 🌘🌘🌗🌗 *Mallakin *Waye*
25
"Gaba daya Deejah da Engr kallonsu ya koma ga Irfan dake faman parking mota cikin parking lot, tun daga nesa ya tsare Deejah da idanu, besan meyasa ba ganinta da yayi yasa zuciyansa yin sanyi saidai haka kawai zuciyansa bataji da'din ganinta da Engr zaune a garden ba. Yana isowa kusa dasu dauke kai yayi snn yayi wucewarsa sashensa.
"Engr yamaida dubansa ga Deejah wacce ta bi irfan da kallo har ya 'bace ma ganinta, Sau'ke ajiyan zuciya Engr yayi kafin ya furta "Deejah".
"Da sauri ta bar kallon sashen Irfan gamida saita hankalinta waje guda tace" Na'am Daddy,
"A zuciyansa ya maimaita "Daddy", bata ta'ba kiransa da daddy ba sai yau, kullum Sir take ce masa gashi yau ta kirasa da daddy, kawar da tunanin yayi kafin yace" tashi kije we will talk some other time.
"Cikin sanyin jiki ta mi'ke cike da rusunawa tayi masa sallama ta shige ciki......
"Nadiya dake tsaye window din 'dakinta kan idonta komai ya faru, girgiza kanta tayi kafin ta furta " now I get it, so that was the reason why daddy was so panic sanda Deejah da ya Irfan suka 'bace.... sauke labule tayi kafin ta furta " no way dole nasan meke shirin faruwa a gidan nan, daga haka ta sauko down stirs ta nufo waje....
"Engr kuwa mikewa yayi ya nufi sashen Irfan nan Nadiya tabi bayansa a hankali ta la'be jikin windown parlorn Irfan.
" Zaune ya samesa yana shan fresh milk ga pic din momyn sa ri'ke a hannunsa. Kallo 'daya Irfan yayi wa Engr ya kauda kansa gefe.
"Engr ya fuzar da iska kafin ya zaune kusa da Irfan, ya 'bata lokaci sosai kaman bazaice komai ba sai kuma yayi gyaran murya ya dafa kafa'dun Irfan yace" Son regarding what happened earlier am sorry, nasani duk da ni mahaifinka ne, I shouldn't have slapped you, I should have let explain first......." Dakatar da Engr Irfan yayi ta hanyar girgiza kai ya soma fa'din" Daddy you don't need to apologies to me, you're my father, besides marina da kayi it doesn't hurt me, what hurts me the most shine zargin da kayi min daddy, and sai yanzu na gane saboda me kayimin wnn mummunar zargin, it's because of Deejah.
"Engr ya dan fuzar da iska dan baya so zancen yayi nisa tsakaninsa da 'dansa, a hankali ya furta" ya isa haka Irfan na mareka ne sabida banaso na rasaka sabida next time kasani akwai hanya me kyau da maras kyau na aiwatar da komai, you need to get some rest......
" Idanuwan Irfan sun ka'da sunyi jazur yake kallon Engr kafin yace" Yes Daddy sabida Deejah ne, because you love her, because you don't wanna loose her......." Da mugun mamaki saman fuskan Engr yake bin Irfan da kallo, shi yake kalla yake cewa son Deejah yake, a hasale ya katse Irfan " Enough Irfan!
"Irfan ya mike yana ci gaba da fadin" gaskiya na fadi daddy son deejah kake yi idan ba haka ba meyasa bazaka kebe ka tattauna da ma'aikatan gidan nan ba sai ita, just admit it....,,, " Wata mari meji da lafiya Engr ya sauke wa Irfan saida ya dur'kusa, dafe 'kuncinsa yayi ya dago yana duban daddynsa, bai ta'ba ganin 'bacin ran da ya gani kwance samar fuskansa ba,
"Are you stupid or what, ni kake tuhuma ina mahaifinka, you better be careful. Idan shaye shaye ka fara gwara tun wuri ka daina kafin kaga asalin 'bacin raina, daga haka Engr yasakai ya fice daga sashen Irfan. Har ya fice Irfan bai sake 'kuncinsa ba snn bai daina kallonsa ba.
"Zuciyansa na masa wani irin zafi, for the first time da ya ta'ba samun sa'bani da mahaifinsa tun tasowar sa, this is all because of mace, macen ma Deejah nanny, why why this, da gaske son Deejah yake, meyasa ko ka'dan feelings din da yake ji for her baya raguwa saidaima 'karuwa da yake each and every second, toh idan kuwa daddynsa son Deejah yake he needs to get far away from her. A hankali yayi tsaki ya furta" she's my problem here....
"Nadiya dake la'be jikin window sosai lamarin ya bata al'ajabi, kama kumkuminta ta 'danyi tana me ri'ke ha'barta kafin tace" Toh wai shin Zuciyan Deejah *Mallakin Waye*, I needs to find out, da wnn tunani ta wuce cikin gida....
"A parlor ta samu Ammah na kallon labarun tara, Ammah ta bita da ido kafin tace ina kika fito, Nadiya ta dan langa'be kai ta 'karaso ta kwanta jikin Ammah, kafin tace na fito wajene na dan sha fresh air.
"Ammah ta jinjina kai kana tace" kin ganemun yayanku ya dawo? Tashi Nadiya tayi ta zauna kafin tace" ya dawo Ammah, but he seems depressed, I wonder meke damunsa haka, ko dan marin da daddy ya masa ne.
"Ammah tayi shiru kafin ta ynkura ta mike tana fadin" I need to check on him. Nadiya tace gaskiya kam he needs you granny, barin lekasu Deejah dasu Nilam.
"Dakin Deejah Nadiya ta wuce yanda take jiyo hargowansu Nilam dasu Amir, Deejah na tsakiyan su tana masu story nan Nadiya ma ta zauna aka ci gaba da ita, kaman ba ita bace da ke hantaran Deejah, ita kanta Deejah saida abun ya bata mamaki...
"Knocking Ammah keyi a kofan Irfan yaki budewa, saida yajiyo muryanta kafin ya mike ya bude mata, kallo Ammah ta bisa dashi fuskan sa tayi jazur haka nan idanunsa wande suke farare sol sun koma jazur.
"Komawa Irfan yayi ya zauna bisa sofa bayan ya bu'de mata, ajiye plate din abincin dake hanunta tayi saman center table kafin ta zauna daf dashi, kallonsa takeyi a lokaci guda tana nazarin yanayinsa, hannayensa ta rike tace" I now you must be hungry maza kaci abinci, ta dauko plate din da spoon ta diba cikin spoon tace" oya open your mouth,
"Murmushi Irfan yayi yana kallon Ammah tun yana yaro idan yayi fushi ita ke calming dinsa, girgiza kai yayi yace" Ammah banida appetite, I can't eat anything now.
"Ammah ta ajiye plate din bisa table dan tasan bazaicin ba ko yaya tayi, ta dawo da hankalinta ga Irfan kana tace" Irfan, duk 'da na gari baya fushi da mahaifansa, abunda kayi shi kannenka zasu gani suyi koyi, snn har yaushene zakuyi watsi da wnn mummunar 'dabi'a ta turawan yamma huhm Irfan.
"Ammah pls, ni ba fushi da daddy nake ba, am just tired of this place ne kawai, am going back to the States......" What! Ammah ta 'katsesa kafin tace" no way Irfan, babu yanda zaka je kaji na fada maka, kar na sake jin kace zaka koma America, daga haka Ammah ta mike ta barsa nan wajen. Bayanta yabu da kallo kafin ya girgiza kai yace" dole na tafi I can't stay here, mikewa yayi saman sofa gamida lumshe ido.....
*Two days later*......
"Ko Office bezuwa tin bayan faruwan wnn al'amari, Sadiq ya dubasa a Office dinsa yauma baya nan, yana jin nauyin tambayan Engr dan haka ya yanke cewa kawai bzi dubosa a gida yau ida ya tashi a aiki.
"Hakan kuwa akayi, daga Ofiice gidansu Irfan ya wuce, tin daga nesa ya hangota yauma cikin shigar data saba wato shigar turawa tana tsaye gefen yanda aka ke'be Ostriches tana jefa masu abinci.
"Tsaki yayi a fili ya furta" maras kunyar yarinyar nan tana nan, dan ji yayi dama baizo ba sabida ganin Nadiya dayayi but babu yanda ya iya tinda ya shigo.......
👸🏻Queen Samy😍💄💋.........
[8/19, 06:26] Umar Dalha: 🌘🌘🌗🌗 *Mallakin Waye*
26
"Kallo Nadiya tabi Sadiq dashi har ya shige, tsuka tayi gamida ta'be baki" shikuma wann sai shegen girman kan tsiya gashi ba kowa ta fa'di sanda taci gaba da jefawa Ostrich abinci.
"Haba Irfan abunda kakeyi kwata kwata be dace ba, for goodness sake akan me zaka dauki fushi da mahaifinka, ko meye yayi maka bai kamata kayi judging dinsa ba matu'kar ba dokan Allah ya take ba, da ka dena zuwa Office, are you planning to quit the job or what, haba Irfan kayi tunani kaifa Allah ya maka gata tunda ya bar maka naka mahaifin a raye, snn yana tsananin sonka yana kula da kai, inaga wa'enda babu nasu iyayen, duk wann ni'ima da Allah yayi maka sakayyan da zaka masa kenan, ka tuna yardan Allah na tareda na iyaye, kaman yanda ka rabu da momynka lafiaya kayi fatan rabuwa da daddynka lafiya.
"Kallon Sadiq Irfan yayi kafin ya murmusa yace" na gode friend, you're indeed a good friend Sadiq, I was planning to back to the States, amma kalamanka sun karyan gwiwa, na fasa tafiya snn zan nemi afuwa wajen daddy da Ammah.
"Sadiq yayi murmushi gamida jinjina kai, Irfan ya dan gyara zamansa yace" Friend ya kamata na fa'da maka komai dake faruwa, nan Irfan ya kwashe komai ya fa'dawa Sadiq bai 'boye masa komai ba gameda Deejah....
"Sadiq ya sau'ke ajiyan zuciya kafin yace" Friend the truth is that you're in love.... " What! Irfan ya fa'di yana me duban Sadiq, gya'da kansa Sadiq yayi yace" Of course you're in love aboki na, you love Deejah.
"Girgiza kai Irfan ya soma kafin yace" No no, that can't be, ni bana sonta, as a matter of fact bana son mata, they are always causing trouble, na fa'da maka she was the reason da na sami matsala da daddy na for the first time snn kace sonta nake, in short I want her out of my life.
"Murmushi Sadiq yayi me bayyana ha'kwara kafin yace" abokina just admit it, wllhi sonta kake amma idan ka kasa ganewa with time zaka gane, snn daddy ba irin son da kake tunani yake mata ba, no sonta yake tamkar 'yarsa yanda yake son sauran yaransa.
"Shiru Irfan yayi yana nazarin maganganun Sadiq, Sadiq ya dan dubi agogon hanunsa ya mike yana gyara hulan kansa yace " kasan abunda nake so da kai, tashi muje mu samu Oga, and apologies to him.
"Ba musu Irfan ya mike suka nufi sashen Engr wanda yake can tsakiyar gidan daga center.
"A parlor suka samesa yana shirya wasu documents, da sallama suka shiga, Engr ya amsa yana cire glasses din idanunsa.
"Yana ganin Sadiq fari'an fuskarsa ta 'karu, yana jin son Sadiq tamkar 'dan da ya haifa na cikinsa, dan kwana biyi da fara aikinsa a 'karkashin company dinsa ya gane Sadiq nada gaskiya da ri'kon amana, dan kuwa duk wasu cuku cuku da akeyi a fanni accounting an rage, komai na tafiya yanda ya kamata.
"Rusunawa sukayi suka gaida Engr, nan Irfan ya nemi gafaran mahaifinsa kuma ya yafe masa, take komai ya koma normal dama Engr mutum ne me tsanain damu da damuwar iyalinsa, nan Irfan da Sadiq suka ci gaba da shirya documents 'din aka kuma 'barke da hirar Company gaba daya.
"Sosai Engr yaji da'din abota tsakanin Sadiq da Irfan ko babu komai Sadiq yaron kirki ne, zuwan Sadiq cikin ruwarsu ha'ki'ka alkhairi ne.
"Kai tsaye wajen Ammah Irfan ya wuce da Sadiq dan su gaisa.
"Ammah ma sosai ta sake da Sadiq dashike yanada barkwanci, Ammah ta dubi Sadiq tace saifa kayita fama da abokin naka dan miskili ne bana wasa ba, Irfan ya dan langabe kai yana kallonta ba tareda yace komai ba, Sadiq murmushi kawai yayi kafin sukayi sallama da Ammah.
"Har wajen da Sadiq yayi parking motar sa Irfan ya raka sa, har lokacin Nadiya na tsaye wajen jiminan sai kallon Sadiq take har ya tada motarsa ya fice.
"Daidai 'kofan shiga sashensa suka kusa yin karo hannunta dauke da tray na abinci, kallonta ya tsaya yi itama haka kallon nasa take, sun jima a haka suna aika sa'kon kallonsu ma juna kafin ta sunkunyar da nata idon, dan kuwa gaba 'daya 'kwarjinin sa ya cika wajen.
"Gajeren tsaki yayi gamida sa kai ya wuce cikin parlornsa, jiki a sanyaye tabi bayansa, kaman baisan ta shigo ba haka yayi hayewarsa sama dakinsa, so yake ya rin'ka avoiding 'dinta ko zai 'karyata abinda zuciyansa da Sadiq suke gaya masa gameda Deejah.
"Ta jima tana zaune parlorn sa ganin alamu bazai fito ba yasata mikewa ta fice, bata san me takeji gameda Irfan ba, amma kasancewa da sukayi na kwana guda a tare yasata jin wani irin babban al'amari gameda shi, zuciyanta ne ta shiga garga'dinta" _Ke Deejah ruwa ba sa'an kwando bane, ina ke ina Irfan, matashi meji da ku'di da kyau, komai ya hada a rayuwa saidai wanda ba'a rasaba, tsaya yanda Allah ya ajiyeki matsayin Nanny_. Da wann tunani ta isa zuwa 'dakinta, wayanta ta ciro ta shiga neman layin Anty Larai haka kawai taji tana son magana da wani nata itama....
*08:13pm*
"Engr ne zaune a Office dinsa na cikin gidansa wanda yake a cikin sashensa yana gudanar da wasu 'yan ayyukan sa, Nadiya ce tayi knocking a door din, da shike kofar na glass ne tuni Engr ya ganta, murmushi ya sakar mata kafin yace" come in sweedy.
"Tura kofar tayi dashike irin me zugewan nan ne sann ta shiga, kujera me kallon na Engr ta zauna kana tace" Daddy sannu da aiki, idonsa naga computer yace yauwa sannu Sweedy, is anything the matter, ya tambaya har lokacin yatsunsa na kan keyboard idon sa naga screen din computer din.
"Daddy dama so nake muyi wata magana.
"I guess about your school right? Ya fadi sanda yake ci gaba da aikinsa.
"No daddy is about Deejah..... cewan Nadiya......
"Take Engr ya bar abunda yake gamida cire glasses din dake manne idonsa, ya karkato kacaukwam yana duban Nadiya......
👸🏻Queen Samy😍💄💋........
[8/19, 06:26] Umar Dalha: 🌗🌗🌘🌘 *Mallakin Waye*
27
"Nadiya taci gaba da fa'din" Daddy so nake nasan meke tsakaninku da Deejah.
"Shaye da mamaki Engr ke kallon Nadiya kafin yace" Nadiya are you incense, kin kosan da wa kike magana.
"Daddy na sani, Deejah tazo gidan nan a matsayin Nanny wanda kowa baya sonta, bayan kai da Ammah babu wanda ke sonta cikinmu amma kywawan halayyarta da 'dabi'unta yasa kowa ya fara sonta, kuma naga yanda kayi reacting sanda suka 'bace da ya Irfaan, Daddy ina so nasan ko kaima......"Enough! Engr ya daka mata tsawan da saida ta firgita, get out of here now stupid girl kawai, ya fadi yana nuna mata kofa.
"Jikin Nadiya har na 'bari ta mi'ke ta nufi 'kofa dan bata ta'ba ganin haka daga mahaifinta ba.
"Tana ficewa Engr ya zauna yana jinjina lamarin, wai me 'ya'yansa suke nufi ne, shikenan shi bashida daman yaso ko aso shi, baisan ta'kamemmen abinda yake ji gameda Deejah ba, dan haka dole ya 'dibar mata lokaci, sannan maganan aure kuma yanzu yake jin zaiyi aure, take Laila ta fa'do ransa. Ji yayi kawai ya dau wayarsa ya shiga neman layin Laila.
"Laila kuwa kaman a mafarki haka taga wayan Engr, haba nan fah ta fita da gudu tana 'kwala kira wa Hajiya, Hajiya na zaune tana bawa Alhj Ma'aruf abinci a baki Laila ta shigo da gudu tana nuna mata screen din waya. Haba nan fah Hajiya ta saki shewa tace kinga abinda nake fada maki ko, magpza dauki ki kalallamesa da kalaman soyayya. Da gudu Laila ta fice balcony ta dau wayan....
*Washe gari*
"Kaman yanda ya saba yauma 'karfe 8:30ama ya gama shirinsa tsaf cikin Jampa coffee brown yasha hula zanna bukar, yayi kyau sosai sai ya fito babban mutum, jampa tana kara masa kyau da 'kwarjini,
"Hajja ta gama jera breakfast saman dinning, gaisawa sukayi da Irfan kafin yace" pls Hajja inason fresh blended pineapple, cike da jin dadi Hajja ta amsa dan itama kwana biyu da Irfan yayi yajin cin abinci bataji da'di ba, daidai nan Ammah ta sau'ko daga stirs nan suka gaisa da Hajja cike da girmama juna kafin Ammah ta karaso dinning wajen Irfan, cikin sauri Hajja ta shige kitchen ta tarar dasu Deejah da Zulai suna cin nasu break din, 'kamshin turarensa kawai Deejah ta jiyo saida gabanta ya fa'di,
"Hajja ta dubi Deejah tace" dan Allah Khadijatu tashi ki markada wa 'Karamin Alhaji abarba kin sansa bature ne wai shi zai sha da safen nan, ni zan hada abinci Hajiya ne ta sau'ko 'kasa.
"Deejah ta danyi shiru dan bata son musuwa Hajja, a dan kasalce ta mike ta ciro abarban cikin fridge ta shiga wankewa,...
"Bayan ta gama ne ta shirya cikin cup ta dora kan karamin tray tace Hajja na gama, Hajja tace toh Khadijatu kai masa yana kan teburin cin abinci, Deejah ta danyi shiru dan bataso ta hadu da Irfan dukda songaninshi da zuciyanta keyi, ta 'dan langa'be kai tace Hajja ga Zulai bata komai ta kai masa man. Zulai tace cab'di wnn me turanci wa mutanen, yanzu kana zuwa zai hau fada maka abu da turanci gwara dai ke ki kai masa tinda ke kinaji idan ya maki zaki gane. Deejah ta dan harari zulai kawai a dole tasa kai ta shige dan kai wa Irfan drink dinsa.
"Irfan kayi kyau kaman kullum ka rin'ka saka manyan kaya Ammah tace tana duban Irfan. Murmushi ya 'danyi kafin yace" no Ammah bazan juri saka wadann kayan ba, gaba daya yanzuma am not comfortable sun takurani. Ammah tayi murmushi daidai lokacin da Deejah ta karaso wajen,
"Yana ganin ita ce ya mi'ke yana gyara hular kansa ya rijo hannun Ammah ya manna mata peck yace" Ammah am leaving, idonsa naga Deejah yana jefa mata mugun kallo. A'a ka tsaya mana kasha drini din, Ammah ta fadi, girgiza kai yayi yace no Ammah am Ok ya isheni, besides nayi latti ma already. Daga haka yasa kai ya fice daga parlorn.
"Ammah ta juyo ta kalli Deejah yanda tabi bayan Irfan da kallo, a hankali tace Deejah bishi dashi waje, kinji kai masa.
"Deejah tayi saurin saita kanta kafin ta iya furta toh Ammah.
"A parking lot ta samesa har ya kunna mota, tana tsaye gefen kofar mazauninsa ta kasa cewa komai, tana ri'ke da 'dan tray din data 'daura cup din akai.
"Har yayi rivers zai tafi kome ya tuna kawai sai gani tayi glass din motar yana sau'ka, kaman bazaiyi magana ba yace" are you deaf or what, bakiji sanda nace na koshi bane ko me, yayi dan karamin tsaki kafin ya daga glass din yaja motarsa ya bar wajen, yana kallonta ta glass yanda tayi tsaye tabi bayan motarsa da kallo, zuciyansa ne ta shiga masa zafi ko ka'dan baison yayi hurting dinta, tsaki yadan kuma ja a hankali ya furta" dammn everything, kaman zararre ya soma magana shi kadai yana driving , "no way, bazaki zame mun nightmare ba, I need to do something.......
"Jiki a sanyaye Deejah ta shige cikin gidan, gaba daya su Hajja basu gane mata ba, misalin 'karfe 11:08am ta shirya tsaf cin doguwar rigar abaya ta yane kanta da mayanin abayan ta fito.
"A parlor ta samu Ammah ta rusuna ta gaisheta kafin tace Orphanage take son zuwa wajensu Anty Larai, Ammah tayi murmushi tace yayi kyau Deejah, Ashiru na waje ya kaiki sanda kie son dawowa sai kiyi min waya aje a daukeki, ki gaishe da Larai din.
"Cike da ladabi Deejah ta mike ta nufi waje, Zulai dake la'be tana kallon komai a idonta ya faru, tayi kwafa tace shegiya kaman ta shanye kowa a gidan jin kanta take tamkar ba me aiki ba, Allah ka shigo da Anty Laila gidan nan taci ubanki...
"Tun daga gate din Orphanage ake oyoyo wa Deejah Anty Larai bata nan sun tafi wani taro na gidajen marayu a cikin Abuja, kai tsaye class din 'yan ajinta ta wuce ta shiga raba masu sweets haba nan Orphanage ya dauka gaba daya, Anty Deejah tazo Anty Deejah tazo. Yusra tana dawowa daga sch ta tarar da Deejah, haba nan fah aka 'buge da hirar club.
"Waike yaushe zaki koma zuwa club ne, Yusra ta tambaya sanda ta kafe Deejah da ido dan ba karamin kyau ta kara ba, kana ganinta kasan hutu ya kama jikinta.
"Deejah ta danyi murmushi dan yanzu duk wasu abubuwan tashancin da takeyi a da ta daina kafin tace" tab aikam babu rana dan gaskiya iyayen yaran da nake raino suka sani zai iya shafan aiki na.
"Yusrah ta tabe baki tace" uhum lallai kam, koda yake ba laifinki bane irin wnn hutawa da kike yi, kinga yanda skin dinki ya koma kaman ba aiki kike ba, ke nima na sami irin aikinki wllhi yi zanyi.
"Deejah ta kaima Yusraha dukan wasa a cinya tace" Yussy you will never change, will you.
"Yusrah tace ah toh ai gaskiya ne, ki dubi kanki tun daga kayan jikinki ai ansan baki shan wahala.
"Ke wai ina labarin Safwan? Deejah ta tambaya.
"Kice 'dan iska, cewan Yusrah. Nan suka buge da hiran Safwan saida suka tsayar da ranar leka club kafin Deejah ta wuce wajen Anty larai dan ta dawo lokacin.
"Sosai Anty larai taji dadin ganinta, ta tambayeta babu wata matsala, Deejah tace babu komai, Saida Anty larai ta kara mata en nasihohi da shawarwarin zama da mutane kafin Deejah ta mike dan tafiya lokacin an sauko daga jumma'a.
"Har waje Yussy ta rakata kafin ta soma takawa dan neman abun hawa dan tana jin nauyin kiran Ammah tace azo a dauketa...
"Tafe suke cikin motar Irfan suna dawowa daga masallaci, kai guy wallahi 'kasan nan babu ha'da'd'dun bebs, jiya na zaga clubs sun fi kala nawa amma duk banga wata beb da zance tayi mun ba, haba bebs kam ai se Los Angeles, cewan Ahidjo dake zaune gefen Irfan mazaunin me zaman banza.
"Ta'be baki Irfan yayi kafin yace" there you go again, bazaka ta'ba canzawa ba Ahidjo, kaidai maganan mata kawai, mtsw baka da aikinyi wllhi, pls change the subject I beg you.
"Dariya Ahidjo yayi yace, guy bazaka gane bane kawai, ina missing los Angeles wlhi,........ Muryansa ne ya tsarke sanda ya hango bayan Deejah dake tafe gefen titi..... taba Irfan yayi yana fadin" Kai Dude ga wata hot fah, yi parking yi parking pls.....
👸🏻 Queen Samy😍💄💋.........
🌘🌘🌗🌗 *Mallakin Waye*
28
"You perfectly well known that bana daukan mace a titi, so babu abinda zai sa na tsaya, cewan Irfan dake shirin hayewa Flyover.....
"Ri'ke starry din Ahidjo yayi yana fa'din haba guy don't do this to me pls, ok is it because you giving me a ride? Irfan ban wulakance mana......
"Dole Irfan yayi parking gefen titi badon yaso ba, Ahidojo yace guy rivers fah zakayi, A kufule Irfan ke kallonsa kafin yace" are you trying to annoy me what, tsaki yayi a hankali kafin ya bude motan ya fice ya zagayo mazaunin Ahidjo yace" oya fita kayi driving motan, babu musu Ahidjo ya koma mazaunin driver nan da nan ya shiga yin rivers da motan.
"Deejah kam taji anata horn amma ko juyawa batayi ba, Irfan ya ta'be baki gamida turo hulansa gaban goshinsa ya dan kishingi'da jikin seat.
"Daidai gefen Deejah Ahidjo yayi parking, 'Yan mata barka dai, ya fadi yana fito da kansa ta glass, juyowan da Deejah zatayi a kufule dan tayi niyan wanke me motan nan, idonta ya gane mata Irfan..., Ahido sai zuba yake inaaa Idon Deejah nakan Irfan ko kyaftawa batayi, Nan fah Ahidjo ya gane hankalinta gaba daya naga Irfan,
"Jin shiru yasa Irfan matsar da hulansa yana me jan tsaki, dago kan da zaiyi sukayi ido hudu da Deejah wacce ta kafesa da idanu..., Kallon juna suka shiga yi dukansu biyu, Ahidjo kam sai suka zame masa tv,
"Ina kika fito tsakar ranan nan, Irfan ya tambaya sanda Deejah ta dauke idonta daga dubansa.
"Gajeren tsaki tayi a ranta shikuma wnn sai kace wani ubana, jibi yanda yake wani tambayan mutum, wnn ko ya girme mun ai befi ya bani wani shekara biyar ba.
"Ba tambayanki ne ke ba, ya kuma fadi,
"Sai snn tace" Orphanage,
"Orphanage" ya maimaita a hankali kafin yace, Oya shige mu tafi, babu musu ta bude backseat ta zauna, Ahidjo kam gaba daya sai abun ya masa wani iri, shidai baisan Deejah a gidansu Irfan ba, zuciyansa ne ta shiga tambayansa to wacece ita... Da haka har suka isa kofan gidansu Irfan, a gate suka ajiye Deejah kafin suka nufi gidan su Ahidjo.
"Kai guy itama wnn din kanwarka ce, shiru kaman bazai amsa sa ba sai kuma yace, itace yarinyar da nake fada maka, she's my worse nightmare here, she causes nothing but trouble.
"Ahidjo yayi dariya har yana buga starry kafin yace, oh kace mun she's your crush, .... "What my crush, no never, Allah sawake mun, on the contrary she's always annoying me, snn kace she is my crush,
"Wani murmushi Ahidjo yayi yana nazarin Irfan, kafin yace" guy yarinyar nan ta sace zuciyanka, I can see it from your eyes.
"Shiru Irfan yayi bece komai ba, meyasa mutane suke cewa son Deejah yake, kai kode da gaske sonta yake, toh wai dama hakan son yake,. Idan kuwa hakane, he needs to find out zuciyan Deejah *Mallakin Waye* kafin ya dasa soyayyanta dake shirin masa shigar bazata cikin zuciyansa. cire hulan kansa yayi ya jefa a backseat daidai lokacin da Ahidjo ke parking, a farfajiyan gidansu.
"Muje mana Ahidjo ya fadi, girgiza kai Irfan yayi yace" kaje kawai ni zan wuce sai munyi waya, Ahidjo yace alright no prob, gobe dai su mum zasu iso Nigeria insha Allah.
"Ok Allah ya kawo su lafiya, Irfan yace kafin sukayi sallama ya wuce gida.
"Dakinsa ya wuce ya fada duniyan tunanin Deejah,.....
"Nadiya ce zaune a 'dakinta takan tunanin abinda ya dameta, itakam Allah sa Ya Irfan son Deejah yake, idan hakan ta tabbata babu yanda za'ayi Daddy yace yana son Deejah, da daddynta yayi aure ai gwara ya Irfan ya aureta, itafa ta tsani kishiya a rayuwarta, Koda yanzu da babu momynta bata fata daddy ya sake aure itakam tana jin kishin daddy yace zaiyi aure, zuciyanta ya shiga tambayan ta yanzi idan kuma mijin da zaki aura zai maki kishiya fa? Mikewa tayi tana girgiza kai, haba haba never Allah ya tsareni, aiko za'ayi gawa uku a gidan, koni ko shi ko ita kishiyar.
"Lumshe ido tayi sanda ta tuna fuskan Sadiq, tayi saurin budewa tanason 'karyata zuciyanta amma inaa, kai wnn shine dan hakin daka raina shike tsole maka ido, Sadiq data raina masa gashi ta kasa yakishe tunaninsa a ranta...
"Misalin 'karfe 8:30pm, Engr.Nazif Mumtaz ne zaune gaban mahifiyarsa, cikin nutsuwa yaci gaba da fa'din" Ammah kan magann aure na da Laila ne, inaga lokaci yayi da za'a tsayar da rana, na sani ba lalle yayiwa yaran nan da'di ba, dukda bawai son airen nake ba, gwara nayi sabida takai 'ya'ya na nacikina sun fara tuhumata akan abinda nake da dama akai, idan na zauna babu auren nan gaba abun sai yafi haka. Snn Baba Alhj har yanzu babu lafiya, gwara na cika masa burinsa na auri tilon diyarsa.
"Ammah na murmushi tace Alhamdulillah, naji da'din wnn zance naka Nazif Allah ya tabbatar mana da alkhairi, yanzu zan kira Hajiya Kariman mu soma shirye shirye, Engr ya amsa da ameen kafin ya mike jiki a sanyaye ya nufi sashensa..
*Kuyi hakuri da wannan babu yawa, zakujini later idan na sami chance insha Allah.... Luv you all*
👸🏻Queen Samy😍💄💋.........
🌗🌗🌘🌘 *Mallakin Waye*
29
"Zaune yake a Office dinsa sai juyi yake kan kujera, ba komai yake tunowa ba sai fuskan Deejah, musamman da yanzu daddynsa zaiyi aure, hakan ya tabbatar masa daddy ba son Deejah yake ba, mikewa yayi ya 'karasa jikin dan karamin fridge dake cikin office din ya dau goran ruwa, ya zauna can wasu kujeru ya soma sha yana lumshe ido, bai ta'ba tsintan kansa a yanayi irin ta yau ba tun tasowan sa,.
"Sadiqne ya shigo rike da takardu a hanunsa, koda ganin Irfan yasan he's in a good mood,
" Friend ka iso, Irfan ya fadi sanda ya mike ya nufo Sadiq sukayi musabaha, murmushi Sadiq yayi kafin yace " Architect I can see that you are in a good mood, are you guys started to get along.
"Murmushi Irfan yayi yace" I just don't know Sadiq bansan ta yaya zance mata ina sonta ba, nifa gani nake kaman saita raina ni. Kasan am not used to that love stuff, I'm new in the system.
"Sadiq yayi murmushi kafin yace" kar ka damu Architect that's norms, you'll soon get used to it, tashi muje Daddy na nemanmu, akwai Invitation Cards na magann daurin aurensa da zamu kaima jama'ansa. Mikewa Irfan yayi yana murmushi suka nufi Office din Engr.
"Kuttisi, Nadiya ta fadi cikin zuciyanta sanda ta shiga dakin Engr tana gyara masa, check ta gani na Naira miliyan hudu da note a 'kasan, _Ki saya kayan lefe_.
"Nadiya ta maimaita kalman yafi abunda yafi, yanzu da gaske de daddy aure zaiyi, shikenan za'a rabasu da daddynsu, haka kurum taji jikinta yayi bala'in yin sanyi, a sanyaye ta gama gyaran 'dakin ta fice zuwa nata 'dakin, tinda aka soma maganan bikin Engr Nadiya take avoiding mahaifin nata, gaisuwa kawai ke hada su, itakam ta tsani matan da daddy zai aura,.
"A 'bangaren Deejah ma jitayi kwata kwata bata son auren, ta rasa me hakan ke nufi, shi kansa Engr ko haduwa da Deejah bayaso suyi, snn ranan haka kurum ya sakata gaba yana bata hakuri, gaba daya ta rasa me hakan ke Nufi, hakan kuma yasata yin sanyi sosai, ko Irfan bata so hadu, ji take inama Engr yace ya fasa wnn aure, da tafi kowa farin ciki, gani take kaman idan su Nilam suka samu new momy zasu kyaleta, ita kuwa yaran sun shiga ranta.
"Gaba daya iyalen gidan Engr basa son wnn aure sai Ammah, harta su Hajja ma'aikata basa so sai Zulai wacce itake kulla komai wa Laila a gidan, dan da taimakon Zulai Laila da Hajiya Karima suka samu hakan su ta cimma ruwa. Shi kuwa gogan wato Irfan bai damesa daddy yayi aure ko kar yayi ba, shidai kawai yasan zuciyan Deejah *Mallakin Waye* shine babban burinsa.
"Ranar asabar 12 ga watan September aka daura auren Engr. Nazif Mumtaz (President M&M Builders) tareda amaryarsa Haj. Laila Ma'aruf. Aurene da ya sami hallartan manyan mutane kama daga kasashen ketare zuwa cikin gida Nigeria.
"Amarya Laila tasha huduban cikki burutsi wajen mahaifiyarta Haj Karima.
"Kina jina ko, sakin jiki zakiyi kija kowa jikinki a gidan, 'ya'yan sa kisannyanda zakimsaye zuyansu da kissa da kisisina da makirci da en dabaru irin tamu ta mata, kinsan Nazif babu abunda yake so kaman farin cikin 'ya'yansa da mahaifiyarsa , to ki kula da wann kina jina, Hajiya ta fadi tana mai jan kunne wa laila.
"Laila ta mirmusa tace Hajiya karkiji komai, ai na riga na shirya zaman gidan Engr, babu saki balle yaji, yawwa er garin, Hajiya tace tana me tafe hannu da laila, ina er kullin maganin da na baki,
"Laila ta ciro shi cikin daurin lafayyan ta tace kin ganta nan hajiya. Hajiya karima tayi shewa tace ashe er tawa er garice, toh kina jina, wnn kulli ki tabbata kinyi hayaki dashi kin turare illahirin jikin ki dashi a cikin dakin Nazif, toh fah shida kallon wata mace har abada.
"Laila tasa shewa suka tafe hannu.... duk wann abu a idon Alhj Ma'aruf akeyi, hawauene kawai ke fita a idonsa soboda zafin da zuciyansa ke masa.
"Laaaa kinga makirin nan wai kuka yake, hajiya Karima tace, tsuka laila tayi kafin tace bakin ciki yake mun dan ba shi ya haifeni ba,. Kece ma me biyesa Hajiya , ki daina basa magani ki karasa banza ki huta.
"Hajiya ta tabe baki tace kyale maye babu abinda zai iya sai hawaye..... wata shewan suka kuma sakawa kafin Hajiya tace muje yanzu zasu taho su tafi dake.... A parlor suka tarar da Aziza shigowarta kenan tana fadin momy masu daukan amaryan sun iso..... take wata kawar hajiya karima Hajiya Delu ta shigo tana guda...
"Har gidan Engr Aziza ta raka momynta burinta bai wuce ta zama close to Nadiya ba ko zata samu ta sami gurbi a zuciyan Irfan,
"Engr zaune gaban Ammah tayi masa nasiha sosai ba fuskan kowa yake tuniwa ba illa Fatima, Allah sarki Fatima Allah yayi ba matarsa bace, baisan sanda idonsa suka soma zuban hawaye ba, sosai Ammah ta tausaya masa da kanta ta rakasa har kofar sashensa, zuciyanta na cike da tausayin dan nata,
"Laila tanajin rufe kofa alamun shigowan Engr tayi saurin rage muryanta cikin waya, kai Safwan my Engr is here, you need hang up... Safwan ya kece da wata dariya yace, ni kinsan ma meke damuna, duk wann gyaran da kika sha wa tsoho akayi, I wish na sameki yanzu nan, kai tsoho zai kwasa ganima, toh nidai damuwata shine na mallaki kaso a M&M Bulders.... tsaki Laila tayi kafin tace zamuyi waya gobe, daga haka ta katse wayan, ta shiga duba fuskanta a madubi, bayan tayi duk abunda Hajiya ta umurce ta.
👸🏻Queen Samy😍💄💋........
[8/21, 06:18] Umar Dalha: 🌗🌗🌘🌘 *Mallakin Waye*
30
"Washe garin da Laila ta tare gidan Engr da sasafe ta tara gaba daya ma'aiktan gidan kowa taji aikinsa, kallon Deejah take cike da tsana dan Zulai ta fada mata komai gameda Deejah, tsayuwa tayi a gaban Deejah tana kare mata kallo, Deejah kuwa ganin irin kallon da Laila ke mata yasata dauke kai gefe.
"Deejah kike kowa? Laila ta fadi tana mai yatsina fuska, biyo ni zuwa dakina.... daga haka tasa kai ta wuce.
"Hajja da asabe suka kama baki suna masu zullumin yanda rayuwar gidan zata kasance. Zulai kuwa wani murmushin 'keta tayi tana juya ido.
"Kinajina so nake ki fito da kayana daga cikin akwatina sann ki jera minsu cikin wardrobe, idan kin gama ki share dakin nan tsafa ki wanke toilet, snn bana son 'kazantar ku ta masu aiki, ki tabbata kin tsaftace ko ina idan ba haka ba, sakewa zakiyi daga farko.
" 'kerere Deejah ke kallonta kafin tace" Anty nifa ba wnn ayyukan nake a gidan nan ba, ni aikina kulada yara ne, amma akwai su Zulai sune ayyuka irin wnn ya shafesu.
"Kanbuuu! Shaye da mamaki Laila ke kallon Deejah ita take fadawa wann ba aikinta bane, murmushin 'kasaita tayi kafin tace" I don't care ko wani irin aiki ne ya shafe a gidan nan, as far as you're a Maid here, kome nake son saka ki zan sa ki a lokacin danaga dama, kar ki mance I'm the Lady of this house dan haka sai abinda nace. If you don't want your self to fired, sai kiyi abinda na saka.... Har ta soma tafiya ta juyo tana watsa wa Deejah kallon 'kas'kasnci snn tace" this should be the first and last time da zan saka ki wani abu kimin musu. Daga haka Laila ta fice parlor cikin takun isa.
"'Kwalla ne suka ciko idon Deejah a hankali ta goge ta soma aikin da Laila ta sakata...
"Zama Laila tayi a parlor gamida kunna Tel ta soma kallon program din The Drs a mbc4, AC na dukan 'bargo da tsokarta yayinda drink me sanyi yake ajiye gefenta, sallaman Azee ne ya dawo da ita daga duniyan kallon da tayi nisa a ciki, da gudu Azee ta fado kan Laila ta rungume, "Momyyyyy, rungumeta Laila ma tayi kafin tace" Azee baby wani irin abune zaki zo min gida yau, jiya jiya fa na tare, turo baki Aziza tayi kafin tace" kai Momy keda kika ce da zaran kin tare nima zaki zo ki daukeni, toh naga bakizo ba shine nima na biyo ki, ga luggage dina can a waje, Uncle Saff ne ya kawo ni, momy wllhi na 'kagu na dawo gidan nan na soma rayuwa tareda Irfan Handsome,
"Laila bake sake take bin Aziza da kallo, kai amma ke wnn yarinya akwai ki da jaraban tsiya, kuma yanzu Hajiya tana gani kika taho harda kayanki gaba daya,
"Aziza tayi kicin kicin da fuska, haba momy, idan bakison ganina a gidan nane fine sai na tafi kuma wllhi bani 'kara dawowa.
"Jawota jikinta Laila tayi kafin tace" kwantar da hankalinki 'yar lelena, gidan nan gidanku ne, ki saki jiki tamkar na ubanki, shewa Aziza tasaka gamida tafe hannu da Laila tana fadin" Sai momyyyy,
"Laila tayi murmushi tace, ke ba wani momy dalla, sekace wata tsohuwa, from now on, kema Aunty zakina kirana, Aziza ta kuma saka dariya tace kuma fah hakane, ki ganki wazaice kin haife ni, gaskiya Aunty ne ya dace da ke... dariya suka saka gaba daya yauwa koke fa.... Kira Laila ta shiga rangadawa Zulai, nan da nan Zulai ta bayyana a gabanta, tana mai durkusawa hadi gaisuwa, Aziza ta kalli Zulai ta she'ke da dariya tace" shegiya zulai anyi kilin, ji yqdda fatarki ta canza, dariya zulai tayi tace" Anty Aziza kiyi shiru kar a jiyo mu kinsan 'ywr sirrine abin ba'asan nida Auntu munsan juna ba, Laila tace kawo mata drinks da snacks... babu musu Zulai ta wuce dan aiwatar da umarnin Laila.
" tadi suka ci gaba da yi ita da Aziza, Aunty yanzu ina ne dakina, gacan wani daki nan cikin sashena ba saiki zauna ba, girgiza kai ta soma kafin tace" no Aunty nifa nafi son daki kusa da Nadiya dan kinsan so nake ta zama best friend dina, so nake duk mu zama close da yan gidan nan sabida Handsome Irfan, murmushi Laila tayi tace sha kuruminki, duk yanda kike so zaki zauna gidan nan...Allah Aunty Aziza tace tana me zaro ido, tafewa sukayi dukansu biyu sekace wasu 'yan tasha....
"Engr ne yayi sallama ya shigo cikin shirin fita, take Laila ta mike tana masa sannu da shigowa, da fari'a saman fuskansa ya ansata, a'a yau daughter tazo mana ne.... murmushi Aziza tayi ta dur'kusa har 'kasa tana gaida Engr, Laila tayi caraf tace" Wllhi My Engr wai ta kasa zama babu ni shinefa daga kwana guda har ta biyoni, murmushi Engr yayi kafin yace" ai ni na dauka tun a jiyan itama zata dawo nan, ai yanzu batada gidan daya fi nan, ko ba haka ba daughter. ?.. murmushi kawai Aziza tayi tana sunne kai, kai kace me kunyar gaskiya ne, Laila ta murmusa tace kai Azee new daddy dinki na sonki...... Dai dai nan Deejah ta fito da Mop jkiknta duk ya ji'ke tayi gumi zata shanyawa.... " Kallo duka suka bita dashi, take taji kunyan yanayin data fito babu Hijabi ga Engr a wajen, dan durkusawa tayi ta soma gaishesa.... " A a Deejah ya na ganki haka da mop, ina sauran masu aikin gidan...... kan Deejah tayi magana Laila tace, wllhi my Engr ita tayi insisting wai zata ke mun ayyukan dakina ta karashe maganar tana me gallawa Deejah harara tace maza tashi mana kije ki shanya, mugun kallo Deejah ta watsa mata kafin ta mi'ke.... girgiza kai Engr yayi snn yace" no ba aikinta bane, aikin Deejah a gidan nan shine kula dasu Nilam, pls next time ki saka wata cikin sauran ma'aikatan, Azee baki sake take kallon Engr yanda yake defending Deejah.
"Laila kuwa ba'kin ciki ne ya turnu'keta a fili murmushin ya'ke tayi tace, toh my Engr amma ai yanzu kula dasu Nilam ya dawo hannu na tunda na iso, ko baka so na zame uwa a garesu ne...
"Cike da jin da'din kalaman Laila yace" gaskiya naji dadi, idan kikamin haka kin gama mun komai, maganarki haka ne, ke uwace a garesu, ya mike yana gyara agogonsa yace ni zan fita.
"Mikewa Laila tayi gamida saka fuskan tausayi tace, my Engr I thought yau bazaka fita ko ina ba, dan murmushi yayi yace" kiyi hakuri hakane ya kamata, na zauna maki a gida yau, fitan ne tazo min urgent, akwai kaya da mukayi ordering dinsu daga Turkey, toh an sami short shiyasa zan fita.
"Murmushi tayi tace" toh Alllah bada sa'a ya kuma dawo min dakai lafiya.
"Sosai yaji dadin addu'an nata har cikin ransa, har wajen motarsa Laila ta rakasa saida taga fitarsa, Ammah na kallonsu ta window din dakinta, wani dadi taji ya mamaye zuciyarta, yanzu kam tilon 'danta ya sami mai kula dashi....
"Sauri sauri ya gama shirinsa cikin suite dinsa, kana ganinsa kasan he's in a hurry, kaman ance ya kalli backyard ya hangota tana wanke mop, tsayuwa yayi yana kallonta, cikin takunsa na 'kasaita ya 'karasa gabanta, Deejah kam batasan da zuwansa ba saida ta dan razana, kallo daya ta masa ta sunkuya gamida gaishesa, a takaice ya amsa kafin yace" me kikeyi a nan,
"Kaman bazata amsa ba tace aiki nake, na gama ma. "Daure fuska ya kumayi kafin yace" yaushe kika soma irin wnn aikin a gidan nan, snn kinzo nan waje yanda securities zasu iya ganin ki babu ko mayafi, next time idan zakiyi aiki a nan make sure kin rufe jikinki da nayafi, tsayua kawai Deejah tai tana sauraren 'jarfin hali irin na Irfan...... Har ya soma tafiya ya juyo ya dan kalleta yace" kar ki sake aiki a nan, shiga ki kawo mun fresh drink ina mota ta, idan Amma ta tambayeki kice mata na makara, sauri sauri ya wuce parking lot.
"Mamaki ne ya ishi Deejah shi kuwa wn bawan Allah akwai krfin hali sekce wani ubanta, ji tayi bata iya masa musu, snn kwarjininsa ya zarce tunanin mai karatu.
"Sauri sauri ta wuce cikin gida, a parlor ta hadu da Nadiya saukowanta 'kasa kenan, Nadiya ta bita da kallo ganinta a jike kfin tace, Deejah yau ina kika shiga kika jike haka, nasan dai su Nilam sun tsufa a sch balle nace wasan ruwa kukayi, ta karashe maganar tana dariya...... Dariya Deejah ma tayi sanda suka nufi kitchen a tare kafin tace" wllhi Anty ce ta sakani aiki gyaran sashenta.... "Shaye da mamki Nadiya ke kallon Deejah hfin tace wacece kuma Anty. Ci gava da hada drink din Irfan tayi tana fadin" Aunty Laila mana, tsaki Nadiya ta buga tace, ai inajin sanda take assembly wa ma'aikata, toh wayce mata ke aikinki kenan, wllho yanzu zanje na sameta bazata sake sakaki irin wann aiki ba... Deejah ta nufi kofa tana fadin" wlhi idan kikaje mun 'bata kenan, gwanda ke master na jiran drink dinshi, daga haka ta wuce waje.
"Cikin motarsa ta sameshi sauke glass yayi ya kar'ba hadi da jifanta da wani asirtaccen kallo wanda ya saukar mata da shock, murmushi taga Irfan yayi ya furta thank you a hsnkali....sann ya juya starry ya wuce.. har ya bar wajen Deejah bata var kallon motar ba, yau Irfan was nice to her for the first time, ji tayi wani da'din da bata sn dalilinsa ba ya dirar mata....
"Duk wnn bidiri a idon Azee akayi shi, tana kallon irin murmushin da Deejah tabi motan Irfan dashi, kutumele si, wllhi bazata taba sakuwa ba, itafa sabida Irfan ta dawo gidan nan ba don kowa ba, wann shegiyar me aikin da ita take zance, a saba'in ta wuce sashen Laila taca kwal mata kira.....
0 comments:
Post a Comment