"A hankali ta soma bud'e idonta da suka mata nauyi tana me dafe kanta gamida jijjuya kan nata, ta yunk'ura zata tashi saiji tayi zafi sosai ta k'asanta, kasa d'aga koda k'afa guda tayi balle tayi tunanin tashi,... Take komai ya soma dawo mata kwanyanta, Jarrr ubancan wato Ahidjo fyad'e ya mata, wani wawan ihu ta sake wanda yasa Ahidjo fitowa daga bathroom babu shiri, ganinsa sindir da tayi gabanta yasata sake runtse idanunta tana ihu tana bige bige, ..... "Da sauri ya zuri towel ya d'aure k'ugunsa kafin ya k'araso yanda Azee ke kwance, rungumeta yayi sosai cikin jikinsa yana fad'in" Calm down baby, calm down take it easy......" Bangaje sa tayi kafin ta soma fad'in" dama wann shine k'udirinka akaina, dama kayi niyayyan ka rabani da abinda na jima ina tattalinsa wa masoyina ne, ka cuce ni I was stupid da na biyeka daka ce zaka taimaka min Irfan yasoni, dama wann shine taimakon, na tabbata koda ace Irfan zaiso ni bazai tab'a sona yanzu ba,..... "Ahidjo yayi saurin saka bakinsa cikin nata, da k'arfin gaske Azee ta turesa ta shiga goge bakinta, tana watsa masa mugun kallo take fa'din" ka cuceni ka cuceni mugu kawai azzallumi....." Sosai Ahidjo ya rungumeta cikin jikinsa kafin ya soma fad'din" ki saurareni kiji me zance, da kike ta cewa I raped you wayace maki fyad'e na maki, cikin sauk'i kika bani had'in kai mukayi komai...... "Cike da masifa take fad'in " Sabida ka bani kayan maye nasha hankalina ya gushe shiyasa na biyeka ai......" Enough!!!! Ya daka mata tsawan da saida ya firgita ta kafin yaci gaba da fad'in" Ke mahaukaciyar ina ce, did I force you to drink it, ai bani na na tilasta maki sha ba in the first place, kuma da kika sha am pretty sure yanzu kinji canji a jikin ki,....." yayi wata murmushin k'eta kafin yaci gaba da fa'din " Ke barin fad'a maki yanda muka fara ki bari mu ci gaba, idan kika k'i kin san zan sanarwa Irfan komai snn zai da'da tsanar da ya maki akan nada, and babu wanda zai yarda fyad'e na maki tunda ke kika kawo kanki....so just corporate baby and get what you want, idan kika amince mun kin samu Irfan an gama. Daga haka yayi ficewarsa zuwa parlor ya barta nan cikin k'unci
"Dafe kanta tayi ta shiga kuka me tsuma rai, tabbas abinda Ahidjo ya fad'i gaskiya ne, idan ya fada kowa ma a gidan zai tsaneta harta momynta balle Irfan da dama ya washeta, biyewa Ahidjo shine kad'ai mafita a gareta. Da wnn tunani ta yunk'ura zata tashi taji zafi, haka ta rarrafa ta shige bathroom dinsa ta kintsa kanta.....
**************************
*Police Station Wuse 2, Abuja*
"Suna zaune shida Engr a reception bayan Engr yayi filing case d'in b'atan Azeeza, har no motan Laila data fita dashu da time din da suke expecting ta fita Engr ya fad'i....
"'Dan gajeren tsaki Irfan yayi sanda wayarsa ta soma k'ara kafin ya matsa gefe yana amsa wayan, Sadiq ne ya kirasa bayan sun gama waya da Sadiq Deejah ta kirasa ta soma tambayarsa ko an samu Azee, " So you also believed that she was lost, babu wani b'atan da tayi kawai dai yawonta ta tafi, ya fadi cikeda b'acin rai,
"Haba ya Irfan don't talk like that, ina zataje ta zauna har dare, da gaske b'ata tayi, wait a minute...... "idan kace haka kenan muma lokacin da muka b'ata yawonmu muka tafi.? "A hasale ya soma fadin karma ki hada b'atanmu da nata, two different things ne, ke da kanki kikace ba ki ganta a sch ba, toh ina taje inba yawo ba. " Deejah ta sauk'e ajiyan zuciya kafin tace" dukda haka dai idan mutum ya fita tofah sai Allah ya dawo dashi lafiya, mudai muyi addu'an Allah sa tana cikin k'oshin lafiya,..... " Gajeren tsaki ya kuma yi kafin yace" bari ku gani babu b'atan da tayi, am quite sure zata dawo da kanta, ... Zatayi magana ya canza zancen zuwa na soyayya na suka b'uge da hiran soyayyar su har ya d'an sami sauk'in haushin da yakeji.....
" Yana gama wayan ya dawo yanda Engr yake, sauro duk sun soma cizonsa abunka da ajeboter take jikin ta soma canza launi, "Daddy pls mu koma gida haka tinda munyi filing complaint besides yarinyar nan fah yawonta kawai ta fita tunda kowa ya sani ba sch taje ba,...." Ya isa haka Irfan Engr ya daka masa tsawa, kafin yaci gaba da fad'in" bana son irin haka yarinya ta b'ata kuma kana cewa yawonta ta tafi, zuwa anjima securities na Nile din zasu kawo CCTV information mu gani idan ta tafi sch, munddin taje makarantar kuwa zasu fito mana da 'yar mu dan k'ara zan shigar dasu.
"Irfan dai baice komai ba, Amma zuciyar sa ta ci gaba da ayyana masa Azee yawonta kawai ta tafi, gaba d'aya ji yayai ta k'ara sane masa.
_8:39pm_
"Daidai lokacin da securities na Nile University suka kawo CCTV information nan aka soma playin, Engr da sauran officers din suka maida hankalinsu kan video din yayinda Irfan ya koma gefe yana ci gaba da danna wayarsa.
"K'arara motar Laila da Azee a ciki aka nuno ta shige cikin Nile.... jim ka'dan aka nuno ficewarta daga makarantar......" Engr ya sauk'e ajiyan zuciya, tabbas Aziza ta fita daga makarantar toh ina ta nufa? Wnn shine babu wanda yasan amasar. Engr yayi godiya sosai wa securities din Nile yanda sukayi cooperating kafin suka wuce.
"K'arfe 9:00pm daidai Engr da Irfan suka bar station din kan idan an sami wani labari gameda Azee zasu kira Engr. Sosai Engr yayi masu godiya bayan ya cikasu da arziki.
"Ran Irfan idan yayi dubu ya b'acu kan wnn k'azamar yarinyar aka fito dashi da daren nan, dabadon Daddy yake tu'kawa ba da tuni ya fincike motar, haka ya rink'a sak'e sak'e a zuciyarsa har suka isa gida.
"Suna isa Laila ta fito a guje tana tambayansu, Ammah da Deejah dasu Hajja suka rufo mata baya, "Dan takaici Irfan kam wucewa yayi sashensa ba tareda yako tsaya ba.
"Suna zaune parlorn Engr sai faman lallashin Laila yake, I zuwa yanzu harta su Nadiya sun shiga damuwa, suna a haka sai jin Sallama sukayi...." Ahidjo ne ya shigo Azee na biye dashi,
"A tamanin Laila ta isa ta rungume Azee dukansu biyun suka fashe da kuka, Ahidjo ya k'arasa can gefen Daddy ya soma gaishesa, da mamaki Engr yace" Ahidjo ina ka samo ta??
"Ahidjo kansa na k'asa uwa mutumin arziki ya soma sharo k'arya yana juyewa.
"Daddy I found her can wajen gari, amrobbers sunyu mata robbery, sun kwace motarta and all, I was shocked lokacin datace min ita 'yarka ce, sai nace mata nima kai baba na ne, so that's why I brought her here, bayan na kaita asibiti anyi treating nata, ....
"Illahirin mutanen parlorn godiya suka shiga yiwa Ahidjo babu kaman Laila da Engr. Ahidjo ya saci kallon Azee dake kwance cinyar Laila ya kashe mata ido d'aya, nan ta mayar masa da martanin alamun yayi k'o'kari. Daga haka ya mike yana fadin" babu komai daddy barin duba Irfan.
"Azee ta kuma shigewa jikin Laila tana cije cijen leb'e sabida azaban ciwon da Ahidjo yaji mata.
"Police ne sukayi wa Engr waya cewa an sami motan a so so place, yanzu haka suna nan zuwa.
"Engr ya kuma masu godiya gamida fada masu an samu yarinyar.
👸🏻QueenSamy😍💄👄...........
[8/22, 14:45] Umar Dalha: 🌔🌔🌘🌘 *Mallakin Waye*
45
*Na Sameena Aliyi*
"Kallon mamaki Irfan yabi Ahidjo dashi kafin yace" itama club d'in kenan ka ha'du da ita kuka gama watsewarku a can snn ka d'auko ta ka kawo ta gida kuka shera k'aryanku, Am I right? Ya k'arashe maganar yana mai kallon Ahidjo da witsiyar ido...."
"Haba Irfan "what the heck are you talking about, why on earth could make me lie to you, ka tuna fa we've been friends for long time kai our friendship has gone beyond ordinary friendship tinda mun zama kaman 'yan uwa you're my brother from another mother, wllhi Irfan this is whole truth, I found her wajen gari, and she's been robbed.......burki Ahidjo yayi da maganar tasa kafin yace" wait a second, why do you even care, meyasa kake tambaya kodai sonta kake???....." wani mugun harara Irfan ya watsa masa kafin yace" Watch your mouth guy, ko na rasa macen so ai bazan so that thing ba, kai I've never seen a disgusting being kaman ta ba tunda nake a rayuwata, the next time da ka sake hadani da yarinyar nan you gonna be sorry, ...
"Murmushi Ahidjo yayi kafin yace" naga dai tafi yarinyar da kake nema asali da kyau......" Bai gama rufe baki ba Irfan ya kaimai naushi sai a bakinsa...." huci yake kaman rud'en dake tafasa bisa murhu...." Dukda jini dake bin bakin Ahidjo bai hana Irfan sha'ko wuyansa ba, yana huci yake fad'in" Didn't I warn you idiot,......" Securities ne suka nufo su a guje da shike a farfajiyan gidan suke tsaye jikin motar Ahidjo, take Ahidjo ya fizge wuyan rigarsa yana fad'in" Let go of me, Irfan ya kalli securities din yace su koma bakin aikinsu ba fad'a suke ba norms ne 😂, babu musu suka koma.
"Ahidjo yasa hannu yana d'an goge jinin kafin ya d'ago yana duban Irfan yace" You need someone to tell you the truth Irfan, kar ka bari soyayya ya rufe maka ido, how on earth zaka soma soyayya da mere girl irin Deejah yarinyar da baka san asalinta ba for goodness sake, all you know about her is that daga Orphanage take, you don't know her real family who knows ko street girl kake nema, you and she are from different world Irfan, ka dubi girman family dinku, ka dubi arziki irin na mahaifinka, you're his eldest son you suppose to marry from responsible family, wanda za'ayi recognizing nasu, duk mutanen da za'a gayyata daga k'asashen duniya ka rasa wacce yarinya zaka kawo of all people duk matan da suke dying akan ka turawa larabawa kai har koreansa kanada masu sonka sai wann street girl din... haba ..... haba Irfan don't be a disgrace to your Family..........."ENOUGH OF THIS Ahidjo!!!!! Ya ishe ka haka, What is your stress da abun da ya kasance zab'i na, don't make me hate you for the rest of your life, Duk abubuwan da ka lissafo akan Deejah haka na ganta kuma nake sonta, it doesn't matter her status in life, what matters here is that I loves her..... I love her with all of my heart and nothing will change that love that I feel for her, snn duk emmatan da kake k'irgowa basu gaba na, ni ita na gani kuma nake so, fatana burina ta zamto mata *Mallaki Na*..... "So idan kana so relationship din mu ya dore kar ka kuma fad'in nasty things about her or else......" ya dan ja birki kafin yace " Ahidjo just leave pls, ka tafi dan Allah befor I hate you.
"Kad'a kai Ahidjo yayi kafin yace" Irfan bazan tab'a gajjiya da fad'a maka gaskiya ba..... don't make a wrong decision, choose wisely......● daga haka ya bud'e motar sa ya wuce●●●●●●●● Duk wnn abun da akayi Ahidjo yayi dialing wayan Azee ta gama sauraren komai.....
"Har ya fice daga gidan Irfan be dena bin motarsa da kallon mamaki ba, ikon Allah banda d'aurawa kai damuwa ina ruwansa da matar da ya za'ba, gajeren tsaki yayi gamida girgiza kai kafin ya wuce sashen Ammah.....★
"Azee na gama jin wayan nan wani ihu ta kurma gamida zubewa k'asa ko zafin ciwon dake jikinta bataji ba, nan kuwa jini ya shiga bin k'afafunta...... "Shigowar Laila kenan a rud'e taga jini na bin k'afafun Azee burki tayi sabida abinda idanunta ya gane mata k'rjinta na faman lugude...... _Toh fa wata sabuwa inji en chacha😂_
"Ammah na zaune saman darduma ta idda shafa'i da wuturi yayinda Deejah keta faman jera mata kayan guga cikin wardrobe Irfan ya shigo da sallama, Deejah ce kawai ta amsa sallaman dan Ammah na tasbihi lokacin......" Sak'o suka aikawa junan su ta idanu kafin ya k'arasa ya soma tayata jeran kayan..... "Dan marairaice fuska tayi alamun ya daina tana mai masa nuni da Ammah dake lazimi.
"Satan kallon Ammah yayi dashike can gefe dasu take kafin ya matso kusa da Deejah sosai cikin sigan rad'a yake fad'in" Why? Bakiso Ammah ta gano ki ne, kina son mata kwacen miji......" Deejah ta turo baki saida ta saci kallon Ammah ta tabbatar hankalinta baya wajensu kafin tace a hankali" pls mana ya Irfan Ammah might hear us, ni dai babu ruwana....." Yanda tayi maganan sosai ta bawa irfan dariya, yana k'ok'arin maida dariyan Ammah ta mik'e tana k'ok'arin linke darduma.... da sauri Deejah ta k'arasa ta karb'a tana fad'in, Ammah barin linke maki.
"Ammah na murmushi tace"Khadeejah baki gajjiya,..... "Ammah takai dubanta ga Irfan wanda take kan masa magana amma inaa hankalinsa na kan Deejah duk wani movement nata yana kallo gashi sanye take cikin doguwar rigar atamoa wanda ya zauna d'aram a jikinta sai d'an k'aramin vail a wuyanta, sosai ta tafi dashiii...." Gyaran murya Ammah tayi kafin ta kuma kiran sunansa..... " Da sauri ya amsa yana mai sosa k'eya.
"Deejah da gaba d'aya kunya ya lullub'eta sad'af sad'af ta fice.....
"Ammah ta k'araso ga Irfan dake faman cewa" Granny ashe kin ida sallahn......" kunnensa ta kama har suka isa bakin gado ta masu masauk'i kan gadon, irfan na rik'e da kunnensa yana fad'in" Auchhhh Granny it hurts......" Sake kunnen tayi kafin tace" Hankalinka yana kan soyayya yaya kuwa zaka san na iddah.
"Hannunta na cikin na Irfan tana kallonsa fuskanta dauke da murmushi tace" You loves her right???.,...... "kafin yayi magana ta kuma cewa" Yeah I know you do, you do loves her, am so happy for you child, Deejah yarinyar arziki ce Allah ya tabbatar mana da alkhairi.... "Rungume Ammah Irfan yayi cike da farin ciki wanda saida ya tuno masa da mummyn sa.....
"Tambayanki ne dan ubanki wani 'dan shegiyan ne kika bud'e masa cinyoyinki.....Cewan Laila bayan ta shak'e wuyan Azee...
"Da kyar Azee ta kwaci kanta kafin tayi wa Laila bayanin komai......" Zama dirshan Laila tayi a k'asa ta shiga jero salati tana tafe hannu....Na shiga uku na lalace" yanzu Aziza dama wayon banza ne gareki, shukenan ya maki wayo ya raba ki da abunda bazaki tab'a samu ba koda da kud'i ne. To kuwa ya tsokalo wutar da bazai iya kashewa ba, sai naje har gidan ubansa naci ubansa tunda ya lalata min 'ya...... "cikin sauri Azee ta katseta da fad'in " Ki rufa mun asiri momy wallhi yace idan magann ta fito zai fadi komai, kuma dole Irfan ya tsane ni har abada, snn babu me yarda damu,......
"Wai ma miye abun damuwa momy, tinda dai yace zai min hanya na sami Irfan ai shikenan ko raina ne aka ce na mik'a sabida Irfan zan mik'a balle....... "bata gama rufe baki ba Laila ta bige bakin tace" Rufe mun baki sokuwar banza kawai, ki shirya da sassafe zan kaiki asibiti...... daga haka ta fice zuciyarta naci gaba da zogi. Wani b'angare na zuciyanta na fad'a mata" Gado tayi, barewa bazatayi gudu 'yarta tayi rarrafe ba.
★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★
*A week later*
"Zaune yake cikin office dinsa wanda yake a parlorn gidansa, gaba d'aya ya kasa tab'uka komai tinda Ammah tazo masa da maganar Irfan da Deejah, " wai meke faruwa dashi ne, deep inside his heart ba son Deejah yake ba, amma ko kad'an baijin yana son aurenta da Irfan shin me hakan yake nufi, kai he needs to have some time and talk to his son, da wann tunani ya dauki waya ya kira Irfan yace ya shirya masu dawaki su fita zagawa.. Da shike Engr mutum ne me son doki tun yana US yake da manyan dokuna irin na turawa wanda yakan fita kilisa ko polo dasu.
"Daddy naji dad'in fitowa kilisa ni da kai, mun jima bamu samu time haka ba, cewan Irfan yayinda suke kan sukuwa bisa doki a hankali.
"Murmushi Engr yayi kafin yace" Son I know you must be missing those moments da nakan dauke k gaban doki tun muna _Los Angeles_.......
"Irfan yasa hannunsa ya goge hawayen da suka zubo masa kafin yace" when mummy was still alive, "Engr ya juyo ya kalle sa take tausayin d'an nasa ya kamasa, sauk'owa yayi bisa dokin dama already sun iso wani park, kama dokin Irfan yayi ya taimaka masa ya sauko ya cire masa helmet din dake kansa shima ya cire nasa kafin suka k'arasa kan wani dogon kujera me daukan sama da mutum biyu suka zauna.
"Har lokacin Irfan na share fuskansa......" Engr ya rungumesa take shima yaji k'walla na nema ciko masa ido sabida tausayin d'an nasa, a hankali ya soma lallashinsa. " It's Ok Son, dukanmu munyi rashin Khadeejah Allah yayi mata rahama, she's in a better place right now.
"Daga kansa yayi kafin yace haka ne daddy I love you,.... I love you too son.
"Daddy meyasa 'yan uwan mummy tinda ta rasu basu tab'a zuwa Nigeria ko sau d'aya sun duba mu ba......." Take annurin fuskan Engr ya dauke cak..... Irfan ya sake maimaita masa tambayan da cewa" Daddy meyasa tun tasowarmu bamusan dangin mummyn mu ba, tun lokacin mummy na raye idan na mata maganar fada take min why daddy...." Mikewa Engr yayi kafin yace" Enough Irfan, zan gaya maka, but this is not the right time, we are here to talk based on another issue.
"Irfan bana son aurenka da Deejah, ka nemo wata yarinyar na aura maka........" Kaman sauk'an aradu haka Irfan yaji kalaman mahaifin nasa yayinda k'irjinsa ya koma tamkar an d'aura dutse.......●●●●
*Tofah masu karatu muje zuwa*
👸🏻QueenSamyNovels😍💄👄....
[8/22, 14:46] Umar Dalha: 🌘🌘🌔🌔 *Mallakin Waye*
46
*Na Sameena Aleeyou*
" K'irjinsa ne yaci gaba da dukan tara-tara sanda ya dago yaga fuskan Dad dinsa babu alamun wasa. Da k'yar Irfan ya iya lalub'o kalamai ya soma fad'in" Daddy pls don't do this to me, I love Deejah...... I love her with all of my heart. I can't bear loosing her...." Enough!!! Engr ya daka wa Irfan tsawan da yasa yin shiru babu shiri.... "
" Irfan na riga na gama magana, kaje ka samo wata na aura maka but Deejah,......"Daga haka Engr ya wuce ga dokinsa ya gyara linzamin ya soma tafiya....
"Tashin hankali wacce ba'a saka mata rana, jinsa yake tamkar a wata duniya..... da kyar ya iya mikewa dan barin wajen....
"Tunda Engr ya isa gida zuciyar sa ta shiga tuhumansa kan bai kyautawa Irfan ba, take kuma shawarin matarsa Laila ya fad'o masa" _Irfan shine danka na fari bai kamata ka barshi ya auri wacce batada asali ba, wata rana idan baka nan irfan shine magajinka, shin zaka so manyan mutane abokan ka suyi tattaki daga kasashe zuwa auren danka da matar da batada asali balle tushe_........ " Take ya toshe kunnuwansa dan kuwa gaba d'aya ji yayi bai son tuno kalaman Laila, kai duka wann abu marassa kyau da Laila ta fad'i gameda Deejah ko kad'an bai rage abunda Engr keji akanta ba, _Toh wai me Engr yake ji gameda Deejah ne_..... "Shi kansa Engr Nazif bashida wann amsar.
"Kaman wanda aka jefo shi haka Ammah ta gansa tsaye akanta...." Irfan lafiya meke faruwa, ta tambaya sanda ta k'arasa ta rik'o hannunsa....." Rungume Ammah yayi sanda yaji hawaye na k'ok'arin bin k'uncinsa" Ammahhhh ki fada mun meyasa Daddy baiso na auri Deejah pls Ammah..... yayi maganar cikin rawar murya.
"Kalaman Irfan sunyi matuk'ar bawa Ammah mamaki, yanda take ganin Engr ya rik'e Deejah tamakar 'yar da haifa batayi tunanin za'a sami mishkila daga garesa ba, mussaman duba da yanayi na hankali da nutsuwa da Deejah keda shi. "Ammah ta rik'o hanunsa suka zauna bakin gado, ta rik'e hannayensa sosai cikin nata kafin tace" Irfan ta yuwu Daddynka ya hango wani abu damu bamu hango ba, child kayi hakuri........" bata gama rufe baki ba Irfan ya mik'e idanunsa sun kad'a sunyi jajur haka fatar jikinsa tamkar jan gauta haka ta koma....., kallon Ammah yake yana girgiza kai kafin ya soma fad'in" So you don't want my happiness too, you want me to live a miserable life.... Granny I thought you loved me, I thought you'll be by my side, I thought I could feel presence of my mum with you... ashe ba haka bane, I was wrong all this while danayi tunanin kinfi kowa understanding dina, how I wish my was here or even her own mother or maybe her relatives nasan su zasu fahimce ni bazsu taking side din daddy ba,......" Shut up Irfan Ammah ta katse sa!!!!
"Irfan ya d'ago ido yana kallonta tun tasowar sa bata tab'a mas irin wnn tsawan ba. "Yana huci siririyar hawaye take bin idanun sa guda d'aya. " Gyada kansa yayi yana murmushin takaici kafin yace" Na dauka idanazo maku da batun aure zaku saurare ni and you'll be happy, but I was wrong.
"Yasa bayan hanunsa ya goge hawayen da ys sauk'o masa kafin yace" Zan tafi zan koma loss Angeles, I can't stay here any long...." Zai fice Ammah tayi saurin rik'osa hawaye na k'ok'arin kufce mata take fad'in" No Irfan dan Allah kr kuma tafiya ka barmu, bansan meyasa Daddynka bai son aurenka da Deejah ba,,,, she's not the only girl ka nemi wata koma er gidan waye I assure you zansa ya aura maka ita.....
"Girgiza kai ya soma yana k'ok'arin fizge hanunsa yake fad'in " Granny I LOVE ONLY DEEJAH....... JUST HER ONLY HER. Can't you understand, zan tafi zan nemi 'yan uwan mummy na duk yanda suka shiga I know they will support me. Daga hak ya fincike hanunsa daga rik'on da Ammah ta masa cikin sarsarfa ya isa k'ofa tana kiransa ko tsayawa beyi ba,.
"Daga yanda suka lab'e sun gama ganin komai, Lail ta shek'e da dariya tace ashede maganin malamin nan aiki.... Azee da damuwa ya d'an nuna a face dinta tace" momy what if he leaves yaya zanyi na shiga uku, kinga yanda ya koma tamkr damisa anya zaiji lllashi ya yarda ya zauna, karfa ya tafi American. ?......" Murmushi Laila tayi ta shafi kan Azee tace" yaro dai yaro ne, Azeeza ki kwantar da hankalinki malam na kan buzu ya tabbatar mana babu yanda Irfan zaije, haka dai zasu gama fadace fadacensu da iyayensa har ya sauko tinda ya ksance yaro mai biyayya dukda kafiya da taurin kan da yake dashi.... Azee ta sauke ajiysn zuciya... ganin Ammah da Engr sun nufi sashen Irfan hankai a tashe yasa su saurin juyawa da niyyan barin wajen, saiji sukayi Azee ta buge tukunyar da Malam na kan buzu ya basu, yana isa k'asa kuwa ya fashe tushhhhhh!!!! Wani ihu Azee ta sake Laila tayi k'arfin halin toshe bakinta dukda itama masifan tashin hankaline ya ziyarceta, dan kuwa na kan buzu ya sanar dasu kwaskwan nan tana fashewa to babu abinda zai hana auren Irfan da Deejah......
★★★★★★★★★★
"Da k'arfi Engr ya shiga doka k'ofan Irfan yana kiran sunansa," Irfan!...Irfan!! Son open this door........
"Jifa da kayans yaci gaba da yi daga cikin sip yana cusawa cikin trolley... " kome ya tuna kuma sai gani nayi ya nufi k'ofan jiki a sab'ule.... ysna budewa ya koma cikin dakin
"Ammah da Engr sukabi d'akin da kallo yanda duk ya haustina yayi fashe fashe. Bai ce masu komai ba sai kobawa da yayi yaci gabs da hada kayansa......" Irfan will you stop this nonsense and listen to me!!!!"" Engr ya fadi cikin daka tsawa.
"A hankali ya dago kansa wasu hawayen na k'ok'arin zubo masa yake fad'in" Daddy I need to go and find my mum's relatives tinda ku kunk'i gaya mana yanda suke, idan zan iya tunawa lojacin mummy tana raye ta tab'a cemun ita er asalin Lebanon ne, garin Berut, zan je na neme su,... su nema mun auren tinda ku....."Marin d Engr ya kifa masa ne ya hanasa k'arasa maganar, da sauri Ammah ta k'araso ta rungume Irfan......."Ya isa haka, ya isa Nazif, kar ka sake tab'asa, idan baso kake yayi irin rayuwar da kayi a baya ba toh ka aura masa wacce yake so,,.... " Cikin kunan rai Engr yake fadin " bazan aurawa d'ana yarinyar da bamusan salinta ba, Ammah pls kar ki biye Irfan har yanzu yaro ne....."Kasacewa komai Irfan yayi sai kallon mamaki da ysbi daddy dashi, watarana idan daddynsa yayi wani abu tamkar bashi ba.....
"Cikin zafin rai Ammah take fad'in " idan har Khadeejan yanzu batada asali ka fada mun shin khadeejah ta farko kasan asalinta? Shin kasan iyayenta ne har ka yarda ka aureta.....Kasa karasawa Ammmah tayi dan kuka dake shirin kufce mata, da sauri ta fice daga dakin Irfan.
"Engr ya dago yana kallon Irfan duk shima jikinsa yayi sanyi, kirjinsa na dukan uku da kyar ya iya furta, "Irfan.........." Irfan yayi saurin katsesa da girgiza kai kifin ya soma fadin cikin rawar murya irinta me kuka"
"Daddy dama mahaifiyar mu batada asali..... daddy dama wann ne dalilin da yasa muka kasa sanin dangin mahaifiyarmu tun tana raye.... daddy dama wnn ne dalilinku na b'oye mana......
"Girgiza kai Engr ya soma cikin rawar murya yake fad'in" Irfan mahaifiyar ku tanada asali, mahaifiyar ku tanada asali. Da kyar ya k'araso yanda Irfan yake su duka biyun suna kuka.
"Hannun Irfan ya rik'o suka zauna bisa sofa kafin ya soma fad'in " Son yau zan baka labarin sirrin da muka birne maku ya goge hawayen idonsa kafin ya soma fad'in"
" Tunda nake da mum dinku ban tab'a sonta ba, macen da na so a rayuwata guda d'aya ce tak, kuma tunda na rasata ban kuma son wata ba, d'iyar Baba Alhjai 'yar uwar Laila FATEEMAH itace macen danaso da duka zuciyata,
"Mahaifiyar ku....... Sai kuma ya danja fasali hawaye na k'o'karin ciko idonsa. Irfan ya bude idanunsa sosai yana sauraren me Daddy zaice.
"Engr ya share hawayen idonsa kafin yaci gaba da fad'in " Mahaifiyar ku aiki take a wani resturant dake cikin makrantar mu a lokacin, kullum idan naje sayan abinci ita ke kawo mun, nasha mamaki ganin ita kdaice musulma cikin masu aikin wajen, kullum zaka ganta cikin yalwateccen kaya snn gashinta a rufe ba kaman sauran ma'aikatan ba,
"Toh ana nan wata rana na shigo cin abinci sai na tarar shugan wajen wato me rusturant din yana faman cin zarafinta..... yana k'o'arin rabata da suturunta wai bata kawo masa customers, ma'ana bata zan ra'ayin masu zuwa cin abinci.
"A ranar nayi duka ma baturen nan dan kuwa duk yanda naga za'aci zarafin mace tofah sai yanda k'arfina ya k'are..... a takaice dai na kwaci yarinyar nan a wann rana. Na kafa masa doka kan cewa duk randa ya takurata tofah zan hada sa da hukuma. Kasan bature idan
Kwai abinda yake tsoro tofah hukuma ne. Da wnn yarjejinya muka rabu.
"Bayan wasu kwanki naje wann resturant har sau kusan biyar bani ganinta, koda na tambayi wata daga cikin ma'aikatan sai cemun tayi ai an koreta. Ban kwo komai ba a lokacin nace yamafi mata sauki..
"Toh bayan kaman sati na ganta a ksan gada tana kwance dashike watarana da kfa nse shiga cikin schl dan gidanmu babu nisa da sch.
"Tunda ta ganni naga t soma murna, toh nan dai ta bani labarin itama zuwa tayi illegally ma'ana ba ta amintecciyar hanya take zaune a US ba, koda na tambayeta dalili sai ta fashe mun da kuka, haa nayita lalashinta, krshe har ta hakura ta bani kabarin knta, yanda ta sanar dani iyayen mahaifiyarta sun kasance masu kudi sann ita kadai Allah ya basu, sun rasu sun bar mata tarin dukiya, tanda masoyi wanda ashe dan kudinta yake sonta, yan uwanta basuso aurenba amma kasancewar ita tanaso dan haka suka aura mata shi, koda ta haifi Khadeejah suka hade baki suka kasheta shida matarsa dama batasan yanada wata mata ba, nan sukayita gallazawa khadija azaba har kawo girmanta yanda mahaifinta da kishiyar uwarta suka tassama kasheta ta tsere ta biyo jirgin ruwa ta taho US......labarin gallazawan da wad'an nan bayin Allah sukayi wa Khadjia babu dadin maimaitasa. Na tausaya mata sosai, dan kuwa taga rayuwa.
"Da kaina na kawota gida wajen Ammah, na bata kabarin ta, Ammah ta tausaya mata snn ta riketa tamkar 'yar da ta haifa, toh ana a haka Ammah ta matsa sai na auri Khadeejah ganin yanda take bala'in sona, ni kuwa a da nayi kudirin nida aure har abada tunda ban samu Fateemah ba, da matsi da naci dai har na yarda na aureta... tunda muke tare ban tab'a fada mata kalman so ba koda daidai da rana guda ne, tayfarkin hakan ta ksance yafi sau babu adadi amma hakan bata kasance ba, Khadeejah tana mun son da bansan adadinsa ba, a haka har taifa min ku, yanda ta rok'eni kar na nunawa yaranta bsna sonta, na kuma mata wann alk'awari. Toh har bayan ta haifi Nilam randa zata bar duniya saida taso na fada mata kalman so "amma ban fad'a mata ba dan ban kawo mutuwa zatsyi ba......... " kuka me k'arfi ya kufce wa Engr...... "Irfan wanda shima hawayenne ya wanke masa fuska da sauri ya rungume dad dinsa yana kuka, saida sukayi mai isarsu babu me iya lallashin kowa kafin Engr yaci gsba da fad'in " Khadeejah ta mutu bataji wann kalma na so a bakina ba, nayi kukan rashinta nayi kuka sau babu adadi. Shiyasa nayi alk'awarin son abinda ta haifa ta bari da iya abinda na *Mallaka* shiyasa na dauki son duniya na daurawa 'ya'yanta shiyasa nayi devoting my entire life to her children...... "Shiru sukayi na dan lokaci yayinda kowa a cikinsu ke sharan kuka.
"Ammah dake zaune a parlor ta gama jinsu, ta share hawayen da ya wanke mata fuska, hakika yau mutuwan khadeeja ya zame mata sabuwa, yarinyar arziki wacce a iya zamansu bata tab'a sab'a umarninta ba koda da rana guda. A haka Ammah ta shigo ta zauna a tsakiyan Engrr da Irfan ta dafe kafad'unsu.
"Da kyar ta daidaita kanta kafin ta soma lallashinsu. Gaba daya suka rungume juna.
"Addu'a sosai Ammah tayiwa mummyn su irfan gaba daya suka amsa da ameen Ammah.
"Engr na kallon Irfan yana murmushi shi kadai yake ayyanawa a zuciyarsa _"koda ace son Deejah yake toh kuwa hak'ik'a zaiyi yak'i da zuciyarsa ya kalleta a matsayin d'iya danta kasance da Irfan, hak'ik'a farin cikin y'a'yan sa shine nasa_.
"Dafa kafadan Irfan yayi kafin yace" Son na amince ka auri Khadija na amince Son...... "
"Kallon Engr Irfan yake full of surprise kafin ya mike yana fadin " Really daddy, you mean ka amince na kasance da farin cikin rayuwata. Gyada masa kai Engr yayi yana murmushi kafin yace" yes Irfan na amince zan cikawa Khadeejah burinta na sanya yaranta cikin farin ciki ko yaushe, forgive me Son akan abunda na maka earlier I lost my mind ne that's why, I don't know why did that......... "Irfan kam baisan sanda ya rungume Engr ba yana masa godiya"
"Ammah ta goge hawayen idonta tana kallonsu cike da si kauna, kaikace yaya ne da k'ani.
"Ya karaso ya rungume Ammah kafin yace" Ammah I'll be with her forever...... Murmushi Ammah tayi ta shafi kansa kafin tace " farinckinku shine namu Irfan.
"Engr yana kallonsu yana murmushi ya k'araso ya dafa kafadun Irfan yace" suna hada ido Irfan yaji kunya ya dan suke kansa k'asa yana sosa k'eya.
"Murmushi Engr yayi kafin yace zamuyi maganar ranar auren da Granny dinka kaji, for now ka mayar da kayanka mazauninsu.
"Rungume Engr Irfan ya kuma yi yanai masa godiya.
"Ammah ta jawo kunnesa tana fadin " ko kunyata bakaji ko oya wuce bathroom kayi wanka ka hau doki...... zaiyi magana ta mika masa towel ta jefa sa cikin toilet. Tana murmushi sanda ta jiyo shi yana fad'in " I'mmmmmmmmmmm in looooooooooveee.
"Murmushi kawai tayi ta shiga tattara masa dakin tana fadin "Silly boy hadi da girgiza kai......
👸🏻QueenSamyNovels😍💄👄...........
[8/22, 14:47] Umar Dalha: 🌖🌖🌗🌗 *Mallakin Waye*
47
*©Sameena Aleeyou*
"Na shiga uku momy yanzu inaji ina gani shegiyar yarinyar nan zata auri Irfan..... gaskiya momy bazata saku ba, ni danaga auren Irfan da wata ai gwara naga mutuwata.. cewan Azee da damuwa ya nuna k'arara a fuskarta.
"Murmushi Laila tayi kafin ta dafe kafa'dun Azee tace" yaro dai yaro ne, idan banda abinki ina kika tab'a ganin anja damu, ki daina sarewa kinaba dani Azee saikace ba d'iyar Laila jikan Hajiya Karime kike ba, ki kwantar da hankalinki, idan sunsan wata basu san wata ba, idan mun b'ulla masu ta sihiri da asiri baiyi aiki ba sai mu b'ulla masu ta makirci kissa da kisisina...." shiru tayi na d'an lokaci kafin ta d'ago tana duban Azee tace " yawwa ina abokin Irfan da kwanaki ya amshe pride d'inki na d'iya mace.
"Azee ta d'an tab'e fuska kafin tace " wai Ahidjo tabb niko me zanyi dashi...
"Laila tayi murmushi kafin tace" ai kuwa dole yanzu yayu mana aiki tinda dama kince son Deejah yake...." tsalle Azee ta daka kafin tace " ai kuwa nama tuna momy turn dinsa yazo dole ya bani something in return na abinda na basa kwanaki, dole yasan yanda za'a k'ulla sharri wa jarabebbiyar Nanny din nan.
"Dariya Laila tayi tana kallon d'iyar tata yanda farin ciki ya mamayeta kafin tace" Oh Azee bansan wani irin so kike wa Irfan ba... "Azee ta murmusa kafin tace" Wllhi momy ina masa son da bana maki yanzu dai I should get rid of that so called nanny din dan ita taimin cikass....." Laila kam dae baki sake take kallon Azee cikeda mamaki( _Wai tafi son shi akan uwar data haifeta... what a mess 😕_)...
★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★
*"Two weeks later*
"Zaune suke a Cafeteria suna cin snacks fitowarsu kenan daga Enxamz yau sukayi last paper gaba d'aya jinsu suke cikin farin ciki dan kuwa zasu samu hutun zangon karatu na farko wato first semester.
"Nadiya sai faman nunawa Deejah pics din brides take wai ta zab'i shigar da zatayi a bridal shower dinta.... "Azee kam gaba d'aya ji take tamkar zuciyarta zai tarwatse dan tsananin tashin hankali, gaba d'aya k'arfin hali take tana dannewa musamman da yanzu aka tsaida maganar auren Irfan da Deejah.
"Shigowan su Mus'ab Turaki course mates dinsu cikin Caf din ne ya katse masu hiran da suke... Take Deejah ta had'e rai dan kuwa ko kad'an bata son yanda su Mus'ab dasu Nadiya ke shaking hannaye tamkar ba yaran musulmai ba, ko tai masu magana cemata suke ai sch life ne so let's be social, gwarama Nadiya zata iya cewa tashin Turai ne har yanzu a jikinta amma Azee kam zunzurutun son wasa da maza ne kawai snn itake dad'a influencing Nadee. Dan haka nema ko kadan Deejah bata sake masu Mus'ab.
"Table din gefe suka k'arasa suka zaune, Mus'ab ya d'an tab'a k'afar Sudais gamida kashe masa ido d'aya alamun kar ya spoiling masa mission dinsa.
"Murmushi Sudais yayi kafin ya d'aga masa gira d'aya ya mik'e ya nufi table d'in su Deejah.
"Guys you're all invited to the farewell party of MUS'AB TURAKI (VICE PRESIDENT SON) As you all know that he's living the country tomorrow.
"Cikeda masifa Deejah tace" and who cares, kaga mun maka kama da masu zuwa party ne..." da sauri Azee ta katse ta da fad'in " Aaa haba Deejah zamuje mana, miye a ciki dan zamu partyn ban kwana da d'an ajinmu.
"Murmushi Sudais yayi kafin yace" Your presence is very important must especially you Arab girl.... yayi nuni da Nadiya da tun tsayuwarsa take faman danna wayarta. Sai snn Nadiya ta d'ago tana dubansa. Nuni tayi zuwa k'irjinta da phon dinta tace "Mee!! Surprisingly!
"Sudais ya gyad'a kansa kafin yace" yeah the vice president son have a surprise for you, anyway idan kun gama deciding ku samemu wajen cars dinmu sai kuji venue din. Daga haka Sudais ya juya ya wuce wajen zamansu..
"Deejah ta gallawa Azee harara tace" haba Azee meyasa kika biyesa ya maidamu 'yan iska ne masu zuwa party.... " kai Deejah meye iskanci a ciki dan munje farewell party din Mus'ab, kina gani mu kadai suke kulawa dukda ji da kai da 'yan click dinsu sukeda.... "Ringing din da wayar Deejah tayi ne yasata tashi ta nufi restroom ganin Sahibinta ne me kiranta,...
"Haka Azee tayita zuga Nadiya wai she's special tunda har Mus'ab na shirin bata surprise duk fadin Nile, nan kuwa Nadiya ta biyeta tana jin yes kenan duk tafi sauran 'yan matan sch din haduwa, mikewa sukayi suka nufi yanda Su Mus'ab suka pake Luxurious Cars dinsu.
"Suna isa wayan Azee dake cikin jaka ya soma ringing tana ganin Ahidjo ne tace wa Nadiya bari taje amsa wayan Hajiya, hajiya ke kiranta, nan Ahidjo ya sanar da ita su had'u a guest house dinsa urgent.
"Sudais ne ya bud'e wa Nadiya bayan Range Rover din Mus'ab take ta soma jin jiri bata san yaya akayi ba sai shigewa cikin motan da tayi...
"Sadiq da shigowarsa Nile kenan ya hangi wata kaman Nadiya ta shige bayan range rover da wasu maza take yaji k'irjinsa na dukan uku uku, sauri sauri ya ajiye Mamie wajen aikinta wato Cafeteria ya juya da kan motarsa nan ya tarar motan da Nadiya ta shige na k'ok'arin ficewa daga Nile, take ya soma binsu a baya cikin sauri dan kar su b'ace masa.
"Deejah tana dawowa Caf ta tarar babu su Nadiya, layinsu ta soma kira amma bai shiga, na Azee nema ya shiga sau d'aya ba'a d'aga nan tayi tunanin ko Department suka koma dan dama sunyi missing examz guda d'aya, tayi tunani ko sun koma yin complain ne. Ganin Mamie na shigowa da kaya yasata saurin k'arasawa ta amshi wasu kayan suka soma gaisawa.
"Yana shigowa cikin Nigerian Turkish Nile University ya shiga neman layinta, tana d'agawa yace gashi ya iso tana ta ina ne, nan ta sanar dashi tana Caf.
"Kai tsaye Irfan ya wuce Cafeteria, yana gama parking ya fito ya nufi cikin Caf din,
" Daga yanda take zaune ta hangosa... "Sanye yake cikin k'anan kaya Royak blue shirt wanda ya k'ara fito da hasken fatarsa yana sanye da wando ash chinos, gashin kan nan nasa sai shek'i yake as usual, idanunsa sanye cikin bak'in sunshade, yana hangota ya sakar mata murmushi nan itama ta maida masa martani, ganin yamda emmata kai harma da samarukan da suke zaune a caf din sun k'urawa Irfan ido wasu na faman fad'in "Woow handsome" yasa Deejah jin kishi sosai har saida taji dama bata ce ya shigo caf din ba, ita kanta bata son tana son Irfan tana kishinsa irin haka ba.
"Kan ya k'araso ta mik'e ta nufi yanda yake dan bata isa ya zauna a Caf din nan ba emmata su cinyesa da kallo. Gaishesa tayi sai ture turen baki take,
"Irfan ya sunkuyo da kansa ya rage tsayinsa saitin kunnenta kafin yace" Why the long face baby, I hope the examz was sweet like you,.
"Turo baki ta kumayi kafin ta gyada masa kai alamun examz yayi dadi.
"Murmushi ya kuma yi kafin yace" toh ture turen bakin me ake bayan examz was fine, ko ba'ayi murnan gani na bane... "zatayi magana yayi saurin sunkuyo da bakinsa saitin kunnenta cikin sigan rad'a yace" Ohh na tuna baby you must be exhausted kina buk'atan massage,.... muje gida nayi maki tausa....
"Zaro ido waje Deejah tayi tana kallonsa, irin yanda yake so yaga tayi da idanunta.. harara ta b'alla masa kafin tace " ya irfan muje ka gaisa da Mamie gata a can. Irfan ya amsa da toh yana binta da kallo me kashe mata jiki.
"Bayan sun gaisa da Mamie ta tambayesa aiki dasu Ammah, Irfan ya amsa da lafia lou Mamie, yaya Dada da jiki, Mamie ta amsa masa dacewa " Da sauki Irfan, kaida Deejah kun gujemu kwana biyu ko duk shirye shiryen bikinne.. "Irfan ya murmusa yana sosa k'eya kana yace" zamuzo insha Allah Mamie musamman mu duba jikin Dada, Deejah kam sunne kai tayi a k'asa . Mamie tace "toh Allah ya kawo ku Allah kuma ya sanya alkhairi, gaba daya suka amsa da ameen.
"Deejah ta bar sallahu wa Mamie cewa" Idansu Nadiya sun dawo ta sanar dasu ta tafi tareda ya Irfan.....
"Dukda driving yake amma hankalinsa na kanta ganin tasha kunu ta turo baki,
"Baby wai waya tab'a min kene na ganki haka, ko exams dinne.
"Girgiza kai tayi ba tareda tace komai ba,
"Toh ko dai baki son surprise din da nace zan nuna makin ne.
"Nan ma ta girgiza kai....
"Ok na gane ganina ne knn baki so.
"Da sauri ta dago tana dubansa gani tayi idonsa naga titi. Zaiyi magana tace " ba kaine kazo duk emmatan dake cikin Caf sun kare maka kallo...... " Dariya sosai Irfan yake harda buga starry kafin ya juyo yana dubanta yace" ashede duk acikin kishina ne, toh kiyi hak'uri zan fara saka emmmm what's thay ting that women use to ware... yayi shiru kaman me tunani.... Deejah tace" me kenan.
"That black thing like ningers......
"Ohh nikab.
"Ehen nikab timda bakiso a kalle maki ni......" Dariya suka fashe dashi gaba dayansu.... gwanin ban sha'awa kana ganinsu kaga masoyan juna.
"Master ina zaka kaini ne..... tayi maganan cike da shagwab'a.
"Ya kwaikwayi muryanta yace" am not gonna kidnap you baby, just wait and see.
"Murmushi kawai tayi tana kallon yatsun hanunsa masu kyau dasu yanda yake driving, sonsa da k'aunarsa na ratsa illahirin jikinta.
"Sadiq na ganin sun shige gate din wanu gida a asokoro yabi bayansu shima ya shige kasancewar samari ne da emmata keta faman zarya a gidan gaba daya babu wanda ya lura dashi.
"Yanayin da yaga emmatan da samarukan ya basa tsoro take yaji k'irjinsa ya tsanan bugu.......
"Azee ne kwance saman k'irjin Ahidjo tana wasa da sajansa yayinda shikuma ke shafa gashin kanta.
"Gaskiya Ahidjo you need to do something..... we can't let that happen, we can't let them get married we need to stop them kota halin k'ak'a, dan gaskiya I can't bear loosing Irfan, shine rayuwata.... Azee ta fad'i sanda ta soma yi masa wasu salo.
"Murmushi Ahidjo yayi kafin ya dad'a matsota cikin jikinsa ya d'aura yatsansa kan lips d'inta ya shafawa yake fad'in " just calm down baby doll na gaya maki, auren Irfan kaman kinyi an gama as far as ina raye, yanzu dai bala'in yu warki nakeji feed me kafin ayi wancan zancen..... ya k'areshe maganar yana saka bakinsa cikin nata..........
*Muje zuwa readers.... luv you all😍😘*
Queensamynovels★
[8/22, 14:47] Umar Dalha: 🌗🌗🌗🌗 *Mallakin Waye*
49
*©Sameena Aleeyou*
_Queen Samy Novel Forum......📖📚_
"Irfan na murmushi ya dubi Deejah data rufe idanunta da tafukan hannayenta yace" Oya open your eyes....... "Deejah na bud'e idonta tayi tozali da makeken gida me kyaun gaske wanda zamu iya cewa is more of glass kaman dae ginin k'asashen turawa. A hankali ta furta" Woooow! Masha Allah this is so amazing.
"Irfan na murmushi yana kallonta hannayensa hard'e a k'irji yana karkad'a d'an makullin mota yace" yayi maki???
"Kallonsa tayi da mamaki kafin tace" Kai ya Irfan this is awsome infact this is spectacular. Babu wanda zaiga wnn gida yace bai masa ba. Gidan waye?? Ta k'arashe tambayar tana d'an satan kallonsa.
"Murmushinsan nan mai tsada ya kuma yi kafin yace" this is your house, our house...... Yanda zamu building namu family din yanda zaki haifa mun yara masu kama dake, tun ranan dana d'ora idanu na akanki na soma zanamana gidan da zai dace da rayuwarmu, toh finally yau an gama ginawa shiyasa na d'aukoki ki gani, idan akwai abinda be maki ba sai a canza shi right the way......." Kasa daina kallonsa tayi har saida yai mata far da idanu.
"She just couldn't believe it a bit, wai wani irin so irfan ke mata haka, a hankali ta sauk'e idonta zatayi magana sai jiyo muryansa tayi yana fad'in" let's go in, mu shiga kiga yanayinsa... "jiki a sab'ule Deejah tabi bayan Irfan....
"Duk abin duniya ya dami Sadiq yama rasa wanne zaiyi, ya kai Nadiya gida ne ko ya koma can sch dinsu wajen Mamien sa ne, yana tsaka da wann tunani ya jiyo muryanta idonta a lumshe take fad'in" plssss don't take me home, I beg of you pls kar ka kaini gida a haka am sure Daddy da ya Irfan kasheni zasu yi.....tana maganan cikin magagi tamkar me maye tana lumshe idanu......
"Shiru Sadiq yayi yana nazarin kalaman nata.... Bai tab'a k'are mata kallo ba sai yau, a shekare bazata wuce 17 ba dan su Deejah sun girme mata, farace tass irin na larabawa kaman dai Irfan saidai bata kaisa hasken fata da kyau ba. Sadiq ya lumshe ido dan kuwa take yaji ya rasa tunanin me yake gameda Nadiya, kai tsaye gida ya wuce da ita dan ya tabbata by now Ruqayya ta dawo daga sch.
"Laila ce ta fito cikin shiri ta k'arasa sashen Ammah ta sanar da ita ta tafi gidan Hajiya, Ammah tace a dawo lafiya ki gaida min Kariman, nima inason zuwa duba jikin baba Alhj yau nake cewa idan Nazif ya dawo gwara ayi maganar fitar dashi waje baza a biye nashi ba ai shi Baba Alhajin dukda baya so gwara a jaraba wani k'asar ko za'a dace.
"Laila da k'irjinta ya soma harbawa a tsaitsaye ta amsawa Ammah duk ta dabirce kafin ta fice sai faman sauri take ta k'wala wa Habu kira ya fito mata da mota daga parking lot.
"Habu yace Haj ina muka nufa kinsan Alhj baya so kina driving......."Galala Laila ta kalle sa kafin tace" Dalla fice ka bani key if you dont wan to get your self fired. ?.. ban son iayayi me ya shafeka tsakanina da mijina, ...... Habu cikin sauri ya fice jiki har na b'ari ya mik'awa Laila key.... "tsaki tayi ta fizge key din gamida jefa masa harara tace"en shishigi d sa ido.......
"Yaya wacece wnn Ruqayya ta tambaya fuska cike da damuwa, Sadiq ya sauk'e ajiyan zuciya yace" k'anwar Irfan ce wasu yarane suka so suyi attacking nata shine na kawota nan ta d'an warware kafin na kaita gida.
"Ruqayya dai bata gamsu da batun yayan nata ba gaba d'aya mood dinta ya canza dan kuwa tana kishin Sadiq sosai..... "Ya d'an kalleta yaga yanda ta had'e rai murmushi kawai yayi dab abun ma dariya yaso basa..... ganin ta mik'e zata fice yasa sa cewa" lil sis zo mana, dawowa tayi ba tareda tace komai ba. Shima din dan dakewa yayi kafin yace" kawo min ruwa a bowl da d'an towel....... "Zaro ido Ruqayya tayi tanai masa kallon mamaki, me zaiyi da ruwa da towel.
"Sadiq kuwa fuska babu alamun wasa ya dago kai ya d'an dubeta yace" you heard me right, ki kawo mun ruwa da towel.
"A fusace ta fice daga parlorn tana fita kuka ya kufce mata, me ya Sadiq yake nufi, me ya dauketa, me yadauki soyayyansu data jima tana dakonsa, irin kallondata ga yanai ma yarinyar nan ya firgitata... zama tayi dirshan a wajen tana sharen kuka, ta ma mance da batun aikenta da Sadiq yayi.....
"Dawowan Mamie kenan ta tarar da Ruqayya zaune a tsakakr gida tana sharan kuka......
*kuyi hak'uri da wnn dearies idan na sami time da dare will continue..... luv you all*
_Queensamynovels👄_
[8/22, 14:47] Umar Dalha: 🌗🌗🌗🌗 *Mallakin Waye*
50
*©Sameena Aleeyou*
_Queen Samy Novel Forum.... 📖📚_
"Cike da manaki Mamie ke bin Ruqayya da kallo, ajiye kaya hanunta tayi kafin ta k'arasa ta dafata tana fad'in" Lafiya Ruqayya me ya faru waye ba lafia? Duka lokaci gud Mamie ta jefa mata tambayoyin,
"Kasa amsawa tayi sai wani sabon kukan da ya kufce mata.
Sadiq daya gaji da jiran Ruqayya a fusace ya fito daga parlorn.
"Mamie ta had'e giran sama da k'asafin tace" banson sakarci meke faruwa kinyi shiru, ko wani abin ne ya faru.... daidai nan Mamie ta hangi Sadiq rik'e da labulen parlor yana binsu da kallo.
"A'a Sadiq wai meke faruwa ne. Mamie ta bid'a, cikin sauri Ruqayya ta mik'e ta shiga goge hawayenta.
"Mamie sannu da dawowa ya fadi yana sauke hannun rigarsa da ya nad'e,
"Gajeren tsaki Mamie tayi kafin tace kun soma er fad'an naku ko, kunfi kusa ku kuka sani daga haj tasa kai ta wuce.
"Yakai dubansa ga Ruqayya wacce ta had'e fuska tamau shima babu alamun wasa a fuska a d'aure yace " ina abinda na aikeki?.... "Kiran da Mamie ta kwala wa Ruqayya ne ya katsesu. Cikin sauri Ruqayya ta wuce ta barsa nan tsaye.
"Mamie gani, ta fad'i tana satan kallon Nadiya dake mutsu mutsun tashi.
"Meke faruwa naga Nadiya a nan? Mamie ta tambaya.
"Yaya ne ya shigo da ita tana tangad'i na en maye, Mamie dama kinsan ta ne?
"Shiru Mamie tayi tana nazarin magsnganun Ruqayya kafin tace "ina Sadiq din..... "Kan ta gama rufe baki Sadiq ya shigo da bowl da towel. Mamie ta bisa da kallon "I need an explanation.... "Sadiq ya fada wa Mamie duk abinda ya faru nan Mamie ta gano musabbabin fushin Ruqayya kishin Nadiya take, tai murmushi ta karb'i towel da ruwan ta shiga shafewa Nadiya a jikinta, shi kuwa Sadiq yarrr yaji a jikinsa cikin sauri yabi bayan Ruqayya...
***********************
"Tun daga nesa ya hango motan Laila ns pake alamun shitake jira, gaban Safwan ya fad'i rasss! Yasan bazasu wanye ta dad'i ba muddin ta gansa da budurwa musamman da yanzu take k'ok'arin nema masa aiki a M&M Builders. Juyowa yayi ya kalli Yussy dake faman danna wayarta yace" My Yussy zanyi dropping naki a nan ki shiga adaidaita ki wuce gida da daddare zanje na sameki. "Galala Yusra ta kalle safin tace" Ban gane ka canza mind d'inka ba, inji daga gida ka d'auko ni da kasan baka buk'atana ai dabaka taho dani ba......" Oh pls mana my yussy calm down, don't get the wrong idea, Yakumbo na gani yanzun nan ta shige cikin gidana kinga idan ta ganni da budurwa kuma ai akwai matsal dama ta tak'ura saidai na koma can gidanta, kinga yanzu idan ta ganki zatasa dole na koma, pls mana my yussy you know I love you and I'm dying to be with you... ya k'arashe maganar yana jawo kunkuminta had'i dayi mata kiss cikin salo.
"Take Safwan ya jshe jikin Yusra da kalamansa da kuma salon soyayyarsa. A haka ya sami kan Yusra ta fice neman adaidaita. Saida ya kintsa kansa jikin madubin motar kafin ya k'arasa wajen Laila bariki😂 .
"Wani kallon sha biyu saura kwata Laila ta masa kfin tace" 'Dan cutie wai ina ka tsaya for goodness sake ka barni ina jiranka for almost an hour, kasan dai I hate to be waiting.
"Bude mata marfin mota yayi yana k'ok'arin tura kai jikin wuyarta yake furta" Haba giwar mata, daga zuwa babu wani kalamai masu dad'i sai k'orafi, kinsan halin Yakumbo yanzu haka ma daga wajenta nike ta kafe saidai na rik'a kwana a gidanta shiyasa na tsaya bata baki kinsan abinki da tsofi.. ya manna mata kiss a wuya yace I miss you cikin sark'ewan murya.
"Murmushi Laila tayi jin Safwan na k'ok'arin afka mata cikin mota yasata saurin turesa kafin tace" wait d'an cutie ko ka mance a waje muke..... Ya mik'e yana kashe mata ido d'aya yace" So ko kina tunanin d'an tsohonki kar ya ganmu ne, "Murmushin k'asaita tayi kafin tace " kasha kuruminka baya k'asa ma tun jiya ya tafi Holland.
"Safwan ya zaro ido waje yana murmushi yace kice yau apzamu kashe dare,.. murmushi kawai Laila tayi kafin tace" dama nan nayi niyyan zuwa amma dole naje gidan Hajiya yanzu dan akwai wani issue da zamuyi discussing nida ita very urgent. Zuwa nayi mu tafi dan kaima maganar ta shafeka. Shafa fuskarta Safwan yay kafin yace barin shigar da motata ciki sai ki bamu ride. Murmushi Laila tayi tana wani jshe masa ido guda. Yana fitowa ya shige front seat suka zuge glass dan kr agansu dashike glass din motar mai duhu ne.
******************************
"Bayan sun gama ganin gidan kai tsaye wani *Shawarma Spot* suka nufa, yana gama parking ya jiyo ya kalli Deejah data langab'e kanta jikin seat yace" my bride to be akwai problem ne? Girgiza mai kai tayi alamun a'a kafin tace" is getting late ya Irfan ya kamata by now muna gida kar hankalin Ammah ya tashi, kuma kaga su Nadiya might get worried tunda a sch muka rabu dasu though nace wa Mamie ta fad'a masu kazo ka d'auke ni.
"Murmushi Irfan yayi zurfin tunani da hankalin Deejah na burke sa yana d'aya daga cikin abinda yasa ya k'ara sonta da bata daraja na musamman cikin zuciyarsa. "Ya d'an turo baki yana kwaikwayon maganarta yace" so probably kinga Ammah tasan kina tareda Husband to be dinki definitely, so nothing to worry about, sauko muje..... "Girgiza kai kawai tayi tana dad'a turo baki tace" am tired fahhh Master bazan iya sauk'a ba,
"Toh fad'i fillings din da kike so, beaf or chicken. Ya fadi yana bude safe din cikin motarsa.
"A hankali tace duk wanda kake so nima shi nake so.
" 'dagowa Irfan yayi yana kallonta sosai ta burgesa, murmushi ya kuma yi kana ya fice, mintuna kadan ya dawo hannunsa rik'e da ledoji suka wuce gida direct.
"Yana gama parking saida suka sha soyayyarsu kafin ya mik'a mata laidanta har kofan sashensu ya rakata kafin yace bari ya wuce ya dan freshing up kafin ya shigo gaida Ammah,
"Har ta soma tafiya tajiyo sautin muryansa a hankali daidai saitin kunnenta yana fad'in" baby ko zamuje ki min wankan ne..... Zaro ido waje tayi tana kallon sa gamida jefa masa hararan wasa...., shi kuwa Irfan dariya yayi dan tayi abinda dama yakeso tayi juya idanunta, kantayi magana ya furta" I love you baby, daga haka ya wuce yana murmushi. Kallo ta bisa dashi har ya b'ace mata sonshi da k'aunarshi na d'awainiya da ita.
"Ammah na zaune a parlor tana kallon program din *The Dr's* Deejah tayi sallama ta shigo.... "Ammah sannu da gida, ta fadi sanda take k'arasa shigowa, Ammah ta amsa da yauwa sannu Khaddejatu, ina sauran 'yan uwan naki.
"Turus Deejah tayi jin tambayan da Ammah tayi mata, dan ita ta nata tunani su Nadiya sun tsufa a gida........
_Queensamynovels.....👄_
[8/28, 14:07] Umar Dalha: 🌗🌗🌗🌗 *Mallakin Waye*
51
*©Sameena Aleeyou*
_Queen Samy Novel Forum...... 📖📚_
*Wannan page d'in naki ne Mrs Haidar Waziri Allah ya bar k'auna... it's indeed a blessing having someone like you as a friend, May The Almighty bless you and your entire family 💖*
_Masu k'orafin ci gaban *Zubaidah* kuyi hak'uri yana nan tafe da zaran na idda mallakin waye insha Allah, lot's of luff guyz😘_
"Ammah su Nadiya basu dawo ba ta tambaya fuska cike da mamaki.
"Ah a, ince daga makaranta kike? Ammah ta jefo mata tambayar... "Eh na baro sch tun d'azu ya Irfan ya d'auko ni na d'auka by now suna gida.
"Gajeren tsaki Ammah tayi kafin tace" duk kun kama kun kashe wayoyinku, na kira wayoyinsu baya shiga har naki na kira bai shiga, shi Irfan din meyasa be d'aukoku gaba d'aya ba, inama kukaje da tsakar yamman nan, wato dan kunga daddynku baya gari bari ku tsira yawo ko......"Tunda Ammah ta soma fad'a idon Deejah ke kallon k'asa, da kyar ta iya furta "Kiyi hak'uri Ammah.....l muryanta na sark'ewa, "Maza kira min yayan naku Ammah ta katseta.
"Da sauri Deejah ta fice kiran Irfan.....
"Duk ta gama rud'ewa ganin ran Ammah sosai ya b'aci gaba d'aya bata tab'a mata fad'a irin haka ba, dan haka ko tunanin sallama batayi a kofan d'akin Irfan ba, kai tsaye ta danna kanta cikin d'aki....
"Yana tsaye gaban *closet* dinsa towel ne kawai d'aure a K'ugunsa yana shafe gashin kansa da shampoo alamun wanka zai shiga.... turo k'ofan da tayi yayi daidai da juyowarsa aikuwa nan sukayi ido hud'u...... "'kara ta sake gamida rufe fuskanta da tafukan hannayenta, jikinta ya soma rawa.
"Irfan kuwa abin sosai ya basa dariya ganin ta tsaya cak ta k'ank'ame idanunta ta kasa koda motsawa daga yanda take.
"Baby lafiya, ya tambaya yana k'arasowa gabanta..... "Still idanunta a rufe muryanta cike da tsoro take fad'in" Emm.... emm kayi hak'uri Master it was unintentional, I shouldn't have bang into your room, dama Ammah ce ta kazo..... Tana gama fad'in haka ta juya da sauri, juyawan da zatayi kuwa ta bige kanta jikin k'ofa.... "Irfan kuwa baisan sanda yayi kanta yana fad'in baby...... "Ai kuwa nan ta fad'o cikin k'irjinsa, Kallon juna suka shiga yi na d'an dak'ik'ai da sauri Deejah ta soma kiciniyan mik'ewa, cikin sauri shima ya saita kansa kana yace" hope dai bakiji ciwo ba, d'aga masa kai kawai tayi tasa kai zata fita sai jiyo muryansa tayi yana fad'in" be careful baby, am coming right away. Jallabiya kawai ya zura yabi bayan Deejah.
"Isowarsu yayi daidai da shigowan Mamie da Nadiya, da mamaki suke kallonsu gaba d'aya, yanayin Nadiya tayi sanyi sosai tamkar ba ita ba, Sadiq ne ya shigo da murmushinsa ya nufi yanda Irfan ke tsaye ya gaida Ammah kafin suka fice farfajiyan gidan shida Irfan.
"Ammah tayi wa Mamie sannu da zuwa Nadiya ta sha jinin jikinta sosai ganin irin kallon da Irfan yayi mata, tasan yau sai ya kusa b'allata a gidan nan, da sauri taja hannun Deejah suka nufi backdoor.
"Mamie bata fad'awa Ammah asalin abinda ya faru da Nadiya ba, saidai tace mata ita ta tafi da Nadiya gidanta bayan an tashi a sch. Ammah ta d'an nuna rashin jin dad'inta dan kuwa at least ko waya ita Nadiyan zatayi ta sanar zata gidan Mamie, Mamie tayi apologizing unbehalf of Nadiya.. ...
"Suna tsaye a backdoor tana narrating abinda ya faru wa Deejah, Deejah ma tana bata labarin fad'an da Ammah tayi suka jiyo muryan Ammah na doka masu kira. Cikin sauri suka k'araso sai snn Deejah ta sami zarafin gaida Mamie Nadiya kuma ta gaida Ammah.
"And where is Azeeza? Ammah ta tambaya tana dubansu, Deejah ta kalli Nadiya, Nadiya ta kalli Deejah..... "Ba magana ake maku ba! Ammah ta kuma daka masu tsawa.
"Nadiya ce tayi saurin cewa Ammah wllhi a sch muka rabu da ita tace Aunty ta kirata a waya bansan ko gidan Hajiya ta wuce ba
"Ammah ta gyad'a kai kafin ta ciro waya ta shiga neman layin Laila, bugu biyu Laila ta d'aga cikeda ladabin munafunci. Ammah ta tambayeta ko Azeeza na gidan Hajiya tareda ita.... cikin inina Laila ta amsa da Eh.... eh Ammah gata muna tare a nan wani abu ne? "Ammah tace" a'a no ba komai next time dai idan zata wuce can gidan sai ta fad'a kar hankula ya tashi.
"Laila ta amsa da toh Ammah zan mata fad'a, kiyi hak'uri.
"Ammah tana gama waya Deejah da Nadiya suka kalli juna, haka kurum sukaji basu yarda cewa Azee gidan Hajiya ta wuce ba, sosai Mamie da Ammah suka masu nasiha a matsayinsu na emmata kafin suka haye sama suka bar Mamie da Ammah na hira akasarin hiran gameda jinyar Dada ne, Ammah tace insha Allah zanzo na dubata ban tab'a zuwa ba. Mamie tayi murmushi tace" haba dai ai babu komai, Jibi ma za'a wuce da ita can garinmu Daura wajen mai magani zata kwana biyu a can.
"Ammah tace dama ku en Daura ne, Mamie ta amsa da eh Ammah daga can muke.
"Allah sarki toh kuwa ai daga jiha guda muke dan muma asalinmu 'yan Katsina ne, "Mamie tace Allah sarki ashe abin duk abu guda ne..... suka suka b'arke da hira sosai..
"Har saida su Mamie sukayi sallahn Magrib kafin suka wuce...
"Nadiya da Deejah kuwa sun k'ule a d'aki suna hiransu, akasarin hiran Nadiya keyiwa Deejah gameda abinda takeji akan Sadiq, I zuwa yanzu kam ta gama yarda sonshi take with all her heart.
********************************
"Wani pills Ahidjo ya ciro cikin drawers ya mik'a wa Azee yace "oya shanye.... "Kallonsa take cike da mamaki kafin ta yamuysa fuska tana mai girgiza kai tace ban gane ba?
"Mayaudarin murmushi yayi kafin yace" bazaki gane ba sai kin farka kin ganki da ciki nan ne zaki gane idan Irfan yak'i aurenki.
"Murmushi Azee tayi ta karb'i pills d'in ta jefa a baki ta had'iya da ruwa kafin tace" toh ai kaine baka min bayani ba, shiyasa nake ji da kai kasan kan hark'a, mayaudarin murmushi ya kuma yi kafin ya kuma jawota cikin jikinsa yanai mata wasu salo yace" sweet girl yanzu haka zaki tafi ki barni, kinsan zanyi kewarki anya ma kuwa zan iya kwana ba tareda ke ba.
"Turesa Azee tayi tana me ci gaba da gyara zip d'in rigarta tace" baka ganin dare ya soma yi ne, za'a nemeni a gida, a kunnan ac ka rufe ko ina gaba d'aya ban gane dare yayi ba, com on ka tashi kayi dropping dina gidan Hajiya pls ni yau canma kawai zan kwana........ "Kan ta gama rufe baki wayarta ya soma ringing kunnawanta kenan... ganin Momynta ne me kira yasa gabanta mugun fad'uwa tasan tayita kiranta bai shiga. Da k'yar ta saita kanta kafin ta d'aga wayar.
"Hello momy........
"Dan ubanki gidan uban wa kikaje kika zauna har iwar haka da baki koma gida ba, Laila ta katseta da fad'in haka.
"Azee murya na shaking take fad'in" momy fah gidan Hajiya naje......."Hajiyar uwaki, munafuka gani nan a gidan Hajiya ina kika shiga. Toh dama duk yanda kike kiyi maza kizo gidan Hajiya ki sameni daga haka ta katse wayan.
"Ai kuwa cikinmsauri ta shiga tattara komatsanta ta cusa cikin jaka, Ahidjo ya jawo side drower ya ciro bandir d'in 'yan dubu dubu wato hundred thousand ya saka mata cikin jakar yace muje nayi dropping naki baby.
"Sai kallon mamaki Azee take binsa dashi lallai Ahidjo d'an masu maik'o ne, ai kuwa ta samu wajen samun kud'i, cikin sauri suka wuce mota shima Amminsa tai masa waya tana son ganinsa,.
"Safwan ya kuma jawo Laila cikin jikinsa snn yace" giwar mata ki kwantar da hankalinki nasan Niece d'ita is a good girl, she'll take good care of her self, she will soon arrive here safely, yanzu yaya batun namu zaki bini mu tafi ko dan kinsan I can't afford to miss you to night..... ya k'areshe maganar yana kashe mata ido guda.
"'Dan turesa Laila tayi kafin tace" haba dai Safwan ai yanzu kam 'yarka ta b'ata mana plan d'inmu dole na jirata ta iso nan snn ni na koma gida na kwana, idan yaso gobe sai ka dawo da Azee can gida kaga babu wanda zai zarge mu.... ni kuma nai maka alk'awarin samun farin cikin kasancewa dani.
"Murmushi Safwan yayi ya shafi wuyanta zuwa k'irjinta yana wani kashe mata ido guda kafin yace" dui yanda kika ce sarauniyar mata. Murmusawa Laila tayi kafin tace" kadaiji abinda Hajiya ta fad'a maka aiki sosai zaka mana a company din nan bamu so gane ka, har sai ka samu shiga sosai wajen Engr.
"Ki kwantar da hankalinki idan dai wnn anyi an gama Engr Nazif sai ya yarda dani fiye da yanda ya yarda da d'ansa Irfan. Zanyita cin dunduniyarsu har sai M&M Bulders ya zama *Mallakin mu*.
"Dariya suka fashe dashi gaba d'aya uwa babu kwab'a.... _Allah ka tsarkake mana zukatanmu ka kiyashemu aikata danasani.....Ameeen!_
"Sosai Laila tayi fad'awa Azee kan abinda tayi harsaida Hajiya tasa baki,
"Alhaji Ma'aruf dake kwance kan gadonsa kallonsu yake hawayen takaici na gangaro masa _Allah sarki rayuwa, wann shine barewa bazatayi gudu 'yarta tayi rarrafe ba, wnn shine illan zina takanbi zuriya gaba d'aya, tun daga kan kakar har jikan abu guda suka tashi a kai, kaico masa auren Karime da yayi_ ya runtse runtse idanunsa kafin yaci gaba da addu'a wa Engr Nazif da family dinsa gameda sharrin Karime da zuri'arta....
★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★★
*Some weeks later*
"Engr ya dawo daga k'asar Holland, Safwan ya soma aiki gadan gadan da companyn M&M Bulders, snn an saka bikin Deejah da Irfan wata guda kacal me zuwa,
"Shirye shirye ake babu kama kafan yaro, duk yanda Azee da Ahidjo suka so b'ullo wa lamarin Irfan da Deejah abin yaci tura, hankulansu na ci gana da tashi, gaba d'aya sun rasa yanda zasu b'ullo wa lamarin auren suna hanashi aukuwa, kullum sukanhad'u toh kuwa sai sun aikata masha'ansu.
"A b'angaren Nadiya kuwa son Sadiq a kullum kaman k'ara azamata wutarsa ake, tunda sukayi resuming sch kullum saitaje Caf ko bazataci komai ba, sai taje ta gaida Mamie, gaba d'aya duk wani arrogantly nata ta rage, ta soma living simple life, duk wann so da k'auna da take wa Sadiq bata tab'a gigin fad'a masa ba koda da wasa ne, dukda a yanzu ya rage tsanan da yayi mata a baya ,sukan gaisa sosai, sukan jima suna waya, wasu lokutan ya bata shawarwari gameda karatu. Mamie ma sosai suka saba da Nadiya fiye da sabin da sukayi da Deejah.
"A b'angaren Ruqayya kuwa a duniya idan akwai wanda ta tsana toh a bayan Nadiya ce, ko kad'an bata son ganinta musamman da yanzu ta sake sosai da Sadiq, kullum Sadiq cikin tausanta yake yana fad'a mata babu komai tsakaninsa da Nadiya face ya d'auketa tamkar k'anwa.....
"Ammah ta had'a lefe na gani na fad'a, Engr da kansa ya yayi masu visa zuwa k'asar Dubai shi Ammah, Laila, Irfan da Deejah dan zab'an dangin furniture da kuma sauran kayan lefe, wann abu ba k'aramin d'aga hankalin Azee da laila yayi ba.., "Koda suka koma wajen boka abu guda ya k'ara gaya masu, Irfan shine mijin Deejah dukda sai an sami tangard'a a auren, zullumi da tunani babu irin wanda basu shiga ba, Laila dai k'arfin hali take tana tsunduma kanta a hidiman dan kar a d'agota. Azee kam har rama da bak'i saida ta d'anyi kaman wacce ta kwanta cuta.
"Gaba d'aya yaran gidan murna suke musamman dashike bikin fari kenan da zai kasance a gidansu, bama kaman Nilam wacce ta kasance 'yar gaban goshin amarya da ango, kullum tana mak'ale da Deejah, Deejah ta dage zaidai ta tafi da Nilam can gidansu bayan biki.
"A b'angaren Aunty Larai ma ba'a barta a baya ba, dukda yanzu bata orphanage na Abuja tazo maganan shirye shirye, nan Yusra take jin labarin kwatsam sai kuma ta gani a shafukan sada zumunta na yanar gizo.
"Duk wann bidiri Safwan bai tab'a sanin wai Deejarsa ce ta club ake zance zatayi aure ba........
_Toohh fah, yaya kenan zata kaya readers? Shin kuna ganin Safwan zai bari ayi auren nan, shin Azee ta hak'ura da Irfan kenan, shin Ahidjo ya janye k'udirinsa akan Deejah kenan. Toh wai ina kuka baro Yussy shin zata rufa wa Aminiyarta asiri har ta cimma burinta na auren Irfan..... Shin yaya zata kaya tsakanin Ruqayya, Nadiya da kuma Sadiq........ Wai yaya batun fita da baba Alhaji k'asar waje , shin Hajiya Karime zata bari hakan ta kasance???_
_Toh ku biyo Queen Samy dan jin ci gaban wann rikiceccen al'amari zata kaya_👌🏽
_👸🏻QueenSamy.......😍💄👄_
[8/28, 14:08] Umar Dalha: 🌗🌗🌗🌗 *Mallakin Waye*
53
*©Sameena Aleeyou*
_Queen Samy Novels Forum...... 📖📚_
"Gaba d'aya Irfan sai wani shisshigewa jikin Deejah yake yanai mata salon soyayyarsa, wanda duk wani mahaluk'i dake wajen saida suka burgesa, koda Mc ya bak'aci amarya da ango su fito suyi rawa dan nuna farin cikinsu, Deejah kam kasa tashi tayi, Irfan babu ko kunya ya kamo hannunta duk tabi ta daburce, a hankali ya tallafo k'ugunta suna rawa a hankali wanda zamu iya cewa motsa jikinsu kawai suke, jin yanda jikinta ya soma rawa a kunnenta Irfan yake rad'a mata, "just calm down baby I love you dukda daurewa kawai yake amma yana tsananin buk'atan babynsa...., kaji Mc ya soma fad'in"Wooow so fascinating, this Groom really luvs his beautiful bride, nan su Ashraf mutan US suka nufosu abinda sukafi so kenan Ahidjo ma ba son yaso ba ya taso amma ji yake kaman ya shak'a Irfan ya huta, lik'i suka yi masu babu k'kautawa suna tayasu rawan k'arshe hannun abokinsu suka rik'e aka saka masu music d'in da suka fi so suna tik'a rawa tamkar su ke rera wak'ar, Deejah kuwa a haka ta sulale ta koma mazauninta, duk gaba d'aya sai kunya take faman ji yanda irfan keta wani riritata..... tana zama taji muryan Nadiya a kunnenta tana fad'in" Ohhh gaskiya wnn angon daga gani babu d'aga k'afa Deee zakiyi bayani mudai babu ruwanmu, ta k'areshe maganar tana k'unshe dariya. "Harara Deejah ta narka mata ba tarera ta iya furta koda kalma guda ba, dan gaba d'aya ji tayi jikinta yayi sanyi kaman wani abu na shirin faruwa da ita, ta hangi fuskan Irfan farincikinsa a bayyane yake, annuri ne tsantsan ke tashi a fuskan nasa, a hankali ta sauk'e ajiyan zuciya gamida runtse ido jin yanda k'irjinta ya soma lugude haka kawai...
"Daga yanda suke tsaye sun gama ganin komai Safwan ya jawo hannun Yussy suka nufo waje, fizge hannunta tayi kafin tace" wllhi bazan tafi ba ban nuna wa Deejah b'acin raina na rashin gayyata ta da batayi ba, kaidai idan zaka tafi bisimillah go ahead,.... " Gajeren tsaki Safwan yayi kafin yace" that's enough am not in the mood... just don't provoke me Yusra. Deejah will never ever get married, she need to stop that dreaming of hers. Ya k'areshe maganar yana mai shafe namar goshinsa.
"Harara Yussy ta galla masa kafin tace" tace kan me zata fasa aurenta, sabida har yanzu kana sonta ko? ...... "Shiru Safwan yayi bai iya amsa ta ba, "Yusra ta kuma tunzura..... "Ka fad'a mun Safwan har yanzu son Deejah kake ko, Deejah will never love you back, you'll never ever win her heart, ta sami wanda take so, ka dubi yanayin mijin Deejah ka dubeka babu had'i wutsiyar rak'umi ya riga da yayi nesa da k'asa, Mijin Deejah yafika da komai da komai..... "Ji kake Tasssssss!!!! Safwan ya kifa mata mari, dafe k'uncinta tayi tanai masa mugun kallo gaba d'anyansu sai huci suke, jawota yayi daf da jikinta ya matse ta sosai kafin ya soma fad'in" be careful witj what you're sayin right now, so kike kiji daga bakina "Noo I don't love Deejah anymore, right now am fighting for my niece to achieve her dream. Fad'a zanyi wa 'yar yaya na ta sami farin cikinta Irfan, but not for my self... did you get thaaaaat!!! Ya karashe maganar cikin daga murya.
"Laila da ta gama jin komai ta karaso gamida janye Yusra daga jikin Safwan..... "Kallonta yussy tayi tsaf ta ganeta karuwan Safwan ne kuma matan Ogan sa na Company snn mahaifin Irfan. Fizge hannunta tayi daga rik'on da laila tayi mata. Murmushi Laila ta sakar mata kafin tace" Yusra ki bani hankalinki a nan keda Safwan idan kina so kiyi kud'i fine zakiyi shi yanzun nan if you cooperate, zamuyi wani aiki tare dan na riga naji kalaman ku"Deejah was once a club member.!!!!! Ta k'areshe maganar tana wani murmushin k'eta.
"Sauk'e ajiyan zuciya Safwan yayi, dan kuwa ya shirya a wargaza wnn aure da Deejah ke k'ok'arin yi, har yau har gobe bazai daina sonta ba, snn farin cikin 'yarsa Azeeza shine farin cikinsa, muddin Azee zata samu Irfan tofah babu abunda bazaiyi ba dan ta samu koda hakan na nufin shi ya rasa nasa farin cikin.
"Motan Laila suka shige su duka ukun suka zuge glass yanda babu mai noticing nasu suka shiga tattauna ya da al'amarin zai kasance,
"Suna gama tattaunawa Yussy ta kanne ido tana kallon Laila kafin tace" Banda wuce gona da iri, ku min alk'awari iyaka abinda kuka fad'i zakuyi ma Deejah banda k'ari, dan Deejah aminiyata ce kuma ina sonta har gobe dan tana d'aya daga cikin mutane masu muhimmaci a rayuwata.
"Laila ta murmusa kafin tace" idandai wann ne bakida matsala, you have my word, just count on me. "Gyada kai Yussy tayi kafin tace inaso naji alart first thing in the morning if not zan b'ata komai, murmushi Laila ta kuma kafin tace bakida wann matsalan as far as I'll get rid of that witch kin gane... Juya idanu kawai Yussy tayi ta kalli Safwan tace bani wasu mintoci ina zuwa snn ta fice...... "Nan ta bar Safwan da Laila suka soma watsewar su dan basu raina had'uwa, koda na minti guda ne sai sun rage lokaci.... "Wa'yazubillah.
"Sanda Yussy ta shiga hall d'in an buk'aci amarya da k'awaye su fito su nuna nasu farin cikin, dan haka kai tsaye cikinsu ta nufa, ta sauk'o da gashin attach dinta ya rufe mata Sideview nata dan bata so wanda suka santa su ganeta.
"Kai tsaye wajen k'awarta Deejah amarya ta k'arasa yanda aketa faman rawa ana having fun.
"Kunnen Deejah ta k'arasa a hankali take rad'a mata "Congratulations my dearest aminiya,........ "Gaban Deejah ne yayi mugun fad'uwa "Yusra ta fad'i a zuciyarta, d'ago kai tqyi suna kallon juna, Yussy ta sakar mata murmushi kafin taci gaba da fad'in" You did a great catch, you choose the most handsome guy on earth, Ohh dear partner in Crimes, don't tell me kin k'i gayyata na ne dan kar na ruining maki happy life da kike ciki, am I right??, perhaps am quite sure husband to be dinki baisan true color dinki ba. But don't worry am not here to ruin your event, anyway nazo ne na tayaki murna though baki gayyace ni, but remember this friend *" Be careful with the people around you,watch your steps, my advice to you* daga haka Yussy ta kutsa tana neman hanyan ficewa..... "Irfan dai ya lura da yanda yanayin Deejah ya sauya sosai tunda wnn yarinya ta nufota, yaga alamun tanai mata magana snn baiga fuskan ta sosai ba dukda yaso gane kamannin yarinyar, ganin abun na neman damunsa yasa sa watsar da tunanin guje ma rushewar farin cikinsa.
"Ahidjo kuwa sauri sauri yabi bayan Yussy a sace saidai kan ya iso yanda suke ya hangi Laila Safwan da Yussy sun fice daga wajen, murmushi yayi yana shafa sajensa kafin ya furta "Something is goin on.
"Jiri ne ya soma d'iban Deejah, tabbas kalaman Yussy sunyi mugun d'aga mata hankali, me Yusra take nufi, patner in crimes, yeah quite alright ta sani zuwa rawa a club babban haramun ne, sab'awa ubangiji ne, amma ko ada lokacin tana zuwa club rawa kawai take bata tab'a bin wani namiji ba balle shaye shayen kayan maye, me Yussy take nufi tayi hankali da mutanen da take tareda su Anya ba wani abin take shirin k'ulla mata ba, if Irfan finds out she was once a dancer in a club ta sani he'll definitely hate her, dan kuwa yasha fad'a mata the wotse abinda ya tsana a rayuwarsa toh fa mace maras kamun kai nee,.
"Sosai Jiri ke d'iban Deejah sai faman kama goshinta take tana yunk'urin fad'uwa, cikin sauri Irfan ya k'arasa ai kuwa nan ta fad'i cikin jikinsa, nan hankulan mutane yayi kansu. Kiran sunan ta yake yana jijjiga ta amma inaaa tamakar macecciya haka ta koma, cikin d'aga murya ya d'agi yana duban jama'an wajen yanda sukayi caaa in a shock suna kallonsu ya soma fad'in" Get a car, Sadiq just do something, ya ci gaba da jijjjiga Deejah yana ambaton sunanta.... 'Kaman zararre ya fice yabi bayan Sadiq da Deejah a hannunsa, su nadiya dadai sauran relatives nasu gaba daya suka bi bayansu hankali tashe.....
👸🏻Queensamy😍💄👄............
[8/28, 14:08] Umar Dalha: 🌗🌗🌗🌗 *Mallakin Waye*
54
*©Sameena Aleeyou*
_Queen Samy Novels Forum......📖📚_
"Nazif lafia dai ko na ganka haka, you don't seem normal, kaman wani abu na damun ka, cewan Ammah dake k'ok'arn zama gefen Engr.
"Sauk'e ajiyan zuciya Engr yayi kafin yace" Ammah baki kwanta ba,
"Kai kawai ta gyad'a kana tace" Ai bazan iya kwanciya ba har sai naga dawowan yaran nan gida.
"Murmushi Engr yayi kafin yace Amman Irfan kuma Ammah na.
"Zama tayi tana me murmusawa kafin tace" ina saurarenka meke damunka.
"Shiru kaman mai nazari sai kuma ya shafi gashin kansa ya soma fad'in" Ammah, akan Deejah ne, gaba d'aya d'abi'un ta yana mun shige dana Fateemah, ina ganin fuskan Fateemah a fuskanta, yanayinta yana mun tamkar Fateemah,...... "Shiru yayi kaman wanda ya tuna wani abin.
"Cikeda tausayin d'an nata Ammah ta matso dap dashi hannayensa ta rik'e cikin nata, a hankali ta soma fad'in" Nazif har yaushe zaka cire son Fateemah a ranka, har yaushe zaka fuskanci rayuwa yanda tazo maka, Fateemah ta tafi she's gone forever. Koda ace Fateemah tana raye bazata zama *Mallakin Ka* ba, ta riga tayi aure da waninka balle ma bata raye." Soyayyan da Irfan keyiwa Deejah da kuma soyayyan da gaba d'aya ahalin gidan nan suke mata shiyasa kake ganinta tamkar Fateemah. Ammah ta kuma rik'e hannun Engr sosai kafin tace" Son, you need to let go of your past, ka mance da Fateemah har abada a duk sanda ka tunota kayi mata addu'a, snn kayi k'ok'ari yakice tunanin ta a zuciyarka, Allah yana tare da kai bazaka tab'e ba da yardansa,
"Murmushi Engr yayi yana mai sunbatan hannayen Ammahn sa, hak'ik'a Ammah jigo ce babba a rayuwarsa, yayi godiyawa Allah da ya bar masa uwarsa har yau a raye, wacce ta kasance garkuwa ma rayuwar sa......."Suna a haka wayar Engr ta soma ruri, Nadiya ce me kira.
"Engr yana dagawa daga d'aya b'angaren Nadiya ta soma fad'in "Daddy it's Deejah, she fainted a while ago a wajen event....."Innalillahi wa inna'ilahirrajun Engr ke fadi, ya mike tsaye yana tambayan Nadiya me ya faru wani asibiti, suke,..... "Ammah ma mikewa tayi tana kallon Engr cikeda firgici.
"Engr na gama waya da Nadiya ya sanar wa Ammah halin da ake ciki, salati Ammah ta shiga yi babu shiri ta fice zuwa sashenta dan dauko mayafi, Engr da kansa yayi driving nasu zuwa hospital din.
"Irfan na zaune a gefenta tana jingine da pillow hannunta na hangu mak'ale da drip ruwa yake bata a cup tana kurb'a da kyar. Yayinda Ahidjo, Sadiq, Nadiya da Ruqayya ke tsaye gefe duk suna mata sannu.... "Su Ammah da Engrne sukayi sallama suka shigo, kai tsaye wajen gadon suka nufa sunai ma Deejah sannu suna tambayan me ya faru, Irfan ne ya soma masu bayani"
"Dr yace there's nothing to worry about, she's been stressed up da hidiman biki and bata son cin abinci yunwa ne yasa ta sume.
"Ammah ta karasa ta dafata tanai mata sannu, nan sauran jama'an dake cikin d'akin suka soma gaida Engr da Ammah. "Engr ya matsa kusanta yanai mata sannu" Gaba d'aya sai kunya ya lullub'e Deejah, sai faman sunne kai take.
"Engr ya dubi su Nadiya yace" ina Aunty naku??
"Cikin sauri Azee ta soma fad'in" daddy dama zata biya gidan amarya tace zasu kai kaya itadasu Aunty Salma.
"Gyada kawai yayi dan kuwa abun Laila ya soma damunsa, aiko da biki ake ta sanar dashi idan zata wani wajen, ganin halin da ake ciki yasa sa kau da tunanin, daga haka su Sadiq Ahidjo dasu Nady da Azee suka fice zuwa reception
"Engr ya dubi Irfan yace" Son" daga yau a dakatar da sauran Events din da ba'ayi ba, idan Allah ya kaimu ranr daurin auren kawai sai a daura auren. "Ammah tace hakan yayi lafiya ai yafi komai.
"Kai kawai Irfan ya gyada kafin yace" toh daddy.
"Ina Dr din I want to speak with him. Cewar Engr, kan ya gama rufe baki Dr ya shigo lokacin drip dinma saura kadan.
"Bayan sun gaisa da Engr, nan suka soma tattauna lamarin, Dr yace babu komai stress ne kawai da yunwa, drip na karewa za'a discharging nata basai ta kwana ba. A tare Dr da Engr suka fice suna magana.
"Azee tana fita ta shiga neman layin Laila, nan ta shafa mata komai abinda ake ciki, wata shewa Laila ta kwashe dashi ta dubi Safwan dake gefenta ta kashe masa ido guda, nan tace wa Azee ta kwantar da hankalinta komai zai zama normal, Irfan ya kusa zama *Mallakin ta* daga haka tayi hanging up. Azee kuwa rik'e wayar a hannu tayi tana nazarin kalaman momynta Laila.
"Drip na k'arewa aka sallamesu.
"Suna tsaye a haraban asibitin su uku kafin su Ammah su fito da Deejah, Irfan ya kalli Sadiq da Ahidjo yace, Friends na gode sosai da kulawarku a gareni.
"Murmushi sukayi kafin Sadiq yace" come on guy babu godiya ai, you are indeed our bro from another mum right Ahidjo??? Ya k'areshe maganar yana duban Ahidjo. Ahidjo ya gyada kansa kana yace "Sure haka ne Sadiq. Hannu Ahidjo ya mik'a masu kafin yace barinje na duba su Ashraf, daga can zan wuce gida, ya dubi Irfan yace "Friend Allah k'ara sauk'i a gaida madam sosai. Murmushi Irfan yayi suka danyi hugging juna kafin yace Alright sai munyi waya..
Sadiq ma nan yayi waya ya sanar da mamie jikin Deejah da sauki gashi nan dawowa da Ruqayya. Nan sukayi sallama da Irfan shima ya wuce.
"Su Ammah na fitowa itada Nadiya rik'e da Deejah, ji yayi kaman yaje ya sungumeta ko ya rungumeta cikin k'irjinsa, da sauri ya k'araso ya bud'e masu mota suka shige nan shima ya shihe driber seat sai faman juyowa yake yana mata sannu...kai tsaye suka nufo gida,
"Irfan sai faman rirtata yake, baby ko na d'aukeki ne? Bata iya ce masa komai sai girgiza kai kawai, parlorn Ammah ta zauna da kansa ya shiga kitchen had'o mata shayi, babu yanda su Ammah dasu Nadiya basuyi ba ya bari suyi d'awainiyar Deejah fir yak'i da kansa ya had'o tea din. Ammah ta tan'e baki gamida yin murmushi, tace baban soyayya ba d'aki ta wuce bayan tayi ma Deejah Allah k'ara sauk'i
, "ya zauna gefenta yace oya seat up ki shanye wnn yea din,.... zatayi gardama taga babu alamun wasa a fuskansa.
"Babu musu ta karb'a ta soma sha, ....."Laila ce ta shigo fuskanta cike da damuwa kaman gaske, kai tsaye wajen Deejah ta nufa ta soma mata sannu
"Oh my dear you must be nervous, but dole kici abinci, ai hidiman biki ya gaji haka, tasa hannu ta karb'i cup din daga hannun Irfan, ta shiga bata a baki. Ta kalli Irfan cike da kulawa tace" Son I know you must be exhausted, you need some rest, kaje ka kwanta I'll look after her for you kaji son, ta k'areshe maganar cikin sigan yaudara.
"Babu yanda Irfan ya iya dole ya amince da batun Laila, yana bata matsayi sabida yanda take kula dasu baki d'aya.
"Kallon Deejah yayi wanda itama shi take kallo kafin yace" baby make sure you take all your prescriptions okay, I love you, ya hura mata kiss kan tafin hannunsa,
"Ba Azee dake lab'e kan staircase tana kallonsu ba harta Laila dake zaune gabansu kaman hoto saida abun ya tab'ata, tabd'ijam wani irin so Irfan keyi wa Deejah, ganin dai zata rasa mind dinta yasata saurin composing kanta ta maida hankali wajen kula da Deejah, Azee kuwa sulalewa tayi a wajen tana maysan k'walla dan kuwa tasan Irfan bazai tab'a sonta ba, babu shakka zuciyan Irfan *Mallakin Deejah ne*......
👸🏻QueenSamy😍💄👄.......
[8/28, 14:08] Umar Dalha: 🌗🌗🌗🌗 *Mallakin Waye*
55
*©Sameena Aleeyou*
_Queen Samy Novels Forum.....📖📚_
"Tunda ta kwanta ta kasa samun nitsetsen barci sakamakon wasu irin sararan mafarkai marassa kyau da take tayi, mik'ewa tayi da k'yar ta shige bathroom ta d'auro alwala tazo ta tada sallah.
"Tana nan zaune bisa sallaya wayanta ya soma ruri, wanda haka ya sauk'ar mata da mummunar fad'uwan gaba, da kyar ta iya k'arasawa jikin socket ta shiga kallon screen d'in wayar, ganin bak'uwar lamba ce yasata kuma jin wani fad'uwan gaban wanda ita kanta batasan dalilinsa ba.
"Har saida wayar ya yanke bata sami courage na d'auka ba, nan aka kuma kiranta, da k'yar ta iya sa hannu ta cire daga jikin chargi kafin ta k'ara a kunnuwanta had'e da sallama.
"Daga d'aya b'angaren aka bushe da dariya kafin yaci gaba da fad'in"
"Congratulations my dearest one, So kin zata zaki guje min a cikin garin nan kije kiyi aure, kin zata zan daina sonki ne har abada ko kuma kin zata zaki iya b'ace mun ne Deejah??
"Cikin k'unan rai Deejah ta soma fad'in" what do you want from me Safwan, me kake so a wajena, meyasa kake kirana....."Saurin k'atseta yayi da fad'in" Ke nake so Deejah, ke kanki kinsan da haka, ever since I met you my dream is to be with you, how dear now zaki juya mun baya, after all that I've done to you is that how repay me Deejah, com'on fad'a mun me kike nufi da kika gudu kika barni, kin mance duk irin taimaka ma rayuwarki da tsare rayuwarki da nayi a can baya.
"Cikin kuka take fad'in" Safwan banci amanarka ba hasalima ban tab'a furta ina sonka ba, dan Allah na rok'i arzikinka ka fita hanyata pls, kar ka rusa mun farin cikin da nake ciki......"Dariya Safwan ya kwashe dashi kafin yace" Deejah yaushe kika yi sanyi haka, yaushe kika soma bada hak'uri wa mutane, tabbas lallai kina son wann miji naki da kike shirin aura, "amma dai inaga Familyn Nazif Mumtaz basu wacece d'ansu ke shirin aura ba, kokuma nace shi angon naki baisan wacece ke ba....
"A zabure Deejah ta mik'e daga yanda take zaune ta nemi kukan da take ta rasa, cikin sark'ewar murya take fad'in" Me ka isa ka min you juck, let me make this clear to you wllhi baka isa ka rabani da farin ciki na Irfan ba, da kake cewa basu sannni ba, k'warai sun san ko ni wacece tinda sunsan daga Orphanage nake daga gidan marayu nake sunsan labarin yanda iyayena suka salwanta, and still they accepted me the way I'm, so am quite sure there's nothing you can do to make them reject me....... "Woow! Bravo my dear, ashedai har yanzu bakin naki na nan, toh barikiji na gaya maki, ni nan Safwan inada abinda zaisa su tsaneki su tsani saninki da sukayi har abada, ba Irfan kawai ba duk wani masoyin Irfan sai ya tsaneki...... "Ki duba whatsapp dinki kiga pictures da videos din na tura maki, am quite sure zaki kirani ki nemi solution if not am gonna revealed it to the world. Daga haka ya katse kiran ya barta a tsaye tamkar gunki.....
"Jiri na neman kada ita sanda ta shiga whatsapp dinta taga Vidieos na rawan da tayi a club wanima maza sun sakata a tsakiya, ga kayan jikinta duka babu kyaun gani, ga pictures dinta marassa kyaun gani duka na club ne..... "Runtse idonta tayi ta soma karanto "Innalillahi wa inna'ilaihirraji un tana mai sulalewa a k'asa...."Me Safwan yake nufi da ita, me zai faru idan ahalin gidan nan suka ga wann pics da videos, wani irin kallo Irfan zai mata... "Tunaninta ya katse sanda ta tuna Irfan yasha fad'a mata babu abinda ya tsana a duniya kaman mace me zuwa club mace maras kamun kai, shin idan yaga wnn abu wani irin kallo zai mata...."Kuka ya kuma kufce mata da sauri ta shiga dialing numbern Safwan tana mai girgiza kai tana fad'in" No that can't be, bazai yuwu ba.......
"Da dariya ya d'aga wayan kafin yace" I knw you must call back, now kin yarda inada abinda zanyi ruining life d'inki...."Cikin kuka take fad'in"Safwan videos da pics din daka turo tsohuwar Deejah ce ba Deejahn yanzu ba, I've changed already, dan Allah kar ka ruining mun life din da nike ciki a yanzu I beg of you pls....."Cikin d'aga murya Safwan ya katseta da fad'in" Just shut up Deejah, did you think you I can let you go, kina tunanin zan daina sonki ne, well if you think that I'll leave for someone else then you're mistaken. I prove you wrong, bazan tab'a barinki ma wani ba Deejah, you are mine we are meant for each other besides we bothe suite each other mun dace da juna. Ina mai baki shawara idan baki so su san wnn hali naki just called up tje wedding just cancel your wedding with Irfan if not your precious life is inndanger, zannk'ara da abinda bakima yi ba na kuma sanar dasu har yanzu muna had'uwa a club....."Enough of this you juck, how could you blackmail me Safwan, if you truly loved me kaman yanda kake fad'a then let me be with the love of my life Irfan, let me with the family I love the most,... "Ta d'an sassauta murya kafin taci gaba da fa'din" Dan Allah Safwan karka min haka kar ka rabani da mutanen da nake jinsu kaman 'yan uwana na jini, kar ka rabani da mutanen da suka nuna mun tsan tsan so da k'auna......"Safwan ya katseta da fad'in" And if you don't want that to happen then ki fasa auren Irfan, ki janye batun auren Irfan ni kuma na miki alk'awarin babu wanda zaisan wancan abu da kikayi a baya, ki yarda dani Deejah na maki alk'awarin samun farin ciki maras misaltuwa farin cikin da kike mafarkin samu zan tanada maki su a gidana... "Shawara ya rage naki Deejah kinada zab'i guda biyu" Is either ki fasa auren Irfan asirinki ya rufu ko kuma ki amince da aurensa asirinki ya banka'du... daga haka Safwan ya kashe wayar yana murmushin mugunta.
"Dafe kanta tayi ta zube a wajen zuciyarta na barazanar tarwastewa, ta nemi addu'a ma ta rasa, wani irin tausayin kanta ne ya kamata, Allah sarki rashin iyaye babban ciwo ne, yau da tanada nata iyayen ta tabbata da makamancin haka bai faru da ita, tana tsananin son Irfan fiye da yanda take sin kanta, bata jin zata iya rayuwa da wani mahaluk'i bayan Irfan, ta tuna irin kalan soyayyan da yake nuna mata, ta tuna yanda ya yarda ya amince da ita koda basu san tak'amemmen iyayenta ba, ta tuna yanda familyn Irfan suka d'auke ta, shin idan suka ga wann mummunan hotuna da videos me zasu kalleta dashi, "Zuciyarta ya shiga raya mata zasu tsaneki yanda baki tsammani, babu kaman Irfan sai ya tsaneki fiye da mutuwa, shin kin tuna wani rana sanda kuka d'auko Ahidjo da Yusra a club, kin tuna yanda Irfan yayi reacting, wata d'iya mace ma kenan balle ace matan da yake shirin aure itace cikin irin wnn yanayi yaya kike ganin lamarin zai kasance...."Da sauri ta shiga toshe kunnuwanta tana girgiza kai ta soma gamida tak'urewa jikin gado tana rawan d'ari dan kuwa zazzafan zazzab'i ne ya sauk'ar mata. Sai yanzu take d'an danasani maras iyaka gameda rayuwar zuwa club da tayi, dama haka ne kar mutum ya raina aikin sab'o komin k'ank'ancinsa sanadiyan k'arami yakan iya zama babba, ko wani sharri Safwan ya lak'a mata babu wanda bazai yarda ba muddin suka ga wann video, Allah sarki rayuwa kenn mutum baya wuce kaddaransa a rayuwa... Runste idanunta tayi hawaye masu zafi suna bin k'uncinta, yayinda kyakkyawan fuskan abun k'aunarta Irfan ke mata gizo.....Baccinnda bata samu har wayewar.
"Duk bai wani sami ishesshen barci ba, hankalinsa na kanta, ya k'agu gari ya waye yaga yaya ta kwana, gashi through out the night neman wayarta yake daga farko yaga line busy daga baya yaji wayar gaba d'aya a kashe, ya danganta hakan da rashin wadaceccen network, .
"Tsaf ya shirya cikin Royal blue Jampa ya saka hula zanna bukar dark blue, woow zokaga yanda shigar ya karb'esa musamman dashike ba gwanin saka manyan kaya bane, turaren Vasece ya feshe jikinsa dashi ga agogo mai tsadan gaske da ya d'aura a hannunsa, kai masha Allah, sosai Irfan yayi kyau kana ganinsa ba sai ance maka ga ango ba, kai tsaye sashen Engr ya wuce dan gaishesa nan ya sami Laila na serving Engr break fast.
"Da sallama ya shigo yayinda suka amsa gaba d'aya fuskokinsu d'auke da murmushi suna daga dinning area. "Son k'araso mana Engr ya fad'i yana mai alama da hannu.
"Karasowa yayi ya zaune gefen kujeran Engr kadin yace" Daddy ina kwana, Engr ya amsa masa da sakin fuska kafin ya gaida Laila, itama faram faram kaman kullum ta amsa masa sai zolayansa take shikam Irfan murmushinsa mai class kawai yake yai.
"My dear I know you haven't eaten your break... let me serve you cewar Laila dake k'ok'arin bud'e warmers.
"Dan murmushi Irfan yayi kafin yace" No Aunty barin lek'a Deejah am ok though, daga haka ya mik'e, muryan Engr ya jiyo yana fad'in" Irfan yau mutanen Katsina zasu iso, nayi bucking masu flight, inaga by 12noon zasu iso, so sai ka sanar da drivers suje su dauko su a airport idan time din yayi, ni yanzu Office zan wuce I hope kaima zaka lek'o dan akwai wani desing na nake so kayi observing kafin a soma ginawa..... ."Da sauri Laila ta katse Engr da fad'in" Haba dai Daddy ai yau ranar Irfan ce, bai kamata yaje Office ba har sai nan da sati uku kafin nan ya gama cin angoncinsa.... "Engr na murmushi ya dubi Irfan dake faman sosa k'eya kana yace" wai hakane Son, hutun bai maka yawa ba... "'Dan murmushi Irfan yayi kafin yace" hakane daddy huyun baiyi yawa, I was even planning to go for Honeymoon, Engr ya kuma yin murmushi gamida fad'in" come here son ya bud'e masa hannunsa alamun runguma, nan irfan ya karasa yayi hugging mahaifin nasa, Allah yayi maka albarka Irfan cewar Engr, Laila dake ta faman murmushin yak'e da sauri tace ameen. Shima Irfan din da ameen ya amsa kafin yace thank you daddy, thank you for always been there for me, I love you, murmushi Engr ya kuma kafin yace" anything for you son, I love you too, when you finish deciding wani country kuke son zuwa Honeymoon you should let me know ok, sai na maku arranging komai. Godiya Irfan ya kuma yi wa Engr. Laila tana tayasa godiya kamar mutuniyar arziki. Mikewa Engr yayi ya nufi stirs
"Irfan ya juyo da dubansa ga Laila kafin yace" Aunty I forgot to ask you, jiya kuwa baby tasha maganin?
"Nan da nan Laila ta saka fuskan tausayi kafin tace" uhm Irfan bansan meke damun bride to be d'inkan nan ba, babu yanda banyi ba ta fad'a mun idan akwai abinda ke damunta amma tak'i, I don't know ko har yanzu bata sake dani bane, amma kai nasan zata iya fad'a maka tunda you are about to be her husband bazata b'oye maka komai ba.
"Kallon mamaki Irfan keyiwa Laila kafin yace" meke damunta Aunty...
"Laila ta dan saka fuskan tausayi kafin tace" my point exactly, nayi nayi ta fada mun tak'i watak'ila kai zata fad'a maka..... "Cikin sauri ya mik'e ba tareda ya gama jin me Laila ke fad'i ba ya fice.
"Babu yanda Hajja batayi ba Deejah ta saka wani abu a cikinta amma tak'i, Deejah ta kalli Hajja da idanunta da suka rine kafin tace"Hajja dan Allah kosu Ammah sun neme ni kice ban tashi ba.
"Hajja ta sauk'e ajiyan zuciya kafin tace" Ammah dai ta tashi amma su Nadiya kam basu tashi ba, su nilam kuma sun tafi sch duk da anyi yak'i dasu kafin suka tafi, wai yau bazasu ba ana biki a gidan su.
"Sauk'e ajiyan zuciya Deejah tayi kafin tace" Irfan fah? Kinga itowarsa.... "Girgiza kai Hajja tayi alamun a'a kafin tace" Khadeejatu wai meke damunki....."Knocking din da akayi a k'ofa ne ya katse su........
0 comments:
Post a Comment