A hankali ta tsallako tatitin kai tsaye kuma ta shige dogon layin dake gabanta,ta dubi tsahon layin duk da yawan al'ummar da yake da shi a dade yake babu kowa tankar anyi shara,hakan baya rasa nasaba da irin ranar da ake kodawa kamar mutum yaa dora hannu akansa yace wayyo Allah
sannu a hankali take ci gaba da tafiya tamkar mai tausayin qasa,a zahirance idan ka ganta sai kayi tsammanin ranar bata dameta ba saboda yanayin yadda take tafiya,saidai sam tana daga cikin wadanda rabar ma tafi gallaba,don har Allah Allah take taga ta isa gidansu,saboda leshin dake jikinta dinkin riga da skert da kuma dogon hijabinta mai hannu dake qara mata zafi wanda ya zamo too match ne da kaya jaka da 'yar jakar swagger dake maqale a kafadarta
babu wata doguwar tafiya ta iso qofar gidan nasu wanda ke rukunin gidajen marasa wadata,duk da ginin bulo da bulo ne saidai bai samu arziqin fulasta ba bare a kai ga fenti,ta cire jakar kafadarta tana shirin shiga soron gidan idanunta ya sauka kan hauwa wadda ta cakare cikin kwalliyar atamfa,wani matashin saurayi ke fiskantarta wadda yanayin tsaiwar tasu kawai zai fahimtar da kai zance suke,dauke kanta tayi tamkar bata gansu ba don wannan dabi'a ta hauwan bama ita ba duka yaran gidan na bata haushi
ta tsakiyarsu ta raba zata wuce kasancewar babu wata hanya sai ita taji saurayin na fadin‘’barka da dawowa antyn mu‘’
‘’yauwa sannunku‘’ta amsa masa ba yabo ba fallasa tare da shigewa cikin gidan
hauwa dake binta da harara kamar qwayar idonta zai fado ta ja wani matsiyacin tsaki
''gaskiya haruna kana bada ni wallahi,wai ksi me yasa kullum baka da,burin da ya wuce ka yarfani a gun wannan matar ne,me ma kake nufi ne ni fa ban gane ba''
''yanzu laifi ne kulu don na gaisheda yayarki,kuma fa kin sani tana da kirki wlh,uwa uba ilimi da nutsuwa''
cike da masifa hauwa ta qwalalo ido
''iyeee,to ko zaka koma gurinta ne haruna,a gabana zaka dinga yaba wata uwar mata da ta shekare gaban iyaye aka rasa mai dauka?''
‘’yauwa sannunku‘’ta amsa masa ba yabo ba fallasa tare da shigewa cikin gidan
hauwa dake binta da harara kamar qwayar idonta zai fado ta ja wani matsiyacin tsaki
''gaskiya haruna kana bada ni wallahi,wai ksi me yasa kullum baka da,burin da ya wuce ka yarfani a gun wannan matar ne,me ma kake nufi ne ni fa ban gane ba''
''yanzu laifi ne kulu don na gaisheda yayarki,kuma fa kin sani tana da kirki wlh,uwa uba ilimi da nutsuwa''
cike da masifa hauwa ta qwalalo ido
''iyeee,to ko zaka koma gurinta ne haruna,a gabana zaka dinga yaba wata uwar mata da ta shekare gaban iyaye aka rasa mai dauka?''
ganin hauwan ta hau da yawa yasa ya sassauto''haba kulu na,wata kai yake a gurina ai kema kin sani,ni mai zanyi da wata mace a duniya indai ba ke ba?''
duk da koda tan da yayi ta dade a kumbure kafin ta sauko ta yarda suci gaba da tadinsu
duk da koda tan da yayi ta dade a kumbure kafin ta sauko ta yarda suci gaba da tadinsu
sallama tayi tsakar gidan kamar yadda ta saba duk da ta san babu mai amsa mata matuqar ba mamanta bace a tsakar gidan ko hindatu,ile kuwa bata samu kallon arziqi ba bare na tsiya duk da inna hadiza dake zaune gabas da tsakar gidan nasu tana kasa wake da shinkafar siyarwarta cikin samirun da duka suka sha lamba,zaune kusa da ita kuma huwaila ce ke nata zarafin na qulla kunun tsamiya cikin farar leda tana lodawa a botiki
bata fasa ce musu sannunku ba kamar yadda basu fasa ja mata tsaki ba tare da binta da harara har ta cire toms dinta ta kwashesu a hannunta don gudun samun sabani ta shige rumfar mahaifiyarsu ba da sallama,tana iya jiyosu sun fara sana'ar tasu wato yada habaici da baqaqen maganganu
''hmmm idan da ranka kasha kallo,kaje ka gama yawon dandinka ka dawo dakin uwa kayi zamanka''
''kema huwaila idan banda abinki a banza suka qi aurar da ita?ba ana fasa musu kai da cewar kyakkya wa,bace 'yarsu?,ai dole su maisheta jari''
''hmmm,Allah wadaran naka ya lalace kuwa,wataran kuwa za'a dire abun kunya cikin gidan nan,a juri,zuwa rafi da tulu debo ruwa''
''hmmm idan da ranka kasha kallo,kaje ka gama yawon dandinka ka dawo dakin uwa kayi zamanka''
''kema huwaila idan banda abinki a banza suka qi aurar da ita?ba ana fasa musu kai da cewar kyakkya wa,bace 'yarsu?,ai dole su maisheta jari''
''hmmm,Allah wadaran naka ya lalace kuwa,wataran kuwa za'a dire abun kunya cikin gidan nan,a juri,zuwa rafi da tulu debo ruwa''
duk sunajin abunda suke fada daga ita har maman tata,wanda idan da sabo tuni sun saba,saidai babu mai tanka musu,kan dadduma ta taradda maman tata,da alamu sallar azahar take abatarwa,saboda haka ta sabule jakarta ta ajjiyeta saman kujera hade da hijabinta ta sake yowa tsakar gida don,dauro alwala,har ta gama,alwalar tata basu fasa muna nan maganganganunsu ba,babu wadda ta daga kai ta kalla a cikinsu duk da irin suyar da zuciyrta ke mata da radadi,ta ajjiye,silifas,din da ta daura alwalar tana niyyar shigewa rumfar tasu
isyaku dan wajen inna,hadiza ya tawo a guje hannunsa dauke,da kwanonsha cike da kunu,bata ankara ba taji shi yana bin skert dinta ziwa qafafunta,da,sauri ta kalli yaron dake tsaye qerere ya zuba mata ido tace''haba isyaku me yasa baku iya tafiya ne a hankali?''
baki ya murguda ya galla mata harara
''eh din,ba sai a koya min ba,ban iya ba,aikin banza taqi aure ta damu mutane cikin gida''
ranta ne yayi masifar baci,yaron da a qalla ta bashi shekaru kusan goma sha biyar shi zai tsaya a gabanta yana gaya mata haka,hannunshi ta,finciko ya qaraso gabanta,kafin ta aiwatar da komai ta jiyo muryar inna hadiza cikin kaushi da haya gaga tana fadin
''ke,kada ki kuskura ki taba min yaro wallahi,idan kuwa kika sake hannunki ya kai kanshi to zamu kwashi 'yan kallo dake wallahi''
baki ya murguda ya galla mata harara
''eh din,ba sai a koya min ba,ban iya ba,aikin banza taqi aure ta damu mutane cikin gida''
ranta ne yayi masifar baci,yaron da a qalla ta bashi shekaru kusan goma sha biyar shi zai tsaya a gabanta yana gaya mata haka,hannunshi ta,finciko ya qaraso gabanta,kafin ta aiwatar da komai ta jiyo muryar inna hadiza cikin kaushi da haya gaga tana fadin
''ke,kada ki kuskura ki taba min yaro wallahi,idan kuwa kika sake hannunki ya kai kanshi to zamu kwashi 'yan kallo dake wallahi''
bata saurari kurarinta ba ta yarfawa isyaku mari domin dama ko da,safe kafin ta fita sai da ya mata wata tijarar kuma tana kallo bata ce uffan ba sai dariya ma data sheqe da ita ,ai kuwa kanta tayo yana fadin
''kutumar uba,wallahi yau sai kin gane shayi ruwa ne''
gadan gadan ta nufota wand hakan yayi daidai da shigowar malam mamuda cikin gidan
''kai kai lafiya?''
''yauwa malam gwara da Allah ya kawoka,wallahi mun gaji da zaman wannan balagaggiyar tsakaninmu,ita ba aure ba ita ba karuwanci ba,ta ishemu ta ishi yarranmu?''ya katseta da fadin
''to yanzu me kuma ya faru?''
''wai wannan dan talilin yaro ta daddage ta zabgawa mari don kawai ya zuba mata kunu bai sanig bau,to wallahi ba zan yarda ba,ko ya rama ko ni na rama masa da kaina''
''kutumar uba,wallahi yau sai kin gane shayi ruwa ne''
gadan gadan ta nufota wand hakan yayi daidai da shigowar malam mamuda cikin gidan
''kai kai lafiya?''
''yauwa malam gwara da Allah ya kawoka,wallahi mun gaji da zaman wannan balagaggiyar tsakaninmu,ita ba aure ba ita ba karuwanci ba,ta ishemu ta ishi yarranmu?''ya katseta da fadin
''to yanzu me kuma ya faru?''
''wai wannan dan talilin yaro ta daddage ta zabgawa mari don kawai ya zuba mata kunu bai sanig bau,to wallahi ba zan yarda ba,ko ya rama ko ni na rama masa da kaina''
''kai isyaku me yasa haka''
''baba ban sani bane ba fa,kuma ni wallahi sai na rama''
''ke *maryam* bashi haquri''
babu yadda ta iya haka tace kayi haquri
shi kuma ya tubure ramawa zaiyi,da qyar uwar tasa ta lallabashi ya haqura
hawaye na bin kuncinta ta shige dakin nasu,maman na zaune bisa daddumar yadda ta barta ko motsawa bata yi ba bare tasa baki a cecekucen da akeyi,bata ce da maryam din uffan ba kamar yadda itama batace din ba,ta dauki dadduma guda daya daga inda suke ajjiyewa ta tayar da sallah
''baba ban sani bane ba fa,kuma ni wallahi sai na rama''
''ke *maryam* bashi haquri''
babu yadda ta iya haka tace kayi haquri
shi kuma ya tubure ramawa zaiyi,da qyar uwar tasa ta lallabashi ya haqura
hawaye na bin kuncinta ta shige dakin nasu,maman na zaune bisa daddumar yadda ta barta ko motsawa bata yi ba bare tasa baki a cecekucen da akeyi,bata ce da maryam din uffan ba kamar yadda itama batace din ba,ta dauki dadduma guda daya daga inda suke ajjiyewa ta tayar da sallah
ta dade akai tana miqawa Allah kukanta kafin ta sallame,tana ninke sallayar ne taji maman tace
''na sha gaya miki maryam dole kici gaba da haquri matuqar dai kina zaune ne cikin gidan nan''wasu sabbabbin hawayen ne suka zubo mata,ta koma gefan daya daga cikin kujerun falon ta zauna tana fadin
''mama,ke kanki shaida ce akaina,amma duk yadda kakai ga haqiri wataran mutanen gidan nan sai sun saka kayi misbehaving,yanzu mama kamar isyaku fa qanin bayana mama?''
''ya isa kada ki saka abun cikin ranki,Allah yana tare dake ba wai ya manta da ke bane''
cikin sanyi wanda ya zamto halittarta ta goge fuskar tata cike da tawakkali da miqa lamuranta ga Allah
''to mama''shine abunda ta fada a sanyaye
,
Hundatu ce tayi sallama ta shigo rumfar sanye da unifoam ruwan tsamigaye riga da zani sai farin hijabinta kafadarta rataye da jakar makaranta fara,tana cire takalminta hade da socks tace
''anty maryam ya na ganki yau a gida da wuri?''
dan dafe kanta tayi kadan tace''yau da wuri na kammala aikin ne shi yasa,kuma dama bana jin dadi sosai''
cikin nuna damuwa ta zauna saman kujera
''sannu antin mu,ko na karbo miki magani?''
murmushi tayi har fararen jerarrun haqoranta suka bayyana
''idan banda abun hindu wanne me chamist za'a samu da uwar ranar nan?''
ta dage gira''haka ne fa anty''
''ki duba locker kusa da gadona akwai paracetamol ki dauko ki sha,tuntuni da kika shigo baki gayamin ba har kika tsaya fada da mutane ko?''
''na sha gaya miki maryam dole kici gaba da haquri matuqar dai kina zaune ne cikin gidan nan''wasu sabbabbin hawayen ne suka zubo mata,ta koma gefan daya daga cikin kujerun falon ta zauna tana fadin
''mama,ke kanki shaida ce akaina,amma duk yadda kakai ga haqiri wataran mutanen gidan nan sai sun saka kayi misbehaving,yanzu mama kamar isyaku fa qanin bayana mama?''
''ya isa kada ki saka abun cikin ranki,Allah yana tare dake ba wai ya manta da ke bane''
cikin sanyi wanda ya zamto halittarta ta goge fuskar tata cike da tawakkali da miqa lamuranta ga Allah
''to mama''shine abunda ta fada a sanyaye
,
Hundatu ce tayi sallama ta shigo rumfar sanye da unifoam ruwan tsamigaye riga da zani sai farin hijabinta kafadarta rataye da jakar makaranta fara,tana cire takalminta hade da socks tace
''anty maryam ya na ganki yau a gida da wuri?''
dan dafe kanta tayi kadan tace''yau da wuri na kammala aikin ne shi yasa,kuma dama bana jin dadi sosai''
cikin nuna damuwa ta zauna saman kujera
''sannu antin mu,ko na karbo miki magani?''
murmushi tayi har fararen jerarrun haqoranta suka bayyana
''idan banda abun hindu wanne me chamist za'a samu da uwar ranar nan?''
ta dage gira''haka ne fa anty''
''ki duba locker kusa da gadona akwai paracetamol ki dauko ki sha,tuntuni da kika shigo baki gayamin ba har kika tsaya fada da mutane ko?''
ta karyar da kai ''ayyah maman mu ba haka bane,sallah kinga muka gama yanzun ai''
''dawa antin tayi fada mama?,wannan maras kunyan ne isyaku ko?''
''shine mana''
a fusace ta miqe zata fita maman ta yi kiranta
''ina kuma zaki?''
''mama don Allah ki barni naje naci uwar yaron nan don Allah,yayi matuqar raina yaya maryam,dan iska mara kunya kawai''
''ko da wasa naji kinje gurinsu sai na sabarmiki''
ba haka taso ba amma babu yadda ta iya haka ta wuce daki tana kumbure kumbure ta sauyo unifoam dinta ta dawo dan kitchen dinsu wsnda daki ne gudun tashin hankali suka maida shi kitchen ta zubo musu shinkafa da miya da salad da maman tayi a faranti daya,duka suka sa hannu
''dawa antin tayi fada mama?,wannan maras kunyan ne isyaku ko?''
''shine mana''
a fusace ta miqe zata fita maman ta yi kiranta
''ina kuma zaki?''
''mama don Allah ki barni naje naci uwar yaron nan don Allah,yayi matuqar raina yaya maryam,dan iska mara kunya kawai''
''ko da wasa naji kinje gurinsu sai na sabarmiki''
ba haka taso ba amma babu yadda ta iya haka ta wuce daki tana kumbure kumbure ta sauyo unifoam dinta ta dawo dan kitchen dinsu wsnda daki ne gudun tashin hankali suka maida shi kitchen ta zubo musu shinkafa da miya da salad da maman tayi a faranti daya,duka suka sa hannu
hindatu tace''dama zamu samu ruwan sanyi yadda ake zabga ranar nan wlh''
''ai insha Allahu da na dauki albashina,zan siya mana qaramin firji''
cike da doki hindatu tace
''eh wlh yaya''
mama ta dubi maryam din''yanzun maryam ba zaki yiwa kanki fada ba?,bama zancan aure kike ba zancan siyan firji kike ki saka mana,duk yadda mutane ke maganganu tamkar ma ke din baki damu ba maryam?''
''ai insha Allahu da na dauki albashina,zan siya mana qaramin firji''
cike da doki hindatu tace
''eh wlh yaya''
mama ta dubi maryam din''yanzun maryam ba zaki yiwa kanki fada ba?,bama zancan aure kike ba zancan siyan firji kike ki saka mana,duk yadda mutane ke maganganu tamkar ma ke din baki damu ba maryam?''
duk sai taji abincin ya fice mata a ka,ta sunkuyar da kanta,Allah ne kadai yasan abinda take ji a zuciyarta,itakam tasan ba domin mamanta bata sonta take mata wannan fadan ba,tana yine sabida qauna,ita din ma da za'a tona zuciyarta tabbas babu dadi
.
Zaune take cikin rumfar tasu wadda ke da madaidaiciyar yalwa,kujeru ne one sitter two sitter da kuma three sitter masu dan sauqin farashi,falon malale yake da tyles ruwan madara da labulaye suma ruwan madara masu sauqin kudi,sai kayan kallo da suka hada da t.v ta xaune da d.v.d,komai na falon madaidai cine dai dai talaka wanda albashin maryaman ne da qoqarinta ya kai falon ga zama haka
kusan kaf gidan babu muhallin da yakai tsaftar nan,ko yaushe zaka sameshi a goge qal yana qamshin turaren garwashi ko na tsinke,hakan ke qara haddasa qiyayya da kishi mai zafi tsakanin mama *amina* da sauran abokan zamanta
sanye take da pakistan riga da wando wanda rigar tasa ta kai mata har gwiwa,dan kwalin pakistan dinne daure a kanta,duka hankalinta ta tattarashi kacokam kan wayarta da tayi googling din wasu sabbin girke girke,shirun da dakin da ma gidan baki daya da yayi shi ya qara mata nishadi da fahimtar abunda take karantawa,
sallamar da ta jiyo anayi cikin tsakar gidan ita ta ja hankalinta,ta sauke wayar tana amsawa tare da cewa ''a shigo''
mai sallama ta sake maimaitawa lokacin da take shigowa rumfar tasu,da sauri maryam ta sauke wayar a gefanta fuskarta dauke da murmushin farinciki wandayayi sanadiyyar bayyanar dimple dinta ta miqe
''radiya..saukar yaushe kenan mutanen south africa?''
harara wadda aka kira da radiyan ta cilla mata
''hmmm,babu wani nan,wlh baki da abinda zaki kare kanki da shi,yanzu ma ni ba gunki nazo ba,mama na kawowa jikanta ta ganshi''
''oh ni maryama,laifi baya qaremin,me kuma nayi''ta fada cikin murmushi da dafe kai
harararta dai ta sakeyi''kinfi kowa sanin laifinki maryam,sati na guda da dawowa qasar nan amma ko mai kama da ke ban gani ba,ina dira nigeria kece ta farko da na fara yiwa tex amma ko matsayin reply ban samu ba''
mai sallama ta sake maimaitawa lokacin da take shigowa rumfar tasu,da sauri maryam ta sauke wayar a gefanta fuskarta dauke da murmushin farinciki wandayayi sanadiyyar bayyanar dimple dinta ta miqe
''radiya..saukar yaushe kenan mutanen south africa?''
harara wadda aka kira da radiyan ta cilla mata
''hmmm,babu wani nan,wlh baki da abinda zaki kare kanki da shi,yanzu ma ni ba gunki nazo ba,mama na kawowa jikanta ta ganshi''
''oh ni maryama,laifi baya qaremin,me kuma nayi''ta fada cikin murmushi da dafe kai
harararta dai ta sakeyi''kinfi kowa sanin laifinki maryam,sati na guda da dawowa qasar nan amma ko mai kama da ke ban gani ba,ina dira nigeria kece ta farko da na fara yiwa tex amma ko matsayin reply ban samu ba''
''yanzu dai yo haquri don sonki da annabi ki zauna tukun,don mama bata nan ta tafi kitso''ta fada tana karbe kyakkyawan baby boy din dake sabe a kafadarta,tare suka zauna idon maryam na kan yaron''masha Allah laquwwata illa billah fadil''yana kan kadarta ta shiga kitchen din su ta dauko mata ruwa da lemon sobo cikin fridge din da daqyar ta shawo kan mama da dadin bakin hindatu aka siyoshi suke lemon siyarwa a kuma fita kunyar baqi idan anyi
''bismillah''tace da ita bayan ta tsiyaya mata lemon
''bani dana kawai na wuce''
''haba sister,kada fa ayi mana dariya a ganmu a rana''
''ke kika jawo hakan ai''
''kinsan Allah banga saqonki,ki yarda dani bani da lokaci wallahi yanzu isashshe idan ba weekends ba saboda aiki''
da qyar ta samu ta shawo kan radiya bayan ta mata alqawarin zuwa mata a wannan weekend din wanda daga nan suka fada hirar duniya
''bani dana kawai na wuce''
''haba sister,kada fa ayi mana dariya a ganmu a rana''
''ke kika jawo hakan ai''
''kinsan Allah banga saqonki,ki yarda dani bani da lokaci wallahi yanzu isashshe idan ba weekends ba saboda aiki''
da qyar ta samu ta shawo kan radiya bayan ta mata alqawarin zuwa mata a wannan weekend din wanda daga nan suka fada hirar duniya
radiya ta ajiye glass cup din bayan ta kalli maryam
''maryam har yanzu dai batun aure shiru?''sakin ajiyar zuciya tayi sannan ta tabe baki
''hmmm,barni kawai radiya,samun miji na gari yanzun ya zamo wuya,mazan yanzu duka 'yan garari ne,yawancinsu ba aure ke kawosu gurinki ba''
''anya maryam,bana manta fa yawan samarin da kike da su tun muna school''
''radiya kenan......manta da wannan,na fada miki yawa yawansu ba don Allah suke sonki ba,sun lallabo ne kawai su kwashi abunda suka kwasa na rasa wannan masifa kamar hadin baki?kamar ni kadai sukewa haka,ke dai ki sani kawai a addu'a radiya''ta qarashe maganar muryarta na dan rawa alamun kuka keson zuwa mata
''shikenan maryam,insha Allahu na miki alqawari ba zan fasa sakaki cikin addu'o'ina ba,komai yayi farko yana da qarshe''
''maryam har yanzu dai batun aure shiru?''sakin ajiyar zuciya tayi sannan ta tabe baki
''hmmm,barni kawai radiya,samun miji na gari yanzun ya zamo wuya,mazan yanzu duka 'yan garari ne,yawancinsu ba aure ke kawosu gurinki ba''
''anya maryam,bana manta fa yawan samarin da kike da su tun muna school''
''radiya kenan......manta da wannan,na fada miki yawa yawansu ba don Allah suke sonki ba,sun lallabo ne kawai su kwashi abunda suka kwasa na rasa wannan masifa kamar hadin baki?kamar ni kadai sukewa haka,ke dai ki sani kawai a addu'a radiya''ta qarashe maganar muryarta na dan rawa alamun kuka keson zuwa mata
''shikenan maryam,insha Allahu na miki alqawari ba zan fasa sakaki cikin addu'o'ina ba,komai yayi farko yana da qarshe''
a hankali suka fada wasu hirarrakin nasu a haka maman ta cimma su,tunda ta dauke fadil bata dawo da shi ba sai da zasu tafi,sabulai ta bawa radiyar sinqi biyu da turare,hannu biyu amsa tayi mata godiya sannan maryam ta amsheshi ta biyo radiyan qofar gida don raka ta
''ke da nasir fa muka zo''
cikin mamaki take kallin radiyar''amma baki da mutunci,ki bar bawan Allah a mota duka lokacin nan yana zaman jiranki''
fuska ta yatsina''rabu da shi,fada mukayi da shi sulhu yake nema shi yasa''
''Allah ya shiryeki radiya ''abunda ta samu ta iya fada kenan don sun qaraso gaban motar''
''ke da nasir fa muka zo''
cikin mamaki take kallin radiyar''amma baki da mutunci,ki bar bawan Allah a mota duka lokacin nan yana zaman jiranki''
fuska ta yatsina''rabu da shi,fada mukayi da shi sulhu yake nema shi yasa''
''Allah ya shiryeki radiya ''abunda ta samu ta iya fada kenan don sun qaraso gaban motar''
gidan gaba ta shige ta dora mata fadil saman cinyarta suna gaisawa da nasir din
''munfa yi fushi maryam gaskiya''
sassanyan murmushinta tayi''to ayi haquri tunda na wanke kaina next week ina tafe insha Allahu ranan sunday''
''to Allah ya nuna mana''
sallama sukayi ta koma cikin gidan radiyan na jaddada mata ta cika alqawari fa
''munfa yi fushi maryam gaskiya''
sassanyan murmushinta tayi''to ayi haquri tunda na wanke kaina next week ina tafe insha Allahu ranan sunday''
''to Allah ya nuna mana''
sallama sukayi ta koma cikin gidan radiyan na jaddada mata ta cika alqawari fa
tana cusa kai gidan suka ci karo da *BINTA*
dauke da botikin awara zata fita inda aka fi kaurin,maryam dince ta fara ja da baya don tasan bata qi ta bangajeta ta wuce ba,duk da hakan ma dai bata tsira ba daga tsaki da harar da qanwar bayanta ta saba jifanta da su ba koda zasu hada hanya ne sau miliyan
dauke da botikin awara zata fita inda aka fi kaurin,maryam dince ta fara ja da baya don tasan bata qi ta bangajeta ta wuce ba,duk da hakan ma dai bata tsira ba daga tsaki da harar da qanwar bayanta ta saba jifanta da su ba koda zasu hada hanya ne sau miliyan
ta rasa me ra tsarewa yaran da iyayensu,gaba daya anbi an cika zukatansu da qinsu,qannenta ne duka amma babu daya dake ganinta da gashi,saidai duk da haka rashin mutunci wani yafi na wani
ga tsantsar rashin tarbiyya da qin karatu da aka dasawa zucoyoyinsu,ta rasa wannan wacce iriyar rayuwa suka zabawa kansu,da wannan tunanin ta qarasa falonsu ta zube saman kujera tana rowon Allah daukinsa kan halin da take ciki
ga tsantsar rashin tarbiyya da qin karatu da aka dasawa zucoyoyinsu,ta rasa wannan wacce iriyar rayuwa suka zabawa kansu,da wannan tunanin ta qarasa falonsu ta zube saman kujera tana rowon Allah daukinsa kan halin da take ciki
.
sanye take da material silk dark pink wanda aka yima ado zane na qaqen flowers manya,yayin da ta yane kanta da mayafi baqi tayi rolling dashi wanda ya maisheta tamkar jinsin larabawa,qaramar jaka ta sagale a gwiwar hannunta sai baqin toms mai kyau,sosai shigar tayi mata kyau tamkar bata da wata matsala a rayuwarta
sanye take da material silk dark pink wanda aka yima ado zane na qaqen flowers manya,yayin da ta yane kanta da mayafi baqi tayi rolling dashi wanda ya maisheta tamkar jinsin larabawa,qaramar jaka ta sagale a gwiwar hannunta sai baqin toms mai kyau,sosai shigar tayi mata kyau tamkar bata da wata matsala a rayuwarta
a rumfa ta tadda mama tayi mata sallama tace mata a dawo lafiya ta gaida fadil da mamarshi,suna zaune a tsakar gidan kamar ko yaushe ko wacce ta maida hankalinta kan kayan sana'arta,wanda da zaki tambayesu suk cikinsu babu wadda zata iya gaya miki taqamaimen inda yaranta suke,sana'arsu ta fiye musu komai
da sauri ta fara qoqarin ficewa daga gidan don bata fatan daya daga cikinsu ta,ganta balle ta jefeta da kalmar da zata bata ranta,saidai duk iya saurinta bata ci nasara ba sai da huwaila ta ganota
''uhmmm,mutanen burtali,an fita kenan''
bata fasa sauri don ta fice a gidan ba kamar yadda bata ko waiwayo ta dubesu ba
''uhmmm,mutanen burtali,an fita kenan''
bata fasa sauri don ta fice a gidan ba kamar yadda bata ko waiwayo ta dubesu ba
cikin soron sukayi kacibus da *AZARA*,qanwar ta ce ta hudu wadda tayi aure da yaranta uku,ba laifi mijinta na iya bakin qoqarinsa duk da wasu abubuwan bai iya dauke nauyinsu,sai kuma Allah ya hadashi da mace mai izgili izza da rainuwa,azara akwai rainuwa da izgili saidai ba laifi rashin kunyanta da sauqi akan ta sauran yaran,tunda ko babu komai idan sun hada zata tsaya su gaisa koda zata jefeta da habaici a fakaice
yanzun ma hakance ta kasance,fuskar maryam din fadade da murmushi ''maraba da mutanen fanshekara(unguwar da take aure)''ta fadi tana miqa hannu zata amshi yaron axaran yaqi zuwa saboda dan banzar qiwar da yakeyi,azaran tace
''hmmmm,sannunku kuma''
''azara yaron nan qiwa yake haka?''
''ko ba ya qiwa aike yayi miki tunda ba ganinki yake ba,mu ko nsmu gidan ba'a zuwa saboda bamu da komai''
murmushi maryam tayi,don ta fahimci inda tasa gaba
''ko daya ba haka bane azara,kinsan bani da lokaci sai weekends,to su din ma sai wani zarafin ya shigo ya cinye wunin naka duka''ta kawar da maganar don kada tayi nisa ta hanyar cewa
''ina sauran yaran?''
''kunun aya ne bai qare ba na,barsu su qarasa saidawa don kada ya lalace shi yasa ma ban taho da su ba''
''hmmmm,sannunku kuma''
''azara yaron nan qiwa yake haka?''
''ko ba ya qiwa aike yayi miki tunda ba ganinki yake ba,mu ko nsmu gidan ba'a zuwa saboda bamu da komai''
murmushi maryam tayi,don ta fahimci inda tasa gaba
''ko daya ba haka bane azara,kinsan bani da lokaci sai weekends,to su din ma sai wani zarafin ya shigo ya cinye wunin naka duka''ta kawar da maganar don kada tayi nisa ta hanyar cewa
''ina sauran yaran?''
''kunun aya ne bai qare ba na,barsu su qarasa saidawa don kada ya lalace shi yasa ma ban taho da su ba''
wani abu ya tokare maryam,wato irin rainon da aka mata shi zata yiwa nata 'ya'yan,a maimakon ta bata amsa da sun tafi islamiyya don a yanzu lokacinta ne sai tage gaya mata ta barsu gun talla?,du du du yaran nawa suke?,kamar tayi mata magana kuma sai taja bakinta ta tsuke don kada cibi ya zama qari
''sai ina kuma?''azaran ta tambayeta bayan ta gama qare mata kallo
''wallahi zani gidan raliya ne''
''hmmm,babban goro sai magogin qarfe,su ai sun isa ayi da su din,bari na qarasa ciki ko,sai kin dawo''
danne zuciuarta tayi ta murmusa
''to shikenan,idan na dawo na tadda ke to''
''o'o,anya zaki tadda ni kuwa,wannan fitar taku ta manya wa yasan ranan dawowarku''
''to ki gaida gida''
''gida zaiji''
''sai ina kuma?''azaran ta tambayeta bayan ta gama qare mata kallo
''wallahi zani gidan raliya ne''
''hmmm,babban goro sai magogin qarfe,su ai sun isa ayi da su din,bari na qarasa ciki ko,sai kin dawo''
danne zuciuarta tayi ta murmusa
''to shikenan,idan na dawo na tadda ke to''
''o'o,anya zaki tadda ni kuwa,wannan fitar taku ta manya wa yasan ranan dawowarku''
''to ki gaida gida''
''gida zaiji''
tana tafe a layin zuciyarta cunkushe da tunane tunane,hasbunallahu wa ni'imal wakeel ta dinga karantawa har ta iso titi,akwai qarqncin motocin haya kan titin nasu ko kuma ace kusan duk wadda tazo cike take da 'yan makarantar boko da suke dawowa gida,kusan motoci uku ne suka tsaya don bata lift saidai ko kallo basu isheta ba,hakan,na yawan faruwa da ita kasancewar unguwar nasu na maqotaka da unguwar nasarawa G R A,duk sanda hakan ta faru takan yawaita neman tsarin Allah,sannan takaici mamaki gami da tsoron maza kan sake yawaita cikin zuciyarta,basu da burin da ya wuce suga sun samu damar da zasu shiga rigar mutuncinki su wuce su barki babu batun aure
da qyar ta samu wata da yara yan makaranta biyu a ciki,ta masa kwatance inda zai ajjiyeta
cikin murna raliya ta tarbeta,cikin falonta suka zube bayan ta cikata da kayan ciye ciye suka hau hirarsu da bata qarewa fadil na bisa cinyarta,
''kinga kawo fadil din na riqe miki shi tunda yayi bacci ki samu kici wani abun,idan ba haka ba bazai barki kici komai ba''
''a'ah qyalemin shi''
cikin haka wayar raliyan ta soma tsuwwa,ta cirota ta duba screen din tana fadin ''abban fadil ne''
magan sukayi ta tsawon minti biyar sannan ta kashe tana duban maryam bayan ta miqe
''yace yana miki sannu da zuwa,bari,na saka miki wani film ya dan debe miki kewa ni shiga kitchen ya kamani,abban fadil ne zaiyi baqi''
''haba kema raliya naji zancan shiga kitchen kuma na zauna,ai kinsan sai anyi da ni''
''sannu uwar madafa''ta fada cikin zolaya
''na karba,ko kin manta kan abinda na samu degree kenan''
''wannan gaskiya ne,bani fadil din to na kwantar da shi sai mu wuce kitchen din ko?''
''kinga kawo fadil din na riqe miki shi tunda yayi bacci ki samu kici wani abun,idan ba haka ba bazai barki kici komai ba''
''a'ah qyalemin shi''
cikin haka wayar raliyan ta soma tsuwwa,ta cirota ta duba screen din tana fadin ''abban fadil ne''
magan sukayi ta tsawon minti biyar sannan ta kashe tana duban maryam bayan ta miqe
''yace yana miki sannu da zuwa,bari,na saka miki wani film ya dan debe miki kewa ni shiga kitchen ya kamani,abban fadil ne zaiyi baqi''
''haba kema raliya naji zancan shiga kitchen kuma na zauna,ai kinsan sai anyi da ni''
''sannu uwar madafa''ta fada cikin zolaya
''na karba,ko kin manta kan abinda na samu degree kenan''
''wannan gaskiya ne,bani fadil din to na kwantar da shi sai mu wuce kitchen din ko?''
qarfe hudu da mintina ashirin suka kammala,lafiyayyen girki ne wanda maryam ta gwada basirarta akai,ita kanta raliya komawa tayi gefe tana kallonta don bata zaci qawar tata takai haka ba,biyar saura ta suna falo,ta soma hada kayanta don tafiya gida ''amma diyana(haka suke kiranta wani lokaci a makaranta)ki sake wanka mana wannan aiki da kika sha''
''ai dole ne,amma fa idan na isa gida''
''ai ko wlh anan zakiyi''
murmushi tayi wanda har dashashinta sai da ya bayyana
''kinsan dai bana wanka na maida kayan da na cire,ni kuma ban taho da spare ba''
''tsarabarki ta south africa tana nan,saiki zabi daya a ciki kisa''
duk wayon,maryam sai da raliya ta sata yin wankan ta kawo mata ledar tsarabar ta zabi doguwar riga guda daya da tasha adon jajayen dutsina masu yawa da sheqi
''ai dole ne,amma fa idan na isa gida''
''ai ko wlh anan zakiyi''
murmushi tayi wanda har dashashinta sai da ya bayyana
''kinsan dai bana wanka na maida kayan da na cire,ni kuma ban taho da spare ba''
''tsarabarki ta south africa tana nan,saiki zabi daya a ciki kisa''
duk wayon,maryam sai da raliya ta sata yin wankan ta kawo mata ledar tsarabar ta zabi doguwar riga guda daya da tasha adon jajayen dutsina masu yawa da sheqi
a falo ta taddata''kinga kuwa maryam yadda rigar nan ta miki,Allah ya kawo miji na gari,gaskiya ba qaramar hidima zamu sha ba''
''har yanzu babu abinda ya ragu a surutun raliya''
''haka miskilanci kyau da ajin maryam diyana har yau yana nan''duka sai suka sa dariya,yana daya daga abinda ya sa qawancensu ke ma maryam dadi,raliya akwai vbarkwanc,inda kuma halinsu yazo daya ta bangaren haquri da dauke kai
''har yanzu babu abinda ya ragu a surutun raliya''
''haka miskilanci kyau da ajin maryam diyana har yau yana nan''duka sai suka sa dariya,yana daya daga abinda ya sa qawancensu ke ma maryam dadi,raliya akwai vbarkwanc,inda kuma halinsu yazo daya ta bangaren haquri da dauke kai
qarar bude get din gidan ne yasa suka ankara da isowar abban fadil
''kinga har sun iso ina nan a zaune,biyar harda kwata''maryama ta fada tana miqewa
''kinga malama koma ki zauna tunda sun riga sun iskemu tare ai bakya tafi ba,ki bari mu tari baqinmu qarasa ladarmu tare''babu yadda ta iya haka ta koma ta zauna,ta fiddo wayarta tqna yiwa hndatu texs ta sanar da mama tana nan tahowa raliya ce ta tsaidata
''kinga har sun iso ina nan a zaune,biyar harda kwata''maryama ta fada tana miqewa
''kinga malama koma ki zauna tunda sun riga sun iskemu tare ai bakya tafi ba,ki bari mu tari baqinmu qarasa ladarmu tare''babu yadda ta iya haka ta koma ta zauna,ta fiddo wayarta tqna yiwa hndatu texs ta sanar da mama tana nan tahowa raliya ce ta tsaidata
tana cikin sending sallamar baqin ta ratsa dodon kunnenta,a sanyaye ta dago tana amsawa,su uku ne abban fadil na hudu,duka sai taji ta a takure gashi raliya ta shiga ciki sako mayafi,sai ta miqe tana daukar jakarta tace
''sannunku da zuwa,abban fadil yanzu raliyan ta shiga ciki bari na mata magana''
dakatar da ita yayi
''a'ah yi zamanki,nasan a gajiye kike kunsha aiki bari na fito da ita,jabir bari na fito da madam''
''sannunku da zuwa,abban fadil yanzu raliyan ta shiga ciki bari na mata magana''
dakatar da ita yayi
''a'ah yi zamanki,nasan a gajiye kike kunsha aiki bari na fito da ita,jabir bari na fito da madam''
falon yayi shiru su duka harda baqin,wayarta na hannunta tana danne danne amma sai take jinta a takure,gashi daga raliyan har nasir din shiru kamar an shuka dusa
''madam haka ake kula da baqi?''
tajiyo maganar lokaci guda,ta daga kanta don ganin me maganar,shije zaune opposite dinta,sanye yake da shadda hartin da hula,murmushi ta danyi a taqaice
''ai bani bace matar gidan,ku jirayi fitowarta''
''ke da ita din ai daya ne,don na tabbata yarda ce tasa suka barki da baqinsu''
sai ta maida idonta kan wayarta don bata da abun ce masa,Allah ya taimaketa masu gidan suka qaraso
''madam haka ake kula da baqi?''
tajiyo maganar lokaci guda,ta daga kanta don ganin me maganar,shije zaune opposite dinta,sanye yake da shadda hartin da hula,murmushi ta danyi a taqaice
''ai bani bace matar gidan,ku jirayi fitowarta''
''ke da ita din ai daya ne,don na tabbata yarda ce tasa suka barki da baqinsu''
sai ta maida idonta kan wayarta don bata da abun ce masa,Allah ya taimaketa masu gidan suka qaraso
gaishe gaishe ne suka biyo baya da 'yan hirarrki,saidai duk lokacin da bisa kuskure idonta ya kai sashen da wanda ake ka kira da jabir sai ta tsinci idanunsa na bisa kanta,wanda hakan har ya fara damunta,nasir ya musu jagora zuwa dining domin cin abinci hakan yasa ta cema raliya
''to ai na gama ko,bari na wuce gida''
''tunda ba da mota kika zo ba ki bari mu kammala sai mu wuce tare ko?''
ta jiyo muryar jabir din na fadi
''kasan kuwa kusa da unguwar take ba''inji nasir
''haka,ne fa,shikenan kin huta hawa keke napep''inji raliya
''amma kinsan baxaiyiwu su kaini gida ba,idan mama ta ganni kuma nace mata su waye?''
''indai mama kike ji zan kira tq na gaya mata''inji raliyar
''to ai na gama ko,bari na wuce gida''
''tunda ba da mota kika zo ba ki bari mu kammala sai mu wuce tare ko?''
ta jiyo muryar jabir din na fadi
''kasan kuwa kusa da unguwar take ba''inji nasir
''haka,ne fa,shikenan kin huta hawa keke napep''inji raliya
''amma kinsan baxaiyiwu su kaini gida ba,idan mama ta ganni kuma nace mata su waye?''
''indai mama kike ji zan kira tq na gaya mata''inji raliyar
cikin zuciyarta ta ja tsaki,
''wannan jabir dan shiga hanci ne wlh''babu damar musu tunda duka ido na kanta haka ta koma ta zauna tana jira su kammala,yana bisa dining din amma idanunsa na kanta har raliya ta ankara,cike da gulma ta tabota
''ke,inafa tsammanin kinyi tsuntuwa yau a gidannan''
cikin rashin fahimta tace
''ta me fa?''
hararta tayi ''kiji min 'yar rainin sense,kina nufin baki lura da irin kallon da jabir ke miki ba?''
''shine me?''
''wlh sonki yake bisa dukka alamu''
wannan karon ita ta maida nata hararar''kijimin mata,kawai daga kallon sarkin fawa sai miya tayi zaqi?''
''wlh da gaske nake,jabir mutumin kirki ne diyana,kada kice zaki qishi don Allah''
''a'ah,kinji ta da wani guntun wa'azinta,ashe har yace miki ma yana sona ko?''
''ni na gaya miki zai fada miki''
''wannan jabir dan shiga hanci ne wlh''babu damar musu tunda duka ido na kanta haka ta koma ta zauna tana jira su kammala,yana bisa dining din amma idanunsa na kanta har raliya ta ankara,cike da gulma ta tabota
''ke,inafa tsammanin kinyi tsuntuwa yau a gidannan''
cikin rashin fahimta tace
''ta me fa?''
hararta tayi ''kiji min 'yar rainin sense,kina nufin baki lura da irin kallon da jabir ke miki ba?''
''shine me?''
''wlh sonki yake bisa dukka alamu''
wannan karon ita ta maida nata hararar''kijimin mata,kawai daga kallon sarkin fawa sai miya tayi zaqi?''
''wlh da gaske nake,jabir mutumin kirki ne diyana,kada kice zaki qishi don Allah''
''a'ah,kinji ta da wani guntun wa'azinta,ashe har yace miki ma yana sona ko?''
''ni na gaya miki zai fada miki''
Can saman dining dinma jabirne ke cewa cikin qasa qasa da murya
''kai mutumina nifa nazo gidanka a sa'a,Allah yasa bata da wani''
dariya ya saka''tuni na harbo jirginka ai,indai bilkisu ce a iya sanina ba'a tsaida mata miji ba''
''ai kuwa bazan tsaya kallon ruwa ba,a yau zan kafa kaina''
''kai mutumina nifa nazo gidanka a sa'a,Allah yasa bata da wani''
dariya ya saka''tuni na harbo jirginka ai,indai bilkisu ce a iya sanina ba'a tsaida mata miji ba''
''ai kuwa bazan tsaya kallon ruwa ba,a yau zan kafa kaina''
A bakin layinsu tasa ya tsaida motar,ta bude murfin tana cewa
''na gode''
''haba madam da sauri haka?''
sai ta juyo cikin mamaki tana dubansa
''eh mana,ya zaki min illa kuma ki tafi ki barni ba tare da kin bani magani ba''
ci gaba tayi da dubansa,sai ya saisaita nutsuwarsa,baiji ko,nauyi ba ya bayyana mata duka manufarshi,da farko ta ja masa yace shikam yace baisan wannan zancan ba,babu inda,zata tafi ta barshi cikin qila wa qala,idan,ko ta tafi to zai tare ne a qofar gidansu har sai ta amsa masa koda zai shekara
''na gode''
''haba madam da sauri haka?''
sai ta juyo cikin mamaki tana dubansa
''eh mana,ya zaki min illa kuma ki tafi ki barni ba tare da kin bani magani ba''
ci gaba tayi da dubansa,sai ya saisaita nutsuwarsa,baiji ko,nauyi ba ya bayyana mata duka manufarshi,da farko ta ja masa yace shikam yace baisan wannan zancan ba,babu inda,zata tafi ta barshi cikin qila wa qala,idan,ko ta tafi to zai tare ne a qofar gidansu har sai ta amsa masa koda zai shekara
maganar da sukayi da raliya ce ta fado ranta
''maryam,wlh indai aure kike so kiyi kada kiqi karbar tayin jabir matuqar yayi miki maganar,jabir bazai taba tararki da maganar banza ba,nasan jabir tuntuni,abokin nasir ne da dewa,halayensu kusan daya,hakan shi ya qara danqon abotarsu''
ita kanta a zahirance bata ga wani aibu ba tattare da jabir din,yana da kyau daidai wanda duk hassada ba zaka kira shi mummuna ba,a iya abinda ta gani da bayanan da raliya ta mata ta fuskanci zata iya amsa tayin jabir,ko don ma ran mahaifiyarta yayi fari,ko don ta samu itama ta zauna a nata dakin kamar sauran qawayenta da 'yan uwanta
.
''maryam,wlh indai aure kike so kiyi kada kiqi karbar tayin jabir matuqar yayi miki maganar,jabir bazai taba tararki da maganar banza ba,nasan jabir tuntuni,abokin nasir ne da dewa,halayensu kusan daya,hakan shi ya qara danqon abotarsu''
ita kanta a zahirance bata ga wani aibu ba tattare da jabir din,yana da kyau daidai wanda duk hassada ba zaka kira shi mummuna ba,a iya abinda ta gani da bayanan da raliya ta mata ta fuskanci zata iya amsa tayin jabir,ko don ma ran mahaifiyarta yayi fari,ko don ta samu itama ta zauna a nata dakin kamar sauran qawayenta da 'yan uwanta
.
ganin shirun nata yayi yawa yasa ya sake marairaice mata ga tsammaninsa zata wofantar da buqatarsa ne
''shikenan,Allah ya shige mana gaba''
''um um maryama,wannan ba amsa bace,kice ina sonka jabir shine magana''
kanta ta girgiza cikin alkunya tace''don Allah ka barni na wuce gida,na tabbata zan sha fada gun mama,don na kai magariba a waje,tunda ka kwaahe min numbers ai sun isa''
''shikenan,Allah ya shige mana gaba''
''um um maryama,wannan ba amsa bace,kice ina sonka jabir shine magana''
kanta ta girgiza cikin alkunya tace''don Allah ka barni na wuce gida,na tabbata zan sha fada gun mama,don na kai magariba a waje,tunda ka kwaahe min numbers ai sun isa''
fitowa yayi ya zagayo ya bude mata murfin yana cewa''shikenan,kin bani izini na kiraki?''
kai ta gyada masa,kafin ta dauko jakarta yayi sauri ya rigata ya bude zif din ya jefa mata kudi,ta noqe alamun ba zata amsa ba shi kuma yace indai bata karba ba to tana nufin bata sonshi,tilas ta karbi kyautar tasa,sukai sallama amma sai taga ya ja ya tsaya,kallonshi tayi ya daga mata gira
''sai na hango,shigarki gida don tsaron lafiyarki da kuma gane gidan naku koda na tashi zuwa''
murmushi kawai tayi tajuya domin shigewa layin nasu
kai ta gyada masa,kafin ta dauko jakarta yayi sauri ya rigata ya bude zif din ya jefa mata kudi,ta noqe alamun ba zata amsa ba shi kuma yace indai bata karba ba to tana nufin bata sonshi,tilas ta karbi kyautar tasa,sukai sallama amma sai taga ya ja ya tsaya,kallonshi tayi ya daga mata gira
''sai na hango,shigarki gida don tsaron lafiyarki da kuma gane gidan naku koda na tashi zuwa''
murmushi kawai tayi tajuya domin shigewa layin nasu
katsam idonta kan isyaku,kai ya gyada sannan ya kwasa da gudu yayi gida,la'ilaha illa nata subhanaka inni kuntu minaz zalimin,tasan tamkar a idanun iyayenshi tayi,cikin fargaba taci gaba da takawa jabir na mata rakiya da idanu har ta shige gidan
.
sai da tayi dira dira a soron kafin ta gano ainihin hanyar wucewa,saboda cike yake da 'yan zance,can hauwa can binta can maijidda kai abun takaicin ma harda zainabu wadda du du du ba zata wuce shekaru goma sha hudu ba kacal a duniya
ta tsakiyarsu ta raba ta wuce,taji dadi sosai da babu wadda ta tanka mata a cikinsu
sai da tayi dira dira a soron kafin ta gano ainihin hanyar wucewa,saboda cike yake da 'yan zance,can hauwa can binta can maijidda kai abun takaicin ma harda zainabu wadda du du du ba zata wuce shekaru goma sha hudu ba kacal a duniya
ta tsakiyarsu ta raba ta wuce,taji dadi sosai da babu wadda ta tanka mata a cikinsu
cirko cirko ta samesu a tsaye cikin tsakar gidan,inna hadiza ce da baba huwaila sai babansu dake bakin famfo yana daura alwala da alama haramar sallar isha'i yake yi,sai kuma isyaku dake qame a gefe da alama tuni ya gama fesar da abunda ya qunso
''la ha ila ha illallahu,muhammadu dan abdullahi''suka dauko salatin tare yayin da huwaila ta dire ita daya ta kuma dora
''wlh yaya da gaske ne yaro baya qarya,tayani gani don Allah,suturar jikinta ma ai ba da ita ta fita ba,lallai dandi na dada samun gindin zama a gidannan''
''la ha ila ha illallahu,muhammadu dan abdullahi''suka dauko salatin tare yayin da huwaila ta dire ita daya ta kuma dora
''wlh yaya da gaske ne yaro baya qarya,tayani gani don Allah,suturar jikinta ma ai ba da ita ta fita ba,lallai dandi na dada samun gindin zama a gidannan''
.
inna hadiza dake ta faman gyada kai tana kallon maryamu wadda ke tube takalmanta a qofar dakinsu ba tare da ta dubedu ba tace''qwarai da aniya,ya gama yawon barikin da ita ya kwashi na kwasa ba dole ta canza sutura ba,yo zata shigo mana gida ne da najasa ne''
''ke meramu zo nan''
kiran baban nata da baqin qazafin da suka jefeta da shi ya daki zuciyarta lokaci guda,a sanyaye ta dawo gabansa ta durqusa kanta a qasa
''wanne dan iska ne ya dauko ki a mota har gidan ubanki?''
muryarta a sanyaye tace''ba dan iska bane baba,gidan raliya muka hadu yace yana sona''
''yana sonki?''
huwaila da hadiza suka fadi kusan a tare
inna hadiza dake ta faman gyada kai tana kallon maryamu wadda ke tube takalmanta a qofar dakinsu ba tare da ta dubedu ba tace''qwarai da aniya,ya gama yawon barikin da ita ya kwashi na kwasa ba dole ta canza sutura ba,yo zata shigo mana gida ne da najasa ne''
''ke meramu zo nan''
kiran baban nata da baqin qazafin da suka jefeta da shi ya daki zuciyarta lokaci guda,a sanyaye ta dawo gabansa ta durqusa kanta a qasa
''wanne dan iska ne ya dauko ki a mota har gidan ubanki?''
muryarta a sanyaye tace''ba dan iska bane baba,gidan raliya muka hadu yace yana sona''
''yana sonki?''
huwaila da hadiza suka fadi kusan a tare
bai biya ta kansu ba ya dora da nashi bayanin
''alhmdl dama ni na gaji,na gaji wallahi kullum rana a unguwarnan sai anyi da ni kan na ajjiye babbar mace a gida,saboda haka ki shaida masa matuqar da gaske yake to na bashi kwana goma ya fito ayi kowa ma ya huta''
''yo idan banda abunka malam amadu saurayin qwarai ne zai dinga yayibar yarinya yaro kwararo kwararo kuma yace zai aureta,ai qarya ne dan yaudara ne kawai''inna hadiza ta,cafe maganar
''oho,koma dai meye nidai na gama magana,tashi ki bani guri''
''alhmdl dama ni na gaji,na gaji wallahi kullum rana a unguwarnan sai anyi da ni kan na ajjiye babbar mace a gida,saboda haka ki shaida masa matuqar da gaske yake to na bashi kwana goma ya fito ayi kowa ma ya huta''
''yo idan banda abunka malam amadu saurayin qwarai ne zai dinga yayibar yarinya yaro kwararo kwararo kuma yace zai aureta,ai qarya ne dan yaudara ne kawai''inna hadiza ta,cafe maganar
''oho,koma dai meye nidai na gama magana,tashi ki bani guri''
jikinta a sabule ta miqe tayi hanyar dakinsu,har yanzu kunnuwanta badu daina jiyo mata qananun magan ganun da suke yi bq marasa dadi akanta ba,taimakon da Allah yayi mata daya yau baban nasu bai bi ta kansu ba yayi ficewarsa masallaci,wannan wace iriyar masifa ce?,tamkar ita ke da ikon rubutawa kanta qaddararta?,ita ta hana kanra aure ne?,shikenan a rayuwa babu dama Allah ya qaddara maka wani abu sai jahilan cikin mutane su dinga ganin tamkar kai ka jawowa kanka ko da amincewarka hakan ta faru?,
.
mamanta na cikin rumfar a zaune amma tamkar bata a cikin gidan,wannan dabi'arta ce,tana da dauke kai da yakana akan 'ya'yanta,da wuya ka taba mata yaro kaji bakinta,da wannan damar mutanen gidan ke amfani suke cin karansu babu babbaka a kansu,duk da wasu lamuran hindu na masu tambotsai idan taga cin kashin yayi yawa,don ma mama na kwabarta
mamanta na cikin rumfar a zaune amma tamkar bata a cikin gidan,wannan dabi'arta ce,tana da dauke kai da yakana akan 'ya'yanta,da wuya ka taba mata yaro kaji bakinta,da wannan damar mutanen gidan ke amfani suke cin karansu babu babbaka a kansu,duk da wasu lamuran hindu na masu tambotsai idan taga cin kashin yayi yawa,don ma mama na kwabarta
yanzun ma baqinciki ne ya hanata motsi da kuma umarnin maman,don tana zaune ne tana karatun waec da fitilar qwai a gabanta,sallamar ta kawai hindun ta amsa ta dora da cewa
''yanzu fisabilillahi yaya maryam haka zaki ci gaba da zama ana miki cin mutunci ba zaki kare kanki ba?''
''kinci gidanku nace hindatu,nace kinci gidanku,da baban nata zatayi sa'insa ko da matan ubanta?,ke maryamu,ina kika samo kayan jikinki?''
kai ita kam dai ta shiga uku,wato ko ina cikin tuhuma take
''mama tsarabar da raliya ta bani ce,na tayata aiki tace bazan taho ba sai nayi wanka,shine aciki na cire nasa wannan''
''madalla,amma daga yau kada ki sake ki sake kaiwa magariba a waje kina jina ko?''
''to mama''
''yanzu fisabilillahi yaya maryam haka zaki ci gaba da zama ana miki cin mutunci ba zaki kare kanki ba?''
''kinci gidanku nace hindatu,nace kinci gidanku,da baban nata zatayi sa'insa ko da matan ubanta?,ke maryamu,ina kika samo kayan jikinki?''
kai ita kam dai ta shiga uku,wato ko ina cikin tuhuma take
''mama tsarabar da raliya ta bani ce,na tayata aiki tace bazan taho ba sai nayi wanka,shine aciki na cire nasa wannan''
''madalla,amma daga yau kada ki sake ki sake kaiwa magariba a waje kina jina ko?''
''to mama''
.
dakinsu ta shige ta ajjiye jakarta saman katifarta,qoqari take ta shanye dukkan wani bacin rai,batason ta barshi yayi tasiri a ranta,tunda idan da sabo ai yaci ace ta saba,sau nawa ake ruwa qasa tana shanyewa,ta zare rolling din kanta ta dawo tsakar gida ta daura alwala,sai da tayi nafila raka'a biyu ta kaiwa Allah kukanta,ta dade saman carfet tana jan,hasbunallahu wa ni'imal wakeel sannu a hankali taki sauqi na zuwar ma zuciyarta
dakinsu ta shige ta ajjiye jakarta saman katifarta,qoqari take ta shanye dukkan wani bacin rai,batason ta barshi yayi tasiri a ranta,tunda idan da sabo ai yaci ace ta saba,sau nawa ake ruwa qasa tana shanyewa,ta zare rolling din kanta ta dawo tsakar gida ta daura alwala,sai da tayi nafila raka'a biyu ta kaiwa Allah kukanta,ta dade saman carfet tana jan,hasbunallahu wa ni'imal wakeel sannu a hankali taki sauqi na zuwar ma zuciyarta
kira ne ya shigo wayarta data duba agogo sai ta tabbatar jabir ne don bata da alaqa da wani da zai kirata a irin wannan lokacin,shi dinne kuwa,awanni kusan biyu sukayi akan wayar har ta soma gajiya don bata saba doguwar hira irin haka waya ba,cikin awanni tayi amanna da kyawawan halayen jabir,bayan ta,jada da wanda raliya ta gaya mata,a yanzun mafita kawai take nema,koda wanda bai kai jabir din ba zata iya aurenshi matuqar zaya riqeta da daraja
sunayin sallama hindatu ta shigo dakin da tarin litattafanta ta watsasu tata katifar,kasancewar dakinsu daya don maryamu bata da sha'awar raba daki da 'yar uwar tata,doguwar hamma ta ja,maryam ta dubeta tana dariya ''boko wahala''
''mtsw,ke dai bari yaya maryam,yanzu a haka kukayi degree?''
''me kayi da maza inji karya,idan banda abun hindu ke,da sai yanzu ma zaki bar secondry din''
''gaskiya ne kuma fa''ta fada tana fadawa kan katifar tabayan ta ture liattatafan da ta watsa gefe
''mtsw,ke dai bari yaya maryam,yanzu a haka kukayi degree?''
''me kayi da maza inji karya,idan banda abun hindu ke,da sai yanzu ma zaki bar secondry din''
''gaskiya ne kuma fa''ta fada tana fadawa kan katifar tabayan ta ture liattatafan da ta watsa gefe
.
''yauwaaa''maryayam ta gada tana janyo jakarta ta ciro kudin da jabir ya bata dazu
''ungo irga kiga nawa ne''
''an biya ku salary ne ya maryam?''tace lokacin tame lissafa kudin
''a'ah jabir ne ya bani''
''ya maryam Allah ya tsaida jabir din nan mu sha budiri''murmushi itadai kawai tayi
''ten thousand ne''
''ok...to ko riqesu,zan cika miki kudin rigistration din exam dinku''
''na gode ya maryam,na gode''
''don mind,ni dake duka daya ne,kawai ki tayani addu'a hindu''
''ai babu fashi wannan ya maryam
.
''yauwaaa''maryayam ta gada tana janyo jakarta ta ciro kudin da jabir ya bata dazu
''ungo irga kiga nawa ne''
''an biya ku salary ne ya maryam?''tace lokacin tame lissafa kudin
''a'ah jabir ne ya bani''
''ya maryam Allah ya tsaida jabir din nan mu sha budiri''murmushi itadai kawai tayi
''ten thousand ne''
''ok...to ko riqesu,zan cika miki kudin rigistration din exam dinku''
''na gode ya maryam,na gode''
''don mind,ni dake duka daya ne,kawai ki tayani addu'a hindu''
''ai babu fashi wannan ya maryam
.
cikin sati,guda kacal sabo ya shiga tsakaninsu da jabir,yana da sauqin kai,fara'a da haba haba da jama'a,yan sonta ji da ita da tattalinta,cikar satin ta isar masa da saqon baban,murna da farinciki tamkar zai goya ta,washegari kuwa magabatansa suka iso,a take aka tsaida magana harda sa rana,farincikin mama bazai misaltu ba duk da tana boye wa,yayin da huwaila da hadiza sukejin kamar an musu transfer zuwa jahannama
.
shiye shirye tuni suka fara kankama domin sati biyu kacal ya rage,cikin yammacin gab da sallar magariba jabir yazo gurinta kawo mata invitations kasancewar akan hanya yake yasa bai shiga daga cikin gidan ba,suna tsaye jikin motarsa taga kamar an wulgasu,ta dago kanta don ganin me wucewar,maraqisiyya ce har ta gota su taga ta dawo,da baya,qare musu kallo tayi sannan ta gyada kai ta shige cikin gidan fuuu da uban akwatinta dake rinjayarta
wani faduwa taji gabanta yayi wanda yasanya har sai da ta rufe idonta,duk lokacin da maraqisiyya tazo gida to babu alkhairi a zuwanta,don bata taba komawa inda ta fito sai ta assasa wani bala'in cikin gidan
''lafiya?''jabir ya tambayeta cikin kulawa
murmushi tayi wanda yafi kama da na yaqe ta girgiza kai''babu komai''
''lafiya?''jabir ya tambayeta cikin kulawa
murmushi tayi wanda yafi kama da na yaqe ta girgiza kai''babu komai''
.
Babu sallama sam bisa tsarin maraqisiyya,don kaf gidan tafi kowa lalacewa,jamila ke rufa mata baya,a tsakar gida ta iske uwarta hadiza da 'yar kanzaginta huwaila,basu ga shigowarta ba sai yif kawai sukaji na warbar da akwatinta da tayi da zamanta jabar kusa da su
Babu sallama sam bisa tsarin maraqisiyya,don kaf gidan tafi kowa lalacewa,jamila ke rufa mata baya,a tsakar gida ta iske uwarta hadiza da 'yar kanzaginta huwaila,basu ga shigowarta ba sai yif kawai sukaji na warbar da akwatinta da tayi da zamanta jabar kusa da su
inna hadiza ce ta dafe qirjinta''na shiga uku ni dije,kada dai kice min yauma korokin yayi?''
fuska ta yatsine
''yau ba shi ya kore ni ba ni na taho,don na gaji da zama da matsiyaci direban babbar mota kuma mashayi''
''oh ni 'yar nan,auwalu matsiya cine''
''lamba daya''maraqisiyyan ta qarashe mata
huwaila tace
''aini na ma kasa magana,yara duka aure ya zama na tafashi kada,babu daya qwaqqwara?''
matsowa maraqisiyya tayi sosai kusa da su ta ma manta da tata matsalar''wai hadiza ni fa ban gane ba(haka suke kiran iyayen kansu tsaye)idanuna kamar wancan mujiyar nake gani da wani jikin wata qatuwar mota,ko gixo take min''
fuska ta yatsine
''yau ba shi ya kore ni ba ni na taho,don na gaji da zama da matsiyaci direban babbar mota kuma mashayi''
''oh ni 'yar nan,auwalu matsiya cine''
''lamba daya''maraqisiyyan ta qarashe mata
huwaila tace
''aini na ma kasa magana,yara duka aure ya zama na tafashi kada,babu daya qwaqqwara?''
matsowa maraqisiyya tayi sosai kusa da su ta ma manta da tata matsalar''wai hadiza ni fa ban gane ba(haka suke kiran iyayen kansu tsaye)idanuna kamar wancan mujiyar nake gani da wani jikin wata qatuwar mota,ko gixo take min''
caraf huwaila ta kama''itace mana 'yar nan,kinga babarku babu yadda banyi da ita ba mu tashi tsaye ko malaman da mata ke shiga muma wannan karon mu fada amma tace bata da kudi,dame zata ji,da matsalolinku ko da kisan kudinta da take nema da qyar?kawai mu qyaleta tunda wancan karon hakanan taqi auruwa to wannan karon ma hakance zata faru''
''hadiza ai ranar biyan buqata rai ba a bakin komai yake ba,ku yanzu ko kunya bakwaji,ai abun kunya ne a tattarw da ku maryama ta auri irin mijin dai da na ganta tare da shi,wlh dukkanin alamu sun nuna mai akwai ne,yaranku suna zaune?,wadanda ma aka aurar din gamu cikin wahala?,kuma ita tahaye?,si wallahi inaaaa,zaman gida bai qarewa maryam ba,ku matso kuji''
''hadiza ai ranar biyan buqata rai ba a bakin komai yake ba,ku yanzu ko kunya bakwaji,ai abun kunya ne a tattarw da ku maryama ta auri irin mijin dai da na ganta tare da shi,wlh dukkanin alamu sun nuna mai akwai ne,yaranku suna zaune?,wadanda ma aka aurar din gamu cikin wahala?,kuma ita tahaye?,si wallahi inaaaa,zaman gida bai qarewa maryam ba,ku matso kuji''
.
shewa sukayi bayan sun tafa kamar wasu,sa'anni wanda yayi daidai da shigowar maryam din
''sannunku,maraqisiyya ya hanya?''babu amsa sai uban tsaki da taja kamar zata cire harshenta
shewa sukayi bayan sun tafa kamar wasu,sa'anni wanda yayi daidai da shigowar maryam din
''sannunku,maraqisiyya ya hanya?''babu amsa sai uban tsaki da taja kamar zata cire harshenta
washegari ta shirya tsaf don zuwa karbo dinkunanta da kuma yin sallama da uwar dakinta wadda take aiki a qarqashin katafaren kamfaninta nayin girke girke da shirya guraren biki,tayi sallama da maman ta,fito tsakar gidan
saiji tayi maraqisiyya na dura ashar,cikin takaici ta,juya don ganin da wa take,ita da hindatu ne ta,sirka ruwanta ta wanke kanta rabi zatayi wanka maraqisiyyar ta,sheqar mata ta,tara wsni don shiga nata wankan
''wannan banzar yayar taki ma bata isheni ba bare ke karan kada miya''
hindatu dama dake qullace da su tace
''dalla gafara can malama,banza a banza kawai,wadda ta kasa zsmsn gidan aurenta,yayar tawa kuma da,kike maganarta kuwa wallahi tako ina ta sha gabanki,aure kuwa nasan bazati irin naku ba auren jeka nayi ka,wanda dashi gwara babu''tofa baki yasan abinda zai fada baisan me za'a mayar masa ba
''wannan banzar yayar taki ma bata isheni ba bare ke karan kada miya''
hindatu dama dake qullace da su tace
''dalla gafara can malama,banza a banza kawai,wadda ta kasa zsmsn gidan aurenta,yayar tawa kuma da,kike maganarta kuwa wallahi tako ina ta sha gabanki,aure kuwa nasan bazati irin naku ba auren jeka nayi ka,wanda dashi gwara babu''tofa baki yasan abinda zai fada baisan me za'a mayar masa ba
kamar ta zubawa maraqisiyya ruwan zafi ta,lsilayo wani uban ashar din''wlh zaki san kinyi da huwaila 'yar hadiza,auren da kike taqama ayishi mu gani''
''Allah ya fiki ya fi wanda ya fiki ma''hindatu ta fada wadda maryam ta tura daki tana mata gargadin kada ta sake cewa komai,sai kuma abu ya dawo kanta bata kula kowa ba ta fice inda ta nufa cikin zuciyarta cike fal da tsanar halayensu
''Allah ya fiki ya fi wanda ya fiki ma''hindatu ta fada wadda maryam ta tura daki tana mata gargadin kada ta sake cewa komai,sai kuma abu ya dawo kanta bata kula kowa ba ta fice inda ta nufa cikin zuciyarta cike fal da tsanar halayensu
Saura kwana goma biki aka kawo lefe,lefe ne na gani na fada wanda ita kanta maryamu ta yaba qwarai da gaske,qarara rudewar su huwailan ta fito,sumbatu suka dinga yi don duka cikinsu babu wadda ta aurar da 'yar da ta samu lefe kwatankwacin haka,komai sai da suka masa dilla filla suka qare masa kallo
abinda ya bata mamaki ganin dukkan 'yan gida sun shiga shirye shiryen bikin gadan gadan,kada ma inna hadiza taji labari,duk da ba shiga sabgar su maryamun take ba,harda cin bashi da sauya furnitures din daki
maryam na zaune gefan mamanta tana lissafa mata sunayen mutanen da zata tura hindatu takaiwa cingam tana rubuta mata a takarda hindatun ta shigo,hannunta ledar dinkunanta ne da ta door mat da maryam ta bada ta siyo,ta zauna kan kujera tana fadin
''sannu harkin dawo?''
''eh wlh amma fa na sha wuya''ta fada tana shiga kitchen ta dauko ruwa cikin gorar faro da suke durawa susa a fridhe dinsu,sai da tq shanye sannan tace
''mama''
''na'am''
''nifa abun nan na bani mamaki''
''mefa?''ta tambayeta tan duba rubutun,da maryam keyi
''su hauwa mana da su jamila,gaba daya sai hidimar biki ake yi,kada ma jamila taji labari ita da mamanta,mutanen da aduniya babu wadanda suka tsana kamar mu?''
sai a lokacin maman ta kalleta duka harda maryam din
''to,banda abinki hindatu sai ku godewa Allah,me yiwuwa Allah ne ya ganar da su gaskiya,tunda babu wanda za'ace *ABADAN* zai dawwama a halin da yake,dole watarana akwai sauyi,qila Allah ya ganar da su ne''
''nima dai mama haka nayi tunani,kuma wallahi bakiji dadin da naji ba,Allah yasa silar gyaruwar tsakanin mu kenan''
''ameen''cewar mama,ita dai hindatu tabe baki tayi tace ''to Allah yasa,amma ba girin girin ba tayi mai''
''sannu harkin dawo?''
''eh wlh amma fa na sha wuya''ta fada tana shiga kitchen ta dauko ruwa cikin gorar faro da suke durawa susa a fridhe dinsu,sai da tq shanye sannan tace
''mama''
''na'am''
''nifa abun nan na bani mamaki''
''mefa?''ta tambayeta tan duba rubutun,da maryam keyi
''su hauwa mana da su jamila,gaba daya sai hidimar biki ake yi,kada ma jamila taji labari ita da mamanta,mutanen da aduniya babu wadanda suka tsana kamar mu?''
sai a lokacin maman ta kalleta duka harda maryam din
''to,banda abinki hindatu sai ku godewa Allah,me yiwuwa Allah ne ya ganar da su gaskiya,tunda babu wanda za'ace *ABADAN* zai dawwama a halin da yake,dole watarana akwai sauyi,qila Allah ya ganar da su ne''
''nima dai mama haka nayi tunani,kuma wallahi bakiji dadin da naji ba,Allah yasa silar gyaruwar tsakanin mu kenan''
''ameen''cewar mama,ita dai hindatu tabe baki tayi tace ''to Allah yasa,amma ba girin girin ba tayi mai''
sallamar jamila ce ta katse hirar tasu,dukkaninsu suka bita da kallo,don basu iya tuna yaushe ta shigo dakin na qarshe,koda sun tuna ma ba alkhairi ne ya kawo ta ba
''sannu mama''
''yauwa sannu''
''gurin maryamu nazo''
''to gani''injita
''cewa nayi yaishe zqki lalle,ina son na biki ne muje tare,kinsan qannan amarya dole su fito kamar amaryar''
''sannu mama''
''yauwa sannu''
''gurin maryamu nazo''
''to gani''injita
''cewa nayi yaishe zqki lalle,ina son na biki ne muje tare,kinsan qannan amarya dole su fito kamar amaryar''
sosqi maryamun taji dadi har ta saki tattausan murmushin ta
''ai ba damuwa,jibi ne sai mu tafi tare ai''
''to shikenan''ta juya ta fice
hindatu ta kalleta
''haba ya maryam,nidai gaskiya bazan hada tafiya tare da su ba''
''sai ki fasa zuwan ai''inji mama
''don kuwa ni zan biya mata ma kudin lallen,haba hindatu dan uwanka dan uwanka ne fa,kuma ka dinga kyautatawa dan uwanka musulmi zato,ki zama mai tsarkakkiyar zuciya kinji qanwata''dole hindatun taja bakinta ta tsuke
''ai ba damuwa,jibi ne sai mu tafi tare ai''
''to shikenan''ta juya ta fice
hindatu ta kalleta
''haba ya maryam,nidai gaskiya bazan hada tafiya tare da su ba''
''sai ki fasa zuwan ai''inji mama
''don kuwa ni zan biya mata ma kudin lallen,haba hindatu dan uwanka dan uwanka ne fa,kuma ka dinga kyautatawa dan uwanka musulmi zato,ki zama mai tsarkakkiyar zuciya kinji qanwata''dole hindatun taja bakinta ta tsuke
Tare suka je lallen maryam hindatu da jamila,ita biya kudin dukkaninsu
cike gidan yake da mutane kasancewar yaune ranar daurin aure,ga gauyar yan uwa daga bangaren mama da inna hadiza,kusan yawancin danginta na cike a gidan danqam,har ita kanta maman tayi mamakin hakan,amma sai ta share,batun sanin cewa babu yadda Allah baya iya sauya lamarinsa
maryam na maqotansu ita da qawayenta ciki harda raliya,tayi shar cikin atamfa super riga da zani plain,ba qaramin kyau tayi ba,fuskarta cike da walwala da farinciki
guda suka dinga ji tana tashi sosai tamkar a cikin gidan akeyi kasancewar maqota ne gida jikin gidan,raliya ta saki tata gudar tana fadin
''shikenan alhmdlh an daura,tazama tazama,yau diyana ta shigo sahu,Allah yasa wata tara iwar haka mu hadu suna''dariya duka aka saki wasu na cewa amin wadda shigowar hindatu cikin gunkin kuka ya katse musu ita
maryam ce ta soma miqewa tanajin qirjinta na bugawa tun kafin taji me ya samu hindatun zuciyarta ke mata saqe saqen munanan abubuwa
''shikenan alhmdlh an daura,tazama tazama,yau diyana ta shigo sahu,Allah yasa wata tara iwar haka mu hadu suna''dariya duka aka saki wasu na cewa amin wadda shigowar hindatu cikin gunkin kuka ya katse musu ita
maryam ce ta soma miqewa tanajin qirjinta na bugawa tun kafin taji me ya samu hindatun zuciyarta ke mata saqe saqen munanan abubuwa
.
zubewa tayi gaban maryam tana fadin
''ya maryam don Allah me kika yiwa ya jabir?,me kika yi masa da zai miki wannan sakayyar?,me kika yi masa da har ya guje miki ya maida aurenshi kan *JAMILA*?''
dum taji kunnuwanta sunyi,qwaqwalwarta lokaci guda ta gaza yin aikinta,sai ta daina gane komai,meke shirin faruwa d ita?tambayar da taji qwaqwalwarta na mata kenan,kafin bijirowar amsar sai taji tamkar an zare dukkan wata garkuwa da ta sata ta iya tsaiwa da qafafunta,yaraf taji ta zube,daganan komai ya dauke mata dif kamar an dauke wutar nepa adaki mai tsananin duhu........
zubewa tayi gaban maryam tana fadin
''ya maryam don Allah me kika yiwa ya jabir?,me kika yi masa da zai miki wannan sakayyar?,me kika yi masa da har ya guje miki ya maida aurenshi kan *JAMILA*?''
dum taji kunnuwanta sunyi,qwaqwalwarta lokaci guda ta gaza yin aikinta,sai ta daina gane komai,meke shirin faruwa d ita?tambayar da taji qwaqwalwarta na mata kenan,kafin bijirowar amsar sai taji tamkar an zare dukkan wata garkuwa da ta sata ta iya tsaiwa da qafafunta,yaraf taji ta zube,daganan komai ya dauke mata dif kamar an dauke wutar nepa adaki mai tsananin duhu........
.
''ya maryam,me kika masa da har ya guje miki ya maida aurensa kan jamila?''
maganar da keta amsa kuwwa cikin kunnenta kenan bayan ta farka,sai hawaye ya fara turereniyar fitowa daga runtsatsun idanunta da ta kasa budesu suna bi ta gefan fuskarta su sauka har cikin kunnenta,wani irin yanayi take ji daban cikin zuciya da gangar jikinta
me ta aikatawa jabir da zafi haka wanda har ta cancanci wannan hukuncin?
a iya saninta ba zata iya tuna abu guda ba mara dadi da ya taba hadasu a tarihin rayuwar soyayyarsu ba
''ya maryam,me kika masa da har ya guje miki ya maida aurensa kan jamila?''
maganar da keta amsa kuwwa cikin kunnenta kenan bayan ta farka,sai hawaye ya fara turereniyar fitowa daga runtsatsun idanunta da ta kasa budesu suna bi ta gefan fuskarta su sauka har cikin kunnenta,wani irin yanayi take ji daban cikin zuciya da gangar jikinta
me ta aikatawa jabir da zafi haka wanda har ta cancanci wannan hukuncin?
a iya saninta ba zata iya tuna abu guda ba mara dadi da ya taba hadasu a tarihin rayuwar soyayyarsu ba
hindatu ce ta fara ankara da farkawar tata ta sanadiyyar hawayen fuskar tata dake bi ta gefen kuncinta,da sauri ta taso
''sannu ya maryam,me yake miki ciwo yanzu''
kai kawai ta gyada mata alamar babu komai
mirya can qasa tace
''dagoni hindatu''
a hankali ta taonaka mata ta tashin ta jingina da filo sannan tace bari na kira ''mama''
''sannu ya maryam,me yake miki ciwo yanzu''
kai kawai ta gyada mata alamar babu komai
mirya can qasa tace
''dagoni hindatu''
a hankali ta taonaka mata ta tashin ta jingina da filo sannan tace bari na kira ''mama''
maman ce ta takurata kan ta tashi hindatu ta rakata asibiti,bata biqatar fita koda falon nasu ne don bata san da wanne iso zata kalli jama'a,hakanan suma batsan da wanne ido zasu dubeta ba,ta tabbatar maganar ta gama zaga unguwar ma gaba daya ba gidan ba,amma ba zata iya misa mata ba don ita don ma so take tadan gusa daga gidan saboda haka ta zura hijabinta hindatun tace bari ta nemo dan adaidaita sahu sai tayi mata magana
bayan fitar hindatun shiru dakin yayi,baka jiyo komai sai hargowa da hayaniyar jama'arsu huwaila da inna hadiza cike da farinciki,mintuna biyar sai ga hindatun ta dawo ita ta riqe maryamun suka fito yayin da 'yan uwan maman nata dake zaune jugum a rumfar tasu suke mata sannu da jaje,don tuni wasu ma soma hada kayansu don komawa inda suka fito
Sun samu ganin likita cikin qanqanin lokaci don private clinic suka je,likitan yace zai riqe ta zuwa magariba ta huta sosai tasha magungunanta,bata musa din ba suka bata gado hindatu na tare da ita
basu bar asibitin ba sai magariba,suna hanya ne hindatu tace''anty raliya ta kira ki har sau biyu kina bacci,tace zaga sake kira,ya nasir ne yayi kiranta tunda kuma ta fita bata dawo ba''
kai ta iya gyada mata kawai don bata jin zata iya bude bakinta
suna shigowa layin gabanta ya dinga dukan uku uku,ji take tamkar ta,canza wani gidan ba nasu ba,ji take kamar ta yanka a guje ta bace a nemeta a rasa,motocine a jere har zuwa qofar gidan nasu,sauka sukayi suka biya shi sannan suka dutfafi gidan wanda har qofar gida jama'a ne
kai ta iya gyada mata kawai don bata jin zata iya bude bakinta
suna shigowa layin gabanta ya dinga dukan uku uku,ji take tamkar ta,canza wani gidan ba nasu ba,ji take kamar ta yanka a guje ta bace a nemeta a rasa,motocine a jere har zuwa qofar gidan nasu,sauka sukayi suka biya shi sannan suka dutfafi gidan wanda har qofar gida jama'a ne
duhun da garin yayi yasa babu wanda ya shaidasu har suka shige gidan wanda tun daga soron suke jiyo tashin muryoyi cike da hargowa,babu wadda tace da 'yar uwarta komai har suka shigo ainihin tsakar gidan,ga mamakinsu qofar dakinsu ne cike yake da jama'a wanda ya tabbatar musu da koma mene ya shafesu
.
da qyar suka kutsa cikin rumfar tasu,mamansu ce zaune bisa kujera fuskarta dauke da tashin hankali,sai anty kubra qanwar mamansu,inna hadiza da baba huwaila sai jamila dake gefansu tana zuba ruwan bala'i har daurin zaninta na kwancewa anty kubra na maida mata da raddi
baba huwaila ke riqo,jamilan ta fincike kana ta zabga mata harara
''kinga malama ki qyaleni kawai,wallahi babu inda zani sai da lefena koda motocin daukar amaryar zasu shekare,a qa'ida ai lefe nawa ne kuma sai in zuba ido a take min haqqina,wallahi babu wanda ya isa ko duk duniya gatanshi ne yau sai kun fiddo lefen nan''
''qwarai kuwa haqqinki ne ai''babarta hadiza ta fadi cike da nuna goyan baya,wani abu ne ya tsirga wa huwaila,wato tsiyar ma har da ita a ciki yau
da qyar suka kutsa cikin rumfar tasu,mamansu ce zaune bisa kujera fuskarta dauke da tashin hankali,sai anty kubra qanwar mamansu,inna hadiza da baba huwaila sai jamila dake gefansu tana zuba ruwan bala'i har daurin zaninta na kwancewa anty kubra na maida mata da raddi
baba huwaila ke riqo,jamilan ta fincike kana ta zabga mata harara
''kinga malama ki qyaleni kawai,wallahi babu inda zani sai da lefena koda motocin daukar amaryar zasu shekare,a qa'ida ai lefe nawa ne kuma sai in zuba ido a take min haqqina,wallahi babu wanda ya isa ko duk duniya gatanshi ne yau sai kun fiddo lefen nan''
''qwarai kuwa haqqinki ne ai''babarta hadiza ta fadi cike da nuna goyan baya,wani abu ne ya tsirga wa huwaila,wato tsiyar ma har da ita a ciki yau
'yan mata biyun dake tsaye bakin qofa cikin 'yan daukar amarya suka hada ido,cikin tashin hankali dayar ta cewa 'yar uwarta,muryarta can qasa''mun shiga uku malika,wacce iriyar mace ya jabir ya kwaso mana''babu mai amsar duk cikinsu,saboda haka jiki a sanyaye suka zame,suka fice daga gidan
.
hindatu dake jiran qiris ta saki jakar hannunta tana huci ta qaraso gaban jamila
''rufe mana baki matsiyaciyar banza matsihaciyar wofi 'yan taka hayen arziqi,lefen banza lefan wofi,mj jabir ma yanzu bai ishemu kallo ba balle abinda ya fito daga hannunsa,idan kinsa ranki a inuwa ma zamu fito muku da gayuar tsiuarku ba sai kinzo kina haushi kina ragewa kanki daraja ba idon dangin miji ba''
sai ta,hau ihu
''e hooo,munji dai duka haushin rashi ne ,kaya dai sai kun bada su''
''ai dama zamu bada din amma ba saboda wannan hayagagar taki ba,zamu baku ne saboda mu a gun mu ba yanke talauci jabir ya bamu ba,kune nake tsammanin zai iya zama yanke talauci a gunku''
hannu inna hadiza ta saka zata zabga mata mari,tuni ta tare ta kana ta sake taku uku zuwa gabanta tana huci da nuna ta da yatsa
''kada ki kuskura wallahi,don idan a baya kin saba tabani ina qyaleki ta yanzu babu wannan maganar,idan kuma kika yi gigin aiwatar da hakan wallahi ko kadan bazaji kunyarkk ba daga hannu zanyo nima in nuna miki salon nawa iya marin,tsohuwar banza wadda shekarunt basu dade ta da k.....''
hindatu dake jiran qiris ta saki jakar hannunta tana huci ta qaraso gaban jamila
''rufe mana baki matsiyaciyar banza matsihaciyar wofi 'yan taka hayen arziqi,lefen banza lefan wofi,mj jabir ma yanzu bai ishemu kallo ba balle abinda ya fito daga hannunsa,idan kinsa ranki a inuwa ma zamu fito muku da gayuar tsiuarku ba sai kinzo kina haushi kina ragewa kanki daraja ba idon dangin miji ba''
sai ta,hau ihu
''e hooo,munji dai duka haushin rashi ne ,kaya dai sai kun bada su''
''ai dama zamu bada din amma ba saboda wannan hayagagar taki ba,zamu baku ne saboda mu a gun mu ba yanke talauci jabir ya bamu ba,kune nake tsammanin zai iya zama yanke talauci a gunku''
hannu inna hadiza ta saka zata zabga mata mari,tuni ta tare ta kana ta sake taku uku zuwa gabanta tana huci da nuna ta da yatsa
''kada ki kuskura wallahi,don idan a baya kin saba tabani ina qyaleki ta yanzu babu wannan maganar,idan kuma kika yi gigin aiwatar da hakan wallahi ko kadan bazaji kunyarkk ba daga hannu zanyo nima in nuna miki salon nawa iya marin,tsohuwar banza wadda shekarunt basu dade ta da k.....''
.
tsawa mamarta ta daka mata''kada ki kuskura kici gaba,zo ki wuce ki debo musu kayansu kawai idan na isa da ke''yarfar da hannun inna hadizan tayi a fusace ta shiga dakin maman inda anan kayan ke ajjiye ta soma fiddo da su tana watsosu falon
''kada fa ta barnata muku kaya kuyi mata gana''
''ina ruwanki,da muka zo da ke wanne taimako kika iya yi,tunda dai sun fiddosu ai shikenan''inji jamilar
takaici yasa huwaila jiyawa ta bar dakin
tsawa mamarta ta daka mata''kada ki kuskura kici gaba,zo ki wuce ki debo musu kayansu kawai idan na isa da ke''yarfar da hannun inna hadizan tayi a fusace ta shiga dakin maman inda anan kayan ke ajjiye ta soma fiddo da su tana watsosu falon
''kada fa ta barnata muku kaya kuyi mata gana''
''ina ruwanki,da muka zo da ke wanne taimako kika iya yi,tunda dai sun fiddosu ai shikenan''inji jamilar
takaici yasa huwaila jiyawa ta bar dakin
a warwatse haka hindatu ta dinga jefomusi su tas tun mama na mata magana har ta gaji da qyaleta,bayan kuma ta gama tace wallahi ian basuyi gaggawar kwashesu daga rumfar tasu ba zasu ga qasqanci,duk iya ikancinsu sun sqn halin hindatu sqrai bata iya fushi ba,don haka cikin rawar jiki suka dinga kwashewa ciki harda uwar amarya inna hadiza
.
sai da suka gama sannan taji kuka yazo mata cikin dakin nasu da ta shiga da niyyar rage qincin zuciyarta,sai ta tadda maryam nayin nata,kasa lallashinta tayi hala suka hada kai suka dinga risgar kukan da qyar anty kubra ta sha kansu
sai da suka gama sannan taji kuka yazo mata cikin dakin nasu da ta shiga da niyyar rage qincin zuciyarta,sai ta tadda maryam nayin nata,kasa lallashinta tayi hala suka hada kai suka dinga risgar kukan da qyar anty kubra ta sha kansu
haka suka kwashi amaryarsu suka kaita gidan da aka shirya shi da sunan maryam din,wanda hatta kayan gado fiye da rabi kudinta ne ta baiwa baban nata ya hada da na gurinsa aka siyesu,abu daya ne inna hadizan tasa aka jado aka dawo musu da shi kayan kitchen,duk da haka sun cire manya manyan warmers masu tsada da maryam din ta siya cikin albashinta
kwana biyu gidan yayi da ragowar baqin su inna hadiza da basu ida tafiya ba,kwanakin biyun nan daidai suke da shekara goma na tsanani gurin maryam,kallo daya zaka mata ka dauke kai,hatta da mamarta wannan karon ta kasa daurewa zuciyarta sai da ta taya diyar tata kokawa
ciwon kwana na hudu bayan sallar la'asar raliya ta iso gidan,maryam na kan dadduma bata kai ga tashi ba tunda tayi sallar la'asar,suna hada ido ta soma share qwalla,itama raliyan sai ta kasa daurewa duk da alqawarin da tayi ma nasir din bazata zo su hada kai suyita kuka ba
kusa da ita ta zauna suka soma aikin kuka wanda mama dake dakinta bata ji shigowarta ba sai rishin kukansu,leqowa tayi don ganin waye''ashshsha,haba raliya,abu da ya riga ya wuce kuma,don Allah ya isa haka,tashi ku shiga daki''ta fada tana karbar fadil daga gunta ta fice ta bar musu rumfar
da taimakon ambato Allah da take ta samu zuciyarta ta rage zugin da take
''raliya me n yiwa jabir haka da zafi?,wace iriuar qiyayya ce wannan ya gwada min,idan yasan tun farko baya sona me yasa bai gayamin ba tunda ba tilas aka mishi ba?''
girgiza kai kawai raliyan take
''maryam,ke kanki idan kika ga jabir sai kin tausaya masa,kallo daya zaki masa ki tabbata ba'a cikin hayyacinsa yake ba,kinsan me ya fafu ne?,lafiya suka zo gurin daurin auren amma kafin a kai ga gama taruwa ana zaune kawai su nasir suka ga jabir ya sume,mintina kadan ya dawo hayyacinsa,kinsan abinda bakinsa ya fara fada?,jamila nidai jamila nake so wallahi,zan iya rasa rayuwata idan ban mallaketa ba wallahi,abbanshi uazo yabi ba'ason maganar sai yace shi wallahi baisan wata maryam b ai tab cewa yana son wata mai suna marym ba,abbanshi ya dauka iskanci ne ya hau maa fada yace bazai maidashi mutumin banza ba,
''raliya me n yiwa jabir haka da zafi?,wace iriuar qiyayya ce wannan ya gwada min,idan yasan tun farko baya sona me yasa bai gayamin ba tunda ba tilas aka mishi ba?''
girgiza kai kawai raliyan take
''maryam,ke kanki idan kika ga jabir sai kin tausaya masa,kallo daya zaki masa ki tabbata ba'a cikin hayyacinsa yake ba,kinsan me ya fafu ne?,lafiya suka zo gurin daurin auren amma kafin a kai ga gama taruwa ana zaune kawai su nasir suka ga jabir ya sume,mintina kadan ya dawo hayyacinsa,kinsan abinda bakinsa ya fara fada?,jamila nidai jamila nake so wallahi,zan iya rasa rayuwata idan ban mallaketa ba wallahi,abbanshi uazo yabi ba'ason maganar sai yace shi wallahi baisan wata maryam b ai tab cewa yana son wata mai suna marym ba,abbanshi ya dauka iskanci ne ya hau maa fada yace bazai maidashi mutumin banza ba,
abu kamar wasa sai ga jabir ya sake sumewa jin an hanashi jamila,da babanku yaga haka sai yace wa abban nashi ya barshi ai dake da jamilan duka daya ne''ajiyar zuciya maryam din ta ski mai tafe da hawaye,idon raliyan ciki natan tace
''maryama don Allah ki dinga saka abir a addu'o'inki,don ya hadu da jarabta,jiya nasir ya debeni muka je gidan,kinga yadda ake zaman?,yadda kika san bawa da uban gidansa,jabir ya zama abun tasayi,da jamila ta yi magan sai kiga ya zabura,tana saman kujera kwatankwacin bawa da uban gidansa''
''maryama don Allah ki dinga saka abir a addu'o'inki,don ya hadu da jarabta,jiya nasir ya debeni muka je gidan,kinga yadda ake zaman?,yadda kika san bawa da uban gidansa,jabir ya zama abun tasayi,da jamila ta yi magan sai kiga ya zabura,tana saman kujera kwatankwacin bawa da uban gidansa''
a maimakon haushi takaici da tsanar jabir sai tausayinsa ya maye gurbi,take taji fiye da rabin quncin zuciyarta ya tafi,bata jin komai a ayanzu sai tsantsar tausayinsa,lallai ya fada cikin jarrabawa mai girma,sun dade tare da raliyan suna tattuna lamarin har daf da magariba sannan tayi musu sallama ta tafi
Bayan sallar isha'i baban su ya shigo falon nasu,bayanin da yayi musu kusan tishi ne kan wanda raliyar ta musu,ya rife da cewa''dln haka ke maryam sai kiyi haquri ki fidda wani mijin,tunda ke da jamilan duka daya ne 'yar uwarki ce''lamarin baban nasu na daure musu kai saidai ko daya maman tasu bata bari suyi maganar da ita kan yadda yake nuna wariyar launin fata qarara su da sairan yaran gidan,daga haka ya kade rigarshi ya fice yace idan ta samu wani mijin ta sanar masa
.
*WACE CE MARYAMA?*
*WACE CE MARYAMA?*
.
Maryama diya ce ga *amina* da kuma malam *mahmud*,za a iya cewa itace diya ta farko da suka fara haifa shi da ita,asalin su fulanin kano ne cikin wani qauye da ake kira da gaya dukkansu shi da amina mazauna garin ne,yanayin nema ya dawo dasu cikin garin kano
amina maca ce mai matuqar haquri da kawaici tsantsar kyau nafulanin usuli,hakan yasa take da farinjinin samari da dama wanda hakan ya kusa haifar da rigima cikin qauyen nasu,dalili kenan da yasa babanta yayi saurin aurar da ita ga mahmuda dan maqocinsa wanda duka cikin samarin nata dama tafi karkata gashi,kasancewarsa shine kadai mai ilimin primary a cikinsu,amina maca ce maison karatu matuqa da gaske saidi a lokacin lokaci ne da ake qamatar karatin boko hakanne yasa bata samu wannan damar ba shi yasa tayi kwadayin auren mahmud din
kusan shekara uku da auren nasu kafin Allah ya azurtasu da samun qaruwa,da namiji ta haifa saidai baizo da rai ba,sosai mamuda yayi takaici kasancewarsa mai son 'ya'ya musamman maza,babu yadda ya iya haka ya haqura
bayan wannan haihuwar saida amina ta sake wata guda biyu duka maza kuma babu rai sai akan maryamu Allah ya tsaida mata,saidai wannan karon mahmuda baiyi wata murnar azo a gani ba kasancewar ba abunda yake so ba ya samu wato namiji,itakam amina hakan yayi mata dadi don a ganinta duka daya ne fatan dai Allah ya kawo mai albarka
bayan yaye maryam ta sake wata haihuwar macen itama babu rai a haka sai da ta haifi hudu dukkan ajajjere tsiran watanni ne ta kuma samun wani cikin duka dai basu zauna ba,lokacin ne mamuda yace ahikam aure zai qara,bata wani tada hankalinta ba tace ''Allah ya sanya alkhairi''
huwaila ya dauko wadda tunda tazo gidan ta fuskanci ba wani girmamawa yake wa amina ba,don haka ta tayashi takata,kusan tuni ya sakar mata duk wata ragamar kulawa da ta rataya tasu a kansa
huwaila ya dauko wadda tunda tazo gidan ta fuskanci ba wani girmamawa yake wa amina ba,don haka ta tayashi takata,kusan tuni ya sakar mata duk wata ragamar kulawa da ta rataya tasu a kansa
Ba'a taba yiwa Allah dole,hakan ce ta faru ga mamuda domin huwailan ma da ya qwallafa rai a kanta haihuwarta ta fari da mace ta fara,a haka ahaka saida ta tara yara shida duka mata,ganin ita din ma babu biyan buqata sai ya tafi ya auro hadiza ya kuma zubar da lamarin huwaila kamar yada ya yowa aminatu
to ita din ma hadizan bata sake zani ba,matan ne dai sai da ta haifo bakwai sai daga qarahe ne Allah ya kawo namijin wato *ISHAQ* da suke kira isyaku,sunan mahaifin mamudan ne,to fa,babu zama wai an saci dan barawo,nan fa hadiza aka shiga daga kai an haifi namiji,rashin mutunci babu kalar da bata shukawa cikin gidan,hakkane yasa huwaila boye kishinta ta shige jam'iyyar hadizan suke gallazawa aminatu baiwar Allah wadda a lokacin ta sake samun qaeuwar diya mace shekarunta takwas kenan
Rayuwa tayi da rayuwa,yau da gobe kayan Allah,babu da talauci ta ishi jama'a hakan ce ta sauka gidan malam mamuda,ya taraau ya sanar da su cewa saidai fa kowacce tayi haquri da abunda zat gani don gaskiya bai da abun ci da su,ranar da ya samu ya bayar a dafa,ranar da babu kowa ya ci da kanshi,to dama ko can baya ba abinda yake masu,abinci ne zai baki kudin awo ranar cefanenki sai makaranta mai sauqin kudi ya sanya yaran ita din ma don ya dan san dadin ilimin kadan,to sai kuma salla salla ya dinkawa kowa kala daidai dama maryamu bata cikin duka wani budget nasa,idan akayi magana sai yace ai ita babbace ta dauki girma daga haka babu dadi babu ragi
huwaila da hadiza sukayi tsallen albarka suka ce sukam ba zasu iya ba,dukkan yaran nasu suka fidda su daga makaranta suka hau yin sana'a suna dora musu talla,to yaya lafiyar kura balle tayi hauka,dama can ba tarbiyya yaran suka cika ba balle yanzun da suka zama *'yan talla*,tashin kunya kule kule kulen maza da diban albarka kala kala,tun malam mamuda nayin magana har sai ya saka ido,don bashi da ikon yayi maganar sai gori
.
kisan hadiza ce ke juya malam mamuda itace mowar mata sakamakon haifar masa namiji da tayi,duk abinda isiyaku ya fada kam baya qarya,sai ya zamanto aminatu baiwar Allah da yaranta sun zama yan kallo cikin gidan,duk da itama huwailar na baqincikin yadda hadiza ke yadda taga dama amma tilas ta bunne cikin zuciyarta don samun damar cin arziqin samun 'yanci a gidan
kisan hadiza ce ke juya malam mamuda itace mowar mata sakamakon haifar masa namiji da tayi,duk abinda isiyaku ya fada kam baya qarya,sai ya zamanto aminatu baiwar Allah da yaranta sun zama yan kallo cikin gidan,duk da itama huwailar na baqincikin yadda hadiza ke yadda taga dama amma tilas ta bunne cikin zuciyarta don samun damar cin arziqin samun 'yanci a gidan
Amina cire yaranta tayi ta maidasu ta gwamnati,da yan kudaden hannunta tayi masu dukkan abinda ya kamata,ko dama can ita din ba mace ce mai matacciyar zuciya ba,ba'a rabata da 'yan sana'o'i,sune kuwa auka zama marufar asirinta,ita ce kitso,daka,wanki,'yan qulle qullensu kuka daddawa kubewa su lalle ne,da sauransu,da su take samu ake gurgura rayuwar da dadi babu dadi
lokacin da maryamu ta kammala primary taci common entrance G.G.S.C duka wuya ta samu dake qofar famfo,wanda yayi daidai da fitowar manema wa yaransu hadiza wato SHEMA'U,HARIRA FURERA DA RABI,uku yaran huwaila ne daya ce ta hadiza,dukkaninsu basu wuce sha biyu ba sha uku sha hudu,tsabar son aure ne da suka saka aransu ya sasu zama dika dika,ba bata lokaci kuwa aka sa musu ranar aure,malam mamuda ya samu amina da auke kira mama ya sanar mata zai hada ne harda maryamu ya airar da su gaba daya,tunda su gasu qannenta ma sun fidda miji
.
cikin ladabi da son fahimtarwa tace''amma malam ni a ganina dukkaninsu basu yi girman da za'a aurar da su ba,yanzu haka ita kanta maryamun bata kai sha biuar ba bare su,ba zata fi sha hudu ba gaba daya,ni a nawa ra'ayin malam nafison maryamu tayi karatu,idan ta qara girma tasan ciwon kanta sai a aurar da ita''
wannan abun ya qullata yace indai bata yarda an aurar da ita ba to babu ashi babu duk wani shirgi nasu,bata damu ba don dama can ba wani abu yake musu ba
cikin ladabi da son fahimtarwa tace''amma malam ni a ganina dukkaninsu basu yi girman da za'a aurar da su ba,yanzu haka ita kanta maryamun bata kai sha biuar ba bare su,ba zata fi sha hudu ba gaba daya,ni a nawa ra'ayin malam nafison maryamu tayi karatu,idan ta qara girma tasan ciwon kanta sai a aurar da ita''
wannan abun ya qullata yace indai bata yarda an aurar da ita ba to babu ashi babu duk wani shirgi nasu,bata damu ba don dama can ba wani abu yake musu ba
tofa,wanna ya sake hura wutar tsanar da sukayiwa maryam wanda dama tun suna qanana aka horesu da ita,don ko wasa bata isa ta shiga cikinsu tayi ba,gashi lokacin bata da 'yar uwa don ba'a haifi hindatu ba alokacin,bugu da qari,kyau da Allah ya bata fiye da duk wata yarinya dake cikin gidan,duk da suma Allah ya basu nasu kyan babu laifi saboda mahaifinsu malam mamuda kyakkyawan bafulatani ne
Allah yayi maryam mai hazaqa da qwaqwalwa,tana da matuqar son karatu,haknne yasa bata yadda ta kula kowanne saurayi wanda su kuma suka fassara hakan da cewa girman kai ne kurum don tana ganin ita kyakkyawa ce,cikin zuciharta ita din tasan ba haka bane tunda ba haka take din ba azahirance
.
maryam doguwar mace ce wadda Allah ya yiwa baiwar diri da structite na jiki duk da tsahonta hakan bai boye kyawun zubinta ba,fara ce amma ba tas ba,idan kaso ma zaka iya kiranta da ja,don irin farin nan ne mai cakude da ja,gashinta sosai irin na fulani mai laushi da santsi,zara zaran gashin ido da na gira da madaidaicin baki,dimple dinta hagu da dama wanda ko magana murmushi tayi sai ya lotsa,hancinta ba mai tsani ba tafe yake da tsohonsa da kuma tudu,idanunta irin idon nan ne da ake cewa oily eyes wanda zakayi tsammanin qwalla ko ruwa ne suka taru cikin qwayar idon,bata da baqin qwayar ido sosai,sanyin muryarta da zaqinta ke dada bayyana kyawun halittar da Allah yayi mata wanda hakan ya ja mata yawan masoya da maqiya ciki harda 'yan gidansu
maryam doguwar mace ce wadda Allah ya yiwa baiwar diri da structite na jiki duk da tsahonta hakan bai boye kyawun zubinta ba,fara ce amma ba tas ba,idan kaso ma zaka iya kiranta da ja,don irin farin nan ne mai cakude da ja,gashinta sosai irin na fulani mai laushi da santsi,zara zaran gashin ido da na gira da madaidaicin baki,dimple dinta hagu da dama wanda ko magana murmushi tayi sai ya lotsa,hancinta ba mai tsani ba tafe yake da tsohonsa da kuma tudu,idanunta irin idon nan ne da ake cewa oily eyes wanda zakayi tsammanin qwalla ko ruwa ne suka taru cikin qwayar idon,bata da baqin qwayar ido sosai,sanyin muryarta da zaqinta ke dada bayyana kyawun halittar da Allah yayi mata wanda hakan ya ja mata yawan masoya da maqiya ciki harda 'yan gidansu
haka aka sha bikin yan uwan nata su hudu yayin da ita kuma ta duqufa karatunta,maryam badai qwaqwalwa ba,hakan ne ma yasa bata samu cikas ko ksdan a karatunta ba,cikin nasara komai ke tafiyar mata,janye jiki da masoyanta sukayi a lokacin bai dameta ba don dama bata buqatar wani damuwa karatunta ne kawai damuwarta,cikin nasara ta shige B U K inda anan ta samu shaidar degree dinta kan fannin girke girke
.
ba jimawa,da kammalawa kuwa ta samu aiki da wani katafaren gurin cin abinci da shirya bukukuwa ,wanda cikin qanqanin lokaco ta samu matsayi mai girma na shugabantar dukka masu girka wani abunda za'aci ko a gurin ko kuma aka basu kwangilar yi na biki,qwazo himma gaskiya da amana su suka jawa maryamua wannan matsayin wanda hatta da wadda ta kafa gurin *HAJIYA ATIKA ABUBAKAR BAFFA* ke qaunarta
ba jimawa,da kammalawa kuwa ta samu aiki da wani katafaren gurin cin abinci da shirya bukukuwa ,wanda cikin qanqanin lokaco ta samu matsayi mai girma na shugabantar dukka masu girka wani abunda za'aci ko a gurin ko kuma aka basu kwangilar yi na biki,qwazo himma gaskiya da amana su suka jawa maryamua wannan matsayin wanda hatta da wadda ta kafa gurin *HAJIYA ATIKA ABUBAKAR BAFFA* ke qaunarta
ta bangaren 'yan uwanta kuwa saidai ace Allah ya rufa asiri kawai domin dukkaninsu cikin shekara guda babu wadda bata da tabon saki wanda tsantsar rashin tarbiyyarsu ya hanasu zaman arziqi da mazajensu,a haka dai ake gurgurawa har kawo wannan lokaci,hankalin maryamu bai fara tashi ba sai da aka zo auren qannanta zagaye na biyu wato *azara* *shamsiyya* da *maraqisiyya*,tsantsar gori habaici da baqar magana idan da tana tsiro a lokacin to da tuni ta yiwa maryam,sai Alla ya halicceta mai haquri da kawaici hakanne yasa bata fiya zafafawa kan lamuransu ba,idan suna yi dauke kanta take kamar yadda tun usuli ta tashi taga mamanta nayi
.
samuwar aikinta ya taimaka qwarai wajen kyautatuwar rayuwarsu,wanda alfanun ilimin da ta gani ya sata jajircewa da tsayawa qanwarta daya tilo don ganin itama ta amfana,duk lokacin da ta daki albashinta bata fasa siyan wani muhimmin abu ta kaiwa mahaifinta ko ta ciri kidin tsaba ta bashi,babu kuma wani jin nauyi zaisa hannunshi ya amsa da sunan ai yarshi ce,haka rayuwar maryamu ta taso cikin tsangwamar *'yan uba* wanda har yau ita take gani ba kuma tasan ranar qarewarta ba
samuwar aikinta ya taimaka qwarai wajen kyautatuwar rayuwarsu,wanda alfanun ilimin da ta gani ya sata jajircewa da tsayawa qanwarta daya tilo don ganin itama ta amfana,duk lokacin da ta daki albashinta bata fasa siyan wani muhimmin abu ta kaiwa mahaifinta ko ta ciri kidin tsaba ta bashi,babu kuma wani jin nauyi zaisa hannunshi ya amsa da sunan ai yarshi ce,haka rayuwar maryamu ta taso cikin tsangwamar *'yan uba* wanda har yau ita take gani ba kuma tasan ranar qarewarta ba
_*WANNAN KENAN*_
.
Cike da tawakkali da yarda da qaddara ta miqa dukkan lamarinta ga Allah,a yanzu kam ta sanya jabir ne kawai cikin addu'o'inta kamar yadda raliya ta shawarceta,domin tausayinsa ne fal cikin zuciyarta,tana ji a cikin zuciyarta ta sanadinta ne ya afka wannan qaddarar
abu guda ne ta kasa tinsa komawa walwalarta da aikinta tamkar,yadda take yi a da duk da yadda take son aikin,ta barwa ranta cewa ta ajjiye aikin zata kuma jira har lokscin da ubangiji zai musanya mata da da wani mijin ko da baikai jabir dinta ba
misalin biyar da rabi ne na yammaci,zaune take a rumfar tasu wadda ta sha mopping tayi fes,dai qamshin turaren tsinke take,mamanta na dakin babansu tana gyarawa don ita ta amshi girki,don sam bata lamunce don ranar girkinta bane ta tura yaranta su share dakin baban nasu ba kamar yafda taga su huwaila nayi tsabar ganda,yayin da hindatu ke makarantar islamiyya
sanye take da maroon din material dinkin doguwar riga da yake ma'abociyar son dogayen riguna ne ko don tsahon da take da shi,yatsunta sunyi kyau da jan lallen da tadan qunsa iya yatsu,a lokaci irin wannan idan bata da abinda duka zatayi,taka duqufa wajen research din girke girke a daga sashukan dake watso kalolin abinci na qasashe daban daban,kadan kadan hankalinta ke rabuwa gida biyu,wani lokaci yayi tsakar gida da yaran inna hadiza keta faman ta'adi cikin falon gyatumar tasu da hayaniya na 'yan fadace fadace atsakaninsu kuma babu wanda ya isa yace zai tsawatar musu
cikin haka ta jiyo sallamar inna hadizar,abu na farko da ya biyo bayan sallamarta shine ashar da ta dura wanda har sai da maryamu tayi ta'awizi cikin zuciyarta
''kaga tsinannun yara shegu,ke balaraba da na bar muku dakin a bude shine kuka maida min shi sansanin fada da kokaye kokaye,kuma saboda tsabar baqincikin Allah yayi maka arziqi a rasa mai tsawatrwa uaran salon su fasa ma abu kosu lalata ma su jawo maka asara,dadin abun ma yanzu kana da arziqin da zaka gyara''
''kaga tsinannun yara shegu,ke balaraba da na bar muku dakin a bude shine kuka maida min shi sansanin fada da kokaye kokaye,kuma saboda tsabar baqincikin Allah yayi maka arziqi a rasa mai tsawatrwa uaran salon su fasa ma abu kosu lalata ma su jawo maka asara,dadin abun ma yanzu kana da arziqin da zaka gyara''
sarai mama tasan da ita take amma kasancewar ko da can ma da jini ajika ba kula shirginta take ba yasa yanzun ma tayi mata dif,saiga huwaila ta fito daga wanka takalleta
''a'a,ina kuma kikaje?''
''yo ina kuwa zanje da ya wuce gidan doyar albarka jamila''ta fada tana shirin shigewa dakinta
sakwatoto huwailan tayi
''amma inace baki tafi ba don wanna wanka da nayi na shirin zuwa ne,tunda munyi tare zamu je''
''kiji hiwaila da wani zance,don,lawai zaka girin naka sai ka jawo bare?''binta wadda tare suka je da innar tata ta maidawa huwaila raddi
''kinga ba dake nake ba 'yar ayi jikar na saba''
''a'a,ina kuma kikaje?''
''yo ina kuwa zanje da ya wuce gidan doyar albarka jamila''ta fada tana shirin shigewa dakinta
sakwatoto huwailan tayi
''amma inace baki tafi ba don wanna wanka da nayi na shirin zuwa ne,tunda munyi tare zamu je''
''kiji hiwaila da wani zance,don,lawai zaka girin naka sai ka jawo bare?''binta wadda tare suka je da innar tata ta maidawa huwaila raddi
''kinga ba dake nake ba 'yar ayi jikar na saba''
''a'a,dakata don ta fadi gaskiyarta,kada kiyi haushin kaza huce kan dami''inji onna hadiza cikin salon tare mata
''au bayanta kike goyo kenan?''
''qwarao,yo akan me?''
baqinciki ya,hanata cewa komai sai qwafa kawai da ta ja ta shige dakinta
qarar wayarta ce ta sata dawowa daga diniyar da su inna jadizan suka shigar da ita,a kullum kwanan duniya sake gasgata zancan raliya takegame da abinda ya faru tsakaninta da jabir,jikinta a sanyaye tabi wayar da kallo ,da kamar ba zata daga ba amma ganin sunan *mama* ya sata babu jinkiri ta daga,cike da,girmamawa take gaidata
''babu abinda zaki cemin maryamu,wa yafi qarfin qaddara a rayuwa?,abun nan ya riga ya wuce addu'a ce kawai mafita,amma anyi anyi ki koma gun aikinki kinqi,na tambayi haj rabi ko wani laifin aka miki sunce babu komai,ko an miki wani abu ne agun?''
cike da girmamawa tace ''babu abinda aka yimin mama wallahi''
''to shikenan,indai da gaske haka ne kizo gobe gida ki sameni da la'asar,da akwai aikin da aka samu kuma gaskiya a iya hasashena babu wadda ta dace da aikin sai ke,don na yaba qwarai da tarbiyya gaskiya da riqon amanarki''
ba zata iya musu da mama ba wato hajiya atika abubakar,banda haka da wata ce zqta ce mata ta gode bata buqata,amma girmanta da qaunar da take gwada mata ta wuce haka a gurinta don haka tace
''to mama,na gode Allah ya saka da alkhairi insha Allahh goben ina hanya''
''to shikenan a gaida mutan gidan''
''zasu ji insha Allah''
.
''au bayanta kike goyo kenan?''
''qwarao,yo akan me?''
baqinciki ya,hanata cewa komai sai qwafa kawai da ta ja ta shige dakinta
qarar wayarta ce ta sata dawowa daga diniyar da su inna jadizan suka shigar da ita,a kullum kwanan duniya sake gasgata zancan raliya takegame da abinda ya faru tsakaninta da jabir,jikinta a sanyaye tabi wayar da kallo ,da kamar ba zata daga ba amma ganin sunan *mama* ya sata babu jinkiri ta daga,cike da,girmamawa take gaidata
''babu abinda zaki cemin maryamu,wa yafi qarfin qaddara a rayuwa?,abun nan ya riga ya wuce addu'a ce kawai mafita,amma anyi anyi ki koma gun aikinki kinqi,na tambayi haj rabi ko wani laifin aka miki sunce babu komai,ko an miki wani abu ne agun?''
cike da girmamawa tace ''babu abinda aka yimin mama wallahi''
''to shikenan,indai da gaske haka ne kizo gobe gida ki sameni da la'asar,da akwai aikin da aka samu kuma gaskiya a iya hasashena babu wadda ta dace da aikin sai ke,don na yaba qwarai da tarbiyya gaskiya da riqon amanarki''
ba zata iya musu da mama ba wato hajiya atika abubakar,banda haka da wata ce zqta ce mata ta gode bata buqata,amma girmanta da qaunar da take gwada mata ta wuce haka a gurinta don haka tace
''to mama,na gode Allah ya saka da alkhairi insha Allahh goben ina hanya''
''to shikenan a gaida mutan gidan''
''zasu ji insha Allah''
.
ta sauke wayar tana jin wani abu na dan taba zuciyarta,mama da bata kima da shigowa ba tace ''ke da waye?''
ajiuar zuciya ta saki
''haj atika ce,wai tana nemana gobe''
''to Allah yasa lafiya,ko zancan komawarki ne gurin aikin?''
''a'a,tace wani aiki ne ya samu,amma sai naje goben zanji''
''Allah ya rufa asiri ''ta fada maman tana ficewa dauke da wankakken zanin gado da rigar filo
murmushi maryam tayi tana jinjina kai,wato miji da mata sai Allah,maman ta tana burgeta matuqa,bilhaqqi take kula da mijinta,bata duba komai sai zatin Allah da kalmar nan ta *aure bautar ubangiji*
ajiuar zuciya ta saki
''haj atika ce,wai tana nemana gobe''
''to Allah yasa lafiya,ko zancan komawarki ne gurin aikin?''
''a'a,tace wani aiki ne ya samu,amma sai naje goben zanji''
''Allah ya rufa asiri ''ta fada maman tana ficewa dauke da wankakken zanin gado da rigar filo
murmushi maryam tayi tana jinjina kai,wato miji da mata sai Allah,maman ta tana burgeta matuqa,bilhaqqi take kula da mijinta,bata duba komai sai zatin Allah da kalmar nan ta *aure bautar ubangiji*
washegari ta shirya tsaf cikin atamfa dinkin riga da skert yaluwa sosai tayi,mata kyau ta qara haske da rama,hakan sai ya sake fidda tsayinta,kasancewar lahadi ce yasa ta nemi rakiyar hindatu ko zata ji dadin tafiyar,don ita kanta bata son tafiya ita kadai,gani take kamar idan ta fita nuna ta za'a dinga yi,tsawon watanni kusan biyar amma tunda abin ya faru baifi sau biyi ta fita ba zuwa uku shima sai dare
babu dadewa suka isa gidan maman,a falon qasa aka saukesu mintina biyar aka haura da su samanta wanda ba kowa take kaiwa ba,cike da fara'a ta tarbi maryam din,ita dai ranta yanason maryam din,natsuwarta na burgeta,
kayan ciye ciye ta sa aka kawo misi ta dan basu lokaci kadan sannan ta dawo
''maryam''abinda ta fara cewa kenan
''kamar yadda jiya na shaida miki a waya aiki ne ya samu,yayi shige da na gurina amma yana da bambanci domin wannan a gida zaki dinga yinshi,zaki samu albashi mai tsoka fiye da na gurina''
ta,dubeta da aily eyes dinta''mama wanne irin aiki ne a gida?''
''kinsan marigayi *alhaji abdulkareem mai nasara*?''
sai da tadan shiga tunani sannan tace
''eh ina jin sunanshi mama''
''yauwa,kinga sanannen mutum ne kuma fitace tun kafin rasuwarshi,yaro daya Allah ya basu wato *Abdallah*duk da cewa yana da wata matar amma Allah abi bata haihuwa da shi ba,saidai ya riqe mata nata uaran da ta taba haifa awani gidan mata ne su biyu da nimiji daya yanzu haka duka suna tare a gidan duk da rasuwan shi alhj abdulkareem din hakan baisa sun raba mazauni ba,mamanshi na matuqar sonshi da kaffa kaffa da lamuranshi,duk da haka ana farautar rayuwarsa don kusan sau biyu kenan ana zuba poising abincinshi,ta rasa daga ina matsalar take,kuma duk lokacin da hakan ya faru idan aka tashi binncike sai a samu da hannun kukunshi,hakan yasa take canza masa kuku kala kala,amma har yau babu wanda hankalinta ya kwanta da shi
kayan ciye ciye ta sa aka kawo misi ta dan basu lokaci kadan sannan ta dawo
''maryam''abinda ta fara cewa kenan
''kamar yadda jiya na shaida miki a waya aiki ne ya samu,yayi shige da na gurina amma yana da bambanci domin wannan a gida zaki dinga yinshi,zaki samu albashi mai tsoka fiye da na gurina''
ta,dubeta da aily eyes dinta''mama wanne irin aiki ne a gida?''
''kinsan marigayi *alhaji abdulkareem mai nasara*?''
sai da tadan shiga tunani sannan tace
''eh ina jin sunanshi mama''
''yauwa,kinga sanannen mutum ne kuma fitace tun kafin rasuwarshi,yaro daya Allah ya basu wato *Abdallah*duk da cewa yana da wata matar amma Allah abi bata haihuwa da shi ba,saidai ya riqe mata nata uaran da ta taba haifa awani gidan mata ne su biyu da nimiji daya yanzu haka duka suna tare a gidan duk da rasuwan shi alhj abdulkareem din hakan baisa sun raba mazauni ba,mamanshi na matuqar sonshi da kaffa kaffa da lamuranshi,duk da haka ana farautar rayuwarsa don kusan sau biyu kenan ana zuba poising abincinshi,ta rasa daga ina matsalar take,kuma duk lokacin da hakan ya faru idan aka tashi binncike sai a samu da hannun kukunshi,hakan yasa take canza masa kuku kala kala,amma har yau babu wanda hankalinta ya kwanta da shi
abdallah shine shugaban jami'an tsaro na farin kaya wato *S S*na nijeria gaba daya,wanda aikinsa kansa na buqatar ya zamo cikin kulawa da tsaro na musamman
bata da lokacin zama agida kasancewarta cikakkiyar likita kan fannin matsalolin da suka shafi mata,wannan ne yasa ta bayar da cigiyar amintacce ko amintacciya wanda ya qware kota qware afannin girki,to qawarta aminiya ta ce hakan ne yasa ta bani cigiya ni kuma naga ke kika fi cancanta da wanna aikin maryam,ina fatan kin fahimceni abunda kuma ya shige miki duhu kina iya tambaya ta''
shiru tayi domin tana jin abun da kamar wuya,sam bata ji ya kwanta mata ba aikin,tamkar aikatau zata tayi,kenan tunda aikin dafa abinci zata gidan wasu?,anya kuwa zata iya amsar tayin maman,amma tana jin nauyinta ,ba zatq kallon tsabar qwayar idonta tace mata a'a kai tsaye ba,kusan minti biyi sannan ta ajjiye numfashi
''ina ganin mama zanje na sanar da maga batana tukun,idan yaso duk abinda suka yanke akai zan sanar miki''
''yayi kyau,hakan dai dai ne maryam,wannan shike dada nunamin hankalinki da kaifin tunaninki,amma ina fatan bazaki watsa min qasa a ido ba''
''insha Allahu''
ta fada ka a qasa''
a haka sula rqbu bayan ta baiwa hindatu dubu daya tace ta siyi kayan kwalliya
''ina ganin mama zanje na sanar da maga batana tukun,idan yaso duk abinda suka yanke akai zan sanar miki''
''yayi kyau,hakan dai dai ne maryam,wannan shike dada nunamin hankalinki da kaifin tunaninki,amma ina fatan bazaki watsa min qasa a ido ba''
''insha Allahu''
ta fada ka a qasa''
a haka sula rqbu bayan ta baiwa hindatu dubu daya tace ta siyi kayan kwalliya
cikin mota hindatu ta isheta da karadin wallahi yaya maryam ki amshi aikin nan
murmushi kawai tayi
''yarin ya ce ke hindatu har yau baki da hangen nesa''
''to,ya maryam meye aibu a ciki?''
bata amsa mata ba sakamakon jin ringing din wayarta da tayi ta soma kiciniyar cirota dqga aljihun jakar,raliya ce mai kiran
''hello ummin fadil''
''na'am mommyn fadil kina ina ne?''
''kin ganni a hanya na dawo ne a wata unguwa''
''yauwa don Allah ina son ganin ki ne ya za'ayi?''
''babu damuwa bari kawai na qaraso''
''yauwa ta gurina''
dariya ta bata tace ''sai na qaraso''ta maida wayar jaka sannan ta yiwa mai adaidaita bayanin inda zai juya da su''
murmushi kawai tayi
''yarin ya ce ke hindatu har yau baki da hangen nesa''
''to,ya maryam meye aibu a ciki?''
bata amsa mata ba sakamakon jin ringing din wayarta da tayi ta soma kiciniyar cirota dqga aljihun jakar,raliya ce mai kiran
''hello ummin fadil''
''na'am mommyn fadil kina ina ne?''
''kin ganni a hanya na dawo ne a wata unguwa''
''yauwa don Allah ina son ganin ki ne ya za'ayi?''
''babu damuwa bari kawai na qaraso''
''yauwa ta gurina''
dariya ta bata tace ''sai na qaraso''ta maida wayar jaka sannan ta yiwa mai adaidaita bayanin inda zai juya da su''
''daga ina kuke da yammacin nan ne?''raliya ta tambayi maryam sanda take dire musu drinks
''hmmm,wallahi kinga haj atika ce tayi kira na,wai ta samamin aiki gidan marigayi abdul kareem mai nasara''
sai taga fuskar raliyan ta sauya ta dan tsuketa
''ba zaki koma wani aiki ba,aure zakiyi maryam''ta gada kai tsaye tana kallon maryam din
ba tare,da kawo komai cikin zuciyarta ba tayi murmushi
''banda abinki qawata ba sai Allah ya kawo mijin ba?''ta fada cikin rashin kulawa
''Allah ya kawomiki miji maryam''sai da taji qirjinta ya wani irin buga
''miji?,wa ya gaya miki,qarya ne ni babu mijin da na samu''
matsowa tayi sosai ta kama hannayen ta
''maryam kin amince da ni kin kuma yarda da amincin dake tsakaninmu?''
''me ya kawo wannan tambayar kuma raliya?''ta tambayeta cikin yanayi na shiga duhu
''maryam so nake ki auri nasir mijina''
''hmmm,wallahi kinga haj atika ce tayi kira na,wai ta samamin aiki gidan marigayi abdul kareem mai nasara''
sai taga fuskar raliyan ta sauya ta dan tsuketa
''ba zaki koma wani aiki ba,aure zakiyi maryam''ta gada kai tsaye tana kallon maryam din
ba tare,da kawo komai cikin zuciyarta ba tayi murmushi
''banda abinki qawata ba sai Allah ya kawo mijin ba?''ta fada cikin rashin kulawa
''Allah ya kawomiki miji maryam''sai da taji qirjinta ya wani irin buga
''miji?,wa ya gaya miki,qarya ne ni babu mijin da na samu''
matsowa tayi sosai ta kama hannayen ta
''maryam kin amince da ni kin kuma yarda da amincin dake tsakaninmu?''
''me ya kawo wannan tambayar kuma raliya?''ta tambayeta cikin yanayi na shiga duhu
''maryam so nake ki auri nasir mijina''
a hagunce take kallon raliyan,jo tayi lamar ta doka mata guduma atsakiyar ka,gani take kamar ba'a hayyacinta take ba''raliya,me kika sha yau,ko baki da lafiya?''
murmushi tayi
''nasan zaki fadi haka maryam,amma ras nake,kuma nasan me nake,cewa nayi mijina nake so ki aura nasir''
''shi ya aiko ki lo ke kika aiko kanki?''ta tambaueta tana mata kallon ba a hayyacinta take ba
''ni na aiko kaina tare da amincewarsa''
zame hannayenta tayi ta miqe
''idan kin warke kya kirani muyi maganar da kika rani domin ita,don dai wannan ban daukeshi da muhimmanci ba''
kamo hannunta tayi
''zauna maryam,wallahi a hayyacina nake,kuma lafiyata lau''
murmushi tayi
''nasan zaki fadi haka maryam,amma ras nake,kuma nasan me nake,cewa nayi mijina nake so ki aura nasir''
''shi ya aiko ki lo ke kika aiko kanki?''ta tambaueta tana mata kallon ba a hayyacinta take ba
''ni na aiko kaina tare da amincewarsa''
zame hannayenta tayi ta miqe
''idan kin warke kya kirani muyi maganar da kika rani domin ita,don dai wannan ban daukeshi da muhimmanci ba''
kamo hannunta tayi
''zauna maryam,wallahi a hayyacina nake,kuma lafiyata lau''
wani kallo ta watsa mata''sake ni raliya,ni 'yar halak ce kuma nasan halacci na kuma yi imani da akwaishi,idan haka kike to ni ba haka nake ba,idan kuma nasir din ne ya saka ki to ki gaya masa ni maryam 'yar halak ce''ta zame hannuwanta ta fice yayin da raliya ta bita tana qwala mata kira amma ko waiwayota bata yi ba,hindatu dake farfajiyar gidan tana waya itama wucewar maryam din ta gani sai binta tayi a baya
kuka zata yi ne ko ihu?me kuma yake shirin faruwa da ita?me yasa guguwar rayuwa ke walagigi da ita?,yau wai amiyarta ke gaya mata ta auri mijinta,ta ina ta yaya ma zata iya auren mijin raliya ko su biyu ne suka rage a duniya,ko da suka ke gida mama kasa gane kanta tayi,don tunda ta shigo gidan dakinta ta wuce kai tsaye,cikin damuwa maman ke tambauar hindatu me ya faru da maryam din
''ni dai mama da mukaje gidan hajiya lafiya lau muka fito,kuma iki ta samar mata gida alhj abdulkareem mai nasara,amma dai mun biya gidan anty raliya,to nidaiina waje bansan me suka tattauna ba naga dai ta fito da sauri ma biyo bayanta''
''alhj abdulkareem mai nasara?''mama ta maimata sunan don ba boyayyen mutum bane,mai arziqi ne na gani a fada wanda akayi qiyason duka nigeria babu wanda ya kama qafarshi
''ni dai mama da mukaje gidan hajiya lafiya lau muka fito,kuma iki ta samar mata gida alhj abdulkareem mai nasara,amma dai mun biya gidan anty raliya,to nidaiina waje bansan me suka tattauna ba naga dai ta fito da sauri ma biyo bayanta''
''alhj abdulkareem mai nasara?''mama ta maimata sunan don ba boyayyen mutum bane,mai arziqi ne na gani a fada wanda akayi qiyason duka nigeria babu wanda ya kama qafarshi
''to Allah ya kayuta,indai raliyance ai ba'a ashiga tsakaninsu,idan kuma aikin ne ma zamuji,qyaleta hindatu,nasqn zata min maganar da kanta''don shaquwar dake tsakaninsu yasa maryam bata boyema maman tata duka damuwarta
.
kwana guda da yini daya bata ce da maman tata komai ba,itama zuba mata idon tayi bata tambayeta ba
kwana guda da yini daya bata ce da maman tata komai ba,itama zuba mata idon tayi bata tambayeta ba
kwana na biyun ne qarfe uku taji sallamar raliya,tana kwanve can cikin dakinsu saman katifarta,don yanzu zaman daki da kwanciya kuma ta aira wanda hakan baya rasa nasaba da yawan tunanin da take fama da shi,sai da gabanta ya fadi lokacin da tqji suna gaisawa da mama ta fadi mata tana cikin dakin
jawo dankwalinta tayi tana dauraqa tare da qoqarin yashi duka a lokaci daya,raliya ta iso bakin katifar ta zauna bayan ta shimfide fadil dake sharar bacci a gefanta
''na gode diyana,na gode''
''ai ni ke da godiya''ta fadi tana sake matse fuska
''wai ni zan ta kiranki maruam amma kiqi dagawa?''
''kadan ma kika gani matuqar kina kan qudirinki,nan da dan qanqanin lokaci zansa almakashi na datse igiyar mu'amala ta dake,tunda ba son Allah da annabi kuke min ba,so kuke ku cutar da ni''
dafe bakinta raliya tayi tana kallon maryam din kamar yau ta fara ganinta,ta sani babu shakka ba qaramin baci ran maryam din yayi ba tunda har ta iya furta mata haka,tafi kowa sanin halinta na rashin son fada da tashin hankali
''na gode diyana,na gode''
''ai ni ke da godiya''ta fadi tana sake matse fuska
''wai ni zan ta kiranki maruam amma kiqi dagawa?''
''kadan ma kika gani matuqar kina kan qudirinki,nan da dan qanqanin lokaci zansa almakashi na datse igiyar mu'amala ta dake,tunda ba son Allah da annabi kuke min ba,so kuke ku cutar da ni''
dafe bakinta raliya tayi tana kallon maryam din kamar yau ta fara ganinta,ta sani babu shakka ba qaramin baci ran maryam din yayi ba tunda har ta iya furta mata haka,tafi kowa sanin halinta na rashin son fada da tashin hankali
''sonki muke kuwa maryam,saidai ke dake ahirin juya manufarmu ta alkhairi ki maisheta ta sharri,meyw aobu cikin aurenki da nasir maryam?''kafeta tayi da ido cikin bacin rai tace
''baki bar maganar,nan ba kenan ko raliya?''
''ta yaya kikeso nabar alkhairin da na hango miki ha wofanta kenan a banza?''
''lallai babu shakka kin gaji da hulda da ni.....ina zuwa''sai ta yunqura ta miqe kana ta fice
''baki bar maganar,nan ba kenan ko raliya?''
''ta yaya kikeso nabar alkhairin da na hango miki ha wofanta kenan a banza?''
''lallai babu shakka kin gaji da hulda da ni.....ina zuwa''sai ta yunqura ta miqe kana ta fice
mintina kadan sai gata sun shigo tare da mama
''wai me ya hadaku ne da raliyan?''maman ta tambaya tana daga tsaye ba tare da ta zauna ba
''mama kinji abunda raliya ke fada kuwa,ba shakka ina tsammanin ta haukace ne,wai mama na auri nasir mijinta fa take cewa''
ba shiri mama ta nemi giri ta zauna,ta dubi raliya sosai
''da gaskene abunda maryama ke fadi?''
cike da tabbatarwa ta girgiza kai
''eh mama haka ne,ni a ganina ni da maryam mun zama daya,na yadda da ita na kuma aminta da kyawawan halaye da dabi'unta,na tabbata ba zata cuce ni ba,to mama laofi ne don na gayyatota tazo mu zauna qarqashin inuwa guda?''
''wai me ya hadaku ne da raliyan?''maman ta tambaya tana daga tsaye ba tare da ta zauna ba
''mama kinji abunda raliya ke fada kuwa,ba shakka ina tsammanin ta haukace ne,wai mama na auri nasir mijinta fa take cewa''
ba shiri mama ta nemi giri ta zauna,ta dubi raliya sosai
''da gaskene abunda maryama ke fadi?''
cike da tabbatarwa ta girgiza kai
''eh mama haka ne,ni a ganina ni da maryam mun zama daya,na yadda da ita na kuma aminta da kyawawan halaye da dabi'unta,na tabbata ba zata cuce ni ba,to mama laofi ne don na gayyatota tazo mu zauna qarqashin inuwa guda?''
azafafe maryam tace
''kinjifa mama irin abunda take cewa,ro billahil azim indai raliya bata sauka daga kan bakanta ba na miki rantsuwa mama har da Allah daga yau babu ni babu ita har abada''
tsot dakin yayi son su kansu aun sani matuqar maryam ta rantse akan abu to sai ta aiwatar,kuma alamu duka sun nuna irin yadda batun ke taba mata zuciya ba qarami bane,maman ce ta soma magana
''koda maryamu ta amince da maganar ma ni bazan amince ba,haba raliya aisai duniya ta zagemu,jama'a su saka mu a tadinsu,idan banda abunki ma raliya kwata kwata shekarunku nawa da yin auren,banda quruciya haka kawai kuna zamanku gwanin sha'awa ki dinga kira ma kanki kishiya uhm raliya?,na roqeki nima ki bar maganar haka nan kinji?''
qwalla ta cika mata ido ta tausayin maryam don qaunar da take mata ta fisabilillah
''shikenan mama,koda baki roqeni ba zan bar zancen ko don kada na rasa aminiya irin maryam,saidai....maryam na gode,na gode da kika nuna min iyaka ta''
duk da taji rashin dadin batawa raliyan da tayi amma sai taji kamar an tafiyar mata da wani qullutu da ya tokare mata wuya,sai taji damuwarta ta rage farashi zuwa kaso tamanin
''kinjifa mama irin abunda take cewa,ro billahil azim indai raliya bata sauka daga kan bakanta ba na miki rantsuwa mama har da Allah daga yau babu ni babu ita har abada''
tsot dakin yayi son su kansu aun sani matuqar maryam ta rantse akan abu to sai ta aiwatar,kuma alamu duka sun nuna irin yadda batun ke taba mata zuciya ba qarami bane,maman ce ta soma magana
''koda maryamu ta amince da maganar ma ni bazan amince ba,haba raliya aisai duniya ta zagemu,jama'a su saka mu a tadinsu,idan banda abunki ma raliya kwata kwata shekarunku nawa da yin auren,banda quruciya haka kawai kuna zamanku gwanin sha'awa ki dinga kira ma kanki kishiya uhm raliya?,na roqeki nima ki bar maganar haka nan kinji?''
qwalla ta cika mata ido ta tausayin maryam don qaunar da take mata ta fisabilillah
''shikenan mama,koda baki roqeni ba zan bar zancen ko don kada na rasa aminiya irin maryam,saidai....maryam na gode,na gode da kika nuna min iyaka ta''
duk da taji rashin dadin batawa raliyan da tayi amma sai taji kamar an tafiyar mata da wani qullutu da ya tokare mata wuya,sai taji damuwarta ta rage farashi zuwa kaso tamanin
durqusawa tayi bayan ta miqe tana qoqarin daukar fadil tace da mama
''mama ni zan wuce''
''kinga malama ajjiye fadil din ni zan daukeshi,tunda ba ke kadai bace ai uwarshi ba''cewar maruam tana yafagyalenta don yi mata rakiya,don ta fuskanci tafiya,zata yi,ta san halin raliya ciki da bai tasan fushinta koda ta tsaidata ma ba hirar atziqi zasu yi ba
''ni kadai ce mana uwarsa tunda kinqi ubansa''ta maida mat martani tana qoqarin ficewa,murmushi kawai maryam din tayi ta saba fadil din ta biyo bayanta
''mama ni zan wuce''
''kinga malama ajjiye fadil din ni zan daukeshi,tunda ba ke kadai bace ai uwarshi ba''cewar maruam tana yafagyalenta don yi mata rakiya,don ta fuskanci tafiya,zata yi,ta san halin raliya ciki da bai tasan fushinta koda ta tsaidata ma ba hirar atziqi zasu yi ba
''ni kadai ce mana uwarsa tunda kinqi ubansa''ta maida mat martani tana qoqarin ficewa,murmushi kawai maryam din tayi ta saba fadil din ta biyo bayanta
''halan driver ne ya kawoki?''
''ban sani ba,idonki ya baki amsa''tave da maryam din lokacin da auka fito tana gaba ita na binta abaya,mirmuahin dai ta kuma yi har beuty points dinta suka loba
''Allah ya baki haquri,yau kam ai akan gwiwa kike sai lallabe''
''a'ah,akan haba nake''
amsar da ta bata ta sanya maryam tuntsirewa da dariya har itama raliyan ta dan murmusa don fushinta da maryam ba ya wani tasiri
suna isa gaban motar ta ganshi zaune,shi ya kawota kenan,raliya ta bude ta shiga yayin da maryam ta galla masa harar lokacin da suka hada ido,dariya ya tuntsure da ita yana kallon raliya da tayi kicin kicin
''kada kice komai,don babu ruwan nasiru,kinga kanwar nan''
''babu wani nan,waye baisan halinku maza ba,to wllahi bari kaji,idan ka sake ka yiwa aminiya ta kishiya ban yafe ba koda wace ce kuwa,ke kuma kici gaba da nema masa aire kinji ko solobiyo''ta fada harda dan kama kunnen raliyan
dariya abun nata ya basu
''ni don Allah sake min kunne,tunda kin gujemu dai ba shikenan ba''
''indai irin wannan gudun ne raliya am sorry to say....zanta gudunku har abada''ta dan ja da baya ta rue musu qofar tana murmushi sanna ta dan sara mata shigen yadda sojoji suke
''Allah ya huci zuciyar ranki shi dade,oya kai kuma kaja mini aminiya ta ahankali''
''oho dai abanza tinda yau gaku a rana''ya fadi yana yiwa motar key tare da cillawa raliya gwalo
''wlh a inuwa ka ganmu,kuma duk qwaqwqwafinka ba zaka taba ganinmu a rana ba,ku sauka lafiya,sister am sorry,sai munyi waya''
''ban sani ba,idonki ya baki amsa''tave da maryam din lokacin da auka fito tana gaba ita na binta abaya,mirmuahin dai ta kuma yi har beuty points dinta suka loba
''Allah ya baki haquri,yau kam ai akan gwiwa kike sai lallabe''
''a'ah,akan haba nake''
amsar da ta bata ta sanya maryam tuntsirewa da dariya har itama raliyan ta dan murmusa don fushinta da maryam ba ya wani tasiri
suna isa gaban motar ta ganshi zaune,shi ya kawota kenan,raliya ta bude ta shiga yayin da maryam ta galla masa harar lokacin da suka hada ido,dariya ya tuntsure da ita yana kallon raliya da tayi kicin kicin
''kada kice komai,don babu ruwan nasiru,kinga kanwar nan''
''babu wani nan,waye baisan halinku maza ba,to wllahi bari kaji,idan ka sake ka yiwa aminiya ta kishiya ban yafe ba koda wace ce kuwa,ke kuma kici gaba da nema masa aire kinji ko solobiyo''ta fada harda dan kama kunnen raliyan
dariya abun nata ya basu
''ni don Allah sake min kunne,tunda kin gujemu dai ba shikenan ba''
''indai irin wannan gudun ne raliya am sorry to say....zanta gudunku har abada''ta dan ja da baya ta rue musu qofar tana murmushi sanna ta dan sara mata shigen yadda sojoji suke
''Allah ya huci zuciyar ranki shi dade,oya kai kuma kaja mini aminiya ta ahankali''
''oho dai abanza tinda yau gaku a rana''ya fadi yana yiwa motar key tare da cillawa raliya gwalo
''wlh a inuwa ka ganmu,kuma duk qwaqwqwafinka ba zaka taba ganinmu a rana ba,ku sauka lafiya,sister am sorry,sai munyi waya''
koda ta koma gidan cikin al'ajabi suke tattauna zqncan da mama,maman ta kuma yabwa qwarai da irin qaunar dake tsakanin maryam din da raliya,ta musu addu'ar Allah ya dorar har tsufansu
sai a san nan ne maryam ta samu sukunin yiwa maman zancan aikin da hajiya atika ta samar mata,shiru maman tayi kamar yadda maryamun tayi tana jirqn cewa maman,shudewar mintina kusan biyu kafin tace
''ke me kike gani game da aikin,tunda kinga azahjrin gaskiya zamanki babu aikin babu dadi,tunda kin riga kin saba,hakanan zai debe miki kewa,baya ga haka harkar makarantar hindatu wa zqi ci gaba da daukar nauyinta idan har kika daina?,amma ke me kike gani mene ra'ayinki?''
''aini mama banida wami zabi sai abunda kika ce''
sai a san nan ne maryam ta samu sukunin yiwa maman zancan aikin da hajiya atika ta samar mata,shiru maman tayi kamar yadda maryamun tayi tana jirqn cewa maman,shudewar mintina kusan biyu kafin tace
''ke me kike gani game da aikin,tunda kinga azahjrin gaskiya zamanki babu aikin babu dadi,tunda kin riga kin saba,hakanan zai debe miki kewa,baya ga haka harkar makarantar hindatu wa zqi ci gaba da daukar nauyinta idan har kika daina?,amma ke me kike gani mene ra'ayinki?''
''aini mama banida wami zabi sai abunda kika ce''
''kina da zabi mana maryamu zan tauye miki haqqinki ne?,amma dai abinda yafi kawai shine kici gaba da addu'a,Allah yayi miki zabi mafi alkhairi''
''ameen mama''
da haka suka saki maganar suka shiga kuma wani batun daban kuma,haka rayuwarsu take su uku suke yinta,su kashe su binne abinsu babu maiji,hakan ne ke qara haushinsu,cikin zukatan al'ummar gidan
''ameen mama''
da haka suka saki maganar suka shiga kuma wani batun daban kuma,haka rayuwarsu take su uku suke yinta,su kashe su binne abinsu babu maiji,hakan ne ke qara haushinsu,cikin zukatan al'ummar gidan
sati guda da maganarsu da haj atika amma har yau ta kasa yanke komai a kai,kwana bakwai daidai da azahar tana sharar tsakar gida ta jiyo sallamarta,cike da mamaki ta yi mata sannu da zuwa sannan tayi mata jagora zuwa dakinsu
ruwan sanyi na pure water da alalen da sukayi ta ajjiye mata sannan ta zauna suka gaisa
''baki da kirki maryamu''haj atika ta fada tana dubanta
murmushi tayi ta dan sunkuyar da kai
''kiyi haquri mama''
''tashi kike abunki da mamanki ma zanyi magana,ko abbanki yana nan?''
''eh,bari na dubo miki''ta fadi tana miqewa,
taci sa'a kuwa yana niyyan fita ta tadda shi,ta sanar da shi sannan ta zura mayafinta ta fita gidan maman fatima maqociyarsu
''baki da kirki maryamu''haj atika ta fada tana dubanta
murmushi tayi ta dan sunkuyar da kai
''kiyi haquri mama''
''tashi kike abunki da mamanki ma zanyi magana,ko abbanki yana nan?''
''eh,bari na dubo miki''ta fadi tana miqewa,
taci sa'a kuwa yana niyyan fita ta tadda shi,ta sanar da shi sannan ta zura mayafinta ta fita gidan maman fatima maqociyarsu
mintina talatin suna cikin hira isyaku ya shigo yana zumbure zumbure
''ke kije bana yana kiranki''ya juya ya fice abinsa,maman fatima tace
''oh ni Allah,Allah ya kyauta''
''hmmmm,ameen bari naje maman fati sai anjima''maryamu tayi mata sallama ta fice
''ke kije bana yana kiranki''ya juya ya fice abinsa,maman fatima tace
''oh ni Allah,Allah ya kyauta''
''hmmmm,ameen bari naje maman fati sai anjima''maryamu tayi mata sallama ta fice
bata tarad da haj atika ba,sai babanta da mama dake zaune
''baba gani''ya fada bayan ta samu guri gefe da su ta zauna
''maryam''
''na'am baba''
''ki shirya gobe idan Allah ya kaimu ki hada duka abunda kike da buqata hajiya zata zo zaki tafi gidan nan da kukayi magana da ita ta samar miki aiki''
cikin rashin fahimta ta dubeshi
''amma baba ni ina ganin koda zanyi aikin ma ai bani da buqatar tafiya da kaya na,tunda ba wani garin bane ko?''
''ke,bani son sakarcin banza,na riga da na gaya miki,ki hada kayanki,suna da buqatar zamanki ne a can gidan,yo idan kin zauna anan din me zaki tsinana min,illa inyita ganinki baqinciki na ci gaba da damu na?,kije kawai banason kuna sauran qorafi kinji ko?''
''baba gani''ya fada bayan ta samu guri gefe da su ta zauna
''maryam''
''na'am baba''
''ki shirya gobe idan Allah ya kaimu ki hada duka abunda kike da buqata hajiya zata zo zaki tafi gidan nan da kukayi magana da ita ta samar miki aiki''
cikin rashin fahimta ta dubeshi
''amma baba ni ina ganin koda zanyi aikin ma ai bani da buqatar tafiya da kaya na,tunda ba wani garin bane ko?''
''ke,bani son sakarcin banza,na riga da na gaya miki,ki hada kayanki,suna da buqatar zamanki ne a can gidan,yo idan kin zauna anan din me zaki tsinana min,illa inyita ganinki baqinciki na ci gaba da damu na?,kije kawai banason kuna sauran qorafi kinji ko?''
kai ta gyada hawaye na layi bisa kuncinta,wannan sam bai dadashi da qasa ba ya miqe ya fice abinsa,kai ta hada da gwiwa ta rushe da kuka,duk yadda taso daurewa zuciyarta ta kasa
''wai me yasa baba baya sona ne mama,me nayi masa?''ta tambaya cikin kuka
''kul maryam,kada na sake jin wannan mummunar maganar a bakinki,mahaifinki ya isa da ke,saboda haka nima bana buqatar wani qorafi kibi umarninshi kawai''
bata iya cewa konai ba face miqewa da tayi ta shige dakinsu zuciyarta na zafi tare da jin tsanar wannan sabon aikin,aikin da zai nisanta ta da mahaifiyarta,zai nisan tata da 'yar uwarta,mama binta tayi da kallo tana jin tausayin diyar tata sosai na sauka cikin zuciyarta,addu'a kawai take mata cikib ranta Allah ya yanke mata wahala,ya kawo lokacin da zata zauna ta huta cikin dakin mijinta
''wai me yasa baba baya sona ne mama,me nayi masa?''ta tambaya cikin kuka
''kul maryam,kada na sake jin wannan mummunar maganar a bakinki,mahaifinki ya isa da ke,saboda haka nima bana buqatar wani qorafi kibi umarninshi kawai''
bata iya cewa konai ba face miqewa da tayi ta shige dakinsu zuciyarta na zafi tare da jin tsanar wannan sabon aikin,aikin da zai nisanta ta da mahaifiyarta,zai nisan tata da 'yar uwarta,mama binta tayi da kallo tana jin tausayin diyar tata sosai na sauka cikin zuciyarta,addu'a kawai take mata cikib ranta Allah ya yanke mata wahala,ya kawo lokacin da zata zauna ta huta cikin dakin mijinta
jikinta duka a sanyaye take shirya kayanta cikin sabon dan trolly dinta mai kyau pink wato ruwan hoda,hindatu ce ta rufe mata sannan ta jawo mata shi cikin parlour don bata da kuzarin da zata iya janshi
tsaye tayi cikin falon ta kasa cewa maman nata komai,don hawaye ne fal cikin idanunta da suya da zuciyarta ke mata,ji take kamar ta bar gida kenan,tana jin tamkar ta bar mamanta kenan,sai maman ce tace
''kuje hindatu jiranta suke,Allah ya bada sa'a,abu guda zan fada miki,ki riqe mutuncinki a duk inda kike,ki tsarw ksnki maryam ki kuma ji tsoron Allah,don babu wani abu da zan iya yi miki a lahira,iya kacin amfani na a duniya ne wajen tunatar da ke bin hanyar Allah,ki riqe amsna ki zauna da kowa lafiya''
kuka ta saki ta fada jikin mama,sai da taci kukanta sannan a sabule ta fice hindatu tabi bayanta da akwatin
''kuje hindatu jiranta suke,Allah ya bada sa'a,abu guda zan fada miki,ki riqe mutuncinki a duk inda kike,ki tsarw ksnki maryam ki kuma ji tsoron Allah,don babu wani abu da zan iya yi miki a lahira,iya kacin amfani na a duniya ne wajen tunatar da ke bin hanyar Allah,ki riqe amsna ki zauna da kowa lafiya''
kuka ta saki ta fada jikin mama,sai da taci kukanta sannan a sabule ta fice hindatu tabi bayanta da akwatin
sam basu lura da su ba sai shewa suka ji,inna hadiza nw da binta har da tafawa kamar sa'annin juna
''haka dai za'a qare a boyi boyi''inji inna hadizar,hindatu na shirin maida mata martani maryam ta damqe hannunta ta jata suka fice ba tare da ta bata damar tsayawa sun taya yinsu ba
''haka dai za'a qare a boyi boyi''inji inna hadizar,hindatu na shirin maida mata martani maryam ta damqe hannunta ta jata suka fice ba tare da ta bata damar tsayawa sun taya yinsu ba
0 comments:
Post a Comment