shiru tayi cikin motar tana maida ajiyar zuciya,zugi take jo tana yi mata
har ga Allah da tana da iko ba zatayi aikinnan ba,sam bai kwanta mata ba ko kadan a rai
''maryam,kiyi haquri kinji,na fuskanci baki son aikin nan,amma ni mai sonki ce maryam,na yadda da tarbiyyarkk,ke yarinyace mai hankali da nitsuwa,idan da nasan zaki cutu a gidan wlh bazan gaba kaiki ba,ki kwantar da hankalinki na tabbatar zaki samu nutsuwa da jin dadi cikin gidan *haj hasiya*na da dadin mu'amala,insha Allahu ba zaki samu matsala ba,ki cire damuwa a ranki don Allah kinji maryamu''
ta sake sakin ajiyar zuciyar a bayyane ''to msma insha Allah''ita kanta tasan ta fada ne kawai amma Allah ne kadai yasan ranar daina damuwarta,bata taba rabiwa da maman nata ba sai yau
tafiyar mintina kimanin talatin suka iso unguwar,tun daga farkon unguwar zaka gane cewa ba qananan muta ne ke zaune cikinta ba,daga get din farko allo ne mai dan girma dauke da rubutu kamar haka
*welcome to millonier quaters*
sannu a hankali suke ratsa layukan,layuka ne tsararru tamkar a qasar waje,shuke shuke ne jere reras qofar kowanne gida,hakan sai ya yiwa layin ado ya zamo cike da furanni,layin ya burgeta sosai,duk,da uadda,zuciyarta ke mata babu dadi
qofar wani gida suka ja suka tsaya,dauke yake da madaukakiyar katanga da get mai tsawo da girma,horn tayi har kusan uku kafin wata qaramar qofa ta bude
kallo daya zaka masa ka tabbatar cewa qaqqarfan mutum ne,sanye cikin kaya riga da wando ruwan bula wanda ke alamta unifoarm ne a jikinsa
fuska a hade yake tambayarsu cikin karyayyen turancinsa na brooking
''wa kuke nema?''
haj atika ce ta amsa masa''gurin hajiya muka zo,ta san kuma da zuwan mu''ya sake tambayarta mene sunanta ta gaya mishi
bai sake cewa komai ba ya wangale mamakeken get din motarsu ta fada ciki
gurin parking ne wanda yake cike da motoci na alfarma a qalla guda goma,haj atika ta raba tata gefe kana suka fito,sunyi tafiya ta kusan minti biyar kafin su cimma dogon valcony din dake fuskantarsu wanda lullube yake da nau'in furanni kala kala masu qamshi da kyawun kaloli,qofa ce mai fadi cikin valcony din wanda suna shiga ta kaisu ga tafkeken falo wanda ya lamushe rukunin kujeru har set biyar saboda girmanshi
iya qawatuwa an qawata falon iya ganin mai kallo,saidai kawai na barwa mai karatu ya siffanta shi iya yadda zai iya,shiru falon yake sai qamshin freshner da ya gauraye falon da na a.c
.
tsit falon yake tamkar babu kowa cikin gidan,da ido suke kallon falon tare da yin sallama koda zasu samu wani a akusa ya amsa musu,saidai har yanzu babu motsin kowa
qofar dake hannun hagu suka ji an murda an bude,duk da 'yar tazarar dake tsakaninsu suna iya jiyo dariyar su,su biyu ne daya a gaba daya abaya
matashiya ce 'yar kimanin shekara ashirin da biyar sai wata agefenta wadda zata iya bata shekaru uku
basu kula da su maryam ba dake tsaye a tsakiyan katafaren falon ba har sai da suka zo daf da su,ta gaban ce mai kimanin shekaru ashirin da biyar din ce ta soma qare musu kallo,kallo ne na qurilla da saka tsarguwa,sai da ta gama tace
''mu je ko jidda na taka miki''ta fada tana kallonsu sama da qasa
har zasu gota haj atika tace
''ji mana''ba tare data dawo ba ta waiwayo tana jirqn me zasu ce
''don Allah ko zaki mana magana da haj bintu?''
cikin halin ko in kula tace''ku zauna ku jirayi fitowarta,may be yanzu zata fito''daga haka tayi gaba abinta tare da jan hannun wadda suke tafiyar tare,haj atika tace ''zauna maryam,bari na kira hajiyar''
maganar second uku fayi da ita ta kashe wayar,cikin minti biyar katafariyar qofar dake hannun dama ta bude,kyakkyawar mace ce 'yar kimanin shekara talatin amma a zahiri ta kai shekara hamsin da uku,kyawun jiki iya ado da kwalliya hade da tsafta ne suka wawashe ragowar shekarun suka boyesu
sanye take da swiss lace ruwan toka da adon orange,sai labcoat da ta dora fara tas a sama,takalmin qafarta hill ne shima fari ne qaf kamar ranar ta fara sashi,ta nade wuyanta da mayafi orange,fuskarta qunshe da yalwataccen murmushi
''sannu hajiya,maimakon ku shigo sai kuma ku zauna anan,ku taso don Allah''ta fada tana nuna masu qofar,gaba tayi suka bita abaya
abun mamaki sai gasu a wani gurin,guri ne mai kama da gurin shan iska,saidai dauke yake da tyles fari qal illa tsakiyar gurin da aka yiwa shafe din cycle aka cika shi da 'yan shuke shuke masu furanni dake fidda qamshi
qofa ce ta glass wanda na waje baya iya ganin na ciki bayan sun shiga ciki ta fahimci hakan,falo ne shima mai dauke da kujeru set biyu,gini ne sama da qasa wato mai bene,wanda matattakalar na acikin falon,tsarinshi abun sha'awa ne matuqa duk iya iya tsarinka sai ya burge ka,komai na cikin falon fari ne da milk,babu alamun qura ko dauda a tattare da shi sai kace yanzu aka bare komai aledarsa aka sanya
''bismillah''hajiya bintu tace musu tana shirin zama
''hajiya ga maryam na kawo miki,kuma bani da haufi a kanta,ke kanki,nasan zaki ji dadin aiki da maryam insha Allahu''haj atika ta fada bayan sun gama gaisawa
murmushi ta sake yi
''ina fatan haka,maryam sannu,ina fata hajiya ta gaya miki komai,girki ne kadai nake so ki dinga yiwa yaro na,kada kiji a ranki cewa wai aiki kika zo,kisa aranki taimako na kika zo yi,ki dauki kanki tamkar diyata,domin dama ina cike da kewar rashin yarinya mace,to ina ji a raina yau Allah ya bani,abu daya kawai nake buqata daga gareki,ki riqe amana don Allah,ki kula ki kuma yi taka tsantsan da abincin yarona,nasan kinsan komai game da abubuwan da ya faru a kanshi,ina son *abdallah* don Allah ki kula min da shi,na rasa babanshi bana son in rasa shi''ta qarashe maganar muryarta na bayyana raunin da zuciyarta tayi
duk sai taji tausayin su ya kamata,sai take jin ina ma ita ta samu wanna gatan,ina ma ita ke da gata har kamar haka
''insha Allahu haj na miki alqawarin ba zaki samu wani abu mai kama da cin amana ba daga gareni''
hakan data fada dukansu yayi masu dadi har haj bintan na murmusawa
''idan kika min haka kuwa maryam kin gama min komaibani da abinda,zan saka miki da shi,gyara guda daya,indai kina son insinga jinki kamar diyar tawa da gaske to kada ki sake kira na hajiya,ki kirani da *mami* kamar yadda *Abdallah na* ke kirana''
sai a lokacin maryam tayi murmushi karo na farko,harga Allah taji dadin karramawar da tayi mata''to,mami''
''yauwa,na gode,hajiya atika na gode qwarai da gaske,bazan iya manta wannan taimakon da kika yimin ba''
''babu komai haj bintu,ai abdallah kamar da yake a gurina,ni zan wuce,maryam.....''
hajiyan ta fada tana miqewa
har waiting parlour haj bintu ta taka mata sannan ta dawo,da murmuahin dai nata ta dubi maryam
''taso,maryam na nuna miki daki,don fita zanyi asibiti ina da C S har mutum uku,Allah ne ma yayi ba zamu samu sabani ba''ta gaya mata lokacin da tayo gaba ta bita abaya,wani labule mai kyawun tsari ta daga daga sashen hagu na falon,saiga gajeran corridor ya bayyana,dakuna uku ne a gun,ta tura daki na uku ya bude tace
''bismillah maryam,ga dakinki,ni,zan fita ki zauna ki huta kafin na dawo mu shirya yadda lamuran zasu kasance,yau dai babu aiki,don Abdallan ma baya gari,amma gobe zai dawo''
''to,mami sai kin dawo''ta fada cikin girmamawa
tabi dakin da kallo bayan mami ta fita,daki ne wadatacce shimfide da carfet mai taushi,sai gado cupboard ta jikin bando da madubi hadi da dressing chair,curtains,dukkaninsu pink da fari,cikin dakin akwai toilet,sai a c daura da window din jikin gado,gefan gadon ta ajjiye kayanta sannan ta shiga toilet din ta dauro alwala ta gabatar da sallar la'asar sannan ta soma jera kayanta cikin sif din
sama sama take jiyo sallama a falon,ta miqe ta maida hijab dinta tayo hanyar falon,budurwar da suka gani ce dazu tsaye tana kalle kalle
''sannu''maryam tace da ita don jawo hankalinta ta fuskanci ta fito
a dage ta kalleta
''ina mami?''
''ta fita aiki''
bata tanka mata ba ta juya ta fice itama maryam ta juya ta koma dakinta
*.
Har gefin magariba tana gyaran kayanta cikin drower din,dakin tsaf yake don haka bashi buqatar wani sabon gyaran na daban,ta maida qofofin cupboard din ta rufe dai dai lokacin ta jiyo kiran sallah sama sama saboda haka ta shige toilet
har isha'i tana kan abun sallarta,sai da ta bada faralin isha'in sannan ta nannade ta,zaman shirun ya mata yawa,sai kewar gida ta soma damunta,ta jawo wayarta ta lalubu number din hindatu ta kira,ba bata lokaci ta daga
''wayyo ya maryam dita,i missed you wlh wuni guda kawai''
ta gatsine fuska tamkar tana gabanta
''hmmmm,ba wani nan,kinyi missing din nawa kika gaza kira na sai da ni na nemeki''
''ayyah anty na,kinsan dai halin student,wayan,ba credit,am sorry ya maryam''
''shikenan,ya gidan ina mama ta''
''gata kusa da ni bari in bata''
kusan minti goma suna hira har aka fara mata warning kudinta sun kusa qarewa sannan sukayi sallama
toilet ta koma ta hada ruwan dumi tayi wanka ssnnan ta sauya doguwar rigarta mai kauri ta bacci ta dora hijab,tsna maida kayan da suka fadl daga cikin sif din ta jiyo sallaman mami
kan kujerar falon ta taddata a zaune tana cire agogon hannunta
''sannu da dawowa mami''cikin fara'ar nan dai tata tace
''yauwa maryama,ya baqunta,na barki ke daya ko,gurin nawa ba yara ni daya ce,gun haj laura kuma basu sanki ba bare ki shiga,sannan na manta ban nuna miki kitchen ba,ina fata yunwa bata takura ki ba''
murmushin itama tayi
''banjin yunwa ma mami''
''a'ah,ban yarda ba,bari na shirya na fito saiki dafa mana wani abun mai sauqi''
''to mami''
miqewa tayi tana nuna mata jakar da ta shigo da ita
''taimaka ki shigo min da brief case din nan''inji mamin ta haura sama maryam din ta bita a baya tana mamakin sauqin kai irin na mamin,tamkar ita ba wata bace,tsabar sanin qima irin ta dan adam
saman ma wata duniyar ce,komai nashi fari ne tun daga parlour har bedroom din mamin sai dan ratsin baqi kafan wanda bai taka kara ya karya ba
''hmmm,wani aikin sai likitoci''maryam ta fadi a zuciyarta
a falon qasan suka sake zama bayan sun kammala cin abincin daren
''gaskiya maryama my son zai morewa girkinki,haka kija iya abinci''a kunya ce tayi mata murmushi
cikin seriouse tone tace
''maryam kamar yadda na fadi miki dazu inason Abdallah so na haqiqa saboda shi kadai Allah ya mallakamin,cikin irin abinciccikan da Abdallah keso akwai irin namu na gargajiya,sannan yanason kayan snacks,aikinki zai kasance ne ranar weekend zaki dinga breakfast lunch da dinner,amma ragowan kwanakin breakfast ne kawai sai dinner,amma idan ke kina da buqatar ci zaki iya dafawa,saidai majority idan da wuri abdallah zai fita yana tafiya ne da breakfast dinshi
sannan anan zaki dinga shirya masa saman dining dina anan yake karyawa,ina fata nima za'a dinga sammin idan an dafa din''ta qarashe cikin sigar tsokana,dariya ta baiwa maryam
''me zai hana mami,ai sai kince ya isheki ma''
''to godiya nake,amma please maryam ki riqe min amana don Allah,na yarda da muta ne da dama akan Abdallah na amma sun ha'inceni,and pls feel free ke 'yar gida ce''
taji dadin bayanin mamin sosai har zuciyarta
kadan kadan mamin ke janta da hira bayan ta nuna mata store da kitchen din nasu,tace ta duba idan da abunda take buqata ta fada zuwa gobe da safe a siyo tunda da yamna take tunanin zuwan Abdallan
girgiza kai tayi
''komai yayi mami''
''to masha Allah,sai waj.....''
maganr tata ta katse sakamakon shigowar kira wayarta qirar iphone 7
murmusho maryam taga tayi har haskrn haqorin makkar ta ya bayyana
''dan halak,yaqi ambato''mami ta fada a bayyane tana shirin daga wayar
''salamu alaikum my son yanxu nake zancenka''
''mami na ke da wa?''
''sabuwan mai dafa abinci nayi maka abdallah''
sai da ya danyi jim
''anya mami ba za'a haqura haka ba?''
''kada ka damu son,insha Allahu wannan karon ba za'a samu matsala ba kaji,saboda hankali na ya kwanta da ita fiye da wadancan''
''tunda kin aminta mami shikenan''maryam dake tsaye sai ta danji ba dadi,duk da bata jin abinda yake fadi amma ta fuskanta kamar bai marhabin ne da zuwanta gidan
''insha Allahu ba damuwa,yanzun ma muna tare,muna tsara tarbarka gobe''
ya narkar da murya tamkar qaramun yaro
''ayyah mami na,abinda nakw ta fargabar gaya miki kenan tun dazun,aikin ne mami bai kammalu ba sai nan da kwana uku,kinga ya zama dole na qara kwana hudu kenan,bazai yiwu na taho na barsu ba gudun samun matsala,but....i promise mami na nan da kwana hudu a gida zan kwana kiji mamina,kuma pls kada ki saka damuwa cikin ranki''
ta danji a ranta kam don tana matuqar son Abdallah,amma sai ta share
''shikenan my son,Allah ya kaimu ya kuma kare min kai,ya bada sa'a,ka ci gaba da addu'a don Allah banda wasa''
''insha Allah mami na,i love you''
sai da tayi murmushi sannan tace
''i love you too my son''
daskarewa maryam ta kusa yi a tsaye,tana sake jinjina soyayyar dake tsakanin mami da dan nata
''kinji ma maryam,abdallah ya hutashsheki,sai nan da kwana hudu zai dawo''tace da maryam wadda ke duba,cikin wani dan qaramin oven dake gabanta wanda a badini duniyar tuna ni ta tafi,ta dan washe fuska
''ayyah,Allah ya nuba mana''
''ameen ameen,mujeko sai kiyi kwanciyarki abinki''
tare suka fito falon sai suka tadda ta a zaune saman kujera,budurwar dazu ce
''sannu mami''tace tana dan murmushi hade da kallon maryam da hakanan tun ganin farko taji ta tsone mata ido,ko don kyawun da take hangowa baro baro ne kwance a halittar maryam din oho?
''yauwa sannu zubaida''
''na shigo ai dazu baki nan sai waccar na gani''
mami ta juya tadan kalli maryam
''sunanta maryam....ya akayi zubaida?''
tadan murmusa
''zuwa nayi na amshi key na part din ya abdallah zansa a gyara,naji kamar gobe zai dawo ko?''
'' damuwa jeki abunki zubaida zan gyara miahin da kaina,tunda kinga waccan karon yayi fada''
''to zan gyara da kaina mami''
''kada ki damu zubaida,jeki abunki''raahin,kin dadi qarara ya bayyana a,fuskarta,amma sai ta juya zata fice
''am....zubaida''mami tayi kiranta
ta juyo a sanyaye,kana ta amsa
''ku tafi tare da maryam ta gaida nene,ma'aikaciyar da na daukarwa abdallah ce''
dif zubaida tayi a ciki ciki tace ''to''ta juya tqci gaba da tafiyarta
momy ta kalli maryam''kije ku gaisheta,abokiyar zama na ce tin kafin rasuwan abban abdallah''
to din itama tace kana tabi bayan zubaida da tuni ta fice daga falon nasu har ta isa filin dake cikin bangaren nasu
Tana biye da ita har suka shiga bangaren nasu,ginishi iri, na mamin ne babu maraba sai bambancin furnitures,mutum biyu ne zaune a falon kallo suke na wani american film a M B C ACTION wanda volume dinsa ya gauraye falon,zubaidaida batayi sallama ba sai maryam wadda siririyar muryarta bata wadatar da su sun jita ba,zubaida ta zauna kusa da matar wadda ta kusa ahekara hamsin da biyar tana fitar da numfashi daga bakinta
matar na juya ta dubeta
''um hmmm,ai nasani iska ce ke wahalar da mai kayan kara,ni nasan ba baki za'ayi ba,amma tunda ke kika g....''
''nene ga mai aiki nan mami tace na kawo miki ki ganta''ta katse babar tata don ta lura basu lura cewa ba ita daya ta shigo ba
lokaci daya suka zuba mata ido nenen da daya budurwar dake zaune kusa da ita har maryam din taji faduwar gaba
nenen ta maida kallonta ga zubaida
''mai aiki,kodai baki ji bane sosai''
cikin yamutsa fuska da alamun qosawa tace
''wadda zata dinga wa ya Abdallah girki da ta canza''
nenen ta dawo da kallonta gun maryam,ta dan tara qarfin gwiwarta tace
''ina yini''second kusan biyar kafin tace
''lafiya,Allah ya taimaka''
''ameen,sai da safenku''maryamun ta fada tana juyawa ta fice a bangare nasu,sai da ta fita sannan ta samu nutsuwa,don ta tabbata rakiyar idanu suka yi mata
.
cikin kwanaki ukun da tayi da mami ba qaramin dadin zama da ita taji ba,maca ce mai sauqin kai da iya mu'amala,haba haba da jama'a kowa nata ne,duk lokacin da suka zauna bata da labarin bawa maryam da ya wuce labarin abdallah
halayenshi
me yakeso mene baya so
quruciyarsa da shirmensa
tun maryam na daukar abun qarami har ta maida shi babba,lallai qauna ce mai girma tsakaninsu wanda Allah ne kawai yasan iyakarta
takanyi kuka aduk lokacin da mamin ta gama bata labarin mu'amalarta da Abdallah,tana dadewa kafin tayi bacci
me yasa ita bata ganin irin wannan qaunar musamman daga gurin abbanta?
me tayi masa?
wanne irin laifi tayi masa da yasa take samun rashin kulawa da raahin damuwa da ita daga abbanta?
saidai tana godiya ga Allah saboda uwa ta gari da ya bata mai jajircewa kan lamuranta
duk lokacin da zata fito zata tadda sashen nasu tas,ma'aikatan har sunzo sun gama aikinsu sun tafi,saboda mami gwanar tashi ce da wuei ta saba,sai aka hada biyu don itama maryam din haka saboda yanayin aikinta da tayi a abaya
ita daya take wuni bangaren nasu musamman idan mami ta fita,takanyi mamakin yadda gidan yake shiru kamar babu kowa a gidan,don ita dai tun ranar farko bata qara ganin wani ba,daga ita sai mami idan ta dawo,ta saba gidansu cike yake da jama'a,hayaniya kuwa sai dare ya tsala kake daina jinta,wannan yasa ta kuma maida hankalinta kan wayarta,research kan nai'ikan girke girke ya sake zama abokin ta wanda hakan yake sake bata damar qwarewa da samun experience duk kwanan duniya
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
ta fito kenan dauke da kayanta kala biyu sukayi kacibus da mamin hannunta riqe da maqullai
pakistan ne ajikinta riga da wando sai mayafinsa da ta yane kanta,yana daya daga jikin abinda ke boye shekarun mamin
tadan rusuna
''barka da warhaka mami,na zaci kin fita da muka gaisa dazu''
fuskarta a sake kamar kullum tace
''ban fita ba maryam,na tsaya gyaran dakunan Abdallah ne,kada ya dawo ya iaheni da mitar na bayar an gyara masa daki''
murmishi itama tayi
''ina fatan diya ta baki mance gobe ne aikinki zai fara ba''
gyada kai tayi
''ina sane mami''
''yayi kyau,kayan meye a hannunki''
ta kalli kayan sanna ta kalli mamin
''waje,zan dan fita ne na wanke su,bana son in tara kayan datti''
dariya tayi
''to wa yace miki bamu da mai wanki maryam?,ajjiyesu,zan baki num din mai mana wanki ki kirashi yazo ya karba,zan fito da nawa duka ya hada''
''to mami''
da la'asar mak wankin yace mata ya iso yana waiting parlour wato falon su na farko,ta jado kayan duka ta sameshi tsaye,yana amsa ya juya zai fice,kafin yakai ga fitar zubaida da zahariyya 'yar uwarta suka shigo,dukkaninsu dogayen riguna ne ajikinsu masu santsi,babu mayafin da suka yafa yana saqale ne agwiwar hannunsu sunyi fashion da shi,kwatan kwacin irin shigar da 'yan matan yanzu keyi espicially gurin dinner din biki(wadda a nasu ganin suke kiranta da iya ado ko wayewa,wanda sam ko kusa,tsabar rashin sanin ciwon kai ne,Allah ya yiki mai tsada amma kin maida kanki mai arha,jikin da sai mutim ya biya sadaki zai gani kin raba shi kyauta kowa yagani,tinda hatta dinkunan da akwyi na fityed gown babu shatin abinda bai bayyana ba,ki sani bakya burge mai ilimi sai jahili,duk wanda yace kina burgeshi da irin wannan shigar to qarya yake,jikinki ne yake burgeshi,aqalla nasan bazai bar qanwarsa tayi irin wanna shigar ba bare 'yarsa,kin fito sak hadisin da annabi ya siffanta irinsu wadanda yace ba zasu shiga aljanna ba baza su kuma ji qamshinta yace kaasiyatin Aariyatin masu tufafi ne amma tsirara suke,maa'ilaatin mumilaat,karkatattu ne masu kuma karkatar da hankalin maza,sadaqa rasulul kareem)
kuma da yaci moriyar ganga zai yada qoranta,tuni zahariyya wadda me qaras qaras da chewing gum ta bangajeshi,sannan ta kuma juyo cikin gatsali da qasqanci
''dalla can malami,saboda ysabar rainin wayo da rashin mutunci kana gani zaka bangaje mutane?''
''Allah ya baki haquri''yace da ita yana sake kauce mata
''wallahi next time idan ka sake ka sake kwatankwacin haka na ranste sai na maka qasqanci,kuma ka tsaya ka jada a namu wankin,aikin banza kawai,mtseew''taja wani matsiyacin tsaki ta wuce,zubaida ma nata tsakin ta ja tabi bayan 'yar uwarta ba tare da ko sun dubi maryam ba
suna tsaye sai ga zubaida ta dawo dauke da kayan ta watsa masa
''kuma kada su wuce gobe na gaya maka''tajuya tayi shigewarta ciki
maryam ce ta tayashi tsince kayan tana bashi haquri,don duk gaba daya jikinta yayi sanyi,bata son taga ana wulaqanci wa dan adam
murmushi yayi
''ai babu komai hajiya,idan da sabo ai mun riga mun saba,banda darajar hajiya mami ma da tuni cin abincinmu ya qare agidannann tun bayan rasuwar alhaji''
ita dai bata fasa bashi haqurin ba har ya fice,a tausaye ta bishi da ido,wato a fayuwa idan dai kai talaka ne to baka to da kai da banza duka daya ne?,mutane daidaiku ne suka san waye dan adam wanne matsayi yake da shi cikin halittun ubangiji
''aikin banza''
taji am fada cikin dan daga murya
da sauri ta waiwayo,zubaida ce tsaye,cikin valcony din benansu wanda aka yishi ta cikin waiting parlour din,dauke kanta tayi don tasan sarai da ita take,itakam idan wannan ne itama ba naqonta bane,idan da sabo ai ya zame mata ruwan shata tun tasowarta cikin sararin duniya bata huta da makamancin wadannan dabi'un ba cikin mutanen da take rayuwa da su
🎄🌲🎄🌲🎄
Washegari tun bakwai mami ta fita tace zata ta nada excuse wa patients dinta don gobe da jibi bazata samu fita ba saboda dawowar dan lelenta wanda ya koma england cheekup bayan dawowarsa ta farko ya sake komawa tun bayan poising din da yasha,mutum ne mai qulafucin aikinsa saboda haka ya jefi tsuntsu biyu da dutse guda,bincike suke kan wani dan nijria tun kafin ya kwanta jinyarsa ta poising din da yaci wanda ake zargi da safarar muggan qwayoyi,a dan binciken da ya fara ne ya gano ya gudu england saboda haka yana gama ganin likita ya kutsa binciken mai laifin,cikin taimakon Allah
gogewa jajircewa da qulaficin iya aiki ya gano shi,abunda ya tsaidashi ya sashi qara kwana uku shine kamo ragowan abokan sana'ar tasa guda uku wanda dukkaninsu ya samu nasarar daqumosu ya aunosu nijeria gaba daya dan su girbi abunda suka shuka
jirgin da zai sauka qarfe shida na maraice ne zai sauka da su don haka tun misalin sha biyu na rana maryam ta shiga kitchen,tun jiya ta gama redy din duka abunda zata biqata ciki kuwa harda qullin waina da sinasir,miyar agushi ta soma hadawa wadda ta wadat ta da busashen kifi hade tantaqwashi sannan ta hada lemuka kala uku
bayan sallar la'asar ta hau suya wainar da sinasir,ta kammala tana shirin wanke kwanukan da ta bata ta jiyo shigowar mami,kan ta fito ta taddata cikin kitchen din,da fara'ar dai tace
''gaskiya an tayarmin da yunwata,qamshin kawai yasa naqagu inji dandanon ya yake,tunfa daga waje maryam nake jiyo qamshin nan,kai yau kice Abdallah da santi kenan''
murmushi tayi
''ko na zubo miki mami?''
sai da takalli agohon dake daure atsintsiyar hannunta sannan
''a'ah,jirginsu Abdallah ya kusa sauka,sauri zanyi na shirya kafin a daukoshi,idan naci abincina kuma ai masha qorafin don me banyi jiranshi ba''
sallamar zubaida ta ratsa dodon kunnensu,mami ce ta amsa mata tana fadin qaraso kitchen din
.
Sallamar zubaida ce ta katse hirar tasu,mami ce ta amsa mata tace ta qaraso suna kitchen
taci ado ta cake cikin code lace dan ubansu wanda kana ganinshi kasan ba qananun kudi aka kashe wajen siyanshi ba
orange ne don haka ya haska baqar fatarta,tayi kyau sosai
''mami zamu je airphort taro ya Abdallah'' ta fada tana dan sunkui da kai
''Allah ya tsare sai kun dawo''
''ameen''
har ta juya mami tace
''am...zubaida,cikin ayarin su zai iso,ina ganin zaifi idn kika jira isowar a gida ko''kada kai tayi
''mota ta daban da tasu ai mami''
itama kan ta kada ''shikenan sai kun dawo''
.
sai da ta fice mami ta dawo da kallonta kan maryam
''zan haurq sama maryamu,idan kin kammala kema kije ki huta,sannunki,lallai kin aikatu''
''to mami,sai kin fito''ta fada cikin
murmushi
sai da ta sake biyawa ta dining din ta tabbatar komai yayi neat kana ta wuce dakinta
wanka tayi ta sauya kayanta zuwa atamfa dinkin riga da skert,gashinta kawai ta kama ta daureshi da qaramin ribbom saboda bata fiya sa babban ribbom ba kasancewar gashinta akwai tsaho da cika,gefan gadonta ta koma ta zauna bayan ta dauko man da zata sjaf ta soma sjafawar a kasalance tamkar mai tausayin kada ta jima fatar tata ciwo,haka kawai take jin wata kasala na saukar mata,ji take kamar ta lwanta abinta tayi bacci
bata kammala shafa man ba ta jiyo jiniya da hayaniyar motoci cikin harabar gidan,a hankali ta miqe ta isa bakin window din dakin ta dan yaye labulen,bata hango komai yadda ya kamata sai dan abunda ba'a rasa baba kasancewar window din ba dirwct harabar gidan yake kallo ba ya dan fi karlata wani sashen,na doguwar valcony dinsu,bugu da qaro jama'ar da auka shigo gidan cikin motocinsu wadanda dukansu yan rakiya ne
tawagar mutanen suka biyo ta cikin valcony din tanan ta hango zubaida wadda fuskarta ke a dinke tsaf da alamu cikin bacin rai take
.
yana tsakiyarsu,saidai dukansu ya fisu tsaho,tafiya yake cikin hanzari wanda alamu ke nuna cewa cikin kuzari da qoshin lafiya yake,fari ne sol wanda yasa ya zarta duka jama'ar dake tare da shi hasken fata,ko ba'a gaya mata ba ta fuskanci shine *abdallan mami*yawan jama'ar dake baibaye da shi ya sanya bata iya ganin fuskarshi saboda juya kanshi da yayi daya bangaren yana magana da wani saurayi da sauran jama'ar dake gefan nashi,abu uku zuwa hudu zata iya fadi a kanshi suit ne a jikinsa baqa wul mai sheqi wadda ko da bakasan kudin sutura ba kallo daya zaka mata ka tabbatar bata qananen kudade bace,sumar kanshi cike take kuma akwance luf ba tsayayya tamu irin ta hausawa ba,tafi kama data jaruman fina finan india ko larabawa,sai abunda ke saqale bayan kunnenshi guda daya wanda take gani gurin masu aikin tsaro,saidai wannan mai azabar kyau ne haka nan shima baqi ne
har suka kammala wucewa tana tsaye a gun,ita kanta batasan me ya tsaida ta din ba,sai daga bisani ta saki ajiyar zuciya hade da sakin labulen ta koma ciki ta lalubo hijabinta ta zura ta tayar da sallah don wasu guraren har sun idar
mami na tsaye qofar sashenta harde da hannayenta,duk yawan 'yan rakiyar abdallah bai hanata gano yaron nata ba,yayin da murmushin farin ciki yaqi bacewa fuskarta,daga hannun hagun falon kuma haj nene ce tsaye ita da zahariyya,idonsu tsaye car kan abdallah da zubaida wadda a yanzu ta bar bin bayanshi ta nufo inda suke tsaye
zahariyya ce ta tabe baki''don Allah nene dubeta,aikin banza shegiyar yarinya kawai mahaukaciya,wai har wani murna take da dawowar abdallah,don Allah ki barni da ita nene wallahi sai na gyara zamanta''
dafa kafadar zahariyyan tayi tana wani murmushi da na kasa fassara shi''um...um,kinga matsalarki kenan zahariyya gaggawa,idan bakiti wasa ba zaki bata mana plan,ki bar zubaida tayi yadda take so loka ci ne fa,kuma ke kanki kinsan nasan me nake yi ko?''
''to amma nene wallahi idan ba muyi taka tsantsan ba zata zame mana matsala''
''ita din ubanta,ni na haifeta ko ita ta haifeni,ki rabu da ita dai a yanzu,akwai lokaci kamar yadda na gaya miki''
''ko tazo kada ki mata maganar''nenen ta fada da sauri ganin zubaidar ta kusa cimmasu,dama mutanen dake falin ne suka hanata isowa da wuri
har isha'i maryam na jiyo sauran hayaniyar jama'a,don haka tana idar da sallar isha'in tayi rigingine abunta bisa gado,kusan goma saura tunanin mamanta ya fado mata,layin hindatu ta shiga nema saboda muryan maman da takeson ji,saidai tayi rashin sa'a is switched off,tsaki taja cikin rashin jin dadi a ranta tana raya cewa da ta dauki albashinta na farko cikin abunda zata yi harda siyawa maman ta waya sabuwa da kuma power bank mai aiki da hasken rana
tana tsaka da tunane tunanen nata taji an turo qofar dakin,mami ce wannan karon cikin kwalliyar atamfa super mai kalan blue maidan turuwa,abunka da fara sai tayi tas
''a'ah maryamu kwanciya akayi?''
''eh wallahi mami''ta amsa mata tana mai miqrwa daga kwanciyar da tayi tana maida daurin dankwalinta da ya zame
''a'ah,yi kwamciyarki abinki,ai kinsha aiki bsna tasheki ba''
tana saka slipper dinta dake bakin gado wanda mami ta bata take amfani da shi tsakanin edroom din zuwa parlour zuwa kitchen
''ba komai mami me kije buqata''
tana shirin amsa mata wayarta ta dau ringing
ta kara a kunnenta kai tsaye tace
''ya akayi abdallah''
cikin kwantar da murya yace
''mami yunwa nakeji,wayyo cikina mami''
dariya tayi
''kajimin shi don Allah,yaron goye ne kai,ka soma ci gani nan fitowa na shigo in taho da maryam ne don muci abincin tunda tare muke ci bayan baka''
''wace haka?''
''sabuwar mai girki kuma diyata''
''ayyah mami,ayyah....,nikam nasan kin rage ji da ni,banda haka daga dawowata mami yau inason musha hirarmu mu biyu kuma saiki yo gayya,nidai mami ki taho ke daya abinki kamar yadda muka saba ko inzo in taho dake''
''naji ya isa sarkin qorafi,kada ka shigo mana daki gani nan fitowa''
''thank you my mammy,ki sauri na qagu ki fito''
dariya ma ya bata,abdallah kenan,ko yaushe idan yana gabanta daukan kanshi yake kamar qaramin yaro
sai da ta dan kalli maryam ta gefan ido dake zaune gefan gado kanta a qasa tana fatan bata ji ba,ta riga da taji amma sai ta nuna kanar bata ji din ba saboda bata ji komai a ranta ba don itama batason ta shiga tsakanin wannan uwa da dan masu azabar shaquwa
''kinci abincinki e maryam''
''sai anjima,amma dai na shigo da shi''
''to shikenan ki kwanta ki huta,Allah ya huta gajiya,sai gobe idan Allah ya kaimu''
''to mami''
har ta kusa ficewa maryam din tace
''a cewa ya Abdallah ina masa barka da zuwa''
murmushi mamin ta saki don har cikin ranta taji dadin kulawar da maryam din ta nuna kan tsoka daya a miyanta
''zaiji insha Allah''
ta fice bayan ta ja mata qofar
kayanta ta cire ta sauya na bacci ta ja abincinta ta danci sannan ta kwanta baki daya
Qarfe takwas a kitchen tayi mata,tana cikin hade haden abinda zata tanadar musu na bre fast taji an shigo kitchen da sallama,ta waiwayo tana amsawa,mace ce wadda a qiyasce zata doshi shekaru hamsin,ta qaraso kusa da maryam,a ladabce maryam din ta gaidata,itama ta amsa mata cikin fara'a sannan ta dora da cewa,ni suna na uwani,ma'aikaciyar haj bintu ce,naje hutu na ne da take bani na shekara sai yau na dawo,kin ganni da wuri ko?,qauyen mu ba mai nisa bane shi yasa na fito dacwuri gasji Allah ysa na iso da wuri,ni daga qauyen sumaila nake''
murmushi maryam tayi jin cewa suna da maqwaftaka da qauyukansu
''sannu baaba,ni kuma suna na maryam sabuwar ma'aikaciyar data dauka ce saboda kula da girkin yaronta,ni a cikin gari nake saidai asakin mu yan qauyen gaya ne''
cikin jimami da 'yar fara'a tace''Allah sarki kice maqota ne mu,kingawadancan ma'aikatan hajiyan maha'inta ne,da su aka hada baki aka zubawa yaron nan guba wallahi,Allah ne yayi da sauran shan ruwansa a gaba,don Allah mero ki riqe amanar hajiya saboda mutuniyar kirki ce''
dariya baba uwani ta bata jin ta ambaceta da mero
''insha Allahu baba,Allah ya bamu ikon riqe amana''hira baban ta shiga zubawa maryam tana maida mata labarin yadda lamarin ya auku,taso ta karbi wani abin ta taya maryam din amma ta qiya don hirar ma kadai da take mata tana debe mata kewa da sata jin qwarin gwiwar aikin,da haka har ta kammala hada fried plaitain with sauce,ta dafa tea da ya wadatu da kayan qamshi lemon grass,kimba da ginger,ta jada da coconut flour pancakes saboda tea din
da yake ba mai yawa tayi ba duka kadan kadan ne daidaisu hakan ne ya bata damar kammalawa da wuri,ta zubawa bab uwani tana ci tana santi maryam na dariya,cikin haka mami ta shigo suka gaisa itama ta shiga dariyar santin da baaba uwani take bayan ta yi mata sannu da isowa,itama tayi mata barka da dawowar abdallah gida,mami tace ta bar baaba uwani ta gyara kitchen din ta wanke kwanukan don dama aikinta ne
cikin kitchen din ta barsu ta shiga dakinta ta gyarashi kana ta shige wanka bayan ta wadati shi da freshner,koda ta fito karyawa tayi ta kuma kwanciya,babu dadewa kuwa bacci ya sureta,sai sha biyu da rabi ta farka,agogo ta duba da hanzari ta shiga toilet ta wanke bakinta da fuskarta ta zura hijabinta dan zuwa saman mamin ta tambayeta a dora girkin rana
.
A qofar falon ta tsaya tayi knocking,daga can ciki taji mamin na tambayar wane,ta amsa mata sannan ta mata izinin ta shigo
A bedroom ta tarad da ita tana gyaran wadrob dinta
''sannu da aiki mami''
''yauwa maryam,sannu''
''mami ai da kin kirani na miki aikin''
''haba,kina bacci maryam ya zan tada ke''
''mami dama cewa nayi me za'a dora,naga rana tana ta yi''
tana zuba wasu kayan cikin sif din tace
''indai don ta Abdallah ne rabu da shi,don ko breal fast din ma baici ba,yana can yana yawon bacci,na yi da shi ua tashi ma ko laruawar ne yayi ya koma kinga yaqi,baqi sai ziwa suke masa sannu da dawowa amma kinga yaqi fitowa wai ramuwar bacci yake,saidai kawai ki dan dafa wani abun ba mai hawa ba saboda ke da baba uwani,ga baqi kuma don nasan yau ba za'a rasa baqi ba''
''to,mami''ta amsa tana shirin juyawa ta fice
''tsaya ki dan taya ni hira,ai yayi wuri a dora shi yanzu mamin ta dakatar da ita tana murmushi
kadan kadan suke hirar tasu har soma taya mamin aikin,tana shirya kayan ta miqa mata ita kuma ta zuba acikin drower din
Bata shirya kallon qofar dakin ba amma tilas tayi hakan,sallama akayi cikin wata murya mai cike da dadi da kwarjini wadda ke bayyana cikar haiba da halittar mamallakinta,second daya da yin sallamar qamshi ya baibaye dakin gadon mamin duk da cewa an dan turo qofar ne kadan an kuma boye a bayan qofar daga waje ba'a kai ga shigowa ba
hannun wanda ya bude qofar mai daure da agogon rolex ne kawai da barin jikinsa zaka hango
''mami na shigo ko na koma?''
''taya zance abdallah ka koma,bismallah qaraso''ta bashi amsa tana kallon qofar fuskarta qunshe da murmushi
ya qarasa turo qofar a hankali ya bada wata 'yar qara kadan,ya sako farar qafarsa mai dauke da zara zaran yatsuda maau qunshe da gargasa saman kowannensu,sanye yake da shadda fara qal babbar riga da 'yar ciki da wandonta,baqar hula ce zanna ahannunsa wanda da alama yana tafe ne yana mata kari bai qara sa ba ya iso dakin,fuska cike da qayataccen murmushi yake fadin
''nayi zaton kinyi fishi saboda banyi break ba''
''banyi fushi ba amma banji dadi ba''
''Allah ya bako yawan rai mami na,nima banso nayi missing daddadane n break fast ba,saboda na tabbata zaiyi dadi kamar abincin jiya''
''to ai ga mai girkin nan,sai ka mata sannu''ta fada tana nuna maryam wadda ke,daskare gu guda,kallo daya ta masa ta kasa yin na biyu,ba don komai ba sai wani kwarjini da cika ido da taga yayi mata,duk kyawun mami da take gani aahe nafila ne,wannan tabbas idan da mace ne saidai a hanata fita zuwa ko ina saboda fitar ba qaramin hadari bace tattare da ita da ssauran mutane
ya dan dubeta a fisge atill,kanta na duqe yace
''sannu fa''
ba tare da ta dago ba tace
''ina wuni?''
''lafiya''
ya amsa yana diban mami
''uhm,sai ina kuma''
yana ci gaba da karin hularsa yace
''masallaci mami,kin manta yau juma'a''
''haka ne,ka ci wani babban riga kamar gaske''
''kamar ranar daurin aure na ko mami''ya fada yana qarasawa bakin mirror yana dai daita hular a kanshi
''gafara can,mutumin da ya kasa fidda mace shike zancan ranar aurenshi,kaci gaba dai da zama a tuzurunka har a rasa mai aurenka''
murmushi ya fidda mai dan sauti ya dukin turaten mamin yana sake fesawa
''haba mami,ba irinmu kerasa macen aire ba ko shekara sittin sukayi a duniya,ki kwantar da hankalinki ina nan ina duba miki,kinsan sai na zaba na darje''
''garin ruwan ido kuma fa...''
da sauri ya tare ta
''wayyo mami....yi shiru don Allah,you will be suprise in sha Allah''
''hmmm,Allah yasa....maryam ina zuwa?''ta tambaheta ganin ta miqe
''zanje ne na dora girkin mami''
''abdallah maka lunch ne?''
''kai kuci kayanku kawai mami ni zan wuce gidan baffa mu gaisa''
''to yayi kyau,ka gaishe min su da kyau,muje maryam nima saukar zanyi,kada a shigo a yita nema na''
tare suka sauko dukansu abdallah na gaba,mami na bayansa maryam na binsu a baya
''banza a banza kawai,maras kunyar qarya,gidan da kike taqama da shi ina cewa 'yar karo ce ke''
surutan wata matashiya kenan lokacin da take shigowa falon,matashiya ce 'yar zamani wadda shigarta kadai ta isa nuna maka hakan,sanye take da fitted gown wadda tabi lafiyar jikinta,kanta daure da roses sai swagger dinta mai sarqa rataye a kafadarta,takalmin qafarta kuwa kai kace sama take shirin tabowa saboda tsininsa,fuskarta tasha fente fenten kwalliyar zamani
''a'ah salma,ke da wa kuma,hali zanen dutse''inji mami da ta tsaya tana kallonta
''ni da waccar agolan gidan taku mana,duk randa nazo gidan nan sai ta nemi raina min hankali,wallahi abdallah ka ja mata kunne ni ba sa'arta bace,ni na hana ka sota da zata dinga neman huce haushinta akaina,ina ruwan biri da gada,nafsi nafsi kawai''
kafadunshi ya daga yana ware hannayenshi
''ina ruwan abdallah ya taku,kina da baki kema fa''ya fada cikin ko in kula
ta yamutse fuska
''baka fa da kirki wani lokacin wallahi,watsamin to qasa a ido,mami kina jinsa ko''
murmushi tayi
''bismillahi Allah,ai kun fara kuma kenan''
ya dubi mama
''manta da ita mami,ni zan wuce masallaci''
''ni matsalata da kai waqanci wlh,ka sani fa sarai saboda kai na zo,shine zaka wani fita''ta fadi mishi tana kallonshi bayan ta zauna tana sabule cogen qafafunta
''sai na fasa sallar juma'a saboda sarauniyar matan duniya ta zo''ya fada yana yin gaba abinsa
''a'a,ni bance ba amma sai yaushe zaka dawo?''
''qarfe biyar,bit ban tabbas ina iya wuce hakan,idan zaki iya jira na fine''
''ina jira sai ka dawo''
ba tare da ya amsata ba ya qarasa ficewa
maryam na kichen take jiyo su
tunda ta shiga kitchen din bata fito ba sai da ta kammala girkin,lokacin da ya fito mami bata falon sai baquwar da taji an kira salma dake kwance dai dai kan three sitter,kanta ta dago tabi maryam da kallo,hada idon da sukayi bak sata dauke idonta ba
''sannu maryam,kada dai ace har kin kammala?''
inji mami dake saukowa daga saman bene
''eh na gama mami''ta amsa mata bayan ta tsagaita daha tafiyar da takeyi
''sannunki''ta amsa mata sannan ta juya don shigewa dakinta,tana jiyota tana tambayar mamin wace ita?saidai bata ji amsar da mamin ta bata ba
kiran da mamin ta yi mata ne ya sake fito da ita tun bayan shigarta dakin wanda wanka kawai taui ta saiya kayanta tayi salla,biyi taga 'yan matam sun zama,saidai iya wannan sanhe take da riga da wando wadanda suka bayuana surarta,inda Allah ya taqaita siririya ce sosai,
tadan dauke kanta zuwa sashen da mamin ke zaune
''gani mami''
''yauwa maryam,baki fito kinci abincinki ba,ga baqi yau agodan amma kin zauna a daki''
''mami na qoshi ne sai anjima''
''to zauna muyo hira,bana son kina zaman dakin nan ke daya,na gaya miki nafison ki dinga jin a ranki ke diya ta ce,wannan sunanta salma 'yar qanwata ce,waccan kuma sunanta saddiqa ita kuma 'yar yaya na ce,dukansu sunzo yoma abdallah sannu da zuwa''
''sannunku''ta fada cikin sassanyar muryarta
amsawar ganin dama suka mata tamkar wadanda aka tilasta,wanda hakan sam bai,mata dadi ba,har taji zamansun ma guri daya babu marching,don sam bata son wulaqanci,maca ce ita mai karamci shi yasa ako yaushe take tsammanin karamci daga gurin duk wanda zata mu'amaleshi
''am...mami da wai kitchen zan koma in dora abincin dare''
''baki gajiya maryam,a qa'ida ai kin gama girkinki na yau tunda sau biyu ne a rana ko''
kanta na aqasa tayi murmushi
''ba aikinta kenan ba,ki barta mana mami''inji saddiqa wadda ta dora qafa daya kan daya tana danne danne waya da bai wuce tana charting ne
''ba komai mami,ai ba wani qa'ida tsakanin mu,kuma ko ba haka bama ai kinga baqi aka yi,kuma aikin ya abdallah nake,tunda aikinsa nake kinga ba laifi na giwa wadanda suka zo gunshi abinci''
sosai ta burge mamin,tana son mutum mai sauqin kai,wanda ta fuskanci halin maryam ne
yayin da salma da,saddiqa suka dago kai suka kalleta,salma ta kasa shiru
''hmmmm,lallaikam,dadin abun ma biyanka ake ba''
sai abun ya bawa maryam din mamaki,to meye kuma hadin kaska da kifi,me haka kuma,me tayi mata,gaza bawa kanta amsa taui don ita dai yasan yau ta fara ganin salma,babu kuma abunda ya hadata da su balle tace ko ta mata wani abun ne
''salma,bana so fa irin wadan nan halayyar naki kin sani sarai ko''mami ta fada cikin dan hade gira
''yi haquri mami,nima ba wani abu nake nufi ba''
''jeki maryam ki hutar da kanki kiyi iya cikin abdallah kawai,shima din kiyi simple kada ki dauka da wuya''
''to''
ta gada sanna ta miqe ta shige kitchen dinmami ta nita da kallo,yanayin yarinyar na burgeta,sanyi sauqin kai da kawaic yakanah da danne abu cikin rai
.
jallop din couse couse ta hada mishi wadda ta wadata da carrot grean beans da piece,sai qoda da hanta a madadin nama,qamshin curry da tyme kadai ke tashi a ciki,yayi shar gwanin sha'awa,sannan ta hada banana apple anda strawberry juice,baaba uwani ta barwa gyaran gun ta wuce ta shirya dining,duk suna zube a falon kowacce da abinda take,ko saahen da 'yar uwarta ke zaune bai isheta kallo ba tamkar ba 'yan uwa ba,taji dadi da bata tadda mamin cikin falon ba don haka tana kammalawa ta ahige daki don ko alama bata buqatar zama acikinsu
mutum ce ita mai jan mutuncinta da gudun wulaqanci,
har magariba abdallah bai shigo ba hakanan basu fasa jiransa ba,ana kirayen kirayen sallar isha'i sannan salma fa fara hada tarkacenta tana yima mami sallama,bata kai ga fita ba abdallah ya shigo
sanye yake da jeans baqi da red din t.shirt hannayensa soke cikin aljihun wandonsa,kan sa yasha gyara sai qyalli yake sumar ta masa kyau sosai,ma'abocin qamshi ne hakan yasa turare ke masa rakiya duk ta inda zai gifta
duk yadda salma ta dauki zafi ganinshin da tayi sai taji sakayau tamkar ma bai mata komai ba,ta saki ajiyar zuciya wadda har sai da ta fito fili
''a'ah,yaushe ka shigo gidan?''inji mami
''b fore isha,na shigo nayi wanka ne zan fita sallar isha ne waccar yarinyar ta tsaidani zubaida take ko''
dukansu babu wadda bata shaqa ba,mami ce ma ta dan tare masu don ba dadi
''amma dai kasan ana jiranka tun dazu ko''
ya karuar da wuya yana kallon mami
''hakan ne yasa ma na shigo yanzu mami,don nasan kaskar nan na jirana''
kasa magana mamin tayi salma ko da tasan cewa da ita yake wani abu ya tokare mata wuya,tuni qwalla ta ciko mata ido,cikin rawar murya tace
''abdallah ni kake cewa kaska''
yayo wani dan qaramin murmushi irin na gefan bakin nan
''mene don ance miki kaska,ita ba halittar Allah bace kamar yadda kike''
kai ta girgiza tare da cewa
''na gode abdallah''
fuu ta zagayeshi ta wuce
mami ta soma kiranta tare da yunqurin binta,da sauri ya sha gaban mamin yana murmushi
''qyaleta don Allah mami,indai salma ce zata dawo''
harararshi ta danyi
''saboda ka saba mata haka ko,to saddiqa na daki saura itama ka wulaqanta tan kaji abdallah''yarfe hannu hayi cikin gajiyawa
''again mami?''kafin ta bashi amsa saiga saddiqar ta fito tana sakin hannu rigarta wanda ta tattareshi saboda alwalar data daura
bakinta a waahe take fadin
''oyo yo ya abdallah''hannu ya dan daga mata
''qanwa,yaushe ke kuma kika zo?''
murmushi ta saki hade da kashe ido daya cikin sigar son jan hankali
''cikin awa ta ta kusan hudu nake da zaman jiranka,kuma naga na kiraka nace maka zanzo''
ya dage kafadunshi
''nayi,tsammanin mami zaki gaida ko qanwata''
''ni gunka nazo''tace cikin salon shagwaba
''kuma kinga yanzun bani da time,time din mami na ne,jiya na dawo kinga baici ace mun gama hirar yaushe rabo ko,da zaki yi tafiyarki next time na baki appointment''yana murmushin mugunta qasan zuciyarsa ya fada,duk da yana jin yadda mami keta zungurinshi amma sai yayi kamar baiji ba
saddiqa gwanar girman kai da ganin ta isa ce,ki tayo tafi qarfin abdallah ya mata haka,son haka ta figi gyalenta wanda shi da babu duk daya
''abdallah....wai da ka fuskanci ina sonka shine ya baka damar takani yadda kaga dama,to wallahi aji na ya wuce nan''
murmushi ya kuma saki wanda ya qarawa kyansa kyau da kwarjini
''ni kaina nasan ke me aji ce''qufula ta sake yi don tuni ta fuskanci magana yake yaba mata a fakaice
''to indai don son da kake taqama ina maka ne daga yau na daina son naka sai me?''
''fine kin huta wallahi,kin kuma burge abdallah''wani zafi taji ranta na mata tuni ta durfafi fita ba tare da ta yima ko mamin sallama ba kamar yadda salma tayi
da sauri mamin tayi yunqurin binta,ya sake shan gabanta da hanzari
''pls mami ki qyaleta itama,wallahi hutu ta zabarwa kanta,hukuncinta yayi dai dai''
wata iriyar harara ta maka mishi
''matsa min abdallah agun tun ban sabar maka ba''
baice uffan ba ya janye gefe ya bata hanya,sai yayi komawarsa saman dining yayi zaune abinshi yana kallonsu
tana cimmata sai ta saki kuka,mamin tadan daddaki kafadarta a hankali
''meye kuma na kuka haka saddiqa da girmanki''ba don mamin bace da sai ta daka mata harara,amma sai ta toge tace
''haba mami,don kawai ana sonshi zai tsaya yana wulaqanta ni,yasan fa koni wace,su waye ke sona,to an daina sonshi din ma''
''ya isa daina kukan haka,ki barni da shi kinji''
da qyar ta lallaba saddiqan ta tafi,ta iso kan dining din inda abdallan ke zaune hankalinshi kwance tamkar babu abinda yayi,kujera ta ja ta zauna
''abdallah so kake kawai ka dauko min magana,kasan Allah akan haka zamu saba ni da kai?''
''ya salaaam....mami me kuma nayi da kike fadin wanna maganar mara dadi?''
''ka sani sarai abdallah yadda muke da yaran nan,ka san kuma irin magan ganun da ake tayi a kanka ko?,to ni na gaji gaskiya,ka zabi wadda kake so acikinsu kawai kowa ya huta abun ya isa haka''
''for god sake mami,ni babu wadda fa na taba cewa ina ina so duk cikinsu,yanzu mami anan kinga matar aure,kinga wadda ta cancanci zama surukarki matar danki qwaya daya abdallah,ni ban gani ba mami kuma kema na san baki gani ba''
ajiyar zuciya tayi don ta sani gaskiya abdallan ya fada
''amma wulaqancin bai da amfani abdallah,gwara arabu cikin mutunci da salama''
''mami ai bani na kawosu ba,kuma ni ba wulaqanci na musu ba,zuciya sukayi suka tafi''
murmushi tayi cikin zuciyarta,idan banda abun abdallah ai kora da hali ka musu,tace cikin zuciyarta
''tunda kace duka basu maka abida fa?,itadai nutsatstsiya ce ai ko''
yadan yatsine fuska
''ai nutsuwa kam akwaita,amma ba kamun kai,itama ina tabbatar miki mami gobe ko jibi zaki ganta da uban tana tana sum sum sum,marabarsu kadan ce ai''
''abdallah
abdallah,Allah ya shirya min kai''
''ameen mami na''
takaici ne ya rufeshi jin sallamar zubaida,ta qaraso tana wani satar kallonshi
''mami barka da dare''
''yauwa zubaida''filet ya zara ya bude warmers ya zuba abincin ya haura saman mamin abinsa
zubaidan binshi tayi da kallo yayin da ami ta dafe goshinta
abdallah na bata damuwa da yawa kan yaran mutane
''ya akayi zubaida?''
maganar mamin ce ta janyo hankalinta daga kallon saman inda abdallan ya haye ya barta
''bab....ba komai mami,cewa nayi dama sai da safe''tace cikin in ina
''Allah y bamu alkhairi,ki gaida nene yau duka bamu hadu ba,insha Allahu zan shigo gobe''
''zasu ji''ta fice daga bangaren cike da takaici
a kwance ta tadda ahi saman three sityer wanda saboda tsahonsa kansa na daya hannun kujerar qafafun na daya hannun har sun zarta sosai
yasan qorafi zata yi don haka yayi saurin riga ta
''nidai,mami banji dadin dawowar nan tawa ba sam,duka yaran nan sun hanani sakewa,gaskiya daga yanzu kada wadda ta sake shigowa indai ina nan har sai na fita kawai''
''to uba na''
dariya yake ciki ciki don yasan tunda ta fadi haka ya quleta ne kuma ba zata sake cewa komai ba
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
a fusace huwaila ta fito daga dakin nata,kai tsaye qofar dakin inna hadiza ta durfafa,a fusace ta saka hannunta ta yaye labulen tana fadin
''fito hadiza,wallahi na gaji na wannan iskancin da ake min cikin gidan nan ni da yara na''
inna hadiza dake kwance kan kujerarta da daurin qirji ta miqe ta soma qoqarin zama tare da jawo dankwalinta tana fagamniyar qulle danqararren kanta tare da fadin
''ai ni na girmewa fitowa saidai ashigo a sameni''
ba tayi wata wata na ta gado falon wanda saura ladan ta take qafar binta dake kwance saqe saqe,tayi saurin janye qafar tata tare da fadin
''Allah ya isa na wallahi''saidai bata ji ba kasancewar cikin masifa take da hayagaga
''hadiza,ki jawa diyarki
binta kunne,iskancin da take cikin gidan nan ya soma isata,haka kawai sai ta kama lubabatu ta dinga jibga,babu dama ta dauki aron wani abu nata''
''ahaf,kince haka kawai sannan kin dawo kin warware maganarki kince tana daukan aron abun ta,to ke da ita ku bude kunnuwanku da kyau,indai lubabatu bata daina daukar aron kayan binta bazan hana binta jibgarta ba,wutsiyar raqumi ai tayi nesa da qasa,mu yanzu cikin gidan nan babu sa'an mu don arziqi ba qarya bane''
kallon tara saura huwaila tayi mata,kana ta saki guda
''aikin banza....hara ra aduhu,arziqin nan fa da kike ta taqama da shi a sa hannuna ya samu,amma da yake butulu ce ke had kina da bakin goranta min,baya ga butulcin da kullum kwanan duniya kike min na hanani morar duka wani abu da jamila ta kawo cikin gidan nan,to bari kiji wallahi ki bini a hankali,don wallahi duk abinda kike taqamar da shi a yau idan naso sai na warware miki zarenki tas ta yadda baki isa ki maidashi ba''
hindatu dake parlour tana yiwa mama tsifa ta dubeta
''mama...kunnenki yana jiyo miki abinda nake ji kuwa?''
duk da cewa,zamcan ya duketa amma sai tace
''ina ruwanki hindatu?manzan Allah yace yana daga cikin kyawun musulincin mutum ya bar abinda babu ruwansa''gilma na cin hindatu amma dole haka ta ja bakinta tayi shiru tana addu'ar Allah ya kawo mata ya maryam,kai qila ma sai ta kira ta ayau din cikas din kawai mama da zata hanata
sai kuwa inna hadiza ta hauro itama huwailan dake kusa ta bi mata,sai fada ua zama hudu,binta nayi da lubabatu,huwaila nayi da hadiza ,mama ta yunqura zata fita bada haquri hindatu ta tareta tace wallahi mama babu inda zaki,lokacin da suke 'yar dadin babu wanda auka dauka abanza ieinki saboda haka yanzun ma ba ruwanki,su kashe kansu''a haka malam mamuda ua sjigo ya tadda gidan nasa
zancan ya bibiya amma daga qarshe sai ya goyawa inna hadiza baya,ko dama can itace mowar,balle yanzu da jamila ke satowa tana kawowa uwarta ita kuma take yagar masa,bayan sun shige daki ba qaramin ciwo abun ya yiwa huwaila ba,ta cizi yatsa yafi sau ashirin,lubabatu dake tsaye tana taya uwar tata takaici tace
''wallahi huwaila duk ke kika ja mana tun asali,da tuni nice kan matsayin jamila kika tsaya gina wasu kika qi gina kanki,ai da arziqi,a garin wasu gwara a garinku a garinku ma aunguwarku a unguwarma agidanku a gidanku ma adakinku''
''duk banga haka na lubabatu sai yanzu,nayi dana sani wallahi yafk a qirga,tsinanniyar mata ta kuma samun power a gida?''
''ato,shawara dai ta rage ga mai shiga rijiya,saiki zauna ki tuna bunyi''
kamar tayi mata allura ta figo mayafinta dake ajjiye saman qofar falon ta tace
''kinga zauna ki jiremin daki na,ba'a bori da sanyin jiki,bari naje gidan talatuwa''
saman tabarmar dakin ta zube tana fadin
''sai kin dawo''cikin zuciyarta tana addu'ar Allah yasa adace,tuni ta fara hango kanta a irin daular da jamila ke ciki,tana yin son ranta wanda tuni an maida jabir wani sususu,aure dai an yishi amma amma fa na cin abinci da cin kayan dadi da dibar kudi
*.
sama sama hadarin ke hadowa yana bajewa tun daren jiya,hakan ne ya sanya har safiyar yau garin yake da lullumi,lullube sama take da hadari mai duhu saidai sanyi sanyi yake bayarwa har yau ruwan bai kai ga sauka ba,qarfe goma ta kammala komai,wankanta tayi ta shirya cikin pskistan riga da wando daya daya daga cikin tsarabar da raliya tayi mata ta south africa,orange ne wanda aka yiwa adon dutsina dark blue daga gaban rigar da qafar wandon
mayafinshi shara shara ne amma yana da dan girma shi ta saka ta yane kanta da shi,tun baiwai yau mami ta fita saboda ta cinye hutunta na kwanaki ukun saboda haka bangaren babu kowa sai ita daya,kusan tunda tazo gidan bata fita ko ina ba saboda hala tayo sha'awar dan zagaya wa,wayarta na hannunta ta saka flat shoes ta fito
iya girma gidan yana da shi,ba ma wannan ba yanayin ginin ya burge maryam,bugu da qari yanayin da gafin yake ya qarawa maryam nishadi,lokaci gida hadarin ya yaso garin yayi duhu sosai,cikin qanqanin lokaci iska ta taso ruwa ya kece
da sauri sauri take nufar hanyar sashen nasu don bata son ruwan ya tabata,su uku me ysaye a waiting parlour din,nene zahariyya sai wani matashi da ya bawa qofa baya yana fuskantar nene,shigowar tata taji sunyi dif a maimakon sauti sautin maganar da take iya ji duk da cewa baka iya tantance abunda suke fadin,binta sukayi duka su biyun da kallo wanda hakan ya ja hankalin saurayin ya juya shima don ganin abunda suke kallon
har cikin jikinta take jin kallon nasu hade da faduwar gaba,hakanan take jin wani tsarguwa duk lokacin da suka bita da irin wannan kallon,saida ta shige sannan suka dauke idonsu
''nene,wace wannan?''ya tambayeta idonsa cikin nata cikin son jin amsa
sai da ta kuma tsuke fuskarta kafin ta amsa masa
''yar aikin da bintu ta sakewa abdullahi ce,bana buqatar kuma kace komai,idan ma wani abu kake shirin sawa zuciyarka kayi gaggawar cireshi,don wannan karon babu gudu babu ja da baya sai mun cika burin mu,a shirye nake da kawar da duk wani abu da zai kawo wa plan din mu cikas,kuma ina fatan haka ne cikin zuciyarku''
zahariyya ta tauna chewing gum dinta ya bada sautin qas qaqass
''nifa nene na fiki son cikar burin nan,sabodda haka har abunda ma ke ba zaki iya ba ni tsaf zan aikata shi''
''to balle kuma ni da nake namiji,ina da burika da dama...saidai fa...gaskiya naji yarinyar cikin jini na,tana da fitinannen kyau,any way zan ajiiyeta a side har sai bayan kammaluwar plan din mu''
''ato ya dai fi maka alkhairi''cewar nene tana buda hanci
garam taji taci karo da wani abu wanda tsabar sauri da rudewa yasa bata gane ko meye ba,ga duhu da ya mamaye falon kasan cewar duk wani qwan lantarki ta kasheshi lokacin da zata fita din
tsoro yaso kamata da tabi inuwar abun da kallo dogo ne wanda duk tsawonta ya kereta,yana kuma tsaye qiqam bai ko motsa ba
gabanta yayi mummunar faduwa,bata sake rudewa ba sai da taji muryarsa na fadin
''wannan wanne irin shshanci ne haka da hauka,kina tafiya kamar mai tabin qwaqwalwa,yanzun kuma da kinji min ciwo fa''
haushi maganar ta bata,wato ita ce ma mahaukaciyar?,shi da yake namiji baiji mata ciwo ba sai ita ce,zata ji masa?ita fa bata son rainin hankali shi ya sanya har yau bata bari su hada gu da shi,don ta fuskanci ya raina ajawalin mata saboda yaga yadda suke masa rushing
cikin dan daga murya yace
''kin wani tsaya kamar wata doluwa,ina breakfast din mu yake?''
''tun dazu na dora saman dining ai''
''ok it means ni zan sarving da kaina kenan,haka kika ga mami na na yimin''
kamar tace mishi to ai ni ba mamin ka bace,sai kuma taga bai dace ba,don tana kallonta ne tamkar mamanta
''comone dallah...dole ki dinga showing caring like my mami,babu buqatar nana ta miki aikinki,duk da cewa u can't replace my mami ko da digo daya cikin kaso dari ne,idan kuma ba zaki iya ba the door is opened''
bata ce masa komai ba ta zagayeshi ta wuce bayan ta kunna qwayayen lantarkin din dake falon,ta riga shi isa dining din don haka ta soma hada mishi tea don kafin ta kammala zuba mishi komai zafin ya dan sarara
kujera ya ja ya zauna daidai lokacin da wayarshi ta soma ringing
tamkar wani mace haka yake amsa waya,ba hayaniya ba daga murya
''shi don ubanshi bai san kai wane ba da,zai hanaka shigowa?,to ya bari mintina biyar su cika ya gani,idan ka ahigo ka sameni gefan mami''abinda kawai taji yace kenan ya kife wayan saman table,fuska a murtuke ya ja kofin shayin ya kai bakinsa,tana ahirin dakatar da shi amma tuni ya kai bakinsa,ai kuwa babu shiri ya dawo dana bakinsa ya fesar
''ke wacce iriyan muguwa ce don Allah,haka ake bawa mjtum tea da azabar zafi kamar za'a dafa mishi baki?''
muryarta a narke tace
''ayyah,don Allah kayi haquri,ina shirin dakatar da kai naga har har ka sha''
''mtswee...you are verru stupid''ya fada sannan cikin hanzari ya dauki wayarshi dake bisa teburin ya fara danne danne
''hello abdallah,lokacin aiki ne fa ina tare da patients''muryar mami kenan
''mami yarinyar nan aiki aka kawota ta min ko kisa?''a razane maryam ta dago ta kalleshi,sai kuma ta maida kqnta qasa ta sadda shi,tini oily eyes dinta suka qara sheqi ssakamakon qwallar da ta soma dan taruwa mata
cikin faduwar gaba mamin tace
''me ya faru abdallah?''
''mami zata kasheni da ruwan zafi,tea mai azabar zafi mami ta bani zai qona ni''
ajiyar zuciya ta saki
''oh my god abdallah,kasan yadda ka bani tsoro kuwa?,just ruwan zafi kawai ahine kake wa haka,sau nawa kana shan tea ba tare da ka fifita shi ba,sannan nasan maryam bazata taba baka tea da zafi tana sane ba''
''gaskiya mami bata san aikinta sam''
''enought abdallah....bani maryam din''
qyashin bata wayarshi yake,sai ya saka handsfree kawai ya dan tura ta gabanta kadan
''maryam,ya akayi''cikin rawar murya tace
''wallahi mami ba da niyya bane kaw....''
''manta da abdallah kinji,kici gaba da aikinki,but ki kula da shi kinga bani nan,hakanan sai kinyi haquri da tabarar abdallah don na....''
cikin hanzari ya dawo da wayar gabanshi bayan ya kashe handsfree din yana cewa
''omg mami''
batasan me tace masa ba ta dai ji yace
''ok bye take care''
daga bakin falon ake sallama,bai dubi gun ba yace
''comone guy,idan zaka shigo ka shigo duk ka cikawa mutane kunne da sallama''
matashi ne kusan sa'a,ne ga abdallah
''kaifa baka da mutunci wallahi''
''kai shine da kai ai''
dariya ya saki bayan ya iso ya bashi hannu suka cafke,kujera daua ya ja ya zauna yana leqen flate din dake gaban abdallan
''kai mutumina,irin wannan liyafa haka,rabona ne kawai ya rantse shi yasa na qaraso kenan,da har nayi fushi nace bazan shigo ba''
''kanka ake ji sarkin kwadayi,yi sarving dinshi''yace da maryama wadda ke goge gun da abincin ya taba
sam bai kula da ita ba sai da abdallan yayi magana
''ina kwana''tace masa idonta na kan flaye din da take zuba masa hadin salad
fuakarsa dauke da mayalwacin murmushi ya amsa
''lafiya lau 'yammata ya gida?''
''lafiya''tace masa ataqaice don ta qagu ta kammala ta bar gun,tun dagowar farko ta lura da yadda yake faman kallonta
tana sauka daga stares din dining atea din taji yana tambayar abdallah
''fatabarakallahu ahsanul khaliqin,abokina wanna fa,cikin family dinku take?''
a qufule abdallan yace''dan iska ban sani ba,kaga wannan tayi kamar da 'yar dangin mu ne,dan rainin hankali?''
''pls guy yimin bayani don Allah''
sai da ya gama shan qamshinsa kafin yace
''cook dina ce,mami ce ta kawota''
har wani dan zullo hisham yayi
''wow,gaskiya ta qeru wallahi ba qarya,kai....man ba cook mami ta kawo maka ba,matar aure ce wallahi wannan''
abincin bakinsa ya tofar bayan ya dalla masa harar kamar zai cinye shi
''allah ua,isa tsakanin mu kawai hisham,wanna ai cin fuska ne,house girl fa,ni abdallah,i think ka manta waye abdallah ne ko,ya kamata kayo gaggawar tunawa,har yau ba'a qera matar abdallah ba,ni,mai ysada ne don,haka mace mai tsada ce matar abdallah,ban tsammanin ma zanyi aure cikin jinsin hausa fulani,sai na shiga cikin larabawa,i hope ka fahimceni?''
dariya hisham ya qyalqyale da ita kafin yace
''nasan waye abdallah,d expensive man,amma ina tsammanin man ka makance ko?,bana zato ko cikin larabawa kowa ke da irin halittar babe din nan''
''kaga malam ni ba ganewa nake ba,u know ni ba irinka bane mayan mata,kai da ka gano,sai kaje ka qarata ai ko''
''is ok...is ok,ni na gani to ina so''
cikin i dont care yace
''ok,ba laifi,amma daga ranar ka cire abdallah daga list din abokanka''
''why?saboda me ?''
goge hannunshi da tissue kana ya tire kujerar da yake kai ya miqe yana duba agogon hannunshi
''coz babu mai zubda min class,kaga nifa ina da wani aiki,ina da bincike cikin unguwar tudun maliki,so bana buqatar securities su rakani saboda is screet,idan ka gama zub da mutuncin naka ka fito mu wuce''
daga haka yayi saukanshi,hisham na daroya ya miqe ya bishi
maryam dake saman kujera ta tabe baki
''lallai,Allah ya tsareni da da tarayya da ire irenku,kai din ma baka min ba bare abokanka,mai girman kai kawai,kudi ai ba sune mutunci ba''cikin zuciyarga take zanta hakan,ta jawo wayarta ta kira raliya don kada ma ta batawa kanta rai a banza
*
*assalamu alaikum wa rahmatullah,ina miqa godiya ta ga dukkanin mutanen da suka yimin ta'aziyya wadanda suka kira ni da wadanda suka turamin saqo sms da watsapp,na gode Allah ya saka da alkahiri ya bada lada,akwai wadanda suka turomin saqo ta watsapp ban musu reply ba su yimin afuwa wayar ce tayi misbehaving duka saqonnin sun goge na gode Allah ya bar zumunci*
can cikin uwar dakin suke a zaune su biyu rak,a haka idan ka kallesu sai kayi zaton maganar arziqi suke
''huwaila kenan,ai ni na dade da ganin baikenki,kin kima bani mamaki wallahi''uwani ta fada bayan ta dora qafarta daya kan daya daurin dankwalinta a goshi
''abunda ya faru ya riga ya faru uwale,yanzu meye abunyi mafita nazp nema,tunda na fiskanci abun nata ba na mutunci bane''
''abunyi kuwa akwaishi....''
''cewa nayi kawai mu koma gurin boka mai gayya ya warware aikin da yayi mana da farko,tunda ta inda aka hau ta nan ake sauka''ta gada cikin katse hanzarin uwale
bakinta ta kama tana kallonta
''ai kinji irin wautar taki,ina ke ina dosarsa,ko kin manta cewa yanzu hadiza sun fiki kudin da,zasu biyashi ya musu aiki nan take,ai hannu zamu sauya,ina da wani boka na da ya jima yana min aiki,amma fa sai kin shirya,kudadenki zaki fito da su ajjiyayyun nan''
''amma fa uwale na tarin auren lubabatu ne,na fiddo su kuma a kashe?''
''a aha,to zauna mana kiga idan zasu maganta miki,kin manta cewa idqn aiki yaui kyau wanda zata aura din mai arziqi,ne?,shi zai mata komai da komai ba damu bace ai''
baki huwailan ta washe''kuma fa hakane,kinga ke kin fini hangen nesa,to shikenan babu damuwa,yanzu kina ganin idan na raba su biyi rabi zai yi?''
tabe baki uwale tayi
''kinga malama,idan dqi kina son aiki gangariya ko fiddo da kudi kawai,wai tsoron me kike yi ne?ke da,zaki zama surukar mai arziqi,idan kuma kina ganin abar maganar shikenan sai na barki''
da sauri ta tareta
''a'ah,ba za'ayi haka baai,yanzu kina ganin yaushe zamu tafi?''
sai da ta dan nisa sannan tace
''jibi,jibi laraba kenan,ta bawa ranar samu ba,don mu samu dacewa''
dariya huwailan ta qyalqyale da ita
''gaskiya ne fa,kai Allah ya bar min ke qawata,bari na tashi na tafi kada su fuskanci wani abu,sai Allah ya kaimu kenan''
''to shikenan,Allah ya nuna mana''
tana gama ficewa uwale ta sheqe da dariya
''wawiya kawai,sai na gama tatseki tas,kuma naci halas tunda ba aikin Allah bane,idn banda ke cikakkiyar shashasha ce waye yaqi gidan hutu da jin dadi,nima fa 'yan matan nan gareni na hadashi mana da wata daga ciki,ai ba ke ladai ce mai son dadi ba''ta ja dogon ysaki kana ta miqe tana gyara daurin zaninta hadi da cewa
''ai ni kuma na samu sana'a har gida ina kwance kudi zasu dinga shigowa
ta waiwayo hannunta dauke da plate cike da tsiren tukunya wanda ya ji kayan hadi ta miqawa abdallah wanda ke tsaye qiqam a bayanta hannayensa harde bisa qirjinsa yana ta zuba mata surutu
''ungo,ai yanzu kam ka qyaleni na fita ko''
yasa fork guda biyj cikin plate din sannan yace
''kin gama wannan mami na,sauranki ci,don kin sani tare zamu ci''
girgiza kai tayi tana goge hannunta da doster din kitchen
''haba abdallah,me yasa wani lokaci kake da rigima kamar yaron goye?,kace tsiren tukunya kake so nace maryama tayi ma kace baka so nawa kake so,yanzun kuma kace sai na zauna munci tare,kaci naka ka ajjyemin nawa,idan na dawo sai naci,ina da patient da nace yau suzo su same ni''
''yau througout ba inda nake so ki fita,duk sun maida min ke kamar wata engine,weekend din ma ba za su barmin ke ki huta ba,kuma ma ni mami bazan iya ci ba idan babu ke''
''alright,ga maryama nan ta wakilceni sai kuci tare''ta fada tana daukan mauafinta dake saqale kan qofan kitchen din
ya kalli maryama ta wutsiyar ido wadda ke fasa qwai cikin bowl zata hada potatoes bolls sannan ya harareta kadan ya dauke idonshi ya maida kan mamin
''mami kina ragemin matsayi gunki,babu wanda zai iya replacing dinki a guna''
''to tunda ba zaka kaci da maryama ba sai na turo maka zubaida,ita ai na zaka qi ba tunda masoyiyarka ce ko''ta fada tana ficewa a kitchen din
maryam wadda kanta yake sunkuye tana kada qwan bata san lokacin da dariya ta ciyota ba don tuna dramer din da suka gama shi da zubaidan dazun da safe,bata snkara ba dariyar ta subuce ta fito
hannayeshi harde bisa qirjinshi as usual,a hankali ya dora kyawawan qwayar idanunsa gefen fuskarta wanda dimple dinta ya fito radau saboda motsawar fuskarta,sai taji duka ta sha jinin jikinta duk da ba kallonshi take ba,cikin second daya tayi qoqarin mai da fuskarta yadda take
hijabinta taji an damqa hade da jawota wanda har hakan ya haddasa fadowarta jikinshi,cikin zafin nama taji ya ja hijabin ya cireshi sannan yayi wurgi da shi,cike da azama tayi gaggawar barin jikinshi,a tsorace take kallonshi tare da takure jikinta guri daya,sanye take da fitted gown na atamfa wanda yabi lafiyar jikinta,a qa'ida dinkin ya mata kadan amma son da takewa atamfar yasa ta kasa bayar da ita,dalilin da yssa kenan duk lokacin da ta sakata hijabi take sawa
tuni oily eyes dinta suka qara sheqi kan wanda suke da shi a da sakamakon taruwar qwalla cikin idanunta,zuciyarta bugu take wanda a take jin ya wuce qa'ida,tama kasa hada ido da shi kamar yadda ta kasa motsawa,saboda idan tace zata motsa din tofa ko ina na jikinta zai motsa din ne
hucinsa taji a gabanta,a hankali ta dago da kanta don kallin abinda ke gabanta,tafin hannunshi ne mai dauke da zara zaran yatsu bude,tsakiyarshi kuma kunama ce qatuwa,saura kadan nunfashinta ya dauke,da sauri ta ja baya sannan ta daga kai ta kalli fuskarshi
gumi ne sosai yake hadawa yayin da idanunshi suka soma sauya kala bisa dukkan alamu ta hahharbeshi bama sau daya ba,a gigice ta koma gabanshin taci burki ganin yana tsaye qiqam yana kallon abunda ke hannun nashi tamkar ba wani abu bane mai cutarwa,hannunta ta saka ta tankwabe hannun nashi kunamar tayi tsalle ta sauka gefanshi,takalminshi ya sanya ya taketa
batasan ta kama hannunshi ba tana lalubar inda dafin yake ba sai da taji ya fisge hannun yana fadin
''mtswee,sakemin hannu dafi na shigar mutum sai ua masa illa kin tsaya shashanci''
hannunshi ya saka ya riqe inda yake tsammani iya nan dafin ya tsaya
zaune yake a falon tunda ya fito a kitchen din,da alsmu xafin harbin na damunshi sosai,duk da 'yan dabarun da yayi,duk sai ta shiga damuwa tana jin itace sila,ta rasa da me zata taimaka masa,duk sanda ta matso gun da yake sai ta kasa tabuka komai saboda kwarjinin da yake mata,qarshe sai tq koma kitchen din ta dauki wayarta ta kira mami ta sanar mata
sosai mamin ta rude tace ta gaya mishi ya taho asibiti yanzun lallai
kwance ta sameshi saman doguwar kujera
a darare ta matsa kusa da shi kadan cikin sassanyar muryarta
''mami tace ka sameta a asibitinta''
sam bai ji isowarta gun ba sai saukar siririyar muryarta
jin shiru ya sata sake maimaitawa
kusan minti uku kafin yace
''leave me alone pls,bani son naci tunda ni ba kurma bane,sannan bani son gulma,har kin kirata saboda tsaban gulma,bace min a gun''
bata damu ba tunda ta isar da saqon mamin dai,kitchen din ta koma ta fara soya patatoes bolls din duk da rabin hankalinta na ga abdallah wanda bata ji motsin tafiyarshi ba,dalili kenan da yasa taa kammala suyar ta sauke man ta leqo falon,yana kwance abinshi yadda ta barshi,sai 'yar nutsuwar da ta samu tayi qaura,waishi wane irin mutum ne da ciwo ke cin jikinshi amma bai damu ba
cikin dan qwarin gwiwar da ta tattara ta sake nufarshi da nufin tunassr da shi koda qila ya manta,saidai kafin ta qarasa wayarshi dake ruwan cikinshi ta dauki sassanyar ringing alamun shigowar kira
da alamun kasala ya dauki wayar ya duba mai kiran nasa ya amsa bayan ya maidata handsfree ya dorata saman cikin nasa
''abdallah yaya me na jika shiru?,ko maryama bata sanar maka saqona ba?''
cikin murya mai kama da ta mai bacci yace
''ta gayamin mami,kawai....''
''ya isa bana buqatar uziri,na baka minti talatin in ganka a office dina ok?''
''yes mami''ya fada daga bisani wayar ta katse
cikin sanda ta juya don komawa da baya tunda bai ganta ba
''dakata a nan''ya fada cikin kaurara murya,cak ta tsaya din yayin da shi kuma ya miqe a hankali
''sai ki fito amma zan sake maimata miki ni bani son shishshigi''daga haya ya juya yayi waje
motoci hudu ne baqaqe masu azabar kyau a jere,tun kafin ta qaraso taga abdallah tsaye jikin daya,xubaida ce ke fuskantarta bisa alamu magana suke,isowarta ne ya sanyata jin maganar qarshe da abdallah ke fadi
''nacinki kullum sawa yake ina dada tsanarki,bana son shishshigi bana son naci kuma bana son takura,ki tambayi nene tun asali ke ba type dina bace,bazan taba auran macen da bata yimin ba,ba ko wacce irin mace nake so ba,for now ya kamata ki gane hakan''
ya sanya hannunsa ya janue hannunta data tokareshi da shi ya bude bayan motar da kanshi
''naji abdallah,amma atleast dai a yanzun ka barni na raka ka asibitin bai cancanci ka tafi kai daya ba''
ko kallo bata isheshi ba don tuni ya gama maganarshi da ita
ya juya bayanshi yace da daya daga cikin security dinshi su rage biyu daga cikin motocin da biyu za'a tafi,ya rufe maganar da fadin
''ko kun manta muna bincike kan alhj haladu uba mai qusa,kuma banson yasan ina cikin garin nan,ku kiyaye''
''yes,sir''ya fada cikin girmamawa
kusan tare shi da zubaida idonsu yake kan maryama dake tsaye daura da su
''me kika tsaya kina wa mutane a gurin?''
cikin tattausan muryarta tace
''bansan wacce mota zan shiga ba ai''
''saikiyita sanqamewa anan har a tashi qiyama''ya fada yana shirin shigewa motar
''amma abdallah wannan ita kuma fa?''
wani kallon biyu babu ya mata cike da quluwa da tarin tambayoyin da nabu macen da isa ta masa su idan ba maminshi ba,tsaki ya ja mata sannan ya ja motarshi ya bame
sun gama reverse suna shirin ficewa maryama dake motar baya cikin gidan baya a takure saboda su uku ne maza biyu ita ta ukun taji an dakatar da su,abdallah ne ya fito ya qaraso har gaban motar,glass din duka motar yasa suka sauke ya qare musu kallo sannan yace da na gaban motar
''you are verry stupid lawal,oya getout ka koma baya,ke kuma ki fito ki dawo gaba saunar yarinya kin shige cikin maza kin wane qwame''
yana tsaye akayi hakan sannan ya bisu da tsaki ya kona tashi motar duka direbobin suka ja suka fice a gidan
*ABDULLAHI SPECIALIST HOSPITAL* shine abinda ke rubuce jikin wani makeken allo dake maqale a goshin ginin benan asibitin,wanda ko daga ina ka taho zaka gani saboda girman allon da rubutun da kuma tsahon benan,gini ne na alfarma tamkar ba asibiti ba,komai neat bisa tsafta tsari da kuma qwarewa,tun daga parking space ma'aikatan dake cikin harabar asibiti leburori da masu gadi suka soma tururuwar zuwa gaida abdallah,ga mamakin maryam hannu yake basu suna mudabaha cikin fara'a da sakin fuska
a haka suka ratsa cikin asibitin har zuwa sashen da office din mami na musamman yake
''wonderful,abdul dama kana nigeria?''suka ji an fada,wani matashi ne wanda ke nufosu yake fadar haka,sanye yake cikin qananun kaya wanda kallo daya zaka mishi kasan dan birni ne yasan gayu gayu ya sanshi,ba wani mugun kyau ne da shi ba amma iya adonshi ya bashi sunan kyakkyawa
da fara'a sukayi musabaha da abdallah
''idan ban manta ba shekaru biyar rabona da kai abdallah,yanzu laifin kudrat sai ya shafi mansur?''
dan qaramin murmushi ya saki kana yace cikin basarwa
''manta kawai friend ya bayan rabuwa?''sai alkhairi abdul,hala wannan ce madam din tamu?''
wani haushi ya kama abdallah don yasan ba kowa yake nufi ba sai maryam,sai ya zuba mata ido yaga yadda zata karbi maganar,babu abinda ya fuskanta tattare da ita don kanta a sunkuye yake jinta take kamar ta,zura a guje,ta takura matuqa cikin tafiyar nan
maida kallonshi yayi gun mansur
''kada ka sake fadi,cook dina ce,nazo ganin mami na ne ta shigo cikin sahun bodyguard''
murmushi mansur din yayi
''tofa wannan karon babu rabuwa abdul,bani adress dinka,zan sameka har gida,ina da magana da kai''
saboda yanayin aikinshi yasa bai bashi adress din gidan ba kai tsaye sai ya amshi phone num din mansur din yace zai nemeshi duk lokacin da zasu hadun,sukayi sallama kana suka nufi office din mami
duka a waje suka tsaya abdalla ne ya shiga ciki,fitowar mamin kenan daga toilet ta daura alwala
''ina maryam din''ta tambayeshi tana shimfida abun sallah
''suna waje''
''kana nufin har ita din''
''eh mana mami,har da ita''
''koma ka shigo min da ita''
cikin shagwaba yace
''yanzu mami a gabanta za'a min treatment din bayan da zafi kuma salon ta raina ni''
ita dai mami bata kulashi ba ta tayar da sallarta,tilas ya koma yace da lawal ya shigo da ita
*
0 comments:
Post a Comment