*_ina so nayi amfani da wannan 'yar damar wajen miqa jinjinar ban girma tare da ddu'o'i na fatan alkahairi wajen jajirtaccen dan kishin qasa da al'ummarsa BARRISTER ABDU BULAMA BAKARTI duk da cewa ban masa sanin ido da ido ba saidai tarin gaskiya amana taimakonsa da jajircewa kan qasarshi da garinsa ya kewaye kunnuwanmu,ina tare da duk wani jajirtacce mai gaskiya da amana dan kishin qasa da al'ummarsa,ubangiji yayi maka jagora ya tsare gabanka da bayanka,ya qara yawaita mana irinku cikin wannan alumma tamu dake fagamniya cikin wani irin hali,Allah yayi ruqo da hannayenka ya dorar da kai kan gaskiya har abada ameen suma ameen_*
Kanta bisa kafadar mamin tana rabza kuka tamkar wadda zasuyi rabuwar har *ABADA*,sai yanzu take kuma jin zugin rabuwa da mamin,tabbas sabo turken wawa ne,ita kata mamin zuciyarta a karye take ta kasa cewa komai,tanajin zatayi asarar diyarta ne guda zata rabu da ita,da qyar tayi,conrtolling kanta kafin,su tsaya suyi sallama
''naso a gudanar da komai da ni maryam,saidai ga yadda lamarin Allah ya kasance,date din bikinku da abdallah yazo daya,kinga ma ko a yanzun gidan ya fara cika da mutane wasu ma rabonsu da gidan nan an jima,kinga bazan iya tsallakesu ba na fita wani guri ba,amma nayi miki alqawarin bayan komai ya lafa wuni guda zanzo nayi a gidanki,hakanan zan dinga dubaki akai akai da yardar Allah''
kafin tace komai muryar abdallah ta ratso falon yana kiran mamin
''gani nan abdallah''
da azamarsa ya shigo hannunshi daya riqe da leda baqa mai kauri mai dauke da tambarin wani gurin saida kayan maza na ado,daya hannun kuma rafar yan dubu dubu ce dauri biyu,cikin shigar qana nan kaya yake,sai ya sake wani dan banzan kyau,farar fatar nan tayi luf da ita tamkar rainon larabawa,ko dama can yafi yanayi da su din sam sai ka rantse babu abinda ya hadashi da nijeria ,sai ya danyi turus yna dubansu
''qaraso mana abdallah,ya ake ciki?''
ya qaraso ya zauna gefanta
''mami duka guest house din guda biyu sunyi kadan,yanzun dai hisham ya samar ma ragowar mutanen hotel''
''yayi kyau hakan,sai ayi total abiya kudin kwanakin da zasuyi da abincin da zasu ci basai an yi jigilar kai musu daga nan ba''
'to''yace yana dora mata daurin kudaden kan cinyarta
''wannan fa na meye?''
''wani abokin aikina ne ya bani gudun mawarshi.......''yayi maganar yana qiqarin zaro wayarshi daga aljihu wadda keta faman ringing,ya kara a kunnenshi kana ya niqe tsaye yana fadin
''gani nan zuwa''yadan dubi nami yana yin gaba
''mami ina zuwa''
''uhm,yanzu haka abincin na da nasa aka kaima baka ciba,kadai kula da cikinka abdallah''
''ok mami''ya fada yana mata murmushi gami da qarasa ficewa a gurguje
nasiha ta mata sosai irin ta 'ya da mahaifiya kafin ta saka driver ya kaita zuwa gidan cikin kuka da kewar rabuwa da juna
ita ta ruqota suka dinga tsallake mutanen da suka fara cika gidan ta rakata har bakin motar sai da suka fice kana ta juya ta koma ciki
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Tun lokacin da idanunsu sukayi tozali da katin daurin auren abdallan hankalinsu yayi qololuwar tashi
''wacce irin hasara nuke shirin tafkawa haka,me kuke tunanin zai faru matuqar muka bar abdallah yayi auren nan,cikin watanni tara ko goma da yin surensu matarshi kan iya haihuwa,zata iya kasancewa ta haifi namiji ma,wannan shike nuna munyi bankwana da cikae burinmu?''
cewar nene dake faman safa da marwa,can cikin dakinsu zahariyya da zubaida kuwa kowa da abinda ya dameshi,zahariyya irin tunanin nene take,ba qaramin tashin hankali take ciki ba,burin da take da shi ya girme mata,yau idan abdallah yayi aure daidai yake da nisanta da dukiyar da suke kwadayin zareta daga hannun mamallakanta su su amfana da roman nata.
Afusace ta kalli zubaida dake zaune a cure can quryar gadon tana ta faman surfafa kuka wanda tunda labarin auren ya isa kunnenta itama ta hana kanta sukuni,kuka take tuquru kamar ba gobe,udanunta duka akumbure suke sun ui luhu luhu sosai daga jiya zuwa yau
''dalla malama ki wa mutane shiru,banza shashasha mara kishin kanta bare yan uwanta,yasan dake din ai ya zabi ya auri wata ba'a gabanshi kike amma ke kin quntata rayuwarki saboda shi''
dama a fusace take maganar zahariyyan sai ta qara tunzurata
''anqi ayi shirun bazanyi shiru ba,kece babbar shashsha da bakison so na haqiqa ba,babu ruwanki da sha'ani na ehe''sai kuwa zahariyyan tayo kanta a zqbure tana cewa
''ni kike gayawa haka,yau zan nuna miki baya ga shekaru da na fiki na fiki iya rashin mutunci''dambe ne ya sarqe tsakaninsu har nene dak samanta ta jiyo hayaniyarsu ta sauko,da qyar ta iya rabasu tana fadin
''sai ku kashe kanku ai,yan iskan yara marasa hankali da tumani,mazq ku raba abun fada cikin taron mutane''
sai sukayi tsit suna maida numfashi kowacce zuciya iya wuya,nene ta kalli zahariyya tace ''ki sameni a sama''ta juya ta fice ita kuma ta rufa mata baya,gware suka kusa yi da adnan wanda ke qoqarin hawa saman da gaggawa
''lafiyanka kuwa?''nenen ta tambayeshi bayan ta danja baya tana qare masa kallo
''muje sama nene akwai magana''ba tare da kowa ya sake tankawa ba suka duru saman gaba daya
''barin yarinyar gidan nan babban abun farinciki ne a garemu,mun riga da mun gama magana da malam na hayi ya tabbatar min da cewa zai mana aiki ammafa matuqar tana cikin gidan nan babu lallai yayi tasiri,tana da wani irin dafa'i a jikinta tun na kakanni da iyayen kakanninta,tunanin da nake yanzu kenan ta yadda zamu gabatar da aikinmu don auren abdallah ba qaramar barazana bace da faduwa garemu sai ga kuma kyakkyawan labarin da na jima banji irinsa ba,mun gode Allah faduwa tazo mana daidai da zama,yau din nan ba sai gobe ba zamu isa vurin,malam na hayi,kwana daya zamuyi a hanya zuwa jibi zamu dawo ya kama ranar daurin aure kenan ko ana gobe daurin aure?''
ta tambayi,adman,sai da ya danyi tunani kadan sannan yace
''ana gobe daurin aure ne''
''to yayi,kai adnan ka zauna muje da,zahariyya,ka shiga ayi duk wata hidima da kai,banason a fahimci komai,zan sanar da haj bintu qanwar ubanku ce ba lafiya zamuje dubota''
a nan suka gama dukkan wani shiri da tsarinsu kana suka shirya ta gayawa mami abinda ta shirya gaya matan,cikin tausayawa mami tace ayi mata sannu Allah ya qara sauqi,idan sun isa zata kira su sai ta bata ta mata sannu
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
tun daga qofar gidan ta soma ganin alamun cika,mutanene maza da mata keta kai kawo,a haka ma ba'afara gudanar da bikin ba kenan ina ga kuma an fara,gefe driver din ya samu yayi parking,akwai sabo tsakaninsu da mutunci da girmama juna duk dacewa ya kusa shekaru hamsin dattijon mutum ne mai hankali da nutsuwa,malam baaba direba ya kalleta bayan ya fito
''to malama meramu(haka yake kiranta sunan diyarahi ce ta fari data rasu),Allah ya sanya alkahairi yasa ayi a sa'a,ayita haquri da rayuwa,mu sai ranar daurin aure idan mun dawo daga na mai gida abdullahi''
kanta a sunkuye tace''na gode sosai baaba,Allah ya nuna mana''ya bude boot din motqr yana cewa
''bari in shigar miki da kayan ko''da sauri ta amshi jakar da ya fara fitowa da ita
''a'ah baaba,ka barshi ga yara zansa su shigar min da su''tayi kirqn yaran maqotan dake zaune can gefe da su wadanda da wasan qasa suke tayi da yan guje gje ganinta yasa suka bar abinda suke suka tsaya kallonta,kiransu tayi kunsan amarya da farinjini a guje suka taho dukkansu har ana rige rigen zuwa,kqn ta qarasa mqganar ma sun fara zundumar kqyqn,nata suna shige mata da su cikin gida,dubu biyar ta qirgo cikin dubu dari biyun da mami ta bata tace ta riqe a hannunta tasan amarya kudi basa zama a hannunta,da fqri qin karba malam baaba yayi
''idan da ni mai wadata ne meramu ai nine mai baki ma a matsayin gudun mawa,ke yarinya ce ta gari merama,babu komai tsakaninmu dake saidai muyi miki sai fatan alkhairi''
sai ya kuma karya maya zuciya
''indai ka daukeni 'ya baaba ka karbi kudin nan,ayi min addu'a''da qyar ta shawo kansa ya karba yana sa mata albarka,sukayi bankwana ta shige gidan ta juya don shiga gidan,tun daga qofar gidan ta fara ganin canji,yasha fenti radau ruwan madara tun daga waje har cikin gidan
mutanene da suka kusa dosan ashirin a tsakar gidan,hira ce kawai ke tashi cike da farinciki,dangin mamanta ne da na babanta na nesa,na garin gaya da sauran garuruwa,sallamarta ya sanya su saka guda atare kowa na fadin albarkacin bakinsa ganin yadda tayi kyau ta canza tamkar ba maryam din ba ,kunya ta kamata ta qarasa gurinsu suka gaggaisa,maryam mai alkahiri,ce duk da yanayin gidansun hakan bai hanata idan ta dauki albashinta ta duba mabuqata sosai cikin dangin nasu ta taimaka musu da dan abinda ba'a rasa ba iya abinda zata iya
daga nan dakin mamanta ta wuce,nan din ma da mutane dakin yayi kaca kaca da kayyaki samiru da kayan robobi wadana aketa kwashewa za'a tafi jere,suka gagggaisa ta shige dakin gadon mama,ita da hindatu ne a dakin kayan sawa ne zube saman gadon sunata aiki,gefan gadon ta samu ta zauna ta soma gaida maman,dafe bakinta hindatu tayi
''la la la adda maryam,tabdijan irin wannan canzawa haka gaskiya mami ta iya kiwo,za'a gigita ya abdur rahim kenan''alamu tayi mata da ido tayi shiru don Allah
''qaraso maryamu ki fidda kayan da kike so za'a bada na bayarwa''
''um um mama kawai a bawa wadanda za'a bawa dim babu komai''hindatu ta janyo jakar bakko gaban maryam din tana fadin
''duba kayan nan adda maryam dinkunanki ne jiya adda raliya aiko idris direba ya kawosu gobe zata amso miki sauran''
da daidaya ta dinga daga kayan,ba qaramin burgeta dinkunan sukayi ba duk ciki babu na kushewa
''Allah ya saka mata da alkhairi''ta fada bayan ta kammala dubawar
A bakin fanfo ta fito yin sallar la'asar ta tadda jamila ta fito ita kuma daga bandaki,gaba dqya ta fige ta lalace kamar mai cutar qanjamau,wani banzan kallo ta yiwa maryam din tare da jan tsaki,bata kulata ba ta bude fanfon ta kunnashi ta fara alwala,bata kai ga gamawa ba taji an bangajeta tayi taga taga kamar zata fadi sauran qiris ta qume goshinta Allah ya taqaita mata ta dafe kan fanfon,miqewa tayi tana duban bayanta,binta ce a tsaye cike da tsabar rashin kunay tana girgiza,ta arkade jikinta da ya debi qura kana ta kalleta
''baki gani ne binta kika bugeni?''
''ina gani mana sai me?,dama jiran dawowarki nake cikin gidan nan,tsofaffin munafukai maciya amana masu aure mijin yar uwarsu''
duk da kalamanta sun mata ciwo amma sai da ta bata dariya,tsayawa tayi kallonta kawai,cikin yaran gidan susu goma sha bakwai binta ita ce qanwarta ta tara,aqalla ta bata ahekaru kusan goma,sai taga ada ma ba ni ta kanta take ba sai ayanzu,ranar tqrihi a rayuwarsu,kada kai tayi tana sake yin murmushi ta juya don ci gaba da alwalarta kafin tace
''duk wadanda kika kira da wadan nan sunayen ai aun riga da sunsan kansu,kinga kenan bada ni kike ba''
''dake nake mana,kuma idan kin isa ki tanka kiga yadda ake ruwan bala'i cikin gidan nan''
ta zubar da ruwan dake bakinta ta gyara daurin dankwalinta kana ta dafa kafadar bintan
''mai abun fada baya fada,harkar girma muke da mutunci bata bala'i da masifa,ina da damar da zan miki dukan tsiya binta hakan ba gagarata zaiyi ba,amma bazanyi hakan ba abinda kuka shuka kuke girba ma kadai ya isheku duka mai taba qololuwar zuciya''ta sake mata kafada tayi dakinsu
''ki dakeni mana kinji ko karuwa kawai''
''ke kuwa tunda bata kulaki ba ai sai ki shafa mata lafiya''inji kulu dake diban ruwan wanka
''babu ruwanki munafukai,dama tun jiya naga kunatavrawar kai ke da uwarki a kansu''kulu ba haquri kamar yadda bintan keji da kanga,take suka hau dambatawa,ragowar dangin babansu da basu je jere ba ne suka rabasu
Dawowar yan jere suka hau hirar gidanjan su maryam din yadda Allah ya musu baiwar samun mazauni mai kyau da qayatarwa ta,maganar ta qara hasala hadiza da yaranta wadanda suka zame mata qawaye,suke kuma tayata haukan da take ta faman yi,don tuni jikin huwaila yayi sanyi,saidai atafau hindatu ta hanata shiga jikinsu,tace sam baza'a maimaita abinda ya faru shekarar bara ba,an dai fidda kayan sawa jakanku na da takalma cikin kayan maryam din an bawa yaranta kuku lubabatu da batulu,da murnarsu kuwa suka arba koba komai sun samu na fitar biki,wannan karbar ma da sukayi saida ya zama bala'i,hadiza da yayanta suka fito suna zubda ruwan rashin mutunci cikin dangin ubansu,hali kam sun saidashi,wanda baisan halisu ma ba ada ayanzun ya sani,kowa ya budi baki tir yake da halayensu
🎄🎍🌲🎍🎄🌲
Tara ga wata ya kama ranar talata ranar sukayi kamu,washegari laraba sukayi budan kai duk shigar da sukayi iri daya ne komai da komai ita da hindatu hatta da yari,alhamis aka musu wani wani dan reception na fulani wanda shiga ce ta fulani kowa da kowa yayi,ba qaramin qayatarwa tsarin nasu yayi ba,komai a tsare cikin nutsuwa da kwanciyar hankali
Ranar juma'a ya kama daurin aure,a gaya aka tsara za'a daura auren wannan karon,dalili da yasa kenan gidan ya zamto sai mata kawai mazan duka sun tafi gaya
Da yammacin gidan maman zahra suke zaune maqotansu,tana tsakiyar qawaye da 'yan uwa,tayi kyau cikin shadda 'yar ubansu lemon green da akayiwa adon light blue,rigace da zani dinkin ba qaramin mata kyau yayi ba,tamkar wata fure haka ta koma,raliya na gefanta tana zuba mata abinci cikin plate kana ta miqa mata
''maryam,karbi kici,tunda aka fara sabgogin nan baki ci abincin kirki ba fa''
ya mutsa fuska
''banajin dadin bakina raliya,faduwar gaba nake fama da ita tun da safe''
murmushi tayi
''fargabar shiga sabuwar rayuwa ce,kowacce mace najin hakan har da bacin rai ranar daurin aurenta,wasu ma har kuka suke kafin suji sanyi cikin zuciyarau,kiyita ambaton Allah''
kafin tace komai waurta ta fara kuwwa,a kasalance ta ciro mami ke kiranta,mirmushi tayi sanan tace
''Allah sarki mami na''
''tun da safe naso kiranki maryam,nasan tuni an daura tun safe ko diyata girma ya hau kanta an zama manya''murmushi ta sake yi tace
''na yamma ne mami,suna can dai''
''to Allah yasa ayi a sa'a a gaida maman kice ina mata Allah ya sanya alkhairi''
''ameen mami,na gode''
batulu tayi sallama falon sanye da daya daga cikin kayan da maryam ta bata an gyara mata daidai ita,sun mata kyau kuwa don duka yaran gidan nasu babu laifi akwai kyau irin na fulanin usuli
''adda maryam kizo kinyi baqi suna falon mama''cike da mamaki ta kalleta,gau ta zama adda,sunan da koda wasa bata taba jin wani daga cikin uaran gidan ya kirata da shi ba idan ka dauke hindatu,hatta da isyaku autan gidan
''kice ina zuwa''ta bata amsa tana janyo mayafonta ta lullube jikinta,ta dubi suwaiba dake zaune gefe tace tazo ta rakata
da qyar ta samu ta kutsa ta ahiga gidan nasu saboda yawan jama'a musamman da masu kidan qwarya suka baje hajarsu cikin qwarewa don daga cikin gidan sarki aka daukosu
qannenta shamsiyya,azara,balaraba da yasira na zaune daga gu guda an samu abinci suda yaransu anata kwasa,sannu tayi,musu kafin ta shigesu,yasira da shamsiyya suka danyi qus qus kana suka tabe baki
''an samu duniya''inji azara
tayi sallama falon,maman ma zaune tayi kyau cikin dinkin atamfarya,sai ta koma kamar yarinya mai qananan shekaru,Allah ne kadai yasan farincikin da take ciki,babu shakka komai yayi farko zaiyi qarshe,aure kuwa lokaci ne idan yazo ko ba'a shirya ba sai anyi shi,fata dai kada gaggawar anason ayi auren tasa aje ayi zaben tumun dare
abokan aikinta na na gurin haj atika,taji dadin zuwansu kuwa qwarai da gaske
qarfe shida suka fita meena event center suka gabatar da wata qwarya qwaryar dinner,ta maryam ce ita da qawaye da iyayenta,su hindatu kuwa tuni jabir yazo ya dauke matarshi suka wuce dinner,fir maryam tace ma abdur rahim bata buqatar wata dinner,su din ma da zasuyi sai sun dawo,hindatu da jabir na mata dariya sukayi tafiyarsu,bashi kuwa ya dawo da ita gida ba sai daya saura na dare,maryam din zata soma mata fada tayi shigewarta bargo tayi kwanciyarta
''hindatu rawan kan amarci ya fara tabaki kenan''cewar raliya wadda ke gyara kwanciyar fadil,suna jinta tana musu dariya
🎄🎍🌲🎍🎄🎍🌲
tun qarfe biyar da rabi na yammacin ranar asabar motoci suka cika layin har suka musu kadan,tilas ya sanya wasu motocin suka dinga parking a bakin titin unguwar,moto cine na kere sa'a waccan tana wace wannan haka wannan ma haka,a nutse kowa ke zaban wadda zai shiga kasancewar tare za'a tafi,sai hindatu ta raka maryam din tukunna.
''da Allah malama kihi ki foto,kunzo kun sanya uwarku a tsakiya kuna neman sata kuka,ina cewa ba'a kanku aka fara aure ba,haba da Allah''inji yayar mama hajiya aysha,hindatu da maryam dinne duqe gaban maman,maryam ta soma qoqarin taahi amma kuka yaci qarfinta ya hanata,sanye take da atamfa riga da simple zani an lullubeta ruf da wadataccen mayafi,hajiya aushan ce ta taimaka mata ta miqe ganim da gasken ta kasa miqewar,addu'o'in fatan alkhakri ta biyo yayan nata da shi.
caraf sukaji an damqe hindatu,jamila ce a zabure kamar mahaukaciya sabon kamu surutai take zage zage da sumbatu kala kala
''shegiya tsinanniya,wallahi babu inda kika isa kije,gidan mijina nawa ne ni kadai,wallahi bazan baki damar cin irin daular da naci ba don uwar ubanki''ganin abin na gaske ne daya daga cikin qannen malam amadu sailuba ta qaraso ta daga hannu ta zabgawa jamilan mari
''saketa 'yar iskar yarinya mai kama da 'yar Allah bani,dul abinda kika aikata akayi muku shuru ba'ace muku komai ba bai isheku basai yau ranar da Allah ya tashi nina muku kuskurenku,shekara nawa kuna cutar amina baiwar Allah ta taba tadakai ta kalli waninku,tunda aka fara bikin nan baku,bar mutane an zauma lafiya ba,uwarku dai ta cuceku wallahi,kuma ki saketa tun kafin ki debi haqoranki a hannu,idan tsiyace kowa ma ya iyata''ba shiri ta saki hindatun taja da baya sai gata yaraf a qasa.
da gudu inna hadiza ta qaraso gurin,hannu ta dora a ka cikin qaraji tana fadin
''huwaila amina dake kanki sailuba,zaku kashemin 'ya,munafukai tsinannu,dama ai na dade da sanin kun fi son amina saboda 'yar garinku ce,to Allah ya fiku kina ranar daukan fansa na tafe''
babu wanda yabi ta kanta,hssalima zamewa kowa ya dinga yi ko ruwan da za'a kwarawa jamilar an rasa me miqowa,su kansu sauran 'ya'yan nata na qofar gida suna jallin yadda motocin sukayi farin dangon daukar amare,kwalliya kowaccensu taci tare da fatan daya daga cikin mamallakan motar ya taya
ta dubi sailuba sata zo wucewa tana sauri don kada ta rasa motar tafiya
''da Allah sailuba miqo min ruwa na kwarawa jamila kinga bata numfashi''kallon banza tayi mata
''kici mutuncinmu kici na uwarmu kice zaki moremu,saidai ki nemi wata ta baki wallahi badai ni ba''ta buga qafa tayi ficewarta,tilas ta saki jamilan ta debo ruwan ta sheqa mata kana ta jata zuwa cikin daki tana fyace majina.
Gwanin sha'awa motocin ke tafiya cikin tsari da nutsuwa,sam babu irin mahaukscin gudun nan da 'yan kai amarya keyi,mitoci ne kimanin guda arb'in banda na security guda goma
wani matsananciyar faduwar gaba take fama da shi idan ta tuna izuwa gidan aurenta fa take tafiya,addu'o'i ne fal cikin zuciyarta na samun sa'a da nasarar sabuwar rayuwar da zata fuskanta
🍃🍂🍃🍂🍃
sau uku tana sako qafarta waje da niyyar fita saidsi ta kasa,sakamakon mutanen dake giftawa bata da buqatar kowa ya ganta,aiki ne na sirri wanda bata da buqatar haduwarta da wani,wayarta ta fara vibration jikinta na rawa ta daga,muryar nene ta cika dodon kunnenta
''kada fa kiyi kuskuren da zaki jawo mana bacin aiki,wannan ce damarmu ta qarshe''murya can qasa take fadin
''na gama aiwatar da komai nene,fitowata ce ke neman gagara mutane na kai kawo a gun''
''kada ki kuskura ki wuce mintina talatin baki baro area din ba,wuce hakan na nufin bacin komai''din din din wayar ta katse,hankalinta ta msida sosai kan hanyar ficewarta,wuf ta faki idanu ta fice ta nufi bangaren nasu cike da farincikin nasarar aikinsu
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Qarfe goma da rabi ne na dare,gefan lallausan gadon dakin nata take a cure guri guda,tafiyar yan kawota da mintina ashirin yayyafi ya fara sauka wanda ya haddasa sanyi da garin yayi hade da qamshin qasa,bai kankama ba ruwan hakanan yayyafin bai tsaya ba,kusan tunda suka tafi suka barta anan take zaune bata ko motsa ba
hayaniyan data soma ji cikin paflour na muryoyin maza daban daban suka qara mata fatgaba,ta runtse idonta tana jin yadda zuciyarta ke dukan uku uku kamar zata yi tsalle ta fito
''ko baka fadi ba ba shiga muma za muyi ba don an dade da daina wannan''ta jiyo muyar wani daga cikinsu,tun tana jin hayaniyar tasu sama sama har taji dif alamun basu cikin sun fice kenan
da gudu gudu sauri sauri ya qaraso cikin parlojt din saboda ruwan da ya sake danyin qarfi,duk da haka ya jiqa masa fararen kayanshi,ya tsaya ya kulle ko ina ya rage yawan qwayayen dake kunne kana ya doshi dakin kai tsaye
a hankali ya tura qofar dakin kana ajjiye tarin ledojin dake hannunshi,qamshin dake dakin kawai ya isa ya tabbatar maka rana ce ta musamman,tsaye gayi hannunshi harde a bayanshi,sai ya lumshe idonshi yana zuqar qamshin qasa hade da turaren jikinsa da na dakin baki daya yadda suka hadu suka fidda wani qamshi na musamman kuma na daban,gwagwarmayar da ya fada kacin samunta ta zama mallakinsa ya dinga dan tunawa,a hankali ya bude idanun nashi ya tsaya yana qarewa shigar tata kallo
gaba daya jikinsa ya saki lokacin da wani tunani ya darsu a ransa wanda ya qada maaa qwarin gwiwa da azamar isa gareta,tamkar mai tausayin gadon haka ya hau ya dinga rarrafawa har ya isa gareta kana yayi zaman dirshan a gabanta
sannu a hankali ya dinga yaye mayafin dake kanta har ya cimma nasarar cireshi duka fuskarta ta bayyana,saidai ya cimma idanunta aruntse ne,ya karyar da kai yana ci gaba da kallon fukartata irin kallon da bai taba samun dama ya tsaya yayi mata shi ba,kyawunta yaci gaba da fito masa muraran,sosai ya shagala har baison abinda zai shiga tsakaninsa da yanayin
Qememe zuciuarta taqi amincewa da daina mugun tseran gudun da take,gashi ya sata agaba,nauyi da kunyarshi sun hanata bude ido,jin shirun yayi yawa ya sanyata yanke shawarar bude idanun nata ko yama fita adakinne ma bata sani ba
da kadan da kadan ta dinga budesu har sai da suka kammala buduwa tar,da qafafunshi ta soma tozali a hankali ta dinga daga kan nata har ya sauka bisa fuskarshi da ruwan sama ya jiqa har ruwan da ya soma taba kanshi ke diga kadan kadan,batasan lokacin data ta wuntsila gefe ba cike da *TSORO RAZANI DA FIRGITA BA* sakamakon wanda ta gani
*ABDALLAH* ne cikin daren nan cikin gidanta kan gadon aurenta?,idanunta ke mata gizo koko meye?,me yake faruwa ne?,hauka ce ta samu qwaqwalwar abdallah ko bashi bane bama gaba daya aljanu kesan mata wasa da qwaqwalwarta da tunaninta,ina abdur rahim da ya bar abdallah ya keto dakinsu na sunnah?
dimbin tambayoyin da suka nemi jirkita mata qwaqwalwa kenan tashi guda ba tare da tasan duka amsoshinsu ba
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣8⃣
*_JIRGINSO ZAYA TASHI KE DAI AKE JIRA ...'YAR GATA DUNIYAR SO.... KECE DA SARAUTA_*🎶🎶
*_na dawo gunki nazo baqo da sallama....kai kawo nayi qarshe...a qauna na tsunduma....kin jawo nayi roqo nazo ki ban zuma....na sawo dubi tufata mai kyau da karrama....ke naiwa kwalliyata shiga ta alfarma....._*🎶🎶
*_soyayya gaskiya ce ya zanyi in raina....wanda yake aac cikintaaa nima don na zauna.......nayi dare ban masauki gidanki in kwana....zo ka shige har abinci zan maka kwadon rama....._*🎶🎶
*_riqe sirri sai mai sirriiii....da fari a cikin taurariiiiii...._*
*wannan waqar na sadaukarwa da readers don jin dadinsu kana iya sauraronta bayan kammala karanta wagga shafi*
😜😜😂😂
Matsowa kusa da ita ya sakeyi tattausan murmu kwance bisa kyakkyawan fuskarshi,duka hannayenshi ya ware da nufin ta iso gareshi,take jikinta ya soma bari,qwaqwalwarta so take ta tsaya cik da aiki saidai ta ware qwanjinta wajen hana hakan faruwa,bata da buqatar tsayawar tunaninta a yanzu,tama fi buqatarshi fiye da ko yaushe,ya sake matsowa gareta yana nufin janyo ta jikinshi
wata hadaddiyar tsawa ta sakar masa bayan ta dira daga kan gadon jikinta na qyarma,tuni zuciyarta ta karye hawaye ya soma sintiri bisa fuskarta,dukkan tunaninta sun gama vata fyade abdallah yazo yi mata,tunda ba wannan ne karo na farko data taba ganinshi kebe da diya mace ba,amma wanne irin tsoro abdur rahim kewa abdallah da ua bashi irin wannan damar?,ko wani abu yayiwa abdur rahim din nsta har ya kai ga shigowa dakinta shi daya ba tare da wani qwaqqwaran motsi ko hayaniya ba.
Abdallan ya sake motsawa don biyota qasan,cikin daga sauti hargagi fushi bacin rai da tashin hankali ta dakatar da shi
''dakata marar tsoron Allah,me kake nema da ni?,me ya shigo da kai dakina?,kana shirin tozarta sunnar ma'aiki?,kana shirin cin mutuncin matar da bata yi maka komai ba?,to Allah ya fika''
jikinta na rawa ra fara daddan na wayar dake hannuna tun dazun da aka kawota lubabatu ta danqa mata a hannunta
Numbers din abdur rahim ne guda uku,saidai duka wadda ta kira sai taji ringin dinta cikin aljihun abdallah,cike da wani tsoron ta dago ta dubeshi,hawaye ne kawai ke kwaranya da sintiri kan fuskarta
''abdallah!,ina abdur rahim?,me kayi mishi?me ka yiwa mijina!?''ta qarasa maganar cikin qaaraaji
baisan sanda yayi alkafura ya diro daga gadon ba,gadan gadan ya nufeta don ya riqeta ganin yadda take kuka tuquru tana dafe bango,saidai kafin ya kai ga riqeta ta goce
''kada ka tabani,kaji tsoron Alkah kasan cewa ni matar wani ce''cikin cool voice dinsa mai cike da jarumta da mazantaka wadda a yau rauni ya cikata ya saje maidata sassanya yace
''pls cool down mana,ki natsu in miki bayani kinji,ki saurareni''
''bazan nutsu ba,in nutsu ka cucu ne,me kake nufi abdallah,me nayi maka,ka shigo dakin aure na,banga mijina ba,na kira wayoyinshi suna jikinka,ka gaya min me ka masa!!me kayi masa!!!''
duk yadda yaso tayi shiru ta saurareshi abun ya faskara,idanunta sun rufe bisa dukkan zatonta ko abdallah ya kashe abdur rahim ne
''ki zauna ki fahimceni...'''
''bazan fahimceka ba.....ina mijina.....ina ka kaimin mijina abdu........''
''maryam!ni ne nan mijinki,ni ne mijinki ba abdur rahim ba,ni abdallah da ni aka daura miki aure!''ya fada yana nuna kanshi shima cikin daga murya har jijiyar wuyanshi na tashi
sai kukan nata ya tsaya cak,ta tsaya tana kallonshi tamkar doluwa ko sakarya,jin maganar tayi tamkar cikin mafarki,da saufi ta kama hanunta ta mintsina sai ta tabbatar cewa gaske ne,girgizq kantq ta shiga yi tana fadin
''ba kaine mijina ba,bakai ka aureni ba ni zaka yaudara?''
''bari in baki shaida don ki tabbatar''ciro wayarsa yayi ya kira wasu nimbers,ga mamakinta sai ga muryar abdur rahim radau
''kai,bakasan ganganci bane kiran ango daidai wannan lokacin ba?,ko baka shiga dakin marya bane?''yake tambaya cikin sigar zolaya
''hmmm,abdul maryam zata amince nine mijinta kuwa?''
dariya yayi
''a'ah,mai zai hana,idan ma taqi ta amince ka dauketa kuje gidansu tunda su sun sani kaine ka aureta din,ko ni inzo gobe sai in dauko gimbiya muzo in mata bayani''
baiga qarasowarta ba sai waftar wayar da tayi,cikin rawar jiki ta kara wayar a kunnenta
''abdur rahim,ka cemin kaine mijina ba abdallah ba,ka gaya masa don Allah''
''kiyi haquri maryam bani na bada sadakinki ba bani ke neman aurenki ba,duniya bani ta shaida a matsayin mijinki ba duka wannan abdallah ne,nine *abdurrahim a fili a boye kuma abdallah,nike neman aurenki a gaban idonki a bayan idonki abdallah ne*,banyi hakan ba don komai sai don *DACE DA JUNA* da kukayi ke da shi,babu wadda ta dace ta zauna da abdallah saike......''
bata bari kunnuwanta sun qarasa ji mata kalmomin da ta yiwa laqabi da munanan kalmomi ba ta saki wayar ta tarwatse agun,taji daga baki mai tushe to shin kuma wa take jira?me take jira da zai tabbatar mata fiye da abinda taji yanzun?babu,babu shi,take taji garkuwar jikinta na raguwa,qarfinta yana yin qasa,sai ta soma sulalewa agun
da gudu abdallah ya isa gareta ya tallafota,tabbas da tana da isashen qarfi bazata yarda ta sauka ajikinshi ba,rungumeta yayi yana jijjigata,numfashinta na fita hakanan idanunta akansa suke hawaye na bin gefan kunnenta saidai numfashin na gware ne gurin fita,rungumeta yayi tsam cikin jikinsa cikin wani tashin hankalin,daukarta yayi tsam tamkqr wata 'yar tsana ya komar da ita kan gadon ya shimfideta.
mahaukacin bugu yaji ana yiwa qofar bangaren nasa ,sai ya sake diriricewa,cikin qanqanin lokaci kuma ya gayyatowa kansa dakiya da jarumta yana tafiya yana waiwayen maryam din tamkar wanda aka ce masa kafin yaje ya dawo zata bace ya sauko ziwa bakin qofar ya saka key din ya bude
jikinsa ta fado tamkar wadda aka hankado,cikin hanzari yasa hannunsa daya ya cireta daga jikinsa yayi gefe da ita saidai ita qoqarin dawowa take zuwa jikin nasa tana gunjin kuka duk ta wani burkice kamar mahaukaciya
''wai meye haka zubaidq!bana son hauka fa!''ya fada cikin hargagi
''bazan iya ba abdallah,wallahi bazan iya jure rashinka ba,ka tausaya min abdallah,ta yaya muna cikin gida daya zaka kwana da wata abdallah?''
ya tabbata idan yace ma zaya tsaya bata baki ne wahal da kansq kawai zaiyi don ba zata taba fahimtarsa ba,kai infact ma a yanzu bai da time baijin yana da time din wani a yanzu a duniya koma bayan maryam,ya tabbata idan yayi sake kwabarsa zatayi ruwa ne tsululu kuwa,a nashi zaton da hasashen abun bazai kai bacn haka ba,yayi zaton cewa duk randa maryam din ta samu labarin shine miji a gareta zatayi farin ciki ne fiye da kowa kodon,dimbin dukiya da Allah ya mallaka masa
ganin yadda take faman ahigewa jikinsa kamar hauka yasa yq cira hannu hankadata baya tayi taga taga kamar zata fadi
''ki shiga hqnkalinki zubaida,bana cike da iskanci da hauka kina jina ko,bace min da gani''
maimakon tayi kamar yadda yace din sai ta qara tasowa kansa,cikin zafin nama yaja qofqr ya rufe ya maida muqullin,ta kuwa fada jikin qofar ta saki wani kukan tana bubbugawa iya qarfinta
''ka bude min don Allah abdallah,wallahi na kasa barci,na kasa cin abinci,na gaza jurewa,ka bude min abdallah''haka ta dinga fada tqnq bubbuga qofar,yana jinta hqr ya haura sama ya barta anan
ruwan roba mai azabar sanyi yq ciro ya hado da cup ya koma dakin,yadda ya barya haka ua sameta sai qaruwa da ruwan hawayen fuskarta sukayi
ajjiye cup din yayi a side drower ya haura gadon,ya zame mayafin dake jikinta ya wulla shi gefe,ya janyo cup din ya tsiyaya ruwan yana tsoma hannunshi cikin ruwan yana shafa mata a fuskarta zuwa wuyanta,duk da yanayin da yake ciki hakan bai hanashi kin laushi da santsin fatarta ba,duk lokacin da hannunshi ya taba fuskarta ji take tamkar yana dora mata wuta ne a jikinta,zuciyarta,cike fal da tsanarshi,sannu a hankali numfashinta ya soma daidaita,qwarin jikinta ya soma dawowa,da sauri tasa hannunta tayi wurgi da hannunshi dake ci gaba da shafa mata ruwan,ta miqe dqga kan gadon tana shirin sauka,da sauri ya tareta
''ina zaki maryam?''
''ina ruwanka da inda zani?,ka rabu da ni!''tayi maganar cikin tsawa,ganin da gasken fita zatayi yasa ya tareta ya riqe dukkan kafadunta,ta soma zile zille da qoqarin qwacewa tana fadin ya rabu da ita ya saketa,ci gaba yayi da qoqarin tsaidata
''ina buqatar hankalinki maryam,ina buqatar nutsuwarki,ki zauna ki bani dama muyi magana,ki nutsu ki fahimceni,me kike so ne maryam,me kike buqata''
sak ta sakeyi tama kallonshi
''sai yanzu kake da buqatar hankali na?,sai yanzu kake d buqatar nutsuwata?me kake son gaya min,ka aureni ba da sani na ba kuma kace nutsuwata kake buqata?wacce nutsuwa kake sa ran samu daga gareni?,haka ake aure?,ok saboda kana tsammani kana da dukiyar da zata iya kawo maka duk macen da kake so kamar yadda naji kana alfahari kana gayawa abokanka?,koda dukiya zata iya kawo maka kowacce mace da kake miradi yes na yarda zata iya amma banda ni maryamu aciki,koda ina da muradin dukiyarka ina cewa saida izini na zaka aure ni?,after all ma bana aonka abdallah bana qaunarka,bani da burin auren ire irenka ma,abu guda nake da buqata daga gareka shine ka rubuta min sakina guda uku a yanzu ka bani,ni kuma na maka alqawarin bazan kwana maka cikin gida ba,ka sakeni abdallah ka sakeni!''
ta qare maganar cikin hargowa
hannayensa ya harde aqirji yana kallonta,ba qaramin duka kalamanta sukayi masa ba,tunda ya tashi mace bata taba kallon qwayar idanunshi tace bata sonshi ba,akoda yaushe kalmomin so yake samu da karba daga garesu,kalmomin da bai taba samin suna da dataja ba sai yanzun akan maryamun,ya fuskanci ba qaramin fita tayi daga controll dinta ba,kome zaya fada bai da tasiri yanzun cikin kunne da ziciyarta don hakq ya dan jada baya,ya zame rigar jikinshi ya rage daga shi sai farar vest da dogon wandon shaddarsa,ya nufo inda take gadan gadan sai ta juya zata sa gudu caraf ya kamota,duk iya yada taso qwacewa abu ya faskara,qyaleta yayi taci gaba da qoqarin qwatar kan nata har jikinta yayi tubus qarfinta ya qare
''haka kurum zaki bata mana farin darenmu kan dalilin ki wanda kika qi tsayawa kiji nawa dalilin,dare ya tsala lokqcin da ya kamata mu samu hutu amma kin hana mana''ya fada yana mirginata tare da zuge mata zif din rigarta,ganin yana qoqarin cire mata rigar jikinta ya sanya ta sake sakin wani kukan cikin dausashshiyar muryarta da kuka ya dasheta tana ci gaba da qoqarin ture hannauenshi wanda saboda tsabar rashin qwarin jikinta ko motsi hannun nashi baiyi ba
''ka qyaleni abdallah,wallahi idan ka taba mutuncina zan maka Allah ya isa kuma bazan taba yafe maka ba''
duk da yana cikin rashin nutsuwa sai da ta bashi dariya
''kome zan miki ma ai nawa ne,dukkaninki halas dina ce,so ko kin min Allah ya isan ma ba bina zata yi ba''ya qarasa sabule rigar tata,hannayenta tasa ta fara kare qirjinta tana cewa
''ka zalunci rayuwata abdallah,zamu tsaya fa hisabi gaban Allah''
hannu daya yasa ya kawar da hannayen nata wanda ita iya ganinta duka qarfinta tasa gun kare su,ya balle bra din ya zameta daga jikinta,take numfashinsa ya dauke da sauri ya lumshe idanunsa kana ya squka agadon ya isa bakin wardove dinsu ya zabo rigar bacci mai adon fari da pink mai sulbi da taushi ,saidai kafin ya qaraso har ta isa bakin qofa cak ya sake daukota kamar wani kara ya maidota kan gadon ya danneta da rabin jikinsa ya sanya mata kayan baccin
fillow guda ya ajjiye musu bayan ya duba lokaci qarfe biyu da rabi na dare,cikin jikinsa ya jata ya matseta gam suka kwanta ba tare da ya damu da sauya nasa kayan ba,yana jinta tana wutsil wutsil dinta da dan ragowar qarfinta hade da hawaye don tuni muryarta ta gama dakushewa koda tayi maganar ma ba fita take ba,gashinta mai sulbi da taushi kawai yake shafawa yana jin digar hawayen nata tamkar na dalma kan tsokar zuciyarsa.
a hankali ya zagaya da kansa kan kunnenta ya rada mata
''kiyi haquri,na yarda na cutar da ke amma relax pls mu barwa gobe,kome kikeso zan maki,kiyi bacci zuciyarki tayi sanyi''
''ka sakeni bazqn kwana daki daya da kai ba bare jikinka,ka sakeni abdallah''abinda take ta fadi kenan saidai ina muryarta bata fita bare yaji abinda take fada,gaba daya ma taga ya maia abun kamar wani wasa saboda tsabar qarfin hali irin na abdallahn.......
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣9⃣
🎶🎶🎶🎶
*_alqawari ki riqeeee..komai wuya karmu rabu kinji..._*
*m sharif song for dis page*
😜😂
A hankali ta dinga bude idonta da taji ya mata nauyi sakamakon kumburar da sukayi,tana gama budesu tarwai komai ya dawo kanta,abu na farko hawaye ne ya fara bin idanunta kamar yadda ya ta kwanta da shi,jin alamun motsi daga qasa ya sanyata wurga idanunta can,abdallah ne zaune kan sallaya,ta dubi agogon dakin qarfe bakwai saura na safe,da sauri ta miqe cikin zuciuarta tana istigfarin rashin yin sallar asubahi akan kari,jiki babu qwari ta zuro qafafunta qasa motsin wannan ne ya juyo da hankalin abdallah kanta
sai ta kasa tashi don batasan ina toilet yake ba,da suka hada idanu kuma sai ta dauke kanta gefe guda
''ga toilet din can''ya fada yana kada yatsunsa tare da yi mata nuni,ta jishi sarai saidai ba zata oya tashi ba saboda rigar baccin jikinta gajeriya ce,gashi ta wuwwurga idanunta ko ina bata hango kayanta ba,zanin gadon ta yayaye kawai gaba daya duk da girmansa ta lullube jikinta da shi kana ta samu sukunin shigewa bandakin
kuka ta zauna yi riris kan daddumar,tana ji har cikin zuciyarta abdur rahim ya zalunce ta abdallah ya cuceta,don ko kadan bata da plan din airen abdallah akundin rayiwarta,sai gashi dare daya wata qatotiwar qaddara mai wuyar afassara ta fada mata,abdallah mai girmankai,mai izgili mai taqama da dukiyarsho,mai titiya da kyawun surar da Allah ya bashi,abdallah mai tarin 'yammata,ko baya ga haka ma sama ai ta yiwa yaro nisa,ina zata kai abdallahn,batajin cikin yarin masoyansa ita din karanta ya kai tsaikon da zata daga hannu,me take da shi da zata nunawa duniya amatsayin matar abdallah abdulkarem mai nasara?,yaro dan gata gaba da baya da daya tilo tamkar taoka daya cikin miya,mai tarin kyau asali dukiya da arziqin ma baki daya,ta ina tarayyarsa da maryam diya ga malam amadu zatqyi daidai,masu nema da qyar suci da kansu da qyar,diyar da ta taso cikin qunci hantara da takurar rayuwa?,rufin asiri take nema da girma ba bankada da tonon sililin asirinta va,ta iya talaucinta haka zalika ta iya tsayawa iya matsayinta,to akan me yanzu zata yadda ta sarayar da dulka wadan nan abubuwa?,ko ta zuba ido abdallan ua sarayar mata da au lokaci guda
tasha ji daga bakunan wasu matan yadda auren mai dukiya quruciya da kyau yake zamewa mace qarfan qafa alaqaqai,don me zata zira kanta rijiya mai gaba dubu?bata taba sha'awar auren mai tarin dukiya irin abdallah ba,balle shi din da tasha jin kalmomin nuna ko ahi waye da matsayin da yake ji ua taka daga bakinsa,idanuwanta sunsha nuna mata kal kalan 'yammata dake hauka akanshi,tana cikin wanna tunanin ta tsinci tafin hannunshi dafe da saman qafafunta,da sauri ta janyesu ba tare data daga kai ta dubeshi ba
''maryam''ya kirata asanyaye
''ko baki fada ba kuka kike''
''kuka na ya zama dole,auren dole qiriqiri?,irin auren dolen da ko a fina finai ban taba cin karo da ahi ba sai gashi yau ya faru a kaina?,ka fada min wanne mataki ka dauka game da zaman mu,zaman mu ba mai yiwu bane''
''ki bani dama mafyam ni zan mai da ahi mai yiwuwa,indai matsalar taki ta zuciya ce,zuciyarki bata san abdallah,ta bawa abdallah dama na kwana talatin cif na rantse miki sai taso abdallah fiye da yadda take son kanta''
''ka taba ganin inda ruwa da wuta suka cakudu suka zauna guri guda lafiya lau?''
ya fuskanci mai take nufi da maganarta don haka bata buqatar amsa
kusan mintina goma ahiru ya ratsa tsakaninsu,ta qagauta ya janye jiminahi daga inda take,ganin babu niuya tasa ta bude bakinta murya can qasa
''ka matsa daga kusa da mi,kuma ka cika min alqawarin da ka dauka min daren jiya yanzu ba sai anjima ba''
gayara zamanshi ya kuma tamkar ma basa ahi take maganarta ba
''naji,zan sakeki.....amma bisa wani sharadi guda''
tunda suka fara maganar bata dago ta kalleshi ba sai a yanzu
''ba buqatar wani sharado daga gareka ko wanne iei ne saki nake so,kuma dole ka sakeni''
ya sanya fitinannun qwayoyin idanunshi cikin nata kana ya tabe baki
''babu dole fa maryam,abdallah ne mijin ba wai maryam ba,idan kin amince zan gaya miki sharadina daya ne zuwa biyu da zarar kin cika sharadina ba tare da bata lokaci ba agobe ma kina iya tafiya da takardarki''idanunta ta lumshe saboda yadda ya nutsa qwayoyin idanunshi cikin nata yake mata magana haka kanshi tsaye kamar ba mai laifi ba
shiru tayi,cikin dan taqaitaccen nazari zuciyarta ta bata shawarar sauraranshi kanta kawai ta gyada masa,ya sake sanyaya murya tamkar mai jin bacci tare da sake matsowa kusa da ita,tayi yinqurin matsawa da sauri yace
''babu buqatar ki kuma matsawa baya,kin manta sirri zamuyi,ko kina nayita daga sauti na bayan jiya kinsa maqogarona nata zafi har yau?''tilas ta zauna a hakan qamshin turaren da tun jiya ya fesa shi amma har yanzu yana tashi a jikinshi
''tambayoyi ne zan miki su da farlo wadanda nake buqatar amsarsu daga yau zuwa gobe da safe kafin ki bar gidan nan,kada kiyi tsammanin samun takardar sakinki daga gareni matuqar kika gaza amsa min tambayoyina cikin gamsashshiyar amsa,na farko mai yasa kika damu da abdallah da yawa,kika gaza barinshi yaci guba da aka zuba cikin abincinshi har sau biyu?''da hanzari ta dago cikin mamaki da tsoro ta dubeshi,yaushe abdallah yasan da maganar gubar data hanashi ci?
gira ya daga mata yana mata killing smile dinshi
''hey,meye na tsorata haka,bayan tambayoyin basu qare ba,daya cikin wadanda zasu biyo baya fa''
sai ta duqar da kanta zuciyarta na dukan uku uku
''me yasa kika damu da sanin irin gubar da ake ahirin kasheni da ita sai da kika dangana da asibiti a washegari aka tabbatar miki da irin qarfi da illarta ga duk mutumin da yaci?,me yasa kika gaza barin gidansu abdallah duk da irin takura raini da abdalla ke miki?,me yake saki rudewa harda kuka duk lokacin da kika ganni kebe da wata cikin tsakiyar dare?suke nan tambayoyina''
gaza daurewa tayi a wannan karon ma sai data dago ta dubeshi cikin mamaki shin abdallah yasan akwai masu farautarsa ua qyale ya zuba musu ido?,tamkar yaji abinda take zantawa cikin zuciyarta yace
''kada kiyi tsammanin abdallah wawa ne bansana ana farauar rayiwanshi cikin gidan ubanshi ba,i know kuma zuwa gobe zaki ga abinda zaya faru,naki kawai answer din question dina.....gaba ta gaba,are you ready madam?''
kai ta sake gyada masa kamar qadangaruwa
''ok,mami is unaware game da wadda na aura,nayi haka ne saboda ina son inyi suorising dinta,ta bani komai a rayuwa bansan me zan bata ba,na sani baya ga ni kece ta biyu cikin diyoyin da take so,bata san diyarta na dawo mata da ita ba,na tabbata zatayi matuqar farinciki da mamaki da ganinki...saidai kinsan me?,farincikinta da mamakinta zai dore ne matuqar taji cewa auren so da qauna ne tsakaninmu,kinsan abun duba?duk wani motion da act namu zai zama irin na masoya a gabanta daga wunin yau zuwa goben tafiyarki babu musu tsakaninmu,yi nayi bari na bari wannan shine abubuwan da zasu sana miki takardar rabuwa da ni thats all''
gaba daya ji tayi ya daurera da duka jijiyoyin jikinta,wadan nan tsauraran sharuda har ina?,har gwara ya samu bulala ya bugeta yadda yakeso kana ya sallameta yafi nata sauqi,ina zata sami tulin amsoshin tambayoyinsa wadanda bata tab tunanin ma a kansu ba?me yake nufi yace da ita?,ama ture ta wannan baki daya,ya zata iya tanqwara zuciyarta ta nuna alamu na soyayya ga mutumin da babu so ko qwauar zarra tasa cikin zuciyarta.....
''idan kuma baki iya tsallake wadan nan abubuwa.....fine....sai ki shimfida ta barma da daura damarar zama da abdallah kiga idan bazai saceki gaba dayanki ma ba zuciyarki ba cikin kwanaki talatin kacal,hakan kuwa kinga bazaya miki dadi ba tunda kince wai baki sonshi bayan tsayin daka da kikayi wajen kare mishi ranshi da lafiyarshi don kina da buqatar ra......''
''naji....naji na amince''ta fada da sauri don katse soki burutsun da tace yana shirin yi mata
''good job,shikenan Allah ya bada sa'a''ya miqe daga inda yake,har yayi taku biyu ya kalleta still tana duqe
''kada ki manta da answer din tambayoyi na,don sune bqngare na farko na yarjejiniyar mu''
Sakaliyar la'asar ce data gama hada hadari wanda ya tilastawa garin lumshewa,sannu a hankali suke taku wanda idan ka gansu sai ka rantse shaqiqan masoya ne guda biyu hannayensu sarqafe cikin na juna,sanye suke da kaya kala daya saidai bambancin sunan yadikan,nata material ne na mata yayin da nashi ya kasance na maza,dukkansu sea green colour ne,abu daya zai saka duhu yadda fuskanshi ke qunshe da wani irin haske da annuri,yayin da nata fuskar ke duqunqune cunkushe da bacin rai duk da hakan bai hanata yin kyawu ba,maryam ne da abdalla kan hanyarsu ta zuwa gaida mami bayan ya tabbata da jama'ar gidan kowa ya koma inda ya fito
sunfi minti talatin cikin bangarensa yana nuna mata salon kallo magana da ladabin da yakeso tayi masa gaban mamin wanda hakan shi ya kusan janyo rikici
ya sake waiwaya ya dubeta suna gab da ahiga bangaren mamin kana ya dakatar da tafoyar tasu,tsatstsareta yayi da kallo,ta kauda kanta tana qoqarin sabule hannayenta dddaga cikin nashi
''malam bamuyi da kai zaka dinga min akallon mayi ba ko,idan kuwa kaci gaba daidai nake da na koma inda na foto na hada ya nawa ya nawa na koma inda nafi wayo''
''kya sha tsinuwar Allah data mala'iku,runda ko banza miji nake agareki koda qarshen duniya zaki gudu,nike ma da magana dake,kinfara karya wasu dokokin tun yanzu,wanda hakan na nufin tangal tangal da muradinki ne,haka koka ga fuskar amarya na kasancewa washegarin ranar da aka kanta,look at ur self don Allah,jiya kin kwana kuka idanunki sun koma kamar kumburarren qullin qosai,an samu da qyar sun daidaita kafin yamma,sanna kina son ki sake wargaza mana shiri,to wlh u hv to make sure idan kika bari mami ta dago wani abu babu ke ba samun takardar sallama''
wani tafarfasa zuciyarya ke mata,ta debi a qalla mintina biyar kafin ta iya controlling kanta ta sauyawa fuskarta mood sabanin na dazu,cikin tafasar zuciyq ta miqa masa hannunta shkuwa yasa nashi hannu ya riqe suka ci gana da tafiyarsu daga nesa tamkar ka sacesu don kyai tsaro da marching da sukayi
A guje ta juya kamar zata ci da baka ta koma bangaren nasu tana zabgawa nene kira,saura kadan ta take zubaida dake kwance agashiyyan wanda cikin nene adnan da zahariyya an rasa wanda zai ce da ita yi haquri ba don komai ba sai don tsananin haushinta da sukeji kan wanda ta shiga halin sabo da shi
da sauri nenen itama ra iskota don dana a tsaye take cikin safa da marwa
''yaya?,ya ake ciki?''
cike da tsananin tashin hankali kamar wadda aka gaya mata uwa da uba duka sun mutu tace
''wallahi nene yana nan bai mutu ba,tas na ganshi babu abinda ya tabashi wallahi,tare suke da yarinyar nan nene bata bar gidan nan ba,hannayensu riqe da juna,mun shiga uku nene kada dai ace ita ya aura?''maganar ba qaranin sa nenen tayi a tashin hankali ba,a aukwane ta juya kan kujerar data tashi zata dauki wayarta,garin rarumar wayar ta dauki remote,sai data fara dannawa ta lura ahine,wurgar da shi tayi ta suri wayar kai tsaye ta kira malam na hayi
Mgunyar dariya ya dinga kwarawa kafin yace
''sanda muka gudanar da aikin bata cikin gidan,don haka ki kwantar da hankalinki ki zuba ido kiga abinda zai faru,saidai babu lallai abunda zai farun ya zama abunda mukai nufi da shine,kasantuwar yarinyar na tare da shi''yana gama fada ya katse wayar,nene ta dubi wayar tana jadda maganar daya gaya mata,saidai ta samu relief jin cewa wani abu na iya faruwa da abdallan,nasu kenan yanzu zuba ido suga mai zai faru kenan?
cikin falon mamin babu kowa sai yan surutai da yake iya jiyowa cikin kitchen,hanyar saman mamin yai direct da ita,bai saki hannunta ba sai da suka dangana da bedroom din mamin yace zquna ina zuwa,cikin sassarfa ya sauko qasa ya dawo kitchen din
Tun daga falon ya soma qwala mata kira,ita da wasu mata ne su uku ta hudunsu baaba uwani da alama gyara kitchen din ake sakeyi da wanke abubuwan da suka babbaci
''omg,abdallah taushe zai girma ne jama'a''ta lumshe idonta tana fada jin irin kiran da yake mata
ya qaraso kitchen din cikin hanzarinsa ya kama hannayenta
''suprise mami suprise''yake fada cike da murmushi yana dubanta,sai ta dan hade rqi
''suprise wanne iri?wai shin ma wanne abu ne ya fito da kai daga gidanka?,salon kaci gaba da takuramin ya sanya kaqi tarewa gidanka kace sai bayan sati biyu''
''mami nidai kizo muje ols mami,nasan zan sanyaki fafincikin da kika jima baki irinsa ba''
''abdallah barni in gama da aikin nan tukun kahe zan sameka ko wanne irin suprise ne sai in gani''
ya langwabe mata kamar qanqanin yaro
''mami bana ao ya huce fa don Allah kizo muje''
baaba uwani ce ta sanya baki dole ta ajjiye plates din hannunta ta bishi tana mita shikam yana qyalqyala dariyanshin nan dake fidda sigar kyawunshi
*_kuyi manage da wannan pls_*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶4⃣0⃣
*_An karbo daga Abu Hurairah Allah ya qara yarda da shi,Manzon Allah S A W yace''ana bude qofofin aljanna duk ranar litinin da alhamis,sai Allah ya gafartawa ko wanne bawa musulmi indai ya kasance baya shirka baya hada Allah da abokin tarayya,sai dai wani mutum wanda ya kasance akwai qulli ko gaba tsakaninshi da dan uwanshi musulmi,sai ace''ku qyale wadan nan har sai sun shirya,ku qyale wadannan har sai sun shirya_*
mami na gaba yana take mata baya,sai mita take masa na ya tasota tana cikin mutane,shidai baice uffan ba in banda murmushi da yakeyi,suka ahiga falo tana qoqarin zama yace
''a'ah mami mu qarasa daki''
''kai abdallah.....abdallah trouble maker,muje dai inga suprise din nan da aka hanani sakat,amma ka tabbata indai bai kai ya kawo ba to zan ck tararka''
''na amince,amma mami idan ya kai ya kawo din fa,me ni kuma za?a bani?''
''sai abinda naga ya dace....''
''zoben daddyn dake gunki kadai nike so''
hara rarshi tayi lokacin da take tura qofan bedroom din nata
''kayi kadan yaro,gwara ka fadi amount na kudi in baka da na baka wannan zoben,bakasan tarihinshi bane har yau.....''
maganar ta maqale mata saboda ido hudu da sukayi da maryam,jikinta a sanyaye hankalinta a tashe ta nufeta ta kama kafadunta bayan ta zauna kusa da ita
''maryam,lafiya?daga ina?,ya akayi ika baro gidanki a idin wannan lokacin?,ina fata ba matsala bace ta faru?,ina maigidan naki?''
''gani...''taji ance,ta waiga da sauri don tabbatarwa,shaf ta mance ma tare da abdallan suka shigo sai da yayi magana
harararshi tayi
''kaga malam bana aon wasa,fice min a daki zamuyi magana''
idonshi ya kanne guda daya h
gami da daga girarshi
''wannu batu kam ai mu ya shafa mami,nima diyankin ne,nine kuma mijin diyar taki dai,tuwonki manki''yayi maganar yana zama kusa da mami hade da dora kanshi saman kafadarta suka sanyata a tsakiya
Ba don murmushin dolen da maryam ta qirqira ta dorawa allon fuskarta ba da babu shakka mami qaryata abdallah zata yi,duk da hakan sai da ta dubi maryam din
''bana son shashanci,maryamu gayan meke faruwa?''
da sauri ya karbi zancan
''ko zan miki wasa kan komai mami bazan miki kan wannan ba,idan maryam bani ta aura ba ina zan ganta ma a irin wannan lokacin naje na daukota''sai ya dawo gaban mamin yayi zaman dirshan harda lanqwashe qafafuwa,ganin haka yasa maryam itama zamowa tayi irkn zaman da yayi gabam mamin,saidai ita zuciyarta cike take da rauni,badon namijin qoqarin da take ba wajen danne zuciyar tata ba da tuni hawaye ya fallasa fa,cike da salo na iya sarrafa harshe cikin nutsatstsiyar muryarshi yace
''mami,zai iya yiwuwa kiga na miki qaton laifi,zai iya yiwuwa ma daga qarshe kice sai kin hukuntani kan maganar da zan gaya mikin yanzu,maryam bata da laifi ko daya don ni na nemi a boye abun,mun fara son juna har ta kaimu ga buqatar muyi aure,na boye miki ne mami saboda ina sane da dimbin so da qauna da kike wa tilon danki,farinciki bazaya bari idan na sanar miki ba ki kasa sanarwa da wasu mutanen ba musamman wadanda muke zqune gida daya da su wadanda bana buqatar kowa ya sani cewa maryam nake da muradin aura saboda tsaro,mami kinfi kowa sanin irin traps din da na shiga,an farauci dayuwata ba sau daua ba ba sau biyu ba kuma sau uku ba,wadansu trap din sun yi aiki wasu kuma Allah ya kareni basuyi tasiri ba,na tabbata da ansan maryam ce wadda zan aura ba abun mamaki bane wani mummunan abu ya faru da ita''
''mami...ga maryam nan ta sake dawo miki a karo na biyu,saidai wannan karon uasha banban da sauran lokutta,wannan karon ta dawo gareki da matsayi guda biyu,diyarki kuma aurukarki,nayi kwadayin ganin irin farincikin da zako shiga ta sanadiyyata ne mami shi yasa na sake dawowa da maryam cikin rayuwarmu,sanin maryam kikayi mami a fili amma a badini nafiki saninta kuma zuwa gobe zan warware miki ita don wace a sarari ki gani,ina fatan samu sassauci cikin hikunci boye miki wadda zan aura da nayi mami na''
ga mamakinsu saiga mamin itama ta sauko gabansu,hawaye ne bisa fuskarta wani na nin wani,a rude abdallah yasa hanninshi yana shate mata hawayen
''idan na bata miki mami kiyi haquri,hawayenki bala'i ne mami a gurina''
sai ta kasa cewa komai,jikinta ta janyosu gaba daya ta rungumesu
''barni abdallah na nayi kuka,kuka ne na tsantsar farin ciki ba baqinciki ba,tabbas addu'a bata faduwa qasa banza,na jima ina addu'ar Allah ya baka mace ta gari,lokacin da maryam ta shigo rayuwarmu na fuskanci dukkan halayenta na gari sai maji ina maka sha'awarta,domin hasken alkhairai da nake iya hangowa qunshe da ita,ganin hankulanku bai gamu guri guda ba yasa na fidda burin daga daina na dungumi yi muku addu'a gaba dayanku,kai har wayewar garin yau maryam ce a raina da ita na tashi har ka cimmani a kitchen tunanin maryam nake''
ta janye daga jikinsu bayan ta dauke qwallar idonta,kama hannun abdallah tayi da na maryam ta hade guri guda bayan ta dora nata a saman nasu
''na godewa Allah da irin wannan zabi da ya mana baki daya,naji dadi matuqa da kasancewarki maryam cikin zuri'ata,maryam,ga abdallah nan amana ce na baki ita har bayan raina,na baki amanar abdallah har abada,bani da kowa sai shi,ki zauna da abdallah cikin amana da aminci,abdallah kaima na baka amanar maryam,matuqar ka cuceta bayan zamowarka miji a gareta ban yafe maka ba,ku kula da junaku''abinda ta fada kenan tana jijjiga hannunsu
Duk yadda yaso ya daure sai da ya kasa,qaunar shi da maryam qarara yake ganowa cikin idanun mamin,baiso maryam din taga kasawarshi saboda haka ya kifa kanahi saman hannun mamin ya sumbata cikin dabara ya goge qwallar idonshi
''nikam na dauka mami,na dauka,Allah ya tayani riqo''
''kefa maryamu na?''ta fada tana kalllob maryam wanda kanta ke duqe take cure guri guda,abune goma da shirin suka cunkushe a qwaqwalwarta,zuciyarta na gaya mata wayo kawai abdallah yayi mata,mai yasa bata bar gidan salin alin ba tare da mami ma tasan wadda abdallah ya aura ba bare ta mata wanna kandagrakin mai daddaure jijiyoyin jiki?,zata iya watsawa mami mai dimbin alkhairai da karamck qasa a ido koko zata yarda ta zauna da abdallan ta sarayar da dukkan wani haqqi da 'yancinta da ya take,ya aureta ta sigar 'yar burum burum,zata barshi yaci nasara a kanta ya sameta a bulus ya sameta ta sigar qarfa qarfa da banga banga?,wani sashen na zuciyarta ke mata qarfafa ata gwiwar alqawari ya daukar mata,kuma ta riga da ta cika masa gabar farko na yarjejeniyarsu,bata jin kuma zai karya alqawarin
daga qasa kuma hannunta yaketa yamutsa mata cikin wani irib salo da yake sa taigar jikinta tashi saboda nata hannun na kife ne cikin nashi tafin hannun,dob samun hanyqr tsira do son cire hannunta daga nashi tayi saurin cewa
''na karba mami,insha Allahu''cikin zuciyarta tana sauya qudirin ma'anar na karba in don kada Allah ya tuhumeta
Mami dake sauri ta koma gun mutane sai gata ta rashe a cikinsu,hira sabuwa ta barke duk da maryam na rakube gefe guda,ga zaton mami surukuta ce da kunya irin wadda tasan maryam din ko da can baya da ita bare yanzun,saidai ga maryam kuwa takura ce data sanyawa zuciyarta na nemo amsoshin tambayoyin abdallah,sai ta hada amsar sai taji duka sun wargaje,idan ta kamo nan ta qulla da can sai ya tsinke,ita kanta ta rasa dalilin da ya sanyata kasa barin gidan a lokacin da ta fahimci abunda ke faruwa,dik da tana ta bawa kanta amsar cewa girma da darajar mami ne saidai ita a karan kanta take jin amsar ba gamsashshiya bace bare ta doshi abdallah da ita
''ina zuqa,bari naje kitchen indauko wayat na kira mr stephien,dinner nakeso a shirya mib sabuwa daga nan zuwa takwas na dare a compound din gidan nan''mamin ta fada ikin zumudi da farinciki tana fita daga dakin
bayan fitarta shiru ne ya biyo baya,abdalla nata qate mata kallo ba tare data sani ba don kanta na duqe ne
''sai faman duqar da kai kike kamar wata mai gajeran wuya,amma dai ba haka mukayi da ke ba ko?,sauran qiris ki wargaza wannan matakin da kika kusa kammalashi,ki tashi ki dauko drink cikin fridge ki zuba kin,ki kuma zauna agaba na har sai maki tazo ta ganmu a haka dn mu sake wanke zuciyarta''
batasan lokacin da ta dago ba ta kalleshi da oily eyes dinta ba ta balla masa harara,idanu ya lumshe yana jin wani abu na tsirga masa,ko banza buqatarsa ta biya,burinshin dama ya kalli oily and brown ayes nata wanda tun jiya rabonshi da su
''ka isa ma?''
''haka kika ce?''
''eh''ta bashi amsa kanta tsaye tana kawar da kanta daa kanshi,gyada kansa yayi cike da mamakin tsiwarta
''za kuwa kiga kalar tawa isad,ki bar gani na kodaki gaban mami na baki muhimmanci,ina iya qin sakin naki naga wanda ya isa ya sani in sake ki''
bata san lokacin da kuka ya qwace mata ba
''tabbas abdallah ya gama raina mata hankali,a daki mutum a hanashi kuka haka ake,ita da ya kamata a lallaba ita ake raina ma wayo
dauke kanshi yayi gefe guda tamkar bsi damu bs,saidai shi kadai yasan zugin fitar hawayenta da yakeji,hakan ya sashi gaggawar fadin
''Allah ya baki sa'a kici gaba sa kukan har mami tazo ta ruskeki a haka,idan tabi ba'asi kuma na warware mata zare da abawa kinga daga haka ta daina ganin girma da mutuncin mu baki daya,ni kuma naqi sakinki tunda igiyar na hannu na,qarshe kiyi biyu babu''
Jin hakan ya sanyata miqewa da hanzari kuma cikun nutsuwa ta durfafi fridge din,binta tayi da kallo a sace sakamakon yadda rigar tabi jikinta ta fidda surarta,ta ciro lemon ta dauki glass cup saman fridge,gabanshi tazo ta tsaya ta tsiyaya mishi ta miqa masa,qi karba yayi sai harara ma da ya gallamata
''kina tsammani idan mami ta shigo ta taddaki a haka kina bani abu ba zata zargi komai ba?kin min tsaye a ka kamar zamu shiga filin yaqi''
cikin qufula da hasala tace da shi wasu hawayen sabbi na bullowa
''ya isheni ya isheni fa,don me zaka dinga juya ni kamar wata waina,wannan wanne irin abu ne?''
sake dauke kanshi yayi
''har yanzu ke din a matsayin matata kike,ko babu yarjejiya tsakaninmu dole kiyimin dukka abinda nace tunda ban sakekin ba,ruwanki ne ki rusuna ki bani ruwanki ne ki bar leminki nima na riqe aure na''
ba maganar da taqi jinin ya fadeta kamar wannan,tilas ta rusuna ta miqa masa,sai da ya wani sha qamshi kafin ya karba,bayan zuciyarshi cike take fal da tausayi da qaunarta,daga shi sai Allah sukasan abinda yake ji cikin zuciyarsa
Ai kam a hakan mamin ta samesu
''a'ah me ya sameki maryam?''caraf ya karbe
''don nace ta miqon drink''girgiza kanta mami tayi tana miqar da ita tsaye
''a'sh banson sharri,bansan maryamu da qiwa ko ganda ba bare kan mijinta,halan bata da lafiya tafiyanne batasonyi ko?''ta fada tana kallon maryam,sam ita bata fahimci ma'anarta ba rashin sanin me zata ce yasanyata saurin gyada kai don shine kadai mafita
''ayya sannu,hau gado ki kwanta bari in lalubo miki magani,kai kuma banason takura ka qyaleta ta huta har ta warke,ko kuma na riqeta anan idan bakayi wasa tayi sati''
Wayyo Allah,ai duka sai a lokacin suka fahimci inda ta dosa,a tare suka hada ido ita da abdallah,wata iriyan kunyanshi da bata taba jin irinta ba ta saukar mata,da sauri taja idonta ta qulke gam,shi din na da sauri yaja qafafunshi ya fice a dakin don bazai iya hada ido da mamin ba tunda kallon da take masa kenan,ita kam ko a jikinta,cikin gurin da take ajiyar magungunanta ta duba ta fito da pain killer da paracetamol ta hado da ruwa ta kwowa maryam din
''tashi kisha kinjk marya,kada ki biyewa abdallah ya cutar da ke ba tare da kin warke ba,idan kinga ma da takura kimin magana zan maganinsh don nasan halinshi da rawar kai sarai,idan kinki jikin bai miki daidai ba ki sanar min sai a haqura da dinner din''ita dai kamar qasa ta tsage ta shige haka ta dinga ji,wannan abun kunya har ina,sai da taga ta sha ta kwanta taja mata bargo sannan ta fice a dakin
Tayi nisa sosai cikin saqe saqe da tunani taji dumin mutum a bayanta wanda sam bata san lokacin da ya shigo din ba,a zabure ta miqe zata sauka ya damqeta da hannu daya
''kiyi a hankali kada ki fama ciwon naki''ya fada cikin salon rainin wayo,kasa motsi tayo abdallah zai kasheta kam wallahi,sai kuma ya hade rai
''kikaci gaba da kuka zuwa anjima idanunku zasu kumbura,kinga idan anzo dinner sai ki tanadi amsar basu''ya miqe tsam daga gadon ya fice abinsa adakin bako waiwaye,ajiyar zuciya ta saki,sai da ya fita din sannan taji kamar ta bishi ta rufe da duka,gaba daya ma shi babu abunda ya shalleshi,babban isue da ya kamata ace yana cikin rashin nutsuwa amma ko a jikinshi.
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Bayan ta kammala sallar magariba mami ta shigo
''yaya maryamu jikin,dinner din zai yiwu kuwa?''
kanta a duqe ta amsa mata da eh don kawar da zargin da mamin keyi na wani abu ya faru da ita,amma a zahiri ba don wannan zargin da mamin keyi ba da cewa zata yi bazata iya zuwan ba,saboda har yanzu zuciyarta cikin qunci take,nan mamin ta sakata ta shiga tayi wanka duk cikin dakin,mai makeup ta tadda na jiranta,hakanan tanaji tana gani ta zauna aka zuba mata kwalliya ta gani ta fada aka sata ta shirya cikin wedding gown irin ta larabawa fara tas mai dige digen adon zaiba kadan kadan,rolling aka mata sak irin na larabawan wanda iyakarsa saman qirjinta,hill shoes shima da earings sarqar hannu data qafa duka ruwan zaiba ne.
Kada kaso kaga kyawun da maryam din tayi,kusan duka cikin event din bikin da suka gabatar wannan itace shiga mafi kyau da tayi.
Tana zaune nan cikin bedroom din shiru kamar yadda mami ta umarceta,qofar taji an turo wanda kafin ma ta daga kanta taga waye qamshin turaren data jiyo ya sanar mata,saboda haka taci gaba da dauke ganinta daga bakin qofar,tsayawa yayi kawai ya zuba mata ido cike da sha'awa da burgewa,tayi masa kyawu fiye da tunani,bai qara amanna da kyawun da Allah ya bata ba irin yau,kasa controlling din kanshi yayi ya miqa hannunshi da nufin shafa lebenta da yaci jambaki maroon colour,har ya kusa da ita kome ya tuna kuma sai yayi saurin janye hannunsa ya daidaita nutsuwarsa hadi da cunkushe fuska
''ki tashi muje mu ake jira''
sai a sannna ta daga kai ta kalleahi cikin sakannin da basu wuce uku ba ta qare mishi kallo
eh yes ta yadda abdallah mai kyau ne,sanye yake cikin jacket mai bala'in tsada da kyau fara tas da ita komai nashi farine idan ka cire necktied dinshi takalmi da agogonshi duka ruwan zaiba kalar nata shigar sak,kau da kanta gefe tayi don bata son fiya hada inuwa da mutumin da ya yiwa rayuwarta karan tsaye
''kayi naka wuri nima nayi nawa''sunkuyowa yayi saitin fuskarta har numfashinsu na gware
''kin manta a idanun duniya mu masoya ne da mukayi auren qauna,qwarai ni airen qauna nayi amma ke da aka yiwa auren dole na fada miki dole ki ari acting na ma'abota so ki dorama kanki matuqar kina buqatar cikar burinki,wannan ne magana ta da ke na qarahe,harshe na ya gaji da yi miki tuni''
Kanta ta sake kaudawa ta yadda babu yadda zai iya ganin hawayen dake qoqarin fita a idanunta,cike da zafin rai tace
''saidai kayi dukkan abinda kaga zakayi,kaga,nifa na gaji da wanna game din naka,kawai ka sallameni a yanzu na san inda dare yayi min''
''idan anqi fa?''
ya fada bayan ya miqe tsaue ya goye hannauenshi a qirjinsa yana leqa dan qaramin bakinta dake raahin kunya
''tilas ma ka sakeni tinda nace bana so bana yi akai gaba wataqila asamu mai tayawa''
Yaji zafin maganarta amma son biye mata balle a gamu da matsalar da tafi ta baya
''lallai kam yarinya wuyanki yayi kauri,naga alama kinga makwancina da yawa,don kin samu kamar ni abdallah na nuna sonki har na aureki kikeda bakin fadin haka,kinsan kalan 'yammatan dake rububi da fatan na zame musu miji ba tare da aisin kwabo na ba ma?''
A sukwane ta juyo tamkar mai jiran ya gama fada,ido cikin ido tace masa
''ni ba irinsu bace,na sha ban ban dasu nesa ba kusa ba,baka yimin ba sam ko kusa ko alama,kuma na fada na gaya maka bana sonka bana buqatar igiyar aurenka a kaina,ka ssakeni mana dole ne,kaje ka auri masu rububin naka,idan ka taya akace ba'ayi ai sai ka matsa ga masu yi inda kake da muhalli,bawai ka tsaya ka nace a inda babu muhallinka ba''
Mamaki kam kusan kasheshi yayi a tsaye,gadan gadan ya nufota yana fadin
''ba irin mu mace ke kalla kai tsaye tace bata son mu ba duk isarta da tsadarta,bamu cewa muna so ace ba'a son mu,ni abdallah na miki alqawari sai na azabtar da zuciyarki da kalar soyayyar da baki taba yiwa wani da namiji irinta ba''bai bata damar furta komai ba ua sirute gaba daya ita da wedding gown din nata harda 'yar purse dinta marching na kayan,dike doke da zille zille ta fara tana fadin ya saketa ita ba 'yar iska bace yana sauka daga step din benen zuwa falon mami na qasa yana fain shi kuma tantirin dan iska ne sai yaya kenan?
kafin su qaraso falon tuni ta soma jiqa fuskarta da hawaye,ajjiyeta yayi saman kujera ya dora qafansji daya saman kujerar kusa da cinyarta yana huci kadan kadan,sai da ya gama qare mata kallo kana ya bude 'yar jakarta dake hannunshi yaci sa'a kuwa ya samy tissue turare da powder,cirosu yayi ua cilla mata
''ki gyara fuskanki nan da minti biyu''
cikin muryar kuka tace
''idan naqi fa?''
wani dan gajeran qayataccen murmushi irin na gefan baki yayi idanunahi sun kada sunyi ja don ta soma bashi headach bai taba fuskantar irin wanna trouble ba daga gun mace,idan suka botsare basu da dadin sha'ani saidai ka bisu ta yadda suke so ka ka musu jan ido.
''meyi baya fada,kiqi yin kiga mai zai faru a aikace kinga ai yafi dadi akan na fada miki da baki''ya sauke qafanshi ya nufi fridhe ya ciro sassanyar ruwan swan na madaidaiciyar roba ya soma daddaka,sai da ya shanye tas ya juyo inda take,tuni har ta gyara atsoronta na kada ya hanata takardarta,tamkar ya qyalqyale da dariya sai kuma ya maze yasha mur
tana shirin miqewa ya hangi igiyar takalminta ta kwance da sauri ya duqa don daure mata zata ja baya ya riqe qafan gam ya soma daure mata,lokacin mami ta ahigo tana fadin har yanzu basi fito ba me suka tsaya yi ne?,yanayin data gansu ya matuqar burgeta ta sake amanna da soyayyar dake tsakaninsu,tayi murmushi tana tunanin tana tsakiyarsu basu taba nuna mata soyayya suke ba saima fada kullum ashe ninketa suke baibai.
Compound di ya cika babu laifi da jama'a,wanda kusan rabinsu duka 'yan uwane irin mugun na jikin nan sai daidaikin maqota da abokai,tayi mamkin yadda adan taqaitaccen lokaci irin haka ma aka tara jama'a mai dan dama har haka,ko ina ka duba gurin walwali yake da decoratiom na farin yadi da wasu fararen fitilu,komai na gurin fari ne hatta da kayan mahalarta taron farine
tayi mamaki da ganin raliya da nasir lubabatu qanwarta batulu harda hindatu da jabir,to wama ya gaya musu wa ya gayyacesu?,daga sashi guda kuma nene ce da adnan sai zahariyya,idanun zahariyya da nene na kan abdallah duk wani motsi nashi suna ankare da shi,fatansu daya suga mummunan sauyi tattar da shi,yayin da adnan ya tattara nashi ma mujiyar kan maryam wanda babu abinda yake sai aukin hadiyar yawu,cikin zuciyarsa yana yiwa nene Allah ya isa da ta hanashi mallakar maryam din har abdallah ya sameta,gefe guda kuma yana tainewa abdallahn yana fadin duk taurin ranshi ne ya jawo,amma yaci alwashin da zarar burinsu ya gama cika kota tsiya kota arziqi sai ya mallaki maryam din,ko nenen na so ko bata so,kai baiqi ya kawar ma da duk wanda zaice zai kawo masa cikas ba,zubaida na gida nene ta qulleta cikin dakinsu kana ta qullen bangaren ma baki daya,ta rantse ta maya babu inda zata fito har a watse.
cikin wani irin salo mai qayatarwa dinner din ta dinga gudana,kowa ranshi fari tas cikin burgewa,tana zaune a muhallinta suka mutane suka dinga zuwa suna gaisawa da taya su murna,saidai babu daya cikin yammatan da suke son Abdallah data gani a gun,da alamu kuwa hansu zuwa gun akayi,kodai iyaye ko yan uwansu,qarfe aha daya aka taahi kai tsaye mami tace su quce bangarensu maryam taje ta kwanta ta huta.
Yana iya hangota cikin dan qaramin hasken fitilar barci takure saman gadon yayin da shi kuma ke kwance saman sofa din dake cikin bedroom din,a haka sai kayi tsammanin bacci suke saidai ko kadan kowannansu da duniyar daya shiga ita nata tunanin har yau kan amsar tambayoyinne da takeson bada su a gobe batasan ta samu failure,ya miqe ya ciro paper cikin ma'ajiyar da yake ajjiye takardu yar qarama dake can qasan gadon wanda sai ka danna wani abu take iya bullowa ya hada da biro ya dawo yayi kwanciyar rigin gine ya soma rubutu ajiki.
a qalla mintina goma ya samu kyawawa yana ruutun,a hankali yaji jikinsa ya soma masa nauyi tamkar an dora masa dutsen dala,ya sake yunqurawa da nufin daga hannun nashi a karo na biyar saidai ko alamar motsawa baiyi ba,wasa wasa sai magana ta zama babba,ya bude bakinsa da niyyar yin magan amma sai yaji kamar super glue aka saka aka manne fatar lebansa ta sama da qasa saidai.
Cikin mintina da basu gaza ashirin ba komai nasa ya daina motsi face idanunshi da kunnuwansa dake iya jin abinda ke motsi da qara baya ga haka babu wani abu dake moruwa,tuni takarda da biron hannunshi suka sulale suka fadi qasa,hannayen suka zube gefe guda,gasu a jikinsa amma ji yake kamar an cire masa su su da qafafunsa.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶4⃣1⃣
👂🏾👂🏾👂🏾👂🏾
*shin ka/kina da labarin mutune guda bakwai da zasu shiga inuwar al'arshin ubangiji ranar da babu wata inuwa sai tasa?,ranar da rana zata matso daf da kawunun al'umma ta dinga tafasa qwaqwalwansu?,to ku matso kuji daga bakin da baya qarya*
*_An karbo hadisi daga abu hurairah R A yace:Manzan Allah S A W yace: mutane guda bakwai Allah zai saka su cikin inuwarshi,ranar da babu wata inuwa sai tasa_*
1⃣ *_shugaba adali_*
2⃣ *_da saurayi matashi ko matashiya da suka rayu cikin bautawa Allah mai girma da daukaka_*
3⃣ *_da mutumin da zuciyarsa ke rataye da masallaci,ma'ana wanda ko yaushe jira yake yaji anyi kira zuwa sallah ya tafi masallaci_*
4⃣ *_da mutane guda biyu da suka so junansu saboda Allah,don Allah suka hadu kuma suka rabu donshi ma'ana badon wani harkar banza ba ko duniya_*
5⃣ *_da mutumin da mace ma'abociyar kyawun sura tayi kiransa zuwa yin zina ko aikata wani fasiqanci yaqi yace mata ni ina tsoron Allah_*
6⃣ *_da mutumin da yayi sadaka ya boye yin sadakar da yayi har hannun hagunsa baisan me damansa ta ciyad kota bayar ba_*
7⃣ *_da mutumin da ya tunq girma Allah a kebe shi kadai idanunsa suka zubda hawaye saboda tsananin girma da tsoro Allahn_*
Duk yadda abdallah ya kai ga son motsa sassan jikin nasa bun ya faskara,ya yarda ya kima saddaqar da cewa wani mummunan abu ya gama faruwa da shi,tamkar wanda dannu ya danneshi haka yake ji
babu tsumi babu dabara sai Allah haka yake ta faman ambata
sam bata san halin da ake ciki ba,saidai gaba daya ta nemi bacci a idonta ta rasa wanda ta alaqanta hakan da damuwar dake cunkushe cikin ranta,tayi juyi kan gadon yafi a qirga,ba zata iya tantance lokacin da bacci yayi gaba da ita ba
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
qarfe biyar da rabi na asuba ta farka daidai lokacin da wasu masallatan suka kai tsakiya a sallarasu,da ddu'ar tashi a bacci ta farka a bakinta kamar yadda ta saba sannan ta lalubi wayarta don jaska dakin da babu wadatar haske a ckinsa sakamakon kashe qawayen da akayi,sai data lalubi makunnin ta kunna sanna ta sauko daga gadon,a hankali idanunta suka sauka kan abdallah wanda zuwa lokacin ya rufe idanunsa gam zuciyarshi kawai ke aiki,ya gama amanna cewa tashi ce ta zo qarshe abinda yake jira kadai shine fitar ruhinsa daga gangar jikinsa,kamar ta wuceshi sai kuma taga bai kamata ba tunda dole dai ya tashi yayi sallah.
ta tsaya saitin kanahi cikin muryar dake nuna alamun yanzu aka tashi daga barci tace
''ka tashi kayi sallah lokacin sallah yayi,anyi asuba''jin ahiru ya sanya tayi zaton ko bai farka bane,amma wannan wace idiyar kwanciya ce haka yayi ya yada hannun?,sai ta dan duqa tana bubbugar filon da ya dora kanshi tana sake fadin
''anyi sallar asuba an kusa idarwa''
jin muryarta ya sanyashi bude idabun nashi a hankali tamkar mai tsoron ganin wani abun,sai ta dan zuba masa ido ganin yadda qwayar idanun tayi jazur,a sanyaye ta juya ta ahige toilet ta daura alwala ta fito ta tada sallah,ganin har ta idar bai tashi ba ya sanyata tayi zatob ko komawa ya sakeyi ne
kanshin ta kuma komawa ga mamakinta sai taga idanuwanshi biyu
''lokacin ta zaya fita alfijir na ahirin ketowa''
''bazan iya taahi ba maryam duk yadda naso hakan,ji nake kamar an daddaureni,ki taimakamin in tashi''abinda yake aon fada kenan saidai ina bakin yayi nauyi,ci gaba kawai yayi da kallonta,saita tsinci kanta itama da kallon nashi,lokaci guda kuma taji jikinta ya mutu murus,komawa tayi bakin gadon ta zauna ta inda take iya fuskantarsa suna ci gaba da kallon juna
kusan mintina talatin suna a haka har shida da rabi
''rana fa ta fito ba zakayi sallar bane?''sai taga ya maida idanun nashi ya lumshe,hakanan gabanta taji yayi wata mummunan faduwa,sai ta kasa zaman ta qarasa inda yake,abu na farko data fara lura da shi shine hannunshi da ya zamo qasa tunda ya farka bata ga ya gyara kwanciyarshi,ta sanya hannunta tadaga hannun taga ko zai gyara saidai tan sakinshi ya biyo ta,ta sake gwadawa har sau biyu babu banbanci
batasan lokacin data furta
''abdallah lafiya kuwa kake!''cikin tsorata da rudani
idanun nasa dai taga ya kuma zuba mata tamkar zai hadiyeta,sai ta shiga kiran sunansa a jejjere saidai ko guda bai amsa mata da shi ba
Lokacin da zuciyarta tayi mata hasashen abinda ya samu abdallahn jiri ne ya debeta ta zube a nan tana fadin
''me ya sameka?,me ya sameka don Allah abdalkah,ka bude baki ka gaya min''
inda zai iya da ya mata maganar amma babu iko
sai kuma ta zabura ta miqe da gudu ta fice a sashen nasu tayi bangaren mami
da sauri nene ta toshe bakin zahariyya da ta dan saki ihun farinciki ganin shigewae maryam bangaren mamin a hargitse
''nene Allah yasa ya sambade lahira''
''ko bai mutu ba to yana kan hanyarshi ta mutuwar''ta fada tana duban zahariyya
''don da ya kammla wucewar da ihun kururuwatsu kadai ta ishemu albishir''
saman mamin ta haura kai tsaye ta fara bubbuga qofar dakin nata ba qaqqautawa,tunda taji bugun ta tabbatar ba lafiya ba,ga zatonta ma abdallah dinne,tunda ta tashi dama takejin jikinta ba normal ba yadda ta saba jinsa,da hanzarinta ta murza muqullin ta bude qofan,kama hannun maryam tayi wadda taga tsagwaron rashin hankali kwance kan fuskarta
''lafiya maryam ne ya faru?''
fara jan mamin tayi
''mami zo kiga abdalkah,zo ki ganshi mami...''ta qarashe cikin rushewa da kuka
''Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla,wa anta taj'alil hazna iza shi'it sahla''addu'ar da mami keta maimaitawa kenan fili da zuciyarya cikin sassarfa take biye da maryam suka gifta su nene dake labe jikin window dinsu suna jiran jin abinda zai biyo baya
Yadda ta barshib hakan suka sameshi,a raunace mamin ta isa gaban kujerar ta zube,gaba daya rungumoshi tayo tana kiran sunanshi,ita din ma saidai kallo da ido daga bisani ne hawaye ya gangaro daga ianunshi saboda ganin mamin nashi na kuka haiqan babu kuma baki ko hannun lallashinta,kjran sunan Allah kawai sike daidai lokacin da nene ta shigo dakin a rude kamar gaske
kallon da abdallahn yake mata ya sata tasha jinin jikinta,saidai ta nasar kawai don babu baki ko qarfin yin wani abu a kanta,tana ma sa masa tsammanin wuta zai qara zuwa lahira,
wani kallo ta jefi maryam da shi tare da zabura ta kai mata duka''me kika yi masa muguwa azzaluma''
mami ce ta tare dukan
''haba nene''cike da haqiqancewa tace
''wlh ban yarda da yarinyar nan ba bintu,daga aure jiya jiyan nan ace mutum ya kamu da irin wanna lalurar?,anya ba mayya ya aura ba bintu?''
''me ya kawo duka wannan zancan nene,muyi ta lafiyarsa ma mana''
kuka ta dinga yi haiqan tana fadin duk daren dadewa asirinki sai ya tonu shegiya mayya daga jiya zuwa yau kin lashe kurwar yaro saboda tsabar shahara a maitadaga bisani saiga zahariya da adnan,abun nasu ma sai ya zama over acting,don mamin ce ke masu suyi shiru
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Ranar basu kwana gidan ba cikin asibitin amalam aminu kano suka kwana,cikin kwana biyar babu irin gwajin da basuyi masa ba,saidai komai ya nuna normal yake qwaqwalwarsa spinal code dinsa da zuciyarsa kai har hanta da qoda duka sai da suka duba saidai result sai yazo komai normal
A lokacin zaka tausaya wamami da maryam idan kaga yadda suka koma,duk da qoqarin boye cutan da ake saboda yanayin aikin abdallan,shi kanshi ya rame saboda tashin hankalin da yake gani cikin qwayar idanun maminshi da maryamu
cikar shi sati guda suka koma gida mami ta bada umarni ayi musu visa cikin satin zata fita da shi,kafin nan daya daga cikin manyan security dinsa mubarak wanda yake babba ne cikin masu tsaron lafiyanshi da hisham amininshi ke taimaka su mamin gun kula da abdallah,kamar daga shi zuwa toilet da sauransu,mutum ne mai matuqar kirki mubarak kamar hisham,har albashinmubarak din mami tace zata dada yace baya buqata,babu irin alkahirin da abdallah baya musu don haka bashi da abunda zai sakq masa da shi sai ta wannan hanyar,haka hisham babu komai tsakaninsa da mamin sai fatan alkhairi da sa masa albarka.
Batun fitar da abdallahn da za'ayi yayi masifar daga hankalin nene ta soma zaton kada fa a kaishi wajen ya samu sauqi haj bintu ta dawo musu da hannun agogo baya,don nene ta gama tsorata da irin kallon da abdallan ke binsu da shi duk lokacin da suka shigo duba shi
bata bata lokaci ba ta koma gun malam na hayi ta zazzage masa bakin jaka tare da qarin buqatunta
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
Misalin qarfe sha daya ne na safiya suka gama waya da mama ta kirata don jin jikin abdallahn,tana shirin ajjiye wayar taga har sha daya da minti goma,mamaki da fatan Allah ya sa lafiya maryam din ke tayi jin shiruchar yanzu mami bata leqosu ba
mawuya cine qarfe takwas ta gita bata shigo ta dubasu ba,haka nan ba zata tafi ba sai mubarak da hisha amininshi sunzo sun gyara abdallah ita kuma maryam din ta shirya breakfasy ta gyara bangaren nasu ta miqawa mamin break din ta bawa abdallan da kanta sannan taje tayi wanka,to yau kam duka mubarak ne yayi hidimomin shi kadai ita kuma tayi saura,da taga shabiyun rana ta kusa sai ta sanya hijabinta taga gwara taje ta duba mamin,don ta tabata ko bata da lafiya ba zata iya zama ba sai tazo ta gansu
sai da ta sake leqawa bedroom din abdallah ta taddashi har yanzun baccinsa yake don ko break baiyi ba,a haka fes da shi sakamakon kyakkyawar kulawa da yake samu,sai ka rantse lafiyanshi lau,kyau dac kwarjininsa duk suna nan sai 'yar rama da yayi,tausayi yake bata sosai,ta sake girmama kadaitar zatin Allah,dan adam ba'a bakin komai yake ba,yanzu kake mutum yanzu kake ba mutum ba,duk kuwa kyau asali dukiya da kake da shi idan yaso sai ya maidaka abun Allah sarki
ta share hawayenta sannan ta fito daga sashen,sai data tsaya ta tabbatar ta qulle ko ina don yanzun bata yadda da kowa ta barshi daga shi sai abdallah idan ba mami ko mubarak ba
Ba zato taji ansha gabanta,da sauri taci burki tana dubanshi,adnan ne ya tsaya yana qare mata kallo kamar wani tsohon maye
''babe ina zaki haka?''duk wanda ya fito daga tsatson nene yanzu haka ta tsaneshi bata qaunar ganinsa,hakanan taji bata qaunar koda hada inuwa guda da su,tsaki ta ja kana tabi ta gefansa da niyyar rabeshi ta shige,sai ya sake binta ya tare hanyar yana fadin
''haba baby ki tsaya ki saurareni mana,nifq sonki wallahi nake ki bani dama mu huta abinmu,da kyaunki da komai kin tattare kanki guri daya kin batawa kanki lokaci wajen jiyyar wancan nakasashen,kada ki cuci quruciyarki mana baby,ki bani hadin kai ni kuma na miki alqawarin biya miki kowacce iriyar buqata kike da ita''.
dan ya tsanta ta nuna shi da shi
''ka bani hanya na wuce malam ko baka ji ba''
''common baby ki.....''
batasan lokacin da ta daga hannu ta tsinka masa mari ba cikin zafi da huci tace
''ni ba irin matan da kake tnani bace,hakanqn ni ba butulu bace irinku,nakasashen mijina ya fiye min kai da yan uwanka kai da duka ma danginka,daga rana irin ta yau kada ka kuma kuskuren tarata da banzayen magnganu irin wadan nan,banza shashaaha bani hanya na wuce''
''ni kika mara,wallahi zaki san ba'a ja da ire irenmu,zaki san kin sanya hannunki kin mari adnan''
''na marekan,sai me,na mari banza na mari wofi?''ta fada bayan ta masa wani kallon banza ta kewayeshi ta shige gun mamin
Baaba uwani kawai ta taras itama tana qoqarin fitowa akitchen da alamu wanke wanke ta gama,suka gaisa a mutunce tana tambayarta mai jiki,ta amsa mata da sauqi kana ta tambayeta mamin
''hajiya tana sama,nima tun jiya da yamma rabina da ganinta,tace dqi da yammacin jiya kanra na mata ciwo zata ta kwanta,to tunda ta hau kuma har yanzu bata sauko ba''
''bari na dubata to,Allah yasa lafiya''inji maryam wadda ta fara taka benan
''ameen,kice ina mata sannu''inji baaba uwani dake ficewa daga sashen
''zata ji''
knocking tayi ya kusa goma kafin taji cikin murya kamar ta fada fada ance waye ne?''a sanyaye tace maryam ce''
ta kusa minti talatin kafin ta bude qofar bedroom din
mamin ce fes da ita ikin lace da alama bata dade da gama wanka ba saidai babu make up a fuskarta kamar yadda taje a hade kamar wadda aka aikowa da labarin mutuwa ,kusan zata iya cewa bata taba ganin kwatankwaci yanayin a gun mami ba,kullum cikin fara'a take.
fuskar maryam qunshe da murmushi ta dan rusuna tana gaida mamin,duk da adaqile take amsa mata bata kawo komai cikin ranta ba,tayi tsammanin ciwon kan ne ke damunta
Shiru ne ya ratsa tsakani bayan ta gama gaishetan
''wai lafiya malam kin min tseye a gaba na?''ta fada cikin sautin fushi
a tausashe tace
''ah.....dama ji nayi shiru baki shigo ba,shine nae bari inzo in duba ko lafiya,ga abdallah ma baici abinci ba saboda rashin shigowarkin''
''banga damar shigowar bane,ni baiwar idan ubanku ce,siyata kukayi da zanta muku bauta,ok....na ganoki ma,wato bani da lokaci sai naku ko?,to kada Allah yasa ahima yaci abincin kinibabbe,ruwansa ne daga yau kada ya kuma cin abinci a duniya,ni da zaya mutu ma da bai hutar da muta ne ba,mtswee aikin banza shine kika zo kika taahi mutane suna cikin hutawatsu,to wannna ya zame miki na qarshe da zaki sake takomin saman ma,duk abinda kuke buqata ki tsaya daga qasa har sai na sauko,kinji na gaya miki''
daga haka ta ja qofarta ta bame ta bar ta anan
tamkar gini haka maryam ta koma,mafarki ne koko gaske,almara ce ko tatsuniya ce,ji tayi wasu hawaye masu dumi na sauko mata,batasan sanda ta tsinci bakinta na furta
''ya Allah kada ka jarrabemu da wata jarabtar ta daban bayan wadda muke ciki,ubangiji idan ka saka mana wannan cikin sabuwar karrabar da zaka mana ba zamu iya jurewa ba nida abdallah,ya Allah sassaucinka muke nema''bibbiyu ta dinga gani a haka ta bar bangaren zuwa nasu,tafi qarfin minti talatin zaune afalonsu tana rasgar kuka
wanna wace iriyar jarrabar rayuwa ce da suka wayi gari da ita da safen nan,anya ma kuwa da mami tayi magana?,mamin abdallah fa,mai tattali da qaunarshi akoda yaushe,mai son ganin farinciki da walwalarsa,mamin da tasha bata amanar abdallah,tasha gaya mata bata da kowa sai shi ta kula mata da shi bata so ta rasashi yadda ta rasa mahaifinsa
cike da tantamar ba mamin bace ta dauki wayarta ta kira number dinta don ta tabbatar,saidai dagawar farko ta kuma cin karo da muryarta tana fadin
''wai nikam sa'arki ce maryam?,lallai na sakar miki da yawa kinga gadon barcina,sai na dauki tsatstsauran mataki a kanki kamar yadda nene tace''jin sunan nene kawai data ambata ya sata dauke wayar daga kunnenta tana kiran sunan Allah,tabbas akwai wani abu na daban dakeaon kunmo kai
''Allah na roqekakoma meye ka kawoshi da sauqi ya arhamar rahimeen''ta qarasa fada tana rufe fuskarta da tafin hanunta hadi da rushewa da kuka
kiran sallar la'asar ya fargar da ita abdallah data bari,da sauri ta miqe a rude ta tura qofar dakin ta shiga,yanayin fuskarsa kawai ta kalla ya tabbatar mata ya gaji da kwanciyar,sai tausayinsa ya kamata,da sauri ta qarasa kan hadon cikin rawar murya
''kayi haquri don Allah,mun barka kai kadai wallahi ma.....''
maganr tata ta katse saboda yadda taga ya zubawa fuskarta ido,tamkar mai son tambayarta abinda ya sanyata kuka,sai a lokacin ta tuna da hawayen fuskarta,kawar da kanta tayi gefe tana qoqarin boye damuwarta,kusan minti biyar kafin ta dawo da kallonshi saiai har yanzu ita din yake kallo,data fuskanci tambaya ce yake mata sai ta girgiza kai
''ba kuka bane abu ne ya fada min io kuma daga nan sai ma dauro alwala da yaqi fita....bari na kawo maa abincinka''ta fada tana miqrwa da saudi ta fice adakin yayin da ya bita da kallo zuciyarshi cike da wani abu dake masa yawo ko ina cikin jininshi
Da qyar ta iya jingina ahi da fuskar hadon ta tattare si da filota zauna dab da shi har cinyarta na gogar tasa,ya lumshe ido cikin zuciyarshi data zame masa abokiyar tadi yake fadin
''so bala'ne,duk cikin yanayin da kake baya barinka ka huta?''
''bismillah karbi''yaji tana fada saitin kunnenshi,tsigar jikinsa ta tashi,a hankali ya bude idonshi ya sake zubasu a kanta,yana hango bacin rai da tashin hankali qarara kan fuskarta,da yana da baki zaiso ya tambayeta yaji me ya sameta?,bai taba tunanin zata ci gaba da zama da ahi a yadda yake ba,yayizaton a washegarin randa lalurar ta sameshi zata hada yanata yanata ta qara gaba ko babu takardar saki,kwatankwcin yadda yaji wasu matan nayi ga mazajensu idan lalura ta samesu,wasun su kun hayayyafa ma tare amma basu iya zama da kai da,bare su da kwana bihu kacal sukayi a matsayin ma'aurata.
kallon taga yayi yawa
''ka karbi abincin''a maimakon taga ya karba sai ya juyar da kanshi yana duban bakin qofa,hakan ya nuna mata mami yake son gani,hakan sai ya sake karyar mata da zuciya,ta sani mawuyaci ne ya karbi abinci idan bai ga mamin ba,saboda haka ta ajjiye cokali ta kuma daukar wayarta cike da fatan ta samu sauyawar yanayin mamin
''mami ya farka yaqi ya karbi abincin keyake jira''
''ke!ke fita daga idona,wai shin komayyar ce ke da gaske?,to wallahi zan ci iki mutunci fiye da zatonki,ko rayuwarku wajibi na ce,kuje kuji da kanku kada ki kuma kira na na gaya miki''daga haka ta katse wayar,hada idanu sukayi da abdallan da alamu yaji wani abu cikin abina mamin ta fada,mutum ne mai kaifin ji,hadiye kukan da yake taso mata tayi ta kuma diban abincin a cokali ta miqa masa tana fadin
''kayi haquri ka karba,anjima mamin zata zo kaji''
🎄🌲🎄🌲🎄
wasa wasa abun sai ya zama gaake,tun ranar data yi shigowar qarshe mami bata sake waiwayarsu ba,sam ta mance da su ma baki daya,gaba daya an canza mata alqiblar rayuwa,kusan gidan ma baki daya ya koma hannun nene sai abinda ta shimfida wa jama'ar gidan ciki harda mamin,a hankali a hankali suka dinga karbar takardun lamfanoni filaye gidaje da duk wata plaza na abdallahn daga hannun mamin,ba tare da musu ba haka zata dauka ta damqa musu
hisham baisan halin da ake ciki ba,bai an kara ba sai da yake duba kamfanin yin flower na abdallahn ya tadda adnan dare dare kan kujerarshi kamar wanda ya gada daga gurin ubanshi,da ya sami mamin ya mata maanar ranar ya ga bala'in da bai taba gani ba gurinta,har da ja mishi kunnen matiqar bai dauke idonhi daga lamuransu ba zata sa ahanaahi shigowa gidan kamar yadda tasa aka hana duk wani dan uwanta ko na maryam zuwa gidan,tilas ya ka bakinshi on ya san daina zuwanshi gidan ba qaramin tagayyra zai haifarwa abdallah da maryam ba,ya dai cika da mamakin canzawar mamin lokaci guda,tsana nin biyayya da bi sau da qafa da takewa nene
🎄🌲🎄🌲🎄
Sau biyu tana leqowa taga ko bacci ya daukeshi?wanka take son tayi ta sauya kayan bacci ta kwanta,a karo na uku ta tadda idanunshi ruf alamun ya samu bacci kenan,ta jima tsaye akansa tana qare masa kallo,a hankali ta sanya hannunta cikin tattausan sumarshi,yana buqatar a rage masa ita saidai bazai iya magana ba,cikin ranta ta qudirci gayawa hisham gobe ko zai iya masa yana da clipper tunda ita bata iya ba,jin ya motsa ya sanyata saurin janye hannunta tsoronta kada ya farka,sai da taga ya bar motsin kana ta tofa masa fatiha da yatul kursiyyun da take yawan tofa mishi akai akai ta juya ta isa bakin cupboard dinsu ta soma cire doguwan rigan jikinta
a hankali ya bude idanunshi ya zuba mata ido duka batasan me akeyi ba,ta janyo towel ta daura tayi banaki,ya lumshe idona wani dan murmushi ya subuce masa,maryam maryam bai san maryam ba sai yanzun,yanzun ne yasan maryam,cikin tunaninshi yaji tana qoqarin itowa ya maza ya maida idanunshi ya lumshe,yana iua hagota tana shiryawa tsigar jikinhi na tashi,ji yake ina ma yana da lafiyar da zai nuna mata irin soyayyarta dake danqare ciki zuciyarshi,har ta kammala ta zura rigar baccinta ta dora dan hijabinta a kai
Bata taba yarda ta kwanta kan gadon matuqar idonshi biyu,sai bacci ya daukeshi take lallabowa ta kwanta ga tsammaninta duk bai sani ba,saidai data kwanta din ko cikin bacci yake zai farka saboda wani dumi na musamman yake ji daga garta,yau din ma lallabowa tayi ta kwanta gefanshi bayan ta gama qare masa kllo kamar yadda ta saba,a hankali gajiya ta mamayeta,bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita,a irin wannan lokacinne shima yake samun damar qare mata nashi kallon,yakan tsinci kansh ciki wani irin nishadi a lokacin
ya daga hannunshi da niyyar janyota cikin jikinshi ya kusa sau goma amma ya kasa,ya saki nannuyan ajiuyar zuciya yanajin radadin hakan cikin ranshi.
cikin sa'a tayi wani juyi tashin farko sai gata cikin jikinshi,murmushi yayi yana godewa Allah tare da dora kanshi saman kanta,duk da hijabin jikinta hakan bai hanashi jin dumi da qamshinta ba
sannu a hankali sai kuma ya dinga jin motsi kamar ana hawowa saman da suke,yaci gaba da kallon bakin qofar don ya tabbatar yau maryam tayi mantuwa bata rufe qofofin ba,idanunshi fes kan qofar yaji an turo an shigo,tashin farko aka dallare dakin da fitila mai tsananin haske kai tsaye hasken ya iso har inda suke
''wal masakinu bakayi bacci ba?''yaji an fada kana aka kunna duka qwayayen dakin,fuskar adnan ta bayyana
''gwara ma da bakayi baccin ba ai kaga ka gani da idonka tunda gani ya kori ji ko?,yau zan cika burina,zan kwanta da matarka agabanka,zan cusa maka baqinciki abdallah irin wanda na dade ina sha akanka,ka fini kyau,ka fini matsayi ka fini kudi ka fini nasaba hakanqn ka fini farinjini,yau zan kuma nakastaka kafin lokain da muka diba maka na mutuwarka ya cika,kabi bayan tsohonka ku hade acan kafin tsohuwarka ta biyoku''
gadan gadan ya hauro gadon yasa hannunshi ya janyo maryam dake jikinshi wanda hakan ya sanyata farkawa afirgice,ba qaramin kaduwa tayi da ganinshi cikin dakinsu ba cikin takiyar dare,bata ankara ba ya sabule hijabnta ya wurgar take gashinta mai tsaho da santsi ya warwatsu,runtse idonshi abdalah yayi yana jin tamkar an ciro zuciyarsa ana tststsagata,kamar an karata kusa da tukuba turiri kawai take maa,ya bude idonshi yaga yadda ake dambe tsakanin adnan da maryam,gashi kwance bashi da ikon tsinana komai,qoqari yake na daga hannunshi saidai hakan ya faskar,ihi yakeso ya kurama na baqinciki da takaici amma ko bakin ya kasa motsawa,sai ya koma kiran sunayn Allah ciin zuciyarshi tare da yunqurin motsa hannun nashi
0 comments:
Post a Comment