_Manzan Allah S A W yace:shaidanu suna nisantar gidan da aka karanta suratul baqra a cikinsa har na tsawon kwana uku_*
*_mala'iku sukanyi duba izuwa sararin duniya,yayin da suka kalleta suna hangota ne baqiqqirin basa ganin komai face hasken gidaje ko guraren da ake karanta alqur'ani a cikinsa_*
A bakin murhu suka tadda inna wuro tana kwashe tuwo,sallamarasu ce ta janyo hankalinta bakin qofar shigowar
''kun dawo kenan mer.....'''sauran maganar ta maqale wa inna wuro ganin har da abdallah cikin masu sallamar,marar hannunta da take kwashe tuwon ta saki ta miqe tana fadin cikin dafe qirji
''Allah qaadiran ala mai yasha'u,bawan Allah?''ta fada tana kallonsa tare da qarasowa gabansu.
murmushi yayi yana kallon innar ganin ta kasa magana
''babu mamaki cikin ikon Allah inna,nine da bakina nake magana,yau Allah ya amince min''
kiran sallar magariba ya katse su
''inna muyi sallah tukun''ya dubi maryam dake tsaye guri daya tana faman goge qwalla lokaci zuwa lokaci
''gimbiya a dauran alwala,inna ki mata magana tun dazun nace tabar kukan nan taqi''inna wuron dake daura da maryam din ta dafa kafadarta
''haba meramu,farincikin da zaki nunawa ubangiji shine ki masa godiya ba wai kika ba,share hawayenki ki daurawa mijinki alwala''
''to inna''ta fada cikin rawar murya
tuni har mero ta debo ruwa cikin buta tazo gaban abdallan ta ajjiye ta koma bakin rijiyar ta ja wani ta fara daura tata alwala,dukkansu nan bakin qofar dakin innar suka shimfida karauni biyu sukayi sallar magaribar,shiru ya ratsa tsakar gidan kowanne na tasbihi cikin zuciyarshi banda mero da moysa bakinta kawai takeyi duk motsin abdallah ta cikin hasken qwan solar na kan idonta,har maryam ta fuskanci haka,dauke kanta tayi don ji da tayi ranta na aon baci taci gaba da tasbihi da yatsunta.
Ranar har sha daya na dare suna zaune suna hira,hiransu suke sosai shida inna wuro da yake jinta kamar maminshi.
Yana jin kewar mamin nashi sosai har bazai iya fadar adadi ba,mero ma tsakiyarsu tana sanya musu baki yayin da maryam taja bakinta ta tsuke,lokaci lokaci abdallah yana satar kallonta,ji yake tamkar ya jawota jikinshi ya rungume ko ya shiga zuciyarta ya jiyo damuwarta,shirun nata bai masa dadi sam,don haka sha daya na cika yace da inna wuro yana jin bacci zai kwanta
''nikuwa kamar mu kwana nan hirar yau tayi min dadi abdullahi,gashi yau kaima da bakinka akeyi da kai''mero ta fada yana kallonshi baki a washe,murmjshi kawai yayi ya girgiza kai,bata bar gidan ba sai da taga sun shige dakin kana ta waiwayo ta yiwa inna wuro sallama ta fice cike da jin dadin jin daddadar muryar abdallah da yau ta morewa.
sanye yake da jallabiya milk mai gajeran hannu yana zaune saman katifar tasu hannunahi dauke da qaramin al'qur'ani,daya hannun kuma riqe yake da wayarshi ya kunna torch din yana haskawa,ya sake satar kallonta sha biyu har da kwata amma bata da niyyar kwanciya,hakanan kuma ta kashe musu qwan solar dakin saboda ta lura da yadda yake ta nacin kallonta,tana zaune dirshan bisa dadduma sanye da hijabi da carbi a hannunta tana ja,ya saka zare kan shafin da yake na karatun qur'ani ya shafa addu'anshi,ya tabbata koya kirata kam ba zuwa zata yi ba indai ba cewa yayi yana buqatar wani abu ba.
''madam,a ataimakawa bawan Allah da ruwa mana''ya fada murya qasa qasa kamar mai rada har yasa tsigar jikinta tashi,ta ajjiye carbin kana ta miqe ta isa inda catoon na ruwan gora ke ajjiye ta ciro daya tare da cup ta hawo gadon,ta tsiyayo ta sake matsowa gabanshi ta miqo masa,jadawa yayi harda hannun nata ya riqe gam yana son saka qwayar idonshi cikin nata,ta soma qoqarin qwace hannun nata saidai ta kasa garin hakan har fiye da rabin ruwan ya zube a katifar.
Ta dago da niyyar dubanshi idanunta cike da qwalla da ya rasa ta meye,take idanunsu suka hadu,da sauri ta janye nata idanun don bata iya dauke nauyin idanunshi cikin nata
''ka sakemin hannu kaga duk ka.....''
''bazan sakeki ba,sai kin gayan meke damunki,tunda bakina ya budu baki,barni nayi magana da ke ba sai wasu ke tayani hira?''
ta sake kau da kanta kana tace
''to me kake so muce ko ince maka ne?''
''bana tunanin baki san me zaki gayan ba maryam,nasha hango maganganu da dama boye cikin idanunki,kin hana bakinki ya furta kina cutar da zuciyarki hakanan babu gaira babu dalili ba tare da ta yi miki laifin komai ba''
kamar wadda ya doka sai ta soma hawaye,ita kanta batasan me yake saurin karya mata zuciya ba
''subhanallah,kuka...kuka kuma maryam me na miki''babu amsa don haka ya janyota ta fada jikinshi ragowar ruwan ya zube mata ya jiqa mata gaban dan yalolon hijabin jikinta wanda takansa duk dare idan zata kwanta,dama ba wani kauri gareahi ba,yauqi ne da shi da rashin kauri take kuwa ya manne mata a jiki.
''yi shiru ki gayan matsalarki,bazanso saki kuka ba maryam cikin irin wannan lokacin,baki cancanci haka ba''
''ka sakeni ni babu abinda ke damuna,ka qyaleni''
kai ya girgiza hakanan mutum,bazai yita kuka ba komai na da dalili''
ta tabbatar indai abdallah ne bazai saketa din ba don ya mata riqon tsauri ne don haka tace
''kayana,ka jiqamin kayana ka sakeni na canza wasu''
idanunshi ya kai kan gaban jijabin nata cikin hasken torch din wayarshin,wani abu ya tairga mishi har qasan qafarshi,ya kai,hannunshi gaban hijabin yana fadin
''bari na cire miki''
kan tayi qoqarin hanashi har yaje,gaba dayansu wuta ta dauke musu shi da itan gaba daya,sai ta sakar masa wani kikan harda dan sauti
''am so sorry my dear''kawai yake fada ya cire hijabin ya cillar gefe daya ya sake mannata kan qirjinsa,yana kin sautin kukanta bai hana ta ba don yasan koma mene idan tayi kuka sosai zuciyarta zata sassauta,tun sautin na fita kadan kadan har ta koma ajiyar zuciya kana numfashinta ya fara sauka a hankali alamun bacci yayi awon gaba da ita.
murmushi ya saka mai qayatarwa qasa qasa yace bayan ya leqa fuskarta
''rigimammiya,kin hana zuciyarki sakat''yana gyara mata kwanciya,ya fuskanci duk ranar da ta kwanta a qirjinshi bata dadewa bacci ke daukanta wani lokacin ma har taso makara gun tashi,ya saki ajiyar zuciya qasa qasa yace
''u dont know how u make me feel duk sanda kike jikina''ya dora kanshi saman habarta cike da wata iriyar nutsuwa.
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
A shirye take cikin riga da wando na pakistan ruwan madara tayi rolling da mayafinsu,zaune take kan kujera ko motsi batayi kanta a duqe tana kallon yatsuntsa,ya sake dubanta tini har ta fara zub da qwallar tata abinda bai son gani
''kina son fita amma kinqi ki gyara ni,nikam yau babu wanda zaimin wanka idan bake ba,see you ko tausayina baki ji,kin gwammace mustafa yayi ta yimin bayan bako ina yake wanke min ba wani gun ni nake da kaina''
maryam cikin muryar kuka ba tare da ta dago ba
''taya zan wuce bandaki ni da kai yi maka wanka inna wuro na kallon mu,haba mana abdal....''
''fine,muyi zamanmu ko baby na ni dake yau cikin daki,babu mai cewa don me ko''qara narkewa tayi tana faman hawaye don tana jiyo muryar inna wuro na jajjabin rashin jin motsin daya daga cikinsu,duk da tasan kara da alkunya bazata bar inna wuron tayi magana ba ko zasu shekara cikin dakin.
Narkewa yayi shima cikin filallukan dake kan whellchair dinshi dariya na cinshi,ya sani cewa ba zata taba iyawa ba,ko kaya na shan iska bata yarda ta gani jikinsa kuma duka ua gama karantota,ta daukeshi kamar wani muharraminta
sallama mairo tayi tana daga labulen dakin
''yaya abdullahi muna ta cigiyarku shiru?''ta fada tana kallonashi tana kuma kallon maryam
girarshi ya dage guda daya
''eh,muma muna ta cigiyarku,daman ke nake jira ki taimaka min inyi wanka,yau meramu ta gaji''ya ambaci sunan ta irin salon da yaji suna fada
zuciyar mero qal ta rufe fuskarta da tafukan hannunta,da sauri maryam ta dago babu shiri ta dubi abdallah qirjinta ya buga kamar an dakeshi da guduma,ido daya ya kashe mata kana ya dauke kanshi ya maida kan mero wadda take fadin
''kai yaya abdullahi''cikin salon nuna jin kunya.
kan mero ta bude idonta har maryam ta taashi ta kama wheelchair din tayi hanyar fita da shi,sai data bude idon nata raga dakin wayam har sun fice,jiki ba qwari jtama ta fice a dakin
inna wuro bata a tsakar gidan don haka tayi maza ta tura suka shige bayan gidan
''take it easy mana madam,kada ki fadar da bawan Allah''inji abdallah cike da dariyar mugunta da yake qunsheta
tana tsaye ya soma cire kayanshi ta dauke kanta qirjinta na lugude,saura gajeran wandon daya rage wanda yake bari a jikinsa idan zaiyi wanka,gaba daya ta rude don bata yarda taga jikinshi har kamar haka,hatta da cinyoyinshi dake cike da gargasa sun fito,ganin yana niyyar fidda shi shima yasa ta qarasa rudewar gaba daya,batasan ta dafe hannunshi ba
''ayya mana abdallah ba kyau fa don Allah''ta fada cikin son fashewa da kuka
dariya sosai ta kamshi amma ya hade rai yayi kicin kicin
''to me naki,dazun fa adaki kika gayan babu ruwan wani da wani,kema me ruwanki da ni ko na cire din,ba wanka zaki tayani ba?,kimin wankanki kawai ki maida ni daki,wai haka ma ake jinyar mutum?,oh ni abdallah sam baki iya jinya ba''ba bakin maida amsa girgiza kai tayi yaci gaba da kiciniyarshi,a guje ta kwasa ta fice a bayin dariyar da yake boyewa tilas ta fito,mamaki take bashi tamkar cikin qauyen aka haifeta ko kuma shi din ba mijinta bane,kunyarta ta mata yawa ta maida shi kamar wani dodo,Allah yasa komai na wanka na gabanshi don haka ya qyaleta yayi abunshi tunda hannunshi na kaiwa.
sai da ya kammala ya bubbuga qofan bandakin tazo ta fidda shi,tana ta rarraba ido kamar wadda ta yiwa sarki qarya ta shigo idanunta a qasa taqi yarda su hada idanu,itakam rashin kunyar shi ta fara isarta,daga warkewarsa jiya zuwa yau ya addabeta gaba daya ya hanata sukuni,ina dalili,yana abu kamar su biyu ne kadai cikin gidan.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[7:29pm, 9/25/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
4⃣8⃣
*_Manzan Allah S A W yace:shaidanu suna nisantar gidan da aka karanta suratul baqra a cikinsa har na tsawon kwana uku_*
*_mala'iku sukanyi duba izuwa sararin duniya,yayin da suka kalleta suna hangota ne baqiqqirin basa ganin komai face hasken gidaje ko guraren da ake karanta alqur'ani a cikinsa_*
A bakin murhu suka tadda inna wuro tana kwashe tuwo,sallamarasu ce ta janyo hankalinta bakin qofar shigowar
''kun dawo kenan mer.....'''sauran maganar ta maqale wa inna wuro ganin har da abdallah cikin masu sallamar,marar hannunta da take kwashe tuwon ta saki ta miqe tana fadin cikin dafe qirji
''Allah qaadiran ala mai yasha'u,bawan Allah?''ta fada tana kallonsa tare da qarasowa gabansu.
murmushi yayi yana kallon innar ganin ta kasa magana
''babu mamaki cikin ikon Allah inna,nine da bakina nake magana,yau Allah ya amince min''
kiran sallar magariba ya katse su
''inna muyi sallah tukun''ya dubi maryam dake tsaye guri daya tana faman goge qwalla lokaci zuwa lokaci
''gimbiya a dauran alwala,inna ki mata magana tun dazun nace tabar kukan nan taqi''inna wuron dake daura da maryam din ta dafa kafadarta
''haba meramu,farincikin da zaki nunawa ubangiji shine ki masa godiya ba wai kika ba,share hawayenki ki daurawa mijinki alwala''
''to inna''ta fada cikin rawar murya
tuni har mero ta debo ruwa cikin buta tazo gaban abdallan ta ajjiye ta koma bakin rijiyar ta ja wani ta fara daura tata alwala,dukkansu nan bakin qofar dakin innar suka shimfida karauni biyu sukayi sallar magaribar,shiru ya ratsa tsakar gidan kowanne na tasbihi cikin zuciyarshi banda mero da moysa bakinta kawai takeyi duk motsin abdallah ta cikin hasken qwan solar na kan idonta,har maryam ta fuskanci haka,dauke kanta tayi don ji da tayi ranta na aon baci taci gaba da tasbihi da yatsunta.
Ranar har sha daya na dare suna zaune suna hira,hiransu suke sosai shida inna wuro da yake jinta kamar maminshi.
Yana jin kewar mamin nashi sosai har bazai iya fadar adadi ba,mero ma tsakiyarsu tana sanya musu baki yayin da maryam taja bakinta ta tsuke,lokaci lokaci abdallah yana satar kallonta,ji yake tamkar ya jawota jikinshi ya rungume ko ya shiga zuciyarta ya jiyo damuwarta,shirun nata bai masa dadi sam,don haka sha daya na cika yace da inna wuro yana jin bacci zai kwanta
''nikuwa kamar mu kwana nan hirar yau tayi min dadi abdullahi,gashi yau kaima da bakinka akeyi da kai''mero ta fada yana kallonshi baki a washe,murmjshi kawai yayi ya girgiza kai,bata bar gidan ba sai da taga sun shige dakin kana ta waiwayo ta yiwa inna wuro sallama ta fice cike da jin dadin jin daddadar muryar abdallah da yau ta morewa.
sanye yake da jallabiya milk mai gajeran hannu yana zaune saman katifar tasu hannunahi dauke da qaramin al'qur'ani,daya hannun kuma riqe yake da wayarshi ya kunna torch din yana haskawa,ya sake satar kallonta sha biyu har da kwata amma bata da niyyar kwanciya,hakanan kuma ta kashe musu qwan solar dakin saboda ta lura da yadda yake ta nacin kallonta,tana zaune dirshan bisa dadduma sanye da hijabi da carbi a hannunta tana ja,ya saka zare kan shafin da yake na karatun qur'ani ya shafa addu'anshi,ya tabbata koya kirata kam ba zuwa zata yi ba indai ba cewa yayi yana buqatar wani abu ba.
''madam,a ataimakawa bawan Allah da ruwa mana''ya fada murya qasa qasa kamar mai rada har yasa tsigar jikinta tashi,ta ajjiye carbin kana ta miqe ta isa inda catoon na ruwan gora ke ajjiye ta ciro daya tare da cup ta hawo gadon,ta tsiyayo ta sake matsowa gabanshi ta miqo masa,jadawa yayi harda hannun nata ya riqe gam yana son saka qwayar idonshi cikin nata,ta soma qoqarin qwace hannun nata saidai ta kasa garin hakan har fiye da rabin ruwan ya zube a katifar.
Ta dago da niyyar dubanshi idanunta cike da qwalla da ya rasa ta meye,take idanunsu suka hadu,da sauri ta janye nata idanun don bata iya dauke nauyin idanunshi cikin nata
''ka sakemin hannu kaga duk ka.....''
''bazan sakeki ba,sai kin gayan meke damunki,tunda bakina ya budu baki,barni nayi magana da ke ba sai wasu ke tayani hira?''
ta sake kau da kanta kana tace
''to me kake so muce ko ince maka ne?''
''bana tunanin baki san me zaki gayan ba maryam,nasha hango maganganu da dama boye cikin idanunki,kin hana bakinki ya furta kina cutar da zuciyarki hakanan babu gaira babu dalili ba tare da ta yi miki laifin komai ba''
kamar wadda ya doka sai ta soma hawaye,ita kanta batasan me yake saurin karya mata zuciya ba
''subhanallah,kuka...kuka kuma maryam me na miki''babu amsa don haka ya janyota ta fada jikinshi ragowar ruwan ya zube mata ya jiqa mata gaban dan yalolon hijabin jikinta wanda takansa duk dare idan zata kwanta,dama ba wani kauri gareahi ba,yauqi ne da shi da rashin kauri take kuwa ya manne mata a jiki.
''yi shiru ki gayan matsalarki,bazanso saki kuka ba maryam cikin irin wannan lokacin,baki cancanci haka ba''
''ka sakeni ni babu abinda ke damuna,ka qyaleni''
kai ya girgiza hakanan mutum,bazai yita kuka ba komai na da dalili''
ta tabbatar indai abdallah ne bazai saketa din ba don ya mata riqon tsauri ne don haka tace
''kayana,ka jiqamin kayana ka sakeni na canza wasu''
idanunshi ya kai kan gaban jijabin nata cikin hasken torch din wayarshin,wani abu ya tairga mishi har qasan qafarshi,ya kai,hannunshi gaban hijabin yana fadin
''bari na cire miki''
kan tayi qoqarin hanashi har yaje,gaba dayansu wuta ta dauke musu shi da itan gaba daya,sai ta sakar masa wani kikan harda dan sauti
''am so sorry my dear''kawai yake fada ya cire hijabin ya cillar gefe daya ya sake mannata kan qirjinsa,yana kin sautin kukanta bai hana ta ba don yasan koma mene idan tayi kuka sosai zuciyarta zata sassauta,tun sautin na fita kadan kadan har ta koma ajiyar zuciya kana numfashinta ya fara sauka a hankali alamun bacci yayi awon gaba da ita.
murmushi ya saka mai qayatarwa qasa qasa yace bayan ya leqa fuskarta
''rigimammiya,kin hana zuciyarki sakat''yana gyara mata kwanciya,ya fuskanci duk ranar da ta kwanta a qirjinshi bata dadewa bacci ke daukanta wani lokacin ma har taso makara gun tashi,ya saki ajiyar zuciya qasa qasa yace
''u dont know how u make me feel duk sanda kike jikina''ya dora kanshi saman habarta cike da wata iriyar nutsuwa.
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
A shirye take cikin riga da wando na pakistan ruwan madara tayi rolling da mayafinsu,zaune take kan kujera ko motsi batayi kanta a duqe tana kallon yatsuntsa,ya sake dubanta tini har ta fara zub da qwallar tata abinda bai son gani
''kina son fita amma kinqi ki gyara ni,nikam yau babu wanda zaimin wanka idan bake ba,see you ko tausayina baki ji,kin gwammace mustafa yayi ta yimin bayan bako ina yake wanke min ba wani gun ni nake da kaina''
maryam cikin muryar kuka ba tare da ta dago ba
''taya zan wuce bandaki ni da kai yi maka wanka inna wuro na kallon mu,haba mana abdal....''
''fine,muyi zamanmu ko baby na ni dake yau cikin daki,babu mai cewa don me ko''qara narkewa tayi tana faman hawaye don tana jiyo muryar inna wuro na jajjabin rashin jin motsin daya daga cikinsu,duk da tasan kara da alkunya bazata bar inna wuron tayi magana ba ko zasu shekara cikin dakin.
Narkewa yayi shima cikin filallukan dake kan whellchair dinshi dariya na cinshi,ya sani cewa ba zata taba iyawa ba,ko kaya na shan iska bata yarda ta gani jikinsa kuma duka ua gama karantota,ta daukeshi kamar wani muharraminta
sallama mairo tayi tana daga labulen dakin
''yaya abdullahi muna ta cigiyarku shiru?''ta fada tana kallonashi tana kuma kallon maryam
girarshi ya dage guda daya
''eh,muma muna ta cigiyarku,daman ke nake jira ki taimaka min inyi wanka,yau meramu ta gaji''ya ambaci sunan ta irin salon da yaji suna fada
zuciyar mero qal ta rufe fuskarta da tafukan hannunta,da sauri maryam ta dago babu shiri ta dubi abdallah qirjinta ya buga kamar an dakeshi da guduma,ido daya ya kashe mata kana ya dauke kanshi ya maida kan mero wadda take fadin
''kai yaya abdullahi''cikin salon nuna jin kunya.
kan mero ta bude idonta har maryam ta taashi ta kama wheelchair din tayi hanyar fita da shi,sai data bude idon nata raga dakin wayam har sun fice,jiki ba qwari jtama ta fice a dakin
inna wuro bata a tsakar gidan don haka tayi maza ta tura suka shige bayan gidan
''take it easy mana madam,kada ki fadar da bawan Allah''inji abdallah cike da dariyar mugunta da yake qunsheta
tana tsaye ya soma cire kayanshi ta dauke kanta qirjinta na lugude,saura gajeran wandon daya rage wanda yake bari a jikinsa idan zaiyi wanka,gaba daya ta rude don bata yarda taga jikinshi har kamar haka,hatta da cinyoyinshi dake cike da gargasa sun fito,ganin yana niyyar fidda shi shima yasa ta qarasa rudewar gaba daya,batasan ta dafe hannunshi ba
''ayya mana abdallah ba kyau fa don Allah''ta fada cikin son fashewa da kuka
dariya sosai ta kamshi amma ya hade rai yayi kicin kicin
''to me naki,dazun fa adaki kika gayan babu ruwan wani da wani,kema me ruwanki da ni ko na cire din,ba wanka zaki tayani ba?,kimin wankanki kawai ki maida ni daki,wai haka ma ake jinyar mutum?,oh ni abdallah sam baki iya jinya ba''ba bakin maida amsa girgiza kai tayi yaci gaba da kiciniyarshi,a guje ta kwasa ta fice a bayin dariyar da yake boyewa tilas ta fito,mamaki take bashi tamkar cikin qauyen aka haifeta ko kuma shi din ba mijinta bane,kunyarta ta mata yawa ta maida shi kamar wani dodo,Allah yasa komai na wanka na gabanshi don haka ya qyaleta yayi abunshi tunda hannunshi na kaiwa.
sai da ya kammala ya bubbuga qofan bandakin tazo ta fidda shi,tana ta rarraba ido kamar wadda ta yiwa sarki qarya ta shigo idanunta a qasa taqi yarda su hada idanu,itakam rashin kunyar shi ta fara isarta,daga warkewarsa jiya zuwa yau ya addabeta gaba daya ya hanata sukuni,ina dalili,yana abu kamar su biyu ne kadai cikin gidan.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[2:36pm, 9/27/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶4⃣9⃣
*GA WASU FA'IDOJI*👌🏽
*_daga bakin mai gaskiya abun gasgatawa assaadiq al masduq Annabi Muhammad S A W yace''abinda yake zama hijabi tsakanin al'aurar dan adam da idon shaidanu fadin wannan addu'ar yayin da zaka cire tufarka BISMILLAHILLAZI LA ILAHA ILLA HUWA_*''
*_don samun kariya yayin yin baccinka,bayan ka kammla dukkan addu'ar baccin da annabin rahama ya koyar,ki karanta wadan nan ayoyin suma ki tofa musamman ga 'yan mata da suke fama da jinnul aashiq wato aljanin dare_*
1⃣ *_katamallahu ala qulubihim wa'ala sam'ihim wa ala absaarihim gishawah,ealahum azabun alim_*
2⃣ *_waja'alna min bani aydihim saddan wamin khalfihim saddan fa agshaynahum fahum la yubsirun_*
3⃣ *_wa'iza qara'atal qur'ana ja'alna bainaka wa bainal lazina la yu'u minuna bil aakhirati hijaban mastura,wa iza zakarta rabbuka bil qur'ani wahdahu wallau ala adbarihim nufura_*
Hira suke kamar kowanne dare zaune warqashin rumfar qofar dakin inna wuro,dukkansu sauraron inna wuron suke su ukun tana basu labarin yanayin zaman aure a shekarun baya can da suka shude
ita kam maryam fadi take taga ta kanta,ta sani sarai da biyu inna wuro ta tsiro da wannan tarihin,tana ankare da abdallah yana satar kallonta,da sun hada ido kuma ya dauke kai sai ka rantse ba kallonta yake ba.
wata yarinyarce tayi sallama ta shigo gidan,inna wuro ta kalli yarinyar lokacin da ta duqa tana gaidata
''lpy qalau indo,ya mutan gidan''
''suna nan lpy suna gaisheku''ta juya ta kalli abdallah da maryam ta gaidasu kana ta kalli mero dake qoqarin miqewa tana fadin
''amma indo yaushe kuka dawo daga kanon,gaskiya birni ta karbeki kinga yadda kika canza kika zama 'yar gayu kuwa?''.
Abdallah da maryam suka dubeta dukkansu dariya ce taso kamasu ita marysm cikin zuciyar ta ne,ina wani gayu anan,amma ita mero ganin wayewarta take a haka,abdallah kuwa sai da murmushi ya bayyana a fuskarshi yana duban yarinyar da ake batun wai ta canza din ta waye,idanun maryam yakai kansa,sai taji wani abu ya tokareta,ga zatonta su meron yakewa murmushi,ta janye idanunta a hankali tana gargadin zuciyarta.
Kama hannun indo mero tayi tana fadin ''muje waje indo''
''dan dalin fa?labaran yace tunda na tafi bai sake ganinki a dandali ba,yanzu ma shi ya aikoni na kai masa ke''bata amsa mata ba sai figar hannun indon da tayi suka fice,ci gaba sukayi da hurar wadda kusan inna wuro da abdallah ne jigon.
Kwanukan maryam ta kwashe ta kai cikin tukunyar tuwon da aka cikata da ruwa don inna wuro tuni ta hanata wanke wanken dare
ta tattare gun ta nufi soron inda suke ajjiye abun shararsu don ta zubar,soron babu haske don wearing din solar da kayi banda nan don haka bata iya ganinsu sosai,saidai tana ganin tsaiwatsu daga can qofar ficewa a gidan baki daya,muryar indo ta fara ji
''yanzu ke mero idan banda tsaurin ido inake ina wannan balaraben tsabar daukowa kai masifa da kuma jan abinda yafi qarfinka,ins laifin ma ki tsayawa labaran dinki,tunfa kina mitsitsiyarki yake sonki kuma an bashi ke,rashin kudin kayan daki ne ya hana auranku amma da tuni yanzu ai kina da yara''
''babu jan masifa,wallahi indo kada ki dauka wasa nake,da gaske sonsa nake wallahi tun ranar da na fara ganinsa,inason abdullahi sosai wallahi''
''tab,to kuwa kin debo da zafi,daidai ruwa fa daidai qurji,wai shin wannan 'yar indiyar ta gefensa ba matarsa bace,idan kuwa hakane to inake ina hada kai da ita,aradu baki fice irin aikinsu da ake kai musubirni ba,ta gurin gashi ne kawai zaku goga da ita amma ta wuceki mero,kiyi haquri kada ki wahal da kanki''.
tsaki mero ta ja
''bafulata ce kamar ni shima haka,yo to ni ina ruwana da matarsama indai shi yana sona ai shikenan,kuma ni ban taba ganin ma ta,nuna,wani abu ba sai rashin fara'a da take da ita kuma wannan halinta ne,ke koma mebe ita ta jiyo,nidai ina son abdullahi kuma bazan fasa......''
jin taku ya sanya mero yin shiru suka waiwaya da sauri,sai sukayo tairu tauru,maryam ce ke takowa inda suke ta qarasa gaban sharar tayo bismillah ta zuba kana ta juya ba tare da tace musu komai ba,zucoyarta ke mata wani irin suya,duk da qoqarin kwantarwa da kanta hankali da take kan ba son abdallah take ba don me to zata ji zafi don wata tace tana sonshi.
bin maryam suka yi da ido har ta shige cikin gidan,suka dawo da idonsu kan junansu suka kalli juna,indo yace cikin zare ido
''kinga irinta ko?yanzu gashi ta ji''cikin son nuna dakiya mero tace
''to baki ga babu abinda ta yi ba,na gaya miki ita fa babu ruwanta''harararta indo tayi
''ashe dai baki da kai mero har yanzu,wace ce zata ce bata kishin mijinta,kina kallon yadda kullum sai anje gudan mai gari rabon fadan kishiyoyi kamar zasu hallaka junansu,bakisan halin irin wadannan matan birnin bane,qila wallahi qyaleki tayi ranar da ta tashi saka ki a maqata babu mai fitar dake,ko kin manta yadda akayi da jummai ita da lantana kan mijinta?''tuno abinda ya faru din ya ruda mero tace
''wallahi hakane fa,ni ai na manta''kama hannun indon tayi qam qam tana kallon cikin gidan
''wallahi bazan koma ba ma cikin gidan,zo mu tafi''ta figeta suka fice gabanta na faduwa saboda tsoron abinda ya faru da lantana kada ya faru da ita,don a yanzun tana nan tana fama da ido daya wanda jummai ta tsiyayar mata.
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Tunda nene ta yiwa malam na hayi maganar su gizago yace ta kwantar da hankalinta,ta riga ai da ta sani fada da aljani babu dadi,cikin kwana daya ya masa 'yan surkullensa ya rufe bakinsa bai kuwa sake dawo musu.
********
dukkansu suka qarewa dakin qwaya daya kallo mai azabar girma wanda aka ginashi da laka da ciyawa irin ginin qauye sosai,dukka suka dubi malam na hayi dake tsaye burgijaja cikin babbar riga da ta wadatu da maqale maqale na kayan sihiri,fuskarnam cike da suma ha hana qarya wanda yayi fiqi fiqi kamar yana barazanar tsone idon daya daga cikinsu,turo baki zahariyya tayi
''gaskiya malam nidai wanan abu yayi min tsauri,ina laifin ma asama min gida mai dan kyau ba wanann kwangon ba cikin wadancan kucakan mutanen da ake kira da mata,daga su har yaransu ni basa min,maraba da dabbobi don wallahi gwara na zauna da karnuka,da in zauna da su''ta qare maganar tana jan tsaki.
malam na hayi ya qara farashin muzuran da yake yi
''su mata na ne ke kuwa ba matata bace,matar aljani zulan anfaini ce,saboda haka babu ruwanki da wani cikin gidan nan,shi kuwa aljani ina ruwansa da wani kyawun giri,kwata kwata ke din ma ba zaki wuce wata biyu ba zakiyi naki gu,idan kuma zaman din din din kike so kuyi to sai a gaya masa,ya dauko miki gida daga dubai yazo ya ajjiye miki cikin gidan nan ki zabi wanda kike so ya maida sauran,ko kuma ya mayar da ke can bangon duniya kuyi zamanku daga ke sai shi''ido ta zaro tana ja da baya
''a'ah,ni bance ba malam kada ka jawomin salalan tsiya''
''ato,shine nima na gani ai''ya fada yana murza hana qaruarsa cikin zuciyarsa cike fal da sha'awarta,musamman idan ya dubi shigar da tayi sai yaji kamar ya janyota ya fara sha'aninsa a lokacin,zuciyarsa ke kwabarsa yabi a hankali,kada kwabarsa tayi ruwa tunda dai nan da jibi komai zai qare.
Cikin sigar lallashi nene tace
''yo banda abun zahariyya ma kwana nawa anyi an gama,ai dama bayan wuya sai dadi''
caraf adnan ya karbe zancen yana yarfa hannuwa
''ehenn,shine fa,to ni Allah na tuba ko kuttu aka ce na shiga na zauna ba shiga zanyi ba,daga fa 'ya'yan bankin sunzo fa sai yadda kaga damar yi'',hara ra zahariyya ta balla masa
''kaga idan ana zance fa ka daina sako kanka,gwara ma macen da kai''har zai hayyaqo,mata nene ta dakatar da shi don dukkansu biyayya suke mata yanzun lallaba ta suke.
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
kwana uku tsakani nenen da adnan suka rako zahariyyan gidan malam na hayi a matsayin amaryar aljani zul anfaini,babu abinda aka saka dakin face leda da katifa sai wasu qattin labulaye masu azabar nauyi da kauri wanda malam din ne ya saku su suma a dakin suka tadda shi,wai na aljani zul anfaini ne tanan zai dinga zywa gareta,buta ce kawai sai botikin wanka sai kayan sawarta akwati biyu.
sanda zasu koma ji ta dinga yi kamar ta bisu musamman da ta rakasu qofar gidan taga motarsu ta tashi bayan malam na hayi ya danqa muau 'yan dubu dubu sababbi qar na naira dubu dari uku kudin sadakin zahariyyar inji aljani zul'ainaini,ta dinga binsu da kallo suna keta duhin masara har suka bace mata,ajiyar zuciya ta saki tana jin ba dadi amma data tuna nan da wata biyi komai ya daidaita ta zama wata abar kwatance cikin alumma sai taji hankalinta ya kwanta ta juya cike da qwarin gwiwa ta koma cikin gidan.
gida ne tafkeke mai azabar girma kada ma tsakar gidan nasu yaji labari,ko ina ahimfide yake da jar qasa jazur da ita kuwa,gefe fuda bandakinsu yake mai gajeriyar katanga wadda idan kayi wani wawan tsallen ana iya hangoka,babu mamaki don ita kanta katangar gidan ma tsaf wani dogon mutum din zai kamata ya tsallaketa ba tare da ya taka komai ba,gidan tsakiyar gonaki yake,babu wani gida nan kusa da su su kadaine a gun sai dan gaba kadan bukkar da malam na hayi yake dab da wani rafi hakn ne ma yasa ake ce masa malam na hayi don sai ka hau kwale kwale sanna zaka tsallaka dan qaramin qauyen dake maqotansu inda nan din akwai mutane babu laifi.
dakuna ne rututu a jejjere kuma durqusasau kusan babu dakin,ma da ya kai nata kyua cikinsu sai qwaya daya na malam din dake can gefe guda wanda idan ka kalli dakin shi kadai sai ka dauka ba cikin gidan yake ba,gini ne sosai na zamani don hatta da bangon dakin da yar qaramar baranda da aka yi masa duka tiles ne manne da shi,alatu sosai aka zuba ciki duk da bata ganin ainijin cikin dakin amma kallo daya zaka masa daga waje ka gane hakan.
qofar bandakinsu kaca kaca da qasa da dagwalo sauran kadan ta aheqa amai tayi saurin dauke kanta,yara ne guyin guyin da mata gami da yammata gasunan ko ina tsakar gidan tamkar gidan marayu,kallo suke ta binta da shi kamar mayu manyansu da qana nanau,gefe guda kuwa yara ne zaune cincirondo guda dukakkansu babu mai tufar arziqi dan kamfai ne kawai a jikinsu daidaiku ne masu riga 'yar shar hanci kaca kaca da majina sun zuba mata idanu suna kallonta,daya daga cikin yaran ya taso daga cikin cabalbalin da suke wasa ya sheqo a guje yana mata dariya ya kama gefan rigar material din dake jikinta ruwanmadara take kuwa shatin hannunshi suka fito taya taya,batayi wata wata ba ta tsinkeshi da mari sai ga yaron a qasa warwas ya zube,da gudu wata mace cikin matan dake kallonta ta taho,hannu tasa ta dauke yaran ta janye shi gefe ba tare da tace komai ba,tayi tsammanin jin ihun kuka daga gin yaron saidai ga mamakinta ko uhm baice ba saima miqewa da yayi ya koma gun wasansa,kanta tsaye ta shige dakinta cikin bacin ran kayan da ya bata mata.
***********
tun magariba malam na hayi ya shogo ya gaya mata dokokin zaman aure da aljani zul anfaini,dole dakinta ya dinga kasancewa cikin duhu ana yin sallar magariba har garin Allah ya waye,hakanan duk abinda zata gani kada ta sake tace zatq yi magana ko tambaya a kai idan ba haka ba matsala zata biyo baya da haka ya mata sallama yace ya tafi gun iyalinshi.
wajejan sha daya na dare tana kwance cike da,azabar zafi dq sauro,ga matsanancin duhun da ya mamaye dakin,taja tsaki yafi cikin carbi,addu'a take cikin zuciyarta na bacci yazo ya dauketa kota huta,ta saba kwana cikin hasken qwai da sanyin raba kan tattausan gadonta ta lulluba cikin lafiyayuen bargo,yau sai gata cikin wani irin qadagirin daki,ko qauyensu mahaifinta basu taba marmarin zuwa ba sabida sam bata hada hanya ma da maras shi sai gata yau zata kwana cikin wani daji tsakiyar gonaki''kai neman kudi da wuya yake''ta fada cikin zuciyarta,cikin sa'a kuwa baccin yazo yayi awan gaba da ita.
Saidai ko cikakkiyar awa bata yi da fara baccin ba taji wani irin wari mai gigitarwa na ahirin tsaida fitar numfashinta,a rude ta farka daga baccin saidai nata iya ganin koda tafin hannunta saboda tsananin duhun dakin,tayi yunqurin tashi ta kasa saboda wani uban nauyi da taji samanta tare da wani irin nishi da gurnani,ta riga ta saddaqad aljani,zul anfaini ne ya iso saboda haka bata da wani saufan qarfi na qwatar kanta,haka ta koma ta kwanta daidai.
Tasha azabar da bata taba zaton shan irinta,duk da ba budurci gareta ba amma ko ranar da ta bada budurcinta wa saurayinta bata ji kalar wannnan azabar ba,tun tana ganewa har ta fita hayyacinta,bata farka ba saida hayaniya da haaken rana suka cika idonta
a hankali ta dinga bude idonta,haihuwar uwarta haka ta tsinci kanta,da qyar ta samu ta jawo rigarta ta zura,tun a yau ta fara dana sanin auren aljani zul anfaini,ta jima zaune tana tunanin me ya kamata ma tayi,idanunta suka sauka kan wata baqar leda,maiqon da taga tana yi ya sanyar janyota,kaza ce gasashahiya ciki,ture ledar tayi don bata ko burgeta ba,ganin babu sarki sai Allah donko dan tsakin gidan bata ga ya leqota ba ya sanyata miqewa din ta nemi,bandaki,don hatta da jikinta irin doyin jiya da daddare taji yana yi.
Ta fita kanta tsaye tana dingisawa,tun daga nesa ta hango dogon layi babu babba babu uaro kowa yabi,qofar bandakin suke fuskanta kowannansu da botiki wasu da qwarya wasu da kwatanniya cike da ruwa,bata damu ba ta durfafi qofar bandakin tana da niyyar shigewa,ji tayi an fincikota baya cikin wata iriyar dakakkiyar murya
''ina zakije?''waiwayowa tayi don ganin wanda ya mata wannan cin kashin,mace ce saidai idan baka lura da kyau ba zaka iya kiranta da namiji,a murde take,hakanna a tsaye take qyam,idan banda qirjinta da qudundunanniyar sumar kanta babu abinda zai nuna maka cewa ita maca ce,ba shiri ta hadiye tsiwarta da ta qunso ta sanyaya muryarta don ta fuskanci a banza matar zata dakata
''bandaki zan shiga''wata iriyar ashar da duk duniyancin zahariyya bata taba jin irinsa ba matar ta qundumo kana ta dora
''dan uwarku duka wadan nan da kika gani a gun ba mutane bane,duba har da yaran da,basu wuce shekara biyar ba kowa sai yabi layi,saike wata gundumemiyarki da ke zaki wani taho gandan gandan wai ke zaki shiga bandaki,to sai ki shiga mu gani''inji matar tana muzurai.
Ran zahariyya ya baci,tana ganin kamar ita za'a yiwa haka,tsaki ta ja kana ta juya karo na biyu da niyyar shiga bandakin,bata kai qa ida nufinta ba taji an fincikota an watsar take ta samu masauki cikin tabo da dagwalin dake kwance gaban bandakin,cikin tashin hankali ta dago don ganin wanda ya mata wanann danyan aikin
wata figigiyar matashiyace wadda gaba daya jikinta idan banda fata da jijiya babu komai,sai uban qashi a fuska,kallo daya zaka mata ka tabbatar cewa yunwa ta samu gindin zama a jikinta,tsoro da kunya suka hanata cewa komai haka ta miqe tsamo tsamo ta koma dakinta,dariya taji sun rude da ita muryoyi daban daban babu dadin ji yaransu da manyansu,wani baqinciki da bacin rai take ji ya shaqe,duk yadda takeji da rashin arziqi amma wai har yau za'a samu mai taka ta?,malam kawai take jira ta sauje masa kwanson tsiya,sam bazaiyiwu ta zauna cikin irin wannan qasqancin ba,ai neman kudi ba hauka bane,kuma ita ba matarsa bace bare ta shiga sahun irin rayuwarsu.
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Kamar kowanne maraice da suke qare shi gaban qoramar bayan gari yauma haka ne,saidai yau kam akwai banbanci domin,kwanaki uku kenan suke wasan buya da mero,koda wasa taqi haduwa da maryam saboda tsoro da kunyarta,sau daya da safe maryam ta fito ta tadda meron zaune bakin rijiya ta zubawa qofar dakin su ido suka hada udo,kallon da maryam ta yi mata yasa ta miqewa cikib hanzari da kame kame ta hau yin wanke wanken da dama shi zatayi ta zauna zaman kallon dakin,idan ta zo da safe ta yiwa inna wuro aikace aikacenta a gurguje take barin gidan duk da yadda har yanzu zuciyarta taqi yadda ta rabu da abdallah,batajin zata iya ci gaba da rashin ganinshin.
Material ne ajikinta mai santsi milk ne da adon manyan fulawoyi ash colour,dinkin bubane da ya saukar mata har qasa tayi rolling har zuwa kafadarta da mayafi cotting ruwan madara,yadine tissue a jikin abdallah light blue dinkin boda gajeriyae riga iya gwiwa,ba qaramin kyau yayi ba cikin yammacin,wani lokacin maryam kanyi mamakin yadda fatar abdallahn ke qara kyau tamkar ba cikin qauye yake ba,ta alaqanta hakan da yadda weather din garin ke da kyau da ni'imtarwa.
Kamar kowanne lokaci garin a lullume yake,a wadace da korayen tsirrai,a hankali suke tafiya,jinta take kamar wadda kasala zata lullube,shiru suke tafiya hakanan a hankali,abdallah na sake nazarin qauyan,shiru hanyar tasu take yau fiye da kullum,babu gilmawar mutane kamar ragowar kwanakin,duk dama ba hanya ce ta jama'a ba.
''haqiqa Allah mai hikima ne baiwa da kuma cikakken iko,babu shakka Allah ne kadai masanin sirruka da boyayyun al'amura,wannan garin ya amshi sunansu babu ko makawa,a koda yaushe na wayi gari,cikin qauyen nan nakanyi duba izuwa tarin ni'imomi da baiwa da Allah ya musu,hakan yake sake sakani,cikin sakankancewa da iko da isa ta ubangiji,nake sake nisa da nutsuwa gun miqa qoqon bara ta agareshi,tabbas na yadda babu makawa Allah na ji kuma akwai lokacin da zaya bude min gaba daya qofofin ni'imarshi''shiru maryam tayi na saurarensa
sassanyar ajiyar zuciya ya saki shima yana kin kasalar na saukar masa.
''maryam''ya kira sunanta cikin wani irinsalo da ya qarasa kashe mata jikinta gaba daya,hakanan taji bakinta ya mata nauyi ta gaza amsawa
''maryam.....sai yausge zaki bawa zuciyarki dama ta bayyaba abinda yake cikinta?,sai yaushe zaki bata dama yaushe zaki bata 'yancinta?''
gaba daya sai ya qarasa qulle mata duk wasu qofofin qwaqwalwarta ta shiga kai kawon nazarin maganarsa,bilhaqqi da gaskiya ya sake tubudata cikin wani duhun ne,meke cikin zuciyar tata da yake tambayarta ta bata 'yancinta a kansa?,bata kai ga warware qullin ba ya sake jefo mata wata tambayar.
''maryam,sona ne maqare cikin zuciyarki,so na ne yake hanaki sukuni duk lokacin da na kadaice da mero,so na ke saka ki cikin yanayi na kasala da mutuwar jiki,me yasa zaki takureshi a muhalli guda ki hana shi fitowa inda ya dace?''ya waiwayo yana dubanta tare da qoqarin kallon qwayar idanunta
bugun zuciyar ta ya sake yawa,tayi gaggaqar cire qwayar idonta daga cikin tasa ta maidata gefe wani abu na taba zuciyarta,me yasa abdallah ke mata haka ne,ko yaushe rauninta yake son gani kuma bata jin zata barshi ya gani din
zuciyarta ke qarfafarta ta qaryata batun abdallah,cikin muryar da ka mata dogon nazaei qwaya tal zaka gano akwai wani abu mai qarfi cikinta tace
''kada ka soma bari zuciyarka ta dora ka akan keken bera,don ko digo babu wani abu mai kama da so cikin zuciyata game da kai,ko ka manta abdur rahim ta so shi kuma ta aura a zatonta?,saboda haka babu so tsakanina da kai kaima ka sani''.
dan guntun murmushi ya saki sannan yace
''irin wanna karsashi da jurumtar na maryamu na dade ina ganinshi cikin idonta tun tana a matsayin kukun abdallah a gidan mami,saidai wani abu guda da bata sani ba,ta dade da makarowa,tun ranar farko da taga abdallah ta fada tarkon sonsa,duk da jarumtar boyewar da take amm is too late don abdallah ba a iya boyemiahi ire iren wanann abubuwan,don ya saba ganinshi cikin idanun 'yan mata daban daban,amma fa wani abu daya da maryam bata sani ba,abdallah shima ya fara sonta ne tun lokacin da ta fara sonshi,sunso juna a rana guda lokaci guda a guri guda a kuma sakanni guda''.
Gaba daya ilahirin jikinta ya kama rawa har ta gaza ci gaba da rura wheelchair din,wanne tonin silili abdallah ke son yi mata,saidai sam na zata bashi dama ya riga zare mata duk wata laka da qwarin gwiwa dake jikinta ba yadda yaga dama,don haka ta ttara sauran dukkan wani karsashi nata
''idanunka da zuciyarka sun maka qarya abdallah,ban taba sonka ban taba sha'awar na qaunaceka ba ko ka manta da bakinka kasha fadan ba kowacce mace ta dace da kaiba?bako wacce mace ta cancanci ka sota ba,nasan naso abdur rahim amma ba kai ba kuma bana sonka,bana sonka bana......''
idanunshi a rufe suke yana jin saukar maganarta,sukan zuciyarshi take da wani abu mai kaifi ba tare data sani ba,duk da zuciyarshi na qaryata duk wata magana dake fitowa daga bakinta saidai bai son jin furucin sam,sannu kuma kishin abdur rahim mai qarfi ya fara shigarsa,sanadiyyan katsewar maganarta shine fincikota da yayi ta dire a gabanshi,rashin qwarin jikinta ya sanyata zubewa a gaban nashi.
Murmushi ne kan fuskarsa wanda ko yaushe ke fidda sigar kyawunshi
''banyarda baki son abdallah ba sabida na jima da ci miki alwashin sai kin soni,alhmdlh ban zama looser ba ni nayi nasara,but now ina mai qara tabbatar miki sai son abdallah ya ninku cikin zuciyarki fiye da da,i promise''ya fada yana miqa mata qaramin yatsanshi alamar su qulla,ba tare da jinkiri ba ta miqa masa suka qulle kamar yadda yara keyi,shi ya dagata da kanshi ya kade mata jikinta kana suka ci gaba da tafiya.
suna tafe yana murmushi,raguwar kuzarin jikinta kawai ya isheshi amsar tambayarsa,sai da suka qara mintinan da suke yi akan nada kafin su isa ta ajjiyeshi inda ta saba,qur'aninsa ya ciro gaban aljihunsa don kwana biyu da suke tahowa su kadai da alqur'ani yake tahowa,yana yin tilawa kuwa mai yawa kafin su koma,wucewa tayi gurin da ta saba zama kamar ko yaushe ta zauna.
ta daga idonta take ta hango shanun su baffa da kwana biyu bata ganinsu,murmushi ta saki don sun kwana biyin basu gaisa ba,ciro qafafunta tayi ta karkade jikinta bayan ta miqe ta maida takalmanta ta fara tafiya,daga idonshi yayi a hankali ya bita da kallo,yana lura da yadda ko yaushe idan sunzo idonta na tsallaken rafin bai san meke burgeta ba a gun.
kamar ko wanne lokaci daga baya ta tsaya bata shiga cikin shanun ba sai baffa ne ya isketa,tamkar wadanda suka ahekara tare haka suka dinga hirarsu,ta tambaya kwana biyu bata ganin fitowarsu yace eh mai gida ke fidda zaka cikin dabbobin nasa to sai jiya ya kammala shi yasa sai yau suka fito
ba tare dafa tambaya ba ya ciro wani mazubi mai kyau ya fara tatsar mata madara
''mai gida yace duk sanda ka zo a baka,yana ta tambayarka ma''tayi murmushi tana fadin
''Allah sarki na gode kuwa baffa''ta miqa hannu ta karbi mazubin tayi bismillah ta fara sha
''kisha ahankali idan bai isa ba ma sai a qara miki''taji muryar daga gefanta na gada,ta daga kanta ahankali,mahmud ne yauma cikin shigar kufta,murmushi ta danyi kana ta ja baya tana fadin
''ina wuni''ya amsa mata da ''lafiya lau,tun rannan kuma sai kika bace abunki ban sake ganinki ba''
'?eh wlh ta amsa masa a taqaice tana rufe mazubin ta miqawa baffa
''baffa gashi na gode ni zan wuce''
''a'ah,jeki da shi meramu,duk lokacib da kike so kizo da shi sai a dinga zuba miki ciki''godiya ta masa don abun ya mata kyau,dan mazubi ne maikyau irin na fulani
''zaki gudu kenan kam irin na rannan?''ya tambayeta yana dan dada sauri don su jera tare
''a'ah,bani kadaice bace na fada maka,da yayana kuma mijina muke tare''ta fada cikin rashin sakin jiki
dariya ya saka
''wai ni zaki yiwa wayo,don kin fuskanci na yaba ko?''
kai ta girgiza idanunta a qasa
''da gaake ni matar aure ce''
''nima mijin aure ne''ya maida mata amsa cikin maida maganar wasa wasa,ganin da gaske yaqi yarda din ya sata tsayawa da tafiyar da takeyi don sun,kusa da inda abdallah yake bayan ta rage fara'ar fuskarta sosai
''idan baka amince ba muje ka ganshi da idonka,amma ka fara yin gaba tukun yana nan zaune akan kujera idan yaso sai na biyo bayanka''.
kafada ya daga kana yace
''is ok,bari nayi gaban,amma da sharadin idan qarya kike zaki amshi soyayyata''
kada kai tayi kawai ba tare da tace komai ba idanunta suka sauka kan abdallah zaune kan kujerarsa a gabansu,mamakin yadda ya iya kawo kanshi tayi,sai ta dubi kujerar wasu abubuwa guda biyu ta gani gefe da gefe bata taba kula da su ba wanda bisa alamu da su ya tuqa kanshi.
Kallo daya ta yiwa idonshi bata sake marmarun kuma kallonsu ba,ya kalleta ya kalki mahmud sai taga ya danna wani abu,rivearse kujerar tayi da kanta kana ta saita hanya ya soma tafiya sannu a hankali
''ko baki fada ba nasan shine mijinkin,kiyi haquri don Allah,wlh harga Allah ban dauka da gaske kike ba''mahmud ya fada cike da damuwa
a gagguce ta gyada kai bata samu cewa komai ba ta biyo bayan abdallah.
*mrs muhammd ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[2:00pm, 9/29/2017] Huguma👑: [11:46am, 9/29/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
5⃣0⃣
👁👁👁👁👁👂🏾👅
*_shin ka/kina lura kuwa 'yar uwa?,kin fuskanci kuwa yadda kwanaki keta zura gudu abinsu?,kinsan me hakan yake nufi a gareka/ki?,tamkar gaya miki suke kifa shirya kina kusantar kabari ne,ki shirya kina kisantar ajalinki,ki shirya kwanakin ki na duniya da aka diba miki na qarewa_*
*_daure ki aikata mai kyau don ki tarar da me kyau,babu yadda za'ayi ki shuka qaya kice inibi kikeson cira,duk fitar numfashinki daya daidai yake da kusantowar ajalinki,yadda idan second guda ta kubuce miki har abda bazata dawo ba haka ajalinki idan yazo daidai da qiftawar ido Allah bazai barki cikin duniya ba,to don me zaki batawa kanki lokaci kan cutar da wani?,don me zaki damu kanki da ababan duniya,duniyar da take wulaqantacciya?,duniyar da Allah yace bata kai qima da darajar da girma daidai da na fukafukin sauro a gurinsa ba,saboda me zaki shagala kin manta ki daina tuna mutuwa,bayan kina da yaqinin tabbas/lallai/babu makawa sai kin muyu kamar yadda kika ga wasu sun mace kema wataran haka ne,komai qararre ne banda zatin Allah,ya ubangijin kowa da komai ya mai rahama da tausayin bayinsa kasa muyi kyakkyawan qarshe,mu mutu muna kan tafarkinka na gaskiya_*
*ALHAMDULILLAHI ALA NI'IMATUL ISLAM*
*_kafin na fara shafin nan ya zama dole na gaisar na kuma miqa godiya ta ga masu aiko da saqonninsu gareni,saqonninku sun ishemin,ina muku fatan alkhairi naji dadi qwarai da addu'o'inku,abinda kuketa roqamin na alkhairi ina fatan Allah ya sanyaku ciki kuma_*
*ummi jos*
*mrs tafida*
*haulat m badamasi*
*Aisha kanyah*
*ummu zainab*
*sis rabi'a*
*jammy jammy zbi group*
*zahra hari zbi group*
*na gode Allah ya bar zumunci da qauna*🙏🏽
Cikin kwana goma sha hudu da zahariyya tayi cikin gidan ba qaramar dandana kudarta tayi ba,sauqinta daya malam na hayi ya tsawatarwa iyalin nasa bayan bore da tayi ta samu sauqin abubuwa,saidai babu mai kulata ci kanki babu mai ce mata,ita din ma bata damu ba domin ta dade da raina ajawalinsu,tana ganin babu wadda tayi isar da zqtq rabe ta balle mu'amala ta hadasu,banda neman biyan buqata daya tilasta ta zama cikinsu ba su isa ta zauna da su ba har wata guda,ba don suna waya da nene ba tana tausarta ta tabbatar da tuni ta jima da cika bujenta da iska,wuyar ta isheta,kullum dare kwana ake ana abu daya ita da aljani zul anfaini,ga masifaffen wari da take ji jikin aljanin wanda kullum yake sata tashi da amai da ciwon kai
Dadin bakin neme da lussafin da tayi na saura sati biyu ta bar wanann zaman shahadar,saura sati biyu ta zama mai arziqi irin aezuqin nan na kwatance na gayawa sa'a yasa ta danne taci gaba da lissafin
********
Misalin sha biyu ne na rana wanda ko ba'a fada maka ba kasan lokaci ne da rana ke kan ganiyar zafinta,bare rana irin ta qauye da take budewa sosai saboda wadatar fili da suke da shi,tana cikin dakin amma ji take kamar tayi hauka,ta riga da ta saba zama cikin a.c ko yaushe,rufin dakin na langa langa kawai ya taimaka wajan qaro dumamar zafin ranar zuwa cikin dakin
tsaki ta ja tana goge gumi
''kai,Allah ka tsinewa talauci,me za'ayi da talauci don Allah,Allah ka nuna cikar sati biyun nan nayi na gama wannan aikin na san inda dare ya yimin,ai wlh ko a hanya bazan bari mu hadu da talauci ba,zamana nan gidan kawai ya qara fito min da illarsa qarara wadda a baya ban sani ba,haba wannan azaba dole ne ma fa kasona cikin dukiyar abdallah tafi yawa idan mun karbe wallahi''ita kadai take sumbatu cikin dakin,vest,ce kawaia a jikinta doguwa har zuwa gwiwa amma ji take kamar tayi tsirara
kallo daya zaka mata kaga yadda fatarta tayo baqi ta kuma rame a hakan ma wai aljanin mujinta na dauke mata abinci irin wanda ta saba ci yake kawo mata,ta kuma jan tsaki ta gyara kwanciyarta kan katifar ta don dama ikin kenan,idan ta kwanta irin haka ko sallah saidai ta yi maja ta hadeta baki daya
Karo na farko taji ana qoqarin dago jibgegen labulen dakin da ya qara sawa dakin duhu,kanta ta dago don ganin waye,domin bata taba ganin wani ya rqbo bakin qofar dakin nata ba idan ka dauke malam na hayi
siriryar macace wadda a kallon farko zaka gane sanda duniya na damawa da ita fara ce,wuya da yunwa suka maidata baqa baqa duk da akwai sauran haskenta,tsugunnawa tayi gefan zahariyya da ta zuba mata ido tana kallonta bayab tayi kicin kicin da rai,murmushi matar ta saki wanda ya bayyana jerarrun haqoranta da suka dafe
''sannu amarya,dama zuwa nayi na gaya miki ki fito yau zaki amshi girki''
Ba shiri ta miqe zaune daga kwanciyar da take a dazu,ckkin sake hade girar dama data qasa tace
''ke malama,bana son hauka,wa ya gaya miki ni matar gidan nan ce?,akwai abunda ya kawo ni zama nan kuma nan da sati biyi zan bar muku wanann dajin naku''
murmushi ta gani matar ta yi har da dan darawa kadan
''Allah sarki,ina zaton azal din data hau kaina kema ita ta hau kanki''cikin raahin fahimta take dubanta,daga bisani ganin matar bata da niyyar cewa komai ta kafe zahariyyan da ido yasa ta tambayeta
''kamar yaya?''ajiuar numfashi tayi,wannan karon zama tayi dirshan kan ledar dakin
''malam ga aureki ba tare da sanin cewa shi kika aura ba ko''
''inji uban wa?,ni ba malam na aura ba,aljani zul'anfaini na aura,kuma ina sane,kada ki zomin da maganar banza,malam din da sai da safe yake leqoni mu gaisa ko ya kawomin saqon aljani''
dariya ta subucewa matar sai da tayi iya yinya kana ta tsagaita,zahariyya bata samu faragar tsaidata ba don kanta a qulle yake tamau
qasa qasa tayi da muryata kana tayi yan dube dube don tabbatar da babu wanda yake jinsu
''akwai wani aljani ne bayan malam na hayi?,ai malam shine aljani,zul'anfaini yana biyo dare yana turmusheki da sunan aljani,dalili,kenan da ya kafa miki sharadin zama cikin duhu daga magariba har gari ya waye''
tsawa zahariyya ta daka mata jikinta ya soma bari
''ke malama,banasom hauka don na fuskqnci duka jama'ar cikin gidan nan kamar daga gidan mahaukata aka debo ku''
murmushi fa kuma yi
''kema din kwana nawa ne kinbi sahu,badai kin gama kwana goma sha hudunki ba,ki fara duban hanya to''daga haka matar ta miqe tana niyyar ficewa,ganin indai ta fice din kuma babu lallai zahariyya ta sake samun wasu bayanai ba tunda babu da wanda take magana hakanan babu wanda ke magana da ita ya sanya ta riqo gefan daddaudan zaninta
''ya zaki sakani a duhu kuma ki tafi,don Allah zauna kimin bayani mana''sai data qarewa zahariyyan kallo na kusan minti biyar har taji ta tsargu sannan ta koma ta zauna inda ta tashin
''suna na habiba,ni nan da kika ganni ada yadda kike haka nake koma nace na fiki''cike da mamaki zahariyya ke kallin habiban wadda babu mugumin da zai kalleta baice mahaukaciya bace
''mamaki kike,to ki daina mamaki don kema lokaci kadan ya rage ki koma kamar mu,ba kanki malam ya fara haka ba,'yar gata ce ni gaba da baya,don gaba daya a buja muke zaune ni da iyaye na,haka da na tashi aure ma acan nayi aure na,na auri mijina mai kudin gaske saidai na taddashi da matarsa da yaransa uku,matarsa fatima sam bata da fitina,duk yadda taso mu zauna lafiya fur naqi,burina kawai shine na koreta daga gidan na mallake enginer abubakar,iya adalci yana nina shi tsakaninmu babu zalunci tattare da shi,wani abun ma haqqinta ne fatima amma zata ce ta barmin sabida haqurinta da kawaici,duk inda nasan zan samu malami da zai mini aiki na kutsa kai na sai dai babu nasara,sabida fatima irin matan nan ne masu yawan azumi duk litinin da alhamis bai wuceta,haka tana da yawan salla musamman ta dare,don nasha tashi aiwata da mugun nufina a kanta sai na taddata tana sallah,haka karatun alqur'ani,kafin ka samu fatima kan wata tasha ba saudi qur'an ba kai da wuya,amma hakan bai isheni iahara ba,da yake bata da haqqina Allah na tare da kta kuma yayi nufin kareta sai muka samu labarin malam na hayi
Babu bata lokaci muka shirya ni da mahaifiyata wadda ita ke taya bera bari na yiwa enginer qaryan zamu kano ziyarar yan uwan mama duk da salinmu ba kanawan bane yan katsina ne ya sani amma baice komai ba ya amince ya barni,har da bani kudi nayi tsaraba,har bakin mota fatima ta rakoni tasa yaranta na min a dawo lafiya amma ko kallo basu isheni ba muka taho,tun zuwan mu na farko yaci ace idan da ni mai rabo ce na gane inda malam na hayi ya dosa saboda kalamai da hanyoyin da riqa bi da ni neman biyab buqatarsa amma na kauce na qiya,qarshe ya harhada min duk wani abu da zan aiwatar cikin gidan muka taho bayan iyayen kudi da muka zube masa,amma wani abu da ya bani mamaki tsakanin fatima ko 'ya'yanta babu wanda yayi ciwon kai bare na sa tsammanin wani mummunan abu zai faru da su,ta tsaya tsayin daka wajen yiwa yaranta addu'ar tsari,hakanan lokuta da dama zaka ga ta cika botiki da ruwa ta musu tofin ayoyin tsari ta sa musu a frigde shine ruwan shansu duk da ruwan roba da mahaifinsu ke cika mana firizai da shi
ko cikin dare udan ta farka duk da ba dakinsu daya da yarqn ba sai ta leqa dakinsu ta tofa musu addu'o'i take komawa nata dakin nasha ganinhakan da idona,to duk abuna musulma ce ni kuma masan addu'a takobin mumini ce nice dai nasa qafa na shure,na tabbatar bazan nasar a kan fatima ba don,haka hankalina ya tashi ba bata lokaci muka sake dawowa,ashe zuwan tsautsayi da qaddara mukayi
cemin yayi kada na damu akwai wani abban aljaninsa da zai bawa kwangilar aikinsu fatima amma shifa ba biyansa ake da kudi ba,ana biyansa ne ta hanyar auransa na wasu satitika ko watanni,da fari tuburewa nayi ganin da akwai auren enginer a kaina,amma da dadin baki malam ya ciyo kaina yace sati biyu kacal zanyi zaman auren ina komawa gida na zan taras buqata ta biya,nace ta yaya za'ayi mikina ya barni nayi tafiya har ta tsawon sati uku,wani garin magani da wasu layoyi ya,bani yace na samu dutse cikin gidan mu qato na daga qasanshi na saka na danne,yadda na danne layoyin nan haka engineer zai kasa min musu duk sanda na tambayeshi,haka kuwa akayi baice komai ba face Allah ya kiyaye hanya sai na dawo
satina daya cikin gidan ina wahala don ban saba ba sam,cikin daula na tashi haka cikin gidan mijina ma,amma da yake son zuciya da son duniya ya rufemin ido na daure a haka har nayi kwana goma sha biyu,kamar irin wannan lokacin da na zo miki haka daya daga cikin matansa tazo min da irin maganar da nazo miki uadda kika yimin haka nayi mata nima,yadda na zauna na baki labarina haka ta bani labarinta ita din ma duk kusan hakane,saidai ita maganin mallaka tazo ta karba,mallakar ma ra saurayi,saidai ita tasan malam ne zai aureta don yace wani rubutu zai dinga yi a alqalaminsa yana wanke mata acikinta,ta gayan har yau ta kasa kubuta daga gunsa,na fiki shiga tashin hankali sabida tuno mijina da gidana da iyayena da nayi da yarona qwaya daya da na haifa yana gida hannun fatima tace zqta riqe minshi har na dawo
Na fita da niyyar guduwa daga gidan saidai kinsan me?,wuni nayi ina shawagi cikin duhun masada da na dawa,an qullemin kaina tamau na rasa hanya,duk inda na kewaya ina tsammanin zai fita sai inga na dawo gidan nan,daga qarshe da duhun dare yamin babu wanda ya neme ni haka na dawo,kwana na bakwai ina wannan wahalar cikin gidan babu wanda yace min ci kanki hatta da shi malam din haka zan gama walagigi na na dawo,daga qarshe na tabbatar bazan iya kubuta ba haka na dawo naci gaba da zama na fawwalawa Allah lamura na,ina zaune cikin uqubqar malam din,matansa mu goma sha hudu ne kowacce tana da rana daya a matsayin ranar girkinta,yaransa guda hamsin ne,wasu suna nan tare da mu wasu sun watsu duniya,nima haihuwata uku da shi suna mutuwa yanzu haka yaronmu daya da shi shine wanda kika mara rannan kaltime ta janyeshi,mamata kuwa ban kuma jin duriyarta ba,wani abun ya manta ta manta ni ko itama kasa gane gidan tayi Allah masani''ta qarashe maganar cike dq dacin rai da danasanin butulcewa ni'imar Allah da tayi,ta kasa zama lafiya a gidan aurenta bayan babu abinda ta rasa,dama ance idan baka godewa ni'imar Allah ba ka godewa azabarsa.
Tuni har zahariyya ta saki fitsari a zaune,gumin da take kuwa tuni ya ninka na dazu,ta tabbatar idan da za'a auna jininta banu makawa za'a ga ya hau over ma akuwa
taya za'ayi ta zauna da wulaqantaccen mutum kamar malam na hayin
Tayaya zata yarda ta zama mallakarsa,wallahi bazai yiwu ba''ta fada qarfi kuma a fili tana miqewa ta fara hada akwatunanta
kallonta habiba tayi
''wai me kike shirin aiwatarwa''a fusace kuma cikin ficewar hayyaci
''wallahi sai na bar gidan nan ko da me malam yake taqama din ni ba kalarsa bace,kudin ma raina muku wayau yayi''dariya habiba tayi
''duk yadda kike jin isa taurin kai da kafiya na fiki,malam mutum ne da baisan kalmar imani ba bare tausayi,ina mai baki shawara ki haqura ki maida lamarinki ga Allah ki roqeshi,watan wata rana idan da rabo kowa sai Allah ya kubutar da shi,amma,ina mai tabbatar miki koda kin fita ba zaki iya tsira ba,idan kuma baki yadda ba kina musu bismillah''daga haka habiba ta miqe ta gyara daurin zaninta ta fice
ko kadan zancan habiban bai shiga kunnuwanta ba don haka bata fasa shirinta ba,ta hada kayanta ysaf ta canja kayan jikinta ta jawo akwatunanta tayo tsakar gidan,da ido suka bita duuu kamar ko yaushe,wanann karon sam bata damu da kallonsu ba burinta kawai shine ta ganta ckkin gidansu
Cak ta tsaya a qofar gidan tana wara ido,ruwa ne a gabanta yake ta qugi iya ganinta,,duk hanyar da zata bi ta wuce ta zam hamshaqin kogi wanda ko da kwale kwale zaiyi wuya ka iya tsallakeshi don har wani murdawa igiyar ruwan take,duk lokacin data yi taurin rai ta tunkari kogin ta yunqura dan shigewa ruwan sai yayo ambaliya yayo,kanta tilas ta koma da bay
ta shafe fiye da awa biyu a gun tana abu daya daga qarshe ta gaji ta faahe da kuka don ta fara ganin alamun maganganun habiba
zubewa tayi a dandaganyar gun ta saki kuka tana addu'ar Allah yasa mafarki take,ya rayuwa zatq juya mata baya haka lokaci guda ba tare da ta shirya ba,dabara ta fado mata ta dauko wayarta ta soma lalubar nene don neman daukinta
Daidai lokacin da nene da adnan ke tsaye cikin daki cike da tashin hankali sakamakon waya da muugu yayi wa maman kan ta taryi zuwansa,kuma kada ta taba darsawa aranta zata gudu duk inda suka shiga sai ya bincikota kuma babu shakka kasheta zaiyi
''yanzu adnan meye abunyi?,meye abunyi?,na kikkira malam wayarsa bata samuwa,babu shakka aikin da yayiwa muugu ne ya warware''ta fada cike da tsananin tashin hankalin,shi kansa adanan din a tsorace yace don har yau bai warke ba daga bugun da suka masa,jikinsa na rawa yace
''don Allah mama ki nemo kudinsu ki basu kawai mu rabu lafiya,wlh basu da imani mutanan nan sun saba da kisa fa''
cikin jin zafi take kallinshi,saida ta zageahi sanann tace
''fashi da makami kake so na far ko karuwanci,a ina zan samu wata miliyan biyu?''
''yauwa mama''ya fada da sauri yana dubanta
''ki cewa hajiya bintu ta baki mana bana ko kokwanto akwai a hannunta''
''mtsweew,wlh bansan na haifi jaki mai toshashshiyar qwaqwalwa ba sai yau,ina cewa a gabanka malam ya gaya mana kada mu sake magana ta qara shiga tsakaninmu,ni ko kai ko zubaida idan ba haka ba asirin da yake jikinta zai karye?bacin haka ma kwananta nawa bata cikin gidan nan ni da kai duka babu wanda yasan inda ta tafi?,kuma wa'adin cikar aikin zahariyya har tau bai cika ba saura sati niyi bare mu sa ran samun wani abu''
''gashi babu company din da muka karbe qwaya daya dake aiki yanzu bare mu samu cikinshi,duk a qulle suje mun cinye duk wata dukiya nene dake ciki''ya fada yana kallon nenen da ta kasa amsawa sai ido ta take binsa da shi cikin damuwa
shiru yayi cike da tsoro
''to nene ko gwalagwalan su zubaida zaki karba ki bashi ya saida,idan yaso muji nawa zamu cika masa''
''haka za'ayi''ta fada cikin rawar jiki tana barin dakin ya rufa mata baya
ta tura qofar dakin ta shiga babu kowa ciki saidai tana iya jiyo kakarin amai cikin toilet dinsu,da sauri ta qarasa bandakin,zubaidan ce tsaye gaban sink tana ta faman kwara uban amai,cak nenen ta tsaya tana mata kallon tuhuma har ta kammala ta kuskure bakinta ta juyo
''zubaida me nake gani?''
ta tambayeta cike da tashin hankali,ko kadan zarafin da ta shiga na kwanakin nan yasa bata samu damar zama agida bare ta qarewa zubaidar kallo,ta dashe tayi fari ga cikinta da ya fara dan dagawa kadan,kallo daya tak mai hankali zai mata ya bawa kansa amsar ciki ne da ita
fuska ta yatsina tana kallonta tare da qiqarin boye cikin
''wlh nene nima bansan me yake damuna ba''hannu ya saka ta daki cikin jikinta tace
''don uwarki don ubaki tsinanniya ga abunda yake damunki nan''take zubaidan ta durqushe tana dafe da cikin hadi da cewa ''wayyo Allah na''nenen bata damu ba ta finciko ta sai ganinsu adanan yayi tana janye da ita bata saurara mata ba taci gaba da janya sai da ta kawota har falon qasa kana ta watsar da ita
''don uwarki sai kin gayan wanda ya miki cikin nan,shegiya tsinanniya mara amfani,gwara na kasheki na kashe banza bani da asara,cikin shege a jikinki zubaida''ta kai mata duka ta kuwa sameta,qara zubaidan ta saki wanda yayi daidai da shigowar kira a wayarta
a niyyarta ta cilla da wayar sabida tashin hankalin da ta fada amma ganin sunan zahariyya yasa jiki na rawa ta daga tana fadin 'yar albarka
komai sai ya tsaya mata cak jin bayanan bakin zahariyyan data yi wanda tana kuka tana zayyane mata,bata ma gama ji ba ta dakatar da ita tana fadin
''gani nan zuwa har gun malam din,shi ya isa shi din banza,a kaidina baisan komai ba yau zai sani''qita taji wayar ta katse haka zahariyyan taji,tana dubawa taga kudinta ne suka qare haka wayar ta soma warning na battery low,dama a power bank dinta da ta taho da ita take chargyn tunda ko sau daya bata taba ganinsu da wutar lantarki ba,kai ko igiyoyin wutar ma babu a ina ma zasu samu suna dajin Allah?,tana ji tana gani wayar ta mutu,hannu ta dora aka ta saki wani sabon kukan ta kife kanta tsakanin cinyoyinta
Sau uku nene na trying na kiranta sai ace mata is switched off,tilas ta haqura ta kalli adnan
''muje adnan gurin malam,wani bala'in yake son jawo mana''adnan ya zaro ido don shi,kam ya gaji da jin wannan bala'i kala kala har yau kuma babu sauqi,zaiyi magana tace
''kame bakinka muje koma mene kaji a mota''ta juya ta kalli zubaida dake durqushe
''ke kuma idan ba shirya barin duniya kika yi ba to ki nemo wanda ya miki ciki tin kafin na dawo na aikaki lahira''ta kaimata mari tana sake tsaine mata ta kuwa sameta akuncinta,dafe kuncin tayi tana fidda qwalla ba don komai ba sai don azabar zafin marin
''ga wanda yamin cikin nan''taji zubaida ta fada,ta dago kanta daga qoqarin sanya mayafin ta da take tana duban inda zubaidan ke nuna mata,saura kadan numfashinta ya dauke sakamakon ido hudun da sukayi da muuugu da yaranshi,fuskarnan yadda kasan wanda ya dauko saqon mutuwa a hade take tsaf,abu biyu zuwa uku ne suka daki zuciyar nene lokaci guda,kudinsa da yazo karba wanda a yanzu bata da shi bata da shi bata da dalilinshi,na biyu cikin da yake jikin yarta wai nasa ne?,na uku yadda taga sun cukuikuye adnan ko cikakken numfashi baya shaqa
sakin adnan din sukayi yaci qasa kana ua tako a hankali gaban nene yana jujjuya wuqar dake hannunshi,batason ta nuna masa tsoratarta don haka ta tattaro yar mitsitsiyar dauriya ta dorawa fuskarta don bata kai zuciyarta ba,hannu ya miqa mata,sai ta kalleshi sheqeqe
''me kake nufi?''dariya ya kece da ita wanda har hantar cikin nene sai data kada balle adanan da ya dade da sakin gudawa,don b qaramin tsoron mutuwa yake ba arayuwarshi
''banda ke mara mutunci ce har sai na miki bayani ma,zan mkki bayani amma ki tabbatar a bakin rayuwarki''
ta tsorata ainun amma sai ta fara masa haukan qarya
''banda kai matsiyaci ne baka da kunya ko misqalazarratin,ka dirkawa diyatq ciki sannan kuma kace na biyaka wadansu kudade,to wallahi na fika iya iskanci,baka isa ba''
Daya dagq cikin yaransa ya matso yana fadin
''ke hajiya ki iya bakinki,ai dama kowa yasai rariya yasan zata zubda ruwa,bamu da mutumci kamar yadda ke ma baki da shi don babu mai mutumcin dake hada sabgarsa da mu''
''kai yaro dakata a haife na haifeku gaba dayanku,to wallahi duk ba tsoronku nake ba,kudi ne bazan biya ba kuma ku saurari sammacin kotu sai nayi shari'a da kai kam cikin da ka yiwa diyata tun.......''
wani kyakkyawan duka da ya sauka tsakiyar kanta ya haddasa wa qwaqwalwarta daina aiki na wucin gadi,wasu taurari suka kewaye idanunta take ta sulale ta fadi a gun,sai da ta kusa kusan minti biyu sannan jinta ya dawo sai ta kasa bude idanunta,mugu ya tako inda take ya tsaya qerere a samanta yana dubanta
''da niyyar kasheki nazo ke da wancan wawan dan naki qauran mata,amma kunci darajar abinda yake cikin yarki wanda dana ne kuma jikanki,nasan kina jina don ban miki dukan da zaki mutu ba,amma zan baki zabi biyu,ko ki biyani kudina ko kuma na dauke yarki ta zama matarmu,na baki nan da kwana biyar kiyi shawara''
ya juya ya isa inda zubaida take ya dagata ya rungumeta yana shafa cikinta
''kada ki sake ki bari wani abu ya samu cikinan don ina buqatar wanda zai gajeni,duk dan kaza kazan(ya duro ashar) da ya kuma takuraki ki takashi kema yadda ranki keso''ya fada yana sakinta,ga mamakin adnan murmushi yaga tana yiwa mugu har suka juya suka fice daga gidan wanda shigowar mami suka yi kacibus suna ficewa a qasa ita kuma tana shigowa da motarta
bayan ta faka motar cikin mamaki ta fito ta nufi gun security guda uku da su kadai yanzu suka rage a gidan
cikin girmamawa suke gaidata don har yau suna son uwar gijiyar tasu,tambayarsu tayi
''wadan nan mutanen kuma daga ina suka fito''
daya daga cikinsu ne ya amsa mata
''daga cikin gida''fuskarta qunshe da mamaki ta sake tambayarsu
''cikin gida kuma?,gurin wa suka zo?''
wannan karon wani daban ne ya amsa mata
''gun hajiya nene,ai sun dade suna zuwa gunta,ko kin manta ne hajiya,kwanaki ke ta saka kika basu kudin mota''
cike da mamaki ta nuna kanta
''ni?ni kuma usaini?''
''eh hajiya ke''
ganin sun zuba mata ido sunata kallonta sai ta dauko wani batun
''yanzu ina su samuel da ibrahim''
''hajiya duk an dakatar da sh daga aiki,kuma da aka tambayeki kika ce kin amince,yanzu saura security biyar daga cikin goma sha biyar dake aiki cikin gidannan''
wani mamakin ya sake kamata,jinjina kai ta dinga yi don duka batasan anyi haka ba,ta yaya zata kori su ibrahim bayan sune manya manyan security na gidan tun zamanin alhj abdulkareem mai nasara na da rai,muta ne ne masu amana da cikon alqawari
''ka nemi numbers dinsu ka kira ka kirasu gaba daya kace ina son ganinsu daga yau zuwa gobe,wanda baka samu,contact dinshi ba ka dauki mota ka bishi inda kasan zaka sameshi''
cikin jin dadi yace
''yes madam'' don dukkansu suna fara ganin alamun lallai sauyi ne wata qila yake tunkaro gidan
Har tayi gaba ta dawo
''kada a sake barin wani mutum makamancin wadancan mutanen su shigo gidan nan''
cike da bin umarni suka amsa
waiwayo wa ta sakeyi
''amm...usaini,bama su ba duk baqon da za'ayi ku tabbatar da wane shi kafin shigowarsa gidan nan kamar dai yadda aka saba a daa''nan ma amsa mata sukayi a ladabce kana tayi gaba
idanunta suka kai ga hanyar sashen abdallah,can qasan zuciyarta taji tana son shiga saidai wani abu ya taso ya danneta,haka tana ji tana gani ta sauya akala ta shige bangarensu tana ambaton ya Allahu
har zata shige ta ringa jiyo ihu ihu a bangaren nene,juyawa tayi ta nufi sashen nenen don ganin meke faruwa
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
A hankali ta qarasa shigowa cikin dakin hannunta dauke da tray dake jere da kwanukan abinci a kansa,gabanshi ta qarasa ta ajjiye tray din,wanda har ta shigo ta ajjiye din yana zaune kan wheel chair dinshi kanshi a duqe a qasa,shi kadai ahi da Allahn sa yasan abinda yake ji cikin qirjinsa,wani irin zafi radadi da quna,da zai iya yana kin fiddo da zuciyarshi zaiyi waje ya huta irin azabar da yake ji,bai taba sanin so da kishi masifa bane sai yau,baiyi tsammanin son da yake mata har yayi irin wanann girman ba,ya sani cewa yana ganin qimarta fiye da duk yadda yake ganin qimar wata diya mace a duniya idan ka dauke maminsa,tana da wani girma na daban a idaniyarsa da zuciyarsa ma baki daya,wannan ne karo na farko da tunda yazo duniya kishinsa kan wata diya mace ya motsa,shi kansa baiyi zaton kishinsa ya kai haka ba,duk da agefe guda qoqarin goge firman laifin da ta yi masa yake ta faman yi saidai ina zuciyar taqi aminta,idanuwan su gaza daina hango masa maryamunsa tsaye da wani
batasan gurin da ya tsaya ba tare suka taho daga rafin malam dogo amma sai gashi har ta shigo gidan sukayi sallar magariba da isha bai shigowa ba,sai bayan isha'i ya shigo bai kuma tsaya ba kanshi tsaye ya shigo dakin dama kuma bai tadda inna wuro ba a tsakar gida ta ahiga daki dauko kayan kadinta
Jikinta gaba daya a sanyaye take,wani saahen na zuciyarta na ganin wane laifi tayi ba ita ta kira ahmad ba kuma ta riga da ta gaya masa tare suke,Allah kuma shaida ne bada wani abu ta kula shi ba,gaisuwa ce kawai ta shiga tsakaninsu
wannan tunanin ya qarfafa mata gwiwa tana tsaye a gabanshin tace
''abdallah''
''abdallah''shiru taji tamkar ba da shi take ba
''abdallah ga abincinka,ina ka tsaya na ahigo inna wuro tana tambayata inda ka tsaya sai qarya na mata,me yake damunka ne?''
shiru nan ma taji
''na zuba maka tuwo ne inna ta.....''
dagowar da yayi ya sanyata ja da baya zuciyarta na bugun uku uku,wani irin birkicewa ta ga idanunshi sunyi,wani matsanancin tashin hankali take hangowa qarar cikin idanunshi,farar fuskarshi ta hada ja kamar wanda aka mammara
Ga mamakinta sai taga ya saki murmushi yana fadin
''na gode da abinci,amma bazan iya ci ba''ya maida kansa qas kamar yadda tazo ta taras da shi,ajiyar zuciya ta sauke cikin,mutuwar jiki ta sake dawowa gabanshi ta duqa tana mai janyo kwanunkan
''dazun da rana baka ci abinci ba,bazai yiwu yanzun ma kace ba zaka ci ba''ta fara zuba masa kana ta miqa masa
Sake kallonta yayi,wannan karon raunin dake tattare da idanun abdallahn yafi na dazu,ita kanta sai da abun ya taba ta,irin raunin da ko sanda lalura ta sameshi bata gani,cikin idanunshi ba,murmushin ya kuma yi kana yace
''haqiqa Allah na iua jarabtar bawanshi ta kowanne fanni da yaga dama,ban yarda cewa ni abdallah cikakken maraya bane sai yau,na rasa mahaifina na rasa soyayyar mahaifiyata haka na rasa soyayyar macen da na riga nayi amanna cewa zata zauna da ni a duk yadda nake ko kuma nazo mata,saidai tunani na ashe kuskure ne?,duk da bai kamata naga laifinki ba maryam baki rufeni ba,kin gayamin baki sona bani kike so ba amma na gaza cika miki muradinki na rabuwa da alaqaqai abdallah,baqinciki na daya maryam igiyar aure na da aka hau kan martabarta aka tuburbudawa qasa,na yaba miki kuma ina kan yaba miki kan namijin qoqarin da kika yi kike kuma kan yi na bawa,rayuwata kariya,haqiqa bani da abunda zan iya biyanki da shi,na miki kuma alqawarin da zarar na samu lafiya zan cika miki burinki na rabuwa da ni,kici gaba da yimin alfarma zama da ni kada wasu su fuskanci wani abu,na miki alqawarin daina saki yimin duk wata wahala,kidai ci gaba da zama da ni din har na samu lpy idan da rabon haka ni kuma na baki 'yancinki da kike da muradi''
Hakanan taji maganar ta daki zuciyarta sosai,tayi yinqurin duban qwayar idanunsa saidai ta kasa tilas tayi maganar tana kallan wani gurin daban
''yanzu me nayi maka haka da kake gayamin wadan nan maganganun,duka mai ya taso da su?idan maganar ahmad kake ni babu komai tsakani na da shi hasalima zuwa yayi ku gaisa''
ambatar sunanshi shi ya dago hasalar da yaketa qoqarin dannewa,cikin tsawa yace
''ahmad yake ko watever ba ruwa na da shi,ba maganarsa muke ba anan,magan ce tsakanin na da ke,don kin kula shi kun saba har kunsan juna wannan tsakaninku ne,igiyar aure na nada qima da mutunci a wajena tunda na biya sadaki,ni ba ragon namiji bane tun fil'azar jarabtar da Allah yayimin bazata zama silar zamowa na rago ba,kin cancanci kiyi hakan don a yanzun kinfi qarfin abdallah nakasashshe,sai cikakken namiji mai lafiya ba irina ba,saidai ki sani,har yanzu igiya ta na kanki so kiyi respecting dinta,sannan a hakan na tabbata nima akwai masu sona wadanda zasu iya zama da ni duk yadda nake''
sai ta qarasa gigicewa baki daya,kamar zata shide da jin fassarar da ya mata,kanshi tayo gaba daya tuni idanunta sun fara fidda ruwan hawaye,da sauri ya dakatar da ita
''kada ki cemin komai,bana buqatar naji komai''daga haka ya danna gefan keken ya soma yunqurin ficewa daga dakin,wani irin kuka ta saki ta fada saman katifa bai dakata ba har ya fice daga dakin
tana iya jiyoshi shi da inna wuro suna hirarsu abinsu tamkar babu komai cikin zuciyarsa,yayi qoqari matuqa wajen kawar da duk wata damuwa da yake jin tana taso masa
''bawan Allah in sha Allahu jibi tsoho alhaji zai dawo daga qasa mai tsarki,da izinin Allah kasa rqn warkewarka nan kusa''a fuska ya nuna jin dadinsa sosai,amma farincikin da yake sa ran ji duk lokacin da aka gaya masa tsoho alhaji zai dawo sam baiji shi ba,bai san dalili ba,amma yana zaton hakan baya rasa nasaba da abinda zuciyarsa ke gaya masa na cewa yana warkewa rabuwarsa da maryam tazo
Shigowar musatafa kenan abdallah ya maida shi yace yake ya kira masa mairo,babu jinkiri ya fice kuwa,ya dubi inna wuro yana fadin
''sam yarinyar nan ta daina shigowa inna ko ta miki wani laifi ne?''
kai ta kada
''a'ah a'ah,ni,babu abinda ya hadamu,abinda na lura kawai tana wasan buya ne da maryamu,ban sani ba ko ita ta yiwa laifin''karon farko amsar dalilin wasan buyab ya fado zuciyarsa,tana kwancen ta jiyosu batasan dalili ba sai taji ruwan hawayenta ya dadu ta sake qunshe kanta cikin filo hawayen na sauka qamshin turaren abdallah da ya kama katifar na ratsa qofofin hancinta,cikin sakanni ya haifar mata da wani baqon yanayi cikin zuciya da gangar jikinta
duban inna wuro yayi yace
''inna''
''na'am bawan Allah''ta amsa masa bayan ta dubeshi tana ci gaba da kadin
''magana nakeson muyi da ke inna ta fahimta''sai ta ajjiye abinda takeyi din tq bashi dukkan hankalinta''uhmmm ina saurarenka''
''inna na daukeki tamkar kakata haka nake jinki had zuciyata akwai maganar da nakeson gaya miki tuntini''sai ya matsa gefan kekensa take ya qara matsawa da shi gaban innar kadan sanann cikin qasa da murya ya fara mata maganar
lokacin da taji sallamad meron sai da taji wata faduwar gaba,haka siddan ta kasa zama sai ta miqe ta yaye labulen window din dakin,shi abdallah yake fuskanta don haka ta sake lafewa sosai don kada ya hangota
Tare da mustafa suka shigo,tana ido biyu da abadallah ta fara sussunne kai cikin duqunqunan nan hijabinta,inna wuron ce ta dubeta
''au,to kuma meye hakan,wa kike kunya ne?kinga bani na kiraki ba dama tunda kin gujeni kinga mai kiran naki''
gaban abdallah tazo ta zauna kana ta gaida shi
''bani amsawa tunda bamusan laifin da muka yi miki ba kika gujemu''
qara dunqule kanta tayi guri guda wani dadi ya rikito mata kamar ta tashi tayi rawa
''ni dai babu komai''haka ta fada,abdallahn ne ke janta da hira abunka da gwanar surutu tuni ta saki jikinta suka fada hirarsu,daga bisani maryam taga inna wuro ta tattre kayanta ta shige daki ta barsu
qasa qasa suka koma magan ta yadda bzata iya jiyosu ba,sai fuskar mero da ta gani ta fadada ta fara'a tana sake boye kanta,ji tayi ta soma jin juwa juwa sabida haka ta saki labulen ta koma kan sofa tana dafe da qirjinta
''kada ki jawomina bunda bazan iya ba,kada kimin irin wannan rashin adalcin,ki rabu da abdallah bai dace da ni ba,wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa,abdallah ba mate dina bane''abibda ta ringa fada kenan qasa qasa wani hawaye mai zafi na bin kuncinta
tun tana duba agogo har ta haqura,sai da ya buga qarfe sha daya daidai har ya dora da mintina sannan ta sake jiyo muryarsu
''ki tabbatar gobe tare zamu fita rafi dake kinyi alqawari?''kai ta gyada kamin tace
''eh nayi alqawari''
shima kan ya jinjina
''to shikenan sai da safe goodnight sweet dream''duk da bata fuskanci mai yace ba sai ta saki dariya tana waiwayensa har ta fice
ya janye idonsa yana sauke ajiyar zuciya,har yazu nauyi da zafin da yake ji a qirjinsa yana nan babu ainda ya ragu duk da faman turereniya da yake masa amma sam ya gaza cimma nasara,cike da kasala ya danna madannin tafiya keken ya nufi dakin da shi cikin wani rin yanayi na jin kadaici da zazzafar qauna
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[8:50pm, 9/30/2017] Huguma👑: [3:02pm, 9/30/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
5⃣1⃣
*_Allah S W A yana fada cikim alqur'aninsa mai girma''haqiqa ji da gani da zuciya dukkansu abubuwan tambayane (ranar alqiyama)_*
*_cikin wata surar kuma yana cewa''ku cika alqawari lallai alqawari abin tambaya ne (ranar qiyama)_*
Da sauri sauri mami ke tafiya har ta isa ga sashen nenen,nenen ta taras kwance male male tana zabga ihu saboda tashi data kasa yi,zubaida da danan na durqushe kanta suna qoqarin dagota
ta qarasa gabansu tana shirin taba nenen tana tambayarsu
''me ya sameta,lafiya?''zubaida ta bude baki dom bata amsa,da sauri nene ta sake saka wani ihun tana fadin
''wayyo Allah na,kada ku kulata,kada kuyi mata magana''
itadai zubaida da batasan me hakan yake mufi ba tayi zaton ko qwaqwalwar nenen ce ta samu matsala
''wallahi faduwa tayi ne,bamusan me ya sameta ba''ta bawa mami amsa da haka don batasan me zata ce mata ba
idanu adnan ya zq
aro don yasan babu shakka a yau dai asirin jikin mami ya gama karyewa don sun qetara sharadinsa
''Allah ya tsine miki dai albarka zubaida,haihuwarki bata qare ki da komai ba,kin sake jawo mana wata asafar,kin karya mana asiri''nenen ta fada hawaye shabe shabe,kallon rashin fahimta mami da zubaida ke mata,tuni adanna ya juya ya fice mami ta bishi da kallo
ta dawo da kallonta ga zubaida zata mata magana ifanunta ya sauka kan cikinta sai ta kasa magana ta tsaya kawai ta zuba mata idanu,udon zubaidan ya cika da qwalla don kusan duk gidan babu wanda take ganin mutumci mituncinsa kamar mamin,babu wanda yace komai nenen ta sake sakin ihu
''adnan kaje ka duba min yata zahariyya,kada su hallakamin ita''cikin tashin hankali,mami ta kalli zubaida
''kamata mu kaita sama na mata allurar barci ko zata dawo hayyacinta''
''wallahi bintu kada ki sake kice zakimin allurar bacci,lafiyatq qalau,jikina ne kawai yayi nauyin kuma zai warke,na tsaneki wallahi bintu taurin ran danki abdullahi duk shi ya jawo mana wann masifar da muke ciki''
kiran sunan abdullahi ya sanya gabanta faduwa har sai data kirq sunan Allah,haka suka kinkimeta da qyar suka iya haurawa da ita saboda azanar nauyinta,mamin ta yi mata allurar barcin,tana ta surutanta da su basu fahimvi komai ba ciki saboda basu san me ta qulla ba da haka bacci yayi awon gaba da ita
Ta fito daga sashen nene ta nufi sashenta tana dafe da kanta don tun sanda ta kira sunan abdullahi kanta yake mata ciwo,suna take ta nanatawa cikin zuciyarta
ta qarasa bedroom dinta ta shiga tayi wanka ta daura alwala ta bada faralin sallah,har yaznu ciwon kan uaqi saukar mata don haka ta balli magani ta sha ta kwanta,babu jimawa nannauyan bacci ya dauketa
Yana zaune kan kekensa yayi kyau cikin jallabiyya fara sol,fuskarshi qunshe da murmushi yana kallonta,itama shi take kallo,a hankali ya fara tahowa gabanshi tana miqa masa hamnu saidai duk sanda ta kusa zuwa dab da shi keken da yake kai sai yayo baya da shi taga ya mata nisa
Sai ta fara binsa da gudu keken na sake tafiya da shi saidai yana fuskantarta fuskarsa kuma dauke da murmushi,sai da sukayi tafiya mai nisa kana keken ya tsaya cak,sai taji an,dafa kafadarta da sauri ta waiwayo,maryam ta gani tsaye kusa da ita tana murmushi,ta nude bakinta zata kira sunanta bat taga sun bace mata gaba dayansu,dube dube ta dinga yi amma ta nemesu sama ko qasa ta rasa,wani rami ta gani a gabanta ta tafi a hankali ta keqa sai ta hangosu ciki suna zaune,ji tayi luuu ta tafi itama zata fada ciki
firgigit ta farka tana ambton sunan Allah gami da dafe kanta dake sara mata kamar zai tsage gida biyu,tafi minti talatin a haka sannan taji sannu a hankali ciwon kan yana raguwa yana raguwa har ta daina kinsa gaba daya,sai ta jita sawai kamar wadda aka kunce daga sarqa
''abdallah,maryam''ta fada a hankali
Kamar wadda aka tsikara ta dago da kanta ta miqe da sauri ta sanya hijabinta ta fito,hanyar sashen abdallahn ta nufa kanta tsaye tana tafiya wasu abubuwan da suka faru suna fado mata tamkar mutumin da yayi mafarki yake tuna abunda ya faru,kallo daya ta yiwa sashen nasa jikinta ya gaya mata ba lafiya ba,qofar na nan a lallauye yadda su muugu suka yi mata ranar da suka zo nemansa,jikinta babu qwari ta shiga ciki ta dinfa duba ko,ina da ina ta,iya qurar da bangaren yayi kawai ya isheta amsar cewa gidan ya dade babu mai rai a cikinsa,hotunan abdallahn ta dinga bi tana kalla bata ankara ba kuka ya subuce mata,zaman dirshan tayi saman carfet hawaye masu dumi suka shiga turereniyar fita daga idanunta
''ina ka shiga abdallah,ina ka tafi ka barni''abinda ta donga fada kenan a hankali cikin kukanta
mafarkin da tayi dazun ya dinga dawo mata tar kamar a lokacin takeyinsa,babu shakka ta tabbatar abdallah da maryam duk inda suke suna da buqatarta,suna da kwadayin ganinta
maganganun nene suka sako kai suma
kada kuyi mata magana,shikenan kun karya min asiri
asiri?
asiri wanne iri take nufi,wa aka yiwa asiri kuma akan ne ya karye?duka daga shigowarta gidan a tau tunaninta ke ta mata shawagi,mutanen da ta gani sun fita daga gidan kamar ta taba ganinsu cikin gidan,cikin wani dare cikin kuma wata rayuwa data yi a baya,rayuwar data dinga jinta kamar rayuwar cikin mafarki,cikin rayuwar ta dinga tsinto halin da taga abdallah,abunda ya faru da ita ranar da zata soma rayuwar mai kama da mafarki,a hankali tunaninta ya dawo zuwa yau,maganganun nene sunqi daina yi mata amsa kuwwa a kunne,a dazun sam hankalinta bai nasu muhimmanci ba sabanin yazun data dage kai da fata sai ta tuna dukkan wani abu da nenen ta fada,ficewar da adnan yayi da sauri daga gidan
''taurin ran abdallah ne duka ya jawo mana halin da muke ciki,idan da ya mutu salin alin da mun huta''
maganar nenen ta qarshe kenan sanda take surkuda mata allurar bacci
taurin ran abdallah?
ya mutu?abdallah kenan abdallah na?
tambayoyin sun mata tsauri da yawa,saidai data hada dukkan abubuwan dake wulgawa cikin idanunta sai taso sansano qamshin wani abu wanda ya sata ta qarasa shugewa rudani na haqiqa,ita kadai ke fadin duk inda abdallah yake sai ta nemoshi
ba zata iya rayuwa,cikin duniya ba cikin salama ba tare da tasan ina abdallah yake ba,wanne hali yake ciki?,a kullum addu'arta shine Allah yasa ta riga abdallahn mutuwa,zata masa addu'ar samun juriya da qarfin gwiwa kan rashinta,sabanin ita da bata da wanda zai mata wannan addu'ar,ta yaya zata jure rasa abdallah da mahaifinsa ta iya ci gaba da ingantacciyar rayuwa cikin dunuya
A hanzarce ta kima sashenta ta wuce bedroom dinta kai tsaye,kayan jikinta ta sauya ta dauki muqullin motarta,haqiqa dukkanin wani zatonta game da yadda rayuwarsu ta cukurkude lokaci guda ra dorashi ga nene,duk da ta sani wani bawa,bai isa ya dora maka wani abu ba face da izinin ubangiji amma akwai silar komai,nene ita ce sila haka zuciyarta ke gaya mata
ta bude motarta ta shige tana qoqarin tashinta usaini ya qaraso
''hajiya zaki fita gasu ibrahim kuma na zuwa''ta dubeshi kana tace
''idan sum qaraso kowa ya koma bakin aikinsa na maidashi,gobe idan Allah ya kaimu zamu tattauna da ku duka''ta samu damar fada sakamakon ambaton Allah da take yi cikin zuciyarta wanda hakan ya taimaka qwarai da gaske wajen zaunar da nutsuwarta cikin jikinta
Allah yana fada cikin alqur'aninsa mai girma
(KU SAURARA,TABBAS DA AMBATON ALLAH KADAI ZUKATA KE NUTSUWA)
Babu inda yafi dacewa ta dosa irin gidan kawunta wanda yake a yanzu tamkar mahaifi a gareta,mutum ne mai nutsuwa qwarai da fahimta babu bata lokaci ta fice a gidan kanta tsaye ta nufi can
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Ranar wunin gaba daya akanta ta qare tana zaune qofar gidan ta tasa uban ruwan dake ambaliya agabanta,tun tana zuba ido taga ta inda jirgin agajin su nene zai dira har ta sare baki daya,ta sake laluba wayarta da niyyar kunnata ko zata iya kira saidai sama ko qasa ta nemi wayar ta rasa,wasa wasa ta miqe ta hau zazzage zazzage saidai ko qyallin kalarta bata hango na,abu kamar wasa sai da ta zazzage dukkan akwatunanta amma babu ita babu alamarta,dariya taji ana qyqyata mata ta dago kanta da sauri,malam na hayi ta gano yana keta ruwan yana takashi da qafafunsa tamkar wanda yake kan tsandauri ba ruwa ba,ya qaraso gabanta ya ya daga hannunshi sai ga wayar
''duk abinda kike aiwatarwa yau na sani,kina tsammanin kubuta daha hannu na ne?,to kinzo gidan da idan aka shiga saidai a fidda gawarka,ina jinku habiba ta baki labarin abunda ya faru da ita ko?,wato wanna bai zamamiki izina ba ke yar masu taurin kai,bari na baki shawara qwaya daya a taqaice,ki fidda sa dan komawarki gida muna tare mutu ka raba,koda yan uwanki ma sunzo basu isa su gane hanya ba haka zasu qaraci walagiginsu su koma,mune maganin makwadaitan mata irinku masu butulcewa hanyar Allah,kunqi Allah muma munqi shi kinga kenan mu muka fi dacewa da ku,kin riga da kin zama matar malam na hayi na zama mijinki''
cikin zafi ta bude bakinta da niyyar yaba mishi rashin kunya,bakinta cike yake fal da maganganu masu zafi da takeson ta gaya masa,raahin mutunci ta nado mai uawa zata masa wanda tana tsammanin tunda yazo duniya ba'a taba yi masa makamancinsa ba,da saurinsa ya daga hannunshi na hagu take bakinta ya rufe qam
''daga yau ba zaki sake magana ba sai idan na baki izini ko naso,ba zaki sake min musu ba ko wani ma ba ni ba''kai kawai take gyada masa kamar bawa da ubangidansa
''wuce ki tafi dakinki,daga gobe zaki amshi girki,yau na daga miki qafa kiyi jimamin rabuwa da gida irin na amare iya na yau kawai''nan ma kai ta gyada masa ba tare da tace komai ba ta tsugunna zata kwaahe akwatunta
''shiga ciki kawai,kafin ki isa su sun riga ki isa''nan ma kai ta gyada kana ta juya sum sum sum ta shige cikin gidan,ya isa gaban kayan ya dafa su take suka bace a gun bat,wata magaukaciyar dariya ya saki yaba yiwa kansa kirari kala kala,sai kuma ya dinke fuskarsa cikin yan sakanni tamkar bai taba dariyar ba ya juya ya shige cikin gidan
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Su biyu ne ita da inna wuron zaune qarqash bishiyar lalle take kwabawa innan wanda zata saka a qafarta saboda dawiqar tsoho alhaji gobe daga qasa mai tsarki,har mamakin tsohuwar take bata ganin tsufan kanta ko na mijinta,adonta take daidai shekarubta wanda zai burge mijinta,dazu ta saka sabulu mai qamshi ta wanke kanta tas tace maryam din zata yi mata kitso
Tun kafin ta dago ta jiyo muryoyinsu,gabanta ya soma faduwa don ko kusa ko alqma bata sha'awad ta bude ido taga yarinyar,haka suka shigo cikin gidan tana tura wheelchair din suna hira abinsu,tunda ta dago kanta suka hda ido da abdallah ta dauke kai bata sake marmain kallonsu ba,miqewa tayi tsam ta isa bakin rijiya ta wanke hannunta sai tayi shigewarta daki duk da ba wani abun zatayi cikin dakin ba,tsaye tayi tana jin uadda suke hirarsu su ukun sun ma maisheta tamkar wata bare,kada ma abdallah yaji labari wanda a a yanzun ya koyi zuwa masallaci daga nan idan yaga damq yayi zamansa qofar gidan nenen suyita hira da samarin qauyen,idan kuwa ya tashi dawowa to mawuyacibe ka ganshi ya dawo shi kadai ba tare da mero ba,duk yadda taso danne zuciyarta da hanata jin kishin abdallah abun ya faskara yafi qarfinta,daga qarshe ta yiwa kanta hukunci ta yarda tana kishin abdallah saboda amanarsa da mami ta barta amma ba wai don so ba
Ko daya bata ji shigowarsa ba sai gyaran murya da ta ji a bayanta,ta dan waiwayo da sauri wanda hakan kadai ya isa ya gaya maka tunani takeyi
''excuse me madam''ya fada yana nuna mata hanyar da zai wuce din ba tare da ya kalli fuskarta ba
sai ta janye gefe ta zauna saman kujera ya qaraso ya wuce bangon dakin inda laptop dinshi ke ajjiye,tayi qasa da yawa hannunsa bazai iya kaiwa ba,tayi zaton wannan karon zai nemi taimakonta sabida gaba daya yanzun duk abinda hannunshi zai iya da kansa yake yi,ta manta yaushe rabon da ya sata wani abu,ko kwanciya ce ko dorashi saman kujerarsa mustafa ke taimaka masa
Bata ankara ba taji yana kiran mero,cikin rawar jiki ta qaraso dakin ganin maryam sai jikinta ya mutu kuma,ta soma rabe rabe
''shigo mana,wancan computer din zaki dauka min da ita zamu tafi saboda hoto ko?''sai ta washe haqoranta ta rave maryam ta wuce ta dauko conputer tana qare mata kallo din ba qaramin burgeta tayi ba ta miqa masa suka fice a dakin,wani dubqulallen abu ne ya tokare mata wuta ya hanata ta hadiyi koda yawu ne,tana jiyo su suna yiwa inna wuro sallama sun tafi rafi sai kawai ta qarasa zamewa ta kwanta gaba daya kan kujerar tana hawaye sosai
''meramu fito,ki saka min lallen nan mana,so nake na cireshi kafin mangariba ki kitse min kan nan,don malam alhaji saukar hantsi zaiyi''ta jiyo inna wuro tana fada,da zata iya da ta cewa inna wuron ba zata iya fitowa ba ta saka da kanta,tilas ta miqe ta goge fuskarta bayan ta sake saka kwalli duk don kada innar ta gane ta fito
tana kan tabarma lallen na gefanta,kallo daya ta yiwa maryamun ta maida kanta kan kwanon lallenta ba tare da tace mata komai ba,tun inna wuron na sako hira taga maryam din bata karbarta hannu biyu itama sai taja bakinta ta tsuke suka ci gaba da zaman kurame,duk yadda taso ta hana qwallar fita hakan ya faskar,haka ta dinga sulalowa tana sa gefan dankwalinta cikin dabara tana gogewa
''hmmmm,duniya kenan,Allah yana baka kana bana so,ba shikenan ba,garin kallon ruwa dama kwado kema mutum qafa,dana dam kuma dama ai butulcinsa yawa gareshi''shiru tayi gana jujjuya maganganun inna wuron cikin qwaqwalwarta masu zubi da gugar zana,sai tayi ta maza don kada ta gano kuka take ta tambayeta kanta na duqe kan qafar inna wuron da take sawa lallen
''lafiya inna,wani abu ne ya faru?''
tabe baki tayi ya kau da kanta
''a'ah a'ah,babu abinda ya faru,Allah dai ya rufa asiri,amma shi aure komai lalacewarsa ai aure ne,yafi gaban ace za'ayi shakulaton bangaro da shi''
''hakane''maryam din ta fada tana ci gaba da abunda take,wani takaici ya kama inna wuron har taja qwafa duk da yadda taso daurewa
bayan ta gama sa mata sai taja gefe,gani,zaman shirun ya,isa don innar bata sake tanka mata ba sai ta jawo kwanon lallen wanda yayi ragowa ta qunsa a yatsunta na qafa da hannu
daf da kiran sallar magariba suka cire duka ita da innar,yatsun sunyi kyau kam,lallen ya kama ram da shi gwanin sha'awa
tana gama daura alwala taji sallamarsa,wanann karon ma sai da gabanta ya fadin,idanunta ya sauka kan mero dake riqe da laptop dina abdallah taba ta shafawa bakin nan kamar gonar auduga,har uanzu jan jambakin data sanya kan ta kile yana nan radam baje baje kan bakinta,ta sake saura dankwalinta sai ta shige kawai dakinsu don ta tabbata zaman hirar,nan zasuyi,hirar da ayanzu babu abinda ta tsana kamar ta
Tana shiga ta shimfida abun salla ta tayar da sallar,ko bayan ta idar zamanta tayi kan daddumar bakinta cike da addu'o'i wadanda suk riga da sun zame mata jiki,a kunnenta abdallah ya fita sallah ya dawo,inna wuro tayi kiranta ta fito taci abinci to tace mata har suka kammala bata fito din ba saboda tana jiyo muryar mero
Awa daya tsakani ta sake jiyo innar
''ki fito ki lallabe min kan nan tunda ba zaki ci abincin ba,inaga azumin yammaci zuwa dare kika fara''
abdallah ya kalli innar qasa qasa yace
''inna dama bata ci abincin rana ba?''
baki ta tabe
''ina fa taci ta dorawa kanta nunqufurci''
ya marairaice fuska kamar yqdda yakewa mami idqn yanason wani abu
''amma inna banda zama da yunwa fa''
''qyale shu'uma,cikinta ai da kanta zata nema idan yunwar ta rarakota''
kai ya kada yana jin ba dadi cikin zuciyarsa
''a'ah inna''
''ka qyaketa nace bawan Allah,ai ba wani ya hanata ci ba''
kwanukan ya dauka ya danna kekansa ya nufi dakin,a kwance ya taddata,amsa sallamarsa tayi tana qoqarin boye hawayen fuskarta don kada ya gani,ta miqe tana gyara hijabin jikinta zata fice a dakin
''dawo ki zauna''taji ya fada,haushinsa take ji fal cikin zuciyarta don haka ta masa shiru,taku biyu ta qara ta sake jin muryarsa mai cike da dakewa da kwarjini
''zan saba miki idan kika sake koda taku guda''cak ta tsaya kana ta dawo da baya tayi zaune kan ledar dakinta bayan ta cusa fuskarta tsskiyar cinyoyinta,keanukan ya tura mata
''dauki ki cinye banason inga komai cikin kwanon''ba tare data kalli kwanon ba tace
''bana ci na qoshi''
''tunda bakici ki fadi me kike son ci?''
''na qoshi nace''
''baki isa ba''ya fada kanshi tsaye,yanayin yadda yayi maganar ya tabbatar mata da gaske har cikin zuciyarsa bazai barta ba sai taci
''me zaki ci nace''ya kuma tambayarta cikin dakewa da ginshira
''fura mai kwakwa da shawarma''tana sane ta fadi hakan don tasan mawuyacine a nan a samu abinda ta fada din
baice komai ba ya danna keken ya fice
Awa guda ya dawo da baqar leda
''karbi kici''taji yace da ita
ta miqa hannu ta amshi ledar fuskarta a qunshe,ga mamakinta duk abinda ta lissafa din ne a ciki
babu yadda ta iya haka taja ledar ya tasata a gaba da zazzafan kallonshin nan yace a gabansa zata ci
sosai ta bata masa lokaci duk don ya gaji ya fita amma sai ta lura baiko damu ba gyara zamanshi yayi ma,tamkar ma nishadi yangarta da zaunar da shi din da tayi take sashi
duk motsin da tayi idanunshi na kanta musamman dan qaramin bakinta mai dauke da pink din lips dake motsawa yana rauna shawarmar cikin rashin son cin abincin,wani abu ya darsa cikin zuciyarshi wanda ya sashi limshe idanunsa,ji yake kamar ya kamaau ya tsotsesu tas,wani,barin na zuciyarsa ke gaya masa loka cine
0 comments:
Post a Comment