Da safe bayan nasa uniform na shirya da zan fita sai na
tsaya a dai-dai kofar d'akinshi nayi sallama, ansawa yayi kafin kuma ya
min umarni da shiga, shi d'in ma kayan ya ke sawa da alama aiki zai
fita.
Tsugunawa nayi had'e da gaisheshi, zuwa yayi ya d'agoni gami da rungumata, ba tare da ya ansa ba.
Ganin yadda ya rik'eni yana kallona yasa nace "kawu Hassan
zan makara fa" sakeni ya yi kafin kuma yaje gefen katifarshi, naira
d'aya ya d'auko ya bani.
Kar6a na yi da sauri ina murna, sake kamani ya yi gami da
cewa "karfa ki fad'awa kowa na baki, idan an fita break ki sayi abinda
kikeso"
Godiya na mai sosai don nikam tunda nake ban ta6a zuwa da
koda sile biyar makaranta ba yau gani da naira d'aya, ai ji nake nafi
kowa ranar, ga shi dama ba wani abincin kirki mukaci da safe ba zallan
koko ne shi d'inma bashi Mama ta k'ar6a wurin mai kokon.
Koda na dawo daga school babu yunwa a cikina kasancewar nayi ciye-ciye.
Bayan magriba muna zaune nida Mama, Hassan ya shigo bayan
ya gaishe da Mama kafin ya zauna a gefe, nima na gaishe shi ya ansa
cikin sakewar fuska kafin kuma ya mik'o min naira biyar ya ce naje na
siyo mai fanta idan na siya na ajiye mai a d'akinshi.
Mama ta ce "toh ma za kije ki dawo karki tsaya wasa" na
ansa da "toh" kafin na d'au gyalena na fita, na barsu sunata hira da
Mama.
Koda na dawo ajiye mai na yi ina shirin fita ya shigo,
hannuna ya kama ya dawo dani ciki, zaunar da ni yayi a gefenshi sannan
ya ce.
"Za ki sha fanta?" Gyad'a mai kai na yi da sauri, tabbas ina son sha don rabona da sha tun Ya Umar bai tafi ba.
Cewa yayi "toh zan rage miki kinga ga tsire can ma sai muci tare ko?" Murmushi nayi wanda ya nuna tsantsan farincikina.
Katseni yayi da cewa " amma fa da sharad'in duk abinda na
umarce ki zakiyi shi, kuma idan kina yarda kullun zan dinga baki kud'in
break da irin wannan abincin, kuma inaso kimin alkhawarin bazaki fad'awa
kowa ba"
Nikam sam ban gane maganarshi ba amma dai idan zai dinga
bani abinci da kud'in break ai zan mai komai kuma bazan fad'awa kowa ba.
Katsemin tunani yayi da cewa "zo nan ki zauna" ya nuna min
gefenshi, ba gaddama naje na zauna, janyoni yayi muka kwanta akan
katifarshi ya cigaba da yimin abinda ni bangane ba amma ban hanashi ba,
ya d'auki tsawon lokaci yana wasu abubuwan da sukayiwa kwakwalwata girma
kafin kuma ya d'agani.
D'aukan fanta yayi ya sha kusan rabi kafin ya mik'omin tare
da naman naci sosai kuma naji dad'inshi, sai da na cinye tas na k'oshi
sannan na ce mai zan tafi.
Cemin yayi "karfa na yarda na fad'awa kowa, idan Mama ta
tambaye ni mai yasa na jima, nace shi ne ya ce na zauna ya ragemin fanta
da abincin, sannan ya ce gobe idan zanje school nazo na kar6i kud'i,
kafin kuma ya mik'a min wani sweet mai dad'i.
"toh"
Na ce mai had'e da yin godiya sannan na fita da murna ta.
Da Mama ta tambayeni, abinda ya cemin shi na fad'a, sai dai
abubuwan da yamin a daren yau sun tsayamin a rai inaso na tambayi Mama
meye hakan yake nufi amma ina tsoron kar ya daina bani kud'in da ya ce
da kuma abincin.
Duk yadda naso na kau da abun a raina ya ga-gara, k'arshe dai kusa da Mama na je na zauna sannan nace
"Mama nikam kawu sai ya....." Tsawa Mama ta dakamin sannan
ta ce "kin ganni nan bana son surutun banza da wofi fad'i ba'a tambayeka
ba kibarni kawai, idan kuwa baki daina yawan surutun nan ba watarana
zan cire miki hak'wara"
Tashi na yi na bar wurin na kuma ja bakina nayi shuru amma haka na kwana da abin a raina.
****
Abinda ya cigaba da faruwa kenan tsakanina da Hassan kullun
sai ya kirani ya ce wa Mama zai aikeni Mama ba ta kawo komai, watarana
da kanta ta ke aikana d'akinshi.
Haka kuma kullun sai ya bani kud'i, wani lokacin ya bani
naira d'aya da sile biyar, har naira biyu yana bani, da abinci kai harma
kayan zak'i, wannan yasa nake jure irin wasannin sa yake da jikina, har
zuwa lokacin da ya fara biyan buk'arshi ta bakina, duk ranar da ya
aikata hakan tofa wuni zanyi ina amai Mama ta d'auka tsutsan ciki ke
damuna har ta na cewa da zaran an biyata albashinta zata naima min
magani, kallonta kawai na keyi domin ni nasan inda matsalar ta ke.
Daga baya sai na daina zuwa wurin Hassan d'in ko ya kirani
bana zuwa, haka kuma na cigaba da jure zaman yunwa, har zuwa watarana da
ina zaune ni kad'ai a falo naji sallamar shi alokacin bazan iya tashi
ba saboda yunwar da nakeji domin har jiri nakeji.
Ya jima a tsaye yana kallona kafin kuma ya tsuguna a
gabana, tambayata yayi dalilin gudunshi da na keyi, ban 6oye mishi ba na
fad'a mai irin aman da nakeyi idan ya aikata abinda ya keyi.
Cemin yayi rashin sabo ne amma ba komai yadaina haka tunda
bana so, don shi baya so ya 6atawa matarshi rai, rufe fuskata na yi
saboda kunya, duk da a lokacin ba wani sanin meye aure na yi ba.
Naira biyar ya ciro a ajjihunshi ya bani gami da cewa naje
na siya wani abu naci, tabbas alokacin nayi farinciki da wannan kud'in
sannan duk wani alk'wari da na d'auka na daina zuwa wurinshi na watsar
da su, na cigaba da zuwa wurinshi amma ya daina wasa da bakina saidai ya
sunbace ni.
Wata rana da bazan ta6a mantawa da ita ba a rayuwata, itace
ranar da Hassan ya fara kawar min da mutuncina ta haryar turamin
yatsunshi, tabbas nasha wahala ranar, haka yayita rarrashina da zanbtafi
ya d'auko naira ashirin ya bani kud'in da banta6a rik'ewa ba kenan a
wannan lokacin ita kanta Mama idan ba albashi aka mata ba sai tayi sati
biyu bata rik'e ba.
Haka na dinga tafiya da k'yar na shiga d'akinmu tunda dama
baya bari na fita har sai ya lek'a yaga ba kowa a soron gidan tukunann,
yau d'in ma ba kowa domin ruwan a keyi.
Koda na shiga d'akinmu ban tarar da kowa aciki ba, neman
wuri nayi na kwanta, ban jima da kwanciya ba Ya Abdallah ya shigo, cemin
yayi " tun d'azu nake nemanki ina kikaje?"
Lokaci guda tsoro ya kamani, kar dai ace ya gane halin da nake ciki, cikin fad'uwar gaba na ce.
"daga gidan Ummi nake" gyad'a kai yayi alamar gamsuwa ba tare da ya sake cewa komi ba.
"Ina Mama ?"
Na jefa mai tambayar, a ta ke naga fuskarshi ta juye
yanayin damuwa, cikin sanyin murya ya ce "Ya Hamid ne aka kamasu, yana
can police station"
Tashi nayi da sauri gami da cewe "police station mai yayi aka kaishi can"
Azabar da naji ne lokacin da na zauna ita tasa nayi saurin komawa na kwanta.
Murya mai cike da damuwa ya ce "wai sata sukayi a kasuwa
Allah ne ma ya kare da y'an sanda zukaje da wuri domin niyar mutanan
wurin ma su k'ona su, amma kam sunsha duka akace don ni ban je ba"
Hawaye ne ya fara zubomin ina tausayin halin da muke ciki,
Mama ce ta shigo cikin tashin hankali na kalleta ruwa ya mata duka
idonta ya kad'a yayi jazir ga takalminta ma a tsinke haka take janshi,
wani irin tausayinta ne ya tsirga min.
Zama ta yi gami da dafe kanta, Ya Abdallah ne ya ce " Mama me ake ciki"
Cikin damuwa Mama ta ce "wai sai anbiya kud'in belin kafin
su sakeshi, shi abokin nashi ma na tarar da mahaifinshi acan har sun
tafi"
"Mama to ke kinada kud'in da zaki biya mai ne" na fad'a hawaye na zuba daga idona.
Mama tace "Farida Umar kenan sisin kobo bana maganinshi
amma naga Babanku a waje bari ya shigo na rok'eshi ko zai bayar" ta
k'arashe murya a raunane.
Koda Baba ya shigo Mama ta fad'a mai murmushi yayi sannan
ya ce "su rik'eshi har k'arshen rayuwarshi idan har sai na bada kud'ina
zasu sakeshi wallahi"
Yana gama fad'in haka ya shige d'aki abinshi dukanmu ba
wanda ya sake cewa komai, sai can Mama ta kalleni tace "Farida yunwa ko?
Kiyi hakuri komi mai wucewa ne, watarana sai labari" sam Mama bata gane
halin da nake ciki ba,tayi zaton yunwa nakeji.
Bata san rayuwata tashiga garari ba, washegari Mama taje
school d'in da ta ke koyarwa ta rok'esu da subata albashinta duk da ana
tsakiyan wata, sunsan halin da Mama ta ke ciki shiyasa suka bata.
Mama ta na kar6an kud'in taje tayi belin Ya Hamid daga can
ta wuce kasuwa ta siyo mana kayan abinci wanda zamu jima muna anfani
dashi da sauran kud'in, bata dawo gida da ko sisi ba.
Ranar munyi murna ganin muma ansiyo mana kayan abinci,
tundaga ranar ba k'ara zuwa wurin Hassan ba tunda daman don abinda zan
kashe yunwata nake zuwa, ga kuma abinda yayimin rannan wanda na tsorata
ainun, domin ranar haka na kwana wurin yana min rad'ad'i.
0 comments:
Post a Comment