Bayan dawowan Ya Hamid Mama ta zaunar dashi tayi mai nasiha sosai ta kuma ce karya sake fita ko nan da kofar gida.
Kwana biyu kamar yaji fad'anta baya fita ko'ina, amma sai
ya fara wasu irin abubuwa tamkar mahaukaci, na tabbata rashin samun
kayan maye na kwana biyun da yayi ne ya maidashi hakan.
Haka muke sashi agaba muyita kuka, shima kukan yake yana kuma rok'on Mama akan ta taimakeshi.
Bayan kwana biyu kuwa muka nemeshi muka rasa, abinda yafi
tayar mana da hankali shi ne kwashe kayan abincin da yayi wanda Mama ta
siya harma da d'an kud'in da Baba ya bata da zai tafi, wanda mun san ba
kowa bane fa ce Ya Hamid.
Wannan shi ne ga samu ga rashi, ga k'arshen wata Mama bata
da albashi, munyi kuka ranar, kuma duk inda akasan za'aganshi bayanan,
haka muka kwana cikin tsananin damuwa, rayuwarmu ta koma gidan jiya.
A wannan lokacin ne kuma Hassan ya d'aukemin budurcina.
Haka kuma ya cigaba da mu'amala dani tamkar matarshi,
harzuwa wata rana da na kwana da ciwon ciki washegari da safe naje
fitsari naga jini nanfa na ringa kuka, kai tsaye d'akin Hassan na wuce
naje na fashe mai da kuka, da k'yar ya rarrasheni sannan ya tambayeni
mai ya sameni.
Cikin kuka nace " ba abinda kayi jiya bane inaga ya fasa min kayan cikina gashi sai fitsarin jini nakeyi"
A ta ke ya fahimceni, murmushi yayi irin tasu ta y'an
duniya, sannan ya zaunar dani, ya dinga fad'amin maganganu na k'arya da
yaudara.
Kasancewar bani da kawaye, islamiyya ma idan aka koremu
kud'in wata, sai mu kwana biyu bamuje ba, wannan shi ya sanya duk
maganar da Hassan ya fad'amin sukayi tasiri akaina, ak'arshe ya haneni
da karna fad'awa kowa, harda Mamana, sannan yace da nagama na fad'a mai,
na ansa mai da toh kawai.
Haka nayita 6oyewa ban bari kowa ya Sani ba, tunda Mama dama ba wuni take a gida ba.
Ranar da ya d'auke kuwa na fad'a mai, cewa yayi zaimin wani
abun da bazan k'arayin fitsarin jinin ba, tabbas na tsorata da fitar
jinin shiyasa na yarda.
Wata allura ya d'auko ya ce zaiyimin, rud'ewa nayi domin ni
sam bana son allura haka ya lalla6ani ya ce na tsaya bata da zafi, da
k'yar na yarda, tun daga lokacin kuwa ban sakeyi ba, kuma duk bayan wata
uku sai yamin wannan allurar.
****
Akwai wata rana muna zaune nida Mama ta na yimin kitso mukaji sallamar Ya Umar Mama ta na "oyoyo d'ana"
Da gudu na tashi zan rungumeshi amma sai naga yaja gefe, cikin sakewar fuska ya ce.
"wai yaushe Farida Umar zata girma ne"
Komawa nayi na zauna ina murmushi, Mama ta ce "kaima dai ka
fad'a, likita bokan turai yaushe a garin" ta fad'a da cikin sakewar
fuska.
Shi d'inma fuskarsa k'unshe da murmushi ya ce " d'azun nan "
Mama ta ce "shi ne Ummi bata fad'amin d'ana na hanya ba, kuma fa
shekaranjiya saida mukayi zancenka da ita, aikuwa har gida zan samu
Ummi"
Murmushi Ya Umar ya sakeyi sannan ya ce "Mama ai cewa ta yi idan ta fad'a miki zakiyita hidima ne"
Mama ta ce "kyale Ummi, to ina ruwanta tsakanin uwa da d'a, yanzu dai ya hanya, an kammala karatu lafiya?"
Ya Umar ya ce "munsha hanya, karatu kuma Alhamdulillah an kammala sai dai fatan samun sakamako mai kyau"
Mama tace "Allah yasa muga kyakykyawan sakamako"
Dukanmu muka ansa da "amin " sannan ya ce "Mama wallahi wannan dawowan nawa sai naga Faridana ta k'ara girma sosai"
Na ce " kai Ya Umar ? Na fad'a ina murmushi, shima murmushin yake kafin kuma ya ce " wai yanzu ajinki nawa ne ma"
" S.S 1 fa zanshiga yanzu" na fad'a, ya ce "kai Faridana
yaushe ma kika shiga school d'in gaskiya baici ace har kin kai S.S 1 ba"
Mama ce ta ce "hakane, gaskiya ta fad'a amma fa ta d'anyi
tsallake, batayi aji shida na primary ba sannam batayi aji uku na
secondary ba, a aji biyu ta zana Junior waec d'inta"
Gyad'a kai yayi had'e da cewa da alama dai Faridana mai hazak'a ce"
Mama ta ce "toh ba laifi amma kwana biyu kam tana wasa da karatuna".
Kallona ya keyi kafin kuma ya ce "wai hakane?" Sunkuyar da kaina nayi ba tare da nace komai ba, ya cigaba.
"lalle kuwa bake a tsarabata domin ni kinsani bana shiri da wanda baya son karatu, in dai kinaso mu shirya sai fa kin dage"
Cikin shagwa6a nace "na daina zan dinga dagewa, amma don Allah Ya Umar karka hanani tsarabar"
Daga shi har Mama dariya na basu, haka muka cigaba da hiran
mu, don ko abincinshi ma gidanmu Ummi ta aiko mai tare mukaci nidashi.
*********
Lokacin da Ya Umar ya dawo nayi k'ok'arin kauracewa Hassan amma abin ya gagara domin yayi min gargad'in da na tsorata dashi.
Cewa yayi bawai naga Ya Umar ya dawo ba duk ranar da nayi
k'ok'arin sanar dashi kokuwa nayi tunanin daina zuwa d'akinshi to
wallahi sai ya kasheni sannan ya kashe Ya Umar da Mama, wata bindiga ya
d'auko wacce alokacin na yi tunanin ta gaske ce, yace da ita zai
harbemu.
Tabbas bani da masoyan da suka zarce Mama da Ya Umar da na
rasa su gara na yi hakuri duk da a wannan lokacin ni sam banajin dad'in
wannan mu'amalar ga shi kullun sai kowa ya kwanta nake zuwa, ina tsoron
karna k'i zuwa ya kashemin su.
A wannan lokacin na koma mara walwala na kuma rame sannan
sam bana mai da hankalina a karatuna, ko naje aji ba abinda nake
fahimta, haka malami zai shigo har ya fita bansan abinda yayi ba, saboda
tsaban tunani da fargaban abun da ya ke min.
*********
Ya Umar kuwa ya fara bautar k'asa a Jos University Teaching Hospital (JUTH), bai fiye samun lokaci ba.
Akwai watarana ina zaune ni d'aya a d'aki Mama ta shiga
gidan Ummi, wani yaro d'an makwabtan mu ya shigo ya ce "farida wasu
mutane a waje sunce wai a musu sallama da Baban Hamid"
Na ce "su waye" ya ce shi bai sansu ba, amma dai yaga
d'ayan da kayan y'an sanda" ido waje nace "y'an sanda mai zasuwa Baban
mu" gyalena na d'auka gami da fita.
Ina fita naga matan gidanmu harda makwabta an fito gulma dama sun saba, kad'a kai kawai nayi ina mamakin irin halinsu.
Mutane biyu na gani a tsaye d'aya da kayan y'an sanda
d'ayan kuma shirt ce da jins a jikinshi, tsugunawa nayi na gaishesu
sannan nace kune kuke neman Baban mu"
Sukace "eh " nace baya gari amma bari na kira Maman mu" sukace to ma za nayi sauri.
Na samu Mama da Ummi harda Ya Umar suna zaune a tsakar gida, gaishesu na yi, Mama ta ce min.
"Ungo abincin nan ki d'ebi naki saiki barwa Hamida da Abdallah suma sud'an ta6a"
Ummi ce ta katse ta da cewa "kai Maman Hamid wato shiyasa
kika k'ici, nifa ke na bawa kici su ma ga nasu nan sannan ga buhun
shinkafa da mai can d'anki ya siyo miki an basu kud'n bautar kasa"
Albarka Mama ta yita sawa Ya Umar, "kin rufo d'akin" Mama
tace da ni, sai a sannan na tuna abinda ya kawoni, nace "Mama police ne
suke sallama da Baba suna k'ofar gida"
Dukansu suka rufamin baya muka fita, wato abinda police
d'in suka fad'a shi ya tayar mana da hankali, wai Ya Hamid sunje sata a
wani shago da asuba, garin su gudu shi aka harbeshi, yanzu yana kofar
station d'in.
0 comments:
Post a Comment