Farida da Ummi na zaune a falo suna hira, duk rabin hiran ya ta'allaka ne akan nasiha wanda Ummi ta ke yi ma ta.
Dr Umar ne ya shigo falon, idanunshi na kan Farida, addu'a
yake Allah yasa ba ta sanar da Ummi ba, domin sam Ummi ba ta d'aga ido
ta kalleshi ba, balle ya sa ran za'amai magana.
Tashi ta yi had'e da barin wajen, har sai da ta shige d'akin Ummi kafin ya d'auke idanunshi daga kallon da yake mata.
Zama yayi a gefen Ummi gami da cewa "wash nagaji" yaji ba ta tanka mishi ba, ya sa ke cewa "Ummi Alhaji bai dawo ba ne"
"Ka ganshi ne anan" ta fad'a a hasale, tun daga nan ya sha jinin jikinsa, murya a raunane yace "Ummi wani laifi na yi ne"
Cikin fad'a ta ce "ban sani ba, na ce bansani ba, yau wai ni ce zaka ci amana Umar, wallahi kaban mamaki, bansan haka kake ba"
Murya a raunane yace "Ummi ki yafe min, wani abun akace miki na yi ne, kiyi hakuri ki sanar dani kar Allah yayi fushi dani"
Rai 6ace tace "na yi zaton kai mai rik'e Farida ne bisa
amana, Umar na yi zaton ko wani kaga yana k'unta ta ma ta sai inda
karfin ka ya k'are, mai yasa ka aureta kasan baza ka iya rik'eta ba"
"Ba komai bazan so Allah ya kama ka saboda hakkin baiwar
Allah nan ba, tabbas saki ba abu ne mai kyau ba sai dai ina maka tsoron
kamuwar ubangiji"
"Domin haka ina shawartarka da kaji tsoron Allah ka saiwak'e ma ta Umar"
Ummi na gama fad'an haka ta juya gami da cigaba da duba wasu takardu.
"Ummi wallahi ina sonta, ina sonta, Ummi kiyi min addu'a ban san mai ya ke damuna ba, na kasa mancewa"
Rabonta da ta ganshi yana kuka ta manta, tabbas ya na bukatar kulawarta, ya zama lalle ta taimaka musu.
Murya mai tattare da lallami Ummi ta yi magana "toh kai
wace irin zuciya ce da kai da ka kasa yafe ma ta, yarinyar nan ta nemi
gafararka, Umar karka zamar da kanka jahilin karfi da yaji mana"
"Ummi ban san mai yake damuna ba wallahi hoton yaron ya kasa fita a cikin zuciyata, Ummi Faridana ce fa"
Murmushi Ummi ta yi irin nasu na manya, lalle ba wani abu ba ne ya ke damun Umar sai kishi.
"Yayan Farida" Ummi ta kira sunanshi.
"Na jima da fahimtar kai da k'anwarka kuna tsananin k'aunar junanku, amma ku kanku kun kasa fahimtar hakan"
"Lokacin da kuka kawo girma na yi tunanin zaku fayyace wa juna halin da ko wannenku yake ciki, amma naga ba kuyi hakan ba"
"Sannan ko da Alhaji yayi maka maganar Mariya nan ma na yi
tunanin zaka fito da buk'atar zuciyarka, har zuwa randa ka kawo kaya, da
farko na yi farinciki dana ga akwatuna biyu amma jin bayaninka ya
sakarmin da gwuwa"
"Har izuwa lokacin da yaron na Adamu ya fito, fad'an da
naga kanayi nasan tabbas akwai dalili, sosai naji haushinka lokacin
domin kak'i ka fitar da sirrin zuciyarka"
"Bayan kunyi wanna tashin hankalin da ita sai na fara
k'aryata tunani na, amma randa ka taho daga Bauchi ba shiri, tafiyar da
baka ta6a irinta ba, nasan akwai damuwa, na yi k'ok'arin tambayarka,
amma kace ba komai"
"Ni nasan damuwarka ba zata wuce saka ranar auren Farida da Ahmad ba"
"Hankalina ya tashi matuk'a, wannan ne yasa bacci ya
k'auracewa idona, a daren naji ina buk'atar na sameka dan mu tattauna,
kai tsaye na shigo d'akinka a wannan daran.
Na yi sallama kafin na shigo amma naji shuru, kuma inajin
kukanka da surutanka, wannan ne yasa na shigo, na lura a wannan lokacin
sam baka cikin hayyacinka"
"Hankalina yayi mak'ar tashi da jin kalaman da suke fitowa
daga bakinka, anan na tabbatar da kana k'aunarta k'auna kuma mai
tsanani"
"Ban bari ka ganni ba na koma d'akina, hankalina ya tashi a ranar na samu Alhaji na fayyace mai komai nan fa muka dukufa addu'a"
"Allah ya ansa addu'ar mu, tun daga wannan lokacin
hankalina ya kwanta, duk a tunani na Farida ta samu kwanciyar hankali,
Umar ba zanso Ku rabu da juna ba domin kuna son junanku"
"Sai dai ba zan lamunci ganin Farida a damuwa ba, domin
haka nake rok'onka da ka sauwak'e ma ta, saboda ka kasa rage kishinka,
wanda hakan cutarwa ne a gareku"
Tamkar k'aramin yaro haka ya rik'e hanun Ummi ya na cewa
"Ummi dan girman Allah karki rabani da Farida wallahi ina sonta, zan iya
mutuwa akanta ki taimakeni"
Cikin hikima Ummi ta ce "ni kaina bana so na rabaku, sai dai maslaha nake nema muku domin wannan kishin naka yana cutar daku"
"Addu'a zakimin Ummi na rasa yadda zanyi ki rok'a min
Allah" sosai taji tausayinshi, itama dama ba taso su rabu domin ba wanda
zai rike mata Farida da amana sai shi.
"Zan yarda ku koma amma da sharad'i" "Ummi please banda sharad'i mai tsauri" ya fad'a yana rok'onta.
"Toh ai shikenan sai kaba ni takardar ta" Ummi ta fad'a ta
na k'ok'arin tashi, da sauri ya sha gabanta gami da sunkuyawa gwuwowi
biyu a kasa kafin kuma ya ce "wallahi na yarda da sharad'in"
"Da safe ka rarrasheta idan ta yarda, ta amince zata bika, to sharud'in zai biyo baya"
Ummi ta fad'a gami da tafiya d'akinta, daren ranar Ummi ta
rayashi ne da addu'o'i, ta rok'a musu Allah sosai wanda ta ke sa ran
addu'arta ta kar6u
Ya na fitowa daga masallaci, kai tsaye d'akin kwanan Ummi
ya wuce, ita kawai yake so yasa a ido, sam jiya bacci ya k'auracewa
idanunshi, wani irin kewarta ya keji.
Kwance ta ke a kan gadon ta na bacci, duk rabin cinyoyinta a
waje kasancewar rigar baccin ta tattare, wani irin shauk'in kaunarta ne
ya ke d'ibanshi, a ta ke ya saukar mai da wata kasala.
Kujerar dressing mirrow ya janyo zuwa bakin gadon kafin kuma ya zauna, tallafe ha6arshi yayi da hannu biyu.
Kallonta ya ke tamkar idan ya d'auke idanuwanshi zata 6ace,
ji yake tamkar yaje ya kamata ya rungume abarsa, cikin wata irin murya
mai cike da shauk'i ya ce.
"Farida ina sonki, ina tsananin k'aunarki ba zan iya rabuwa da ke ba matata, domin kece farincikina"
Cikin bacci ta ke tajiyo maganganu, a hankali ta bud'e idanunta wanda suka sauka akanshi.
Da sauri ta janyo zani gami da rufe jikinta har ma da kanta, ya jima ya na zaune kafin daga bisani ya mik'e had'e da cewa.
"Idan kin gama ki sa meni a d'akina" daga haka ya juya ya tafi cikin tafiyarshi ta k'asaita.
**** ****
Sai da ta yi wanka, wannan karan ma ba ta yi wani kwalliya
ba gudun kar a fad'a mata maganganu marasa dad'i, sai da ta feshe
jikinta da turare kafin ta fita.
Kai tsaye d'akinshi ta nufa, sallama ta yi, sai da ya bata
izini kafin ta shiga, ba ta yi k'ok'arin zama ba domin yau kam baza ta
iya jure munanan kalamansa.
Sai dai kuma yanayin da ta ganshi a ciki ya bata mamaki tamkar ba Yayanta ba tagumi yayi da hannuwanshi biyu.
Ya d'an jima ahaka kafin ya d'ago kai ya kalleta, cikin sanyin murya ya ce "Bismillah zauna mana inaso muyi magana ne"
Ba ta re da gaddama ba ta zauna, amma shuru ne ya sa ke
biyo baya, ita kam tana mamakinshi mutun tamkar magana na bashi wuya da
kyar yake magana, itafa ta fara jin yunwa kuma ma bata so Ummi ta fito
bata ganta ba.
"Faridaaa nasan na k'untata miki ba kad'an ba na kasance mutun mara tausayi agareki, ki yafe min"
Ya d'anyi shuru, kafin daga bisani ya cigaba.
"Zuciyata ta kasa mance ranar da naga Faridana da na jima
ina tattali a k'irjin wani kazami, Farida why, mai yasa, na jima ina
tattalinki, duk wani kariya ina baki, me ya rud'eki da wannan kazamin,
wanda har ta kai kina jifata da mugayen kalamai akanshi Farida"
"Dr zargina kakeyi, Mai yasa zaka yi tunanin zan sake yarda
wani d'a namijin ya sa ke rud'ana ya 6ata min rayuwa, kasan yadda nake
ji a zuciyata kuwa"
Sha re hawayen da ya zubo ma ta ta yi gami da cigaba.
"Wallahi na rantse maka da Allah babu abinda ya ta6a shiga
tsakanina da shi, wannan ranar itace rana ta farko da ya fara kamani,
kuma a lokacin ina k'ok'arin kwatar kaina kazo, sannan ina rok'onka
gafara kayi hakuri da irin munanan kalaman da na fad'a maka"
"No Farida ni nafi cutar dake, na musguna miki na hanaki
walwala a karshe na rabaki da masoyinki ta hanyar auranki, ki yafemin,
sannan ki bani lokaci insha Allahu komai zai dai-daita"
"Kin amince za ki ci gaba da zaman aure da ni Farida?"
Shuru ta yi gami da sunkuyar da kanta.
A zahirin gaskiya bata da za6i, idan har tace lalle ta na so ta rabu da Dr, toh wazai aureta, sannan kuma ta yi musu budulci.
Sannan bata kyauta mai ba, shi da ya yarda ya aureta duk da
irin nakasar da ke ta re da ita, bai gujeta ba, dole ne ta jure duk
irin abinda za ta fuskanta arayuwar aurenta, tabbas sun mata karamci.
"Please Farida karki ce a'a, karki guji yayanki, ki amince
za ki bini ki cigaba da zaman aure da ni kinji" Dr ya katse ma ta
tunani.
Tashi ta yi da zummar barin d'akin, cikin hanzari ya tashi
ya sha gabanta gami da rik'e hannayenta a ta ke suka ji wani irin shock,
k'ok'arin zame hannunta ta ke daga nashi, amma ya sa ke rikewa gam,
gami da cewa.
"Noo karki tafi ba ta re da kin ban ansa ba, nasan bakya so na amma please ki bani lokaci"
Wannan magana tashi ji ta ke tamkar a mafarki, wai yau
yayanta ne yake mata magiya akan karta rabu dashi, "Allah nagode maka"
abinda ta ke fad'a kenan azuciyarta.
"Za ki cigaba da zama dani" ya tambayeta, d'aga mai kai ta
yi alamar "eh" gami da barin d'akin da gudu domin bata so ya cigaba da
bata kunya.
Da sauri ta fito daga d'akin, da Ummi ta ci karo, kunya ne
ya rufeta, a take ta hau kame-kame, murmushi Ummi ta yi gami da barin
wurin.
A zuciyarta ta na yan bad'on yara, suna so suna kaiwa kasuwa.
Ranar lahadi sukayi shirin komawa, sosai Ummi ta yi musu fad'a gami da nasiha mai shiga jiki.
Ummi ta k'ara da cewa "yanzu zakuje ku d'auki Mariya Ku wuce ko" cike da rashin jin dadi Dr ya ce
"Ummi wallahi bansan me yake damun yarinyar nan ba, na
fad'a mata lokacin da zamu tafi akan tazo kuyi sallama sai mu wuce amma
kina ganin har yanzu, tana wasa dani, ta biyo motar haya kuwa"
Ummi tace "a'a baza ayi haka ba kaga komai d'an hakuri ne,
kuma kai babba ne karka biye ma ta, idan zaku wuce kaje ka d'auketa
karka ce ma ta komai, nan gaba ko ance ta yi hakan baza ta yi ba"
Daga gidan Ummi kai tsaye gidan Auntyn Mariya sukaje Dr kam bai shiga ba waya ya mata ta fito.
Ta na zuwa ta bud'e kofar gaba wurin da Farida ta ke zaune gami da cewa Farida
"malama fita anan kin dai san wurin zama na ne"
Dr ne ya fito ya zagayo inda ta ke gami da cewa "haba
Mariya ba kiga nan kan hanya bane, please karki jawo mana idon mutane
tunda da zamu zo kekika zauna a gaba yanzu kiyi hakuri ki zauna a bayan
please"
Cike da tsiwa ta ce "wallahi wannan yarinyar ba ta isa na
bar mata wurin zama na ba, akwace min miji sannan gaban ma ahana ni
zama"
Tabbas ta fara kai shi bango, sam baya son ya ma ta abun da
zata ga kamar ya fifita Farida akanta, shi baiga wani abun fad'a akan
zaman gaba ba.
Lek'awa yayi ta widowo motar ya ce wa Farida "Faridana za
kiyi hakuri ki bar mata gaba ki koma baya, amma karki ga hakan a
matsayin tursasawa kiyi abinda zuciyarki ta amince da shi"
Murmushi ta yi gami da cewa "zan koma yayana ai da bayan da gaban duk d'aya ne"
Wannan abu ya 6atawa Mariya rai, don haka koda suka fara
tafiyar ma habaici ta diga yi wanda duk Farida ta ke jefawa magana, Dr
sam bai gane mai ta ke nufi ba amma ita Farida ta gane, banza ta bawa
ajiyarta har suka iso bauchi .
0 comments:
Post a Comment