Ya na fitowa daga masallaci, kai tsaye d'akin kwanan Ummi
ya wuce, ita kawai yake so yasa a ido, sam jiya bacci ya k'auracewa
idanunshi, wani irin kewarta ya keji.
Kwance ta ke a kan gadon ta na bacci, duk rabin cinyoyinta a
waje kasancewar rigar baccin ta tattare, wani irin shauk'in kaunarta ne
ya ke d'ibanshi, a ta ke ya saukar mai da wata kasala.
Kujerar dressing mirrow ya janyo zuwa bakin gadon kafin kuma ya zauna, tallafe ha6arshi yayi da hannu biyu.
Kallonta ya ke tamkar idan ya d'auke idanuwanshi zata 6ace,
ji yake tamkar yaje ya kamata ya rungume abarsa, cikin wata irin murya
mai cike da shauk'i ya ce.
"Farida ina sonki, ina tsananin k'aunarki ba zan iya rabuwa da ke ba matata, domin kece farincikina"
Cikin bacci ta ke tajiyo maganganu, a hankali ta bud'e idanunta wanda suka sauka akanshi.
Da sauri ta janyo zani gami da rufe jikinta har ma da kanta, ya jima ya na zaune kafin daga bisani ya mik'e had'e da cewa.
"Idan kin gama ki sa meni a d'akina" daga haka ya juya ya tafi cikin tafiyarshi ta k'asaita.
**** ****
Sai da ta yi wanka, wannan karan ma ba ta yi wani kwalliya
ba gudun kar a fad'a mata maganganu marasa dad'i, sai da ta feshe
jikinta da turare kafin ta fita.
Kai tsaye d'akinshi ta nufa, sallama ta yi, sai da ya bata
izini kafin ta shiga, ba ta yi k'ok'arin zama ba domin yau kam baza ta
iya jure munanan kalamansa.
Sai dai kuma yanayin da ta ganshi a ciki ya bata mamaki tamkar ba Yayanta ba tagumi yayi da hannuwanshi biyu.
Ya d'an jima ahaka kafin ya d'ago kai ya kalleta, cikin sanyin murya ya ce "Bismillah zauna mana inaso muyi magana ne"
Ba ta re da gaddama ba ta zauna, amma shuru ne ya sa ke
biyo baya, ita kam tana mamakinshi mutun tamkar magana na bashi wuya da
kyar yake magana, itafa ta fara jin yunwa kuma ma bata so Ummi ta fito
bata ganta ba.
"Faridaaa nasan na k'untata miki ba kad'an ba na kasance mutun mara tausayi agareki, ki yafe min"
Ya d'anyi shuru, kafin daga bisani ya cigaba.
"Zuciyata ta kasa mance ranar da naga Faridana da na jima
ina tattali a k'irjin wani kazami, Farida why, mai yasa, na jima ina
tattalinki, duk wani kariya ina baki, me ya rud'eki da wannan kazamin,
wanda har ta kai kina jifata da mugayen kalamai akanshi Farida"
"Dr zargina kakeyi, Mai yasa zaka yi tunanin zan sake yarda
wani d'a namijin ya sa ke rud'ana ya 6ata min rayuwa, kasan yadda nake
ji a zuciyata kuwa"
Sha re hawayen da ya zubo ma ta ta yi gami da cigaba.
"Wallahi na rantse maka da Allah babu abinda ya ta6a shiga
tsakanina da shi, wannan ranar itace rana ta farko da ya fara kamani,
kuma a lokacin ina k'ok'arin kwatar kaina kazo, sannan ina rok'onka
gafara kayi hakuri da irin munanan kalaman da na fad'a maka"
"No Farida ni nafi cutar dake, na musguna miki na hanaki
walwala a karshe na rabaki da masoyinki ta hanyar auranki, ki yafemin,
sannan ki bani lokaci insha Allahu komai zai dai-daita"
"Kin amince za ki ci gaba da zaman aure da ni Farida?"
Shuru ta yi gami da sunkuyar da kanta.
A zahirin gaskiya bata da za6i, idan har tace lalle ta na so ta rabu da Dr, toh wazai aureta, sannan kuma ta yi musu budulci.
Sannan bata kyauta mai ba, shi da ya yarda ya aureta duk da
irin nakasar da ke ta re da ita, bai gujeta ba, dole ne ta jure duk
irin abinda za ta fuskanta arayuwar aurenta, tabbas sun mata karamci.
"Please Farida karki ce a'a, karki guji yayanki, ki amince
za ki bini ki cigaba da zaman aure da ni kinji" Dr ya katse ma ta
tunani.
Tashi ta yi da zummar barin d'akin, cikin hanzari ya tashi
ya sha gabanta gami da rik'e hannayenta a ta ke suka ji wani irin shock,
k'ok'arin zame hannunta ta ke daga nashi, amma ya sa ke rikewa gam,
gami da cewa.
"Noo karki tafi ba ta re da kin ban ansa ba, nasan bakya so na amma please ki bani lokaci"
Wannan magana tashi ji ta ke tamkar a mafarki, wai yau
yayanta ne yake mata magiya akan karta rabu dashi, "Allah nagode maka"
abinda ta ke fad'a kenan azuciyarta.
"Za ki cigaba da zama dani" ya tambayeta, d'aga mai kai ta
yi alamar "eh" gami da barin d'akin da gudu domin bata so ya cigaba da
bata kunya.
Da sauri ta fito daga d'akin, da Ummi ta ci karo, kunya ne
ya rufeta, a take ta hau kame-kame, murmushi Ummi ta yi gami da barin
wurin.
A zuciyarta ta na yan bad'on yara, suna so suna kaiwa kasuwa.
Ranar lahadi sukayi shirin komawa, sosai Ummi ta yi musu fad'a gami da nasiha mai shiga jiki.
Ummi ta k'ara da cewa "yanzu zakuje ku d'auki Mariya Ku wuce ko" cike da rashin jin dadi Dr ya ce
"Ummi wallahi bansan me yake damun yarinyar nan ba, na
fad'a mata lokacin da zamu tafi akan tazo kuyi sallama sai mu wuce amma
kina ganin har yanzu, tana wasa dani, ta biyo motar haya kuwa"
Ummi tace "a'a baza ayi haka ba kaga komai d'an hakuri ne,
kuma kai babba ne karka biye ma ta, idan zaku wuce kaje ka d'auketa
karka ce ma ta komai, nan gaba ko ance ta yi hakan baza ta yi ba"
Daga gidan Ummi kai tsaye gidan Auntyn Mariya sukaje Dr kam bai shiga ba waya ya mata ta fito.
Ta na zuwa ta bud'e kofar gaba wurin da Farida ta ke zaune gami da cewa Farida
"malama fita anan kin dai san wurin zama na ne"
Dr ne ya fito ya zagayo inda ta ke gami da cewa "haba
Mariya ba kiga nan kan hanya bane, please karki jawo mana idon mutane
tunda da zamu zo kekika zauna a gaba yanzu kiyi hakuri ki zauna a bayan
please"
Cike da tsiwa ta ce "wallahi wannan yarinyar ba ta isa na
bar mata wurin zama na ba, akwace min miji sannan gaban ma ahana ni
zama"
Tabbas ta fara kai shi bango, sam baya son ya ma ta abun da
zata ga kamar ya fifita Farida akanta, shi baiga wani abun fad'a akan
zaman gaba ba.
Lek'awa yayi ta widowo motar ya ce wa Farida "Faridana za
kiyi hakuri ki bar mata gaba ki koma baya, amma karki ga hakan a
matsayin tursasawa kiyi abinda zuciyarki ta amince da shi"
Murmushi ta yi gami da cewa "zan koma yayana ai da bayan da gaban duk d'aya ne"
Wannan abu ya 6atawa Mariya rai, don haka koda suka fara
tafiyar ma habaici ta diga yi wanda duk Farida ta ke jefawa magana, Dr
sam bai gane mai ta ke nufi ba amma ita Farida ta gane, banza ta bawa
ajiyarta har suka iso bauchi .
Yau tunda suka iso ta ke gyare-gyare domin ta na sa ran
zuwan mijinta gareta, hatta zanin gado yau sai da ta sauya, babu abinda
ba'a k'alk'aleshi ba.
Kasancewar ya ce ba sai sun dafa komai ba yasa ta na gama gyaran gidan ta shiga wanka, ta jima a ciki toilet d'in kafin ta fito.
Zama ta yi ta tsantsara kwalliya gami da feshe jikinta da turare, wata rigan bacci ta d'auko mai kyau ta sanya.
Ta idar da sallah kenan ya shigo, wani k'ayataccen kallo yake jifanta dashi.
Ita kanta yau ta na bukatar ta jita a k'irjin mijinta, "kinyi kyau" yace da ita,kuma har lokacin idanunsa na kanta.
Sunkuyar da kai ta yi ta na murmurshi, "Faridanaaa" ya fad'a cikin sanyin muryar da saida tsigar jikinta ta tashi.
"Bari na je na yi wanka" ya sake fad'a, "toh" tace dashi
yana fita ta janyo ledar da ya shigo da ita ta na dubawa, abincin da
yasan ta na so ne, "Dr ka jima kana kyautata min yau na maka alkhawarin
faran ta maka.
Ta d'an jira taga bai shigo ba kuma yunwa ta ke ji, don haka ta zuba abincin ta ci bayan ta rage mai nashi.
Ta jima ta na jiran shigowarshi amma bai shigo ba, har
bacci ya d'auketa a falon, wurin sha biyun dare ta farka, ranta yayi
matuk'ar 6aci.
Ita wai me Dr yake nufi da ita ne, haba itafa ba dutse bace
ta na buk'atar mijinta, daurewa kawai ta keyi a wannan y'an kwanakin.
Ranar kasa runtsawa ta yi kewar mijinta ya hanata sak'at, sosai ranta ya 6aci.
Ba ita bacci ya d'auketa ba sai karfe uku na dare.
Sawa kanta dauriya ta yi don bata so ta bada kai, koda ya
shigo da safe sam bai mata maganar rashin dawowanshi ba, ita d'in ma
bata kawo maganar ba.
Ranar ta re sukaje wurin aiki abun gwanin sha'awa, duk wani
motsinta a idanunshi, bini-bini sai ya biyota office wai yazo ganin
lafiyar matarshi, ita kuma ta biye mai.
Da yamma bayan sun tashi, ya d'auketa yace suje su gai da Baba, ba k'aramin farinciki Baba da Aunty sukayi da ganinsu ba.
Haka aka dinga tattalinsu, Aunty ce ta ja Farida d'akinta
ta ke cewa "d'azu munyi waya da Ummi ta ke fad'a min halin da kike ciki,
amma mai yasa baki fara sanar dani ba dota"
"Ayya Auntyna kiyi hakuri wallahi bana so na d'aga muku hankali ne Ummi ma dandai ta matsa ne" Farida ta fad'a.
Aunty ta ce "amma yanzu komi yayi daidai ko" Farida ta ce
"eh Aunty" wani kwalba Aunty ta d'auko cike da magani ta ce ungo maza
shanye mazan yanzu ba'a musu Sanya, ga wannan shiga toilet kiyi tsuguno"
Da dai kamar Farida bazata kar6a ba tunawa da jiya amma sai
ta yi tunanin watakila jiya gajiya ce tasa bacci ya d'aukeshi, kuma yau
kam taga k'aunarta fal cikin idanunshi.
Kafin su tafi sai da Baba ya musu nasiha sosai, ta tafi tana kewar Babanta wanda taga ya sake ramewa.
Suna tafiya a mota amma gani ta ke sam tafiyar bata sauri
wani irin shauk'insa takeji mai sauk'ar da kasala, bata ta6a shiga irin
wannan yanayin ba.
Koda suka isa ce mata yayi bari yaje yaga lafiyarsu Mariya, hannunshi ta kamo gami da cewa "zaka dawo"
Ce ma ta yayi "karki damu kije kiyi wanka yanzun nan ina zuwa my Farida, yau inaso naji matata a jikina"
Kusan awa biyu ta na jiranshi amma shuru, ta rasa me yake damunshi wai shin har yanzu bai hakura bane.
Ita kam gaskiya hakurinta ya gama k'arewa, ta kasa gane
ainihi me yake damunta, gaskiya yau bazata iya bacci ba, wani irin
tausayin kanta taji.
Kiran wayarshi ta yi har saida ta kusan yankewa ya d'auka, "Farida" ya fad'a muryarshi da alamun bacci.
Wani bakinciki ne ya tokareta wato shi baccin shi ma yake, kuka ne ya kwace mata.
Hankali tashe yake tambayarta, kashe wayar ta yi ba tare da ta bashi ansa ba.
Lokacin da ya shigo ta kifa kanta akan gadon ta na kuka,
zuwa yayi ya kamota gami da rungumota, fad'awa ta yi k'irjinshi ta na
kuka.
"My Farida kukanki na d'aga min hankali, na rok'eki ki sanar dani abinda ya sakaki kuka kafin zuciyata ta buga"
Ya fad'a hankalinshi a tashe, kukan ta cigaba da yi, kamo
fuskarta yayi da hannuwanshi biyu yana cewa "oya bani hawayen na shanye
Faridana"
"Bazan iya juran ganinsu suna zuba ba, please ki sanar dani, Farida ina cikin garari"
"Kallonshi ta yi gami da cewa "na tuna da Mama ne na karashe da kuka"
Rungumeta ya sa keyi tamkar zai maidata cikin jikinshi,
kafin kuma yace "addu'a za ki musu, na rok'eki matata ki daina tayar da
hankalinki ko kinaso zuciyata ta buga"
Girgiza kanta ta yi gami da kwantar da kanta a k'irjinshi, shima dad'a manne ta yayi a jikinshi.
0 comments:
Post a Comment