Alhaji abin da na gani ya tsorata ni, tabbas anyi wa
yarinyar nan sammi, shi kuwa yaron nan 'karfin addu'a ne ya ku'butar da
shi, yanzu zanyi k'ok'ari na karya wanda zan iya sauran kuwa dole se
munje gidan domin anyi birne-birne da yawa a cikin gidan"
Cewar Sheikh Muslim.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" abinda su Alhaji suke mai-maitawa kenan,
"Malam toh a gidan mijin nata ne akayi birne-birnen, kokuwa a ina ne?" Ummi ta tambayeshi.
"A'a agidan mahaifinta ne, yanzu ga wannan, ganyen magarya
ne da addu'o'in karya sihiri, ku shiga cikin gida zan sanar dasu yanzu
kije ki ma ta wanka dashi sannan ki bata tasha, sauran kuma sai kun
gama"
Farida na gama sha bayan an mata wanka ta fara wani irin bak'in amai, lokaci guda zazza6i ya rufeta.
Koda Sheik ya ganta yace ba damuwa hakan yana nuna sihirin ya karye kenan.
Alhaji yace "Shiek naji kace anyi birne-birne acan gidan mahaifinta yanzu meye abin yi"
Sheik yace "haka ne amma fa dole sai naje gidan da kaina sanna za'a tone su gami da karya dafin su"
Alhaji ne ya rok'eshi akan don Allah ya sallami iyalanshi suje bauchin haka kuwa akayi.
Sunyi k'ok'arin kiran Baba amma wayarshi akashe, na Aunty kuma bata d'auka ba.
Don haka kai tsaye gidan suka zarce.
Tun daga waje suke jiyo murya Aunty tana fad'a, ko
sallamarsu bata ji ba, abinda suka gani bayan sun shiga yayi mugun d'aga
musu hankali, shin dagaske ne ko kuwa gizo idanuwan su suke musu.
Baba ne zaune akasa Aunty ta na ta surfamai bala'i, kanshi a kasa tamkar yaron gida da ubangidanshi.
Shigowansu yayi dai-dai da kwara mai miyan da ta yi akanshi, cikin gi-gicewa yake cewa.
"wayyo Allah idona bana gani Aunty ki taimake ni" da gudu sukayi kanshi cikin tausayawa.
Cike da 6acin rai Farida tace "mai ya miki" ba ta re da ta bata ansa ba, ta yi hanyar fita cike da rashin gaskiya.
Sheik ne yace."Karku barta ta fita" da hanzari Dr yaje ya rufe kofar da key.
Sheik yace baiwar Allah zo ki zauna kifad'a mana duk wani sharri da kulla-kullen da kika yi"
Cike da rashin gaskiya tace "wani kulle-kulle kuma na yi, kokuma kunzo ne kumin sharri har gidana, toh wallahi bazan yarda ba"
"Akan me zaku zo har gida kuce zaku ritsa min mata ta wallahi ku fita min daga gida munafukai" Baba ya fad'a cikin hargagi.
Alhaji zaiyi magana ya katse shi da cewa "nasan kai
kashirya komai kuma wa ma ka d'auko nake jin muryashi kuka shigo min
gida, to ka kwashesu kubarmin gida"
Duk wannan maganar da yakeyi idanunshi basu bud'e ba, ga kuma rand'ad'in da suke mai.
Ran Alhaji idan yayi dubu ya 6aci zai sa ke yin magana.
Shiek ya sake katseshi da cewa "karka ga laifinshi ba cikin hayyacinshi yake komai ba"
Wannan ya fad'a ne cikin rad'a wanda Alhajin ne kawai yaji abinda yace d'in.
Sheik Muslim ne ya d'auko wani ruwa ya mik'awa Alhaji yace " maza bashi ya kur6a sannan ka shafamai ajiki zai rage mai rad'ad'i"
Shidai Alhaji yaga irin ruwan da akaba wa Farida ne amma sai yabi umarnin Sheik ya aikata abinda yace d'in.
Kasancewar shi Baba azaba ta dameshi a idanunshi har kuma baya iya bud'esu yasa ya yarda.
Cikin hanzari Aunty ta taso da niyar kwa6ar da maganin,
amma kafin takai ga hakan Sheik da yake ankare da ita yasa mata kafa, ba
ta re da ta idar da nufinta ba ta jita a kasa.
Sannan ya bita da wata gigitacciyar tsawa wanda ta sata nutsuwa ba tare da ta yi niya ba.
Hannu biyu ta ke rokon kar azubawa Baba wallahi zasu
kasheta, ba ta re da 6ata lokaci ba kuwa Alhaji yaba Baba yasha, Baba
yana cewa
"Kwantar da hankalinki Aunty da zaran idanuna sun bud'e
zanyi maganin........" Bai kai ga k'arasawa ba ya fara kwara wani bakin
amai tamkar zai fitar da hanjin cikinshi, Alhaji da Umar ne suka
rik'eshi.
Sai da aman ya lafa tukunna Sheik Muslim ya juyo ga Aunty yace "za ki je ki tone abinda kika birne kokuwa saina yi maganinki.
"Kana tunanin zan bi umarninka ne, toh wallahi kayi karya sai naga bayansu"
"mutanan da suka rik'eki amana kike ikirarin sai kinga
bayansu, anya akwai zuciya a k'irjinki kuwa, mai suka miki, mai suka
tsare miki" cike da damuwa Ummi ta ke tambayarta.
"Tabbas da zuciya a kirjina ita d'ince ma ta shawarce ni da abinda nakeyi"
"Sun rabani da farincikina, suna tunanin zan barsu da nasu
ne, kokuma suna tunani zan aureshi ne, na zauna dashi tsawon wannan
shekarun ba ta re da na sa ke haihuwa ba, kuma ace ban damu ba"
Ta k'ara da cewa "toh bari kuji na zauna dasu ne dan d'aukan fansa"
"Mai muka miki, na rik'eki tankar uwa mai yasa haka" Farida ta fad'a
"Idan ku kun manta bari na tuna muku, bayan auran mu dashi
na yi k'ok'arin kawo yarana gidan nan saboda tarbiyarsu da ta fara
lalacewa inaso na kawosu gabana domin na kula da su"
"amma sam yak'i amincewa yace yana tsoron kar asake 6ata miki rayuwa, tunda yarana mazane kuma sun kawo girma"
"Na yi magiyar amma yaki amincewa k'arshe yace sai dai na
nemi yardarki, koda muka miki maganar fashewa da kuka kikayi, nan kuma
mahaifinki yace sam baisan zancen ba"
"Kuna tunanin hakan yamin dad'i ne, sai kuma bayan an kwana
biyu sai ga Umar ya dawo gidan nan da zama, sai nace toh ko shi ba
namiji bane"
"Abun yamin zafi ba kad'an ba, daganan na k'udiri aniyar
d'aukan fansa ta dabara, na mallake Alhaji ba ta re da kowa ya sani ba,
sannan na yi k'ok'arin yiwa Umar asiri akan ya afkawa Farida"
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" abinda su Alhaji suke fad'a kenan.
"Sai dai duk lokacin da malamina ya yi aiki akan shi sai muga haske ya baibaye shi, sam sihirin yakiyin tasiri a kanshi"
"ak'arshe na farrak'a tsakaninsu, sannan aka tura musu sha-shatau a harkar ibadar su, ta yadda asiri zai yi saurin kama su".
"Domin inaso na tozarta Farida ta yadda bakin ciki zai zama
silar mutuwar mahaifinta, lokacin da kuka munafurceni kuka had'a
aurensu, shi ne na tashi tsaye"
"Tabbas da Umar ya sake ya kusanceta da shida mazantarkarsa sunyi hannun riga, ita kuma alokacin zata bak'unci lahira"
"Toh amma sai yayi taurin kai, koda malamina ya duba sai yaga addu'ar da kuke mai ne ta hana sihirin yin tasiri akanshi"
"A wannan lokacin ba dan naso ba dole na 'kyale shi, randa
tazo gidan nan na k'arshe na bata maganin da idan tasha dole ne taje ta
nemi wani namijin.
"Na tabbata da zaran ta mutu shima dole ya bakunci lahira, kuma ko ayau kuka kashe ni na rama bakincikin da suka cusamin"
"Domin sai abinda naga dama yakeyi a rayuwarshi, abinci da magani sai naso yake anfanuwa dasu"
Kuka sosai Baba yake yi yana cewa "kije na sa keki, tabbas
nasan kin bani wahala iyakar wahala, amma me yasa kika nemi ki cutar da
Farida me yasa baki tsaya akaina ba, ni nasan alhakin Sakinatu ne yake
bina, amma mai yasa Farida"
"D'aga hannu sama yayi yana cewa "Allah na tuba ka yafemin tabbas naga rayuwa ina neman yafiyanka ya Allah"
Ummi ce tace " tabbas kin cika muguwa, mai yasa za ki cutar
da yarinyar nan, bayan kin san duk irin abubuwan da ta fuskanta
arayuwarta, Allah ya isa tsakaninmu da ke"
Aunty ko kallonsu batayi ba taje ta fito da akwatinanta
gami da cewa "sauran kayan nawa na aiko a kwashe mun" ta na gama fad'ar
haka ta fice.
Dr yace baza ta fita ba dole a mik'ata ga hukuma, Baba yace "barta Umar wallahi na yi imani duniya zata koya mata darasi"
Daga Ummi, Farida har Baba kuka sukeyi sosai Sheik Muslim
da Alhaji da Dr su suka tono duk wani sihirin da aka birne agidan,
d'akinta ma basu bari ba nan magungunan da aka samu ba'a cewa komai.
"Kai mutun mugun ice ne" cewar Alhaji, nan fa Alhaji da
kanshi yaba Sheik Muslim labarin irin gwagwarmayan da bayin Allah nan
suka shiga, ya tausaya musu matuk'a.
Bayan sun zauna ne Sheik Muslim ya fara magana kamar haka.
"Zan fara ta kanki Farida lalle kin fuskanci jarabawa arayuwa kuma kin jure, wanda muke miki zaton rahmar Allah a rayuwarki"
"Allah subhanahu wata alah yana jarrabar bawanshi yadda
yaso da kuma lokacin da yaso, ba kuma domin baya son ka bane, a'a yana
sonka, sai dai yana gwada imaninka ne"
"Tabbas kin jure irin jarabawar da kika tsinci kanki aciki,
kuma ladanki na wurin Allah kuma za kiga irin sakamakon da zai miki
imma ki fara gani tun aduniya kokuma sai anje lahira"
"Alhaji Sulaiman tabbas kayi *SAKACI* da amanar da Allah ya damk'a maka na iyalinka, ka kuma ga irin kamun da Allah ya maka.
Wannan na duniya kenan Allah kad'ai yasan na lahira, kaga
ahaka ma ka tuba ne da badan haka ba Allah kad'ai yasan a ina abun zai
tsaya"
"Yan uwa ina muku nasiha da duk wanda Allah ya dam'ka muku
amanarsu toh fa ku rik'esu hannu biyu, domin akwai ranar da za'a
titsiyeka a tambayeka irin rik'on da ka musu"
"Don haka sai mun jajirce, abu k'ank'ani shi zai zama silar
shigar da mu aljannah haka kuma abu k'ak'ani na zunubi zai kai mu ga
shiga wuta"
"Alhaji Muhammad kai da iyalinka kun birgeni matuk'a, duk
iyaye nagari ya kamata ace su kasance masu addu'a ga y'ayansu kunga
k'arfin addu'a ko, toh Allah ya shige mana gaba"
"Kai Umar ka d'auki iyalinka ku tafi, ka kuma rik'eta da
amana kekuma ki cigaba da kare hakk'okin Allah, Allah yasa muku albarka
azamanta kewarku"
Addu'a sosai akayi a gidan kafin kowa ya kama gabanshi
Rayuwa kenan, Aunty dai sai labarin rasuwarta sukaji, a
hanyarta tafiya ne, ta yi hatsari, adalilin shigewa 'kar'kashin babban
mota da ta yi, a ta Allah yayi ikonshi akanta, ko shurawa bata yi ba.
Lokacin da Baba ya samu labarin cewa yayi a wuce da gawarta
gidan iyayenta, ba yadda ba'ayiba yace ya yafe mata duk abinda tamai,
sai dai bazai yafe mata cutar da Farida da taso ta yi ba.
**** ****
"Rungumeta yayi sosai ajikinshi yana cewa "Faridana kinga yadda Allah ku6utar damu ko"
Kafin ta yi magana Mariya ta shigo fuskar nan tasha kuka.
"Dr ina buk'atar ka sauwak'a min, please ka bani takardata nagaji, gwara na barka da ita kafin hawan jini ya kamani"
Sa ke Farida yayi daga rungumar da ya mata, kafin kuma yaje
ga Mariya, hannunta ya kama suka fita, bai sa ke hannun nata ba saida
ya sadasu da falonta.
Zama yayi akan kejera kafin kuma ya zaunar da ita agefenshi, bai kai ga magana ba ta fashe da kuka.
Rungumeta yayi yana rarrashinta har ta yi shuru kafin yace "na miki laifi Mariya amma ina rok'onki da kiyi hakuri"
"Dr ni nasan baka sona kana zaune dani ne dan dole, kawai mu hakura da juna"
"Wa ya fad'a miki ina zaune dake ne dan dole, abinda nakeso
kisani ba'ayiwa namiji dole, kuma da zaran namiji ya gaji da mace bazai
zauna da ita ba"
"Zan can kuma kice bana sonki idan bana sonki da tuni
kinbar gidan nan, Mariya kece matata ta farko kuma uwar yarana, bana
rok'on Allah yabani ikon cutar da ke"
"Please ki kwantar da hankalinki, Farida kanwata ce, Mariya
tun Farida na 'karama muke ta re, bani da wata 'kanwa bayan ita, na
sha'ku da ita fiye da tunaninki"
"Farida mace ce mai kyawun halaye, Mariya, don Allah ki
rungumeta da hannu biyu bazan bari d'aya ya cutar da d'an uwanshi ba,
Mariya kizo muzama y'an uwanjuna"
"Please ki cire komai a ranki, ki kwantar da hankalinki"
Tabbas maganganu da ya fad'a sun shige ta kuma sun mata
da'di, dama kishi ne ya mata yawa amma Dr bai ta6a nuna mata wani abu
ba, haka kuma Farida hasalima duk abinda ta ke yi Farida bata ta6a tanka
mata ba.
Gaskiyan Dr ne Farida mace ce mai kyan hali, don haka dole
ta zubar da makamanta, ta rungumi mijin ta gami da zama lafiya da
abokiyar zamanta.
**** ****
Bacci ya fara d'aukanta taji tamkar hannun mutun ajikinta,
farkawa ta yi a firgice gami da kunna wuta, shi ta gani yana mata wannan
murmushin nashi mai tafiya da hankalinta.
"Kai Ya Umar bafa haka ake ba, kawai sai kazo ka firgitani" ta fad'a cikin shagwa6a.
"Oya zo ki koyamin yadda akeyi"ya fad'a yana janyota jikinshi.
"wai meye haka nifa ka tafi d'akinka" ta fad'a ta na ja da baya.
Rungumota yayi sosai har tanaji k'aran bugun k'irjinshi, cikin wata irin murya mai cike da kasala yace.
"Please Farida kizo kimin wallahi inbakiyi min ba mutuwa zanyi" kunya sosai taji, kai amma wallahi Aunty ta cuceta.
Rufe fuskarta ta yi da k'irjishi shima 'kan'kameta yayi a
jikinshi yana ra'da mata wasu manya-manyan kalamai a kunnanta wanda suka
rikita mata tunani, nan fa salo ya canja.
**** ****
Masoyan nan rayuwa suke mai cike da k'auna gami da tattalin
juna, idan kaga yadda suke tafiyar da rayuwarsu abin sai ya baka
sha'awa.
Mariya da Farida sun d'inke sosai ba mai jin kansu, mutunci
da girmama juna ne a tsakaninsu, basu da buri sai na kyautatawa
mijinsu, gami da tattalin yaransu, sosai Farida ta janyosu ajiki dama
kuma sun saba da ita.
**** ****
Dr ne ya shigo d'akin ganin bata falo yasa ya zarce d'akin kwananta kai tsaye, ta na cikin bargo, yaye bargon yayi gami da cewa.
"My Farida kar dai kice min baki shirya ba" murya canciki tace "Ya Umar kaina kamar zai tsage"
Subhanallah tun yaushe" ya fad'a gami da zuwa kusa da ita,
kafin kuma yakai hannunshi jikinta, jikinta yayi zafi sosai, hankalinshi
yayi matuk'ar tashi.
Baya son duk wani abinda zai damu Faridarshi.
"Faridana kinji jikin ki kuwa mai yasa baki sanar dani tun wuri ba"
Kayan aikinshi ya d'auko ya fara gwada ta, kafin kuma yace.
"kina da sirinji na d'ebi jininki ya kamata naje agwada dan na tabbatar da abinda yake damunki, zafin jikin naki yayi yawa"
Nuni tamai da hannu inda ta ke ajiye kayan aikinta, ba ta
re da 6ata lokaci ba ya d'ebi jininta gami da cewa "bari na turo miki
Mariya sai na dawo, zan taho miki da magunguna".
Duk irin gwaje-gwajen da ya kamata amata anyimata amma ba'asamu wata cuta a ta re da ita ba, malaria ne ma aka samu kad'an.
Farida na jinjiki an kuma rasa gane ainihin abinda ke
damunta takamai-mai, idan kaga Dr awannan lokacin sai ka tausaya mai,
Mariya ita ta ke kulawa da ita.
Tun ta na iya tashi har takai sai an kwantar an tayar,
gashi sai kunbura ta keyi daga bayan nan, hankalin kowa ya tashi, dole
Ummi ta dawo Bauchi suka cigaba da jinyarta.
Baba kanshi kullun yana hanyar gidan hankali tashe, ranar da Alhaji yazo dubata ya shiga damuwa matuk'a har ya ke cewa Dr.
"Umar rashin lafiyan Faridan nan ya dameni matuk'a anya
baza ka fita da ita waje aduba zuciyarta ba dubi fa yadda ta ke kumbura
gaskiya abun ya dameni"
Kuka sosai Dr yake tamkar 'karamin yaro, yana cewa "Alhaji bana so na rasa Farida, wallahi bazan iya rayuwa ba ita ba"
Alhaji yace "Umar karkayi sa6o fa, Allah baya barin wani
dan wani, zan cen ba zaka iya rayuwa ba ka daina, Allah zai iya d'auketa
yaga yadda za kayi don haka addu'a zakayi sannan ka nemi kud'i kayi
k'ok'arin fitar da ita k'asar waje ta na buk'atar taimako gaskiya"
Ya juya ga Farida da ta ke kwance da robar ruwa mak'ale a hannunta, yace "sannu Farida, yanzu me yake miki ciwo"
Dafe kanta ta yi da hannu alamar kan ne yake damunta, Ummi
ce tace "wannan ciwon kan na rasa irinshi wallahi, sam baya jin magani"
"Allah ya baki lafiya, ya tashi kafad'unki" ficewa Dr yayi daga d'akin domin sosai wa'dan nan addu'o'in suke kashe mai jiki.
**** ****
Acikin kwanaki k'alilan Dr ya kammala shirye-shiryen fita
da Farida India, shi da ita ne kawai zasu tafi kasancewar yadda ake fama
da rashin kud'i.
Ranar lahadi jirginsu ya d'aga, sai addu'ar dacewa daga masoya.
**** ****
Kasancewar Dr yasan likitoci sosai acan yasa basu wani sha wahala ba, sun samu kulawa sosai.
Dr Shamsudeen, babba likita ne kuma k'wararre a fannin
jikin d'an adam, ana matu'kar ji dashi a 'kasar India, shi ne kuma yake
duba Farida.
Tun bayan zuwan su jikin Farida ya matsa fiye da tunani har takai idan ka ganta sai ka tausaya mata.
Sosai likitoci suke bincike akanta amma har wannan lokacin ba'a samu wata cuta a ta re da ita ba.
Idan kaga Dr za kayi tunanin shima bashi da lafiya ne, ya rame sosai.
Dr Shamsudeen ya gama duba file 'din Farida, gami da tatta6a jikinta, kana ya juya ga Dr Umar.
Yace "Dr Umar maganar gaskiya bazan yaudareka ba, munyi
ikar 'ko'karin mu amma mun kasa gano ainihin abinda yake damunta, kana
gani a idonka akayi komai"
Ya cigaba da magana da harshen nasara, "agaskiya shawara d'aya zan baka a matsayinka na 'dan'uwana musulmi, ku dage da addu'a"
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" kawai Dr Umar yake mai-maitawa cikin matsanancin tashin hankali.
Dr Shamsudden ya d'anyi shiru alamar tunani kafin kuma yace "amma inazuwa"
Ma'akatan lafiya yayi wa umarni da sukai Farida wani d'akin gwaje-gwaje.
Yafi awa guda yana aunata cikin gwanancewa.
Dr Umar yana gefe ya kasa ta6uka komai, damuwa tamai yawa, wai me yake faruwa ne ya kasa gane komai.
" *Allahu Akbar, Allahu Akbar* " abinda Dr Shamsudeen yake fad'a kenan, cikin farinciki, muryarshi har rawa ta ke.
Dr Umar ne ya taso cikin gaggawa yana cewa "me yafaru Dr, mene ne don Allah ka sanar dani"
Kamo hannunshi kawai Dr shamsudeen yayi ba ta re da yayi magana ba.
~Ummu Hanan~
0 comments:
Post a Comment