Ummi ce ta shigo da sallama, da sauri mama ta tashi ta
rungumeta "ta na ga Ummi ga Ummi, oyoyo Hajiya Ummi mutanan saudiya da
India yaushe kuka dawo bani da labari"
Murmushi ne kwance saman fuskar Ummi, zama ta yi gami da cewa
"Jiya muka dawo, ai na aiko Umar aka cemai wai bakya nan"
Mama ta ce "Ummi kinganki kuwa? Kama alatsa jini ya fito" murmushi Ummi ta yi kafin kuma ta ce
"d'azu da safe Alhaji ya ke fad'amin sun had'u da Baban Hamid a masallaci y ke fad'a mai ashe Lamido sa'i yayi?"
Cikin damuwa Mama ta ce "wallahi Ummi, Lamido lokaci yayi" Mama ta k'arashe kwalla fal cikin idanunta.
Ummi ta tausaya wa Mama domin tafi kowa sanin irin k'aunar
da tausayin da ke tsakanin Mama da Lamido, a karshe tayi mai addu'a
sosai Mama na ansawa da Amin.
kafin kuma Mama ta tambayeta da "ina d'an nawa"
Ummi ta ce "sun fita da......." Bata kai ga k'arasawa ba
idonta ya kai kan wannan jik'on da ke gaban Mama, a ta ke fuskarta ta
sauya kafin kuma ta janyon kwanon alokaci guda kuma ta fara salati ta na
tafa hannayenta, sai a sannan ne Mama ta farga.
Cikin damuwa Ummi tace "Maman Hamid kamar jik'on wanke ciki nake gani" ta fad'a ta na juya kwanon kafin kuma ta sake cewa
"Wallahi shi ne, ba dai zubar da ciki kike shirin aikatawa ba, in kuwa hakan ne meye dalilinki?" Ta fad'a cikin fargaba.
murmushi Mama tayi wanda da ka gani kasan murmushi ne mai ciwo kafin kuma ta ce
" Ummi ina bukatar hutu kinga kuma ina karatu, sannan ina
ganin hidiman yara zai iya hanani karatu yadda ya kamata shi ne dalilina
na yanke wannan shawara"
Tabbas Ummi tafi Mama yawan shekaru da wayewa, ta san halin
da Mama ta ke ciki duk da Maman bata ta6a fad'a mata ba, kuma ta san
wannan ba shine dalilin da ya sa Mama tunanin zubar da cikin ba, amma
bata so ta takura ma ta da tambaya, cikin tausayawa Ummi ta ce.
"Karkiyi k'ok'arin aikata sa6o Maman Hamid, karkiyi abinda
Allah zaiyi fishi dake, Allah ba ya ta6a d'aurawa bawa abinda bazai iya
ba, Maman Hamid wannan arzik'in na haihuwa da Allah ya baki ya san za ki
iya ne, idan bazaki iya d'aukan nauyinsu ba Allah bazai baki ba, kuma
kowani yaro da arzik'insa ya ke zuwa, Maman Hamid kada tsoron talauci ko
wani abun yasa ki kashe kyautar da Allah ya baki"
Gyara zama Ummi ta yi sannan ta cigaba da ce wa.
" shin Maman Hamid bazaki godewa Allah da ni'imar da yayi
miki ba, wasu fa neman haihuwan suke ido rufe amma basu samu ba, ni nan
na isheki ishara kina gani tun daga kan Umar Allah baisa na na sake
haihuwa ba, koda kuwa 6ari ban ta6ayi ba, yau shekarun Umar goma, kina
gani duk inda akace ga magani sai naje, na ziyarci asibitoci kala-kala
amma haryanzu ba labari, dalilin hakan naje saudiya"
Maman Hamid na wa kawai kika sa ni akwai mutane da dama a
waje wanda basu ta6a haihuwan ba, amma mai yasa ke kike k'ok'arin
butulcewa ni'imar da Allah ya miki"
Sannan ta k'ara da cewa " banaso kiyi biyayya wurin sa6awa
mahaliccinki, ki dogara ga Allah, nasan halin da kike ciki, amma inaso
ki cigaba da hakuri watarana sai labari"
Kuka Mama ta dinga yi gami da istigfari, Ummi bata bar
gidan ba sai da ta tabbatar maganganunta sun ratsa Mama sun kuma
shigetatukunnan, bada 6ata lokaci ba Mama ta kwarar da maganin.
Ta kuma shiryawa fad'an Baba da kuma kowace irin azabar da zata fuskanta daga gareshi, addu'a kawai ta keyi acikin ranta.
Koda Baba ya dawo ta sanar da shi ta fasa zubar da cikin
zata haifi abinta ga mamakinta baiyi fad'an da ta ke tunanin zaiyi ba,
sai dai ya ce mata.
" Sakinatu kince ina kina son ki haife abinda ke cikinki?"
Mama ta gyad'a kai, ya cigaba da ce wa.
" toh kisani ba abinda ya dameni da abinda kika haifa kuma
karki kuskura ko da zancan wasa kiyi tunanin kwabona zaiyi ciwon kai
akan yaranki, Haram"
Ya na gama fad'an haka ya tashi ya fita, bai sa ke tayar ma ta da maganar ba.
Washegari kuwa yabar gari ba ta re da ya bar ma ta komai ba.
Tabbas a wannan lokacin Mama ta shiga wani irin hali domin
Baba bai sa ke yi musu aike ba, abinci sai dai ummi ta taimaka musu ko
kuma taje ta tsinko zogale ko Rama shine abincinsu harda gishiri cinshi
su ke yi.
A haka rayuwarsu Mama ta cigaba da gudana har lokacin da ta
haihu wannan karan ma ba abinda Mama ta tanada ga me da kayan haihuwa
gabshi wannan karan mace ta haifa, Allah ma ya sa a gida ta haihu ta re
da taimakon wata ungozoma, tabbas Mama ta sha gulma da habaici a wurin
matan gidan.
Abinda yafi damun Mama shi ne Baba na gari ta haihu kuma
bayan haihuwan ma ya shigo gidan amma ko kallonta baiyi ba balle abinda
ta haifa, da k'yar ta tashi taje gabanshi saboda tsananin yunwa da ke
d'awainiya da ita, ta ce.
"Don Allah kataimaka mana da abinda zamuci wallahi yunwa na keji ga kuma yarinyan nan ba ko wandon da za'a saka ma ta"
Tsaki Baba yaja kafin kuma ya tashi yayi hanyar fita, cikin k'aramar murya Mama ta sa ke ce wa.
"don Allah ka taimaka min badan halina ba wallahi har jiri nakeji"
Ba tare da ya juyo ba yace "zan turo muku da kayan abinci
amma batun abinda kika haifa karki sake kawo min maganar da ta dangance
su, wannan matsalarki ce ba tawa ba domin mun dad'e da wannan maganar"
Yana gama fad'an hakan yayi ficewar shi, haka yarinyar ta
cigaba da zama da zani har washegari, har sai da Ummi tazo ita ce ta
siyowa yarinyar kayan da aka saka ma ta.
Ranar suna da Mama ta tambayeshi sunan da za'a rad'awa
yarinyar da fad'a suka rabu ya ce ba abinda ya dameshi, sai wannan
lokacin mutuwar Lamido ta dawowa Mama sabuwa, aranar Mama tayi kuka
harta godewa Allah, k'arshe har washegarin suna ba'a rad'awa yarinya
suna ba.
Dama maganar yanka kam babu shi domin sauran ma Lamido ne ya musu.
Bayan Ummi ta shigo ne Mama ta ke fad'a mata ta kuma ce ta za6a ma ta suna, Ummi ce ta za6amin suna Farida ba mahaifina ba.
Farida ta k'arashe ta na kuka sosai, karshe magana ma gagarta yayi sai da ga bisani
0 comments:
Post a Comment