Sai da Farida ta yi kuka mai isarta, ba wanda ya iya rarrashinta a cikinsu domin su d'in ma hawaye su ke yi, Farida ta goge idanunta sannan ta cigaba.
**********
Haka rayuwa ta cigaba da gudana a gidan mu cikin yunwa da rashin kwanciyar hankali.
Ina da wata hud'u Innayo ta kawo ma su Mama ziyara ganin
halin da Mama ta ke ciki yasa ta samu Baba ta na mai fad'a amma ya
dakatar da ita cikin rashin kunya.
Innayo taji mamakin Baba kuma maganganun da ya fad'a sun ma
ta zafi, har ta d'aukan mai alkhawari ba zata sa ke tako inda ya ke ba,
Mama ce tayita bata hakuri shiko Baba ko a jikinshi.
Kud'i masu yawa Innayo ta ciro ta ba Mama ta ce na gadonta
ne wanda ya ke hannun Lamido amma karta yarda ta bawa Baba tayi tunanin
san'ar da zatayi, kafin ta yiwa Mama sallama ta tafi.
Mama ta samu Ummi ta nuna ma ta kud'in, ta kuma nemi
shawarta akan sana'ar da zatayi, Ummi ta bata shawarar fara siyar da
kayan anfanin gida, wanda ake anfani dashi yau da kullum.
Abubuwan da suka danganci kuka, magi, omo da dai sauransu,
domin sune zasufi tafiya da wuri, ta kuma cewa Mama zata had'ata da wa
ta ma ta awani k'auye wacce zata dinga saran kayan a wurinta.
Allah ya sawa Mama arbarka a cikin sana'arta domin ana samu aci abinci yanzu ko ba yawa za dai a ta6a a gidan.
Tun lokacin da na fara wayo na gane irin tsanar da
mahaifinmu ya mana domin su Kansu su Ya Hamid basa ta6a sakewa idan Baba
na gari dukanmu tsoronshi mukeji, bamu isa mu taka inda ya ke ba, domin
bazan manta ba, akwai wata rana, ina k'arama ya dawo daga tafiya naje
da gudu wai zanyi mai oyoyo ya tunkud'eni na fad'i, tunda lokacin da na
ganshi gudu na keyi.
Lokacin da na cika shekara biyar ne kuma komi ya lalace
domin d'an jarin Mama ya karye, duk mun cinyeshi a ciki, alokacin ne
abinda za'aci ya gagare mu.
Dama Baba ya kammala karatunshi, shekara biyu da suka
shige, ya kuma nemi aiki a Bauchi, cikin ikon Allah ya kuma samu aiki a
Mega Banka reshen jahar bauchin.
Kuma duk da haka Baba sai yayi wata hud'u biyar bai shigo Jos ba, ga shi ba wani nisa ba ne tsakanin Bauchi da Jos.
Aike ma sai yaga dama ya keyi, domin wani lokaci sai ad'au lokaci baiyi aken ba kuma da ya aiko kud'in ba wani yawa ne dasu ba.
Mama ta fara dillanci atamfofi, nan ma bashi ya fara hawa
kanta k'arshe ma aka daina bata kayan, a lokacin komi ya tsaya cak ga
shi su Ya Hamid sun isa shiga school amma ko zaman Islamiyya basu ta6a
yi ba, Mama ce ma take d'an koya musu karatu idan ta na cikin nutsuwa.
Nikam dama y'ar gidan Ya Umar ce, yawanci agunshi nake cin
abinci, domin tun ina k'arama na saba sosai da Ya Umar, Ya Umar yana
matuk'ar sona ko abinci idan aka saka mai tare dani yake ci kuma shi ne
mai koyamin karatu.
Tunda nafara wayo naji Mama da Ummi suna kirana da FARIDA
UMAR shi kuma su kirashi da Yayan Farida, akwai k'aunar mai tarin yawa
tsakanina da Ya Umar.
Ni kam ban san yunwa ba har sai bayan tafiyan Ya Umar
university a k'asar England, tabbas nayi kewarshi, ta 6angaren Ya Umar
kuwa da kyar ya tafi, bana manta irin kukan da ya dingayi, ranar da zai
tafi haka ya rungumeni yana kuka dak'yar aka rabamu.
Ya Umar ya soni tun bansan kaina ba, Ya Umar shi ne mai
hana kanshi abinci ni ya bani har sai na k'oshi, duk lokacin da yaga ina
kuka tofa idan hankalinshi yayi dubu ya yatashi, bayason ya ganni cikin
damuwa, wannan kenan.
****
Akwai wata rana da muka kwana bamuci komi ba ga shi har
yamma, Ya Abdallah kuwa ya gagara tashi ni kuwa kuka nake yi, Mama ta
samu a gaba ta yi tagumi domin bata da sauran dabara, hayaniya muka fara
jiyowa a tsakar gida kafin kuma muji kukan Ya Hamid da hanzari Mama ta
fita waje, abinda ta gani shiya tayar ma ta da hankali.
Domin matan gidan ne suka sa Ya Hamid a tsakiya daga mai
dungure mai kai sai mai zagin shi, wai sauran abincin da yaron Ladiyo ya
rage ta rufe to fa shi ne Ya Hamid ya d'auka yake ci, shi ne fa suke
cewa yayi sata, magana har waje ana cewa Hamid yayi satan abinci.
Hannun Ya Hamid Mama ta kamo kafin kuma ta bawa Ladiyo
hakuri, a dai-dai wannan lokacin Baba ya shigo koda yaji abinda ke
faruwa.
"kunsan mai ya ce"
Farida ta dubi su Dr jidda, girgiza kai sukayi, goge hawayenta tayi a karo na ba adadi kafin kuma ta ce.
"D'an iskan yaro 6arawo kana k'araminka ka iya sata, idan
abinda ka zabawa kanka kenan, to ina tabbatar maka sata itace ajalinka, a
kasheka an kashe banza, wallahi ba abinda ya dameni"
Cikin kuka Mama ta ce " mai yasa zaka dinga yiwa d'anka mugun baki? baka tunanin ya kamashi"
Da fad'a Baba ya ce "d'anki dai shasha, ina ke kinji kin gani sai kin haifesu? Toh wallahi baki ma fara kuka ba"
Yana gama fad'in haka yayi ficewarshi, kuka Mama ta ke
tamkar ranta zai fita, Ya Hamid na kuka ya durk'usa a gabanta yana ki
yafemin Mama wallahi yunwa nakeji shiyasa naci, shafa kanshi Mama tayi
ba ta re da tayi magana ba.
Ummi ce ta shigo cikin tashin hankali ta ke cewa
"Mai nakeji haka Maman Hamid, almajirina yanzu ya shiga ya ke fad'ami wai Hamid yayi sata, wai me yake faruwa ne?"
Mama na kuka ta mayar ma ta, fita Ummi ta yi ba ta re da ta
ce komai ba, cikin k'ank'anin lokaci ta dawo da abinci cikin kwano ta
sa mana a gaba yadda Ummi taga muna cin abinci saida ta zubar da hawayen
tausayi.
Kafin kuma ta ce "Maman Hamid ki shirya gobe zan kaiki
school d'in da k'anina yake shugabanci ko za'a sama miki gurbin koyarwa
tunda kinada takardar gama secondary school, don zamanki haka ba abu ne
mai yuwuwa ba"
Godiya sosai Mama tayiwa Ummi, ta kuma tabbatar samun kaman Ummi a wannan zamani sai an tona.
Ai kuwa an d'auki Mama aiki a makarartar, cikin ikon Allah
ta cigaba da kulawa damu ta kuma samawa su Ya Hamid gurbin karatu a
makarantar gwabnati, duk da hakan yasa kud'in da Mama ta ke samu baya
isan ta amma tasan ba wani gata da zata mana wanda ya wuce ta bamu
ilimi, mafi yawan lokuta haka Mama ta ke zama da yunwa mu ta bamu.
Haka rayuwarmu ta cigaba da tafiya har izuwa lokacin da
nima Mama ta sakani a school tunda dama tuni ta samu a islamiyya, amma a
wannan lokacin Mama sai ta nemin aikin koyarwar rana saboda kud'in baya
isan mu wannan ne yasa idan Mama ta fita tun safe bata dawowa sai
yamma.
Yawanci lokuta nakanje gidan Ummi idan nadawo daga school
duk da gidan baya min dad'in kasancewar Ya Umar ya tafi jami'a, toh
Ummin ma ba mazauniya bace domin ta na fita aiki, haka dai nakanje idan
na gaji na dawo gida, haka zan zauna a d'aki har sai Mama ta dawo
kasancewar da na fita tsakar gida sai ansani kuka, don ma Mama
tsayayyiya ce akan mu don sun so suzamar damu bayi muyi aiki a bamu
abinci Mama tak'i sam tofa sai aka samu a gaba bamu isa fitaba sai yaran
gidan sun dake mu.
Rayuwarmu duk yawanci ta na tafiya ne a bashi domin albashi
Mama baya isa, mutane biyu ne kawai suke bawa Mama bashi a wannan
lokacin daga Ummi sai wani saurayi da ke gidanmu a d'akin soro mai suna
Hassan, ya na aiki ne da company Nasko.
Kuma Ya Abdallah yana fita yin wildbiro ko siyar da rake
idan ya dawo makaranta yawanci da d'an abinda ya samu ne muke d'an samu
ayi girki idan wata yayi nisa.
Hassan d'an d'akin Mama ne domin ya d'auki Mama tamkar
yayarsa duk wani shawara da Mama ya keyi, haka kuma idan ya samu kud'i
zai siyo su biskit da minti ya kawo min, shiyasa nake sonshi a wannan
lokacin.
Daga baya Mama ta fahimci Ya Hamid baya zuwa makaranta wasu
lalatattun yara ya kebi, Mama takan kirashi ta yimai nasiha tayi fad'an
bata san cewa abun yayi nisa ba domin ashe badda shaye-shaye da yaran
sukeyi harda sace-sace kuma tare da Ya Hamid suke komai.
A wannan lokacin Mama ta shiga wani irin hali, daga k'arshe
sukayi shawara da Ummi akan ta mai dashi makarantar kwana idan baya
ganinsu zai nutsu, amma abinda basu sani ba Ya Hamid yayi nisa domin
koda aka kaishi makarantar gudu yayi.
****
Akwai wata rana a rayuwata da bazan ta6a mantawa ba, ranar da itace mafarin komai!!
Wata yayi nisa bamu da komai a gidan asalima wunin ranar ba
muci komai ba ga shi kud'in da Ya Abdallah ya samu a dakon da yayi yasa
a ajjihunshi bai san ya yage ba duk kud'in sun zube.
Hassan ne ya shigo d'akin da sallama gani na ina rik'e da
ciki ina kuka ya sashi zuwa gareni yana tambayata mai ya sameni cikin
kuka nace mai "yunwa nakeji" cikin tausayawa ya ce zan iya binshi na
kar6i abincin, gyad'a kai nayi, hannu na ya kama muka fita Mama bata ce
komai ba.
Muna shiga d'akinshi ya d'auko abincin ya bani gami da cemin naje muci da Ya Abdallah idan mun cinye na kaimai kwanon.
Nazo ina murna muka ci abincin nida Ya Abdallah ba yadda
bamuyi da Mama tazo taci ba amma tak'i duk da yunwa da takeji amma ta
hakura.
Koda muka gama ci na d'auki kwanon na ce "Mama kawu Hassan
ya ce idan mungama ci na kaimai kwanonsa" gyad'a kai kawai mama tayi da
alama ta yi nisa a tunani, nidai na fita abuna.
Sallama nayi ya ansa sai da ya bani izinin shiga sannan na
shiga d'akin, yanayin da na ganshi ne yasani saurin sunkuyar da kai, duk
da k'arancin shekaruna nasan dai bai dace na ganshi haka ba, dagashi
sai d'an tawul d'aure a k'ugunshi.
Kamo hannuna yayi kafin kuma ya zaunar dani akan cinyarsa,
ya na mammatsa hannu na gami da shafani, sam ni bangane mai yakeyi ba
amma na dinga k'ok'arin tashi ya zaunar dani gami da tambayata na k'oshi
na ce "eh" ya ce toh gobe idan zan tafi school na lek'o zai ban wani
abu amma karna fad'a ma kowa na ce "toh" kafin kuma ya sakeni na tafi
bayan ya sunbace ni a goshi.
Ina shigowa d'aki na tarda Mama ta na tsintar abincin da
muka zubar a kasa ta na ci, bazan iya kwatanta muku yadda na keji ba
idan ina tunawa.
0 comments:
Post a Comment