Wai waye ma ya baka amanata? A hankali kawu ya juyo da kanshi ya kalli samha idonshi yana ɓarin hawaye, kamar mutum ya rasa uwa da uba a lokaci ɗaya,
A hankali samha ta matsa kusa da gadon kawu ta dafa da hannunta ta tsuguna sannan tace kawu faɗamin waye ya baka amanata? Ta ƙarasa maganar cikin sigar lallashi,
Cikin ƙarfin hali kawu yace kije gidana, a ɗakina, nishi, sannan yaci gaba da cewa, zakiga wata jaka mai ruwan kayan sojoji, lunfasawa yayi sannan yaci gaba da cewa, a ciki zakiga bayanin komai akan ahalinki da address nasu,
Miƙewa samha tayi, tare da goge hawayen idonta, harta fara tafiya wata zuciya tace mata ta dawo ta tattaka kawu ko zata rage zafi,
Wani irin juyi samha tayi, tare da rugawa da gudu tana bi ta saman gadajen marasa lafiya, dan gani take kafin taje kawu ya mutu, wani irin tsalle takeyi ta dire daga wannan gado ta faɗa wannan harta isa gadon kawu, ta riƙeshi zata fara kai mishi duka,
Da sauri aka riƙe samha, cikin kuka take kwacewa daga jikin mutane tana cewa ku sakeni yau saina kashe ɗan iskan tsohon nan bana sanka bana kaunarka ka wargazamin rayuwa, bazan taɓa yafe maka ba, ta ƙarasa maganar tare dakai ma gadon kawu wani irin harbi da ƙafarta harsai da kawu ya faɗo ƙasa, da sauri mutane sukaso kan samha suka riƙeta,
Sai ihu samha takeyi tare da ɓarar da mutane, idanuwan samha gaba ɗaya sun ɓirkice dole ta baka tausayi tana kuka tana cewa wallahi saina kasheka, riƙon samha akeyi amma sai zuƙewa takeyi tana ƙoƙarin isa wurin da kawu yake a kwance ƙasa,
Wani mutum ne yasha gaban samha tare da cewa samha kiyi hakuri don Allah, samha ta ɗaga daradaran idanuwanta ta kalleshi tare dayin wani irin la'anannen murmushi, sannan tace haƙuri? To haƙurin samha ya mutu, danni a yau haƙurina ba ƙarewa yayi ba mutuwa yayi gaba ɗaya,
Samha sai hararar kawu takeyi tare da cewa saikaci uwarka yau ɗin nan idan baka mayar dani ba a inda ka ɗaukoni ba saina caccaka maka wuƙa na kwakwalo wannan "yan hanjin da sukayi exp,
Asibiti ta taru kan samha, mutane sai hakuri suke bata tare da nuna mata taji tausayin kawu, amma samha tace babu hakuri yaudai a cikin tsarin rayuwarta, tayi hakuri a baya, wani mutum yace ke yarinya ana baki hakuri bazakiyi ba? Murmushi samha tayi da gefen bakinta sannan ta goge hawayen idonta da bayan hannunta, tace kana da uwa da uba?
Yace sun rasu, samha tace ya kakeji idan ka tuno basa raye a faɗin duniyar nan? Mutumin yayi shiru, samha tace nasan kanajin baƙin ciki a ranka ko ba haka ba? Ta ƙarasa maganar tana nunashi da ɗan yatsanta, kallon samha yayi amma baiyi magana ba, samha taci gaba da cewa da kaine ka kasance a halin da nakeci wane irin hukunci zakayi ma wancan ɗan iskan tsohon?
Ta nuna inda kawu yake kwance, mutumin dai baiyi magana ba, samha tace kuma ɗan iska duk cutar dayayi waishi can har wani mutuwa ma zaiyi ya barni inci gaba da lalacewa ba tare da sanin ahalina ba,
Mutumin yace kiyi hakuri, samha tace dattijo kada ka sake bani hakuri, duk wanda ya sake bani hakuri yau a asibitin nan kan mai uwa dawabi ba mara lafiya babu mai lafiya haka zanyi ta cire kawuna daga saman gangar jikin duk wanda ya sake cewa swry samha,
Cike da fushi samha take ƙoƙarin tafiya wurin da kawu yake kwance amma sai taji an riƙeta ta baya gam, taja taja taji fa riƙe take sosai, juyawar da zatayi dan ganin waye taji an zazzabga mata mari mai taɓa kwalwa,
Kiciniyar kwace kanta ta farayi ganin dady, shi kuma sai ƙara kai mata duka yakeyi ta ko ina, kafin wani lokaci samha ta jigata, yana dukanta yana cewa dan uwarki saboda ke hydar yake mana iskanci ai inajin idan na kasheki baki a duniyar mun huta,
Shi kuma hydar shigowarsa katsina kenan, ya kira yusra, ya faɗa mata ya shigo, dan da samha ta kirashi da wayar yusra, bayan ya sake kirane yace ma yusra zaizo katsina amma kada ta faɗawa samha dan idan taji zaizo zata gudu, to isowarsa kenan ya kira yusra ya faɗa mata inda suke, ita kuma tahau napep dan zuwa inda hydar ya tsaya,
Yusra tana isa tayi ma hydar waya tazo, hydar yace na ganki kece mai kaya kala kaza da hijabi da niƙaf ko? Yusra tace Eh nine, hydar yace juyo bayanki, juyawa tayi, ganin hydar yasa gaban yusra faɗuwa ta nemi rugawa da gudu, domin tunda ya ƙarya mata hannu bata sake ganinsa ba sai yau,
Hydar yace ke kada ki tafi zo mana, ina yusra bata sauraren hydar, ganin bazata tsaya ba, yasa hydar yace ma shamsu maza kamo ta, da sauri shamsu yaja mota yabi yusra da gudu, gudu yusra takeyi kamar ranta zai fita, dan ita a tunaninta hydar yazo katsina ne ya ƙara ci mata mutunci,
Da gudu shamsu yasha gabanta da mota ya karce sosai tare da tayar da kura ya fita daga motar da sauri, yusra ganin bata da mafita yasata durƙusawa ta fara bawa shamsu haƙuri tana kuka, shamsu yace ke dan babarki bakiji mai gida hydar yana magana? Maza shiga mota muje banza,
Yusra jiki yana ƙyarma ta shiga mota, shima shamsu ya shiga yaja suka koma inda hydar yake, suna tsayawa hydar yaji kamar ya mareta, amma saiya fasa, yace ina samha take ne?
Yusra tace tana asibiti, hydar yace kai muje asibitin, da sauri hydar ya koma motar shamsu yaja, dan yau tafiyar sirrice daga shi sai shamsu suka zo, yusra ce take nuna musu hanya sukayi ma asibiti tsinke,
Dan uwarki yau zaki baƙunci lahira, dan na daɗe ina mafarkin ganin Asma'u a matsayin matar hydar, "yar uwarsa ce, dani da uban hydar uwarmu ɗaya ubanmu shegiya "yar gidan bani Oho zaki shigo mana ahali har wani cewa yake idan babu ke zai mutu, to bari in kasheki saiya mutu dama ai bama so ya kasance a raye,
Kallon wani lafiyayen ƙato dady yayi tare da cewa ja mana banza muje, idan hydar yana sanki saiya bada miliyan hamsin ya anso rayuwarshi, dariya dady yayi sannan yace yanzun zaki gane irin san da yakeyi miki idan gaskiya ne, yau zamu sheda, samha jin ance hydar ne zai bada kuɗi ya ansota yasa ta kwace jikinta daga riƙon da dady yayi mata dan ita a tunaninta idan dai hydar zai ansota tasan saida ta mutu, wannan dalili yasa samha taji wani sabon ƙarfi yazo mata,
Ta kwace daga jikin dady tayi waje da gudu, dady yace kubi min banza kuna zuwa ku caka mata wuƙa, samha naji lamarin wuƙa ta ƙara fesawa da gudu kamar zata tashi sama,
Gudu takeyi sosai ga ƙatti suna binta, wai duk mutane babu wanda yayi magana kowa sai kallo yakeyi, tun shigowar su hydar a cikin asibitin yaga samha ta taho ɓarke,
Cikin tsananin tashin hankali hydar yace shamsu bimin takan banzan can da mota, dan ya wahalarmin da matata maza takamin banza da mota ko zai tafin zuwa duniyar mutuwa, sanin halin hydar yasa shamsu yayi saurinyin parking dan yasan hydar yana iya kaɗa motar ta taka mai bin samha,
Hydar yace ba nace ka takamin banza ba? Ya ƙarasa maganar cikin fushi, tsaki yayi tare da buɗa motar ya fita da sauri,
Ganin hydar yasa samha tayi wurinsa dan tsira da rayuwarta, da gudu ta isa wurin, a daidai lokacin da yaron dady ya nufi bayanta da wuƙa dan ya soka mata, tana zuwa ta faɗa jikin hydar da hannun haggushi ya riƙe ta, hannun damarsa kuma yana riƙe da wuƙar da akazo za'a cakawa samha,
Ajiyar zuciya hydar yayi tare da cewa ya kike? Cikin kuka samha tace lafiya ƙalau, murmushi hydar yayi sannan yace, ki tausayamin samha zuciyata ta tafi mi zaki bata? Tunda ta ambaci so ban makoma, nayi alƙawari zan baki kulawa har ƙarshen rayuwarki, idan har kinso in huta samha kice nine, idan baki yanda dani ba haƙiƙa zan iya rasa rayuwata, a daidai lokacin daya halba wanda yazo cakawa samha wuƙa,
Ya riƙe samha sosai a jikinshi yana kuka, yace samha don Allah kiyi hakuri haka nan, miye matsalar hydar? Kalli hydar ki gani idan har namiji kayana kowa zai saka a jikinsa yayi gayu dashi idan kika sako hydar a jikin nasan saikinfi kowa kyau da haɗuwa domin hydar ya dace da rayuwarki,
Ɗago mata fuska yayi, yana kallonta, sai yanzun samha ta lura da jinin hannun hydar, cikin kuka samha ta riƙe hannun tace kaji ciwo, murmushi hydar yayi tare da cewa manta da maganar ciwo kawai kicemin kina so na, murmushi samha tayi tare da ƙara kwanciya a jikin hydar a daidai lokacin da dady ya iso wurin, kallonshi hydar yayi ta saman idonshi sannan ya ɗaga samha daga jikinshi, yace dady ashe saika rigani zuwa? Yayi maganar yana kwantar da kansa a gefe, taɓe bakinsa hydar yayi tare da ɗaga girarensa alamar tambaya,
Dady zai fara wani zage zagen banzarsa hydar yace wallahi dandai kada inbar abin faɗi a duniya dana juya maka kai ya koma ta ba, kuma na rabaka da bibiyar rayuwar samha daga yau, idan kuma zakaci gaba dani dakai zamu kunna whyfer kwanakin hari zasu soma daga yau,
Yana faɗin haka yayi masa wani irin kallo mai nuni da zakaci uwarka, sannan yaja hannun samha suka nufi mota, a baya suka shiga, yusra da shamsu suna gaba, shamsu yaja motar suka fita daga asibitin, samha na kwance jikin hydar sai kuka takeyi,
Hydar yace kiyi hakuri samha, insha Allah kuka daga yau ya ƙare babu ke babu ƙara kuka har ƙarshen rayuwarki, daga yau farin ciki ya soma a rayuwarki,
Cikin kuka samha tace bazan daina kuka ba harsai naga ahalina, murmushi hydar yayi tare da cewa kada ki damu ahalinki suna tare dake,
Daga haka hydar bai sake magana ba, sai samha dake kwance a jikinshi tana ta shashshekar kuka, hydar kallon hannunshi yayi daya riƙe wuƙa dashi ya yanke sosai murmushi yayi tare da kyauda hannun gefe ɗaya,
Har suka isa ƙofar gidan su yusra a ƙofar gida suka ajiyeta, hydar ya ciro kuɗi daga jikinshi ya miƙawa shamsu yace yabawa yusra, godiya yusra tayi sosai tare dayi musu addu'ar sauka, su kuma su Ibi hanyar kd sai ɓarin wuta suke bisa titi,
Kawu kuwa bayan zuwan dady aka ɗauki munafikin Allah aka mayar dashi a gado, cikin muryar marasa lafiya ya jirge baki gefe sai kiran sunan samha yakeyi,
Dady kuwa sai addu'a yake Allah yasa hydar yayi haɗarin mota ya mutu a hanya, saida ya gama baƙar fatarsa sannan ya dawo yayi ban kwana wa ahalin kawu tare da musu alheri, sannan suma suka fito suka shige moto suka fara cin kwalta dan zuwa garin kaduna,
Su hydar na shiga kaduna zuwa yayi aka fara mishi dressing a hannunsa daya riƙe wuƙa dashi, bayan an gama ne ya dawo mota samha tace mishi a gidan kawu zata sauka,
Hydar yace kiyi hakuri muje gida kiyi wanka ki huta sannan in kawoki, samha tace nifa bazan wani je ba, kawai ka ajiyeni a inda nace, murmushi hydar yayi sannan yace shamsu kai samha inda take so,
Shamsu ya kaɗa kan mota sai gidan kawu, bayan sunje ne samha zata fita, hydar yace kiyi sauri ki gama abinda kikeyi, danayi magrib zanzo in ɗaukeki, samha tace to,
Fita tayi su kuma suka wuce, gidan da suke bayar da ajiyan makulli taje ta karɓa, bayan ta anso ne tazo ta buɗe gidan, da sallama samha ta shiga,
Kai tsaye ɗakin kawu ta wuce, bayan ta buɗe shima da sallama ta shiga, tun a farlo ta fara ganin ƙattin takardu wanda kawu ya lilliƙa masu ɗauke da hotunan samha,
Gaba ɗaya bangon ɗakin duk yabi ya rubuce shi da i love samha, wani ɓan gare kuma zanen mace da namijine, yanda shi kawu yake nufi shine dashi da samha,
Tsoki samha tayi tare da cewa banza shashasha, duk kware hotunanta tayi sannan ta fito duka ta cinna musu wuta tanayi tana mita tare da cewa mahaukacin banza, kaida kace babu so a rayuwa, so wasa ne, kuma *_SO MUGUN WASA_* ya akayi ka bari san samha ya shiga cikin zuciyarka ba tare daka dakatar dashi ba?
Bayan ta gama ƙona hotunan, ta ɗauko jakar da kawu yace mata, tana ɗauka ta fita daga ɗakin ta fito tsakar gida, zazzage jakar tayi dukanta,
Hotuna suka bayyana sai tarkacen takaddu, ɗaukar hotunan samha tayi ta fara dubawa, lallai ko ba'a faɗa ba wannan mamanta ne, ga yarinya tana rungume da ita jaririya wanda samha ta yanke hukunci cewa itace tana jaririya, murmushi samha tayi tare da ci gaba da duba hotunan,
Haka tayi ta duba hotunan, hoto ɗaya ne tayi tsaye a kanshi, lallai wannan fuskar tasanta amma ta rasa a ina ta sani, haka dai tayi ta dogon nazari amma fuskar ta ɓace mata, tattara hotunan tayi ta ɗauki takarda ɗaya ta duba, adress ne rubuce a jiki,
Wanda ba rubutun kowa bane na kawu ne, ya rubuta ko bayan rayuwarsa ga inda zata nemi danginta, ƙarshen rubutunsa kuma ya rubuta kamar haka,
_Samha na kamu da tsananin kaunarki, ina sanki ina kaunarki har cikin ƙarƙashin zuciyata,_
_Bayan zuciyata ta tabbatarmin da haka saina fara ƙoƙarin ta ina zan farawa lamarin? Amma sai hydar ya shigo cikin rayuwarki, tun a lokacin da kika fara soyayya dashi a matsayin sahib nayi babban bincike akan insan waye sahib? Tun a lokacin da kuka zo wurina a gidan kaso,_
_Bisa dogon bincike da nayi sai na gane babu wani sahib a duniya hydar shine sahib, kuma hydar shine mijinki,_
_Bayan kin bashi m card yaga yanda akayi ma mahifiyarki kisan gilla shima bisa binke da yayi a lokacin sai ya gano cewa mahaifiyarki kanwar mahaifiyar sa,_
_Hydar ya tattara dani da wanda suka kashe miki mahaifiya su akayi musu hukunci daidai da yanda suka aikata kisan kai, ni kuma yasa aka min horo mai tsanani bisa gurɓata miki rayuwa da nayi_
_Bayan hydar ya gano ke "yar uwarsa ce, kuma shi yazo miki a matsayin sahib, tosai yaso ya nuna miki shine hydar kuma ya faɗa miki zumunci dake tsakaninki dashi, amma saiya gane idan har kika sani bazaki yadda ba, saboda bakya sansa,_
_Wannan dalilin yasa yayi ta zama a matsayin sahib a wurinki, wannan dalilin yasa hydar ya ajiyeki a wurinsa domin ya koyawa zuciyarki san hydar, dangin mahaifinki basu san hydar ba shima hydar bai sansu ba, kasancewar iyayen hydar ba mazauna nigeria bane,_
_Wannan M card shine ya bayyana wa kakar hydar ta gano hoton mahifiyarki, a lokacin data gani tayi kuka sosai domin mutuwar ɗiyarta ya dawo mata sabo, hydar kuma yayi mata bayanin komai daga haɗuwar har zuwa lokacin aurenku, kuma duk dani akaje, kuma ta ganni ta shedani tayi tirr da Allah wadai da halina, kuma tace bata yafemin ba, daga taimako amma nayi musu sakayya da tarbiyyar jika bisa mafi munin raino_
_Dan haka mukaje aka ɗaura aurenki da hydar, abinda yasa ya ɓoye aurenku saboda illa irin ta ƙanin mahifinsa, wanda abokina ne, idan kin tuna fuskarshi muna haɗuwa dashi a wurin wasan caca, yana da san zuciya sosai wannan dalilin yasa aka haɗa kai dashi aka kashe ɗan uwansa tunanin zai samu wani abu a cikin kuɗin yayansa hydar dai zai baki baki labari,_
_Na roƙeki samha ki yafemin, kuma ki nema min yafiya a wurin kakarki, ga address nata, ya rubuta daga ƙarshe kuma yace ina miki fatan alkairi kuma inama hydar farin cikin samunki a matsayin matar aure, samha duk namijin daya sameki a matsayin mata ya more domin Allah ya wadataki da wasu sirrintacciyar baiwa da ni'ima wanda ba ko wace mace take dasu ba,_
_Samun irinki ɗaya rak zaiyi wahala a cikin mata, dake da hydar kun dace, kinyi miji fatan Allah ya baku zaman lafiya_
Zufa samha ta goge tare da cewa tirƙashi, ina niyar guduwa ashe dole in tsaya? Lallai bazanje wurin dangin uba ba gareku dan dangin uwata,
Miƙewa samha tayi ta tattara komai ta mayar a jakar, tare da cewa amma hydar yakai ɗan iska, wato shine sahib? Ya akayi ya zama mutum biyu? Ko magana ba iri ɗaya bane, dogon nazari samha tayi tare da tuno maganar hydar,
_Hydar in baka labari? Kallonta yayi ba tare da yayi magana ba, samha tace idan baka so shikenan, murmushi hydar yayi tare da cewa ina so mana,_
_Yau sahib ya kusa faɗuwa, murmushi hydar yayi tare da cewa ai saiki tadashi, Allah ya sawaƙe bazan tadashi ba, miyasa? Saboda yayi girma, murmushi hydar yayi sannan yace dani da sahib waye yafi girma?_
Kam amma lallai hydar kwallon ɗan iska ne, wani tunanin tayi,
_Ki cire kayanki duka, zan baki miliyan ishirin,_
Murmushi samha tayi tare da tuno hotuna da dama da sukayi ta faruwa a tsakanin ta hydar,
Tun farkon haɗuwarta da sahib data fasa mishi waya a bakin holl ɗin training har zuwa yau, ya dawo mata a kwanyarta, amma abinda yafi tsaya mata a kai shine rayuwarta da hydar a matsayin sahib,
_Kizo muyi hoto nasan idan har sahib ya ganmu a wannan yanayin zaiji farin ciki yace muna zaman lafiya, kwanta a jikina hakai zaifi mishi daɗi,_
_Zoki kwanta a jikina ki ɗan lashemin bakina idan har kina so in goyaki a mashin_
_Ke zo nan, ni sa'ar wasarki ne? Mi nayi maka kuma? Ke kamarni zaki riƙa rubutawa a hannunki kina so na? Ni ban rubuta ba, idan aka duba aka gani fa? Kamin komai ma, buɗe hannuwan mu gani, wallahi bani na rubuta, rufe min baki maza kije ki zauna a can ki jirani in gama_
_sahib wallahi hydar fa ɗan iska ne, da gajeran wando yake mana yawo a gidan nan, ka mishi magana_
_Sahib banda lafiya fa, cikina yakemin ciwo, kira hydar ki baɗa mishi, danni ina da abunyi, banda number hydar ai, bara zan turo miki,_
_Hydar zan mutu, subahanalla miyasa zaki mutu kuma wace ce take magana?_
_Mijina yace inzo in maka shara, kuma naga dakin baiyi datti ba, hydar yace ai basai yayi datti ba ake sharewa ba, samha tace to kuma yace in baka haƙuri, hydar yace ai idan mijinki yamin laifi ba haka yake bani haƙuri ba, zo nan, samha tace ai naga babu kaya a jikinka ne, hydar yace ina ruwanki da kayana ko rashin kayana? Kedai ba haƙuri akace ki bani ba? Gidana ne nan dole in zauna yanda nake so, kema ban hanaki ki fito da ɗaurin gaba ba,_
_Samha tace aini ba "yar iska bace, hydar yace niko kinga dan iska ne ni shiyasa ma nake zama da gajeran wando abuna, samha tace to Allah ya shiryeka, hydar yace kai ba amin ba a barni da iskancina nafi jin dadi, nidai bani hakuri tun kafin zuciyata ta fara tsimama,_
Murmushi samha tayi tare da cewa lallai hydar wayonka yayi yawa,
_Sahib yau saina sane abinda hydar yake sakamin a ido, anya zaki iya sane a jikin hydar? Eh mana, sahib kalli na ɗauko kuma hydar bai sani ba,, murmushi sahib yayi tare da cewa shi kuma hydar dayafi wayau sai yayi miki vidio kalli,_
Haka dai samha tayi ta tunano abubuwa da dama tsakanin ta da hydar & sahib, samha tace lallai hydar yafi samha basira,
Sallamar da hydar yayi yasa samha ta tsagaita da tunaninta, kallo ɗaya samha tayi mishi ta ɗauke kanta,
Wata irin munafikar dariya hydar yayi maisa mutum yaji tsikar jikin sa ta tashi, sannan yace ashe ma baki yi wanka ba? Samha tace ban sani ba,
Hydar yace kada Allah yasa ki sani wuce mu tafi gida danni bacci nakeji sosai na gaji da yawa a daidai lokacin daya matsaya kusa da ita yaɗan rungumota,
Yanda yayi mata riƙon yasa taji duk kasala ta baibaye mata jiki, ɗan murmushi hydar yayi sannan yace mu tafi ko?
Samha tayi shiru, ɗagata yayi daga jikinsa ya duka ya ɗauki jakar da take ajiye a gabanta yana cewa wannan fa?
*_Kuɗanyi haƙuri da wannan don Allah_*
*_Jamila Musa_*
[05/04 4:46 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*_Yau wannan shafin ɗungurugum nakune masoya takardar littafin SO MUGUN WASA ina muku fatan alkairi a duk inda kuke domin kune maudi'i na, fatan Alkairi da addu'ar zaman lafiya a garemu baki ɗaya_*
*SO*
*MUGUN WASA*
*_Dedicated to_*👇🏻
_Ramlat Abdulrahman real mai dambu_
*62-64*
Ɗagata yayi daga jikinsa ya duƙa ya ɗauki jakar dake ajiye a gabanta yana cewa wannan fa?
Turo baki samha tayi ba tare da tayi magana ba,
Hydar yace bakiji ina magana ne? Tsoki yayi sannan yaci gaba da cewa waike dan kinga ina lallaɓaki kike min rainin hankali ko?
Cike da tsiwa samha tace to kada Allah yasa ka lallaɓa ko nace maka ina san ka lallaɓa ni? Waikai sahib kai hydar ko? Kai amma kazo da rainin hankali,
Murmushi hydar yayi tare da cewa baki ma san nazo da rainin hankali ba sai munje gida zakiji a jikinki ya ƙara maganar yana shafa gefen fuskar samha tare dayin dariyar ƙeta,
Hannunshi samha ta bige daga fuskarta, hydar yace subahanallah mijinki kike ma haka? Bakisan bige hannun miji a jikin matarsa ba wuta balbal, murmushi yayi tare da cewa amma na yafe miki muje gida,
Samha tace nifa bazanje ko inaba anan zan kwana, kaje kawai zanzo daga baya, hydar yace to bari in siyo mana maganin sauro in dawo dan nasan gidan nan zaiyi sauro kuma ni wallahi sauro hanani bacci yakeyi, ya ƙarasa maganar yana taɓe baki,
Samha tace a ina sauro zai hanaka bacci ne? Hydar yace anan gidan mana, wallahi idan har anan zaki kwana nima anan zan kwana sai mu kwana tare,
Juyawa samha tayi ta fara tafiya zuwa ɗaki cewa wallahi ai nan ba gidan mutun bane kuma sai ka tafi tunda bakaine ka siya ba, binta hydar yayi yana cewa ke ni zaki ma rashin kunya? Baki san akwai banbanci tsakanin sahib da hydar ba?
Samha tace can matsalar ka, kuma idan baka san rashin kunya saika saken..... Wani irin mari hydar yakai mata wanda yasa tayi sujjadar dole tana kuka, hydar yace nine zakice in sakeki saboda ke mahaukaciya ne?
Cikin masifa samha tace ni bana sanka kuma bazan iya zaman aure dakai ba, ko ka taɓa ganin an haɗa ƙarya da gaskiya? Tou wallahi so da ƙiyayya bazai taɓa zama wuri ɗaya ba,
Hydar yace samha nine bakya ƙauna? Nine kike ma ƙiyayya? Cike da masifa samha tace Ey, Ey, Eyyyyyyyyyy, na tsaneka dama bana sanka, kuma kazo ka ƙara daɓa wani ƙiyayyan akan wani waika sahib, kai amma wallahi ka ɗauki samha daƙiƙiya, ni bamma san jaka zan kira kaina ba ko sakara? Ajiyar zuciya hydar yayi sannan yayi ma samha wani irin kallo wanda shi kaɗai yasan abinda yake nufi,
Murmushin ƙarfin hali hydar yayi da gefen bakinsa tare da sassauta gani idonsa, daga haka bai sake magana ba, ya juya a hankali ya fita daga gidan, jirin daya ibi hydar ya hanashi isa wurin motarshi, dan haka ya dafe bango a tsaye yana maida numfashi,
Fitar hydar samha ta taho a hankali dan taga idan hydar ya tafi, a bayan kyaure samha ta ɓoye tana leƙen hydar, shi kuma ya kwantar da kanshi a saman mota, ya bawa samha baya, amma duk abinda samha takeyi a bayanshi ya ganta, murmushi hydar yayi sannan ya buɗe motarshi shige yaja yabar wurin,
Har zuciyar samha bataji dadi ba, da sauri ta fito daga bayan kyauren ta fita da gudu waje hydar harya ɓace daga wurin kamar walƙiya,
Tsaki samha tayi sannan ta koma gida tare da rufe ƙofa, jiki a sanyaye samha ta shiga gida, saida tayi wanka sannan tayi sallah isha'i bayan ta gama ta kwanta tana tunanin hydar, macijin robar daya saka mata ta fara tunani da gudun datayi da lokacin data kwanta a jikin sahib ya cire mata ashe duk hydar ne, Yazo a matsayin hydar yasa mata cuta sahib yazo ya cire mata,
Lallai ta tuno lokacin data ga sahib da kayan hydar ta koma da sauri kuma sai taga hydar to ya akayi haka tayi ta faruwa?
Hydar kuwa da taikon ubangiji ya isa gidan kakarsu, ko parking ɗin kirki baiyi ba ya fita daga motar yayi ciki da sauri,
Da sauri ya shiga farlon baya ganin kowa kuma duk masu gaisheshi bayajin su, lokacin daya shiga bedroom ɗin baya ƙarda komai yasan dai yahau gado da kanshi ya ɗora kanshi jikin kaka daga haka hydar bai sake sanin komai ba,
Tunda hydar ya shigo a birkice kaka ta fara magana cikin yarensu nikam bana gane komai sai sunan samha nakeji tana kira a maganarta,
Wayarta ta ɗauka ta kira faruk tace yazo yanzun tana san ganinshi, babu ɓata lokaci faruk yazo bayan yazo kakata tayi ta faɗa sosai sannan tace akai hydar asibiti kuma duk inda samha take a daren nan a nemota kuma a faɗa mata cewa hydar ya mutu ta huta ɗan uwanta ya mutu saboda ita saita zo ta zuba ruwa a ƙasa tasha,
Haka aka ɗauki hydar akayi asibiti dashi, gaskiya yana jin jiki sosai banda kuka babu abinda kaka takeyi tare da faɗin saita ramawa hydar wahalar da samha tasashi yakesha dan tasan yana santa take mishi wulaƙanci,
Har gari ya waye hydar bai farfaɗo ba, ganin haka yasa kaka tace a tafi dashi waje don ganin likita,
Samha kuwa da safe ta jirayi zuwan hydar ta bashi hakuri abinda tayi mishi kuma ta faɗa mishi tana sansa, amma babu hydar babu dalilinsa, har rana ta faɗi samha bata ga zuwan hydar ba, gaba ɗaya taji babu daɗi,
Lallai batayi ma hydar adalci ba, tuno tsaunin benen wurin training tayi tare da halbowar dasu wawu sukayi mata,
_Kaiiiiii kada ka faɗo da ita na faɗa maka, kada kamin wasa da rayuwa,_
Dariyar su wawu ta tuno hhhhhhhhhh kana santa ne? Sahib yace Zuciyata ce, dariyarsu ta ƙara dawoma samha a cikin dodon kunnuwata, sannan maganar wawu,
_Bari muga idan kana santa, shirya ga zuciyarka nan zuwa gareka_
Hawaye samha ta goge tare da sauke ajiyan zuciya, lallai kuma hydar saboda yana santa bai bari takai ƙasa ba daga saman bene hawa na ukku miyasa baza tayi ma hydar adalci ba?
Tuno jiya tayi a katsina, anzo caka mata wuƙa, amma hydar ya riƙe wuƙar ta yanki hannushi, amma duk da haka ba yanka yakeji ba, saiya fara tambayarta,
_Ya kike? Samha ki tausayamin zuciyata ta tafi akanki mi zaki bata? Tunda ta ambaci so ban makoma, nayi alƙawari zan baki kulawa har tsawon rayuwarki idan har kinso in huta kice nine_
Ajiyar zuciya samha tayi tare da cewa bawan Allah kuma har a lokacin wuƙan yana hannunshi, goge hawayen idonta tayi,
_Kiyi haƙuri samha insha Allah kuka daga yau ya ƙare babu ke babu ƙara kuka har ƙarshen rayuwanki, daga yau farin ciki ya fara a rayuwarki,_
Sallamar da akeyi ya dawo da ita daga tunanin da takeyi, ansa sallamar tayi tare da cewa waye? Faruk yace nine faruk,
Da sauri samha ta fito daga ɗaki tana cewa ka shigo mana, murmushin ƙarfin hali faruk yayi tare da cewa kaka tace inzo inje dake gida yanzun yanzun babu lafiya, samha tace lafiya dai? Faruk yace dama hydar ne ya mut............kafin faruk ya ƙarasa samha ta faɗi kasa tare da tafi duniyar suma,
Salati faruk ya farayi don baiyi tunanin haka samha zatayi ba, danshi dama kaka cewa tayi idan yazo ya faɗawa samha hydar ya mutu,
Da sauri ya ciro wayanshi ya fara kiran kaka babu daɗewa ta ɗauka cikin kiɗima faruk ya faɗawa kaka samha ta mutu, cike da tashin hankali kaka ta fara salati, tare da tambayar faruk ina ne inda suke?
Faruk ya faɗawa kaka tace gata nan zuwa, kaka tana kashe waya sai salati takeyi tare da cewa wannan wane irin masifa ne? Abu daga wannan sai wannan? Shi Aliyu yana ciwon zuciya saboda samha, ita kuma ta mutu saboda hydar?
Waya tayi da drivern ta yazo, bayan yazo ta kira faruk ya faɗa mishi inda suke, driver yace ya gane wurin, bayan sun gama wayarne suka tafi, a hanzarce suka isa wurin mota babu ɓata lokaci kaka ta shiga suka nufi gidan kawu,
Suna isa bayan driver yayi parking kaka ta fita da saurinta ta shiga gidan kawu, faruk yana ganin kaka ya fara wallahi wallahi kaka bata bari yayi magana ba, tace ya kawo ruwa,
Da sauri ya kawo ruwa kaka ta fara yayyafawa samha, ajiyar zuciya samha tayi tare da furta inalillahi wa'inna ilaihir raji'un hawaye yana tsiyaya daga cikin gurbin idanuwanta,
Kallonta kaka takeyi cike da tausayi tare dajin ƙaunar "yar jikarta har cikin zuciyarta, lallai kawu ya cuci rayuwar yarinyar nan, amma haka Allah ya ƙaddara mata dan ko wane bawa da ƙaddararsa, kenan itama tana san hydar? Tunda harta suma saboda shi?
Faruk ne yace hajiya mu tafi a kaita asibiti, kaka tace ba asibiti ba gida, dan bata da cikakiyar hausa sosai, kallon samha tayi tare da kamata alamar ta tashi cikin yarenta take cewa su tafi,
Ɓata fuska samha tayi tare da ci gaba da kuka, kaka take tambayrta kukanmi takeyi? Samha dai ta bita da kallo dan bata san abinda take cewa ba, shima faruk bayajin yaren kaka, wata maganar takeyi da hausa wani kuma baya faɗuwa dan haka suka koma yaren bebaye,
Haka dai samha ta haƙura ta tashi ta koma ɗaki ta ɗauko jakar data ɗauko a ɗakin kawu sannan ta fito tsakar gida suka fita daga gidan baki ɗayansu,
Gidan da suke bayar da ajiyan makulli taje ta bada bayan ta bayar ne, ta fito ta nufi inda kaka take jiranta suka shiga mota suka nufi gidan kaka, tun a mota kake take magana daga gani dai faɗa takeyi kuma da samha takeyi, ga banza tunda dai tunda samha batajin karatun,
Itadai sai kuka takeyi tana ƙarawa, tana so ta tambaya da gaske hydar ya rasu? Amma bata da wanda zata tambaya tunda bata iya maganar kaka ba,
Ganin bata iya haƙuri yasa ta anshi wayar kaka, ta shiga gallery ta fara dubawa, hotunan duk kaka da hydar babu wanda yake shi ɗaya, itama babu ita, ita ɗaya, dan haka ta kalli kaka tare da nuna mata hoton hydar da yaren kurame tace mata yana ina?
Kaka tace mutuwa, idanuwa samha ta zaro sosai tare da cewa waye ya kashe shi? kaka bata sake magana ba, ita kuma samha buɗe jakar kawu tayi ta fiddo hotunan tana dubawa, harsai data zo wurin hoton kaka sannan ta tsaya ta kalli hoton ta kalli kaka, a daidai lokacin da suka iso gida,
Bayan driver yayi parking kaka ta fita, itama samha fita tayi, tana bin bayan kaka tana kuka har suka shiga ciki, ganin samha bataga wasu masu zaman gaisuwa ba yasa ta fara tunani kilama kunnenta baiji mata daidai ba, itama kaka datace mutuwa kila ma batasan abinda ita samha ta tambayeta ba shi yasa tace mutuwa,
Tunda suka shiga farlo samha ta bi hotunan hydar da kallo lallai ko ba'a faɗa ba kana gani kasan hydar anaji dashi, bin bayan kaka samha taci gaba dayi simi simi har bedroom,
Zama samha tayi a gefen gado tana ta kallon hoton hannunta kuma tana ƙarewa kaka kallo, to lallai wannan itace kawu yake cewa itace ta aifi mamanta? Lallai wannan tsohuwa tana kama da momyna babu banbanci,
Towel kaka ta miƙawa samha tare da cewa kiyi wanka wanka, dariya samha tayi sosai jin maganar kaka, har ta fito daga wanka samha dariya takeyi tana maimaita kiyi wanka,
Bayan samha ta fito wanka kaka ta bata kaya ta saka, sannan tace kici abinci, wai taje tace abinci, yanda kaka take maganar ne yake sa samha dariya sosai na farko dai bata iya hausar ba idan kuma zatayi magana da hausa kamar zatayi kuka kana gani dai kasan hausa tana mata wahalar furtawa,
Tou haka dai rayuwar samha tayi ta tafiya a gidan kaka, kwanaki masu yawa anyisu, satittika anyi sun shuɗe, watanni kuma suna ta ƙara hayewa amma babu labarin hydar, saidai lokaci lokaci samha tanajin kaka tana waya kuma tanajin ana kiranta sunanta haka ya tabbatar mata da hydar ne,
Dan haka yauma kaka ta gama wayarta ta ajiye ta fita, samha ta ɗauki wayar ta shiga dialled calls, tana dubawa taga lallai da hydar ne kaka tayi waya dan haka da sauri ta shiga kiran number,
Babu daɗewa hydar ya ɗauka, bayan sallama yaci gaba da magana cikin yaren kaka dan dama basu gama magana ba kaka ta kashe wayan, gyara murya samha tayi sannan tace samha ce, hydar yace samha? Wace ce samha? Samha tace Ni, ni samha mana, hydar yace daga ina kuma? Samha tace samha fa nace maka, hafsat ta faɗi ainayin sunanta, hydar yace kai ni banwani san wata samha ba, yana faɗin haka ya kashe wayarshi,
Jin hydar ya kashe waya yasa samha ta sake kiran wayar cikin sauri, amma hydar bai ɗauka ba, da sauri ta ƙara kira saiya kashe wayan ma baki ɗaya,
Duba number tayi taga numbershi ne kenan yana ma nigeria babu inda yaje tsagwaron iskanci ya hanashi zuwa ma tunda yasan tana nan,
Shi kuwa hydar tunda ya dawo daga jinya yaji labarin samha tana gidan kaka yace bama zaizo ba bare ya ganta taci gaba da tada mishi hankali danshi ya gaji dashan wani maganin ciwon zuciya sai kace ɗan ƙwaya, amma tunda samha bata sansa zai haƙura shidai yasan yana santa kuma makahon so yake mata kuma san da yakeyi wa samha mai ɗauke lumfashi ne, dan haka zai barta ya sama mata farin ciki a rayuwarta dan bazai so yaga samha tana cikin damuwa ko tashin hankali ba, tunda dan yana santa yake san ta samu natsuwa tunda bata sanshi zai hakura kada ya takura mata itama tazo ta samu matsala irin tashi,
Jin hydar ya kashe waya gaba ɗaya yasata jin tashin hankali na karshe, dan haka da sauri ta fara kiran number faruk data gani a cikin wayan kaka, shima saida ta kusa tsinkewa ya ɗauka, bayan gaisuwa tace mishi don Allah kaje ka kaima hydar waya zanyi magana dashi, murmushi faruk yayi tare da cewa ai ina tare dashi bari in bashi,
Samha tanajin yanda faruk yake ƙaraya da hydar ya anshi waya amma yace sam, faruk ya haɗashi da Allah amma wallahi hydar yace bazaiyi waya da samha ba, a hankali samha ta silale saman gado ta kwanta hawaye na ɗiga daga cikin kwayar idonta,
Faruk taji yana cewa miyasa bazakayi waya da ita ba? Cikin tsananin ɓacin rai hydar yace haka nan, cikin sigar lallashi faruk yace dan Allah tunda harta kira tace a baka kayi hakuri ka ansa, hydar yace faruk don girman Allah ka daina min maganar yarinyar nan ni sunanta ma bana so inji ana faɗa dan haka kashe waya, faruk zaiyi magana cikin hayani hydar shiruuuuuu ya ƙarasa magana yana zaro idanuwa kamar zai kaiwa faruk duka,
Da sauri samha ta kashe waya kamar ita hydar ya dakawa tsawa, lokaci guda kuma taji gabanta yana faɗuwa jikinta gaba ɗaya ya ɗauki rawa saboda jin muryar hydar cikin fushi yasa tajita kamar ba'a duniya take ba, ashe akwai ranar da hydar zai tsananeta haka? Goge hawayen idonta tayi tare da ajiyar wayar gefe ta rufe idonta da sauri jin kaka tana zuwa,
Jin samha ta kashe waya yasa sukayi dariya dukansu, hydar yace "yar rainin hankali nima zakiji yanda nakeji, dariya faruk yayi tare da cewa ai tunda kace min ta biyoka tana leƙenka a gidan kawu nasan yarinya ta faɗo tarko, hydar yace barni da ita, nasan yanzun tana san ta ganni kuma yarinya bazaki ga hydar ba,
Faruk yace a, a, kaiko miye haka? Kada ka wani ce bazakaje ba, murmushi hydar yayi tare da jingina bayanshi da jikin gado, sannan yace kiramin farida, zan auno samha inga idan ta fara so na da gaskiya,
Kiran wayar farida faruk ya fara yi bayan ta ɗauka yace mai gida zaiyi magana dake, miƙawa hydar wayar yayi, bayan hydar ya ansa yaɗan goga farida jawabi, karshen wayarsa dai murmushi sannan ya kashe,
Samha kuwa kwance sai kuka takeyi wai ita hydar yake dakawa tsawa, amma ba komai, koda kaka ta shigo ta samu samha tana kuka data tambayi samha kukanmi takeyi, samha faɗa mata tayi hydar yayi mata wulaƙanci, abinda kai kaka ta fahimta shine sunan hydar da samha ta kiraka a cikin zancenta ita kuma kaka tasha wani abun arzikine don haka tace da kyau, tana faɗin haka ta fita,
Samha kuwa saida tasha kukanta ta gaji sannan tayi bacci,
Da safe tunda samha tayi sallah asuba bata koma bacci tana nan kwance kamar wata matacciya sai wani fiƙi fiƙi takeyi da idanuwa, tana nan kwance har 11:09am sannan samha ta tashi taje tayi wanka,
A hanzarce ta fito daga toilet tana gunguni, da sauri ta natsu danjin maganar hydar a farlo, taso ta fita amma gani takeyi kamar hydar zai watsata dan taji maganar mace, ina kuma hydar ya samo ta?
Tana tsaye tana nazari inda hydar ya samo mace, taji muryar macen tana cewa wai ina samha? Ƙasa ƙasa samha tayi da murya tare da cewa tana gidan ubanki,
Hydar yace kai mu babu wata samha a gidan nan gaskiya kaka sai yayi magana da yare, wanda samha bataji abinda yace ba, taji dai kaka tayi dariya tare da cewa samha,
Samha tace ai sai kuje kuyi tayi, in banda munafirci sai ayi ta magana da yaren da mutum bayaji, idan ba gaskiya ba a fito fili ayi magana da yaren da kowa yake fahimta mtswww,
Ganin baza ta fito ba yasa hydar ya miƙe ya nufi bedroom ɗin, fuska a ɗaure ya shiga babu alamar wasa, da sauri samha ta durƙusa ta gaishe da hydar, ya ansa a daidai lokacin da yake zama a gefen gado, yace ke zo nan, jiki a sanyaye samha ta matsa kusa da hydar tare da duƙusawa saman guyawunta cikin ladabi,
Hydar yace bakiji nazo ba? Samha tace wanka nakeyi yanzun na fito, hydar yace da kika fito kuma miye ya hana ki fita ki gaisheni? Samha tayi shiru, hydar yace saboda kin rainani ko?
Samha tace kayi hakuri, tsoki hydar yayi tare da cewa jeki gaisa da farida, samha tace miyasa ni zanje in gaisheta ne? Miƙewa hydar yayi tare da cewa ni nace ai,
Samha tace to kace tazo nan sai in gaisheta, juyowa yayi ya tsareta da idanuwa, wanda yasata ta ɗauki hijabi tabi bayan hydar, tana gunguni, juyowa hydar yayi yace badai kince baki san hydar ba? Zo kiga wanda zan aura gama I V ya ciro daga jikin aljihunshi idanuwa samha ta zaro sosai tare da ciko bakinta da magana shigowar kaka ta hana samha faɗin abinda tayi niya,
*_Jαmilα Musα_*
[05/04 4:46 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*_Bana gajiya da faɗa muku masoyan BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, shahararrin marubutan zamani wato Tweety & Aysal sunzo muku da sabbin labarai masu ƙayatar da zukatan masu karatu, bugu da ƙari ilimantarwa darussa masu girma tare kuma da nishaɗantar da masu karatu, tweety tazo muku da, DUK ABINDA YA BAKA TAUSAYI, hausawa sukace wata rana zai baka tsoro, ita kuma Aysal tazo muku da tata shaharar littafin nata shin, BAKA NI KIYA, tou fa kunji mace ce fa baka nikiya, kada ku bari a barku, ni Jαmilα Musα nake cewa asha karatu lafiya_*
*_Gaisuwa ta a gareki, FATIMA MUHAMMAD ina miki fatan alkairi kuma ina godiya sosai wallahi da addu'arki a gareni nagode sosai Allah ubangiji yabar mutum da masoyinsa, na gode sosai wallahi,_*
*SO*
*MUGUN WASA*
*_Dedicated to_* 👇🏻
_Ramlat Abdul real mai damburabos_
*65-67*
Idanuwa samha ta zaro sosai tare da ciko bakinta da magana, shigowar kaka ta hana samha faɗin abinda tayi niya,
Anshe IV ɗin samha tayi daga hannun hydar saida ta kalleshi sosai sannan tayi murmushi tare da cewa to Allah ya baku zaman lafiya ubangiji yasa ayi a sa'a,
Amma abinda nake so ka tuna shine, kace kanka baya ɗaukan hayanir mata biyu, haka ka faɗa amma yanzun zaka ƙara ko? To nima gaskiya nayi ƙarama da in zauna da kishiya nima kaina baya ɗaukar hayaniyar kishi dan haka ni nabarwa farida kai,
Tana faɗin haka ta yada IV in ta koma bedroom, kaka ta fara tambayar hydar miye? Murmushi yayi tare da duƙawa ya ɗauka iv in amma bai ba kaka ansar tambayarta ba, ya fice daga farlon farida ta tashi tabi bayanshi,
Saida hydar ya fice daga farlon, kaka ta nufi bedroom, tana tambayar samha miye? Cikin kuka samha ta fara gogawa kaka bayani ciken yaren kurame tana cewa,
Hydar, sai ta nuna ma kaka da hannunta tace mata ✌🏻dani ta nuna kanta sannan tace wannan da suka zo tare, ta nuna da hannunta a lamar zowa, taci gaba da cewa mu biyu, biyu zai haɗa ya auremu, kaka tace kai A, a, taci gaba da goga yare, tsoki samha tayi tare da cewa kimin yanda zan gane mana,
Haka kaka ta fita tana ta yare, tsoki samha tayi tare da kwanciya saman gado taci gaba da kuka,
Hydar kuma suna fita, farida tace ranka ya daɗe sai kuma yaushe? Hydar yace idan ina nemanki zanma faruk magana ya turoki, yana faɗin haka ya wuce itama ta tafi inda ta ajiye motarta ta shiga taja tabar gidan,
Yinin ranar nan samha kuka ta yini yi, wannan kuka yasa kan samha ya ansa, lokaci guda taji kanta yana wani irin ciwo kamar zai faɗo ƙasa, daga nan masassara tace salama alaikum,
Koda hydar ya dawo da daddare baiga samha ba, abinci kawai yaci yayi tafiyarshi, dan harya zo yaci abinci itama kaka bata san yazo ba,
Samha kuwa, yaukam haka ta kwana da masassarar ta da ciwon kanta, sai kuka takeyi wai hydar zaiyi aure, da kaka ta shigo ɗakin saidai tayi shiru ta goge hawaye da sauri dan idan kaka ta tambayeta bata san ta yanda zata fara gaya mata ba lamarin ba,
Tun jiya samha taƙi taci abinci tana ɗaki nannaɗe a gado kamar wata misaka, ita kuma kaka bata san samha babu lafiya ba, dan haka huɗɗoɗin gabanta kawai takeyi,
Jin maganar farida a farlo yasa samha ta lallaɓa ta tashi zaune ta jingina jikinta da gado, tunda farida ta gaishe da kaka bata sake magana ba, danma ko tayi kaka bata gane abinda take cewa,
Murmushin ƙarfin hali samha tayi sannan ta sauko daga saman gado ta nufi toilet, wanka tayo tare da wanko bakinta ta fito, tana fitowa tajiyo maganar hydar yana cewa ga kayan yarinyar nan,
Wasu muryoyi da batasan ko su waye ba taji suna ma hydar addu'ar a dawo lafiya, tambayar kanta tayi da ina hydar zaije? Wani irin haushi samha taji ya kamata, dama yau kusan kwana nawa idan hydar yazo ya daina nemanta wannan ai wulaƙanci ne,
Da sauri ta jawo kayanta ta saka, ta fito farlo, tana fitowa abinda idanuwanta suka fara gani akwatinan kayanta da yake ɗauko mata kaya cikinsu a gidanshi, kallon inda kayan suke tayi sosai daga sama ga wayarta nan, tsaki tayi sannan ta mayar da dubanta inda su hydar suke zaune shida da farida suna break,
Daƙel samha ta haɗiye yawun bakinta wanda taji kamar ta haɗiyi kunama saboda tsantsagwaren ɓacin rai, murmushin ƙarfin hali samha tayi sannan ta nufi wurin, tana zuwa taja kujera ta zauna tare da cewa ina kwana, tana gaisuwar ne tana kallon cikin kwayar idon hydar,
Lafiya qalau yace a taƙaice, samha tace banda lafiya, hydar yace Allah ya baki, gyara zama tayi tare da ci gaba da cewa asibiti zaka kaini, baiyi magana ba ya miƙe tare da kwashe tarkacen wayoyinsa, da sauri farida ta miƙe tabi bayan hydar suka fita daga farlon,
Tsaki samha tayi tare cewa can kai ta matse mawa, waini za'a bugarwa zuciya, kwafa tayi tare da tashi ta koma ɗaki,
Tun daga ranar samha bata sake ganin hydar ba, haka farida bata sake zuwa ba, saboda hydar baya nan yayi tafiya, dan haka itama samha huɗɗoɗin gabanta takeyi babu abinda ya dameta, dan babu waya tsakaninta da hydar harya dawo daga tafiya, kuma koda ya dawo bata ganin sa,
Dan haka fitarta takeyi san ranta, tayi tafiyarta biɗinta, idan ta dawo taji kaka tana faɗa da yarenta ma bata bi ta kanta dan bataji abinda take cewa bare tasan faɗa ake mata ko lallashi,
Yauma ta ɗauki uban ƙaton wankanta taci gwalabonta, taci nanaye sosai ta ɗaurayu iya ɗaurayuwa, shahararen wanka tayi na nunawa a filin gasa, ta fito tana tako ɗai ɗaya,
Kaka na ganinta tace ina? Samha tace biki, bikin wata ce zanje, kaka tace A, a, samha tace hakuri zakiyi bazan wani daɗe ba zan dawo, kaka tana magana amma samha tayi gaba tare da cewa yanzun nan zan dawo, tana faɗin haka ta fece daga farlon, da sauri kaka ta tashi tabi samha amma kafin taje har tayi waje,
Dawowa ciki kaka tayi ta ɗauki wayarta ta fara kiran hydar bayan ya ɗauka ta rattafa mishi samha bata zama yanzun kullum yawo yauma bata nan taje biki,
Hydar yace wane biki ne akeyi? Kaka tace itama bata sani ba, tsaki hydar yayi tare da kashe wayar,
Ita kuma samha tana fita napep ta haye tayi gidansu illo, ƙanwarshi ake ma biki ita kuma taje ma illo ƙara, tana zuwa ga motoci nan barjak an ajera dan safarar mutane zuwa wurin farty, dan haka samha ta samu zuƙeƙiyan mota ta shige,
Tana shiga illo yace ta fito ta fara shiga ta gaisa dasu mamanshi, tana ƙoƙarin fitane tace malam don Allah kada fa ka tafi ka barni ga jakana nan da wayana ka ajiye min in dawo na saka layi, mutumi yace okey,
Samha ta fita, tana fita mutumin yana cewa ana waya amma hankalin samha baya wurin saboda hayaniyar mutane, har wayar ta tsinke, ƙara kira hydar yayi saida ya kira da yawa mutumin ya ɗauka tare da cewa dan Allah taɗan shiga ciki idan ta fito zata kiraka,
Hydar yace inane ciki? Yace cikin gida, hydar yace ya akayi wayanta yazo hannunka? Faɗawa hydar yayi, hydar yace wane anguwa ne wurin partyn? Yace basu tafi ba amma yanzun za'a fara tafiya, hydar yace yanzun kuna ta ina ne? Ya faɗa ma hydar inda suke, kashe wayar hydar ba tare daya sake cewa komai ba,
Da sauri hydar ya tashi ya ɗauki makullin motarshi ya nufi unguwar kawu, a ƙofar gidan kawu hydar yayi parking sannan ya fita daga motar, illo na ganinsa ya ruga da gudu yana faɗawa samha yaga hydar,
Samha tace a ina ka ganshi? Yace yana ƙofar gida, da sauri samha ta tashi tace muje, da sauri suka fito ƙofar gida, samha na hango hydar ta tafi wurin shi da sauri, tana zuwa ta fara cewa waye yace ina nan?
Hydar yace ina wayarki take? Samha tace tana moter na bari, hydar yace ina zakije? Samha tace party, jinjina kanshi yayi tare da cewa to muje in kaiki ɗauko jakarki mu tafi,
Da sauri ta nufi wurin motar data baro wayanta a ciki, tana zuwa ta buɗe tare da cewa ɗan uwa na gode sosai ga yayana zai tafi dani, kallonta yayi sannan yace waye yayan naki? Samha tace gashi a can yana jirana,
Yace ke ƙanwar hydar ce? Samha tace Eh, yace amma ba mamanku da baba ɗaya ba ko? Jawo jakarta da wayarta tayi tana cewa Eh, yace to don Allah haɗani dashi zanyi magana dashi naga kamar nasanki ne,
Samha tace kaini baka wani sanni ba, idan zakayi magana dashi kuma harsai na wani haɗaku? Sai kace wata wayar salula gaka gashi ka fito kawai kayi magana dashi,
Tana faɗin haka ta nufi inda hydar yake dan harya kusa isa wurin moter, da sauri ta isa wurinsa tana cewa ga wani can wai zaiyi magana dakai, baiyi mata magana ba ya buɗe moter ya shige, ganin bazaiyi magana ba yasa itama ta haƙura ta buɗe ta shiga tana ci gaba da cewa, yana magana fa, naga kamar munayin kama dashi,
Hydar dai baiyi magana ba yaja motershi ya fara tafiya, samha tace ina ta magana kayi shiru wannan ai babu adalci, dama naga kwanan nan wani neman fitina kayi dani, hydar dai baiyi magana ba, samha taci gaba da cewa nan har rashin lafiya nayi amma baka kaini asibiti ba, saboda kanaso in mutu, ganin hydar bazaiyi magana ba yasa ta daddage taci gaba da aibata farida,
Har tayi ta gama hydar bai ko kalli inda take ba, kallanshi tayi tare da cewa yana ga kanayin hanyar gida? Bayan kasan wurin party zanje? To tunda baza ka kaini wurin partyn ba ka mayar dani gida ni bazanje gidanka ba,
To ka tsaya in fita mana, hydar yace ai zaki iya fita a haka basai na tsaya ba, samha tace wannan wane irin abune? Ya za'ayi in fice daga moter alhalin tana cikin yanayin gudu sosai, so kake inje in faɗi a ƙasa inji ciwo?
Shidai bai sake magana ba har suka isa gida, bayan yayi parking ya fita, ba tare da yayi ma samha magana ba, samha tace sai ka kawoni nan so kakeyi kaka tace na gudu nazo wurinka?
Tace aiko bazan fito ba anan zan kwana, hydar yace to Allah ya baki sa'a, zauniyarta tayi a moter hydar ya wuce ciki abunshi, bayan ya shiga ya kira kaka cewa ya taho da samha gida kada tayi ta jiranta, kaka tace to,
Samha ta daɗe a moter zaune, tun tana zaman marmari harta fara na dole, saidai tayi tsaki ta turo baki, dan tasan da, da ne da yanzun hydar yazo yana lallashinta kilama yanzu ya daina santa, tunda har zai ƙara aure,
Daga wannan tunanin sai kuka, haka samha tayi ta kuka ita ɗaya a moter babu mai bata haƙuri, saida tasha kukanta ta gaji sannan tayi shiru dan kanta, wata zuciya tace ta fita ta shiga ciki wata kuma tace kada kije idan dai har hydar baizo ya tafi dake ba, nuna mishi kema mai zuciyace,
Shi kuma hydar yana gama waya da kaka ɗakinshi ya nufa, yana zuwa yayi wanka yana fitowa ya gama ɗan abinda zaiyi ya haye gado yayi kwanciyarsa,
Wani baƙin ciki ya ƙara turnuƙe zuciyar samha ganin har 10:30pm hydar bai dawo ba, ita kuma ta ɗaukanma ranta yau saidai ta kwana a moter, amma bazata fita ba,
Ganin har 12:04am hydar bai fito ba yasa samha ta ƙara fashewa da kuka saboda tsabar baƙin ciki, ga bacci takeji sosai ta kasa bacci a moter ga karnuka an wani saki sai wani wan wan wan sukeyi, gaba ɗaya sun firgita gidan da kuka, kukan ya hanata ta samu tayi bacci baƙin ciki ya gama ciki zuciyar samha taf, dan haka ta fara kiran wayar kaka,
Saida ta kirata sosai kaka bata ɗauka ba, haka samha tayi ta kiran kaka harsai data farka daga nannauhorn baccin daya daɗe da ɗauketa, cikin muryan bacci kaka ta fara, cikin kuka samha ta fara magana, sai kuka takeyi tana kiran sunan hydar,
Dan bata san ta yanda zata faɗawa kaka hydar ya barta a moter ba, dan haka tayi ta kiran sunan hydar tana kuka, kaka ta kashe waya ta kira hydar, bayan ya ɗauka tace mishi mi yayi ma samha?
Taɓe baki hydar yayi tare da cewa ba komai, kaka tace naji tanayin kuka ne, hydar yace ai samha tayi bacci tun dazu, kaka tace batayi bacci tana kuka, hydar yace to wallahi bai sani ba, kaka tace yaje ya gani, kashe wayan yayi sannan ya tashi ya nufi ɗakin samha,
Bayan yazo ɗakinta gaya bata nan, sai yanzun ya tuno tace zata kwana a moter, tsaki hydar yayi sannan ya sauko ya fito waje, yana fitowa kukan karnuka ya ƙaru,
Sai bin bayan hydar sukeyi suna wan wan wannnn, harya isa wurin moter, samha ganin hydar yasa ta ƙara fashewa da kuka,
Buɗe motar yayi tare da cewa fito, da sauri samha ta fito tana ci gaba da kuka, rufe moter yayi bayan ta fito, yace muje samha tayi tsaye tana turo baki,
Kallonta yayi tare da cewa kada ki sake kiran wani daga yau kina faɗa mashi wani abu tsakani na dake, samha tace ummm ummm tana turo baki gunguni kenan,
Hydar yace ni kike ma rashin kunya ko? To kiyi idan na gaji zansa karnukan nan su cinye minke kowa ma ya huta, gyara bakinta tayi ba tare da tayi magana ba, miƙa mata hannunshi yayi alamar ta taho, itama miƙa hannunta tayi hydar ya riƙe hannun tare da jawota jikinsa a hankali ya rungumeta, wata irin wahalalliyar ajiyar zuciya samha ta sauke mai ɗauke lunfashi na wani lokaci, da sauri ta ƙara kwanciya a jikin hydar sosai,
Hydar yace kiyi hakuri ina tunanin kin taho bansan kina nan ba, cikin kuka samha tace ai kasan ka barni a moter kayi tafiyarka tunda ka daina so na yanzu, hydar yace waye yace miki? Ai san da nake miki har abada bazai goge a zuciyata ba, dake zuciyata ta fara kuma dake zata rufe insha Allah, samha tace ba wani gashi zakayi aure,
Murmushi hydar yayi sannan ya ɗago samha daga jikinshi, ɗago mata fuskarta yayi tana kallon idonshi, ɗan buɗe idanuwanshi yayi sannan ya lumshesu a hankali tare da kashe ido ɗaya, bai bata amsa ba ya dafa kafaɗarta suka fara tafiya,
Samha taci gaba da cewa wai da gaske aure zakayi? Hydar yace umm, samha tace ni ka daina sona ne? Hydar yace A, a, samha tace itama kana santa? Hydar yayi shiru, samha tace bazakaji wani iri ba mata biyu? Nan ma shiru yayi,
Itama bata sake magana ba har suka shiga, saida yakaita ɗaki ya kwantar da ita a gado sannan yace saida safe, zai wuce samha ta riƙe mishi "yan yatsu, juyowa hydar yayi ya kalleta amma baiyi magana ba, cikin shashshekar kuka samha tace sanyi nakeji, idanuwa hydar ya zaro tare da cewa sanyi kuma samha? Ɓata fuska tayi kamar zata ƙarayin kuka sannan tace Ey, dogon kallo hydar yayi ma samha sosai, sannan ta cire hannunshi daga jikin nata,
Matsawa yayi jikin wedrof ya buɗe ya ɗauko ƙaton bargo yazo ya lulleɓeta, bayan ya lulluɓeta zai tafi ta sake riƙe hannunsa, kallonta hydar yayi sannan yace miye? Samha tace na gode, murmushi yayi ba tare da yayi magana ba ya zame hannushi yayi tafiyarsa,
Ajiyar zuciya samha tayi tare da gyara kwanciyarta ta fara bacci,
Don Allah kuyi haƙuri da wannan, bana zaune ne abubuwa sunsha min kai da yawa da yawa, jiya kuma naji ƙorafinku wasu na cewa ina musu short typing, kuyi hakuri nafiku so inyi da yawa dan na ƙosa labarin ya ƙare haka nan,
Ajiyan zuciya samha tayi tare da gyara kwanciyanta ta fara bacci,
A gajiye hydar ya isa ɗakinshi zuciyanshi cike da tunani barkatai, murmushi yayi da gefen bakinsa a daidai lokacin da yake zama a gefen gado,
Ayijan zuciya yayi tare da tambayan kanshi miye yasa samha tace mishi tanajin sanyi? A hankali ya kwanta saman gado tare da rufe idanuwansa, hoton samha ya dawo mishi akai, tare da tuno maganarta,
_Sanyi nakeji_
Murmushi hydar yayi tare da sauki ajiyan zuciya, lallai wani abu yana faru, mi samha take nufi da hakan?
Tunani sosai hydar yayi daga baya ya tashi ya nufi toilet ya ɗauro alwallah bayan ya fito ya fara sallah kamar yanda ya saba,
Samha kuwa bancinta tasha abunta hankalinta kwance kamar tahau jirgi mai ya ƙare,
Da safe bayan hydar ya dawo daga masallaci bai shiga ɗakin samha ba wucewa yayi ɗakinsa abinsa,
Ita kuma bayan tayi sallah asuba, komawa tayi bacci bata farka ba sai wurin 9:55am, toilet ta shiga tayi wanka bayan ta fito taci gayenta sosai, ta saka kaya masu kyau sannan ta fito dan zuwa ɗakin hydar,
Tunda samha ta fito ɗakinta takeji magana ƙasa ƙasa, kuma muryan mace takeji,
Da saurinta tayo ribos kamar wata urban tayo ƙasa, tunda ta sauko ta hango farida sai wani yashe baki takeyi tana dariya, tana ma hydar magana,
Shi kuma ya ɗan duƙar da kanshi yana kallon waya, gaba ɗaya hankalinsa yana kan wayarshi sai wani shashshafata yakeyi ya riƙeta a mutunce da hannuwansa biyu,
Samha bata gama saukowa ba, ta tsaya saman step ɗin ta dafa ƙarfen benen tare da cewa hydar ina magana,
Ba tare daya ɗago kansa ba daga kallon wayar yaɗan taɓe bakinsa tare da cewa zo nan mana kiyi magana dani,
Samha tace ba zanzo anan ba nace kawai kazo, murmushi hydar yayi ba tare da yayi magana ba ko ya kalli inda samha take ba,
Zama tayi a wurin tana ci gaba da cewa hydar an ɗaura aurenka da farida ko kuwa? Yace wani abu? Samha tace kawai na tambayeka ne,
Hydar yace ba'a ɗaura ba, samha tace to gaskiya daga yau sai yau kada farida ta sake zuwa gidan nan, hydar yace dalili?
Samha tace dalili kake so kaji kenan ko? Baiyi magana ba, sai farida dake ta dariya irin mai cin rai ɗin nan,
Tsoki samha tayi amma bata sake magana ba, shima hydar baiyi magana ba, yana dai ta dandanna wayarsa, ita kuma farida tashi tayi ta nufi kching,
Samha taci gaba da gunguni tare da tutturo baki tana harar hydar, shidai baiyi mata magana ba,
Tana nan zaune har farida ta fito daga kching da flet a hannunta tana ta ƙara faɗaɗa murmushinta, ta nufi inda hydar yake zaune ta ajiye a gabanshi cikin girmamawa, da sauri samha ta sauko da gudu ta iso kusa da hydar tare da ɗaukar indomie ɗin ta zubar ƙasa,
Kallonta hydar yayi amma baiyi magana ba, lokaci mai tsayi yana kallonta ba tare da yace komai ba, farida ce tace samha miye kikayi haka?
Samha tace da Allah rufewa mutane banzan bakinki, ina ruwanki? Dani da mijina nake ko kinga tunda na fito na miki magana ne? Murmushi farida tayi tare da duƙawa inda samha ta zubar da abinci ta fara kwashewa,
Hydar yace ma farida kada ki kwashe shi itace zata kwashe kuma saita cinyeshi, samha tace Allah ya sawaƙe inci abinci ƙasa kamar wata jaka,
Hydar yace babu abinda ya dameni kinji dai abinda nace miki, tsoki samha tayi sannan ta nufi inda take zaune a ɗazu ta sake zama, hydar yace ke zo nan, duƙar da kanta tayi ƙasa tare da turo bakinta amma batayi magana ba,
Hydar yace idan na sake miki magana zakisan na miki magana kin min shiru, tashi samha tayi da gudu ta nufi ɗaki tana gunguni, murmushi hydar yayi a ransa tare da bin bayan samha da kallo harya daina hangota,
Ita kuwa farida yinin ranar nan itace ta gyara ko ina a gidan nan ta share ta goge fess, ta dafa abinci saida ta tabbatar ta kammala komai sannan tayi ma hydar saida safe itama ta tafi gida,
Farida bata dade da tafiya ba shima hydar yabar gidan,
Ita kuwa samha tana shiga ɗaki a gefen gado tayi ma kanta masauki, tana zama ta fara dogon nazari wanda ba niba ko ita kanta bata san dalilin yinsa ba,
Tsoki samha tayi a bayyane tare da cewa wallahi idan har hydar ya sake kawo da wannan banzar bazarar kaza matatta a bola bazata yadda ba, idan kuwa yayi taurin ka to lallai saidai a raba ko ina na gidan kowa ya tsaya sashen sa,
Saida ta gama nazarin yanda zata bullo ma lamarin, sannan tayi dariya dan tasan dan hydar ya ɓata mata rai yake kawo farida a gidan nan, dan haka itama tunda tasan baya san mage a rayuwarsa lallai itama saita sa yau an samo mata mage, ta yadda kowa ya ci gaba da ɓatawa kowa rai,
Dariya samha tayi a daidai lokacin da take saukowa daga saman gado, da sauri ta fita daga ɗakinta ta nufi ɗakin hydar,
A inda hydar yake ajiye kuɗi ta ɗauko, sannan ta sauko ƙasa, tana saukowa ta fara kiran wayan illo, bayan ya ɗauka tace mishi don Allah illo magenka zaka bani haya, ni kuma zan baka kuɗi mai yawa,
Illo yace baki da damuwa, zan kawo miki, samha tace yawwa, kuma kafin kazo kaje kasuwa don Allah ka siyo min jan yadi amma a yankamin shi ayi min tsawo dashi sosai, sai a min zikzza, idan kazo duka zan baka kuɗinka, illo yace to baki da damuwa saina zo, samha tace yawwa idan kazo kamin waya, yace to sannan ya kashe wayarshi,
Cikin farin ciki samha ta koma ɗakinta tana zuwa a gaggauce tayi wanka bayan ta fito sallah tayi, bayan ta gama ta shirya fess saida ta gama shirinta tsaf sannan ta ɗauki wayanta ta fara kiran illo,
Bayan ya ɗauka yace mata ya kusa isowa yanzun nan, samha tace yawwa zan jiraka a waje kafin kazo, illo yace to,
Tana gama wayan ta saka hijabinta, ta fito dan tafiya wurin illo, a bakin ƙofar farlo suka haɗe da hydar shi zai shiga ita kuma zata fita, da ɗan sauri ya raɓe ya bata hanya, ba tare daya tambayeta ina zataje ba,
Tana fita Alale ya taso da sauri tare da cewa ranki ya dade ina zakije ne? Samha tace zan anso saƙo a waje, Alale yace bara in anso miki, murmushi samha tayi tare da cewa na gode, tana faɗin haka tayi gaba abinta,
Da sauri samha take tafiya haɗi da ɗan gudu gudu, saboda akwai nisa sosai kafin ta isa inda illo yake, kafin taje har illo yazo yana jiran isowarta,
Tana isa ta bawa illo kuɗin shi kuma ya bata mage a cikin kwali sai yadin data sa ya siyo mata an mishi wiyving, godiya illo yayi sannan yayi tafiyarsa, ita kuma samha tayo ciki da magenta,
Da saurinta ta shiga farlo hydar yana zaune yana cin abinci, da sallama ta shiga farlon hydar ya ansa dakel, samha ta ajiye kwalin magenta saman kujera, sannan ta nufi sama da kyallen yadinta,
Daga jikin ƙafen bene ta fara ɗaurawa, sannan ta jawoshi ta sauko ƙasa tana janshi, saida tazo daidai saitin hydar ta fara cewa ai gara a raba farlon nan kowa yasan wurinsa, idan mutum yayi da jan baki ace saiya goge,
To yanzun nayi da ƙalle danni bana zama sashe ɗaya da kishiya, haka tayi ta jan ƙallen har kching sannan ta ɗaure a jikin window bayan ta ɗaure ta fito,
Inda ta ajiye kwalin magenta ta ɗauka sannan ta zauna a saman kujera bayan ta zauna ta ɗauki kwalin ta ɗora a saman cinyarta, tana hango hydar an wani raba iyaka kamar tsakanin nigeria da niger,
Buɗe kwalin tayi tare da fiddo kirceciyar magen sai kuka take irin na gahurtaccin maguna miyau miyau miyauuuu, da sauri hydar ya ɗauke ƙafarshi daga ƙasa ya ɗorata saman dirning dan duk duniya babu abinda ya tsana irin yaji mage tana shafar mishi jiki,
Ɗaga magen samha tayi sama kamar tana ma jinjiri wasa, ta fara cewa kashedinki kada ki kuskura kije inda bance ba, kuma kada ki sake kibi kowa a gidan nan sai ni, kuma kada ki kuskura ki tsallaka can ta nuna inda hydar yake zaune, sannan taci gaba da cewa anja burtali { iyaka } kowa zai tsaya a wurinsa kada ki kuskura kije ki jawo min fitina, danni ban iya ɗauko samari ba,
Murmushi hydar yayi amma bai kalli samha ba, yaci gaba da cin abincisa, sake magen samha tayi ita kuma ta sauka ta zauna ƙasa saman kafet, tana ƙara ma magen kashedi wai kada taje wurin hydar ta jawo mata fitina,
Tana nan zaune a ƙasa da magen tazo zata tsallaka iyaka sai ta jawota, tace kiyi zamanki anan, dan gidan babu lafiya faɗa masu gidan sukeyi, munayin gaba dani da mai gida kowa babu mai ma kowa magana, sai ƙoƙari kowa yake yaga ya ɓatawa ɗan uwansa rai, nidai kam ina san zaman lafiya shi yasa na kawoki mu riƙayin fira tare shidai hydar budurwarsa tana zuwa masa fira kullum safiya sannan tana girka masa abinci,
Kema bara in kawo miki madara kisha kada yunwa ta kamaki, ni dan ni na ajiyeki bana so Allah ya kamani da laifin na horaki da yunwa, wani kuma ai cikinsa kawai ya sani tun safiya yakecin abinci har yanzun bai ƙoshi shi ba, ni kuma banci abinci ba duk yau ɗin nan,
Haka nan nake ta hakuri, a daidai lokacin data shiga kicin da magen a hannunta, ta haɗo mata madara a flet, sanna ta dawo farlo ta ajiye mata mage kuwa tayi ta lallashewa,
Hydar yace samha wai a ina zaki ajiye mage ne? Ba tare da samha ta kalli hydar ba, hankalinta yana kan magenta tana shafa ta tace anan mana, ai shine dalilin daya sa na raba ko ina na gidan nan magena zatayi rayuwarta cikin jin daɗi da "yan ci,
Cikin tsananin fushi hydar yace wallahi bazai yuwu ba, nine zaki zo ki ajiye mage a tare dani? Dani da mage zamuyi rayuwa a gida ɗaya? Tun wuri ma ki mayar da ita inda kika ɗaukota idan ba haka ba wallahi zan tillata karnuka su cinyeta na faɗa miki, itama samha ciki fushi ta miƙe tsaye da magenta rungume a jikinta tace tunda kake zuwa da budurwarka ni na taɓa cewa zansa kare ya cinyeta? Hydar yace wannan ai haukane!
Kin taɓa gani kare yaci mutum ne? Samha tace ashe kuwa kare bazaici mage ba, kwafa hydar yayi tare da cewa kisan mafita dake da magennan kafin inyo wanka in dawo,
Samha tace wallahi bazataje ko ina ba sai wannan jakar ta daina zuwa gidan idan kuwa ba haka ba ni zan riƙa cinna maka magen saika suma, tana magana tana shafa magen, hydar yace wallahi zan miki duka na faɗa miki, samha tace ai dama ka saba, yau kuma sai ka dakeni saboda mace, tana maganar tana murguɗa mishi baki,
Tsoki hydar yayi sannan yayi gaba ba tare daya sake magana ba, samha kuwa sakin magen tayi tare da cewa sauka kije kiyi wasanki tunda kema ɗiyar masu gidan nan ce, tana sakin magen da gudu tayi sama, da sauri hydar ya raɓe gefe ɗaya tare da cewa samha bana san haka wallahi idan har magen nan ta taɓa min jikina wallahi kema yau sai kinji hydar a jiknki zo ki kamata, zama samha tayi saman kujera tare da cewa zo nan ka faɗamin, wato abinda yace mata kenan a lokacin data kirashi yana tare da farida,
Wayarshi ya ciro daga aljihu ya fara kiran shamsu, bayan ya ɗauka yace yazo ya fitar da mage ta shigo mishi bayaso ta taɓa mishi jiki, samha tana jin yace azo a fitar da mage da sauri ta tashi taje ta kama magenta ta shige ɗaki abinta,
Kwafa hydar yayi sannan ya wuce ɗakinsa, ita kuma samha tana shiga ɗaki ta kulle sannan ta saki magen tayi ta shawagi a tsakar ɗaki, ita kuma ta haye gado tayi kwanciyarta,
Hydar saida ya dawo sallah isha'i sannan ya kira samha a waya tazo taci abinchi dan duk yau bataci komai ba, amma sai tace ta ƙoshi, haka nan hydar ya gama zaman sa shima ya tashi ya nufi ɗakinsa dan hutama rayuwarsa,
Samha kuwa tunda ta gama sallah asuba ta fito, ta gyara daidai wurinta ta goge tass ta shiga kicin ta haɗa abinda zatayi kalaci, daidai nata, bayan ta gama ta koma ɗaki dan wanko bakinta tayi kalaci,
Hydar dake zaune yana karatun Qur'ani yaga samha ta wuce, rufe Qur'anin yayi ya ajiye, tashi yayi ya nufi kicin ɗin, baya fa kalaci irin wannan lokacin amma dan ya ɓatawa samha rai tunda yasan itama dan ta kwana da yunwa tayi sauko zatayi kalaci, yana shiga kicin ɗin ya kalli agogon dake maƙale a jikin bangon kicin ɗin, 7:09am, hmmm hydar yace tare ɗauko abinda samha ta haɗa dan kalaci ya dawo farlo,
Ya nufi wurin tebirin cin abinci, anan hydar ya bige aiki ya lashe kaf abinda samha ta haɗa don kalaci, ga mage kuma yasa an fitar da ita, tunda ya dawo daga masallaci yaga samha tana shara a farlo ya fita ta baya yasa shamsu yazo ya fitar da banzar magen,
Ita kuwa samha tana zuwa ɗaki wanka ta shiga, bayan ta fito mai da powder sai kwalli ta shafa ba wani kwalliya tayi ba, tana gamawa ta saka kayanta bayan ta gama ta fara kiran magenta, amma shiru kake ji,
Ganin mage bazata fito ba, yasa ta hakura ta sauko saboda yunwa takeji sosai, bata ko kalli inda hydar yake ba tayi kicin da saurinta, tana shiga a sikwane ta isa wurin data ajiye kalacinta, tana taɓa flet ɗin data zuba dankali a ciki taji ba kamar yanda ta ajiye ba, da sauri ta ɗauke na saman dan ta gani ba komai a ciki,
Idanuwa samha ta zaro tare da ɗaga flet ɗin ta saddashi ƙasa, a daidai lokacin da hydar ya shigo kicin ɗin da sallama, ba tare da samha ta ansa sallama ba tace waye ya cinye min dankali na? Bayan yunwa nakeji wannan ai ɗaukar alhakine, kuma kaine ma kaci min abuna, hydar yace to ai nima yunwa nakeji,
Hawaye ya gangaro daga idon samha saboda ɓacin rai dan yunwa takeji ta kirki dan jikinta har kyarma yake saboda yunwa, dariya hydar yayi sosai tare da cewa saboda na cinye dankali kike kuka? Ya ƙarasa maganar yana ƙara kyalkyalwa da dariya,
A zuciye samha tayi hanyar fita, da sauri hydar ya riƙota tare da cewa zakisha tea ai ko? Har yanzun samha kuka takeyi, amma batayi magana ba, hydar yace ai laifinki ne, kinsan ni ba rodi bane dole ne zanji yunwa, sai ki wani kama kice ke ɗaya kawai zakiji daɗi an taɓa haka ne?
Cikin shashshekar kuka samha tace ai saikaci ka ragemin, hydar yace ba kinsan mu biyune zaune a gidan nan ba, kawai ina zato nawane ni kuma na wane cinye duka ai bansan banda ni ba,
Hydar yace swry bara in sauri in haɗa miki tea kiɗan fara nuna masa hanya, samha tace ni bazansha tea ba ta ƙarasa maganar tana goge hawayen idonta, murmushi hydar yayi tare da cewa don Allah bakiji kunya ba kina kuka saboda yunwa? Gyara bakinta tayi amma batace komai ba,
Dariya hydar ya sakeyi tare da cewa kinga yanda kike yi? Lallai yunwa tana aiki a wurin nan, juyo samha yayi bayanta ya koma saman jikinsa ita ta bawa hydar baya tana riƙe a jikinsa shi kuma ya ɗora kansa saman ƙafaɗarta hannunsa yana saman cikinta yana shafawa, murmushi yayi tare da cewa bara in ɗauko miki hoton bakinki kiga yanda yayi dan baici dankali ba, wayarta dake ajiye a gefe hydar ya ɗauka sannan ya juyowata tana kallonshi, daidai bakin samha ya ɗauka hoto, da hydar ya nuna ma samha taso tayi dariya yanda taga bakinta amma saita basar, kallon hoton hydar yayi tare da cewa shantu kenan samha don Allah kalli bakinki kamar yaji duka, ya karasa maganar yana dariya mai cin rai,
Saida ya gama dariyarsa sannan ya saki samha daga jikinsa yana cewa bara in dafa miki indomie, samha dai bata sake magana ba ta jingina da bango sai gunguni takeyi,
Harya gama samha bata sake magana ba, dan gaba ɗaya haushi takeji rabonta da abinci tun daren shekaran jiya, dan jiya babu abinda taci, bayan hydar ya gama ya juye a flet ya ɗauka sannan yaja hannun samha suka fito farlo,
Da kanshi yake bata tana ci yana dariya a ranshi dan yasan ya more mata sosai, saida ta gama sannan yace to ki tashi wannan abun da kika ɗaura ki cireshi kinga yanzun an fara zaman lafiya mun daina faɗa daga yau, farida bazata sake zuwa ba, tunda kina sona ko?
Samha tace kaine kaje ka ɗaukar ma mutane mage ko? Taɓe baki hydar yayi tare da cewa haba badai hydar ba, ni kam mi zai haɗani in ɗauka mage ina da hankalina, samha tace nima da hankalina tunda har yanzun ban fara dukan kowa ba, murmushi hydar yayi yana kallon samha ba tare da yace komai ba,
Tashi samha tayi ta nufi kicin ta fara kwanto kyallen data ɗaura, bayan ta fito daga kicin ta haura sama ta kwanto daga inda ta ɗaura, ta tattara kyallen ta kawo ma hydar tare da cewa na kwance gashi,
Hydar yace ta zauna, zama tayi babu gardama, hydar yace don Allah samha ki daina abinda kike, wallahi banajin daɗi inga kina abinda zai ɓatamin rai, yanzun dan na faɗa miki bana san mage ta shafamin jiki shine zakije ki samo mage? Wato idan ma zan mutu babu abinda ya dameki ko? Samha ni nasan baki so na kuma bana tunanin zaki soni kamar yanda nake sanki, nidai nasan sanki ya ginu a cikin zuciyata bana tunanin zan daina sanki, ina sanki ina kaunarki kuma inajinki sosai a zuciyata samha har ƙarshen lumfashina babu ranar da zan daina sanki a zuciyata,
Kuma duk abinda nasan bakya so bana miki, dan bana san kiji wani iri a zuciyarki, to ko bakya so na, don Allah duk abinda kikasan zaki min wanda zaisa inji banajin daɗi a raina kiyi hakuri ki daina kinji ko? Cikin sanyin jiki samha tace tom, ajiyar zuciya hydar yayi sannan yace bara inyi wanka fita zamuyi ki canja kaya, samha tace tom,
Tashi hydar yayi ya nufi ɗakinsa, itama tashi tayi ta nufi nata, tana shiga babu wani ɓata lokaci ta canja kaya, ta ƙara gyara fuskarta bayan ta gama ta nufi ɗakin hydar, shi kuma adaidai lokacin ya fito daga wanka, zama tayi a gefen gado sannan tace wai don Allah ya kakeyi kazo a matsayin sahib wurina? Kallonta hydar yayi amma baiyi magana ba, kuma har yanzun idonshi yana kanta yana mata wani irin kallo mai nunu da nazari yakeyi,
Ɗan taɓe baki hydar yayi ba tare da yace ma samha komai ba, harya gama shirinsa ya saka kayansa bai ƙara kallon inda samha take ba bare kuma tayi tunanin zaice mata wani abu ba,
Bayan ya gama yace ma samha muje yana faɗin haka yayi gaba, samha tace to ai ka jirani dai ko? Juyowa yayi tare da cewa na jiraki, ɗaukar gyalenta tayi da jakarta dama takalminta yana ƙafarta tashi tayi tabi hydar saida suka sauko ƙasa sannan ta yafa gyalenta,
Hydar yana gaba yana waya ita kuma tana bin bayansa, har suka isa wurin motoci, Alale ne ya buɗe hydar ya shiga sannan samha ta shiga ya rufe, Alale ne yaja moter da hydar da samha suke ciki, sannan sauran motocin suka bi bayansu,
Bayan ya gama wayarne kuma kiran wayar kaka ya shigo a cikin wayarsa, samha jin sun fara yaren da bataji yasa tayi tsoki, da wutsiyar ido hydar ya kalleta a ranshi kuma murmushi yayi, sun daɗe suna waya da kaka sannan hydar ya miƙawa samha waya ansa samha tayi ba tare da tace komai ba ta kara wayar a kunneta, murmushi hydar yayi tare da jawo samha a jikinsa,
Kallon hydar tayi tare da ɗaga mata gira, hannusa yakai dan tayata riƙe wayar, samha tace ina kwana, kaka tace lafiya lo, samha tace ya gida ya kuke? Kaka tace lafiya lo, daga haka samha ta miƙawa hydar wayar,
Shima baice wani abu ba, ya kashe wayarsa, har suka iso inda zasuje babu wanda ya sake magana tsakanin hydar da samha, amma har a lokacin tana kwance a jikinsa,
Bayan anyi parking samha ta tashi daga jikin hydar, shamsu ya buɗewa hydar moter, fita hydar yayi amma samha bata fita ba, tunda bai bata izinin fitowa ba,
Samha tana zaune a moter ta jingina kanta da murfin moter tana nazarin rayuwa, hydar yaɗan daɗe sosai sannan ya dawo yace ma samha ta fito, fita samha tayi ba tare da tayi magana ba,
Tsayuwa hydar yayi har ta iso kusa dashi tace nan ɗin ina ne? Hydar yace gidan ahalinki ne, nan gidan yayun dadynki ne, kuma dukansu suna nan sun haɗu a ciki kowa yana san ganinki,
Rungume hydar samha tayi idonta yana fitar da hawayen farin ciki, cikin muryar da bazaka iya tantancewa kukane ko farin ciki samha tace hada dadyna shima? Ɗan lumshe ido hydar yayi ba tare daya ce wani abu ba,
Jin hydar baiyi magana ba yasa samha tace uhum? Hydar yace kedai kawai muje, tare suka jera har ciki,
A tsakar gida suke zaune, gasu nan sun jera layi ringiss sai kace an musu gorin yawa, da matansu da "ya"yansu, kowa yana cikin farin ciki, hydar kuwa a ranshi cewa yayi lallai mutanen nan basu da kunya, wato yau sunga samha kowa yana ƙoƙarin tasan su mutanen kirki ne, bayan nan nazo neman aurenta babu wanda yace ina samha har aka ɗaura aurena da ita, yana wannan tunanin ne yaji ana cewa ranka ya dade ku zauna mana,
Murmushin ƙarfin hali hydar yayi sannan ya ɗan duƙa dan cire takalmin ƙafarsa, bayan ya cire yaja hannun samha suka hau saman tabarmar sannan suka zauna,
Bayan sun zauna gaishe gaishe ya fara, bayan an gama gaisuwa ne, suka ma samha Allah yasa alkairi tare da musu addu'ar zaman lafiya, hydar ne kaɗai yace amin amma samha kanta yana ƙasa,
Hydar yace to wannan itace samha gata nan na kawo kamar yanda nace zan kawota a gaban kawu, hydar yana faɗin haka ya mike tsaye tare cewa samha ina meeting anjima zan dawo in ɗaukeki,
Ƙanin dadyn samha yace A, a, ka barta ta kwana biyu mana dan wanda basu santa ba, su ganta, murmushi hydar yayi tare da cewa A, a, zanci gaba da dawo da ita kullum kullum amma gaskiya bazata kwana ba,
Matarsa ce tace don Allah kayi haƙuri ka barta kwana biyu ne fa kawai, kallonta hydar yayi tare dayin murmushi da gefen bakinsa, dogon kallo yayi mata sosai wanda yasa ta sunkuyar da kanta ƙasa,
Samha tace ka barni zan kwana bayan kwana biyu saika dawo, kallonta hydar yayi tare da cewa tom, zan dawo anjima in kawo miki kayanki, murmushi samha tayi tare da cewa saika dawo,
Tashi sukayi danyi ma hydar rakiya, amma banda samha, yayu da ƙannen dady suka tafi danyi mishi rakiya, wata "yar masakaiciyar jaka taf da kuɗi hydar yace shamsu yakai a ciki, wani yayan baban samha ne yace kai kawo nan shamsu ya miƙa mishi,
Suna tsaye har motocin hydar suka ɓace daga wurin, sannan sukayo gida, bayan sun dawo gida kowa ya manta da lamarin samha suka shiga kiciniyar rabon kuɗi,
Wurin rabon kuɗi harsai da akayi faɗa, duk samha tana kallonsu sai masifa sukeyi sosai saboda tsabar san abun duniya kowa ya manta da kowa ɗan uwansa ne,
Saida suka gama rabon kuɗinsu suka dawo takan samha, dan haka suka shiga rattafawa samha surutu, tare nuna mata lallai tayi babban sa'a a rayuwa data kasance mata a wurin hydar,
Haka sukayi ta nunawa samha girma irin na hydar a ƙasar nan, da nuna mata girma da yawa irin na kuɗinsa, ita samha kallon mahaukata take musu lallai da a wurinsu ta rayu haƙiƙa dasai rayuwata tafi shiga garari akan ta wurin kawu, dan tunda ta haɗu da hydar a matsayin sahib ya hanata sace sace, saida ta auri hydar sahib kuma yace tayi satawa hydar ashe dan ya auna ta yaga ta daina ko bata daina ba,
Anan suka faɗawa samha an kashe babanta da kisan da akayi ma mahaifiyarta da hukuncin da hydar yasa akayi musu, bayan sun gama rattafa ɗiminsu akace samha ta shiga ciki ta huta, jiki a sanyaye samha ta tashi ta nufi ɗakin wata matar ɗan yayan dadynta, tana shiga a saman gado ta kwanta, zuciyarta tana mata babu daɗi,
Hydar kuwa tunda ya tafi yakejin baƙin ciki a ransa danji yake kamar samha bazata dawo ba, harya gama meeting ransa baya masa daɗi, yinin ranar nan duk wanda yaga hydar yasan akwai abinda yake damunsa, bai koma gidansa ba gidan kaka ya wuce dan baiji yana iya zama gidan ba,
A bedroom ɗin kaka ya shige yayi kwanciyarsa saman gado, saida ya kwanta sannan ya fara kiran wayan samha, saida ya kira ta sau biyu sannan ta ɗauka, tana ɗauka hydar yace ina kika ajiye wayar ne? Samha tace bacci nakeyi ne, hydar yace da kyau wato har kina iya bacci bana kusa dake ko?
Samha tayi shiru, hydar yace zanzo anjima da misalin 10:30pm samha tace ai dare yayi a lokacin sosai hydar yace a lokacin nakejin zan iya zuwa, sai nazo, samha zatayi magana ya kashe wayanshi,
Tsoki samha tayi tare da cewa ai sai kaje kayi ta kashewa, Rabi matar ɗanɗan yayan dady tace samha keda wa? Ɗan gajeran tsaki samha tayi tare cewa wai hydar zaizo da ƙarfe 10:30 na dare, Rabi tace sai kiyi masa tsaki? Sai kice Allah ya kawoshi lafiya ko, kam lallai da kinsan yanda samha take ma hydar ashe dasai kinci uwata,
Rabi taci gaba da cewa ke bakisan duk wani kalami da baya da kyau ba'a faɗawa mijishi ba? Mijinki sa'ar wasanki ne? Samha tayi shiru, rabi tace amma ai kinsan hydar ba yaro bane da zaki riƙa mishi rashin kunya idan kina gyarawa ki gyara idan har kina san gamawa lafiya, nan dai tayi ta ma samha faɗa, samha tayi shiru,
Rabi tace Allah ya rufa miki asiri amma bazaki gode mishi ba, ki tarairayi mijinki ki zauna lafiya A, a, sai hauka sai shirme da kumu ƙuruciya dake mike hauka a cikin kwalwar kanki, saida tayi ma samha fess sannan ta fita daga ɗakin,
Samha kuwa tana nan kwance tana tunani daban daban a ranta, Rabi ce ta shigo ɗakin tare da cewa tashi kije kiyi wanka ga ruwa nakai miki a bayi, ba tare da samha tace komai ba ta sauko daga saman gado tabi bayan rabi takaita har toilet, tunda suka fito sauran matan gidan suke zinɗe wai ga ɗiyar karuwa can ta kama samha zata koya mata kwartanci, gidan babban gida ne, ɗakuna kashi kashi kamar ɗakunan makarantar boding, haka sukayi ta zagin Rabi wai karuwa ɗiyar karuwa, saboda karuwanci irin nata yasa bata zama da kishiya duk wanda ta shigo sai ta tafi saboda ta gama da mijinta, tou pha Allah ya sawaƙe,
_Wai da anga mace da miji suna zaman lafiya sai ace ta gama dashi, duk macen da ake ganin ta gama da namiji haƙika yana jin daɗinta, tana kyautata mishi tana mishi biyayya tana da haƙuri kuma tana da kauda kai, duk wanda yayi ma mijinsa biyayya ya zama mai haƙuri duk zafin ransa saiya ɗaga ma matarsa ƙafa saiya rage wani abun, duk tijarar namiji duk wulaƙancinsa idan kikaci maganin zama dashi sai ki zauna lafiya,_
Tou pha, bara muji wane irin karatu rabi zatayi ma samha,
A toilet kuwa Rabi ta nunawa samha wani rober ruwa daban idan ta gama wanka zatayi amfani dashi, sannan kuma wani daban shine zatayi wanka dashi a halin yanzu, tana gama nunawa samha ta fito dan lokacin zuwan hydar ya kusa,
Saida samha ta gama wankan soso da sabulu sannan ta jawo wanda Rabi tace zatayi amfani dashi daga baya, tunda samha ta saka hannunta a bokatin taji ruwan da banbanci da wanda tayi wankan farko dashi, ruwan wani irin sirrin taccen ƙamshi yakeyi mai daɗi da burgewa,
Har samha ta gama ta fito Rabi tana tsaye a wurin, da wani kasko a hannunta samha tana fitowa ta zuwa turaren jiki a ciki tace ma samha anshi koma daga ciki ki turara jikinki,
Bayan samha ta fito Rabi tace muje, a ɗaki bayan sunje samha ta shirya, Rabi ta bata kaya ta saka, saida hydar yayo waya yazo sannan Rabi ta sake turare samha da wani turaren mai ƙamshi gaske,
Sannan ta ɗauko turaruka masu daɗin ƙamshi ta bawa samha ta feshe jikinta dashi sosai, tayi ma samha fatan dawowa lafiya, itadai samha ba dan ranta yaso ba, tunda ta fito taga shamsu tsaye, gasheta yayi ta ansa cikin kulawa sannan ta wuce,
Wurin moter ta nufa tunda hydar ya hangota ya buɗe moter tare da fiddo ƙarfarsa ɗaya har samha ta iso yana kallonta, tana isowa tayi wani ƙerere da ita kamar abun tsiya,
Murmushi hydar yayi tare da cewa inayini, samha tace lafiya qalau, murmushi hydar ya sakeyi tare da jawo hannun samha ya shigar da ita cikin motar,
Raba ƙafafuwansa yayi ya zaunar da samha a tsakiya, rungumeta yayi tare da ɗora kansa saman ƙafaɗarta, kama hannuwanta yayi ya shigar da "yan yatsunta cikin junansu sannan ya ɗaga hannun ta zuwa wurin wuyansa, yace riƙeni kada ki saki, da hannunsa ya ɗago kanta tana kallon fuskar sa, shima duƙar da fuskarshi yayi daidai tata, sannan yace a ina kika samo kamshi haka? Samha ta rumtse bakinta, sannunsa yasa ya kama leɓonta na sama dana ƙasa ya buɗe bakin sannan ya matsa da bakinsa daidai nata ya saka harshensa a ciki yana wasa dashi, tare daci gaba cewa bakiji ina magana ba?
Samha tayi shiru, cire hannunsa yayi daga riƙe lips nata da yayi, ya riƙo haɓarta da hannu ɗaya sosai yana mata wani irin salo mai wahalar fassarawa a bakinta,
Ɗayan hannunsa kuma yana cikin rigarta yaƙi ya ajiyesa wuri ɗaya ɗaya, ringing ɗin da wayan samha takeyi yasa hydar ya saketa, kafin ma ta ɗauka wayar ya tsinke, ƙara riƙota yayi tare da kwantota a jikinsa, leɓonta na ƙasa ya kama da yatsunsa ya buɗe sannan ya ɗan lasa da harshensa, ɗan latsa gefen cikinta yayi tare da shafa wurin samha taji wani tsarrrrrr hydar yace mi kikaci ne?
Cikin dakusashshiyar murya samha tace tuwo naci, ɓata fuska hydar yayi kamar yaga abin ƙanƙami yace tuwo da daddare? Samha tace yo shi kowa yaci, murmushi hydar yayi tare da ƙara yima samha kyakkyawan riƙo a jikinsa, yace waye yake kiranki a waya? Samha tace kausar ne, hydar yace mi zaki mata ne? Saha tace nia ban sani ba,
Taɓe baki hydar yayi tare da ɗan ɗage girarensa duka ya jinjina kansa alamar gamsu, amma baiyi magana ba, samha dai har yanzun tana kwance a jikinsa, itama bata ƙara cewa komai ba,
Haka sukayi jigum kamar wasu masu zaman ta'aziyya, samha ce ta gaji da zaman tace zan tafi, shi hydar ma ya mata da a moter suke dan har ya fara bacci daga zaune,
Ɗan gajeran tsaki hydar yayi sannan ya saki samha daga jikinsa yace muje kada ma ayi tunanin na tafi dake wani wuri, fita samha tayi sannan shima hydar ya fito,
Saida ya rakata har bakin ƙofa, da sauri zata shige hydar ya riƙo hannunta tare da cewa sunbaceni mana, samha tace kai kada wani ya ganmu, tana maganar tana zaro ido kamar wanda dambu ya shaƙe, hydar yace to a ganmu mana sai mi, yimin mana, murmushi samha tayi sannan tace to matso saika sake min hannu, murmushi hydar yayi dan yasan tana so ta gudune, sakin hannun yayi samha tayi ciki da sauri ba tare da tayi abinda hydar yace ba,
Murmushi hydar yayi sannan ya juyo, saida yazo inda shamsu yake zaune ba tare daya kalli wurin ba yace muje, tashi shamsu yayi da sauri kafin ya isa har hydar ya shiga moter shima yana zuwa ya shiga yaja suka ɓace da wirin,
0 comments:
Post a Comment