This is for you "Maman Nu.aym. Allah ya raya mana Nu.aym ya albarkaci aurenki.
Thank you for being a big fan of wata bakwai 7.
Husna kam tana zaune gefen gadonta ta rafka tagumi da tunani kala kala a zuciyarta.
Sanda aka zo aka kawo mata kudi wai inji yarima. Wani abu taji tun daga dan yatsan kafarta har zuwa zuciyarta.
Waye shi dahar zaiyi zaton tana bukatar kudin shi?
Tana kallon mamakin da yake fuskar hadimar data ce ta mayar masa da kudin shi.
Kasa jurewa tai. Batasan lokacin da hawaye suka zubo mata ba tasa hannu ta goge su.
Kirjinta na mata wani irin zafi.
Turo kofar akai da wani irin karfi da saida karar tasa husna zabura.
Da yanayin yanda ya turo kofar haka ya mayar da ita y kulle. Tana kallo yasa mukullin jiki ya na shirin kullewa.
Gabanta ya shiga dukan uku uku.
Murya na rawa tace.
"What are you doing? Ka fitarmun daga daki. Bana........ "
Ganin ya cillar da mukullin gefe ya nufo gadon. Yanayin fuskar shi ya sa ta hadiye sauran maganarta.
Da sauri ta dinga jan jiki tana matsawa har takai karshen gadon. Ta takure jikinta.
Gefen gadon yazauna ya fuskanci idan take.
Cikin muryarshi da ta kara budewa saboda bacin rai ya kalleta sosai yace.
"Zo nan"
Yana bubbuga kan katifar kusa dashi.
Girgiza kai ta shiga yi tana kara matsawa jikin gadon kaman zata shige cikinsa.
"Bazai miki kyau ba inhar na karaso na jawoki da kaina"
Ya fadi a gajiye. Muryarshi da yanayin shi sun tsorata husna. Wasu hawaye suka gangaro mata.
Kallonta kawai yakeyi. Gani tai bata da wani zabi. Batason me yake nufi da ita ba.
Ko menene bata son yazo inda take ya janyota. Bataso hannun shi ya sake kaiwa jikinta. Bataso sam.
A yanayin daya fadi maganar tasan zai aikata. Saboda bata ga wasa a fuskarshi ba.
Gata Allah ya zuba mata tsoron tsiya.
A hankali taja jikinta ta matsa tsakiyar gadon tana hawaye.
Kallonta yake yi. Yanda duk ta firgice ga hawaye wani nabin wani.
"I really don't want to repeat myself"
Ya fada yana kallonta. A yanda yake jin shi komai zai iya faruwa.
Matsowa tai inda ya nuna mata. Jikinta ko ina kyarma yake.
Yaja wani uban tsaki a zuciyar shi. Daga shi har ita auren nan da akai musu an shiga rayuwarsu ya kula.
Kalli yanda jikinta yake kyarma kamar wanda ta ga wani mugun abu.
Ranshi ya kara baci. Bason tabata yake ba. Bata jin magana ya kula.
Ya kuma rasa dalilin dayasa take da karfin bata mishi rai har haka.
Bayason raini. Inhar yan son rage matsalar zaman su dole ya koya mata guje ma bacin ranshi.
Duk tsanar datai masa kuwa. Dan haka ya kamo hannuwanta da baisan mai taje ta tababa sukai sanyi karara haka.
Hannu daya ya saki. Yakai shi fuskarta ta janye.
"Stay still"
Ya fadi da wata irin murya da tasa ta tsayawa. Wasu hawayen suka kara zubo mata.
Hannu yasa ya goge su yana fadin.
"Bana son ganin hawayen nan. Magana nakeso muyi. Kina jina?"
Husna kam a tsorace take. Kai ta daga mishi. Tana kokarin tarbe hawayen ta kasa.
Hannu yakai ya dago mata fuska. Ya tsani yanda duk da hawayen fuskarta tayi kyau.
Cikin idanu yake kallonta dan yana son ya tabbatar da sakon shi ya kai mata.
"Yau ya zama ranar farko da zan aiko miki abu kisa a mayarmun. Matsalolin da nake ciki sun mun yawa bakuma nason kara su da gulmace gulmace tsakanin hadimai na, cewar matata ta raina ni"
Yanayin abinda tagani a idon shi sai taji sam abinda tai masa din bata kyauta ba.
Sai dai shima yanayin da ya saka ta shiga da wanda ta tabbatar yanzun haka ammar yana cikin fin nata bai musu adalci ba.
Bata son yanda jikinta yake bin umarninsa. Hannun shi dayake taba mata fuska take son turewa.
Saidai bata son bijirema umarninsa. Bata son mai zai iyayi ba. Ga dakin ya kulle hakanma shi yafi daga mata hankali.
Kai ta daga masa alamar.
"Eh"
A dake yace.
"Talk to me da bakinki bana son magana da kai"
Sai da ta hadiye wani miyau sannan can kasan makoshi tace.
"Eh naji"
"Good girl"
Ya fadi yana cire duka hannuwanshi daga jikinta.
"I am waiting"
Ya fadi a kagauce. Saida ta sa hannu ta goge fuskarta sannan tace.
"Me zanyi kuma?"
"Kinmun laifi and bakisan me ya kamata kiyi ba kenan?"
Da wata sabuwar tsanar shi tace.
"Kayi hakuri"
Jinjina kai yai ya mike daga kan gadon. Inda ya cilla mukullan dakin ya dauko.
Yana budewa wata hadima zata kwankwasa. Da sauri ta tsugunna kasa tana fadin.
"Allah ya kara maka lafiya"
Ko kallonta bai ba ya wuce.
Tashi tai ta karasa cikin dakin da sallama. Ta tsugunna ta mikama husna ledar hannunta.
Karba tai ta ce mata zata iya tafiya. Dan ta kula inba tace su tafi ba haka zasuyita tsugunno.
Zuciyarta yanzun bata natacce take ba. Ture shi da abinda yai mata tayi gefe daya sai zuwa anjima.
Ta bude ledar ta zazzago kayan ciki. Katin wayar ta dauka ta kankare su duka.
Ta lalubo wayarta tai loading hannunta ma rawa yake. Kaman yanda zuciyarta ke rawa.
Numbar ammar da take kamar tambari a zuciyarta saboda zaman datai ta saka ta danna kira.
Da duk ringing din da zatai da yawan hawayen da suke zubo mata. Sai da ta yanke bai dauka ba.
Ta sake kira bai dauka ba. Saida ta jera kira biyar bai dauka ba. Tanajin zuciyarta kamar zata fashe sabo da fargaba.
A karo na shidda ya daga muryarshi can kasa yace.
"Hello"
.
Ko a mafarki ko a ido biyu ko a cikin dandazon taron jama.a zata iya gane muryar ammar dinta.
Sai yanzun dataji muryarsa tasan kewar sa da zuciyarta tayi.
Numfashinta har wani barazanar daukewa yake.
Cikin murya mai matuqar rauni tace
"Nawan nice."
"Husna ta"
ya fada tasan shi sosai hakan yasata fahimtar yanayin muryarsa da alamar rashin yarda da cewar ita dince ta kirashi.
Shirun da yaji tayi ne yasa shi cewa
"husna da gaske kece? Tawan kimin magana dan Allah."
Muryarta na rawa tace
"nice ammar."
"Ya Allah"
ya fadi yai shiru.
Tasan kuka yake daga yanayin muryarshi.
Can kasan makoshi cikin kuka yace.
"Husna dan Allah kice mun mafarki nake. Kice abinda suke fadamun ba gaskiya bane."
Itama kuma kukan na neman cin qarfinta tasan idan ta kuskura ta fara batasan ranar barinta ba.
Dole ta zama mai qwarin gwiwa tai masa magana.
"Ka saurareni....wallahi bana son auran nan bana son wanda aka auramin ban taba son kowa ba sai kai ammar ka yarda dani."
Tun da take bata taba jin namiji saurayi babba kaman ammar na gunjin kuka haka ba.
Kukan shine ya karasa karyar mata da zuciya. Bata san sanda kukan ya kwace mata ba.
Sun fi mintina goma sun kasa magana kamun ya samu yace.
"me yasa zakimin haka? Ke baki san irin son da nake miki bane? Haba babyna komai da nake nema a rayuwa don na aureki ne."
"Nasani nasan haka wlh ta fada"
zuciyarta na wani tafasa. Lokaci daya zazzabi ya rufeta ruf.
Wani irin kuka take daga zuciyarta yake fitowa dan hawayen ma sun daina zuba.
Cikin kuka ammar yace.
"To ki kashe auren nan indai kina sona da gaske ba qarya kikemin ba husna"
Bata san ya akai ma bata taba kawo ma ranta wannan shawarar ba a tsahon sati biyu datai a wannan qaddararren gidan.
Wani sanyi taji a zuciyarta ta wanni fannin.
Hannunta tasa ta dafe kirjinta saboda zafin da yake mata.
"Ammar zan kashe auren nan na maka alqawari zamuyi rayuwarmu tare."
Tanajin yanda ya sauke ajiyar zuciya. Muryarshi harta shige saboda kuka.
"Husna ina sonki da yawa nasan ba zaki taba barina ba wallahi tun jiya dana dawo aka fadamin na dauka zuciyata zata fashe ne tunda nazo daki na kwanta jiran mutuwata nake...husna kece numfashina."
Murmushi tai duk da halin da suke ciki bai hanata jin son shi har ranta ba wanda ta jima bataji irinsa ba.
"Nima kasan ina sonka aiko?"
"Da auren wani akanki husna zai wahala zuciyata ta yarda da hakan"
Ya fadi a raunane.
Da sauri tace.
"Zan kashe auren nan. I promise you nawa"
Hira sukai tayi abinsu yace mata bara ya tashi yai sallah yai wanka.
Bata bari ya tafi ba saida tasa yai mata alkawari zaici abinci tukunna.
Duk da taji muryar ammar da alqawurransa masu sakata natsuwa.
Itama ta masa alqawarin da bata san yanda za.ai ta cika shiba.
Wani farin ciki take ji ammar bai tsaneta ba yana sonta har yanzun.
Wani bangare na zuciyarta yana son nuna mata kuskuren abunda suka aikata.
Ita kam koma menene bai dameta ba a yanzun da wutar soyayyar ammar take tsarga mata.
Kwanciya tai kan katon gadon maganganun su na mata yawo.
Sanyi taji tanaji dakyar ta iya sakkowa daga kan gadon ta kashe AC din dakin ta koma ta kwanta.
Ta lullube amman jikinta kyarmar sanyi yake saboda zazzabin da ya lullubeta.
A haka asabe ta shigo ta sameta. Da gudu ta sauka kasa ta je ta fada a kira kamala a gaya mishi ya kira prince ishaq uwargida ba lafiya.
*
Prince ishaq kam tunda ya fita daga dakin husna. Ya sa aka kaishi lambu yai zamansa.
Dan sam zaman gidan duk da bangaren su daban dana natacce ya fita daga ranshi.
Baya son yanda take bata masa rai tana saka shi yana abu dan dole.
Yana kishingide kan daya daga cikin kujerun dake lambun ya lumshe idanuwanshi yana tunanin kalar zaman da zasuyi da natacciyar nan a abuja.
Wayarshi ta kama ruri. Yanaji ya share sai da tai har sau uku. A na hudunne ya dauko batare daya duba ba ya amsa ya kara a kunne.
Cikin ladabi kamala ya gaishe dashi kamun ya fada mishi cewar husna bata da lafiya.
Ya bude idanuwan shi a hankali yanajin tamkar duka nauyin duniya aka dora mishi akai.
Ina amfanin wannan auren da babu komai a cikin shi sai matsala da takura.
Yayi niyyar ya kira doc din kawai yaje gida ya dubata sai dai baya son karanta.
Wannan kuma zai nuna cewar bai damu da matarshi ba wanda gaskiyane.
Yadai damu da kare mutunci da martabar gidansu.
Dan haka ya kira cikin hadiman wajen yace ai ma driver dinshi magana yazo au tafi.
*
Yana shiga gida bangaren husna ya nufa.
Ya sallami hadiman da suke zagaye da ita. Gefen gadon ya zauna.
Yanda yaganta sai ta bashi tausayi. Hannu yakai ya taba goshinta yaji shi kamar wuta.
Cikin rawar murya tace.
"Karka sake tabani.... Bana so"
Bai san sanda murmushi ya kwace masa ba.
Cikin taushin murya yace.
"Save it saikin warke. I am stuck with you like you are stuck with me. Badon ina so hannuna ke kaiwa jikinki ba"
Baya son jin kanta. Saboda shi ya kamata ya daga mata kai. Ba wai ita ba.
Duk da yasan abinda ya kamata yai mata. Saidai bazai karya alkawarin daya daukar ma kanshi ba.
Doc dinsu ya kira.
Tashi yai ya shiga toilet dinta.
Ya wani yamutsa fuska ganin pants dinta da bra data wanke.
Karamun towel ya dauka ya jiko shi ya matse ya fito.
Bargon da take lillibe dashi ya janye.
"Banaso" ta fadi dakyar.
Ko bi takanta baiyi ba. A goshi ya fara dora mata towel din.
Ta zabura saboda sanyin da ta kara ji.
Hannuwanta duk biyun tasa tana rike nashi.
Dayan hannun shi yasa ya rike nata duka biyun gam. A dake yace.
"Bana son gaddama. Ba yanda za.ai muyi tafiya bakida lafiya. I am not rescheduling saboda ke"
Bata da karfin yin fadan. Ba kuma tason yana tabata. Musamman yau dataji muryar ammar.
Sai ta sake tsanar shi. Wasu hawaye suka gangaro fuskarta.
Bata manta abinda yai mata ba dazun. Da kuma wanda yake mata yanzun.
"Ka sakeni please. Dan Allah ka sakeni"
Ta fada tana kallon fuskarshi.
Hannuwanta ya saki yaci gaba da dora mata towel din a goshi.
Ta bude baki zata sake magana dan taga bai gane me take nufi ba aka kwankwasa kofar.
"Come in"
Ya fadi dan yasan yace in doc din yazo ya ce a rakoshi bangaren husna din.
Da sallama ta turo kofar. Ta gaishe da prince ishaq da ya amsa cikin mamaki.
"Kayi hakuri. Doc amir ya samu flat tire a hanya saiya kirani coz ina kusa daku fiye dashi"
Jinjina mata kai yai kawai. Ya nuna mata husna da take kwance.
Duddubata tai sosai da aune-aune.
Tace ma prince ishaq. Damuwace tai mata yawa.
Tana bukatar hutu sosai. Ta bada list na prescription din data rubuta.
Kira yai akazo aka karba. Doc din ta zauna saboda za.ayi allurai guda uku dan zazzabin ya sauka.
Ba.afi mintina sha biyar ba aka kawo.
Ai husna na kyalla ido taga allura ta mike zaune. Idanuwa cike taf da hawaye tace.
"Wallahi na warke. Dan Allah karka bari taimun allura"
Doc din ta kalli prince ishaq. Matsawa yai kusa da husna ya kamo hannuwanta.
A tsorace ta rike shi sosai tana magiya.
Tun tana karama harta girma sai an riketa ake mata allura. Bata sonta ko kadan.
Ko wani za.ayiwa hankalinta tashi yake balle kuma ace ita.
Hannuwan shi ya zame daga na husna ya tallabi fuskarta. Ya saba mu.amala da patients irinta da yawan lokutta a baya.
Musamman yara kanana. Cikin idanuwa ya kalleta yace.
"Pull yourself together. Babu zafi fa"
A rikice husna ke girgiza masa kai tana fadin.
"wallahi zan bika abuja karka bari tamun allura"
Girgiza kai yai a ranshi yana fadin saikace zuwan shi abuja da ita zabi ne.
Kamo ta yai. Ya dagota sosai ya rike rungumeta a jikinshi. Kiciniyar da take ta kwacewa ma taso ta bashi dariya.
Sake matseta yai sosai a jikinshi hakan yasa ta yin luf. Alama yaima doc din cewar tazo tai mata allurar.
Ganin tana kokarin zame skirt din dake jikin husna ya sakashi lumshe idanuwanshi.
Yanajin yanda husna ta sake rukunkume shi da shigar allurar.
Haka kawai yaji zuciyarshi wani iri.
Yanda take rike shi yana saka shi jin wani yanayi da baisani ba kuma bama yason ya fahimta.
.
"Na gama"
"Na gama"
Doc din ta fada.
Kai kawai prince ishaq ya daga mata. Ya nuna mata kofa.
Ta tattara kayanta ta fita.
Yana rike da husna har yaji yanayin numfashinta ya canza alamar bacci ya dauketa.
A hankalo ya ajiyeta yana bambareta daga jikinshi.
Da wani irin yanayi a jikinshi mai wahalar fassarawa ya fita daga dakin yana ja mata kofa. .
Da tunani barkatai a zuciyarshi harya tashi da safe.
Tun wajen karfe bakwai daya koma bacci bai tashi ba sai yanzun nan. Yana duba agogo har sha daya tayi.
Dakyar ya rabu da katifar yaje yai wanka. Ya shirya cikin wani kaya na karan miski brown.
Yayi kyau matuka. Har ya wuce zaiyi dining room din ya tuna da yar mutane da take karkashin kulawar sa bata da lafiya fa.
Yaja wani gajeran tsaki sam sam baya son matsala a rayuwar shi.
Bangaren husna ya wuce yaga ko taji sauki. Dan bai niyyar daga tafiyar shi ba saboda ita. Yanda aka lika masa aurenta haka aka lika masa tafiya abuja da ita.
*
Husna kam dayake ba sallah take ba. Tunda ta tashi tai wanka ta shirya cikin wata doguwar riga simple.
Suka sha wayarsu da ammar harya shirya zuwa aiki. Dan ya ce mata ya samu aiki a wani gidan mai.
Suna gama wayar ta kwanta shiru abinda ya faru tsakaninta da prince ishaq yana mata yawo.
Sai taji kaman tanajin kam shi har yanzun kan gadonta. Taja tsaki.
Bakin natacce ta fada a ranta. Tanata tunani har bacci ya dauketa.
*
Kwan kwasawa yai yaji shiru haka yasa shi turawa a hankali yaganta kwance tana bacci.
Babu karya tana da kyau. Shi kyan ta baya gabanshi.
Gefen gadon ya karasa ya zauna. Ya duba magungunan daya ajiye gefe suna nan yanda suke bata sha ko daya ba.
"Yarinyar nan ta rainani" ya fadi a hankali. Sai daya saka aka kawo plantain da fried eggs sannan.
Ba inda zai kwashi kaya ya tafi dashi yake fada ma kansa.
Hannu yasa ya shafi gefen fuskarta. Da sauri ta bude ido ta sauke shi a fuskarsa.
Ganin shi yasa ta saurin tashi zaune tana matsawa. Har haushin yanda take shakkar shi ta ba kanta.
Ga jarababben kamshin shi har ya gauraye dakin.
Hannu yakai zai sake tabata ta kara matsawa. Bai kobi takanta ba.
Ya matsa kusa sosai yaka UK hannu ya taba fuskarta ta rufe idanuwa. Ya taba wuyanta na minti daya yaji akwai sauran zazzabi.
Plantain din ya ajiye mata kan cinya da cokali a ciki yace mata.
"eat ki sha maganinki"
Ya wani hade rai yana kallonta kawai.
Husna ta kule. Bata son yana mata shisshigi. Inba naci ba me zai kawo shi dakinta.
Girgiza masa kai tayi alamar bata ci.
"Ki ci ki sha magani ko kuma ki zauna a dawo ai maki allura. I can't take you ko ina da wannan zazzabin"
Ya ce a gajiye. Kaman maganar kawai ta cinye duk karfin jikin shi.
A hankali ta dauki plate din. Turawa kawai take badan bakinta nada wani appetite.
Dan gara komai da allura. Banda auren natacce babu abinda ta tsana sama da allura.
Jitai inta kara amai zatai. Ta ture plate din. Matsawa tai ta dauko magungunan. Ta duba yanda zata sha su. Ta ballo saidai ba ruwa kusa.
Ga mamakinta prince ishaq ya tashi yaje inda fridge din dakin yake ya dauko mata swan da cup dayake a jiye kan fridge din.
Ya zuba ya mika mata. Saita tsinci kanta da danjin nauyin shi.
Ta karba cikin sanyin murya tace.
"Nagode"
Kai kawai yadan daga mata yanda yakanyi ma wasu cikin hadiman gidan in sun gaishe dashi.
Saida yaga ta shanye magungunan. Tana ta yatsina fuska yace mata.
"Kina jin ciwon kai?"
Ta girgiza kanta.
"Dizziness fa? Ko amai?"
Ta sake girgiza kai dan ya soma isarta. Shi ba likita ba ya tsare da tambayoyi.
Mikewa yai ya karasa daf da ita. Hannu yakai ya sake tabawa yaji yanayin zazzabin. Ta janye fuskarta.
Wani abu ya tsaya mishi a wuya. Ya rasa dame yarinyar nan take ji. Baya son ta zame masa kayane dan suna setting kafarsu abuja bashi da lokacin wannan shirmen.
.
Share ta yai ya matsa ya taba kumatunta. Ganin yanda bata so ne yasa shi dora hannun kan wuyanta.
.
Share ta yai ya matsa ya taba kumatunta. Ganin yanda bata so ne yasa shi dora hannun kan wuyanta.
Yabarshi akai fiye da yanda yake bukata dan kawai ya takurata. Tadai ki kallon shi harya dauke ya fita.
Zanin gado husna ta janyo ta goge kumatunta inda ya taba ta kuma goge wuyanta.
Amman da yake kaman yanda Allah ya zuba masa naci haka ma duk abinda yabar mata ajiki yake da naci.
Yaki fita sam. Ta ki daina jin dumin hannunshi da yanda tsikar jikinta ke tashi.
A fusace ta sakko daga kan gadon ta je wajen dressing mirror dinta. Duk wani collection na turare da take dashi saida ta feshe dakin dashi.
Jin turarukanta sunki korar kamshin nataccen nan yasata bude akwati nan da kayan kwalliya ne kawai a ciki da turaruka lefenta datai ma kanta alkawarin ba zata taba ba.
Tunda bata son mai kayan ba kuma tason abin hannun shi.
Kala uku ta bude daka gansu kasan masu bala.in tsada ne. Ta feshe dakin. Sannan taji yamata kamshi na daban.
Tana komawa kan gado ta kwanta ammar na kiranta.
"Assalamu alaikum tawan"
Ya fada tanajin fara.arshi cikin muryarshi.
Ta amsa da murmushi a fuskar ta.
Yanda yaji muryarta ya sashi tambayarta lafiya kuwa.
Tace.
"Nawan zazzabi nake danyi fa"
A rikice ya shiga jero mata tambayoyi.
"Ya Rabb. Yanzun ya jikin? Kinsha magani? Ko sai kinje asibiti? Husna ko....... "
Dariya tai ta katse shi da fadin.
"Ya kira likita an dubani har gida. Yanzun ma yazo yaban magani ya fita"
Lokaci daya muryar ammar ta sauya.
Can kasan makoshi yace.
"Husna karki soma son shi. Karya tabamun ke, husna in baki kashe auren nan ba wallahi zan iya mutuwa. Ki tausayamun"
Muryarta a tausashe tace.
"Relax nawan. Ka yarda dani mana. Ni bansan meyasa ya aureni bama. Wallahi bai damu dani ba. Bai taba yunkurin tabani ba."
Wani dumi taji inda ya tabata dazun tamkar waje na neman karyata zancenta. Ta kuma tuno yanda ya riketa da za.ai mata allura. Duk da dumin zazzabin da take ji bai hanata tuno nashi dumin ba.
Haka ta samu ta kwantarma da ammar hankali da sake jaddada masa alkawurran da bata san yanda za.ai ta cika shi ba.
*
Kan kujerar falon shi ya zauna yai shiru.
Kanshi ma ciwo yake. Yana so ya hada kayan tafiyar shi gobe duk da yanada kaya acan.
Amman akwai yan abubuwan dazai hada saboda yanayin tsaro. Ko da kwana hotel zai kamasu ba komai na can din yake son amfani dashi ba dul da cewar sababbi ne.
Wani lokaci yakan godewa halayya irin ta ummarshi da duk matsayinsu tai kokarin koya musu yin abubuwa da dama dakansu.
Takance kar matsayin da Allah yai musu ya saka su girman kai ko wulakanta na kasa dasu.
Su dauka cewa matsayinsu wani abune mai nauyin gaske da Allah zai musu tambaya akan yanda suka rike shi.
Duk da haka kamala ya kira dan ya yarda dashi sosai. Shi yasa ya hada mishi duk abinda yake bukata.
Ya kuma ce shine zai kaisu Abuja goben in shaa Allah. Dan haka kawai yake son canji.
A mota zasuyi tafiyar. Rabon shi dayai tafiyar fin awa daya a mota harya manta.
Ya sanar da kamal baya son security saboda hakanma na janyo hankalin mutane akan su.
Normal yake bukata ko da ta rana dayace. Yana son yayi abu kaman yanda kowa yake yi.
Yana son ajiye prince ishaq a gefe yai abu a ishaq dinshi zallah.
.
Tun wajen karfe tara ya gama shiryawa Sai dai baisan ko ita ta shiryaba ko bata shirya ba.
Fitowa yai babban falo ya sami hadima daya dabai san sunanta ba don ba damuwa yai da hakan ba.
Tun wajen karfe tara ya gama shiryawa Sai dai baisan ko ita ta shiryaba ko bata shirya ba.
Fitowa yai babban falo ya sami hadima daya dabai san sunanta ba don ba damuwa yai da hakan ba.
Har qasa ta tsugunna kanta a sunkuye tace
"fatan yarima ya tashi cikin qoshin lafiya?"
Lafiya ya amsa a taqaice mulkin na motsa masa.
Yana son ya tura a ce mata ta fito sai dai yana gudun zata iya fadar magana a gaban hadimansa.
Baya qaunar yarfi da harkar yada girma duk da bawai son matsayin nasa na yanzun da na gaba yake ba.
Da kansa ya taka zuwa bangaren ta ya nufi dakinta. A hankali ya qwanqwasa.
*
Husna kam tunda ta tashi taji jikinta babu zazzabi sam. Tadai yi wanka ne tasa aka kawo mata soyayyen dankali tadan ci.
Tasha magungunanta dan bata da bukatar natacce yazo ya maimaita abinda yai jiya.
Dan ta kula namiji ne shi da yake yin abinda yaso babu kuma wanda ya isa ya hana shi inya tashi.
Chatting suke da ammar a whatsapp dan jiya da dare ya sata tai downloading sabo.
Taji an kwankwasa kofar. A zatonta asabe ce ta dawo kwashe kayan data kawo dan haka tace
"Shigo"
Tura qofar yai tana kwance da wayarta a hannu ta dago.
Saurin sadda kanta qasa tayi tana ci gaba da danna wayarta.
Saurin sadda kanta qasa tayi tana ci gaba da danna wayarta.
Wannan nataccen nema sai dai ya gaji da tsayuwarsa a wajen ya shigo ko ya koma.
Chatting din da take da ammar ya fiye mata komai na gidan nan.
Chatting din da take da ammar ya fiye mata komai na gidan nan.
Shi kullum yaita fama da kaya kaman wani dan sarki. Duk da tsanarsa da tai baya hana mayyar zuciyarta ganin yayi kyau.
"Ki fito mu tafi."
Ya fada cikin wannan muryar tasa ta yanga. Sai lokacin ta tuna yaune yace mata zasu tafi abuja.
A kasalance tace
"ba zani ba aina fada maka"
Wani abu yaji ya tsaya masa a wuya.
Inda ba.ai masa umarnin ya tafi da itaba sai dai kawai taga bata ganinsa.
Zuciyarsa ta dibe shi ta watsa wani lokaci can baya.
**** ****
"Yayana ni fa saina bika......yai dariyarsa
"huddy kiyi haquri ba dadewa zanyi ba kwana uku kawai Kuma zamuyi waya"
Ta sake goge hawayen dake bin fuskarta
"bana so kanamin nisa."
Sauke numfashi yai
"huddy ke kinmin nisa ai"
ya fadi a zuciyar tasa.
A fili kuma yace
"banson jan magana ko bacin rai. Umarni ne na cewar na tafi dake.Ki shirya nan da 15 minutes. I don't want to drag you myself, don't tempt me "
Ganin bata da niyyar cewa komai yasa shi ficewa.
Ita yanzun kam me zai bata mata rai bayan tana manne da ammar a whatsapp....wuni suke hira ko yana office ma haka da dare suna manne yana rikitata da voice notes dinsa.
Da batai niyyar shiryawa ba sai wata zuciyar tace yanzun in ma baki tashi ba dawowa zaiyi.
Kuma ta tabbata tsaf zai aikata abinda ya fada.
Maganar ma da take yi dashi lokacinta take bashi.
Tashi tayi ta sake kayan jikinta. Wani karamun akwati ta dauka badan tasan menene a cikin shi ba.
Gara ma ta bishi abuja din dan ya sake tabbatar da baya gabanta.
Mayafi kawai ta dora kan kayan jikinta taja akwatinta zuwa falo...inda wata daga cikin masu aikin tai saurin zuwa ta karbar mata. Fita akai dashi.
Natacce ne ya fito daga side dinsa sanye da alkyabba ruwan hanta mai cizawa da wata irin hula akansa. Bata so ta tsaya zuciarta ta misalta mata kyawunsa.
"Ungo"
ya fadi.....hannunsa ta kalla daya miqo mata batare data yarda ta kalli fuskarsa ba.
Alkyabba ce mai kalar tasa sai dai wannan akwai ado na mata a jikinta.
"Ki saka saboda zamu fara biyawa ta gida sannan mu wuce."
Karba kawai tayi. Bata son magana mai tsaho na hadasu inba dole ba.
Tanajin idanuwansa na binta har ta saka ba tare data kalle shi ba tace
"muje"
Gaba daya kamshinsa ne cike da alkyabbar jikinta. Ta kuma tsani yanda hancinta ke jin dadin kamshin.
Gaba ya shiga ta bishi a baya har zuwa wajen motar (Range Rover) wata fara mai kyau.
Bude musu akai ta shiga shima ya shiga baya.
Har suka isa gidan babu wanda yacewa kowa komai.
Har suka isa gidan babu wanda yacewa kowa komai.
Ita tana ta chatting da ammar abinta. Dan haka bata kula da komai ba sai tsayuwar motar data ji.
Aka zo aka bude musu qofa suka fito. Ya zo kusa da ita ya tsaya.
"Na iya lokacin da zamuyi a cikin gidan nan kiyi pretending komai normal ne a tsakaninmu."
Ya fada cikin muryar da takanji yaima yan aiki.
Cike da mamaki ta kalle shi.
Bata dai bashi amsa ba duk inda yai nan take binsa suna tafiya.
Tana kallon yanda mutanen cikin gida suke tsugunnawa tun kamin ya qaraso inda suke suna gaishe dashi amman ko kallon arziqi balle taji ya amsa.
"Ana gaishe dakai ko baka ji?" Ta buqata.
Bai bata amsa ba.. Taji haushin kanta ma datai masa magana.
Wani irin daki suka shiga da saita wuni a tsaye a wajen bata gama qarema kyawunsa kallo ba.
Ya zauna kan daya daga cikin manyan kujerun dakin.
"Ki zauna"
ya furta a hankali yana nuna mata waje a kusa dashi. Bata musa ba ta zauna.
Wata kyakkyawar mata ce magidanciya ta shigo dakin cikin shiga ta alfarma.
Sai taga matar ta mata wani irin kwarjini.
Sai taga matar ta mata wani irin kwarjini.
Kasa taga ya sakko ya tsugunna itama bata san lokacin databi yanda yai ba.
Saida matar ta zauna tukunna ya gaishe da ita cike da girmamawa...itama gaishe tan tayi....da fara.a ta amsa musu sannan taga ya koma kan kujerar ya zauna...itama tayi hakan.
Saida matar ta zauna tukunna ya gaishe da ita cike da girmamawa...itama gaishe tan tayi....da fara.a ta amsa musu sannan taga ya koma kan kujerar ya zauna...itama tayi hakan.
"Babana an shirya kenan?"
Ta buqata. Cikin tausasawar murya yace
"yanzun zamu wuce nace saimun biyo ta nan mun gaishe dake."
"Aikam ka kyauta sosai ba zaka je da ita taci wani abu ba kuma kudan zagaya ciki?"
"Uhm uhm umma sai dai ko inmun dawo muna sauri ne kinsan ba jirgi zamu bi ba"
ya fada yana miqewa..
Saita tsinci kanta da sake tsugunnawa tace mata mun tafi.
Saita tsinci kanta da sake tsugunnawa tace mata mun tafi.
Addu.a tai musu sosai. Kamun su kama hanya su fita.
Motar suka koma. Daga su sai driver din.
Tun dazun take mamakin yanda cikin motar yake.
Ba ta inda driver din zaiga me sukeyi saboda akwai barrier a tsakaninsu.
Hannu prince ishaq yakai ya taba goshinta. Ya sake taba kumatunta sanna ya koma cikin kujerar ya zauna sosai.
Husna kam batai mamaki ba. Kadan da aikin wannan bakin nataccen.
.
IPhone din shin ya dauko ya saka headphones yana sauraran wakokin larabci na Rashid Al Majeed.
IPhone din shin ya dauko ya saka headphones yana sauraran wakokin larabci na Rashid Al Majeed.
Ita kam husna suna hira ne da ammar sai dai idan network ya dauke ta tsaya saiya dawo.
Can yace
"Tawan me kike yine haka??
"Muna hanyar abuja"
Ta bashi amsa.
"Abuja???"
Ya rubuto da alamar tambaya.
Tasan mugun kishi irin na ammar koda yaushe saiya tambaya ko natacce yana da kyau tace masa mummuna ne shisa ta kara tsanarsa.
Shirun dayaga tayine batai reply ba yasa yace
"ke dawa zaku je abuja? Kuma me zaku yi?"
"Nima ban saniba ammar haka yace mu tafi ta bashi amsa."
Yafi mintina goma bai bata amsa ba sannan yace
"husna dan Allah karki bari ya tabamin ke kar ki so shi....ki taimakamin ki kashe auren nan."
Wasu hawaye taji zasu xubo na tausaya musu.
Hannunta na rawa ta rubuta masa
"yanda bana sonshi shima haka bazaimin komai ba...kayi haquri saina kashe auren nan munyi rayuwarmu."
"Zanso kina kusa dani yanzun zanyi shirune ina kallon kyawun idanunki masu nutsar dani cikin wani yanayi."
Ya rubuto.
Ta sauke ajiyar zuciya,yama zata fara zaman aure da wani ba ammar dinta ba mai nuna mata soyayyarsa.
Battery dinsa ne ya dauke. Don haka ta sauka akan whatsapp din tana nazarin yanayi na hanyar abuja dan bata taba zuwa ba.
Jingina tai da kujerar. A hankali ta juya kanta ta kalli natacce. Ya lumshe idanuwan shi da alama bacci yake.
Taja dan karamin tsaki a zuciyarta tana fadin bacci da headphones.
Batasan me yasa take jin inta bar masa bata kyauta ba. Hannu tasa ta dauki wayar da take ajiye kan cinyarshi.
Yana jinta saboda ba bacci yake yi ba. Ta dauki wayar tana swiping dayake ba password ta bude.
Pause ta sakama wakar da yake ji ta ajiye masa wayar inda taganta.
Bude idanuwansa yai ya juyo inda take, a kasalance yace.
"Saboda me zaki tsayarmun da waka?"
Shegen shisshigina mana ta fada a zuciyarta. A fili kuma shiru tai ta kyale shi. Dan bata da abinda zatace masa.
Kunnawa yai ya sake komawa yanda yake. Itama shirun tai batama san sanda bacci ya dauke ta ba.
Jiyai ta kwanto masa kan kafada. Ya bude idanuwanshi, daman yasan wannan natacciyar kaya zata bala.in zame masa.
Kamata yai a hankali ya kwanto da ita kan cinyarshi dan yanayin yanda take yana ganin jikinta zai iya ciwo in ta jima a hakan.
Kallonta yake da wani yanayiba zuciyar shi da baigane ba.
Kawai kuma ya basar. Gajiya yai shima yaso ya zame kujerar yadan kwanta sai dai bayason motsa wannan natacciyar.
Yanda bayason a tashe shi in yana bacci haka bayason ya tashi wani.
Saman kafadarta ya dora hannayensa ya dora kanshi. Shima baccin ya dauke shi.
*
Husna tana bude idanuwanta kamshin shi ya cika kata hanci. Abu taji a kafadarta. Takuma ji dumi sosai inda take kwance.
Sai lokacin ta kula da yanayin da suke. Kawai sai taji kasala ta saukar mata. Motsin datai ne ya sashi bude idanuwansa.
Muryarshi da take a bude ta sake zama wata babba saboda baccin daya tashi.
"Dagani to, tunda kin tashi"
Ya fada.
Lallai ma husna ta fada a ranta. Shima fa a jikinta yake kwance dan rainin hankali zaice ta wani daga shi.
Ita bama tasan me take kan cinyarshi ba bayan alkawarin datai ma ammar dinta.
A kufule tace.
"Ka dagani tukunna"
Murmushi ya kwace masa. Tashi yai daga kafadarta.
Ya zuba mata idanuwansa da bata so saboda yanda suke saka ta ji.
Gefe ta matsa ta wani daure fuska har taso ta bashi dariya ma.
Kujerar ya saukar ya kishingida sosai ya koma baccin shi.
Husna ma rakubewa tai can gefe ta koma bacci.
Bata tashi ba sai da suka karasa cikin garin abuja.
Ta glass din motar take kallo tana yaba kyawun garin.
Yanayin tsari na garin abuja ya burgeta matuqa.
Zataso ace da ammar dintane sukazo dataji dadin zuwan.
Bude musu mota akai. Tana fitowa takalli yanayin ginin gidan batasan
"wow"
ta subuce mata ba.
Zagayawa tai dan zatonta zaa bude bayan motar ne su dauki kayansu.
Ganin ta tsaya yasa shi fadin
"Muje mana"
"Zan dauki kayana ne" ta bukata tana masa kallon da yake fassara wannan wacce irin tambaya ce?
Kallonta yai sosai kamun yace.
"Muje za.a shigo maki dashi"
Ganin ya wuce abinsa yasa tabi bayanshi
Tsakiyar wani qayataccen falo suka isa.
"Za.a nuna miki bangarenki. Inkina buqatar wani abu hadiman gidan zasuyi miki"
Ya fada mata.
Bai jira amsarta ba ya wuce.
Wata ce tazo ta rakata har bangarenta. Wajen ya hadu dan duk tsanar mammalakin gidan datai bai sa yaqi burgeta ba.
Wata ce tazo ta rakata har bangarenta. Wajen ya hadu dan duk tsanar mammalakin gidan datai bai sa yaqi burgeta ba.
Wanka tayi dan tagaji sosai tunda bata samu tsarki ba balle tace zatai sallah.
Ta duba wayarta ammar bai dawo online ba har lokacin.
Ta soma kewarshi.
Ta soma kewarshi.
Tunawa tai ashe fa kausar na abuja.
.
Wani murmushi ya qwace mata.
Wayarta ta dauka ta kirata.
.
Wani murmushi ya qwace mata.
Wayarta ta dauka ta kirata.
Bayan sun gama gaisawa tace
"Ke er uwa ina abuja fa"
"Wooo bani address zan shigo gobe in shaa Allahu"
kausar ta fadi cike da farin ciki.
"Ta dora da meye sirrin? Rabon da inji muryarki haka harna manta husna."
Dariya tai tace
"kausar kin cika zolaya akwai labari saikin shigo ke dai"
"Ba damuwa kimin text din address din fa karki manta."
"Zan miki yanzun in shaa Allah."
Husna ta fadi.
"Tam ina jira"
kausar ta ce sukai sallama.
Ajiyar zuciya ta sauke.
Ajiyar zuciya ta sauke.
Yunwa takeji dan haka ta yanke shawarar sauka qasa ta tambayi address din gidan nan ta tura ma kausar.
Daya daga cikin hadiman gidan ta tambaya suka fada mata.
Zuwa tai inda aka shirya musu abinci taci wanda yai mata.
Zuwa tai inda aka shirya musu abinci taci wanda yai mata.
Bataga natacce ba baya gabanta kuma. Ba.a shigo mata da akwatinta ba tun dazun dan kayan jikinta ta mayar. Ta tsani yanda kamshin nataccen nan yake manne dasu.
Sama ta koma tai kwanciyarta dan ammar ya dawo online.
Hira sukai tayi bata sake fitowa ba har qarfe goma na dare.
Tasan Ammar ya tafi kallon ball yace mata suna da wasa.
Ko ya dawo ma ita dai bai kirata ba kuma bata neme shi ba.
Duk da gajiyar dake jikinta baisa bacci yazo mata ba.
Fitowa tai daga dakin baccin zuwa qayataccen falon dake saman nasu.
T.V ta kunna. Channel din yana kan star movies.
Bata canza ba dan tasan suna saka films masu kyau sosai.
Bata canza ba dan tasan suna saka films masu kyau sosai.
Wani horror ne mai tashin hankali.
A tsorace take kallon amman ta kasa tashi ta sauya tashar ko ta kashe.
Lokacin da suka gama sha biyu saura.
Sai yanzun take dana sanin kashe qwayayen wajen da tayi dan ta dauka ba zata ma fito ba.
Ga gidan yayi wani shiru musamman data kashe t.v din.
Sanyin AC bai hanata jin zufa ba.
Sanyin AC bai hanata jin zufa ba.
A hankali take tafiya zuwa dakinta.
Wani abu taji taci karo dashi ta saki wata irin giggitacciyar qara.
*
Sai juyi yake kan tanqamemen gadonsa ya kasa bacci. Dan yanzun wahala yake masa tunani baya barinsa bacci.
Nas ya kira yaji lafiyarsa sukaita hira.
Yana fada masa ya shirya fa dan suprised din da zai masa ya kusa.
Dariya yai duk da sautinta ne kawai yakan fita ya manta yanda launinta yake a xuci.
Sukai sallama.
Fridge din dakinsa ya bude duk apple din daya samu ciki ya cinye shi dan yau babu komai cikinsa sai shi.
Fitowa yai ya dibi wasu dan dare yayi balle ya sa akawo masa.
Mamaki ya cika shi ganin duk an kashe wutacen lungun.
Yama manta natacciya tana rayuwarsa ma gabaki daya balle kuma a gidan.
Tafiya yake dan ya lalubo switch din ya kunna.
Yaji wani abu ya kawo masa karo kuma an saki qara.
Yaji wani abu ya kawo masa karo kuma an saki qara.
Tamkar wanda aka dauka aka watsa duniyar tunani zuciyarsa ta budo masa wani yanayi:
**** ****
Ta baya ya lallabo ganin bataji tafiyarsa ba. A hankali yasa hannu yaja jelar kitsonta guda daya data sauka har gadon bayanta.
Wata qara ta saki a razane hadi da juyowa.
Shi kansa ta bashi tsoron riqeta yai dam a faffadan qirjinsa yana shafa bayanta.
"Huddyna kin cika tsoro daga tsokana."
Cikin tabararta tace
Cikin tabararta tace
"Yayana kaban tsoro sosai."
*
Iya tsoro kam husna ta tsorata numfashinta har barazanar daukewa yake yi.
Rungumeta taji anyi cikin wani faffadan qirji.
Qamshinsa taji tasan shine. Natacce ne ya tsoratata haka.
Qamshinsa taji tasan shine. Natacce ne ya tsoratata haka.
Kanta yake shafawa
"huddyna kin cika tsoro daga tsokana."
Ya fada batare daya sani ba.
"Huddy?"
Ta nanata a zuciyarta.
"Ammar"
zuciyarta ta sake furta mata.
Idanuwansa a rufe suke yanajin duminta dan singlet ce kawai a jikinsa da boxers.
Idanuwansa a rufe suke yanajin duminta dan singlet ce kawai a jikinsa da boxers.
Sai dai akwai wani abu daya banbanta.
Wannan ba kalar turaren huddy bane.
.
Jin an ture shi yasa zuciyarsa ta sake shi daga duniyar tunanin data watsa shi.
.
Jin an ture shi yasa zuciyarsa ta sake shi daga duniyar tunanin data watsa shi.
"Ya salam"
ya furta dai-dai lokacin data kunna hasken wajen.
Idanunta ta sauke cikin nashi.
Da gudy tabar wajen.
Da gudy tabar wajen.
Dafe kai yai? Why? Meyasa zuciyarsa take masa haka ne?
Saboda me zata dinga kaishi irin wannan wajajen dai-dai lokuttan da qaddara zata jeho masa natacciyar yarinyar nan.
Jikinsa ya hada da nata duk da yana qaryata cewar yaji wani abu.
Amman abinda ya qona masa rai ba damuwa dayai da natacciya ba son ganinsa da batayi.
Amman abinda ya qona masa rai ba damuwa dayai da natacciya ba son ganinsa da batayi.
Sai kace wani dodo ko wanda yake da abin qi a jikinsa.
Jibi yanzun tana kunna hasken wajen suka hada ido sai tayi tamkar wadda tai kuskuren kallonshi tabar wajen.
Jibi yanzun tana kunna hasken wajen suka hada ido sai tayi tamkar wadda tai kuskuren kallonshi tabar wajen.
Fasa daukar apple din yai ya koma daki ya kwata kawai.
Husna kam dakinta ta koma.
Kuka take sosai.
Ya zatai ma ammar haka? Wannan cin amana ne.
Tunda tasan natacce ne. Kamshin shi kawai taji tasan shine.
Bata manta yanayin qamshinsa ba tabari ya rungumeta a qirjinsa.
Yanayin rungumar dayai mata batasan ya zata fassara shi ba. Tanajin sawun hannuwanshi akan bayanta har yanzun.
Tana jin dumin jikinsa gauraye da nata.
Da sauri ta miqe ta shiga toilet. Bathtub ta shiga bayan ta cika shi da ruwa.
Soso da sabulu tasa ta durje ko ina na jikinta har ya soma radadi ko zata wanke abinda take ji.
Sai dai ga mamakinta yanayine daya samu waje daram cikin zuciyarta bawai iya jikinta bane.
Da ace zuciyar nan zata ciru. Data fito da ita ta wanke ta tas. Ta goge ko menene ya dasa mata a ciki. Saboda bata son shi sam.
Tai kuka harta gaji.
Tunawa tai wayarta a silent take da sauri ta janyota.
Missed calls na ammar har 26.
Missed calls na ammar har 26.
Text messages guda 10.
Maganar dayai mata a whatsapp 53.
Tana cikin dubawane kiransa ya sake shigowa.
Da sauri ta dauka
"Nawan"
Wani nannauyan numfashi ya sauke da har taji ta cikin wayar.
"Ina kika shiga haka?"
Ta tsani kanta ta tsani qaryar da bakinta yake shirin furta masa.
"Bacci ne ya daukeni nawan wayar na silent yanzun na farka naga kana kira."
Ta karasa maganar cikin sanyin murya.
"Wlh naji tsoro sosai babyna babu tunanin da baizomin ba. Gashi kincemin kin bishi abuja. Husna mutuwa zanyi idan na rasa ki. In ya tabamin ke zuciyata fashewa zatayi wlh kishi kasheni zai husna"
Ya qarasa muryarsa na rawa.
Hawayen dake bin fuskarta ta goge cike da tausaya mishi. Dayasan abinda ta bari ya faru yanzun........
Hawayen dake bin fuskarta ta goge cike da tausaya mishi. Dayasan abinda ta bari ya faru yanzun........
Da sauri tace
"kana karyamin zuciya in kana tunanin zan hada shimfida da mutumin dana tsana. Ni taka ce nawan. Kai kadai bazan taba hada maka jiki da wani ba gara an dauki gawata da hakan ya faru."
"Hmm husna ba zaki gane me zuciyata takeji ba inba kashe auren nan kikayi ba naga kin zama tawa tunani kawai zai iya kassarani."
Sun jima suna waya kamin suyi sallama.
Washe gari tana yin sallar asuba ta koma bacci danko wanka batai ba. Baccin ne a idanuwanta sosai.
Wayar kausar ta tasheta wajen goma da yan mintina.
Ta fada mata tana hanya.
Wanka tayi ta shirya kanta cikin doguwar riga simple ta sakko qasa ta zauna.
Ta fada mata tana hanya.
Wanka tayi ta shirya kanta cikin doguwar riga simple ta sakko qasa ta zauna.
Hadiman gidan ta fadama tana da baquwa su shirya mata wajen cin abinci na falon sama.
Kausar na sallama ta tashi da gudu taje ta ruqunqumeta tana tsalle tsalle.
Kausar na sallama ta tashi da gudu taje ta ruqunqumeta tana tsalle tsalle.
Dariya take sosai
"yau mun banu husna kaman wata yarinya."
Dai-dai lokacin da prince ishaq ya sakko daga benen.
Kausar ta ganshi ita kam husna tsalle tsallenta take yi.
*
Tunda ya fara sakkowa yake jin dariya da tsalle tsallen husna.
Kallonsu yake da mamaki a tsahon ganin da yake mata ko murmushinta bai taba gani ba.
Kullum fuskarta kaman zata saka mishi kuka. Sai kuma hawayen tan nan da baya so.
Inta fara zubo dasu har wani ciwon kai yake shirin kamashi saboda dagula masa lissafi take.
Sai yau tana ta dariya. Baisan murmushi ya qwace masa ba ma.
Sai yaga ta qara kyau.
Ohh ya fada a zuciyarsa yarinyar da ta tsane shi ya zauna yana ganin ta qara kyau kenan ma ya lura tana dashi.
Kauda kansa yai.
Muryar kausar qasa qasa tace
"dan ubanki ki nutsu."
"Wai me kike kallo husna ta fadi tana juya."
Lokaci daya fara.ar da take fuskarta ta dauke.
Tsikar jikinta ta wani tashi duk da ta janye idanuwanta daga fuskarsa zuwa qirjinsa.
Yanayin dumin qirjin ya fado mata a zuciya ta girgiza kai tamkar tana so ta batar da abin ta hakan.
Yanayin dumin qirjin ya fado mata a zuciya ta girgiza kai tamkar tana so ta batar da abin ta hakan.
Hannun kausar ta damqa da niyyar janta suhau sama ganin natacce ya nufo inda suke.
Amman taqi.
Cikin qasaita ya iso inda suke.
Murmushi ya dora a fuskarsa.
Cike da girmamawa kausar tace masa
"barka da warhaka."
"Barkanki"
ya amsa yana dorawa da.
"Mungode da ziyara"
Murmushi kausar tayi tace.
"Bakomai Allah ya kara girma"
Kai kawai ya daga mata ya wuce abin shi.
Husna ta jata suka wuce suma.
Kan hanya taketa faman masifa
"meye na wani gaishe dashi harda girmamawa. Ai wlh kin bani haushi ba kadan ba.A hakan ma sai uban yangar tsiya"
Shiru kausar tai mata saida suka sami waje suka zauna sannan tace
"husna kinsan ko waye shi din?
Naga alama baki sani ba koh?"
Naga alama baki sani ba koh?"
"Kinga nifa baya gabana asalima ke nake jira kizo kiban shawarar yanda zan kashe auren nan. Ammar ya dawo."
Sakin baki kausar tai tana kallonta.
.
"Ba canai ki tsaya kina min wannan kallon kaman na samu haukaba nace miki ammar ya dawo yanzun haka ko yau da safe munyi waya dashi."
Husna ta fada tana kallon kausar cikin fuska.
Girgizata kausar tai tace
"Husna kina da hankali a jikinki kuwa? Kin manta kalar tashin hankali da muka shigane? Tabbas kin manta da har kike son mayar damu."
Ganin tayi shiru tana wani kumbura fuska yasa kausar ci gaba da fadin
"da aurenki kike waya da gardi???"
Cikin bacin rai husna tace
"karki sake kiranshi da gardi. Bana qaunar mutumin nan ko na qaramin lokaci. Idan na zauna dashi son ammar kasheni zaiyi. Na tsane shi kausar dole ne na rabu dashi na auri wanda zuciyata take muradi."
Husna ta karasa tana goge hawayen da suka taru a idanuwanta.
Girgiza kai kausar take cikin tashin hankali:
"kin samu tabin kwakwalwa. Kuma kina gab da saka ammar da duk masu sonshi cikin tashin hankali da rudu. Husna kinsan wa kike aure?"
Ta qarasa maganar cikin rawar murya.
A zuciya husna tace wai natacce din nan waye shine?
Fine a yanzun tasan yanada alaka da sarauta ko dan cikin gidansu data gani. Saidai bai dameta ba.
Tunaninta bai taba je mata wajem bama.
A fili kuwa girgiza mata kai tayi alamar a.a.
"Prince ishaq"
kausar ta fadi tana ci gaba,
"dan sarki kabeer. Wanda yake jiran gadon mulkin garin kano.Husna zaki jefa rayuwar ammar cikin garari inhar ya gane abinda kike. Meyasa ba zaki haqura da ammar bane ki zauna gidan aurenki? Ba kowacce qaddara ake sauyawa ba."
Wata irin dokawa zuciyarta take. Idanuwanta cike taf da hawaye tace
"kausar ki taimakamin wlh bazan iya haqura da ammar ba. Nayi qoqarin hakan na kasa."
Hannunta ta riqe tana fadin
"husna babu yanda zamuyi da Hukuncin Ubangiji, ammar ba mijinki bane."
Fisge hannunta tai a zuci tana fadin babu wanda ya isa ya rabani da ammar ko sarkin ne ma da kanshi ballantana dansa.Saina kashe auren nan ko ta yaya.
A fili kuwa ta goge fuskarta tace Allah yai mana jagora mubar maganar nan kausar sai wani lokacin.
Tashi muje ko breakfast banyi ba.
"Hmm mudai je nikam a qoshe nake."
*
Kausar ta wuni gidan. Da zata tafi ma ta sake ma husna kashe di.
"Kinga ki rufa mana asiri husna. Har yanzun su abba basu gama hucewa dake ba. Karki jawo wata sabuwar matsalar"
Fuska babu walwala husna tace.
"Nafa jiki da kyau. Yanzun yaushe zaki kara dawowa? Ko nice zanzo?"
Fito da idanuwa kausar tai tace.
"Rufamun asiri. Ni yar ubana. Duka satinki nawa da aure daza ki soma yawo. Zan dawo in shaa Allah"
Dariya husna tai tace.
"Yasan da hakan ya jajibo ni har abuja"
Girgiza kai kawai kausar tai ta wuce tana fadin.
"Sai munyi waya"
*
Falon kasa tai zamanta tana ta kallo.
Kamun daga bisani ammar yazo online su sha hirarsu.
**
Satinsu uku kenan abuja. Husna zata iya cewa tun ranar da sukai karo da natacce.
Magana bata sake hadasu ba.
Zasu hadu ko a falon sama. Ko na kasa tana zaune. Ko wajen cin abinci.
Tun satun da sukazo sau uku a haduwar da sukai zai taba fuskarta da goshinta yaji ko da zazzabi.
Badai magana yake mata ba. Wasu lokuttan idan yazo ya ganta a zaune babban falo shima zai zauna.
Sai dai taji idanuwansa na mata yawo alamar yana kallonta.
*
Prince ishaq kam hidimomin shi kawai yake.
Yanajin dadin yanda natacciyar can bata damun shi.
Bata zame masa kaya ba kaman yanda yake zato.
Asalima ya sake kula haduwarsu sai dole. Kawai dai bashida lokacin batawa ne akanta a yanzun.
Amman daya dan samu time dole in yana waje ta dinga kallon shi indai tana son zaman lafiya.
Badon ya damu da ita bane. Aa kawai ya damu da ta girmama shine bai kuma son dalili ba.
Tunani yake in ya tafi har kano bai fada ma natacciya ba sam bai kyauta ba.
Yasan ba magana take hadasu ba sam. Amman duk da hakan baya son rashin adalci.
Beside zai fada matane kawai ko da wani abu ya faru. Tashi yai daga kwanciyar da yake ya fito.
Ya koyi sa.a ta rage masa wahalar zuwa bedroom dinta dan tana zaune falon su na sama tana kallo.
Gidan ba kaman na kano ba. Da kowa yake da part din shi. Duk da nan dinma dai part dinsu daban amman falo ya hadasu.
Sallama yai mata. Yana neman waje kusa da ita ya zauna.
*
Kamshin shi kawai husna taji tasan ya nufota.
Ta lumshe idanuwanta ta budesu a hankali. Batason fitina da yammacin nan.
Cikin sanyin murya ta amsa sallamar shi hankalinta na kan t.v.
Remote ya dauka da yake kan Centre table din wajen ya kashe kallon da take.
Hakan yasa ta fuskantarshi. Idanuwanta a kasa.
Shisa bayason mata magana sai dole. Bayason yanda take yin kaman bata son ganin shi. Kaman wata kazanta ce a jikin shi.
A nutse yace.
"Zanje kano gobe in Allah ya kaimu. But ba dadewa zan ba. Kwana uku zuwa hudu"
Shiru tai ta kyale shi dan bataga dalilin da zaisa ya fada mata ba. Asalima taga zuwan shi kano ba damuwarta bane.
Ba magana suke ba. Saitai kwana biyunma bata saka shi a idonta. To wacce gulmar zata kwaso kafafunsa yanzun?
Kilanma da yai shiru har yaje ya dawo ba kula zatai ba. Bama ta damu ba.
*
Abu na farko da ya tsana shine yai magana ai shiru. Dafe kanshi yai na yan dakikai.
Ranshi ya soma baci. Bayason yanda take bata masa rai sam.
Muryarshi a dake yace.
"Magana nake miki"
Kaman wadda akaima dole tace.
"Naji ka"
Mikewa yai kawai ya nufi bangaren sa. Dan inya biye ta natacciyar nan zai yi abinda zaizo daga baya yana dana sani.
Saboda tagama kure hakurin shi.
*
Wani karamun tsaki taja ta dauki remote ta kunna kallonta.
Share bangaren zuciyarta tayi dake mata fadan cewar ko yankar naman juna suke da natacce dayazo yace mata zai tafiya tai masa addu.a
"Allah ya tsare hanya" ta fada a hankali dan tasan ba zata zauna lafiya da zuciyarta ba inhar bata fada ba.
Zatai tajin wani irine tunda ba sabawa tai ba.
*
Tun da yai asuba baima koma bacci ba. Dan jirgin karfe 9 na safe zaibi zuwa kano.
Bayason ya kwanta baccin bai gama isarshi ba yai ciwon kai.
Tun takwas yagama shiri. Babu wasu kaya dazai dauka. Dagashi sai I.D card sai wayoyi.
Driver ya dauke shi daga gidan zuwa Airport.
Headphones ne a kunnuwanshi yana sauraren karatun Qur.an.
Jiyai kaman driver din na magana kasancewar bai kure maganar ba.
Ya saka pause ya zare daga kunnuwanshi yace.
"Magana kake?"
A tsorace yace.
"Rankai dade kamar ana binmu ne. Tunda muka fito gida wannan motocin ukku suke biye damu"
Tunda driver din ya soma magana zuciyar prince ishaq ke dokawa.
Yasan ba karamar wauta yai ba fitowa babu security. A nashi zaton duk wannan zai kara janyo hankalinsu ne.
Bai zata sun biyo shi abuja ba. Addu.o.in tsari ya shiga karantowa dan yadan samu nutsuwa.
"Kaci gaba da tuki. Karkai gudu"
Ya fada a hankali. Wayarshi ya dauka ya kira kamala.
"Muna hanyan airport akwai motoci uku suna binmu. Do what you can and make it snappy"
Kamala baima amsa shi ba ya kashe wayar.
Ko mintina biyar ba aiba tsakani suka soma jin jiniyar motar yan sanda.
Cikin rawar murya driver din yace.
"Rankai dade sun sha U-turn"
Wata ajiyar zuciya ya sauke. Mutanen nan so suke suga bayansa.
Har airport yan sandan suka rakasu. Tukunna.
Text ya turama umman shi saboda ya tabbata abinda ya faru a abuja dan kadanne da abinda zai iya faruwa a kano.
*
Wayar ammar ta tasheta daga bacci.
Muryarta can kasa tace.
"Hello"
Dariya ya kama yi mata.
"Tawan koma baccinki"
Kamun ta amsa ya kashe wayar. Kwanciya tai shiru dan inta tashi bacci takan dade batai magana ba.
Sai da ta wartsake sannan ta tashi. Brush kawai ta sake yi dan tai wanka tun da asuba.
Kawai sai take jin mugun kewar yan gidansu. Duk da babu wanda ya kirata har yanzun. Ta kuma son fushin suke basu huce ba.
Bayan ita akaima rashin kyautawa aka liqa mata nataccen can da bata so.
Wayarta ta dauka ta kira maheer kaninta. Wayarshi a kashe. Ta tuna safiya ce kuma ranar laraba. Yana makaranta.
Dining ta nufa ta ci dankali da kwai ta koshi abinta ta koma falo ta zauna.
Batasan gulmar datai zuciyarta tunanin ko natacce ya sauka lafiya ba.
Kallo ta kunna dan bata son yanda yai mata katsalandan cikin tunani.
0 comments:
Post a Comment