Taimakon gaggawa suka bashi atake ya farfad'o,kallonshi Dr. D'in yayi yace "Haba sayyeed da kanka en uwanta kuma suce mana me?" kallon mamaki yake masa sannan yace
"Allah yasanya mafarki nakeyi" murmushi Dr. d'in yayi yace
"Ya zakayi da ikon Allah akanta to? Arziqinmu d'aya ma karayar iya hannu ne,se buguwa datayi aka,wanda wannan shine yake san bamu matsala sabida dama akwai wannan matsalar damuwa na d'aya idanta" sauke ajiyar zuciya yayi sannan yace "Indai da ranta komai yazo mana da sauqi ai,indai inada rai da yardar Allah da izininsa seta samu lapiya" ahaka suka dunguma dunkansu dakin da take.......tunda hafsat taji likita awa su daddy bayanin cewar idantane suke tunani adawo baya kuma idan ya samu matsala lallai wannan karon gyaruwanshi se Allah,amma dai bazasukai karshen maganar ba seta farfad'o idan har bata gani da matsala idan kuma tana ganin komai to wannan daidaine,hankalinta ne ya tashi amna bata nuna ta farka ba hasalima ko motsin kirki batayi ba daga kwanciyar datake,har suka fita aka barta ita kadai,da sauri ta bud'e idon nata tana ganin hasken fitila da komai sannan ta sauke ajiyar zuciya had'e da tunano abinda ya faru,dukda tanajin azabar d'aurin da aka yiwa hannunta seta samu kanta da murmushi,ita kadai tasan ma'anar sa kuwa........
Washe gari hafsa ta farka amma qememe tanuna bata gani,wannan abun ya tashi hankalin sayyeed musamman dayake ya sani yanzu kam da matsala tunda shine na biyu,agaban su daddy sanda yayi kuka sosai yana me mata adu'a,shaam kuwa koda Dr. Shuraim yamasa bayani kasa cewa komai yayi gaba ki daya jikinsa ya masa sanyi,dana sanin abubuwa da dama ya farayi ciki kuwa hadda zuwa ya ziyarci Innah,yana ganin dayabi abun a hankali da duk haka bata zo ta faru ba,jan jikinsa yayi zuwa kofar dakin da hafsa take ciki,a hankali ya tura ya shiga ganin ba kowa ita kuma tamkar me bacci ya sanya ya matsa kusa da ita ya kurawa fuskarta ido dayake da tabbacin lallai dabeyi yunkurin tarwatsa farin cikinta ba da duk hakan bata faru ba,da fuskarta bata kumbura har haka ba,da yanzu tana gani yanda kowa ke gani da yanzu hannunta be karye ba lapiyanshi qalau,da yanzu bata kwance a wannan asibitin, dafe kanshi yayi ya furta a sarati cikin muryar kuka
"Mesa arayuwa ni shammaz na cika san kaina da yawa? Mesa zan wulaqanta jinina kuma yarinyar data zab'i zama dani ta sadaukar da farin cikinta akaina? Mesa zan sakaki a had'ari hafsat? Mesa tunda kika fara girma kika san meye so kika fara dani nake kuma kan wulaqanta miki rayuwa? Tunda kikace kina sona nake qasaki ta hanyoyi daban daban,Allah kuwan Allah ze barni kuwa? Zan iya jin dadin rayuwa bayan haqqinki na saman kaina?" fashewa yayi da kuka awurin cikeda ban tausayi sam sam bayasan abunda ze tashi hankalin hafsat yanzu,ita kuwa duk wani abinda yaje fada a kunnenta yake fad'a sedai tana d'aukar kalamanshi cikeda yaudara mara misaltuwa,sam bata yarda dashi musamman a wannan gab'ar data nemi san datake msa ta rasa gaba d'aya........
Uncle sayyeed ne yazo dakinta da dare ba kowa se ita kad'ai,ta rufe idonta ruf tamkar me bacci zama yayi a kusa da ita ya kura mata ido ba tare da yayi magana ba,taji kamshin turarensa wannan ya sanya ta bud'e idanta a hankali,tabbatarwa kanta tayi da cewar shi kadaine ya sanya ta sauke masa su,cikeda tsoro yankalleta dakyau murmushi ta sakar masa tace
"Uncle baby,wannan ita kad'aice hanyar dazanbi in raba kaina da shammaz,na tabbatar a yanda nake nakasasshiya baze aureni ba,nakuma sn bakada labarin cewar Innah ta sokoto ta rantse sena auri shammaz kota tsinewa sundaddy, banje mota ya kadeni da gangan ba,amma jin cewar idona idan na farfado yana a rufe baze taba budewa ba ya sanya naji gaba daya na samu mafita,karka sanar da kowa se bayan aure na dakai" murmushi yayi yace a sarari
"Alhamdulillah,amma hafsat kya baiwa kanki wahala duk akaina? ,
Zama a matsayin makauniya anya ba wahalar da kanki bane" murmushi ta masa
"Uncle sayyeed banida burin daya wuce na ganni a tare dakai,babu abu mafi soyuwa agarareni daya wuce na zamto mata agareka,babu abu mafi bani kwanciyar hankali illah in ganni kusa dakai kusanci mafi dad'i acikin kusance kusance,dan Allah ka tayani cimma wannan burin nawa" murmushi ya sakar mata yace
"Babu damuwa Babyn ubcle say,Allah ya baki lapiya amma kin kware a pretending" dariya tayi sannan tace
"Kaina yana masifar yimun ciwo,da kuma hannun nan,ni samosa zanci" dariya ya kwashe dashi jin excuse nata nasan cin samosa yace
"Madam ina zan samo miki samosa yanzu?" turo bakin tayi
"Ni koma a inane" To naji barinje season seven su dama 24hrs service sukeyi" bata ce dashi komai ba ya miqe yayi waje.....
Shammaz kuwa ya kasa bacci,ga haleema zaune a kusa dashi amma sam yama manta danita,ita kuwa se hotuna take faman dauka tana sakawa a snap gashi batada maraba da tsirarara,kallonshi ta d'anyi a kaikaice tace dashi
"Shaam lapiya nka kuwa ?" dan waigowa yayi ta gefenta ya marairaice
"Hafsat ne tayi accident shekarnjiya fa,kuma idonta ya kuma rufewa gashi babu chance yanzu sabida shine na biyu,ya kamata kije ki duba ta" tsaki taja
"Yo sabida nakasasshiya ta qara naqashewa shine kwana biyu duk ka canja,Allah ma yasanya ta zama gurguwa a had'a mata double" kallon mamaki ya mata sannan kamar ya maketa yace
"Tsabar ba Allah a ranki zakiwa yar uwata kuma jinina mugun fata har haka?"
"mtsww aikin banza,ai inada labarin accident din biris dai na maka wai kare ya taka sisi,in banda rainin wayau akan kanaso ka auri wannan karuwar zataje ta kara mota ya kadeta,kaji na rantse ba inda zani,kuma ka sani wlhu idan kace zakamun kishiya sena yanka tsuliyar uban kowa ma ya huta" tana kaiwa nan tayi waje,dama ya zama mujin hajiya se shiru yayi,shi yanzu damuwarsa lapiyar hafsat......
Muhammad Jalalludden Auwal,shine mutumin daya kade hafsat shekarnjiya,yaune kuma yake shirin zuwa lapiyarta domin tunda ya baro asibiti be koma ba sabida ayyuka sun sha kanshi,sanye yake da babbar rigar farar shadda dinkin sufani yasha kyau,gabaki dayanshi komai na jikinsa fari ne kaikace shirin zuwa qabari yakeyi, hatta hanky daya tiqe fari ne,agogon hannunsa ma haka haka ya taka yace asibiti,hadaddiyar mercedese benz dinsa ya parka a harabar asibitin ya fito yana tafiya irin ta manyan mutane dududu shekarunsa bazasu wuce 37 ba aduniya amma gabaki daya manyance ya masa yawa,ga uban kwarjini daya keda koda ya fito acikin motar kowa qura masa ido yayi,a yangace ya isa kofar dakin dayake tabbacin nanne,a hankali ya tura kofar ya shiga da sallamar sa,momy ce zaune kusa da ita tana ganinsa ta miqe suka gaisa sedai bata shaidasa ba,sabidanita basu hadu ba ranar,murmushi yayi yace
"Mama nine wanda na kade hafsa,nazone in duba lapiyarta sabida gobe zan bar qasar,kuyi hakuri banzoba kwana biyu ayyukane suka sha kaina" kallonsa hafsat tayi da qasan idonta ta dauke kanta lokaci daya,gaisawa sukayi da mama sannan ta masa godiya sosai
"Mama yanzu menene matsalar hafsat?" sadda kanta tayi tashiga rero masa tundaga matsalar farko data samu har zuwa wannan akan rashin ido,taqarashe sanar dashi cikin kuka sosai, girgiza kanshi yayi cikeda damuwa yace bayan ya zare madubin dake fuskarsa ya shafi idonsa
"Bazan yadda cewar idon baze bude ba sedai idan basu san kan aikinsu ba,akwai likitana dake a china,a can zamu da ita,idan mahaifanta zasu yarda zan dauki nauyin komai na aikin da tafiyar" shiru momy tayi hafsa ce tace
"Niba inda zani,ku barni anan kawai Allah ze bani lapiya" kallonta yayi yace cikin fada
"Hafsat idan kika kuma saka bakinki amaganar manya sena sassa b'a miki wlhy" tsoronsa ne ya darsu aranta lokaci daya,tanajin tsoron ayi tafiyar aje garin gyara ayi barna,tunda lapiya ta qalau,amma dai bata kuma cewa komai ba" sallama ya musu akan zece wurin su daddy da kanshi,yana fito wa ya hadu da shammaz,kallon kallo suka tsaya yiwa juna sannan ba tare da sunwa juna magana ba suka raba kowa ya wuce
Hmmmmm toophaa ga oga muhammad ya iso
Mom Nu'aiym
[2/8, 8:47 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅
Love story 2018
Billy galadanchi
*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)
Wattpadd@ 68billygaladanchi
*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*
22
Tunda hafsat taji zancen zuwa china se tafara tsoron tafiyar,lallai idan har ta kuskura akayi tafiyar nan tofa se an ce za'a yi mata aikin,kuma lallai garin neman gira rashin idone ze biyo baya,tana kwance tayi shiru uncle say ya turo kofar dakin ya shigo da sallamar sa,yunkurawa tayi ta tashi zaune sabida yanayin hannunta da har yanzu da sauransa ta tashi zaune,kura mata ido yayi yana murmushi sun dad'e sosai suna hirar su ta masoya kan ya mata sallama harya kai kofa ya juyo ya kalleta,murmushi ta sakar masa tace
"Uncle say yau nakula ka nacewa kallona lafiya dai?" girgiza mata kanshi yayi "Ai dama can kinsan ni sam bana gajiyawa da kallon kyakyawar fuskar nan taki" lumshe idanta tayi cikin sanyin murya tace "Nima haka baby say" batare dayayi magana ba ya juya sanye da murmushi a fuskarsa, gabaki d'aya wani tsoro ne yakeji da yawaitar fad'uwar gaba yarasa dalili seyakeji gabaki daya duniyar tana juya masa....
Shaam zaune yana dannan wayanshi a farfajiyar shan iska dake cikin gidansa haleemah tazo ta sameshi,cikeda rashin mutunci tace dashi
"Wai kaikam me kake nufi dani tunda qanwar ka ta qara zama naqashashiya kake wani shamun mur sekace nice nan na nakasata?" dagowa yayi ya kalleta yace
"Me kuma ya kawo maganar hafsat anan?kuma ban sanar miki cewar kidena ce mata naqasashiya ba?" tsaki taja
"Meye laifina danna kirata da sunan dayafi dacewa da ita? Wlhy akan hafsat zan baka mamaki"
"Kya daiji dashi,amma ki sani wlhy sena aureta a nakashen,ni tazo ma ta haifamun yara tunda kin zama juya,narasa me kika dauki duniya dabazaki haihu ba hakanan,shasha kawai me bakin hali" a fusace ta furta
"Kafi kowa sanin cewar niba juya bace tunda na haifa maka ya qanwarka ta kashe,kuma ka sani wlhy koba hafsa ba indai banice zan haifa maka yara ba kaida haihuwa har gaban abada kuwa" tsaki yaja ya miqe yabarta gun a tsaye......
Tunda haleema taji zancen auren hafsat da say zeyi seta tashi hankalinta ta sani sarai boka ya sanar mata ba ita ba haihuwa har abada sannan kuma gashi yanzu sam asiri ya dena tasiri akan sa,bokansu ya sanar musu sun sanar mata cewar lallai ya riqe addininsa yafi karfinsu ko kusantar sa ma gaba daya bazasu iyaba, wurin ummansu taje ta zayyane mata komai atake kuwa aka shirya cewan ayi airin akan hafsat gaba daya tunda itace banza.....hmmmmm
Say yana zaune tare da hafsat suna hira muhammad ya shigo cikeda taqama yaud'inma acikin shigarsa ta shadda fara amma ba babbar riga bace, yau dinkine dai na zamani me kyau komai nasa fari,hannu ya miqa masa suka gaisa sannan ya mayarda dubansa akan hafsat da alokaci daya qirjinta ya soma dokawa
"Hafsat ya jikin ki?" kallon sa tayi tace
"Naji sauqi Alhamdulillah" shiru sukayi dukansu su uku can muhammad yace "Ke baki iya gaisuwa bane,ko bakisan girman manya bane?" idon tane ya ciciko sannan tace
"Kayi hakuri yaa muhammad" dan guntun tsaki yaja sannan yace
"Mesa zakiyi karyan bakya gani kuma bayan sarai idanki lapiyanshi qalau,bayan yanzu gashinan kina kallo na kuma kallo daya na miki na tabbatar kina gani kema kuma kina kallo na ido cikin ido duk sanda nayi magana" shiru tayi yayinda say ya miqe tsaye yace
"Amma yallabai anya bakayi shishigi da yawa ba kuwa,baka ganin cewar mu doctors mune mukeda haqqin komai nata bawai kaiba,kuma mun tabbatar cewar idan nata bashida lapiya kai miye naka aciki? Kuma idan taimakonta zakayi mu bawai mun kasa bane ka barshi kawai mune family nata zamu mata komai ma har fita wajen" shiru ne ya ratsa wurin dukkansu sun bata dakiku suna kallon juna kafin muhammad yace
"mesa arayuwa zaka kalli girma na kace zaka kirb'a mun k'arya,zanyi magana a d'aga licence dinka na zama likita idan dai har tsabar hauka wannan idan ne zaka ce baya gani" jin ankira hauka ya sanya say ya dago da fuskarsa gaba daya cikeda fusata
"Kai waye? Mekake taqama dashi? Me kuma kakejin ka isa kayi da zaka kalli tsabar idona kace dani mahaukaci,dakake iqirarin cewar zaka sanya akarbe license dina mesa kai bazaka qwace ba idan ka isa,tunda nake ganin mahaukata bantaba ganin mara hankali irin kaba,tayaya zaka kalli idan mutum kace masa mahaukaci beside waye ma ya baka damar yi mana iko anan?" wani murmushin qasaita yayi sannan ya shafi gemunsa yace
"Ba license d'inka ba har abu mafi muhimmanci arayuwarka zan iya kwace wa shine rayuwarka,kuma wlhy kaf fadin Nigeria ba wanda ya isa yamun komai,kuma zaka gani wlhy,ke kuma karna dawo asibitin baki gayawa doctors masu hankali kina gani dakyau ba" yana gama fad'ar hakan ya juya ya fita hafsat ta kasa koda motsi dakyar ta hadiye wasu yawu sannan ta furta
"kayi hakuri uncle say ka rabu dashi,wannan mutumin na tsaneshi wlhy" matsowa yayi kusa da ita yace "Mesa nakejin matukar tsoro da yawaitar fad'uwar gaba hafsat? Gabaki daya banjin dadin tawa rayuwar sekace nine nake ciwo,wlhy hafsat hankalina baya kwance,bawai wannan muhammad dinba da kalamansa aa, komai ma senake ga kamar mutuwa zanyi ayanda nakejin duniyar tanamun qunci" zare idanta tayi waje
"Haba Uncle sayyeed? Ya kake magana haka? Inshaa Allah atare zamu rayu babu abunda ze sameka,kuma inshaa Allah atare zamu mutu" murmushi ya sakar mata yace
"Zanje gida na dawo nanba jimawa inshaa Allah" batayi magana ba haka yaja kofar ya fita, ita dinma dai haka kawai takejin tsananin faduwar gaba me tsanani,hankalinta sam baya jikinta,koda momy tazo bayan isha abinci kurin tabata sukayi sallah seta kwanta,say yazo sun dan taba hira,wuraren karfe tara yamata sallama akan seda safe ze dawo,har kuma ze fita ya dawo ya kalketa yace
"Hafsat idan har Allah yasanya wani abun yafaru dani kimin adu'a ita kadaice nake buqata agareki" kura masa ido tayi dukta rude murya na rawa ta furta
" mesa kake irin wannan tunanin wai? Sabida kawai wannan muhammad din yayi wannan furucin seka damu,inshaa Allah ba abunda ze iya yi maka" murmushi ya sakar mata
"Hafsa nafasan waye muhammad,sam yayi furucin dayayi ne sabida kawai ransa ya b'aci amma mutum ne me nagarta sosai,matsalar sa d'aya kafirar zuciya da rashin human relation amma hes a nice person" shiru ta masa kawai amma bawai danta yarda ba,tanaso ta tsani muhammad dinnan amma zuciyarta taqi aminta da tsanar tasan......
Wuraren sha dayan dare unle say ya dawo wurin hafsat,zama yayi kusa da ita yamata a dua lokacin tamayi bacci sannan ya kashe fitilar dakin ya fito ganin ko momy bacci ya kwashe ta batare data kashe fitilar ba,yana barin dakin ya kula da mutumin daya wuce part din fuskarsa a rufe da mask se suaune kansa yakeyi,harya wuce kuma seyakasa nutsuwa ya dawo baya gaba daya,binsa yayi yaga lallai dakin ya dosa,ya murda sad'af sad'af ya shige aikam say da sauri ya biyo bayansa shima yafada dakin,ganin yayi mutumin ya dauki filo ya danne fuskar hafsa se shura kafa takeyi acikin duhun dakin,kuka kura yayi yayi kanshi aikam fada ya kaure har suka tashi momy,da sauri ta haska torch light dinta tana ganin haka ta kunna fitilar dakin kokawa suke sosai da sauri ta kwallah kara,amma kan wani ya farga kasancewar darene har mutuminnan ya daga wuqa ya cakawa uncle say a qahon zuci har wurare biyu......ko kafin mutane su zo wancan mutumin ya gudu,hafsat ma ta farka tuni sakkowa tayi tama manta zancen karaya,sayyeed kuwa tuni rayuwa tayi halinta,se kuka takeyi tamkar ranta ze fita a haka doctors dake nan sukaxo,kowa se hawaye yakeyi ana fadar mutuwarsa ....
Mom nuaiym
[2/9, 8:55 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅
Love story 2018
Billy galadanchi
*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)
Wattpadd@ 68billygaladanchi
*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*
23
Ba shakka hafsat ta gama haukacewa da mutuwar uncle say,tsakani da Allah tanki tana gani aka fita da gawarsa wanda ko ba'a gaya mata ba ta tabbatar wlhy ya mutu,ko dan ganin jinin daya zuba ajikinsa, kasa zama tayi asibiti dole aka wuce da ita gidansu.......tunda hafsa taje gida take kuka ba qaqqautawa shi kanshi shaam din ya girgiza da mutuwar sayyeed,musamman da yake ko a dakin da hafsat take aka kashe shi,kuma ita bata gane wanda ya danne mata fuska ba da filo,kasancewar acikin dubu ne farkawar momy ne ta ga sayyeed.....
Da yamma yan sanda sukazo gunsu da tambayoyi kallon ta sukayi bayan ta momy ta gama fadar iya abunda ta sani suka ce da hafsat
"Hafsat dukda yake munsha mamakin ance kinada matsalar ido,amma se gashi faruwar abinnan idon naki ya bude,muna san sanin shin sanda abun ya faru kina ganine? Ko kuma aa bayan faruwar abun kika soma gani" kallon dan sandan tayi gaba daya gani tayi ya gama raina mata idan dai har karatun datayi na lauya harta zama qwararriya ba shirme bane a yanda ta fahimci kalamansa zarkin nasa akanta ya fara shi
"Tun ranar danayi a hatsari na farfado komai ina ganinsa lapiya lau" gyaran zamansa yayi ya kalleta sannan yace
"To meyasanya likitoci sukace bakya gani,kema kuma kike ta faman pretending?" kallonshi tayi shima sanda ya razana da kallon sannan tace.."Banasan auren yaa shaam,shikuwa so yake na aureshi sabida wata manufa tashi da ban santa ba,nakuma san ba dan Allah bane da wannan yaje ya sanya kakanmu tace dole sena aureshi,ranar dana samu accident ranar naji doctor yana wa su daddy bayanin cewar idan har na farfado idona ya sake tabuwa baze gyaruba,kasancewar shine na biyu,daganan dabara tazomun ta nunawa duniya cewar bana gani sabida nasan yaa shammaz baze aureniba ina naqasashiya,uncle say da abokinsa Dr.shuraim sunsan ina gani tangaram dama shirine se bayan na auri zabina sannan kowa yasan ina gani clear" nisawa kowa dake wurin yayi ganin tana fad'ar gaskiar ta kai tsaye,police din ya sake cewa
"Menene zaki iya tuna ya faru a daren jiya?" hawayen daya gangaro mata ta saka hannunta ta share sannan tace
" Kawai dai nasan munyi sallama da uncle say tun karfe tara na dare akan se washe gari,daganan yana fita na kwanta nayi bacci,acikin baccin ne naji an sakamun pillow a danne mun fuska sosai bana iya numfashi,can kuma sena ji an sakeni na sanya hannuna da ke lapiya na janye pillow din amma sabida yanayin dakin ba wadatar haske banga komai ba seda momy ta farka ta haska torchlight jin hayaniya,ananne naga uncle say da wannan mutumin me mask a fuska suna kokawa,harya caka masa wukar,kuma kan momy tayi wani yunkuri mutumin ya fita da gudu,amma fa ni naga face d'insa asanda uncle yaji azabar ya caka masa wuqa ya da damko face mask din wacce ina saran tana hannunku" nisawa police din yayi yace
"mungode da amsoshinki kai tsaye,dakuma hadin kai,muna fatar idan muka dawo zamu samu hadin kanki idan buqatar hakan ya taso" a fusace ta miqe tace
"Sabida yana da kudi? Ko sabida yana taqama da isa dacewar shidin wanine ze kashe mun muji ya zauna lapiya,ku sani akwai sadakin sayyees akaina wanda yake nuni ya kuma isa hujjar kasancewata matarsa sabida haka wlhy sena ga karshen shari'ar nan,matsayi na na cikakkiyar lauya nice zanyi bincike me ma'ana idan har ku bazakuyi ba" cikeda rashin fahimta suka kalli juna sannan dayan yace
"Ban gmfahim ceki ba?" atake ta zayyane musu abubuwan dasuka faru tsakanin muhammad da sayyeed da kuma furucin muhammad ta qara da cewar "A shari'ance muhammad ya aikata babban kuskura furta wannan kalamin kawai balanta na yakai ga aikatawa,nice zan sameshi da nawa tuhumar nice zan bincikeshi dan kaina ina ikon tsayawa kaina nima din cikakkiyar lauya ce meji da kanta" kallonta mutumin yakumayi yacewa
"haj amma ina ganin kamar Barrister muhammad kike magana ko?,a iya sanina dai shine mutumin da akace ya kade ki,kuma babban lauya ne da ake fafatawa dashi a fadin kasar nan gaba daya" tsaki taja ta sanya hannunta me lapiya ta bubbuga kirjinta
"Sabida yana taqamar shi babban lauyane seya kashe mutum? To nima babbat lauyace ta kaina,kuma wlhy senabi jinin mijina" shiru sukayi ganin yarinyar nacikin zafin mutuwar....
*Bayan kwana uku*
Shirin ta tayi tsaf kasancewar mahaifinta yamata komai na lauya me zaman kanta bata gwamnati ba,domin kare haqqin sayyeed daya mutu akanta,kai tsaye gidan Barrister muhammad jalalludeen Auwal yana zaune a harabar gidansa yana kurbar lemo a hankali cikeda yanga,dama kuma yasan da zuwanta kuma police ma sunzo sunyi nasu har sun wuce,har a news paper an sanya tuhimarsa da yake wanda wannan ko kadan be daga masa hankali ba sam sabida yasan meya taka hmmmm.....A yangace ta fito daga cikin motar zuwa inda yake zaune shi kuwa tun daga nesa yake kallonta yana wani murmushin kin rainawa kanki hankali,Tana zuwa ya miqe tsaye sinfi mintuna biyu suna kallon juna,hannu ya miqa mata,sanda tabi hannun nashi da kallo sannan a wulaknace ta miqa masa nata yace cikin muryarsa me tarwatsa littafinta
"Bar.muhammad j Auwal AkA j.A" murmushi tasaki me ban haushi ta furta a yangace
"Bar. Hafsat muhammad gaya AKA Miss poojah" murmushi ya sake meban dariya
"Nice meeting u young barrister"
"Nice meeting u too the oldest one" murmushin ya sakeyi tace "ina fatan kasamu labarin suing naka damuka yi a court,ina kuma fatan ka nemi qwararren lauya macecinka" juice ya dauko ya kurba sannan ya zauna ya kalleta ya nuna mata da hannu kujera
"Have a sit miss poojah" zama tayi ta dauki cup na juice da hannunta me lapiya ta kurba sannan ta kai dubanta zuwa gareshi tace
"Bakace komai ba" sanda yaja numfashi sannan yace
"Hafsat lallai kin dakkowa kanki abunda bazaki iya karasawa ina so ki sani bakin rijiya fa ba wurin wasan makaho bane,ni dinnan nafi karfin tunanin ki wlhy"Murmushi tayi har haqwaranta suka bayyana sannan tace
"Tabbas zancenka dutse ne Br. J.A,Amma ina san ka sani wlhy bazan saurara maka ba harse naga bayanka" cup dinshi ya dire akan table yace cikin nutsuwa batare daya kalli inda take ba
"Miss poojah courage dinki yana burgeni sosai,abinda nakeso dake shine wannan fafatwar tamu ta zama deal" kallonshi tayi ta kauda kanta gefe batayi magana ba yace
"Idan har kikayi wining case dinnan zan karbi hukuncin kisa kuma zan mallakamiki daukacin dukiyar dana mallaka fiye da rabinta zan baki,dukkanin abubuwan dana gada awurin mahaifina kuwa kashi uku zan masa in baki kashi biyu in yarona daya tilo dayan kashin,idan kuwa har nine nayi wining wannan case to kuwa ko kina so ko bakyaso sekin aureni" da sauri ta dago ta kalleshi taga shidin ba ita yake kallo ba,sai saita kanta tayi ganin deal din ba wani babba bane kasancewar tanada yaqinin shi yayi kisan kuma zata diddigo abun,tace
"Na amince da wannan kuma zanyi" ta miqe kallonta yayi yace
"Bakida wayo,shiyasanya nace dake bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane ai,an tab'a deal ba'a rubuceba idan na cuceki fa? Zama zakiyi mu rubuta muyi sighning inada photocophy machine se nabaki copy daya nima na ajiye dayan kuma ke zan baiwa orijinal ma" yafada yana murmushi kauda kanta gefe tayi sannan ta zauna amma sam bata karayaba,sanda suka gama komai sannan ya miqa mata hannu yace
"Deal?" murmushin yaqe ta masa tace
"Deal" daganan ta karba ta juya yace
"Semun hadu a court poor poojah" juyowa tayi ta washe masa baki sannan tayi gaba abunta ta shige mota sukayi gaba,ya koma ya zauna yace "Smart poojah".
Toophaaa jama'a wasa farin girki yanzu ake book kam,yanzu race ya fara.
Idan kaji dadin wannan page dan Allah comment and vote.....
[2/10, 10:05 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅
Love story 2018
Billy galadanchi
*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)
Wattpadd@ 68billygaladanchi
*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*
24
Tunda hafsat ta koma gida take nazarin abubuwan da suka shiga tsakaninta da J.A sam bata ankare da wautar data aikata ba se yanzu,idan ya kasance shi yayi wining na case din fa? Ko kuma ya kasance ba shi bane yayi kisan fa?" wani tsoro ne ya shigeta lokaci d'aya qirjinta ya soma wani irin dokawa,dafe kanta tayi ta shiga rero adu'o i kala kala na tsari.....
Brr. J.A kuwa bayan fitar hafsat a fusace shima ya fita,be tsaya ko ina ba se asibitin uduth kai tsaye wurin masu bada katin shiga wurin ya nufa bayan sun gaisa ya nuna musu ID card d'insa sannan yace
"Nazo bincike ne akan wani case na murder da aka samu anan asibitin kwanakin baya,ina matukar buqatar had'in kanku domin tallafawa family d'in wannan babban rashin ba bisa haqqi ba,nima kuma da ake zargi ku taimakamun matsayin na na baban lauya me matsayi ace ana zargina da kisan kai" sosai suka fahimce shi dama mutane da dama sun dad'e da qaryata zancen zargin da ake masa kasancewar mutane da dama sunsan halinsa na nagarta, babban cikinsu yace "Wane taimakao kakeso mu maka yallab'ai?" gyaran zaman madubinsa yayi sannan yace
"Record nakeso na dukkanin motocin dasuka shigo asibitin nan aranar 11/11/2016 tunda shabiyun daren shigar ranar har zuwa shabiyun daren wucewar ranar,na kuma san kunada cctv camera anan so idan ba damuwa ina buqatar video d'in" gyaran zama ogan nasu yayi sannan yace dashi
"Dama plate number ne muke d'auka mubaka card na shiga,se kuma sunan motar da color dinta da model number na motar,cctv kuwa yana daukar shiga da fice na kowa a asibitin nan,sabida haka yallab'ai komai daya dace zamu baka inshaa Allah" godiya ya masa sannan yashiga tattare muhimman informations da aka lokaci daya ya harbo bakin zaren.........
Shammaz kuwa tunda abun yafaru yakejin wani tausayin hafsat,a qasan zuciyarsa kuwa yanajin wani iri tamkar laifin sane komai,zuwa yayi ya samu haj Innah ya sanar mata yafasa auren hafsat baya santa kuma ta janye qudirinta,dama ita tunda taji cewar sabida auren sa da aka ambata hafsat ta gigice harta samu hatsari ta kudurta aranta bazata qara wannan furucinba kuma idan ma hafsat taji sauqi zatace abata zab'inta,shi kenan kuwa ta amince wa shaam akan ya gayawa iyayensu......
*Court*
Hafsat ce a zaune tare da lauyan me kare J.A se wasu lauyoyin guda biyu,acikin babban court dake jihar sokoto,Justice d'inne ya rero bayanin zargin da akewa Brr. J.A tare da baiwa masu qara damar bayyana hujjojinsu daya sanya suke zarkin sa da kashe likitan,batare da bata lokaci ba hafsat ta zayyane komai daya faru agabanta ta qara da cewar
"Furucin sa kad'ai ya isa ya nuna mana cewar shine yayi kisannan" dayan lauya din me kare wanda ake qara ne ya miqe yace
"Objection my load" kallon sa justice din yayi shikuwa yaci gaba
"my load be kamata lauyan wanda suke qara ya riqa alaqanta laifin kisan kai kacokam ga wanda ake zargi ba,tunda ai zargin sa ake bawai an tabbatar ba" justice ya kalli hafsat yace "A kiyaye" ya sake kallon Brr. Khaleed yace
" yallab'ai zamu so akara mana lokaci kadan domin gabatar da shedunmu kuma zasu so a gayyato mana babban Abokin marigayin anan wato Dr. Shuraim" dama aka basu daganan aka d'age zaman sena da sati d'aya.
*Bayan sati d'aya*
Lauyan wanda ake qara ne yace fara magana kamar haka
"My load wannan gabaki d'aya record ne na motocin dasuka shiga asibitin ranar da abun ya faru,acikin mun samu mota iri daya kirar honda civic kalar ja wacce aranar tashiga asibitin kusan 7 times a wannan ranar cctv camera ta main gate data ward din da akayi kisan duk sun tabbatar mana da shigar mamalakin motar so bakwai a wunin ranar, kuma duk shigar sa kai tsaye ward d'in yake nufa wato inda sin din ya faru kuma mayannin dayayi duka ba face mask a fuskarsa se ziyartarsa ta karshe inda har yayi nasarar hallakar da sayyeed,sannan kuma a binciken da muka gabatar,makashin yaje kashe hafsat ne ita kadai bawai da sayyeed,sabida sayyeed ba asibiti bane gidansa,kuma idan ma kasheshi zeyi sedai yaje gidansa ya kashesa acan,abinda muka sani shine sayyeed taimako yaje a yanda muka gani a camera shine harya fito ya ganshi ya shiga seya bisa a baya,abinda camera ta kasa nuna mana shine menene ya soma faruwa acikin dakin kasancewar babu wadatuwar haske ya sanya se bayan yayi kisan ya juya ze fita haske ya wadata kuma har fuskarsa mun gani,abunda masu qara sukace wanda yaje kisan hafsat itace wacce yafara dosawa pillow a fuska kafin sayyeed ya cece ta,idan ko har hakane furucin da muhammad yayi sam bashida alaqa da wannan kisan na sayyeed" shiru yayi hafsat gaba daya kanta ya daure sabida batayi wannan tunanin ba shi kuwa yaci gaba
"Munyi nasarar cafke wanda yayi kisan,kuma munaso yazo nan da bakin sa yayi bayanin wanda ya sakashi kisan idan har kotu ta bamu damar yin hakan" izini. Aka basu akan su gabatar da mutumin......koda alqali ya tambayi mutumin seya fara bayani kamar haka
"Da farko dai sunana kamilu,kuma ni dan area boy ne ina zamane a unguwar iraqi dake cikin garin sokoto,ina zama wani likita me suna shuraim yazo ya sameni akan yanaso in masa aiki akan wata mara lapiya me suna hafsat,ni kuwa dama ba ruwana aiki ko wane irine indai na kudine to kuwa zan yishi yabani details na komai da komai na dakin datake da time da babu yawaitar mutane awurin yakuma ce na danneta da pillow sabida gudun zargi ganin zan samu kudi ya sanya na amsa tayinsa naje nagama monitoring na wurin da komai,nashirya rana daya naje,shine qaddara ya fadowa wanda yazo tare fadan na kasheshi da wuqa ta,shine wayannan suka bi ta hanyar kotar danake hawa suka kamoni" jinjina kai kowa keyi yayinda hafsat ta rikice tabbas wannan shine mutumin data gani kuwa,dama sun buqaci ganin shuraim shi kuwa be karaji daga wurin wannan mutuminba so bezata hakan zata faru ba,koda aka buqaci yazo beyi gaddama yazo a rude ,tambayar sa akayi dalilin san kashe hafsat baiwar Allah yafara magana kamar haka
"Na kasance ina matukar san yarinyar tun tana secondry schoool amma ta wulakantani,har kuka nake mata amma bata damu dani ba,ganin nayi nayi taqi kulani yasanya nashiga malamai na sanya duk wani namiji idan ya kalleta zeji yana matukar tsanarta idan kuwa me riqon addinine yafara santa semu saka masa mafarkai na tsoro akan zamu kashe duka su biyun harse yagaji ya kyaleta,kwatsam mukazo asirinmu damuke mata ya dena tasiri bincike ya nuna mata an mata magani kuma turarukan datake using ba wani aljanin daze iya rab'ar inda take ma, da wannan naji zuciyata tanamun zafi a yanda nakesan hafsat lallai na qudurta araina idan har ban sameta ba to kuwa bazan taba bari ta mori wata rayuwa da wani namiji ba,a wannan karon kuwa naga bazan iya kashe abokina ba kuma asirin yaqi cinsu shine nayi amfani da damar kwanciyar ta asibiti na aikata hakan,amma wlhy nayi nadama musamman rashi aminina na sosai sosai" shiru aka danyi kan mutane su fara mamakin dan wannan guntun laifin ze saka tsabar rashin imani ka kashe mace har lahira,hukuncin daya dace dashi aka yanka mai aka tarwatse karar aka kuma gargadi muhammad akan furucinsa daya janyo masa cin zarafi.......
*Washe gari*
Tsaf J.A ya shirya yaje gidan su hafsat a parlor akai masa masauki,sannan akaje kiran hafsat,jiki a mace ta sakko yana ganin ta ya miqe tsaye yazo suna fuskantar juna yace
"Bakin rijiya poor barrister,the youngest one,nazone in sanar miki ki gayawa iyayen ki one week kawai na saka d'aurin auren mu,lokaci yakusa zuwa dazaki san waye muhammad,menene kuma matsayin wanda ya tozartar dashi yakuma bata masa suna a idan duniya" wasu miyau ta hadiya masu dacin gaske ta runtse idonta sosai ta bude su a hankali sannan tace
"Kayi hakuri muhammad" bece komai ba ya miko mata waya kirar iphone 6 yace zan miki waya,idan buqatar hakan ya taso,yana gama fadar hakan ya juya a nan ta durqushe ta saka kuka me tsuma zuciya.....
Mom nuaiym
[2/11, 8:52 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅
Love story 2018
Billy galadanchi
*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)
Wattpadd@ 68billygaladanchi
*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*
25
Da k'yar ta iya lallasr kanta tayi ciki,tarasa wazata tunkara da wannan maganar a duniya,ganin shirun baze amfaneta da komai ba ya sanya for the first time tun bayan rabuwarta da yaa shaam ta d'aga waya ta kirasa,mamakin ganin sunan ta yayi amma seya dauka da sauri ya kara a kunne tare da cewa
"Hafst ya jikinki" amaimakon ta ansa shi se kawai ta saka masa kuka,mamakin jin kukan tane ya kamashi yace cikin rud'u
"Subhanallah hafsat meya faru? Bakida lapiyane ko kuma shari'an ne be miki ba mu d'aukaka qara?" cikin sheshekar kuka tace
"Dan Allah idan baka komai mu hadu a season 7 park,inaso muyi wata magana dakai ne" batare da bata lokaci ba yace "Babu damuwa in the nxt 25 mnts zan isa wurin"
"To yaa shaam nima a haka" da kanta tayi tuqi tana isa wurin ta tarar ya rigata aranta ta ayyana wata qila yana kusa da gun dama,motarshi ta nufa kai tsaye ta bud'e gidan gaba ta zauna,gaidashi tayi sannan ta miqa masa takarda,cikeda mamakin takardar meye ya karb'a ya bud'e zare ido yayi bayan kammala karatun takardar sannan yace yana kallonta
"Hafsat se yaushe zakiyi hankali ne wai e? Mesa komai naki bakya san ki saka tunanin mezeje ya dawo aranki? Yanzu gashi kin janyowa kanki sabida babu wani wanda ya isa ya watse wannan maganar yanzu,kuma sanin kanki ne j.A babban lauya ne wanda ya shahara a fannin iya shari'a,ni bawai auren sa bane banso kiyi sabi kowa ya masa shaidar halayya ta kwarai kuma sosai reputation dinsa ya girgiza da faruwar wannan abun waya sani koda wata manufar ze aureki ta cutar wa? Babban burina shine ki samu nutsuwa a gidan mijinki wannan shine dalilin daya sanya sam kikaga na janye zancen aurenki da zanyi sabida na tabbatar wa kaina bazaki tab'a samun nutsuwa dani ba musamman akan halima,yanzu sanar dani yaya kikeso muyi kuma yazo miki da wata maganar ne?" Kallonshi tayi tama kasa kukan yanzu kam tace
"Yazo da yamman nan,yake cewa dani wai nagaya wa su daddy aure nan da sati daya yakeso kuma zan fahimci ba'a cin zarafinsa a zauna lapiya,har ya bani wannan wayar akan zemun waya idan buqatar hakan ya taso" nisawa yayi yace
"Hafsat gaskia kinyi kuskure da kika aikata wannan shirmen,babu abinda zakiyi illah kije ki gayawansu daddy ayi masa yanda yakeso kije kiyita hakuri,danni nan matsalolin dakike fuskanta suna daukarmun hankali bamu sani ba ko wannan auren dazakuyi dashi ya zamo sanadiyar jin dadin na har abada ta yiyu ma adu'ar iyayen mu ne Allah ya karba zakiji dadi" kallonshi tayi qirjinta na dokawa tace
"Baka tunanin cewar wani zargi ze iya shiga tsakani na da mutane? Baka ganin wasu ma zasu iya cewa hadin bakine kisan da aka yiwa sayyeed nida muhammad? Baka ganin kuma idan sun fada haka basuyi karya ba,muhammad so yake ya batan suna nima so yakeyi gaba daya nima duniya ta zageni,idan har na yadda da zancen aurennan tofa wlhy kowa zega tamkar ban damu da mutuwar sayyeed bane musamman lokacin nan daya diba kadan,dama ace nanda watanni hudu yace ko biyar"
"Hafsat kije ki lallab'asa da dabarunku na mata cikeda hikima sabida ya yarda abar auren har nan da koda watanni uku ne,kuma kije gidansu sayyeed na nan garin ki nunawa mahaifinsa wannan takardar ta yar jejeniya ,shima mahaifin na say kizo masa da hikima ta hanyar rokarsa akan ya nema miki alfarmar muhammad ya janye wannan agrement din ya hakura da auren ki,ta wannan hanyar kadai zaki tsira da mutuncin ki a wurin iyayen sayyeed koda kuwa an daura auren nanda sati daya" jinjina kanta tayi cikeda gamsuwa da bayaninsa
"Yaa shaam dan Allah mana muje gida na ajiye motana muyi sallan magrib in yaso ka rakani gun baban sayyeed ni tsoron wannan muhammad din nakeyi wataqil idan ya aureni ma mutuwa kawai zanyi" murmushi yayi yace "Kece mutuwan ai,sekace wani dodo".......
Bayan ta gama yiwa mahaifin sayyeed bayani yakuma ga takardar murmushi ya sake yace
"'yata wannan muhammad din yana sani ya miki haka,sabida yasan bashi bane yayi kisan so kekuma bakida wani hujjan dazaki iya cewa aa bayan an gama shari'ar,shawarata anan shine kije ki lallab'ashi" kallon dattijon tayi tace
"Daddy dan Allah ka bashi hakuri akan ya janye wannan zancen nidai bana sansa,kuma idan su daddy sukaji nayi wannan shirmen bazanji da dad'i ba" kallon ta yayi shima yace "To hafat kije gobe zan sameshi da kaina,suna kokarin barin wurin kanwar sayyeed datazo hutu daga india ta shigo,se kallon shammaz takeyi,suna fita ta biyo bayansu da suruun ganin hafsat,a can tace da hafsat
"T loojah waye wannan?" hafsa tayi sannan tace "Bros shaam my big bros kenan"murmushi tayi
"hes handsome ina sansa kuwa?" zare ido hafsat tayi
"Da gaske Baby?"
"Ea mana da gaske wlhy" murmushi tamata tace "Idan zaki auresa shikenan sena gaya masa" dariya tayi tace "Zan aure sa mana ai yafiki kyau" haka dai suka rabu baby se matsawa take da zancen shaam,koda sukaje mota hafsat ta gaya masa dariya yayi yace
"Ina ni ina ba indiya rufamun asiri" cike da zolaya tace
"Kai yaa shaam banda boye boye fa,Allah ina ganinka se wani kallonta kake kana murmushi" dariya yayi yace "Ina wasa dake zan mareki wlhy" seda sukaje gidan sannan ya karbi numer din baby haka kawai yakejin yarinyar ta masa wannan zankadediyar yarinyar lolxx.
Qememe muhammad ya kafe akan lallai baze janye qudirin saba kuma nanda sati daya zeyi auren danita,su daddy hankinsu ya tashi kowa gani yakeyi auren manufa ne na rama sunansa da aka nemi batawa zeyi.
Waya kawai ya kira hafsat bayan magaribar ranar yace da ita ta sameshi a mota,tana zuwa ta shiga gefen me zaman banza ta gaidashi,fitilar motar ya kunna fiskarsa ba yabo ba fallasa yakai hannunshi ya daga hannunta dake ciwo,dan kara ta saki ya juyo ya kalleta itama d'in shi take kallo harta soma kwallah,dauke kanshi yayi sannan yace da ita
"Har yanzu hannun nan be gama dawowa daidai bako?" batace dashi komai ba se hawaye,tausayin kanta takeji sabida sosai take tsoron muhammad,hannu ya saka ya share mata hawayen daya gangaro mata yace bayan ya dauke kanshi
"Mesa kike kuka hafsa? Banasan ganin saukar tsadadden hawayenki yana zuba a banza kinji" sauke kwayar idonta tayi kasa batayi magana ba,ya sake cewa
"Yanzu sanar dani me dame kike buqata,bazakiyi shagalin biki ba,ni zanyi dinner da reception sabida yanzu ne zanyi auren soyayya na kuma zab'ina" kallon shi tayi tana kuka tace
"yaa muhammad dan Allah kayi hakuri" dagowa yayi a karo na farko "Hakurin me kike bani" kukan ta ne ya tsananta ta dukar da kanta taci gaba da yi,tafi minti talatin tana kuka amma bece da ita komai ba seda dan kanta tayi shiru,kanta ne ya soma sara mata ta bud'e mitar da nufin wucewa cikin gida yace cikin izzah
"Nine nace dake na gaji dajin wannan zazzaqar waqar da kika sakani agaba kina reramun? Maza dawo kici gaba dayi harse ya isheni" kallonshi tayi cikeda mamaki idanta ya kad'a yayi jajir,yakuma cewa
"Dawo mana nace ki rufe murfin" a hankali ta sako kafafunta ciki batare da tayi magana ba
"Kalli idanki hafsat,duk yayi ja sabida bakyajin magana,nace dake kukan na menene amma kinki ji,kin zauna kina kuka sekace wacce ke rero waqa,idan ba so kike na sassab'a miki ba karna kuma ganin hawayenki wlhy,sanar dani yanzu tsakanin ki da Allah menene kikewa kukan?" sadda kanta tayi kasa tace "Auren ne bana so" kallonta yayi ya sakar mata murmushi
"Banida maganin wannan gaskia,so kiyita kukan,shika d'aine damuwar kodai da wata bayan wannan?" sadda kanta tai a qasa tace
"So nakeyi ka tausayawa rayuwa ta ka agazamun ka bar aurennan har nan da wata biyu na roqe ka yaa muhammad dan Allah" kura mata ido yayi na yan dakiku kan yace
"sekin mun alqawari guda biyu,tsakaninki da Allah" kallonshi tayi amma batace dashi komai ba yace
"Na farko sekinmun alqawarin bazaki taba kawo matsala me kamada kin fasa auren ba idan na qara miki lokaci,na biyu kuma sekin mun alqawarin bazaki sakeyin kukannan agaba naba sabida gaskia banaso yana batan rai" yawu ta had'iya tace
"Abba haris ya sanar dani muhimmancin Alqwari sabida haka bazan taba fasa auren kaba,sedai idan kaine kace ka fasa,kukan ma zan kwatanta" gyada kanshi yayi yace
"Nima ai alqawarin auren ki nayi,idan ko bazaki karya ba ni mezesa na karya, nasan muhimmancin alqawari ai,kije na yadda nanda watanni uku idan munada rayuwa se ayi auren" godiya ta masa ya tsare ta akan setayi dariya seda tayi dariyar kuwa sannan suka rabu,se dadi takeji......
Shaam ba kad'an ba yake jin yana san baby,sedai be sanar da kowa zancen ba se daddy kasance war shi abba haris har wannan lokacin fushi yake dashi,sedama hafsa ta saka baki yake dan sake masa kadan,cikin sirri kuwa aka shirya auren sa da baby tare da nasu hafsa,sam haleemah batasan wainar da ake toyawa ba,tunda taji hafsa zata auri wani shikenan hankalinta ya kwanta......
Hafsa gabaki daya ta rame tayi baqi,sam wani jarababben tsoron muhammad takeyi gashi abu mafi ban mamaki shine tunda ya tafi akan ya dage zancen aurensu be qara zuwa wurin taba kuma gabki daya ya dena kiranta,ita kuma duk sanda tayi yunqurin kiransa se gabanta ya fad'i, huda ce ta fad'o mata arai ta d'auki wayar ta kirata,komai da ake ciki ta sanar mata,hudan kuwa ta bata shawaran akan lallai ta kirasa,kuma ta basa kulawa as if tana matukar sanshi,wasan da yake so su buga idan ba ta wannan hanyarr ta biyo masa ba lallai akwai matsala,sabida ya shirya daukar fan sane,sosai tayi wa huda godiya koda sun dade basu hadu ba amma sosai suke hurda,huda yanzu tana germany itada mijinta.
Cikin sanyin jiki kuwa tayi kiransa a waya,kamar baze daga bama,se can taji muryarsa me saukar mata da fad'uwar gaba yace
"Hello" sanda ta d'anyi jimm sannan tace "Yaa muhammad Barka da yamma" gyaran murya yayi yace
"Barka dai" a ta k'aice,jikinta ne ya qarayin sanyi tace "Dafatar kana lafiya"
"Ina lafiya" itace amsar daya bata,runtse idonta tayi sannan ta kara budewa tace
"Yaa muhammad ka gane me magana kuwa" kamar baze amsata ba yace
"Na gane mana ba hafsa bace?"
"Ea nice ya kwana biyu?" tafad'a cikeda jin zafin wulakancin data janyowa kanta
"Lafiya lau,ya akayi ne?" dafe kanta tayi dayake barazanar rabe wa gida biyu tace
"Dama naga kusan watanni biyu ban jika ba,shine nace Allah ya sanya lafiya"
"Lafiya lau mana,me zan miki to? Ina auren Agreement ne zamuyi,sekace wata soyayya ke tsakaninmu dazanta damunki,kokuma daze kasance komai nawa sekin sani?" kasa hakuri tayi tace
"Koda na kirak bakaji na ambaci soyayya ba ai,danni a wannan zamanin banajin ma akwai soyayya,kurin dai kamata ya sanya nayi kiranka sabida ni nasanta" sarai ya sani magana ta gaya masa,amma seya dake yace
"Ni ai tun farko na sanar dake yanzu ne zanyi auren soyayah, kuma zab'ina bakijiba ne,kece bakya sona so meye zesanya na nanuqe miki?" jan dogon numfashi tayi sannan ta furzar da wani iska me zafi tace cikin wata rikitacciyar murya
"Yaa muhammad" shiru ya mata tace "Why?" cikin dakakkiyar murya yace
"Hafsatu manga yar sarki wacce maza ke rarrashi,koba haka taken yake ba?" ganin ze raina mata hankali ya sanya tankashe wayar ta ajiye,be kuma kiraba se qarar shigowar message taji a wayarta kamar haka
"This should the very first and last time dazaki ajiye mun waya,koda mun gama magana kuwa lallai nine zan zama na farko da zan ajiye" jikintane ya qara macewa jin kalamansa ta daga waya takuma kiransa yana d'agaba tace dashi
"Yaa muhammad kayi hakuri" cikin sanyin murya yace "wuyarta ka bani hakuri kai tsaye za'a wuce wurin,dama gobe zanzo zancen kayan lefenki ki shirya zuwa dubai"
"To Allah ya kara girma na gode sosai"
"Se anjima" shine abunda ya fada a zatonta ya ajiye wayar ashe be kashe ba,ajiye tata wayar tayi ta sanya hannunta a kirjinta ta shiga rero kuka tana sambatu ta shiga uku,ita dai batayi sa'an zuwanta duniya yazatyi da masifan yaa muhammad,tunda tasan hankalinta take kwasar bakin cikin d'a miji,da karfi ta furta
"Allah na tuba ka yafeni,Allah idan na aikata wani laifin ake jarabtana da wannan masifun Allah na tuba ka yafeni,kuma ka bani ikon cinye jarawar nan daka dauramun" kuka take sosai,muhammad dake saurarenta ma dafe kanshi yayi,ba abunda ke hanashi zuwa gun hafsa illah wannan kukan nata,ya tsani kukan ta masifaffen tausayinta yakeji,shidai bazece yana santa ba kuma bawai wata manufa ta cutar da ita yake da itaba kurun dai tausayinta yakeji yana gani kamar lallai idan ta auri wani zatasha wuya ne,tunda kuwa ya binciki tarihin rayuwar ta kaf,ya sani sarai dabe biyo mata ta wannan hanyar ba,shaam zata komawa kuma matar sa ma masiface a wurinta,kwanciya yayi ya runtse idansa yana mejin zafin zubar hawayenta.....
Menen ra'ayoyinku game da auren hafsat da muhammad? Ina tsumayin jin comments naku.
Vote plss
Mom Nu'aiym ca
[2/12, 8:21 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅
Love story 2018
Billy galadanchi
*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)
Wattpadd@ 68billygaladanchi
*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*
26
Washe gari da yamma hafsat tana kwance mero ta shigo tace da ita
"Kulele kije guest parlor muhammad yana jiranki yace wai baya samun wayanki" k'irjinta ne ya dan doka ta dago ta kalli meron
"Ke kika ganshi da kanki?" kallon ta mero tayi,batun yauba ta fahimci ko zancen muhammad akayi hafsat tsorata takeyi tausayin tane ya kamata tace tana dafa kafad'arta
"Inshaa Allah babu abinda ze sameki,kuma inaji ajikina tarayyarki da wannan muhammad d'in alkhairi ne mutum ne me nagarta sosai na kula da hakan tun a yanayin gaisawar da yakeyi da mutane,dan Allah ki saisaita nutsuwarki gu d'aya" batace komai ba ta sanya hijab dinta ta sauka zuwa qasan......Da sallama ta shiga parlor d'in kanta a kasa,ansawa yayi batare daya kalli inda take ba,karasowa tayi ta zauna kusa a kujerar dake fuskantar tasa tace
"Ina wuni yaa muhammad?" Amaimakon ya amsa ta seya wurgo mata tambaya
"Mesa kika kashe wayanki,bayan na sanr dake tun jiya yau zanzo?" kanta a kasa yayinda qirjinta keci gaba da uban dokawa tace
"Banida caji ne"
"Bakuda wutane?" ya wurgo mata wannan tambayar cikin tane ya juya ta dago da sauri suka had'a ido saurin janye nata idan tayi sannan tace
"Da Akwai wuta caja nane ya lala ce" D'an kishin gida yayi sannan yace
"Mesa baki saka layinki a wayan dana baki ba,kumama mesa bakya amfani da ita tunda na kawo miki ita da layine a ciki"
"Kayi hakuri" shine abunda ta furta,ya tsani wannan ban haqurin na hafsat wlhy ita komai se ban hakuri qara tubire fuskar sa yayi yace
"Zancen zuwa dubai ne had'o kayan lefe,idan ina irqawa daidai yau saura 27 day's daurin aure,so inasan sanin keda wa kuke da intl pasport wacce ayau zaku iya tashi zuwa dubai ko gobe a misali?" kanta a qasa tace
"Nida khairiyya ne,amma inaga anan ma za'a iya siya ai base anje dubai ba" kallonta yayi na yan daqiqu sannan yace
"Ba zuwa nayi ki bani shawara ba umarnin tafiyar nake baki hafsat,abu d'ayane zaki riqe mu zauna lafiya shine rashin yimun gaddama,nine da kaina zan sanarwa da Abba haris zancen tafiyar nanda kwana biyu zakuyi tafiyar,yanzu zamuje gidan Abba haris mu karbi pasport din nata,kema ki bani naki daga can zan masa bayanin tafiyar,akwai kayan dana saka aka kawo daga saudi wasu daga dubai,suma zamuje ki duba ,kayan gidane abinda be miki ba ki fada a sauya wani" kallonshi tayi taso tace dashi ai su daddy zasu siya mata kayan daki,amma tunawa da tayi yace bayasan gaddama ya sanya taja bakinta ta guntse....
Abba haris bayan ya gama jin bayanin muhammad tare dajin cewar wannan tsarin sane kana yanaso ma aqara sati biyu akan ranar daurin auren kasancewar bayaso a samo matsala tunda tafiya na Allah ne,be masa gaddama ba sedai yace sedai suyi tafiyar tare da babbar Aunty d'insu Aunty surayya,sabida zamanto warsu mata qananun yara,zuwan na surayya kuwa shine ze dauki nauyin sa,idan har mijinta ya Aminta,kara kallon abban yayi yace
"Abba zancen kaya gida kuma,dan Allah karkuga kamar na raina iyawar ku kawai dai tsarinane nine nake siyan kayan gidana da komai,matana ta farko ma nina mata, sabida haka hafsat ma na riga na siya komai,kayan kitchen ne kawai bana siya,amma komai nine nakeyi" nisawa Abba yayi
"Bazamu hanaka yiwa matarka alkhairi ba,sedai muma haqqin mune muyiwa hafsat, gyaran daki sabida haka zamu bata kud'inta tsaba,shawarar yanda zatayi dasu kuwa ze shiga tsakanin kai da ita ne,sabida kaine mijinta" Godiya yayi sosai sannan yamasa sallama,waya yawa hafsat tafito suka kama hanyar zuwa ganin kaya,kallonta yayi sosai ya furta
"Hafsat karki qara yimun karya daga yau,a ina kika samu cajin yanzu? Kuma naga wayar kusan full ma? Bakida labarin karya ba kyau,kuma batada kad'an?" sosai taji kunya wannan ya sanya ta sauke kanta qasa tace "Insha Allah bazan kara ba kayi hakuri" murmushi yayi
"Mesa kika kashe wayar ki?" murya a kasa tace
"Nima dai yau sena tashi banso a kirani,shiyasa kawai amma ba komai" be kara cewa komai ba ita mad'in shiru tayi sanda suka isa wani qayataccen gida me kyawun gaske,tun a gaban gidan zakaga had'uwarsa da qayatuwarsa ba karya...Gate din automatic ne wannan ya sanya ya bud'e kanshi yana ganin dosowar motar, a wani farfajiyar ajiye motoci ya ajiye motarsa wanda had'uwars ba'a ma maganarta, kallon ta yayi yace "Bismillah muje ciki" Batayi musu ba kawai ta bishi suka wuce,ta bayanshi take se kallon cikar halittarsa takeyi yanayin halinsa yanayin maganarsa da uban ikon sa,wata kofa taga ya sakawa wani card lokaci d'aya ta wangale,kai tsaye ciki suka shiga tun a parlor ta raina dukiyar datake taqamar wai suna da ita,gabaki dayan parlor din komai na ciki gold ne se daukar ido yakeyi,dakuna guda biyar ne acikin gidan kuma flate ne me masifar kyau se paluka guda uku da fankacecen ktchn wanda ya gama hadewa da tsadaddiyar carbinet,gas cooker ne kawai aciki se freezer ta kwance da double door,a bed rooms din kuwa duka english bed's ne aciki,dayan dakin red and white,dayan blue wanda shi kuma akwai parlor aciki da lubby me kyau ga coffee chairs a walk way na zuwa barin,kuma komai light blue ne da white,dayan dakin purple dayan kuma pink $ white se thee green wanda aciki duk shine yafi burgeta,ko wane daki da toilet nashi,wanda a iya Bathrooms din idan aka barka zaka kwana kana kallon abubuwan ban mamaki,gidan ya hadu over bayan sun dawo parlor ne ya kalleta yace
"Hafsatu manga,sanar dani tsakani da Allah ina kike buqatar a sauya miki?inda bakyso,ma'ana abun be miki ba?" kallon shi ta d'anyi sannan tace
"Ni ko ina ma yamun ko ince yamun yawa ma,wancen corridor dinne kawai za'a saka mun console,se dining shelf dababu awurin dining,shima kuma zanwa daddy magana,nagode sosai Allah ya qara girma yakuma kara budi,Allah jikan iyaye kuma ya biya bukatocinka na alkhairi" har cikin ranshi yaji dad'in adu'arta tunawa yayi da Zainab wacce sam bata taba cewa dashi ci kanka ba duk girman alkhairin daze mata kuwa,murmushi ya sakar mata yace
"Kinsan ni kwangila na bayar bansan wai ya kamata su zauna awurin ba,yanzu kawai muje shops asiya choice naki,ba wani su daddy" kallonshi tayi
"To ai yaa muham......shhhhhh yafada hade da daura hannunsa asaman lips nashi,tunawa tayi da gargad'insa na rashin son gaddama ya sanya tayi gum da bakin nata,koda suka fito kasa hakura tayi dama hafsa akwai surutu tace dashi
"Yaa muhammad gidannan yayi kyau sosai wlhy" Bece da ita komai ba kurun murmushi ya mata......
*Bayan kwana uku*
Hakan kuwa Akayi,da hafsat da khairii da Aunty surayya suka dauki hanyar dubai a ranar wata wednesday,har suka isa suka kwana suna mamakin hali irin na muhammad,be basu ko sisin siyayyar lefenba,illah kawai tunkan su isa ya sanar dasu akwai driver daze kaisu masauki daga airport,kuma suna cin abincin wurin wanda menu kawai ake kawo wa su selecting,haushi duk ya gama kama hafsat kusamman ya da Aunty surayyah ke faman masifa akan ya rainawa mutane hankali,ko cewa akayi dashi basuda aikin yi,Wayan hafsa ne tayi qara tana dubawa taga number dinshi,a dake ta daga wayar sabida ba shakka ta shaqa yau kam,yace da ita
"Hafsat ki fito idan kina masauki ina reception na hotel din" da mamaki ta kalli Aunty surayya dake gefenta tana uban mita,sannan tace dashi "A dubai din?" tsaki yaja yace
"Noo a india,danla malama kizo ina reception ma wurin nace dake ko mun fara wasan banza ne haka?" cikin jin zafin gwasaletan da yayi tace "Kayi hakuri ganinan zuwa" kallonta surayya ta
"Keda waye kuma Ina zakije?"
"Muhammad ne wai yana wajen reception ashe yazo,kuma shi da number shi yake amfani niban sani ba" kallon ta tayi "Au dama shima zezo kika barni ina surfa mar ashar?"
"wlhy Aunty bansan zezo ba,ni kawai zancen dan rakiya yamun" jinjina kai Aunty tayi
"Wannan shegen muhammad din anyi miskilin masifa,ko wa yakewa iya shegen oho,jeki kiji" batace komai ba ta zari dan mitsitin mayafi tafito ga rigar irin straight gown din nan ne na roba ya kameta over, tun daga nesa tana ganin fuskarsa tasan akwai magana a d'an tsorace ta karaso wurin da yake,zama tayi kusa dashi a kujerar da yake tace
"Sannu da zuwa yaa muhammad ya hanya?" kallonta yayi fuskarnan a daure yace "Banasan ya hanyar ki sabida jirgi daya muka zo daku ai,sannan wlhy mintuna goma na baki ki sako sutura dan wannan bakida banbanci tsirara,idan kuma na kuma ganinki da makaman ciyar wannan shigan wlhy sena sassab'a miki,sekace ba 'yar musulmi ba" kallonshi tayi se a lokacin ta tuna yanayinta,waifa ita tayi shigar ne a zuwan tazo garin farar fata kartayi qauyanci, jiki a mace ta miqe,zuwa tayi ta cire kayan ta sako abaya baqa har qasa tayi talha ta fito,surayya na ganin yanayinta tasan shigarta yayiwa masifa amma dai vata dameta da tambaya ba,koda tazo baya nan,wayarta ta daga takirashi amma be dauka ba,anan ta zauna tafi 30 mnt be dawo ba ta qara wayar tashi gaba daya ma tajita a kashe,gwiwa a sace ta koma dakin tace da Aunty surayya wai yace gobe zasuyi magana,kallo daya surayya ta mata kuwa ta fahimci da babbar matsala.......
Washe gari tun asuba ta koma parlor tayi kiransa a waya,yana kallonta harta tsinke be daga ba, kusan 3 msd col,kawai seta fara hawaye tama rasa dalilin daya sanya take damuwa dashi zuciyarta sam batayi adalciba,data saka masa wannan tsoron na muhammad,tana cikin wannan tunanin taji qarar shigowar message
"Room no 10,2nd floor" shine abinda ya aiko mata sarai tabgane nufinsa ta sameshi acan,miqewa tayi ta saka hijab dinta tayi hanyar daze sadata da wurin....knockin tayi yazo ya bude fuskarsa a hade,gaidashi tayi sannan ya janye mata ta shige a daya daga cikin kujerun parlor din ta zauna,ta qura masa ido,shima din ita yake kallo,yaukam seda tagaji da kallon nashi ido cikin ido sannan tace "Kayi hakuri bazan qaraba inshaa Allah" amaimakon ya baiwa maganarta muhimmanci se cewa yayi da ita "Meya faru kike kirana daga yin sallan asuba?" tama rasa mezata ce masa,se kawai ta miqe "zan koma bacci zanyi" tazaci ze dakatar da ita amma bece mata komai ba harta fice,a ranta kuwa taji zafin sa sosai....
*Nigeria*
Sun dawo lapiya dauke da lefe da ban mamaki, har masifa su daddy sukayi,amma surayya tace dasu tamasa magana yace hafsa matar sace,babu kuwa wanda ze qayyade masa yawan suturun dayake buqatar wadata su da ita,kuma ya jibgo dogwayen riguna da qananun kaya over.......Aikam rana daya akayi daurin auren muhammad da hafsat,se kuma Shammaz da maryam,kuma aranar aka kai amaren biyu,wanda sam koda ma akayi auren hajia halima batada labari tana wurin gantalen ta dubai,acewarta taje saro kaya shikuwa da gayya ya ganta,yan uwanta kuwa dasuka ga pictures na ebar hankali da ba indiya se hankalinsu ya mugun tashi,amma sam basu sanar mata wai shaam yayi sabuwar amarya ba.......
Hafsat kuwa tunda yan kai Amarya suka watse wuraren karfe goma na dare seta soma jin tsoron zaman gidan ita kadai, shi kuwa be leqo bama se sha daya da rabi, Abinci ya kawo mata sannan ya sanya hannu ya yane mayafin dake jikinta ya ajiye gefe ya kalleta, "Kina bazawara wani kunya zakiji,zaki wani lullub'e fuska" sosai maganar sa ya doki qirjinta amma bata nuna masa komai ba kurun dai murmushi tayi masa,ganin haka ya sanya yace "Kici abinci kazane da drinks ga youghurt da ice cream idan zaki sha" kallon su tayi tace "Gaskia Alhamdulillah na koshi,sedai zuwa safiya" miqewa yayi be wani damuba,kizo ki kulle kofofin gidan ni zan tafi seda safe" ko motsawa batayi ba daga inda take sabida mamakin daya bata,to gidan uban wa ze kwana?" ta tambayi kanta,ganin fa tsorone ze hallakata ya sanya harya kai parlor ta rugo ta riqe masa hannu,da mamaki ya kalleta tace dashi
"Yaa muhammad zan bika dan Allah" juyowa yayi yabfuskance ta gaba daya "Ina zaki bini hafsat?"
"Inda zakaje mana"
"Ba inda zani fa, gidan zainab zanje na kwana,kishiyarki" tafi minti uku tana kallanshi, juyawa yayi ze fita ta riqe masa hannu again "Bazan iya kwana anan ni kadai ba,tsoro nakeji" murmushi yayi
"Ni ban aureki danna tayaki kwana ba hajiya,ko mun rubuta haka acikin agreement namu?" gaba ki daya tsoro ne ya taso mata ta kalleshi sosai tace cikin dakiya idanta yayi ja sosai amma batasan tayi kuka "Na tuna kuwa babu wannan acikin rubutaccen auren mu,na manta bayan signing takardar yarjejeniya da mukayi ta aure,wurin daurin auren ma mun rubuta cewar kalar auren namu na dabanne ba wanda musulunci ya tsara ba,Kaje amma karka qara kawomun komai daya shafi rayuwar aure,idan bazamu kwana a tare ba babu wani abu dazakamun na aure,na yarda haka tsarin namu auren yake,kaje plss" tafad'a tana me d'addage hannayenta duka biyu alamar naci ka fam, matsowa yayi daf da ita ya sanya hannunsa asaman waist nata yamatse ta sosai da jikinsa yace "Ni kike gayawa magana hafsa? Sabida kin samu sake ko? Yanzu ma idanta ta dago sukayi kaura dana juna tace cikin jin haushin sa
"So nake muyi sighning wani yarjejeniya kanka tafi" sakinta yayi yace yana murmushi muje gayamun wane iri ne?" zama sukayi a kujerun parlor tace
"Sona ke mu kwana a roof daya,muci abinci atare,mu sake wa juna soyayya,mu aminta mudin masoya ne,idan har akayi watanni shida kaci cewar baka buqatar tarawa dani,kuma bakaji sona ko daya a ranka ba,to ka rabu dani,kuma tsakani da Allah zamuyi" kallonta yayi ya kwashe da dariya ya sani yanajin tausayinta amma sam baya santa wlhy, yakuma san baze taba san taba,da wannan ya aminta suka rubuta suka ajiye.....
Hafsat ta kuma yin wauta a karo na biyu,yaya kuke zanin wannan zaman? Ze dore kuwa?" anya hafsat bata kirawa kanta zawarci na biyu ba bayan shaam ya aure fara me gashi abinshi? Muje zuwa dai.....
0 comments:
Post a Comment