BISMILLAHI
INA MIKA GODIYATA GA DUBBAN MASOYANA ,DA FATAN ZA KUJI DADIN WANNAN NOVEL KAMAR YANDA KUKA JI A MA'AIKACIYAR GOMNATI READERS,ALLAH SA A FARA LAFIYA MU GAMA LAFIYA.
Sanye take cikin wata jemammiyar rigar atamfa ko kugu bata kai ba,ga wani wandon yadi ja ajijinta dogo,ta nannade kafa daya iya gwiwarta,wata dagargajajjiyar p cap ce a kanta,tafiya take tana bouncing har wani dinginsa kafa daya takeyi,irin tafiyar nigogi maza takeyi tana shan kamshi tare da dauke kai sama tana hura hanci,tafiya takeyi tare da sa hannayenta a aljihunta tana bouncing tare da yin doro tana kwobarewa hadi da budawa.
Bata kula kowa kawai kwana take sha,wata dandazon majalisa ta maza tazo,tana zuwa aka fara ihu da tafi sai Amana,kallonsu tayi tare da kara kwobarewa tace sai Baba,sa'a dai sa'a dai tayi Gaba bata kara yin magana ba tafiya kawai takeyi,wani yaro taci karo dashi,sai da ya buya a lungu yace Maza Mazaje Cike da bala'i ta dago kanta aifa sai ta hango yaron,da gudu yaron ya zura,ta bishi itama sai da ta kure masa gudu har cikin gidansu yaron ta kamoshi a gaban Uwarsa ta hau jibgarsa kamar Allah ya aikota,mutane sun taru amma ba Wanda ya riketa saboda kowa yasan halinta,in tayi fushi ba a iya tsaidata,suna ji suna gani ta farfasawa yaron nan jiki sannan ta gyara p cap dinta sosai ta da kyar take gani tsabar janyo hular da tayi, gaba tayi tare da bouncing,ta kusa zuwa kofar fita daga gidan tayi tsalle tayi ball da wani baho da ta gani a hanyar kofar fita daga gidan sai da bahon yayi raga raga,sai da ta fita ta bar gidan sannan mutane suka sami bakin tsine mata tare da Allah wadai da zuriyar Gidan baki gaba dayansu,kowa da abinda yake fada akan wannan matashiya da sauran yan uwata tare da iyayensu.
Har kofar wani gidan kasa tazo kato da alama shine gidansu,Babanta ta gani a waje tare da mutane a kofar gidan Sallama tayi musu tare da cewa Allah barmana Baba,sai me gida wlh,tayi cikin gida,da wani gurjejen namiji ta hadu da gani katon dan Wiwi ne,lips dinsa sun nuna da tafin hannunsa,cije baki yayi tare da karkace shi gefe,ke dan Uwarki daga Ina haka?hannayenta biyu a Aljihunta tana hura hanci tare da ja baya,ta kara yin doro tace kafa ja girmanka Hamza,dan zan iya takeshi kasan da wa kake magana dan tsab zan Zagi Amarya uwarka,kasan Halina ko?
Jinjina kai Hamza yayi tare da cewa zan tattakaki in bakiyi hankali ba,bani da mutunci,to ni din an fada ma mutuncin gareni cewar Wacce aka Kira da Amana.tsaki taja tare da banke Hamza tayi cikin gida,tana shiga Ashar ce take tashi a gidan ana ta dambe tsakanin yan mata gidan,
Iyayensu ma sai dirko ashar sukewa junansu,ruwan Ashariya kala kala ce ke tashi a gidan,nan take ran Amana ya baci ko kallonsu batayi ba ta wuce cikin dagargajejen dakinsu,Wanda yake daf da ruftowa.
Sallamar megidan sukaji da alama shine babansu,shima Ashariya ya Shiga dannawa yaran tare da iyayen su hade da kallon wata yar yarinya bata wuce 7yrs tana gatsine da harara yace tafi can shegiya da kai kamar kuda,kallon sauran matan nasa yayi da yaransa maza da mata yace wacce bata fasa ba taci ubanta shegu tsinannu,tambadaddu,bakin da aka sauka a gidan ne suka fito daga masaukin da aka basu suna bada hakuri,
Matan ne sukayo kan bakin da masifa kamar zasu cinyesu da zagi na tashin hankali.
Me gidan ne yayi tsalle ya dire yace kar tsinanniyar data kara zagar min bakina,bakin Alkhairi,dole kuma na dinga saukar baki a gidana,wlh babu yar wata katuwa da ta isa ta taka min birki.
Wata ce a cikin matan nasa tace tambadadden dan iska dama dole kace haka munafuki,Allah ya isa duk ka tarwatsa mana yara,ka lalatasu,dayar ma tace an dai ji kunya kwarton Banza,wata tsohuwa ce tukuf itama ta fito tana ba kwarto bane yaro na,kar ku kara zagar min da shegu jarababbu,haihuwar Asara.
Watace ta zaburo itama a cikin matan ta nuna me gidan,tace ga tsohon haihuwar asara kwarto maci amana.Amana ce ta fito daga dakin tana budawa tare yiwa mutan gidan kallon banza,tace kuna yawa fa,kuna da matsala,dan Allah ku rufe mana baki wlh ko yanzu ayi abin kunya a nan wajen nan ko Baku gane bane eh?
Me gidan yace yawa Yar Amanata kiyi maganinsu,sai Baba kaima fa Baba kana da Matsala fa,ka dinga kiyayewa duk kabi ka jona mana masifa da irin abinda kakeyi a gari.
Baba ne ya kalleta zaki ci Ubanki kema shegiya me suffar maza,jibi yanda kikeyi, wa zaki samu ya aureki haka? Shi yasa baki da mashinshini,kinyi kwantai anyiwa kannenki aure ke kina shirme a gari,
Cike da takaici ta kalli kanta tare da sa hannu daya a Aljihu tare da cewa Baba ni ba gudun maganarka nakeyi ba,bana tsoronku ku kanku kun sani,kawai biyayya nake ma amma dole a fadama gaskiya ka gane Tsoho kana yawa wlh,wannan abin da kakeyi ba me kyau bane,shi yasa muka lalace,dole na fada ma gaskiya,ka gyara badan mu ba ko dan Allah kaji tsoronsa.
Rufe min baki shashasha ubanki nakeyi? Hmmm Allah baka Hakuri Baba nasan yanzu zaka iya tsine min.
Ta inda kikafi yan uwanki hankali kenan akwai biyayya ga iyaye,ga sallah akan lokaci,cewar Baba Dariya amana tayi kadan tare da fadin Allah barmana Baba,ammafa Baba Allah shirya mana kai.ki kiyayeni Amana cewar Baba,sorry Baba Amana ta fadi,
Baba yau ba dan tsire ne?cewar Amana, Babane ya watsa mata harara tare da cewa ubanwa zai sai miki tsire maganin me kike min a gidan nan,ke ba saurayi ba bare nasa rai zan samu kudi,tafi kiban waje shashasha.bouncing ta kama yi tare da kwobarewa tana kunkuni,wofi banza da baki kamar gidan tsutsa cewar Baffa.Anayin kiran sallar Magriba Amanace ta Riga kowa yin Alwala da Sallah a gidan.
Ummanta tana zaune tana tace gasarar kokon siyarwa na safe,bata da niyyar tashi tayi Sallah,Amana ta kalleta a hankali sannan tace Ummammu Anyi fa Sallah ni halina dake kenan wlh anata ta Sallah ke baki da Niyyar tashi,
Wacce aka kira da Umma ce ta daure fuska ke jarababbiya sauraramin,niba uwarki bace zaki dinga gaya min magana inda kika ga dama?,ko ni sa'ar ubankice,har ni zakiyiwa wa'azi kamar kanwar uwarki,sai da safe ki taso sakalo sakalo na sammiki koko,kin dauki aikin banza a kanki,kin rasa me sonki tallanma kinki yi kince ke boko zakiyi ayi mugani ai duniya ce,
Haba Umma daga cewa kiyi sallah shine kike min baki?kin San ma'anar duniya ce,ku gidan nan Baku da aiki sai zage zage,duk kun gama kwashe mana Albarka,taya zamu samu miji,kuma boko tun daga primary waye yake daukan nauyina?itacen kara nake yowa a kauyen nan haka gashi har ina ss2,ai abin ku jinjina minne amm kullum kunfi so kuga na shiga duniya dan na samo muku kudi haba Umma,ya kike haka ai gwara idan bake kika haifeni ba ki fada min nasan matsayana tun wuri.
Ke tashi ki bani waje jakar banza.wani bakin cikine ya cika zuciyar Amana,Sam basuyi dacen iyaye ba,yo ni da za a dinga min fada wani ciyar dani akeyi?sutura ake min ko sabulun wanki bare na wanka ba ayi mana a gidan nan,kuma sai a bimu da zagi nifa bazan dauka ba cewar Amana tare da ficewa daga gidan.
kowa a gidansu babu na gari a cikinsu,gaskiya Allah kawo min sanadiyar tafiya Cirani na yi wajen kudu,na huta kawai da bala'in gidan nan,Allah sa Baba ya turani cirani nima irin su Hamza na tafi na huta da masifar gidan nan.
Wannan wanne gidane kenan,da alama babu me tarbiyya a gidan kaf. bari muji tarihinsa.
GIDAN BAKI kenan gidane Wanda me Gidan yake saukar mutane Baki idan sunzo gari suna Neman masauki sai ya saukesu amma iya mata banda maza,baya saukar maza a gidansa,shine dalilin da ake kiran da gidan Gidan Baki.
Gidane Wanda yake cike Da mata da maza.da yan gidan da kuma baki iya mata amma.
Baba me gidan shine Sulemanu Harka dan Asalin kauyen Albasune LGA ne dake Kano state,Amma aikin gini yasa ya koma garin Wudil da zama,Babar Sulemanu Harka wato Ille ta haifi yara kanne da Yayyen Sulemanu harka amma duk su nutsatsune suna zaune a can kauyen Albasu lafiya da iyalensu yayinda Sulemanu ya dauke Uwarsu wato Ille,saboda tana sana'ar soya kosai sai wayo yake mata tana ciyar masa gida da kudin da take nema,.
Ille ita kanta tasan Sulemanu Harka ba mutumin kirki bane amma ba yanda ta iya dashi,haka take Sana'a tana ciyar masa da iyalensa,
Sulemanu Harka matansa 4 Haule itace ta farko ana ce mata Goggo,yaranta 10 Maza 4 mata 6 Safiyya itace Babar Amana suna kiranta Umma, yaranta Uku maza 2 mace 1 Amana.
Laure Hajiya kenan ta uku yaranta 5 Maza 3mata ,
Sai Raliya Amarya tana da yara 8 maza manya 4 sai mata ma 4.gaba daya yaransa 25 kusan mata 4 kacal akayiwa aure, matan suna gidajen mazajensu a kauyen Albasu wasu a garin Albasun,
Saura mata da yawa suna a gidan ciki harda Amana,maza kuwa ba wanda yayi aure cikinsu kawai iya shege sukeyi a garin, Sulemanu Harka sana'ar gini yakeyi sosai tun yana da kuriciya har ya girma yayi yara magina.baya taimakawa iyalansa da kwandala sai matan banza,Sai kuma yaci me kyau a waje yasha me kyau,ga sutura me kyau,sai ka Rantse Sulemanu ba a gidan kasa yake kwana ba,
Yaransa duk ba munana suna da kyansu,Amana tafi kowa kyau a gidan sai dai wasu su fita haske shima da kadan don itama fara ce Amana.
Talakane na karshen karshe,saboda ko ya samu baya tsinana komai ga iyalinsa,sai dai yaci tsire da kudin,domin kullum yana gaban tukubar me nama,gidansa kuwa ko masara ya kasa siya musu ko wacce Sana'a takeyi tana ci da kanta da yaranta,Sulemanu Harka gawurtaccen dan Neman matane,kaf kauyen da wasu garuruwan sun sanshi,shi yasa idan yaji baki mata to shi zai basu masauki yana zagawa wajensu.
Bashi da Amana,ko yarinya ka kawota gidansa riko sai ya ci amana ya lalata ta karfi,haka baki wasu su gudu wasu su tsaya su sha harka,yaransa ma sunsha kama Baba da mata,matansa har fakonsa sukeyi idan dare yayi,sabo da ko yar uwar matansa ne sukazo sai ya zaga wajensu ya kwashi Harka,
Bashi da abokin da ya wuce limamin garin domin halinsu daya,
Sulemanu Harka ko yarsa kaje nema idan baka da kudi to bazai baka yarsa ba,kuma idan kana zuwa zance wurin yarsa to sai ya dinga rokonka kudi,haka gaba daya sai Allah ya bashi yara gaba daya tantirai,Amana ce ta gari a hakan lol kaf gidan babu me nutsuwar Amana a hakan.
Mazan gaba daya wasu barayine,wasu yan wiwi,wasu yan Neman mata, domin suma suna lallabawa wajen baki masu sauka,na gidan aure ma ko wacce da rashin mutuncin da take shukawa a gidan mijinta,kullum a kawo kara da Sulhun yaran Sulemanu Harka ake,babu na ciki babu ga na wajen,kowa da halinsa,
Su Kansu yaran sun San basuyi dacen iyaye ba,su kuma iyayensu mata matsalarsu rowa, zagi da tsinuwa kala kala,sun gama raina mijinsu saboda ya zubar da mutuncinsa.a cikin labari zaku ci gaba da jin Halin kowa a Gidan Baki.
Amana kyakyawar yarinyace ta kwatance fara ce Amma ba kar ba,doguwace ga shape,duk inda kake neman diri to kazo wajen Amana, shekarunta 18 going to 19, gashine da ita ya wuce kafada kadan baki wuluk,gata da idanu dara dara masu tsananin kyau,gashin gira dumbul dashi,dan bakin nan cut,lips light pink,hancinta dan dai dai bai cika tsini ba kuma ba gajere ba,ga dimple idan tana magana bare tazo yin dariya,hakora yar yar dasu kar kar,saboda kullum cikin yin aswaki take ko yaushe,skin dinta me laushin gaske, gata da tsafta ba laifi.
Amana yarinyace me son al'adun maza,haka take tun tana karama rayuwarta da maza takeyi,shi yasa kaf garin wudil bata da kawa mace ko daya, sai Maza,bata da mutunci ko kadan idan ka shiga safgarta,ko uban waye komai girmansa,macece me karfi da zafin nama,ga juriya da taurin rai,idan fada ya hadaku tofa sai dai a mutu bata ji ba ta gani,idan ta fara dukan mutum sai ta gaji da kanta,kowa daya Santa tsoronta akeji ko a gidansu Amana sarauniyace dan ko waye bai is a ba,iyayenta kawai take dagawa kafa,
Ba wani abu na nafeela takeyi ba amma duk farilla tana cikawa,Sallah bata wuceta duk inda take,gata da son ilmi,gidansu ba a sasu a islamiyya bare boko amma har gona take zuwa tayo ciyawa ko kara ts siyar ta sayi littafan schl,haka ta gama primary yanzu tana ss2 a wata government schl ta garin,duk da ba wani turanci ta iya ba amma tana iya karantawa,haka islamiyya ma,tana da haddar izu 30 ga wasu littatafan tayi,duk gidan ita kadaice take zuwa schl,har yaran gidan sabo da tsoron Amana da sukeji take korasu makarantar Allo dolensu suke zuwa,
Kuma idan baka kawo mata haddar karatun ba sai ta farfasawa yaro jiki,ba ruwanta don kaninta har kashi ta tsaga masa garin duka bai iya karatu ba,har yayyenta tsoronta sukeyi sun san karfin Amana,ba mutunci ba daga kafa,shi yasa a gidan ita kadai ce take sa doka kuma dole abi dokar,
duk masifar Amana bata yi a schl tunda wani malami ya kusa korarta daga schl din gaba daya sai ta daina komai da take musu,sai kadan kadan takeyi, domin tunda ta fara schl take jibgar dalibai,tare da karya kafafun yaran mutane,domin har malami cin kwalarsa takeyi ta fesa masa mari,
Gata da kokari da tsafta,shi yasa aka bata head girl,tunda aka bata mukami idan yaro yayi late sukaganta a gate juyawa sukeyi gida sabo da sun San dole sai ta fasa ma jiki,ta gagari malaman bare abi wa yaro hakkinsa,
Amana yar rigima ce sosai,tunda aka haifeta Ummanta ta zabi wannan suna Amana aka radawa yarta,wajen aiki kuwa ta iya girki kala kala domin Amana har wajen wata Bilkisa me tuwo tuwo take zuwa tana tayata girki ta bata kudi,dasu take biyan bukatunta da dama,
Amana Ummanta bata da halin kirki,ga son kudi,bata iya taimakawa yaranta da ko kwandala,kowa yaro da babba dake gidan Sulemanu Harka Neman na kansa yakeyi,kowa ta kansa yakeyi babu me taimakon wani da ko kwandala,gwara Amana tana bawa babanta wani abun idan ya rasa,har su Hamza takan sai musu kokon safe watarana,sabo da Amana ta fisu zafin nema,ba ruwanta kullum cikin Neman hanyar samu take,kuma in taje neman aiki wajenka tofa dole ne ka bata aiki tayi ma,kuma sai ka biyata dai dai da guminta, sauran yan matan da basuyi aure ba maza suke damfara da yaudara su sami kudin sabulu da sauran kayan sawa,shi yasa suka fi Amana sutura da yawa,sabo da Amana bata da saurayi sai abokai,bata da kayan sawa,atamfarta kodaddu kala 2ne sai tsimmokaran da take sawa,suma wasu wandon duk na su Hamza ne da kannenta,take dauka idan zasu jefar sai ta karba ta wanke taci gaba da sawa tana hadawa da rigar atamfa,Ummanta tana Sana'a tana samun kudi amma sisi bata iya bawa Amana,hatta kokon Safe sai dai Amana ta siya, idan ba kudi ta tafi wajen abokanta maza ta samu,amma tana bawa kannen Amana Maza,basa shiri da Amana da Ummanta sabo da Umman Amana tafiso Amana ta dinga damfarar maza tana samo musu kudi,amma Amana taki yarda kuma bata da me sonta.
Shi yasa Amana tace abokai maza sunfi mata muhimmanci,ga kyauta,gashi basu fiye gulma da hassada irin ta mata ba,Namiji ko ya kuke mutunci zaka moreshi,sabanin mata da yawa sai su dinga yi ma hassada ma,idan sunga ka fisu sai gulma da bakin ciki.
Yawan Hulda da Maza yasa Amana takeyin acting din maza, sauran yan uwanta duk Suna Neman mata,matan ma sabo da son kudi Neman maza sukeyi,Amana ce kadai cikinsu Bata ma da saurayi bare ma ya taba jikinta,kuma mazan da take Hulda dasu tsoron jarabar Amana sukeyi ko yatsanta basa rikewa.
Ci gaban labari
Amana ce ta tashi da asuba tayi Sallah sannan ta fito wajen Ummanta dake gaban murhu zata dama kokon siyarwa,naira ashirin Amana ta mika mata ba wata gaisuwa ba komai,duk dama gidansu haka suke ba a gaishe da kowa,ungo wannan kudin Umma a bani koko damun farko nake bukata kuma yaji gaya a dauraye masa kai da gasara sosai,karba Umman tayi ba kunya tace kawo robarki,tana kwobarewa da takama ta mika mata,koko na a dauraye masa kaifa da gasara in baiji wlh gobe wajen su Zainaba zanje na siya,
To karki isheni kamar wacce ta bani million,cewar Umma,wucewa Amana tayi wajen kakarsu Ille tace karbi tsohuwa bani kosan 10 bana bukatar raini shi yasa kikaga ni komai siya nake da kudina,ba a min kallon banza saboda ni da kudina nake gadarata,iya kudinka iya shagalinka,ille dai shuru tayi tare da zubawa Amana kosanta tace ga gyaran biyu nan nayi miki,Amanace tace kwashe abinki zuciyata bata mutu ba bare ki fadawa danki kin ci dani,na girmi tallafinki,babu Wanda yake ci dani a gidan nan, Ille ce ta kwashe kosanta guda biyu jeki matsiyaciyar yarinya,shegiya wulakantacciya.
Ae naji gwara ni ummata bata haifi me bin mata ba,kin haifo Baba kin jawo mana bamuyi dacen iyaye ba,duk mun lalace,wa yasan me kikayi lokacin kuruciyarki,shi yasa Baba ya gadoki,kisa ya kori waccen yan fulanin daya kawo gidan nan,wlh idan na kara kama Baba dasu suna iskanci a dakinsa sai na dagargaza musu kai,
Ille ce ta fashe da kuka kowanne yaro yazo yaci mata mutunci akan ta haifi Sulemanu Harka.
AsmaBaffa
Comments dinku shine jin dadina fans tnx a lot.
✳CIRANIN AMANA✳
5-10
By
AsmaBaffa
Haka Sulemanu Harka ya shigo ya riski mahaifiyarsa tana kuka,lafiya Iya?gata nan Amanace tsinaniya taci min mutunci,cike da takaici Baba ya kwantarwa da Iya hankali ya mike ya nufi wajen Amana a fusace,Amana tana shan kokonta da kosai,ya fado dakin,Gani yayi fuskar Amana ba rahma nan take ya tsorata yace haba Yar Amanata a dinga salalawa Iya mana,a hankali fuska a daure tace an gama Baba,amma ka fada mata bana so a dinga taimakamin a gidan nan,tunda an San baza a iya tsinana mana komai ba to a daina yi min rangwami da sauki ko arahar abinci bana bukata,da kudina nake Harkata,shi yasa nima nake bearing da Amana Suleiman Harka a schl,
To Amanata a dinga hakuri kinji,sai Baba kar kaji komai,Baba jiya ma fa na kamaka wlh da wata yangwadaddiyar tsohuwa,saura kadan na fasa muku kai,kawai dan Kaine Baba,dan Allah Baba idan iskancin nan zakuyi ka dinga tafiya inda baza mu ganka ba,Amana zamu bata fa dama leke kike min a zaure na?to ka daina mana?cewar Amana,
Kaci sa'a wlh na tuna kai Babane da tuni na Tara ma mutane,wai Baba baka jin kunya ka tsufa haka,kasan bala'in da kake dorawa kanka kuwa,?uwaki Amana kiyi min Addua nima ina so na daina na kasa,ban San dalili ba,wlh na gaji da bata lokacina ina ma Addua Baba bazan iya ba,yanzu kai dadi kakeji da muka zama haka,kalli yaranka fa yanda kowa yake babu na gari,
Ni kadai ce bana iban Harka nan irin taka,kana yawa fa Baba idan na gaji nima na kusa, zan kwace kawai nima nabi sahu,Haba Amana me kike fada haka cewar Baba eh wlh Allah kawai nima fuskewa zanyi na amsa sunan Amana Harka.
Wlh Baba duk randa na kamaka tsanarka nakeyi,bana son ganin ka,jeka kawai Baba za kasa na kasa shan koko na Wanda ba wani ne ya sai min ba da kudina nake harkata.
Baba jikinsa yayi sanyi Amma bazai iya daina halinsa ba,ya rasa dalili,
Amana duk tafi bashi matsala a gidan sabo da tana masa nasiha amma bazai iya dauka ba,gwara kawai ya turata Neman kudi kudu ya huta da halinta,kuma da alama zata nemo kudi sabo da Amana tafi kowa a gidan zafin nema,ga juriya da kwazo.ga karfi ga bala'i dole za a buga da ita,
Amana ita kadai tafi duk yayansa Amfani a gidan,gata me tsananin kyau da diri.
Zama Baba ya gyara kusa da Amana,tare da riko hannunta,kwace hannunta Amana tayi tare da cewa Baba ni ka daina rikeni kar nima ka mai dani irin watsatsun matan da kake Harka dasu,haba Amanata nifa Babanki ne duk abinda zanyi bazanyi da yarana ba,to naji Baba mene ne,yawwa Amanata so nake kema na turaki Lagos Neman kudi,kije Cirani kiyi Sana'a ki dinga samomana kudi,watakil ma Allah ya baki miji me kudin gaske a can ko? Dariya Amana tayi cike da jin dadi zata bar jarabar gidansu,tace Allah barmin Baba,wlh sai Baba,shi yasa watarana kake birgeni idan kayi tsiya ta wani wajen sai kayi dadi ta nan,Allah dai ya biya.
Dadi Baba yaji yanda zai dinga tsula tsiyarsa Amana bata gidan bare ta dameshi da wa'azi.
Kallonta yayi yace yawwa ta wajena,kudi zan baki masu yawa Wanda zasu isheki amfani a can Lagos kafin ki fara Sana'a.
Sa'a dai sa'adai Baba cewar Amana tana murmushi.
Nan da sati biyu zaki tafi Amana,akwai abokina zan masa waya shi zai kaiki wajen kwana,amma Baba ba irinka bane ko ?ai shi Amana daban yake yawwa yanzu naji batu Allah kaimu sati biyun cewar Amana, Baba yace kinga duk manyan maza na suna jahohin kudi cirani,amma basa tsinana min komai sai lalacewa da suka kara yi,
Duk cikinsu babu Wanda yaje lagos suna cross river wasu suna Abuja,wasu Enugu,jibi Hamaza na turashi nassarawa lafiya amma jibi da yazo gida doya kawai ya kawo min,sai 3qurtr da ya zo dasu,dariya Amana tayi tace Baba rannan saura kadan na masge Hamza bashi da mutunci har ni zai zaga,shi din banza,Baba ne yayi dan turancinsa daya koya a garin Tafa kusa da Abuja,yace control control Amanata,
Cike da farin ciki Baba ya fito,
Amana shirin Makaranta tayi ta fito tare da yin ball da wani pow da ta gani a kofar dakinsu,tayi gaba zuwa schl.
Sabon Malami ta tarar a jinsu har an shiga,cike da gadara tana budawa ta shiga class din,Malamin ta gani a kan wata kujera da ba Wanda yake hawanta a ajin sai ita,
Wajen malamin ta karasa tare da cewa daga wannan kujerar,mamaki ne ya kama sabon malamin,yace ke dan uwarki ni zaki fadawa haka,sa'an ki ne ni? Kujerar daga gidan ubanka kazo da ita,ko ta ubanka ce cewar Amana,bude baki malam yayi,yan class kowa yayi luf,
Ke wlh sai na koreki daga schl din nan bari na fadawa p.c hannu Amana ta tura a aljihu tace uwar principal zaka fadawa,p.c yaci uwarsa ka fada masa ni Amana na fada uban p.c yaci Uban sa,
Kujerar ta janye malamin na kai ta zame kujerar da karfi ya fadi kasa ta matsa gefe ta zauna tare da harde kafa daya kan daya.malamin mikewa yayi tare da karkade rigarsa ya fice fuuu wajen p.c,
Wajen principal yaje ya fada masa komai,principal dai ya gaji da halin Amana,nan take aka karkada kararrawa aka tara Assembly duka makarantar,
Guri yayi tsit PC yace ina Amana Suleiman Harka?da sauri tace yes gani nan,nasan a kaina akayi taro, ko bakace ba zan fito gani,
Ta fito ta tsaya gaban dandazon mutane hannayenta biyu cikin Aljihu tana kallon kowa dai dai,PC yace kinwa sabon malami rashin tarbiya da cin mutunci gaban aji?yes nayi masa kuma ko gobe ya kara zan sakeyi masa komai naga dama,
PC ne ya daka mata tsawa ke yar matsiyata,yar gidan Sule tantiri me Neman mata bafa tsoronki akeyi ba,wlh yau sai kowa ya zaneki a malaman schl din nan cewar pc,
karya kake Saminu PC,gaka nan bakin kwarto dan iska,wlh akan ka zagi iyayena ko ku dakeni gwara na bar makarantar,babu Wanda ya isa ya taba iyayena ya kwana lfy,makarantar ku din banza shegu gaba dayanku,PC ne ya cakumo Amana da niyar dukanta nan Amana ta riko makwallaton wuyan PC kamar zata zareshi daga wuyan,ba shiri PC ya saketa,amma Amana zagi takeyi iri iri sai da ta gaji ta kada kai ta kalli PC tare da cewar Wanda ya kirkiro boko ma yaci uwatas,uban uban uwar Bokon an daina bokon dan uwarsa.ta kada kai ta bar schl din,tazo bakin gate zata fita ta tsaya ta zubawa me gadi rankwashi kwas,sannan tayi gaba,
bagazan bagazan ta shiga gidansu,ba Wanda ta kula ta cire uniform dinta ta tattarosu waje ta hada da jakar schl din da littafan a tsakar gida ta zuba musu kananzir ta cinna musu wuta,bal bal suna ci har suka kone kurmus,sannan ta kwashe tokar ta watsar a waje tana bin iska tace bye bye Boko ni da zan tafi Cirani Lagos garin turancin da Bokon gaba daya,
Wani Nishadi taji ya mamayeta da ta tuna zata tafi lagos,
Wanka tayi ta sa wani wandon jean kato Tsoho tukuf gwiwar duk ta yage,tasa rigar Atamfa katuwa ta kai cinyarta,p cap ta sa wata kalar tsohuwa tukuf da ita,ta fita,wani Namijine ya ce sai Amana ya garin ne,kallonsa tayi easy T.j easy dai,ya kk?lfy Amana ,kwana 2,wlh tj wai schl ne zasuyi min iya shege tuni na kwancewa PC number 8 dinsa,dariya tj yayi yace bakya farke shege ko ki kiramu muzo da yaranmu a yi maganinsa haba Amana ya kike masu sauki ne,kyalesu nayi kawai sabo da Lagos zan je Baba,
Iyye kice kin kusa fasowa gari gaskiya Dad dinku yana birgeni,murmushi me kyau Amana tayi ina zuwa tj ku zama cikin shiri zan muku hanya kuma kuzo, sai Amana cewar tj ya zaro 200 ya bawa Amana ga wannan kya danyi eh yane,godiya nake tj,haba share kawai aike tamuce,jiyafa Majalisa ta cika ana ta jiranki baki zo,ai ina nan zuwa yau,sai mun ganki.
Rabuwa sukayi da tj,wasu yan matane sukazo wucewa sunci kwalliya yan makarantar k.u.t wudil ne,sai yanga sukeyi suna yiwa Amana kallon banza,bata kula su ba.har wani turanci sukeyi su a dole yan University suna degree,tafiya Amana tayi tana kwobarewa tare da takama tana wani budawa,
Shekewa sukayi da dariya suka tafa,wata a ciki tace oh budurwa har budurwa kyau iya kyau amma jibi ta kashe kanta,
Amana dai bata kulasu ba,sai wata tace inye kaga maza fa,wannan da gani shaye shaye takeyi,ko ciwon hauka ya kamata,
A fusace Amana taci birki tare da juyowa,ganin yanda amana ta canja lokaci daya yasa yan matan nan suka tsorata,zasu yi gudu gashi sun sa takalmi me tsini da damammen skert,
Daya Amana ta cakumo ta hau dukanta sai da ta karya mata hannu daya,sauran su biyun sun fara gudu Amana ta damkosu saida ta sumar dasu sannan tayi gaba abinta ko juyowa batayi ba,
Ran Amana ya baci ta fasa zuwa inda tayi niyya ta koma gida,Ummanta ta gani tana yin Alalar siyarwa ta Rana,can gefe Amarya tana Awarar siyarwa,Goggo shinkafa da miya,Hajiya shinkafa da wake duk na siyarwa.
Ko wacce ranar girkinta ita zata ci da Sulemanu Harka da sana'ar da takeyi.kowacce tana ci da kanta da yaranta,Amana kuwa ummanta bata bata sai dai ta siya,sabo da bata da saurayi.
Wajen Amarya Amana ta nufa tare da mika mata kudi Bani ta Naira Dari nama biyu zakisa min kuma Manya,harara Amarya ta watsa mata,ubanki ne ya bani kudin?ko bashi ya baki ba wlh in bakisa 2meat ba sai na tankadar da tukunyar miyar baki dayanta,ba shiri Amarya ta zuba mata shinkafa da Nama biyu manya harda gyaran guda,karba tayi tare da cewa cire gyaranki,na fada muku ku daina yi min mutunci a kan na siyi abunku,bana son a dinga taimaka min,
Gyaran da Amarya ta sa mata ta cire tace jeki yar Iskar banza.
2weeks ta cika Amana ta gama shirin tafiya Lagos,fitowa tayi sanye da wani 3qtr jean Wanda wandon kaninta ne Yusuf ta yanke da Almakashi ya dawo gajere,wata falkekiyar t-shirt din Hamza ta sa ja ta gama kodewa da jemewa,siririn gyale ta daura a kanta,da wata kwarababbiyar Jakarta karama tasa yan tsummokin kayanta ciki,
Umman Amana sai murna takeyi zasuyi kudi,yarta ta tafi Lagos,yan gidan suma dadi sukeji masifaffiya zata tafi su Shana,Babane ya kalli Amana sai da dariya ta kusa kwace masa irin wankan lagos da tayi,Babane yace Amanata ki canja kaya jibarki kamar inyamura haka zaki je lagos?Yo Baba so kake nayi yawa,Lagos ce fa gwara na saje dasu.
Har tasha Baba ya kaita ya biya mata kudin mota sannan ya bata dubu Hamsin saboda kafin ta fara aiki,sosai Amana ta Adana kudinta,gashi irin katuwar mota ta hau lexs,
Amana anyi kicin kicin cikin Arna,motarsu ta tashi sai washe baki takeyi tana yin guntun turancinta,sun kwashe tafiya me nisa cikin duhun dare,har sun wuce rabi sun kusa zuwa,kitttt driver ya gangare kasa yana ihu yan fashi,ai kuwa sai karar bindiga ce ke tashi,Amana ko a jikinta,nan yan fashi suka fito da kowa waje,motoci suka gani birjik an taresu,ga wasu motoci daban na Alfarma sun kai wajen 10 a Jere,daga gani na wani me kudin ne,Amana motocin me kudin kawai take kallo ta manta a gaban yan fashi take,
Wani daga cikinsu ne ya bugawa Amana tsawa amma ko tsoro baiga taji ba,su Kansu yan fashi dariyar shigar Amana sukeyi,wani azababben gaye me tsananin kyau da kowa yake tunanin Bature,kyau kamar Aljani,da ganin yanda yake tafiya Naira ta ratsashi,sai kallonsa akeyi kowa,yan fashi ne suka nuna shi da bindiga tare da nuna masa wata tsohuwa sukace kayi sex da wannan maza ko yanzu mu aikaka lahira,
Wani takaici da bakin ciki ya mamayeshi,sai hawaye a idon wannan hadadden saurayi suke zuba sharrrrr,tsohuwa da kamar kakarsa ce,gata Arniyace,kuma shi da bai taba zina ba ko da budurwa sai wannan tsohuwar,cikin matsanancin tashin hankali ya riska,tare da dana sanin zuwa Kano a mota,bai bi flight ba,
Amana ita kanta sai taji saurayin ya bata tausayi,taya zata iya cetoshi,sai kallo take kare masa,gashi kamar Aljani sabo da kyau,a ranta tace wannan da gani bature ne Allah sarki ko Hausa ma naga Alama baya ji.
A ranta tace dole na taimaki me kyan nan,Amana ce ta buda tare da kwobarewa da 3qutr tanta,tace easy sir easy dai,wa yace daku ba ku ba,ai wlh ba mazaje sai ku,duk wajen nan Matane,Allah dai ya biya ogoginmu,sai Mazaje,irinku kuna birgeni Allah wlh ba a shiga dawa dan karya, haka Amana taci gaba da yi musu kirari sosai,murmushi ogan yayi na jin dadin yanda Amana take kodasu,
wani yace Yan mata ina kudi,dubu hamsim din da Baba ya bata ta mika musu ai Mazaje ko Baku tambaya ba dole na Baku,ai nakune dama,ko wiwi kwa danyi eh yane,murmushi Oga yayi tare da cewa sai yan mata me kikeso yanzu ayi miki sabo da ke ta wajen mu ce.Amana taga ma kallai yan fashin nan masu saukin kai ne,kuma basu fiye zalinci ba.nan ta fara magana
Allah taimaki Oga waccan me kyan nake so a bani shi ya kaini har lagos a motocinsa,Allah bar mana oga kar ya taba tsohuwar can,kawai ni a barni dashi,yarinya mun baki shi,kema kina son ki dan dandanashi ko,ai Oganmu tunda na ganshi nake kwadayinsa a dan bani shi nayi masa Eh yane ka gane,
Oganne ya dakawa handsome tsawa kai mike tsaye, Allah ya taimakeka ka godewa wannan yarinyar,ka kuma tabbatar ka kaita inda take so.shi kam wannan me kyau ya cika da mamakin wannan yarinya marar tarbiyya me 3qtr.abin ya bashi matukar mamaki,lallai tafiya mabudin Ilmi ce.
Sauran mutane kowa kallon Amana yake har Wanda basa jin Hausa ma.
AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳
10-15
by
AsmaBaffa
Wannan saurayi tunda Amana ta fara magana yake kallonta yanda take acting kamar a film,gashi a kankanin time ta canja musu ra'ayi,wani farin ciki ne ya mamayeshi,yarinyar nan ta taimakeshi a rayuwa babu abinda zai mata sai addua,
Kudinta ogan yan fashin ya mika mata karbi yan mata kuje,haba Oga ai nakune idan na karba nayi fariya,nifa sabo daku na taho dasu,an gaisheki yan mata kuje abinku,daya ne a ciki ya bugawa handsome tsawa maza kuje a kaita inda take so,Amana ce tace wa me kyau hey guy basu rabonsu su samu suma,nan take kuwa ya rubuta musu check na 5 hundred thousand,sukace tayi kadan ya kara musu 1million,sukace tayi kadan,Amana ce tayi magana ai sai Oga ayi masa afwa haka,angama yar Oga kuje kawai cewar wani daga cikin yan fashin,
Wannan jerin motocin suka nufa da handsome da Amana wata dalleliya da tafi ko wacce kyau a tsakiya ita wani guard ya budewa Amana ta shiga,saurayin bai so kazama ta shigar masa mota ba amma ganin Yan fashin zasu iya canja ra'ayi yasa yayi shuru ya shiga shima,su biyu a bayan motar,shi da Amana,kana yawa master wlh kayi sauri ka bawa guards dinka dama suja motocin muyi gaba,zasu iya canja mind yan fashi basu da tabbas,ya kana abu kamar baka son lafiyarka Baba cewar Amana,harara ya watsa mata,easy man ya kake yawane eh,sabo da kai fa na taimakawa wlh ganin za a hadaka da tsohuwa,nasan duk da Allah bazai kama ka da laifi ba amma tsohuwa tukuf haka,gata Christian,
Harara ya kuma watsawa Amana,ka Adana Harararka malam kar nayi fushi wlh zan iya ma dukan tsiya na jefarka a hanya,banda mutunci,dankwalin kanta ta cire ta zaro pcap dinta tsohuwa ta saka,
Kamar Handsome yayi dariya ya maze,aswakinta ta dakko a jaka sabo ta fara dirzar bakinta,yayinda motocin suka dau hanyar lagos gaba daya guda 10 a Jere suke tafiya,sai satar kallon Amana yakeyi yanda take dirzar hakoranta da aswaki,sanda ta zaro harshenta ta fara yi har can ciki har kakarin Amai takeyi,ita kadai nan ma yaso yin dariya,
Amana dai akwai tsafta sai dai kayan jikinta sun ji jiki da yawa,sai da ta kusa kwashe 1hr tana aswaki,sannan ta gama,tace Baaba dan miko min ruwa kuma ka sauke glass,ko kulata baiyi ba,turancinta tayi am talking to u Mr Man,guard dinsa dake gaban motane ya mika mata ruwan roba, tare da sauke mata Glass,ta kuskure bakinta tare da shan ruwan ta jefar da robar cike da takama,
Mudubi ta dakko karami ta dinga duba hakoran nata sai da ta gama tace perfect,itafa turancin lagos ta fara tun yanzu,kasa kasa me kyau yake kallonta,sanyin ac ne ya fara gigitata, Jakarta ta duba ta dakko wani dan towel light blue sabone Baba ya siya mata shi,har turare ta fesa masa na tafiya lagos,
Ware towel din tayi tare da rufe jikinta da kafafunta da sanyi ya ratsasu,kamshi kawai me kyau yaji,ya dan bigeshi ba laifi kuma turaren da dadin kamshi,minti 2 ta fara bacci baji ba gani,a nutse takeyin baccinta,
Magazine yake dubawa sanye da wani glass fari kal siriri a fuskarsa ko kallon Amana bai kara yi ba,yana duba jaridarsa yana kora ruwan juice,tafiya sukeyi tare da sheka gudu,Driver me kyau ne ya kauce hanya tare da kasa control din motar,nan suka kafa tangal tangal a titi,kafin kace me ya daki motar gabansa ta baya ma ta dakeshi,Allah yasa duk motocin tawagar me kyau ne,nan take Amana ta farka firgigit,amma ko a jikinta bare ta razana,me kyau ya gama firgita amma yaga Amana tsaki taja tare da cewa kai malam parker mortar nan ka bani tukin,ba shiri driver ya gangare kasa suma sauran motocin haka sukayi,saida suka duba lafiyar motocin me kyau sannan driver cike da girmamawa yace Sir a bata key din,
Me kyau kuwa dan ya kure Amana yace a bata ta tukashi,yasan bata iya mota ba,inda take talaka haka ina suka ga motar da zata koyi mota,da gani ma bata da iyaye karuwan tasha ce,
Karbar key tayi tare da fita da karfi ta zauna a mazaunin Driver tacewa driver koma wata motar kar hanjinka yayo waje bana saurarawa a hanya nikam,ai kuwa a cikin motocin ya shiga daya,guard daya dake gaba ya gama tsurewa karfa yarinya bata iya mota ba ta kashesu a hanya.
Key Amana tayiwa motar tare da bata wuta sosai,har wani jiny jiny tayi sannan ta take motar tare da hawa titi,ta fara tafiya a nutse da mitar a cikin nutsuwa na gaba tayiwa Alama su tsaya a baya itace a gaba coz gudu zata sharara,
Ai kuwa ta fara tuki gashi gudu take tsulawa me uban yawa sosai tare da over taking da takewa motoci,amma kai baka is a kace gudu takeyi,irin tuki ne na kwararru,manyan drivers ba kowa ya iya irin tukin Amana ba sai babban kwaro,kamar ka hau jirgi ba wani gargada a titi haka take tuki suuuuuuuuu kawai kake ji,haka takeyin tukin,kafin kace me tayiwa sauran motocin tazara sosai basa hango motarsa duk da suma gudun sukeyi kamar zasu tashi sama,
Amana wucewa takeyi yuuuut yuuut,vol ta karo na kida ta cika motar har stiyari take duka idan kida yayi dadi,kadan Kadan take kallon me kyau ta mudubi,
Ga shegiyar pcap dinta kamar zata rufe mata ido,kara kallon mudubi tayi ai kuwa carab suka hada ido da me kyau,Wanda yake cike da mamakin wannan Aljanar yarinya kamar namiji har ma tafi mazan,
A cikin motocin tayiwa daya Alama da ta shiga gabansu ta nuna mata hanya,saboda sun kusa shiga garin Lagos,me kyau ya gama cika da mamakin Amana,suna shiga lagos Amana ta ciro wata yar wayarta Nokia 1110 da Baba ya siya mata second sabo da kira,number abokin Baba ta kira bugu daya ya dauka ta sanar masa ta iso,
Yace to ki shiga taxi kice ta kaiki mytwelve,parker motar tayi tacewa me kyau na kawoka iya nan zan wuce ni ka gane?
Wani driver ne ya karbi tukin,shi kuma me kyau Wanda tunda suka hadu sai yanzu ya kara kare mata kallon ba tare da yayi magana ba ya Mika bundles na 1k guda biyu
Ganin bata da kudi yasa tace sabo da bani da kudi zan karba amma ka kiyaye ko dan gaba bana son taimako,bana son a dinga taimakamin ni ka gane ko,harda zare masa ido,kai man ko kurmane?idan baka jin Hausa ka fada min na iya English dina,har ta gama surutunta bai yi magana ba,kawai da hannu yayiwa driver alama dasu tafi,kudinta ta boye a jaka zata tafi ta hango ana fada a gefen titi,da Sauri ta karasa wajen su,Wanda suke fadan kawai Amana ta fesawa ko wanne cikinsu mari daya tace Wanda yaji zafi ya rama dan Ubansa,
Ai kuwa yarabawa bata sani ba duk basa jin Hausa nan take suka rufeta da duka,sai da sukayiwa Amana jina jina,da kyar wasu suka taimaka mata suka janyeta gefe,amma saboda da taurin rai irin na Amana ko hawaye batayi ba,Jakarta ta duba ta tare da zaro yar kudigar wayarta ta kira wayar abokin Baba tare da fada masa inda take yazo ya dauketa wai an mata duka.
Masifa ya farayi tare da cewar bazai zo ba idan bazaki hau taxi ba ki shekara a wajen,nan lagos ce fa ditt ya kashe wayarsa,ba shiri ta mike da kyar ta fada taxi tare da fada masa unguwar da mutumin yace mata.
Har mytwelve ya kai Amana basu san Layin ba sai da ta kara kiran wayar sa sannan ya ce Aisha 12 street,sai da suka isa can sannan ta biya driver kudinsa ta dauki jakarta da kyar.
A bakin wani shago taga tsohon mutumin abokin Babanta,
Har gidan da yake ya kaita amma da alama gidan karuwai ne saboda ko ina dakuna ne gashi duk mata arna da musulmai,
A tsakar gidan yace ke yan mata lagos ba a aikin banza kawo kudin dakinki,murmushi Amana tayi tare da yin wani yar jijjiga tana doro,ta zura hannaye a Aljihu tace Tsoho kenan da Alama baka sanni ba,amma ni da ka ganni bana Neman sauki da rangwame a wajen mutum,sannan bana son a dinga taimakamin,da kudina nake harkata,ka Bini a hankali ka gane ko,tsohon bariki na fika iya shege,mamaki ne ya kama dattijon nan dan ko a karuwai bai taba saukar irin Amana ba,
Kaga tsohon banza yi min kudin dakina naji,dubu Dari a shekara kudin dakinki,dattijon banza harda dariyar mugunta irin ya San Amana bata da kudi,nan take yaga ta karkace ta Ciro bundle daya na 1k sababbi kar kar ta mika masa,tace oya karba iya kudina iya shagalina,
Na biya na shekara guda kar kuma ka dawo ka takura min zan iya ballaka a gidan nan.
Key din dakinta ya bata ta shiga harda toilet,ko ciwon raunin da yarabawa suka ji mata bata ji,wanka tayi a toilet din room dinta,ta sa wata rigar atamfa da wani falkeken jean blue,ta fito har wajen tsohon nan,tace Man tashi maza ka rakani kasuwa,yanda yaga Amana a dire gata komai da jikinta takeyi ba wani lako lako,tsorata yayi ya sata a gaba har kasuwa,ta siyo tabarma,da risho da kayan girki,Tsoho yace ke da zaki siyo katifa yan mata,
Tsoho kenan ka gane Neman kudi nazo ba jin dadi ba,shi kuwa Tsoho sai kallon Amana yake yana lashe baki,a ransa yace dole na dandana wannan yar chamai mai din.
Har tukunya Amana ta siyo guda biyu,komai biyu ko daya take siya har ta gama suka koma gida,yau baza ta fara girki ba,a kasuwar ta samu wata me saida doya da miya,nan ta siya taci a wajen,ta siyawa tsohon ma,harda shan lemon kwalba,
Wani me shayi da kwai ta gani tace ayi min hadin kauri,ta manta yanda zata fada da turanci sai tace thick thick tare da gwadawa da hannu 2 cups harda Tsoho,saida suka koshi sannan ta ga wani bahaushe me gashin kaza taje ta siyo biyu manya ta dauki tata ta bawa tsoho tasa,sannan suka Shiga Taxi har gida,
Tsoho dai sai mamaki yakeyi,tare da jin dadi ya samu budurwa me kudi,zai like mata ta zama kawarsa.
Dakinta ta shirya tsab sannan ta fara zaga gidan sannan ta dan leka waje ta kai 1hr a waje amma kafin kace duk ta fara sabawa da mazan layin nasu,ganin kudin da me kyau ya bata suna da yawa har wasu ta siya abinci suka ci,wasu lemo ta siya musu,duk majalisar data je ko shago sai ta raba musu lemuka sunsha hira,kullum haka takeyi har ta kwashe 2wks a lagos,duk ta saba da mutane amma iya maza,dan bata saurarar mata ita,
Yanzu da kaje Layin kace Amana kowa ya Santa,gata dama da karambani,ko mai ta gani sai ta koya kuma ta iyashi,har yau bata samu aikin yi ba,yayin da kudin me kyau daya bata suka kusa karewa,abin na damunta gashi tsohon nan yaki nemo mata aikin,
Amana tana ganin rayuwa kala kala a lagos gasu da Neman mata kamar yan akuya,ita kanta duk abin ya isheta,ko wanne yace zai kawo mata hari,baren ma tsohon daya bata masauki ya dameta da zuwar mata cikin dare wai sai ta yarda sunyi xxx ita kuma baya tsarinta tana tsoron Allah,
Amana zuwanta lagos ta kara wayewa da gogewa fatarta ta kara haske sosai ta kara yin smooth,ta zubar da kayan da tazo dasu daga kano ta siyi wasu wajen 10 amma fa duk ba skert ko doguwar Riga,gaba daya wando dogone pencil da 3qtr maka maka kamar yar America,kamar ta hada dangi da lilwayne wizzy yanda take Burma wanduna manya ga T-shirt dinta har gwiwa suke kawo mata wai shigar kamala takeyi sabo da masu kawo hari hh, p cap kuwa ta siyi kala Uku masu dan kyau,
Har inner wear ta dan siyi abunta,always pad ma da yawa ta siya ta ajiye,Amana har ta fara koyon yarubanci,ga broken English, ga grammar ma tana karuwa sosai yayinda kudinta suke barazanar karewa.ta fara Shiga wani hali
AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳
15-20
By
AsmaBaffa
Amana tana haki tare da addua ta koma gida,Dan Uzuri me gidansu ta gani a tsakar gida suna ta fada da karuwan gidan,sai bin Amana yakeyi da kallo yana lashe baki,yanda yaga zaman lagos yasa Amana ta kara fari sosai tayi yar kiba ga uban hips da breast masu matukar birgewa,yau ya kashi takobin dolene ta bashi zumarta ya sha,ya gaji da hakuri,kuma Dan uzuri gani yakeyi Amana yar iska ce itama karuwa ce duba ga yanda take Hulda da maza da abubuwan da takeyi tare da yanayin shigarta,kai kana kallon Amana zaka San cikakkiyar wayayya ce,
Sai dai zargi da zato ya jawo ya fassara Amana bai bai,domin Amana babu namijin daya taba koda rike mata hannu da niyyar iskanci,ko saurayi bata da shi,har so take taga Wanda zaice yana sonta zai iya aurenta a suffarta,gashi tasan babu me sonta,ta cire a ranta baza ta taba aure ba saboda babu me sonta a haka,itama har so take ta ganta ta dawo kamar mata masu aji da birgewa amma ta kasa.
Da dare misalin 2am tana bacci akan yar tabarmarta,ji tayi kamar ana shafata a hankali dama ita bata da nauyin bacci,firgigit ta farka,mutum ta gani kwance a jikinta touch light ta haska sai ga Dan Uzuri makale a jikinta,Tsoho dashi ko kunya baya ji dan ya girmi babanta ma
Mikewa tayi tare da cewa tsohon banza fitar min a daki wlh iya kwadayinka baza ka sameni ba dakiki,zama Dan uzuri yayi yana mata magiya kan ta amince masa,ka tashi ka fita kafin na kar Karyaka,haba tawan Amana ta,nifa abokin Babanki ne ko dan wannan kya taimakamin,nasan ma kin San komai da ganin Alama kema yar gari ce cikin harkar zumar nan,a fusace Amana ta suri Tsoho Dan uzuri ta bugashi da kasa tare da daga kafafunsa ta lankwasa su saura Kadan su balle kana ta daukeshi ta jefashi waje ai kuwa Dan Uzuri ya saki kara da kuka,
ji kake garam ta kulle kofar ta tare da cewa dan iska ragowar wiwi,ko karfi babu dan kwaya duk ya tsiyace kwanjalallen banza,wannan in banda cuta me zai shafawa mutum,shi da Baba duk together Allah shiryesu,
Ta kwanta tana tunanin halin babansu duk shi ya ja musu,sai ga hawaye idon Amana sharrrr sabo da tuna yan uwanta da gidansu da tayi da mamanta,tare da halayen family nasu,gasu kowa ya tarwatse a gidan babu wani na gari.
Bata marmarin ta koma gida Sam ko kadan,mikewa tayi ta daura Alwala ta fara nafeela ganin bacci ya gagareta,ga tunanin yanzu bata da wani aikin sunyi fada dame shayi,dole gobe ta fita Neman wani.
Washe gari kuwa haka ta dan sha tea dinta tare da siyo kosai tayi Karin safe,ta yi wanka hade da shiryawa cikin wata farar T-shirt fara kal kal siririya dai dai jikinta amma me tsayin gaske ta kai gwiwarta gaban rigar da hoton mace me gashi pink,wandon jean tasa black da fari fari a cinya yayin da wani aka yanka gwiwoyinsa crazy jean dai shi ba 3qtr kuma ba dogo ba gashi birmeme irin nasu wizzy,jikinsa duk aljihuna,wata farar p cap tasa gashinta ya wuce kafada ta tufkeshi ta cusa a cikin hular amma dole ya fito,takalmi tasa black flat me igiya baki,tayi kyau,bata fiye sa dankunne ba,powder kawai da lipstick ta shafa ta fesa body spray dinta me dadin kamshi sai shining takeyi ta fito,amma matsalar bouncing takeyi tare da kobarewa tasa hannu biyu a aljihu,
Tana fitowa tayi ido hudu da Dan Uzuri ya zura mata ido tare da marairaicewa yana mata shagwaba pls babyna aji tausayina mana,wani kallon banza ta watsa masa,sauran karuwan dake gidan su suka kalleta tare da tabe baki,
Ta fara tafiya suka kyalkyale mata da dariya,dawowa tayi a fusace dama haushinsu take ji,wani ruwa ta gani cikin bucket a wajen pampo dauka tayi cak tare da juye musu shi a jiki,ta fara ball da botikin robar saida ta ragargazashi sannan tace ugly prostitute with ur big mouth tayi waje,arnan karuwan nan sun tsorata da bahaushiya Amana mukus sukayi.
Duk inda Amana ta ratsa a lagos gaisuwa ake kaiwa wajenta,saboda girman kai irin na Amana bata taba nuna talaucinta,bata wulakanta kanta,da ta roki wani kudi gwara ta kwana da yunwa, bata harkar karanta shi yasa kayanta masu yar tsada take siya,
Da ace a kauyensu ne to da sai tayi shigarta ko wacce iri tunda kowa yasan asalinta kuma ga talauci bata samun kudi sai yan dabaru,amma yanzu alhmdllh tana samu dole ta kankaro girmanta da mutuncinta, ba raini bata son a rainata shi yasa kullum ake ganinta kamar me kudice.
Direct wani lafiyayyen wajen suya ta nufa wajen masu kudi ne da manyan yara su ke zuwa wajen.manyan guys both christains da musulmai suna zaune a kujerun dake wajen wasu na cin abinci wasu suna jiran take away,
Da ganin wajen Kasan bana talaka bane,a me kudi ma sai ka isa zaka shiga wajen,shiga ciki Amana tayi tana bouncing tare da sa hannu daya a aljihu daya kuma tana danna karmar wayarta touch screen amma yar karama da ita.
Chewgum take taunawa a hankali bakin yake motsawa sai ka kula sosai zaka gane tana cin chewgum, duk da masu kudin gaske ne a ciki kuma manyan yara babu ruwan wani da wani,ba Wanda zai kalleka ma kowa harkar gabansa yakeyi,amma Amana tana shiga wajen duk Wanda yayi tozali da ita bazai so yayi missing kallonta ba,sabo da ko iya tafiyar ta yanda take gadara kamar yar wani shugaban kasa,tana budawa,ga tafiyarta kanta a mazanma sai manyan shegu su keyin irin tafiyar da Amana keyi,ga p-cap dinta yanda ta wani kusa rufe mata ido,Riga har gwiwa ga creazy wizzy jean habawa ai kowa kallonta yakeyi,gata yar fara me kyau sai shining takeyi ga shape,sai ta birge wasu yayin da wasu ta basu dariya,
Kowa dake wajen maza da mata dariyar Amana yakeyi,ita kuwa ko a jikinta,
Manager wajen ta kira a waya sai gashi ya fito wani katon Igbo Arne,yasan Amana ta taba taimaka masa sanda wani yazo zai yankeshi da wuka,ita ce ta taimaka masa,dan haka ya fito da fara'a dauke da murmushi a fuskarsa,yana zuwa ya mika hannu tas suka tafa,da karfi yace Hausa girl How far noooo?tsaki taja tare da riko hantsar wandonta tace a dey woooo bro Steven ,how u na?am fine,wani yorubane ya shigo Frnd din manager shima yasan Amana nan ma suka tafa yana up my girl,u r shining beb,murmushi tayi me kyau wanda ya sumar da mutanen wajen,that's my man cewar Amana,taci gaba man I need a job here,life no easy my man,u know everything Sir,u know how things work,murmushi manager yayi never mind my Frnd u don't have problem with that.nan manager ya bawa Amana aikin me kawowa mutane Abinci,
Za a dinga biyanta 10k duk wata,tayi murna da godiya sosai,a ranar Amana ta fara aiki sabida dama ma'aikata basa sa Uniform,dan danan mutane suka saba da ita amma iya maza dan ita bata kula mata sai maza
Tsakaninta da mata hi hi kawai.yau duk Wanda yazo wajen suya meat dinan da nishadin Amana yake tafiya,dole ta baka dariya,tunda Amana ta fara aiki anan basu sami Matsala da kowa ba,aikinta takeyi,sosai suke jin dadin aiki da Amana a wajen,sun kara samun customers a wajen sosai dalilin Amana
Amana tayi 3wks a wajen wannan suya Meat kamar kullum duty yamma takeyi 5-10pm sanye take cikin Riga fara kal yau ma iya Gwiwa me rubutu da manyan baki Golden a jiki,rigar me hannun singlet din mazace amma ta mata,sai ta Dora wata yar top iya kirjinta ta tsaya amma me budadden gabace top din Golden color,
Wandonta blue jean,da dan karamin takalminta kamar canvas amma dan siriri me kyau Golden shima,p-cap Golden,ga wata doguwar sarka har Rabin cikinta da wata karama da yar wata a makale a wuyanta,a takaice sarka Uku ce a wuyanta duk wasu yan sirara kamar zaren Sarkar Gold haka suke sunyi bala'in mata kyau,powder da pink lipstick kamar kullum su ta sa,
Manager ne ya zo wajen Amana jiki na bari,kiyi Sauri za a hada take away a kaiwa master mota,wanne master kuma Amana ta tambaya?baza ki gane ba shine Wanda yafi kowa a kudi a masu zuwa wajen nan,ke kaf lagos kafin ki samu Wanda ya fisu kudi sai kin tona,zaki dinga jinsu a news.jiya ya dawo daga America,cikin harshen turanci suke maganar.
Baya shigowa yana mota,watace a cikin ma'aikata ta shigo a guje tana manager kaga ga Sir can kaga cars dinsa sun kai 12 wasu kala da babu irinsu,tabe baki Amana tayi tana kallonsu yanda suka haukace akan sunga me kudi, kafin kace me masu hada suya meat sun hada me uban yawan gaske diff colors,Amana ce ta karba tana budawa tare da takama da isa tana bouncing,ta isa wajen jerin motocin nan,ita kanta ta firgita da ganin hadaddun cars din,
Wacce tafi ko wacce kyau ta nufa kafin ta karasa guards sun tarbeta a hanya tare da karba
Can gaban motocin Amana ta ga ana fada mata da maza,wajen ta karasa tana zaginsu da turanci,kafin kace me Amana ta siye fadan,ta zagesu sannan ta juyo zata koma cikin wajen aikinsu yayinda motocin Master suka taso suna garawa a titi a hankali,
Juyawa tayi ta kalli motar ai kuwa sukayi ido hudu da me kyau Wanda ta taba taimakawa da yan fashi suka taresu,Amana bata taba jin tana tsoron wani ba sai wannan me kyau din,mugun kwarjini yake mata,
Ya ganeta tsab amma sai ya dauke kai kamar bai taba ganinta ba,itama Amana hakan tayi don bata son raini.
Amana zaman lagos yasa ta fara zuwa wata hadaddiyar football stadium,manager ne yake daukanta a motarsa ta rakashi haka wuraren hutawa na manya Steven yake kaita,manager steven ma akwai kudi ba laifi ga son jin dadi da hutawa,
Shi yasa tunda Amana ta zama best Frnd dinsa take jin dadi, yana kashe mata kudi ya siya mata irin kayan da take sawa masu tsada,abinci taci me kyau har saloon yake kaita.
In kaga Amana yanzu zakace wata mawakiyar raps ce tazo daga turai,gashi motocin manager tana driving dinsa yanda take so,Amana ta iya mota both auto an manual tun a garinsu ta koya wajen maza Frnd dinta yan tasha direbobin Mota,
Shi yasa ta iya tuki sosai,haka tukin machine ta iya,keke,ta iya sweeming sosai shi yasa ma take zuwa beach na lagos,karambani ne da Amana shi yasa tun a kauyensu ta iya abubuwa da yawan gaske na rayuwa.
Yau ma manager yace taje gida ta shirya zasuje gym,kamar kullum yauma cikin shigarta take Riga light blue me dogon hannu har gwiwa,da wandon jean dark brown pencil ,takalminta Brown tasha sarka guda daya siririya kamar azurfa ta kai har cikinta,
Yau gyale dark brown ta dan Nada a kanta Wanda yasha acuci maza,sai kamshi takeyi,
Wurin aikinsu ta dawo wajen Manager su,yau kamar tafi kullum kyau sai kallonta akeyi,shi kanshi manager sai da ya kasa dauke idonsa a kanta,yana wow u look so cute,murmushi take yayin da dimple dinta ya lotsa abin birgewa tare da cewa tnx,haka abokan aikinta ma suke ta yabawa,manager ne ya karaso suka fito da niyyar fita,wasu kalar Jerin motocin ne suka tsaya guda biyar ne yau,jikin manager ne ya kama rawa da sauri ya isa wajen motocin nan ya kyale Amana tsaye.
Glass din aka sauke kasa suuuuuuu da hannu kawai akayiwa manager magana nan ya gane me master yake nufi, da sauri ya koma wajen Amana tare da riko hannunta, master ne yace a baki suya meat dinsa ki kai masa,hmm kuma sai ni kadai zan kai?haka yace to,nifa bai taba yi min ko da daga hannu ba guards dinsa ne suke min bayani sai yau da kansa ya min magana amma Da hannu ya kwatanta min kuma na gane.
Ita dai Amana shuru tayi nan aka hada mata suyar masters ta fito har motar da taga an zuge glass kasa ta karasa,ta window ta mika wa me kyau suya meat dinsa shikam kare mata kallo yayi a ransa yana dariyar wannan yarinya kamar namiji,wani tunani ne ya fado masa a ransa amma sai ya barshi,kallonsa tayi tana jira taga ko zai mata magana amma shuru sai ma gira daya dage daya irin lfy? A rude ta tsorata tare da matsawa daga jikin motar,manager ne ya cillo mata key din motarsa yace let's go,cafe key dayi tare da shigewa motar manager shima ya shiga gaba,nan fa Amana ta fara tuki cikin kwarewa da bajinta,
Motocin me kyau tayiwa over take ta wucesu fiiiiii, bayan sati daya yau suna wajen da manyan masu kudi suke zuwa domin wasanni,wasu ball,wasu table tennis,handball,bolly ball,wasu keke suke tukawa etc kowa da abinda yakeyi a wajen,wajene kamar a england,wajen manyan masu kudi tsabar son jin dadi irin na manager ya dauki Amana suka je wajen suma,
Amana dama ta iya table tennis da football ba laifi,dan haka wani dan yaro ta gani me matukar kyau fari kar dashi,yana gefe yana buga ball dinsa shi kadai,manager yana can zasu fara handball da wasu,
Amana zama tayi shuru ita daya,wajen yaron nan ta nufa tace let's play nan suka fara buga ball dinsu sosai,sai nishadi sukeyi kamar wani danta,sai yi sukeyi abin birgewa shi kanshi yaron yaga Amana ta iya ball,suna ta dariya,me kyau ne a tsaye a bayansu ya jingina da wata bishiya ya harde hannaye a kirji yana ta kallonsu, sai murmushi yakeyi.
Amana ce take ta cinye dan yaron nan da bai wuce 3yrs ba,haushi yaron yaji tare da kwace ball dinsa ya kwadawa Amana a jiki,ya dauki juice din dake kusa dashi ya watsa mata,tare da rufeta da duka,
Amana a ranta ta tabbatar wannan yaron bashi da kunya bashi da tarbiya,sai zagin Amana yakeyi,nan fa ran Amana ya mugun baci da wannan sangantarcen yaron marar tarbiya,tun yana dan haka amma yake irin wannan abu na cin mutunci,cinci (kinci) uwarki tayaka(talaka) kawai wannan yaron yace da Amana,
Amanafa ta gama kulewa ba imani ba tausayi ta sa kafa tayi short da yaron nan,nan yaron ya fadi can Tim bakinsa ya fashe sai jini,har wajensa taje ta mikar dashi ta fesa masa maruka har biyu,fuskarsa ta kumbura,dagashi tayi sama da hannu daya yana kuka yana am shory(sorry) Anty,bajan kayaba,zare masa ido tayi baka da kunya kana zagin manya,ko Baka da tarbiya?idan ka kara zagin wani na kamaka sai na ballaka na yankaka,
Jikin yaro na tsuma da karkarwar tsoro,ga baki na jini fuska ta kumbura,yace bajan kayaba promise u Anty.
Saukeshi tayi kasa ta zaro wani farin handkerchief ta goge masa bakinsa da fuskarsa,sannan ta bashi ruwan roba yasha,harda wanke masa fuska,tare da goge masa kayan ball din daya sa,bayanta ta juya tare da cewa sorry my boy Kaine u r too stubborn boy,gashi ka jawo zan ma illa,shoyi(sorry) Anty,ya haye bayanta tare da sakalo hannayensa ta wuyanta yana wasa da sarkarta,keke taje biya kudi tare da cewa yaron little rikeni kam zamu tuka keke,
Dariya yaron ya kamayi yana murna ya riketa kam kam,ta hau keken dashi a bayanta. Ta dinga tuki liiiii liiii iska na kadasu,yaron sai dariya yakeyi,
Bayan ta gama ta kara karbar hayar machine Lifan nan ma yana bayanta ta dinga tukasu.
Bayan sun gama yana gadon bayanta suna zaga wajen yayi bacci a bayanta.
AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳
20-25
By
AsmaBaffa
Wajen jakarta ta koma ta dauko wani dogon towel karami a ciki ta Goya yaron dashi a bayanta ta daureshi tam tam,ta koma cikin bishiyoyin dake wajen tana ta dan yawo dashi tana jijjigashi,tana jin son yaron a ranta tana inama danta ne wannan yaron, wajen table tennis ta koma duk table din a kwai mutanen da sukeyi wani table ne guda daya taga mutum daya ne a wajen securities sun zagayeshi suna bashi tsaro,yana ta buga tennis dinsa a nutse,wajen ta karasa tare da cewa Hello guys,juyowa mutumin yayi sai taga Ashe me kyau ne a wajen,
Guards din yayiwa umarni su dan matsa gefe ba tare da yayi magana ba,a ranta tana ko dai kurma ne mutumin nan,Allah sarki na tausaya masa,ga kudi ga kyau sai Allah bai bashi kunnen ji ba,Allahu Akbar,ita kadai take zancen zucinta ta,
Maganar kurame tayiwa me kyau da hannu wai tazo su buga game,a ransa yayi dariya wato ta zata shi kurma ne gashi har maganar kurame take yi masa,
Sai satar kallon yaron da ta Goya a bayanta da towel yakeyi Wanda yake bacci hankali kwance,da hannu ya tambayeta wannan dan natane?ai kuwa tace ae tare da murmushi tana kara jijjigashi,shareta yayi still tana tsaye a wajen sai buga game dinsa yake
cike da nishadi ko wannensu,gashi ta gama kasheshi da dariya kamar wata namiji yanda takeyin abu,a ransa yana gata me kyau she need to change her character wa zai aureta a haka,
Yaron dake bayanta Wanda take cewa little boy shine ya farka daga bacci,
Ido 4 sukayi da me kyau da yaron nan yaron ya buga kara tare da cewa Daddyna kayyi(kalli) nayi new Anty tace na daina zagin mutane,ta hau dani keke,da yifan(Lifan) har ma zaneni tayi Dana jageka(zageta), murmushi me kyau yayi Wanda ya jawo hankalin Amana kansa ta kura masa ido tare da jinjina kyau irin na wannan mutumi.
Yaron dake bayanta ta kwance ta saukeshi,da gudu ya tafi wurin me kyau,me kyau kuwa sai kallon yaron yakeyi yanda Amana ta fasa masa Baki tare da kumbura masa fuska,
Da sauri Amana tace my boy ina zuwa Jakarta ta dauko ta zaro wasu chocolate masu dadi guda 4 da sweet ta mikawa yaron,sai murna yaron yakeyi yana new Anty zakijo jidanmu?murmushi tayi tace yes,yace mu dinga kwana taye kina kaini cukul(SCHl) OK my Boy zanzo insha'allah,bye Amana ta dagawa yaron hannu tayi tafiyarta gabanta sai faduwa yake sakamakon me kyau da take gani kusa da ita,sai da ta bar wajen ta samu saukin zuciyarta ta daina bugawa.
Wurin Manager ta koma shima ya gama game dinsa suka wuce take away ya siya itama Amana ya siya mata ya sauketa a gida kana ya wuce. Shi kuwa me kyau securities ya wa Umarnin su zo akai yaronsa hospital a dubashi, ana ta jin labarin me kyau,
waye me kyau?
Me kyau dai Amana ce ta sa masa suna amma asalin sunansa ALIM USMAN MUSA,Babansa USMAN MUSA DA MAHAIFIYARSA FATIMA asalinsu yan Ethiopia ne,shi yasa idan ka gansu kamar wasu larabawa don a Ethiopia ma su daban ne kalar nasu kyau ya wuce na kasar Ethiopia,
Gaba daya dangin Fatima da iyayenta du suna kasar Ethiopia,
yayin da family Usman na jini suke a Nigeria,sabo da su dama su Usman Baban Alim da kannensa su Biyu a kano aka haifesu,anan suka taso suka girma har Sukayi karatun degree suka gama,dukiyar su ta gado ce tun asali su masu kudi,sun gaji dukiya,basa aikin Gomnati sai zallar business,Usman duk yafi yan uwansa kudi nesa ba kusa ba,sabo da yafi yan uwansa neman kudi,
Babar Usman wato kakar Alim,da kannen Usman Haj Sameera da Alhj Ishaq da iyalansu suke zaune a birnin kano cikin shahararriyar g.r.a shi kuwa yayansu Usman Musa sabo da harkokin tafiye tafiye da business ya koma Lagos da zama tare da matarsa da yaransa, Haj sameera tana auren wani engnr da yaranta maza uku mata biyu, sai Alhj Ishaq yaransa bakwai maza 5 manyan samari sai mata biyu,ko wannensu mata daya daya garesu,babu me biyu,kuma alhmdllh suna zaune lfy suna zumunci cikin so da kaunar juna,kasancewar matar Ishaq yar kano ce basa shiri da fatima matar Usman,
Sameera ma kanwar Usman basa shiri da matar Usman saboda da bata kaunar dangin mijinta kaf,Fatima bata son kowa ya rabesu har Babar Usman wato Haj khadija,suna kiranta Hajja, Usman zuwansa ethiopia wajen sauran danginsu a nan Allah ya hadashi da Fatima kyakyawar mace ya aureta har Allah ya azurtasu da yara.
NURA shine na farko 38yrs yake yana da mata zainab da yara biyu mace da namiji,yana zaune a Finland can yake aiki tare da iyalansa, sai ALIM me kyau yaro da kudi yafi kowa kyau a gidansu,ga dukiya da Allah ya azurtashi dasu,yayi degree da masters nasa a harkar kasuwanci a Germany, 31yrs yake, ASIYA 25yrs take wata uku kenan da gama degree dinta a London, sai Ameer Wanda yake Finland wajen Nura yana karatunsa yana level 2,21yrs yake kuma shine auta.
Ranar da yan fashi suka tare Alim kano yaje wajen danginsu ya dawo yan fashi suka taresu har Amana ta taimakeshi,
USMAN MUSA Baban Alim dattijon arziki ne,me hakuri da kyauta tare da son talaka,duk inda ake Neman mutumin kirki to azo wajen Usman Musa,
HAJ FATIMA kuwa Sam bata da mutunci ko kadan,bata son talaka,bata kauna wani ya rabi yaranta musamman Alim da yake me kudin gaske,
Bata kauna taga yaranta maza suna son wata mace don kar ma ta kwace mata yara,kishi takeyi sosai da matan yayanta maza,Nura ita ta zabo masa mata yar gidan wani kusa a Nigeria, bata kauna taga Nura na nunawa matarsa soyayya wai zata kwace mata yaro,sai ta dinga kishi,da farko da ta sa Nura ya auri Zainab sai murna takeyi ganin Nura bai son Zainab,kasancewar zainab ta gari ce sai ta sace zuciyar Nura,ganin Nura na nunawa zainab so tace lallai sai ya saketa,Nura kuwa yaki yarda haka Abbansu ya nemawa Nura aiki a Finland ya turashi can da iyalinsa,sai bakin ciki Mum Fatima takeyi,
Amma tace duk ranar da Nura ya dawo Nigeria dole ya saki matarsa Zainab,shi yasa Nura yaki dawowa Nigeria,yana son zuwa amma halin Mahaifiyarsu bazai barsu ba,Abbansu ma ya ce kar ya dawo,shi kanshi halin Fatima matarsa na damunsa,yanda take wulakanta danginsa da Wanda ya rabesu gashi yana kaunar matarsa,addua kawai yake mata Allah shiryeta.
Alim yaro da kudi,babban dan kasuwa ne na gaske,sosai yake neman na kansa,bai dogara da kayan wani ba,da kudinsa yake harka,me kwazone da basira tare da zafin nema,ya mallaki dukiya da kadarori masu matukar yawa tun yana 17yrs yake Neman nasa yana karatu yana business.dan Jari Abbansu ya bashi me yawan gaske ya fara juyawa,kafin kace me Allah ya albarkaci abin.
Kyakyawan gaske ne na karshe,fari ne sosai sai kace dangin turawa,idanunsa ma dara dara masu kyau wasu Golden kamar irin kalar na mage shi ba na mage ba,irin dai na turawa,gashinsa kuwa baki ne sosai me santsi da kyalli,girarsa kuwa wow har hadewa takeyi,hancinsa siriri ba sosai ba,normal hanci me matukar kyau,bakinsa karami da shi red, habarsa yar doguwa,dauke da siririn saje da dan gemu kadan,sumar kansa ya tarata da dan yawa gyaran gashin sa ma abin kallo ne,
jikinsa me yar kiba ba ramamme ba kuma ba me kiba ba,gashi karkarfa da damatsa,kirjinsa me fadi sumul dashi,gashi dan dogo dashi ba da yawa ba,yatsunsa kansu abin kallo ne da birgewa,namiji ne na gaske ko ina Alim ya shiga sai ya haske wajen,Amana idan ta tsaya kusa dashi duk da cewar itama yar farace amma sai ta tashi a chocolate me hasken gaske lol,
Alim mutumin kirki ne na gari ga hakuri da kawaici,me kyauta,ba ruwansa da duniya,baya magana sai da dalili,idan zakuyi 1wk tare da Alim indai ba muhimmin abu bane to baza kaji maganarsa ba,ko a cikin danginsa iya gaisuwa ke hadasu sai su kwana 2 basu ji yace ko hi ba,yafi yin magana da hannu,ido,etc amma bakinsa baya magana sosai,shi yasa Wanda basu sanshi ba sai suce kurma ne,haka frnds dinsa sai su yini tare amma daga gaisuwa baya kara cewa komai,
Best Frnd dinsa Mubaraq shima wani hadaddan handsome chocolate ne yaso ya canja halin rashin magana na Alim amma ya kasa.Mubaraq dan gidan wani minister ne a Nigeria,kuma shi lawyer ne,sosai Alim yake kaunar Mubaraq, shima Mubaraq haka.
Halin Mum fatima kuwa abin yafi yawa a kan Alim domin kuwa sai da ta tursasa Alim Auren mata har guda biyar tana sawa ya sakesu dole,
Matarsa ta farko da mum dinsa ta aura masa Salma ce baya sonta yana kyautata mata,ganin haka Mum ta ce dole ya saketa ko ta tsine masa,haka ya saketa yanzu haka Salma ta auri wani mijin tana zamanta lfy, Ramlat Mum ta kara aurawa Alim itama baya sonta,amma tana hutawa,nan ma Mum ta koreta, Sakeena ma hakan take,sai Maryam itama tasa aka saketa, ta biyar itace Nusaiba itace wacce Alim ya dan fara Sonta har yayi saduwar aure da ita ta samu ciki,itace Alim ya hada dabara sai suka dinga nunawa Sam Alim azaba yake nuna mata,shi yasa Mum ta kyaleta tare da Alim,har cikinta ya isa Haihuwa ta haifi zankadeden yaronta me sunan Abba Usman suna ce masa Aabid,satinta biyu da haihuwa Allah yayi mata rasuwa,
Alim yayi bakin ciki duk da cewar ba wani sonta yakeyi ba Nusaiba yarinyar kirkice, shekarar Nusaiba daya da rasuwa Mum ta koma Ethiopia kasarta ta samowa Alim wata yar Uwarta Sageera,amma Sam Abban Alim yace wlh bazai aura ba,ya gaji da Halinta,tana sa dansa auri saki ganin Alim me hakuri ne,Abba yace idan ta sa Alim ya auri wata matukar bashi ya nemo da Kansa ba to taje ya saketa,shike nan Alim ya samu lafiya,
Sai dai Mum ta kulle a ranta baza ta bari wata ta kwace mata danta ba,haka kawai wata tazo ta cinye mata dukiyar yaro ba,
Yayinda take burin Asiya yarinyar kirki yarta ta auri miji na gari me sonta kajifa son kai.Aabid dan Alim a wajen Mum yake zama shi yasa Sam Aabid bashi da tarbiyya,saboda yanda take kaunar jikanta bata yi masa fada,
Ko kukansa taji ta dinga zage zage za a kashe mata jikanta,ko makaranta idan yace baya so to baza ta bari yaje ba,
Aabid ya gama lalacewa tun yana karami ya iya zagi da cin mutunci iri iri,shima baya son talaka wajen kakarsa Mum duk ya koya,Alim abin da ya dameshi wajen Mum yaje yace ta bashi Alim su zauna tare sabo da ya samu abokin zama a gidansa so bored yake.
Sabo da son da Mum kewa Alim ta yarda da kyar ta bashi Dansa Aabid,watan Aabid Uku kenan tare da Alim suna rayuwa tare,yau da suka hadu da Amana yaune birthday na Aabid ya cika 4yrs da haihuwa,yaune kuma Amana tayi maganin rashin kunyar Aabid,
Har ga Allah Alim yaji haushin Amana irin dukan da tayiwa dansa amma sabo da hakuri da kawaici irin nasa bai nuna ko ransa ya baci ba,kuma dama rashin kunyar Aabid ta dameshi ya rasa ya zaiyi dashi,amma gashi ya hadu da Amana ta koya masa hankali.
Ci gaban labari
Asibiti suka nufa da Aabid nan doctor ya dinga masifa taya za ayiwa yaro irin wannan dukan,amma Alim shuru yayi bai ce komai ba,bayan sun dawo da dare gidansu ya tafi wajen Mum tare da Aabid,Mum tana ganin Aabid baki da fuska a kumbure ta gigice tana lfy me ya sami jikana?Alim ne yayi Sauri yace Mum wata yayiwa rashin kunya ta zaneshi,
Aifa Mum tuni ta fara zagi tana wacce shegiyace yar matsiyata ka nuna min ita wlh sai na batar da ita, a hankali Alim yace calm down Mum shi fa ya zageta,dan uwarta ita wacece da baza a zageta ba,ai da nasan gidansu har iyayenta sai sunyi nadamar haihuwarta,Aabid ne yace Mum ki kyayeta ina conta ta au dani keke,ta ciya min sweet,
Rufe min baki sai na kwato ma yancinka,kai dama Alim na lura ba son yaron nan kake ba,idan baka so ka dawo min da jikana aikin banza na gaji da shirmenka,
Kai a dole me hakuri ko kana gani za a kashe bawan Allah,nan fa Mum ta fara lilita Aabid tana Lallabashi tare da cewa bazai koma wajenka ba sai yayi 1wk a wajena ya huta,ba yanda Alim ya iya haka ya mata sallama ya koma gidansa.
AsmaBaffa
Tnx alot readers.
✳CIRANIN AMANA✳
25-30
AsmaBaffa
Mum din Alim ce ta dauki Aabid sai lallabashi takeyi ta rasa inda zata sa kanta,haka ga bacin ran yau birthday na Aabid amma ko dan party ba a shirya masa ba,part din Abba ta nufa da Aabid dauke a kafadarta,ko sallama kasa yi tayi ta shiga zuruf tare da cewa kalli yanzu dan Allah Abban Alim abinda yaron nan yakeyi ya dace,jiba yanda yana gani wata Jaka ta Zane min jika,Abin haushi ma Alim ya kasa hadawa yaron nan ko dan birthday party,
Kallonta Abba yayi da mamaki tare da cewa party addini ne ko dole ne,wannan dabi'ar yahudawa ce da mutanenmu suka daukarwa Kansu da shirme,da ka hada birthday party gwara ka yini kana karatun Qurani,ko tasbihi,ko azumi kana yiwa kanka addua sosai a wannan rana yafi ka kunna kida.
Tabe baki Mum tayi tana yo dama ai haka zakace,ni dai kawai Allah ya hadani da miji ba wayayye ba,kana da kudi,ka zaga duniya,kana shiga mutane amma ka kasa wayewa,na tabbatar duk yarana halinka na gidadanci suka dauko, fuuu tayi waje dauke da Aabid ranar kusan kwana tayi a zaune tana jinyar Aabid dinta.
Alim ne kwance bisa lallausan royal bed dinsa Wanda ya kai karshe wajen haduwa,tunani yakeyi yanda zai samo me kula da Aabid wacce zata bashi tarbiyar da ta dace uwa ta ba danta,kafin Allah ya kawo masa wacce yake so ya aura,
Arniyar Wayarsa ya jawo tare da kiran Mubaraq best Frnd dinsa,yana dagawa a hankali Alim ya fara magana sai ka saurara sosai zaka ji me yake cewa,bakinsa da kyar yake motsawa Frnd maganar da ka bani shawara kan na nemo me kula da Aabid kafin na samu nayi aure,so ya kake ganin za samu?
Mubaraq ne yayi Dariya yace bari zanwa Mama na maganar a samo wata ka barmin komai a hannuna,alright Frnd cewar Alim.
Bayan sati daya tsakani Mubaraq ya kawo wata dattijuwa gidan Alim,Alim shi bai da damuwa nan ya karbeta yana zaune a luntsumemiyar kujera kafa daya kan daya yana latsa waya,ko a bai cewa Rakiya dattijuwa ba,tunda tazo ko da ta gaisheshi ma hannu kawai ya daga mata kamar wani sarki,a.c ce kawai ke ratsa Rakiya har karkarwa takeyi,
Wani remote ya dauka tare da dannawa minti daya sai ga wani me aiki ya shigo da sauri,Umarni ya masa kan ya tafi da Rakiya yayi Abinda ya dace,suna fita ya tura Driver ya dauko masa Aabid wajen Mum,
Sai da Mum ta zage driver tas sannan ta yarda Aabid ya bishi,
Rakiya aka kaiwa Aabid Nan fa yaro ya canja fuska yana yatsina tare da toshe hanci kamar yaga kashi,
Da dare ko da Rakiya tazo shiryashi sai da ya zageta sosai sannan ya tafi part din Daddy sa,Alim duk abinda zakayi zai wahala ya ma magana bare ya hanaka,dan haka tun Rakiya na hakuri da Halin Aabid har ta fara dukansa, kuma Alim bai taba ce mata ta daina ba,
Yana kallonsu watarana Alim na zaginta ita kuma rakiya tana zaneshi amma Alim bai ce musu komai,har Rakiya ta kwashe 2mnths tana kula da Aabid,yauma kamar ko yaushe Suna palon Alim suna kallon film sabo da Alim shi ba ruwansa da kar a shiga inda yake matukar baza ka takurashi ba
,Alim yana ta aiki a system Rakiya tana canja Chanel taga wata tasha suna haska BF ta bar tashar Abinta Suna ta kallon,Alim ne yaji nishi kamar ana Sex da sauri ya kalli TV yaga abinda yake faruwa,Aabid yana ni ki kaimin cartoon Chanel amma ko kallonsa Rakiya taki yi,da Sauri Alim ya dauki remote ya kashe TV gaba daya,ba tare da yace komai ba ya ebo kudi ya mikawa Rakiya yace take this na gaji da Halayenki maza na Sallameki,zama tayi zata fara bashi hakuri,securities ya kira sukayi waje da Rakiya.
Sosai Alim ya shiga matsanancin bacin rai,Mubaraq ya shaidawa matsalar,3days aka kawo wata budurwa ita kuma,nan ta fara kula da Aabid,Aabid kuwa ya tsani wannan budurwa sabo da tsawar da take daka masa,
1mnth ltr budurwar nan ta kamu da son Alim kullum sai ta dinga zuwa tana zama a kusa dashi,yau ma yana nutse kan wata chair 2 seater yar budurwa ta fito tana karairaya tana zuwa kusa da Alim ta zauna kafadarta na gugan tasa,mikewa yayi har ya daga hannu zai mareta ko me ya tuna sai ya fasa,itama kudinta ya bata ya koreta,
Basu gaji ba suka kara kawo wata tsohuwa Yakumbo,nan ma Ya kumbo ta dinga yiwa Alim sibare tana satar masa kudi,ba shiri ya sallameta itama,haka Mubaraq ya dinga kawowa Alim masu kula da Aabid amma basuyi dace ba,sai ma kara lalata Aabid da sukayi,ko wacce halin tsiyarta daban.
Gashi Aabid kullum zancen new Antynsa yakeyi shi ita yake so a kaishi wajenta ta hau dashi keke,Aabid da Alim basa wata hira a tsakaninsu bare wasa,saboda Alim bai son Surutu.shi yasa in ka shiga wajensu sai kagansu shuru kowa harkar gabansa yakeyi kamar basu San juna ba,ko da Aabid yazo yana so suyi wasa da Alim sai kaga Alim yayi murmushi ya bashi hakuri cewar yaje yayi shi kadai,
Watarana yayi kuka haka har ya saba,babu wata shakuwa tsakanin Uban Alim da dan Aabid.
Shi yasa Aabid ya cewa Alim Daddy ka kawo min new Anty ta nafi sonta,shareshi Alim yayi a ransa yana tab wannan yarinyar marar tarbiya me yin abun maza,Amma tunda Aabid ya dameshi zai kai Aabid wajenta Saturday ya yini a wajenta yaga me zai faru.
Haka Alim ya kulla shawararsa.
Gidan baki kuwa can wudil kauyen su Amana Baba yaji Amana shuru tunda ta tafi Amana sau Uku ta kirasu a waya suka gaisa da yan gidan gaba daya,shi kuwa Baba sau daya ya taba kiranta yajita Lfy shike nan bai kara ba,itama Umman Amana ko ta kan Amana bata bi bare tasan halin da take ciki,su kuwa sauran kanne da yayye dadi ma sukeji jaraba ta bar musu gidan zasu Shana,yayinda manyan mazan suke kudu suma cirani suka tafi suna can suna sheke ayarsu.
Wani abokin Baban Amana dake jigawa state ne ya aiko da yarsa yar 16yrs domin Baban Amana ya taimaka ya kaita makarantar Boarding dake garin kacako kasancewar kusa suke da garin,haka sulemanu harka ya karbi Amanar yarinyar nan hannu bibbiyu zai kaita schl ranar Monday,yarinya dai Mariya tana nan dakin Uwar gidan Sulemanu harka kafin a kaita schl,Sulemanu sai kallonta yake yi duk inda ta gifta,akan haka ma ya rage fita wajen aikin yayinda ya gama danawa Mariya tarko.matansa suna hankalce dashi sunga take takensa,sabo da haka suka kara kafawa suka tsare kan a samu a tseratar da yarinya daga tarkon mijinsu fasiki.
Yau Saturday 10am motocin Alim suka parker a bakin wajen suya nasu Amana,manager guard yayi wa magana,few seconds sai ga manager,yau Alim magana yayi da kansa,pls I need to see that Girl dake aiki anan she look like a Boy,nan manager yace oh Amana Hausa Girl.yeah cewar Alim
Cikin harshen turanci Manager yace tana gida sai yamma take zuwa aiki,Alim yace bani Address nata idan ka sani,da sauri manager ya bawa Alim Address na Amana,
Juya motocinsu sukayi har gidan Dan Uzuri,Alim yasha mamakin ragargajewar gidan,yanzu wannan yarinyar anan take zama Amma kayan da take sawa bai dace ace anan take zama ba,
Gashi gaba daya yaga unguwar tantiran yan iska yan bariki take zama,layin su Amana kuwa a unguwar ma na daban ne sai ka shahara a iya shege sannan zaka iya zama ciki.
Sosai Alim yake mamaki tare da cewa no wonder yarinyar take karshe wajen rashin kunya.dole ma Amana baza ta taba zama ta gari ba cewar Alim,Dan Uzuri ne ya karaso jikin motocin Alim a gigice,
Guard ne ya masa magana tare da kwatanta masa yarinyar da suke nema.
Da Sauri yace Amana yanzu baza a sameta a gida ba tana majalisarsu.
Suna haka sai Ga Amana sun fito daga wani corner tare da wasu maza su Uku,sai hira sukeyi.
Alim yana kallonta ta mudubin motarsa a ransa yace lallai wannan ta shahara.
Kafin kiftawar Ido Dan Uzuri ya isa wajen Amana tare da Nuna mata jerin motocin Alim wasu kalar da bata taba gani ba,Dan Uzuri yace wlh ba ruwana Amana Idan masu kudi kika tabo,baza ki jawo min bala'i ba,dama nasan rashin mutunci sai yasa kin hadu da ajalinki,gasu can sai kije wajensu ke suke nema,haka gari banza masu kudi haka baza suzo nemanki ba,
Kallon guards din Amana tayi ta gane Me kyau ne mamaki tayi yanda yasan gidan da take sai ta tuna dasu manager nan tace tabbas manager ne ya basu Address dinta,a fili tace to me nayi musu kuma hmm bari naje naji,
Da Saudi Dan Uzuri yace ke kika sani wlh kar ki nuna kin sanni,idan sun hallakaki na buga waya can kauyenku,aikin banza me jaye jayen tsiya,to nafi karfinki li'ilafi kuraysh baza ki jawo min ba,lakadaja akum a kanki.
Dan Uzuri wani lungu yasha tare da boyewa ciki yana lekowa yaga me zai faru yasan Amana dai kam sai dai ya bugawa Sulemanu Harka waya ya sheda musu ai Amana ta tsufa a prison.
Bude mata kofar motar Alim akayi ba tsoro ta shiga,Amana basu saba da gaishe da mutum ba ko iyayensu basa gaidawa dan haka Sallama kawai tayi ta zauna a cikin motar wani sanyi da kamshi yana Ratsata,ta lumshe ido wani niima,bugawar zuciya hade da kwarjinin me kyau sun taru sun mamaye mata zuciya.
Ta rasa dalilin da yasa me kyau yake mata kwarjini,kuma sai ta dinga jin masifar tsoronsa,da kyar ta iya daga kai ta kalleshi jin shuru baice komai ba,Subhannallah wani azababben kyau taga ya kara,Wanda ya wuce kwatancen me tunani,gashi sanye cikin wata rantsatsiyar shadda ta garari milk color,dinkin irin pencil dai dai jikinsa ga kan nan bai sa hula ba sai gashi baki sidik luf dashi me yawa yash gyaran fuska,ga wani dan Saje da dan gemu das.
A hankali kamar bazai magana ba cike da gadara da izza yana latsa waya ba tare da ya kalleta ba,ya Umarci Guard ya dauko Aabid a dayar motar,nan da nan matakan tsaro suka dauko Aabid ai ido hudu Amana tayi da Aabid da karfi ya kwalla kara ta murna da jin dadin ganin New Antynsa,nan ya karaso da dan gudunsa ya dane jikin Amana sai murna yakeyi,tare da cewa new Anty zan biki,alright My sweet Boy, I missed u cewar Amana,mic (miss)you too Aabid ma yace,ta gefen ido Alim ke kallonsu yana jin Dadi a ransa,Aabid dinsa zaiyi farinciki yau.a hankali Alim yace kuje da Dare after Isha zanzo na daukeshi,Ok Baàbaà sai kuma tace au Sorry pls.
Daukan Aabid tayi tare da sabashi a kafada nan Aabid ya ce Bye Daddy shima Alim ya daga masa hannu suka ja motocinsu suka tafi, sun bar Amana cike da Mamaki mutum bai Santa ba amma ya kawo Mata dansa.Dan Uzuri ne ya fito daga inda ya boye shima yana mamaki a ina Amana ta samo masu kudi haka har yaronsu suke bata raino.
AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳
30-35
By
AsmaBaffa
Ina mika Godiyata ga dubban masoyana makaranta wannan novel.
Dan Uzuri a fili ya firta ko ni Dana taso cikin lagos banyi aboki ko da me Mota ba,amma wannan me suffar mazan gashi tayi masu motoci ma,ko da yake mace ce suna kwashe zumar ta dole haka ta faru.
Wajen Amana ya kara ta watsa masa masa wani matsiyacin kallon da ya sa Dan Uzuri ya bar wajen ba shiri tare da cewa yarinya duniyace bariki ce kici kema watarana ta cinyeki.ni dai ina fada miki kar ji jawo mana abin kunya a gida ato.
Share shi Amana tayi ta dauki Aabid suka shiga zaga gari,sai wasa sukeyi,sai kallon Aabid mutane keyi sunga bature dan Madara,gida suka dawo tayi musu girki suka ci suka sha sai bacci,bayan sun tashi daga bacci,daukansa tayi suka shiga wani boutique na yara,ta siyawa Aabid wata farar Riga Armless da jean black 3qutr na yara a kantin ta gwada masa dai dai shi,sweets dasu biscuits ta siya masa da yawa sannan ta kaishi wajen aski dan kansa ba gyara,nan Amana tasa akayi masa wani arnen aski na yan gayu,na samari masu ji da Kansu,yaron sai yayi masifar kyau,bayan sun gama gida suka dawo ta cire masa kayan jikinsa ta wankesu fes ta shanya,abinci suka kara ci sannan tayi wanka shima yaron tayi masa,
Vaseline ta shafa masa hannu da kafa,gashin nan ta shafawa man gashin da take amfani dashi ta kara gyara masa gyaran gashin da akayi masa,
Turare ta fesa a kayan yaron da ta siyo masa sannan ta sa masa,sosai ta shiryashi yayi kyau,itama shiryawa tayi cikin wandon jean pencil dogo Red,rigarta T-shirt siririya amma doguwa har gwiwa tasa fara,ta fesa turaruka sosai,sannan ta dauko siririn gyale Red yafa sai tayi kyau sosai,
Sai kamshi sukeyi,karatun qurani ta fara Koya masa suna yi dama Amana tana son Bawa yaro tarbiyar karatu,nan da nan yaro ya iya suratul Iklassi,sai wasansu sukeyi har magrib tayi sukayi Sallah da Azkar,
Kayansa data wanke sun bushe kwasosu tayi ta linke tare da zubawa cikin leda wata me kyau irin ta gift,bayan Sunyi Sallar Isha ta kara fesa turare ta fesawa Aabid shima sai dariya yakeyi yana tsokanarta,
Karatun da Amana ta koya masa Aabid yake ta faman nanatawa yana jin dadi,suna Haka Dan Uzuri ya fado dakin jiki na bari tare da cewa kiyi sauri ki kaiwa masu kudi dansu yana waje yace kuje.
Tsaki Amana ta ja tare da gallawa Dan Uzuri Harara ta dauki Aabid yana New Anty ci goyani pls,goyashi tayi a bayanta tare da daukan ledoji biyu a hannunta suka yi waje.
Tana dubawa ta ga motocin sa sai taga wata Azazababbiyar mota guda daya sabuwa gal me shegen kyau a kalla ta ba million 30 baya,horn ya danna musu nan ta gane yau a mota daya yazo,karasawa sukayi wajen motar,Aabid sai faman washe baki yake yana rera karatunsa,
Mazaunin baya ta bude tare da saka ledojin a baya,sannan ta bude gaba ta zaunar da Aabid dake ta faman yin karatunsa,kan Aabid ta shafa tare da manna masa kiss a kumatu good night my Boy,murmushi kawai yaron yayi tare da fafin Anty Jan kwana da ke,kijo muje jidanmu,zanzo da kaina Boy never mind ok,kai kawai ya daga mata amma Baiji dadi ba yaso ta bisu sunyi bacci tare,
Alim Wanda ke a mazaunin Driver tsayawa yayi tsam yana ta kallon Aabid dinsa da Anty Amana,gashi har karatu yaji a bakin Aabid,gashi ta kaishi aski,ta sa masa sabon kaya abin sai ya birgeshi shar shar dasu,dubanta ta kai wajen Alim taga sanye da 3qtr da wata black T-shirt yayi kyau,ga wani kida na tashi a motar me ratsa zuciya,
Amana hannunta biyu cikin aljihu tacewa Aabid bye shima yace bye ta wuce abinta tana bouncing ba tare da ta yiwa Alim magana ba shima bai mata ba.
Motarsa ya ja ya bar unguwar a nutse,yayinda Amana ta juya ta shiga gidansu cike da Mamakin halin Alim baya magana ko kadan kuma shi ba kurma ba,ko dan yana da kudi ne oho.
Alim kuwa mamakin yanda yaga Aabid yake neat dashi gashi ta gyarashi harda sabon kaya ga abinda yafi birgeshi shine karatun da yaji a bakin Aabid yanzu dama wannan yarinyar tasan addini yana ganinta me kamameceniya da maza Jahila Ashe tasan addini
Tunani ya Shiga sosai akanta.
Dole ya dauketa ta kula da yaronsa kuma shima dole ya gyara mata zama ta daina abubuwan maza,nan tunaninsa Alim ya tsaya cak.
Kwance Amana take kan tabarmarta tana tunanin gidansu da halayen yan Uwansu nan kewa ta cika mata zuciya tana so taje gida taga yan Uwanta,da iyayenta amma sabo da halayensu Sam bata marmarin ta koma,nan take hawaye ya fara kwaranya a idanunta tana tausayawa Kanta,gasu da iyaye amma ba gata,ba a damu dasu da rayuwarsu ba su dai kawai an haifesu ne gasu nan a zube a duniya.
Gidan Baki kuwa Baba har yau yaki kai Maryam makaranta tunda aka bashi Amanarta yaki yarda ya kaita,so yake ya cimma Burinsa,kamar kullum yau cikin dare ya lallaba dakin Goggo Uwar gida inda Budurwar take,suna cikin bacci ya lallaba ya fara shafa kafar maryam yana murzawa a hankali,yarinya tana ta baccinta,nan ya kara kaimi ya koma kirjinta ya shiga shafa boobs dinta a hankali yana lumshe ido,sosai yake washe baki yana latsawa tare da murzawa,kamar a mafarki Maryam ta mike zumbur tare kwala ihu,Goggo ce ta mike cike da mamakin Ganin Baba yana ta aikin shafa boobs din yarinya,
Goggo ce tayi tsalle tare da make masa hannu tana zaginsa tsohon banza wlh kayi asara yar cikinka yar Abokinka Yar Amana kake Neman lalatawa rayuwa,wlh nayi Nadaman Aureka,matsiyaci mazinaci,fasikin banza kuka ta saki da karfi nan take matan gidan suka fito dama sun San haka zata faru ba wata wata suka fara zagin Sulemanu Harka shima yana zaginsu,Maryam sai kuka takeyi,su kuwa ashar ce kawai ke tashi a gidan,
Da kyar Goggo ta lallashi maryam, washe gari da sassafe Goggo tasa Maryan ta shirya da kanta ta dauketa ta kai ta makarantar kwana tayi mata komai daya dace.
Ko da Sulemanu Harka yaji labari an kai Maryan schl Ashariya da tsinuwa ba wacce baiwa Goggo ba da sauran matan gaba daya.
Maman Alim ce zaune a kujera sai Huci takeyi tare da tabbatarwa kanta Alim bai isa ya auri wata ba koda zata mutu sai zabinta,gashi ta rasa inda zata shawo kan Abban Alim,tunani ta shiga kan taje wajen kawarta Hajiya Talatuwa suyi shawara yanda zasu bullowa abin,tana zaune wata yar Aikinta cikin ma'aikatan tazo tare da ajiye mata juice tazo tsiyayawa jikinta Na rawa sabo da tsoro ta zubar da kadan a kasa,kafin ta dago da kanta Mum ta kwada mata wani mahaukacin Mari kafin tayi wani yunkuri Mum tasa kafa ta daketa nan wannan dattijuwa ta Daki jikin kujera tare da zubewa kasa wanwar,
Mum kuwa mikewa tayi ta hau sama dalaf dalaf tare da Jan tsaki sunfi goma tare da cewa shashashai talakawan banza matsiyata.
Alim da jerin motocinsa ne sukayi parking a gidansu,bayan an bude masa kofa ya fito cike da tafiyar nan tasa ta izza da kasaita sanye yake cikin wata farin yadi kal dinkin fitted ya amsheshi yasha kyau hannunsa dauke da wayoyinsa guda biyu yana latsawa,cike da yanga kamar bazaiyi magana ba yayi sallama a palon Abbansa,nan ya samu Abba yana shan fruits,har kasa ya gaishe da Abbansa,Asiya kanwar Alim ce ta shigo cikin shiga ta alfarma,wata shadda ce maroon a jikinta tasha aiki,laaa Ya Alim sannu da zuwa kallonta Alim yayi ke kuma yaushe kika dawo daga kano?jiya Na dawo,bro ina Aabid? Yana schl mana,ya Alim Ya Nura yace ya kiraka wayarka a kashe,zan kirashi later, ok ,Ya Alim? Tsawa ya buga mata ke kin dameni ban son surutu,shidai Abba yana jinsu har Mum ta Shigo,
Harara ta zabgawa Alim wato da ban shigo ba Abbanka kawai zaka gaisar ka wuce ko?am sorry Mum tsaki taja, nan Abba yace sarkin kishi aikinki kenan kishi.
Shuru tayi daga bisani tace dama haka zakace mana tunda sun nuna sunfi sonka, kallon Alim tayi tare da cewa Ina jikana? Murmushi yayi tare da cewa yana nan lfy yana schl.
Hirar Nura dake Finland suka farayi Mum kuwa daure fuska tayi bata kaunar ayi mata zancen Nura saboda ya gudu da matarsa yana Nuna mata so,sun kwace mata yaro suna cin kudinsa a banza ya daina sonta.
Alim shikam halayen Mum dinsu mamaki ke bashi,Asiya ma Sam bata kaunar halayen Mum dinsu,
Yau Sunday yaune Alim ya shirya domin kai Aabid wajen Amana saboda ya dameshi kan yaje wurin Antynsa.
Amana kuwa yau bala'i ya sameta sunyi fada da wani Igbo yayan manager sosai sukayi fada akan ya shafa mata wuyanta,
Zaginsa ta farayi Wanda ya fusata ya cafki boobs dinta a taron mutane,nan take Amana ta dauki kujera ta kwada masa a kai,sai jini tako ina,
Ba tare da Manager yayi tunani ba ya fesawa Amana mari har Uku tare da korarta daga wajen aiki. Ita Amana ba korar ce ta sata zub da hawaye ba illa irin yadda bro din manager ya shafa mata breast agaban mutane Wanda ba a taba kwatanta mata hakan ba,
Tun Saturday da yamma tana gida tayi kuka ta gaji har yau Sunday idan ta tuna Babansu Sulemanu Harka shi ya ja musu sai kaga Hawaye Na sintiri akan fuskarta idonta ya kumbura yayi jajir bata da wani kuzari,gashi wani marar Imani yana binta bashin dubu sittin 60 gashi kudin hayarta ya kare Dan Uzuri ba mutunci,abincinta saura kadan ya kare dama da aikin ta laru zata biya wasu don Dashi take son shiga dama sai ta samu ta rage wasu to gashi aikin da ta dogara ma dashi an koreta.
Addua takeyi sosai da nafeela kan Allah ya kawo mata mafita a wannan Al'amari,11am tana zaune a dakinta tayi tagumi hawaye Na zuba Dan Uzuri ya rufto dakin ko lura da Kukan da takeyi baiyi ba yace ke yar chakwaskwas kizo inji masu lokaci me kudin nan yana waje ya bar dakin da sauri kamar zai kifa.
Fuska Amana ta wanke idon nan a kumbure jajir dashi ta fito, Wanda ke binta bashi taci karo dashi,yana busa sigari yace ke yayane?kwana 2?ina kudin ne? Fuska a daure Amana tace kasan bazan ci ma kudi ba dama lalura tasa Na karba, ke yarinya naga kina wani masifa ne,mu zakiwa Jan ido dan me cin uwarki yanzu Na makeki kuma wlh gobe ba mutunci dole kibiyani,dalla ware banza, Amana yau dan tana cikin Bakin ciki ne da tuni an kwashi yan kallon,Alim dake mota sauran jerin motocin suna bayansa yana kallon Abinda ke faruwa, kuma da Alama fada sukeyi.
Tunda ta taho yake kare mata kallo yau salab salab take tafiya fuskarta ba annuri, ido ya kumbura Jajir haka ta karaso jikin motar kanta a kasa tana wasa da zoben azurfarta me matukar kyau.
AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳
35-40
By
AsmaBaffa
Ina ganin sakonninku ta ko ina readers ina godiya sosai.
Tun kafin a bude motar Aabid ya fara ihu da murna yana kiran New Anty,idonta cike da kwalla ta daga masa hannu,ganin zata iya fara kuka yasa ta yi saurin bude motar tare da daukan Aabid ta juya cikin sauri ta bar wajen,Alim kuwa yasan tabbas da gani tana cikin damuwa ba haka ya saba ganinta ba.
Motocinsu suka juya suka wuce direct office ya nufa,ita kuwa Amana yini sukayi da Aabid yana debe mata kewa,bakin cikinta ya yaye sai dai in ta tuna sai kaga tayi shuru kwalla Na Neman zubo mata,karfinta ya gaza,mace me raunice tunda ta taso cikin wahala take tunda ita ke ciyar da kanta,Sana'a kala kala da rayuwa duk tayi,gashi yanzu ba uwa ba uba ba wani Wanda zai taimaka mata ko tana kusa dasu baza su amfana mata komai ba,sai bacin rai da bakin cikin halayyar su,a rayuwa ta ya mace ace babu Wanda ya dau nauyinta,ita kewa kanta komai ,dole yanzu ta gaza kuma dole ta shiga wani yanayi.
Wajen magrib sukayi wanka ta shirya Aabid ta mayar masa da kayansa da yazo dasu tare da fesa musu turare,wani cornflakes ta hada musu ita da Aabid suka sha suka koshi,sunayin Sallar Isha wani ya shigo tare da sanar da ita ana kiranta a waje,
Aabid ta goya suka fita dan tasan bazai wuce Daddynsa ba,tana fita ta hango wata bakar mota me shegen kyau da tsada guda daya,da alama shi ya kawo kansa,wajen ta karasa yana zaune a mazaunin driver cikin shiga ta alfarma,kamshi da kyalli yakeyi,ba bata lokaci ta bude gaban motar ta zaunar da Aabid Wanda ke kuka shi wajenta zai kwana,da kyar ta lallabashi,haka kawai taji bakin cikin dake damunta ya dawo sabo dal,nan take ta fada tunanin rayuwarta bata da wani plan,bata ma San inda ta nufa ba,ita ba karatu ba,ita ba aure ba to waye ma zai aureta a haka,ga shi bata ma gaban iyayenta su Burunsu ta nemo musu kudi,ba ruwansu da halin da zata shiga,
Nan take zuciyarta ta kara karyewa ita waye ma zai so ta a haka yanda take kamar namiji,wani hawaye masu dumi da zafi ne suka shiga ambaliya a fuskarta,sheshekar kuka ta farayi ba shiri ta rungume Aabid kam kamar zata Fasa masa kashi taci gaba da kukanta a hankali,duk inda taso danne hawayenta da zuciyarta abin yaci tura,
Shuru kakejin motar babu Wanda yace ko ehem,kukanta kawai ne ke fita kadan.
Alim kuwa wani tausayinta ne ya lullubeshi da alama akwai Matsala babba tare da ita,bai ce mata komai ba illa bundle Na 1k dubu Dari kenan ya mika mata,Aabid kuwa shima kukan ya fara,yana Anty wane ya dakeki?
Ki fadawa Daddy ya fadawa sojoji,murmushin yake Amana ta farayi ga hawaye Na zubar mata har ta samu saukin zuciyarta,ba tare da ta kalli Alim ba cikin rawar muryar me kuka tace Na gode Allah kara budi ta juya tare da barin wajen tana share Hawaye.Alim yayi tunanin bai kamata yanda take kula da dansa ba ya kyaleta haka iya kudi kawai ya bata bai ji matsalarta ba,
Horn ya danna mata Wanda ba shiri ta juyo a firgice tare da dawowa wajen motar budewa Alim yayi tare da kiranta ta side din kofar sa,ya kai 5mnt tana tsaye gabansa ba tare da yayi magana ba,da kyar ya furta what's wrong with u?meke damunki?da kyar ta kalleshi kadan sannan tace ba komai Na tuna iyayena ne,suna ina parent din naki?ko sun rasu Alim ya tambaya.
Hawaye ne ya zubo mata sannan tace suna kano state, CIRANI aka turo ni lagos Neman kudi,
Da Sauri Alim ya zaro ido waje Ci...ra...ni? Kai ta daga masa tare da cewa yes,mamaki da alajabi ne suka cika Alim,yace aikin da kikeyi fa yau naje bakya zuwa?ae an koreni munyi fada da wani yana son taba min jiki that's y.
Tausayinta Alim yaji tare da cewa wannan Unguwar da kike a lagos bata mutanen kirki musulmai bace,gidan da kike zama Na karuwai nai,hmmmm aini na jawowa kaina tunda da yarda Babanmu ya kawoni cirani, Amana tace tayi shuru.
Damace tazowa Alim dan haka yace ko zaki Bini gidana Na baki aikin kular min da Aabid?matarkafa?cewar Amana,ta Dade da rasuwa,eyya Allah ji kanta, ameen cewar Alim,jeki gobe zan turo driver ya daukeki kiyi shiri.OK tnx Allah kaimu.
Nan ta wuce shima ya bar unguwar cike da mamaki.
Amana tana komawa dakinta tsalle, rawa,sannan tayi nafeela ta godewa Allah cike da murna ta fice kudin da Alim ya bata ta je a Daren ta biya bashin da ake binta,
Bayan ta dawo gida Dan Uzuri tayiwa bayani sannan ta bashi kyautar dubu goma sai murna yakeyi.
Washe gari da wuri Amana tayi shirin komai iya kayan sawa Dana kwalliya ta dauka kawai ta zuba a wata trolley da Manager ya siya mata kafin suyi fada,kayan girki etc kuwa duk ta bawa Dan Uzuri su.
Har kayan sawa ta bayar da wasu iya sababbi ta eba,har boutique taje ta kara siyo inner wears da wasu kayan ta shirya komai irin zata koma gidan yan gayu masu kudi.
Yau Abincin da Amana taci ma me tsada ne,tun 3pm take jiran azo a dauketa amma shuru har tayi la'asar shuru,sai wurin 5:30pm sannan wani driver da motarsa daya me kyan gaske yazo Duk Wanda Amana ta sani dake unguwar sai da tayi musu sallama,da ance unguwa zaki canja da zama? Sai ta yatsine fuska tana yanga sannan tace wlh kuwa Na gaji da zama a nan unguwar tayi min kauye da yawa,Na samu babban aiki a company, haka Amana ta dinga sambada karya kala kala ita dole big girl kar a rainata.
Dan Uzuri har bakin mota ya raka Amana yana hawayen karya,yana to 'yata ga number ta a dinga tunawa da mu,ki tsare mutuncinki kamar yanda Na sanki da kamila,nutsatsiya,a yafemana Amana yar albarka ya karafashewa da kukan maula, driver kuwa Jan motar yayi ya dauki hanyar Gidan Alim,Amana kamar anyi mata bushara da gidan Aljanna saboda murna.
A lagos dinma wata tsantsararriyar GRA suka shiga wacce kaf lagos ba kamarta a kyau sai ka cika me Naira za ka Gina gida cikinta, yawanci turawa ne da sauran jar fata suke zama a cikinta,saboda komai nata tsarin turai ne,gidan da ya fi kowanne kyau,girma da tsaruwa suka nufa,wani gate katon gaske suka nufa wani remote driver ya matsa sai ga gate yayi sama ya dage kansa,abin fa ya bawa Amana mamaki da alajabi tunda take rayuwa bata taba sanin wannan unguwar ba,da badan ita bata da tsoro ba to da tuni ta fara kuka za a yankata,
Cikin harabar gidan kuwa ma'aikata da masu tsaro birjik,wasu sun hau tsani suna goge glasses Na windows,wasu Na bayin flowers wasu kuwa motoci suke gogewa dukkansu sanye da Uniform dark blue wando da riga fara,motoci ne birjik gasu nan sai ka rasa wacce zaka zaba,
Wani new design Na sweeming pool kamar kogi haka yake yabi ta wani lungu ya mike sosai ruwan garai garai blue shar dashi,
Driver ne yace fito hajia,Jakarta ya ja har ciki suka shiga,kalle kalle kawai Amana keyi,kofar ma wasu numbers akayi dialing,sanyi da kamshi ya bigeta,ga wasu kujeru a palon ko a film bata taba ganinsu ba,
Wata TV a jikin bango kusan Rabin bango,sai wasu manyan flowers suna walwal da haske tiririn kamshi Na fita daga jikinsu,sai wani center table Na glass,wanda shima matsa wani abu akeyi a jiki yana juyawa a hankaki,
Center carpet kuwa dake palon idan ka taka sai ka zata nutsewa zaiyi dakai cikin kasa,tana nan zaune tana baza ido wata dattijuwa ta kawo mata abinci saida ta cika gabanta da kayan ci da sha,
Amana da maza ta saba bata Hulda da mata hannu ta dagawa dattijuwar nan tace ai sai Iya Allah dai ya saka,kallo dattijuwa tabi Amana dashi tunda ga shigar Amana matar a ranta tace wai wa kuma Alhaji ya kwaso mana me kama da maza haka,
A mazan ma yan jagaliya,wani matsiyacin kallon matar tayiwa Amana tare da tabe baki taja tsaki tayi gaba,Amana wacce zuciyarta ke tafasa game da matar nan taso daukan mataki sai kawai ta shareta tare da Dora hannunta a kahon zuciyarta ta danne tana lallashin kanta tare da cewar sorry Amana calm Down be patients a fili takeyin maganar,Amana duk kayan dake jikinta ganinsu takeyi masu tsada Na yan gayu amma tana shigowa gidan Alim sai ta raina kanta gaba daya.
Top din data Dora saman rigarta ta cire ta Dora saman kujera ta gyara zamanta a kasa kan tiles ita Amana bata son zama ko kwanciya a kan laushi kujera ko bed
Shi yasa ta baje a kasa tare da jawo tiren abinci ta fara ci ba tsayawa hannu biyu ta jefar da cokular a kasa tasa hannu dayan hannun tana yagar kaza daya kuma ta dauki Apple ta balla,ta dauki kankakana,ta gutsiri waina ta dangwali miya,ta yagi kaza ta kora lemo ko ruwa ta ebo fried rice ta watsa a bakinta.
A fili cikin santi tace banza ta fadi Allah sakawa me gidan nan da Aljanna,wuyanta ta Sosa tace me bamu Allah ka bashi,Wanda bazai bamu ba Allah Bamu tare
Sai da taci tayi bamkam kadan ta rage,Karambanin Amana inda taga matar ta shiga nan ta mike ta fara lallabawa zata ga mene a ciki,handle din kofar ta murda a hankali sai ta ganta a wani daki ya gaji da haduwa,wata kofar ta bude ta cikin dakin sai ta ganta a wata doguwar Palo ya gaji da haduwa yasha kayan alatu,kara mikewa tayi sai taga wata kofar
Budewa tayi sai kawai ta ganta a wani makeken kitchen,hade da store,kofar baya kuma ta kitchen zaka fito compound,
Komawa tayi ta kara shiga kitchen nan fa ta kwashi kallo,fridge ta bude tare da dauko wata fura bowl guda dan karami tayi sanyi,a tsaye ta shanye furar tas ta ajiye bowl din ta dawo palon da take,
Wani cycle steps ta gani daga palon yayi sama,ga wata kofa opposite din wacce tabi dazu,nan ma kara budewa tayi bed room ne da toilet ciki,ta kara bude wata kofar sai ta kara ganinta a compound amma tana hango wasu part guda biyu a gidan da har can taje taga Ashe daya part din Na yan aiki mazane daya kuma part din Na baki ne da mata yan aiki,
Baki ta tabe tare da cewar ni dai bazan zauna a bangaren can ba wannan part Din da Alama shine Na Alim dan haka a nan zan zauna yafi haduwa kajifa Amana,har magrib tayi tana palon,cycle steps din nan ta fara takawa har ta haura sama,
Wow......nan Amana taga aljannar duniya kiri kiri,wakeken Palo ne yasha kujeru Na garari,ga dinning can gefe,wata tafkekiyar plasma TV,da wasu manyan speakers,flowers manya, sai tafkeken hoton Alim a manne,
Jikin bangon kansa abin kallon me,komai Na saman fari kal ne,Na kasan kuma peach color,yan aiki kuwa light brown ne nasu,
Amana fa ta gama rudewa da kallon haduwar gidan,wani kofa ta gani a cikin Palon guda biyu,daya ta nufa ta bude a hankali,wani tangamemen bed ne da sip zureriya,sai madubi,har bedsheet komai fari kal neat,
Ko ina gidan kamshin dadi da sanyin ac, daya room din ta bude subhannallah ta firta a fili komai fari shima yafi ko ina kyau da tsaruwa, komai Na dabanne,
Alim ta hango zaune kan sallaya yana Sallah, Aabid Na jikin gado a zaune yana game.
Asmabaffa
✳CIRANIN AMANA✳
40-45
By
AsmaBaffa
Murmushi Amana ta saki kana ta kutsa kai cikin dakin da sallama, a gigice Aabid ya waigo tare da kwala ihu ya rugo a guje wajen Amana tare da daka tsalle ya daneta yana oyoyo new Antyna I miss u,
Dariya Amana ta saki tare da kankame Aabid suna ta murna tana shafa masa kai,my sweet boy I really miss u,yau tare zamu kwana,za muyi wasanmu cewar Amana,shi kuwa Aabid Jan Amana yayi har Bed din Alim yana nuna mata game dinsa,
Amana kuwa ta manta da wani Alim dake zaune kan sallaya yana Azkhar,kan gadon ta haura tare da Aabid suka fara wasa ba ji ba gani sai dariya sukeyi,kafin kace me sunyi waja waja da bed din Alim,pillows duk a kasa rabin bedsheet dinma yana kasa,
Alim kuwa ba shiri ya daina azkhar tsananin mamakin me suffar maza ya rufeshi,idan banda rashin tarbiya taya zata shigo musu gida har bed room ta hau kan bed ko gaisuwa babu ba komai,in hakane ai tafi Aabid ma rashin tarbiya,ina bazai iya zama da wannan ba,
Rashin tarbiyarta yayi yawa da kuruciya da hauka,ran Alim yayi matukar baci kan abinda Amana tayi yanzu,wata razananniyar tsawa ya daka musu,wanda suka gigice gaba dayansu,musamman Aabid nan take ya fashe da kuka saboda ya tsorata sosai,
Cikin tsananin fushi Alim yace ke baki da hankali?baki da tarbiya?dabbar inace ke?dakikiya jahila wacce bata san me takeyi ba,jakace ke?wa ya baki damar shigowa har part dina,kuma bedroom har bed dina,zaki shafa min cuta a bedsheet,dakikiya dan Na daukeki aiki ba dama Na baki da zaki zo ki min halin mahaukata ba,
Da karfi yace get out now,Amana wacce mamaki da bakin ciki suka taru suka cunkushewa a zuciya,idonta ya kada yayi jajir tabbas yau da badan Alim bane Wanda Allah ya sa mata tsoronsa,kunyarsa da kwarjinin da yake mata to da wani ne yau sai dai a dauki gawarta ko tasa,amma Alim ne tsoronsa takeji amma duk da haka Amana sakkowa tayi daga bed din tana kumbura tare da cijewa,tace hey Baabaa control mana ya kake yawa,hannuna tasa biyu a aljihu tana tafiyar gadara,wannan ai yawa ne master eh idan dan Na hau Bed dinkane ai sai kace na sauka,ya zaka dinga zagina,
Bed din ta nuna masa idan akan wannan bed din ne easy master ni laushi bai dameni ba ko a kujera bana zama bare bed a dalilin danka Na hau,amma ka sani bed dasu kujeru basa birgeni,kaci sa a Kaine ka zageni haka,cije lips tayi jajir dashi gwanin sha'awa tace a kiyaye master tayi gaba abinta ta dawo palon kasa Wanda aka ajiyeta tun farko.
Alim kuwa mamaki ya gama kamashi yayi mutuwar tsaye,Aabid kuwa kuka ya sa an yiwa new Anty fada,kukan ne ya dami Alim,ba shiri ya figi hannun Aabid ya sauko dashi palon kasa wajen Amana,Amana ta bararraje tayi mala mala a kan tiles tana tunanin duniya,kawai tuna irin zagin da Alim ya mata takeyi,
Idonta ya tara kwalla du duniya babu Wanda ya taba zaginta haka sai me kyau,sabo da bakin ciki kawai kuka Amana ta fara babu damar ramawa.
Yana zuwa da Aabid ya ganta haka kallo daya yayi mata ya dauke kai Aabid ya jefa a kan cikinta,a firgice ta mike ba tare da tace komai ba tsaki taji ya ja tare da ficewa daga gidan gaba daya tare da escort dinsa.
Sai lokacin Amana ta sauke ajiyar zuciya tare da saurin kallon Aabid tace kai yaro Daddynka masifaffe ne wlh,idan Na gaji guduwa zanyi,Aabid kuwa dariya yayi kamar me hankali yace Anty me kirkine Daddyna,zai daina fushin fa.
Suna zaune suna kallon cartoon wannan matar ta dazu ta dawo tana watsawa Amana kallon Banza tace taso ki dauko jakarki Na kaiki dakinki,Amana bata ce komai ba ta dauki Jakarta hannunta rike Dana Aabid har part din yan aiki mata aka kaita,mata birjik kowacce da uniform dark blue skert da Riga me cola da dogon hannu fara kal,sai gyale dan siriri fari.
Ko wacce bin Amana take da kallo,sun ganta kyakyawar budurwa ajin farko,ga shigar niggogi tayi abin dariya,ko ina matan dariya sukeyi suna gulmarta,
Bata kulasu ba amma sun ga dan gidan Oga Alim a hannunta,wannan ya nuna me renon dansa ya dauko,
Tunda suka ga haka sai suka tsani Amana suna jin haushinta tare da yi mata hassada tazo ta fisu fada wajen me me gidan gashi ita CE me renon dansa,sunga irin matan daya dauko a baya sun sami kudi da fada a part dinsa ma suke zama amma kwana kadan ake korarsu da wannan suka kwantar da hankalinsu cewar Amana ma korarta za ayi kwanan nan zasu ji abin tsiyarta,
Ko wacce da abinda take fadi kan Amana,har aka kaita wani daki lafiyayye,dan gado karami sai sip karama da madubi da toilet dinta ba sharing, kamar dakin dai yan mata,komai yaji,kayanta ta ajiye sannan tayi wanka sukayi sallah tare da Aabid, sannan tayi masa wanka tare da shafa masa mai sai kamshi sukeyi towel daure a kugunsa,suna ta hirarsu tana koya masa karatu har 9:30 Na dare sannan Alim ya dawo,ya duba ko ina baiga Aabid da Amana ba,da sauri ya kira wannan dattijuwar shugabar ma'aikata mata na gidan wato Saude,
Tana zuwa Alim yace Aabid da wannan yarinyar fa?soshe soshe Saude ta kama sannan tace Na kaita part din yan aiki suna tare da shi a can,harara Alim ya watsawa Saude yace ni nace ki kaita wani waje har yarona za akai wajen yan aiki?how dear u ko kin taba ganin me kula da Aabid a part din masu aiki maza ki kawo min su nan,
Da sauri Saude tace ayi hakuri Ahaji hakan baza ta faru ba insha'allah,jiki Na bari cike da jin haushin Amana ta fada dakin bako sallama,to uwar iya kizo inji Alhaji yana part dinsa ki dauki kayanki da Aabid can zaki zauna,munafuka saura ayi dan hali muna nan muna zuba ido kwanan nan za a koreki,kar kice zaki mike kafa matsiyaciya.
Amana ta dau Aniyar cin uban su saude sai nan da yan kwanaki,
Aabid ta nade cikin towel sosai fuskarsa kadai ake gani,goyashi tayi ta kinkimi akwatinta ta tafi part din Alim zuciyarta cike da tsoro,
Ta rasa dalilin da yasa take jin tsoron Alim,a palon kasa ta sameshi yana kallon News,sallama dauke a bakinta ta shiga,taga bakinsa ya motsa amma Sam bata ji muryarsa ba.
Aabid ta sauke cikin towel yayi fresh dashi,ba tare da Alim yayi magana ba ya mika mata uniform dinta,karba tayi tana budawa taga skert, a ranta tace yaufa akeyinta,a fili kuwa cike da tsoro tace master....master ban iya sa skert ba pls ka bani uniform me wando,
Ko kallon inda take baiyi ba kuma baice komai ba,shuru Amana tayi can tace to Master a bani kayan Aabid zan sa masa,sannan ka nuna min dakina zan je Na kwanta.
Sai da ya dauki 15mnt sannan ya mike yace biyoni ki karbi kayansa,a hankali ta bishi har bedroom dinsa ya nuna mata Sip wani part shake da kayan Aabid,akwati ta cika guda da kayan sawar Aabid har uniform din schl dinsa sanannan Alim ya gwada mata address din dakinta,godiya sannan ta sauka kasa dakin da ta fara shiga da farko me kofa biyu,daya kofar wacce zata kaita kitchen,bedroom din ya gaji da haduwa kamar Na Amarya,
Aabid ta shirya cikin kayan bacci itama tasa nata ta sukayi Addua suka kwanta tare,Aabid ya makalkaleta ya rungumeta sai kamshi sukeyi bacci me dadi ya kwashesu.
Washe gari da asubar fari Amana ta tashi Aabid sukayi sallah abinda Aabid bai taba yi ba sallar Asuba amma yau Amana ta sa yayi har azkhar ta fara koya masa,ita Amana fa yanzu bata da burin da ya wuce taga yaro me tarbiya,tana sha'awan hakan saboda gidansu kaf babu me tarbiya,shi yasa ma ta ke son koyawa yaro tarbiya duk da cewa ita bata da ita,ta sani amma tana so ta koyawa wani,shi yasa take koyawa Alim tofa kaji su Amana.
Wanka da brush tayiwa Alim sannan ta shiryashi cikin uniform din schl dinsa,ta yi wanka itama tare da tsaftace lungu da sako Na jikinta sannan ta fara shiri,uniform din Ma'aikata da Alim ya bata Riga da skert su ta ebo,tana kunkuni tasa pant da wani tight iya gwiwa,sannan tasa skert din,Amana kwai diri da sura,kamar an gwada ta skert din das a jikinta,sannan tasa rigar,gyalenta ba fari Alim ya bata ba kalar skert ne dark blue,Amana gaba daya ji take a takure take ta dabaibaye,ita da wando ta saba,
Gyalen maimakon ta yafa sai ta daura kawai a kanta ta gyaran room din tas,sannan ta fesa turarenta ta fesawa Aabid ma,7am ta riko hannun Aabid suka haura saman Alim,
Aabid da gudu ya shige bedroom Alim yana cikin bacci yaji Aabid Na tashinsa Daddy ina kwana Anty ce tace Na dinga Ce maka ina kwana,
Alim a hankali ya mike tare da shafa kan Alim yana morning son har kayi shirin schl,ae Daddy Anty tana jirana zanci abinci ta kaini schl,maza to jeka kace tazo ina nemanta,
Da gudu Aabid ya koma wajen Amana yace Anty Daddy yace kizo,gabanta ne yayi mugun faduwa kamar kwai ya fashe mata a ciki haka ta shiga dakin tana tafiya bata saba da sa skert ba,kawai garin tafiyar niggoginta skert ya hardeta ji kake rim ta fadi a kasan tiles Na dakin Alim,Alim dake kwance nade cikin bargo yana kallonta,ko sannu bai mata ba,haka ta mike tana Sosa kanta,tunda Alim yake bai taba sanin uniform din ma'aikatansa Na da kyau ba sai a jikin Amana,a ransa sai ayyana irin kyanta da kyan diri irin Na Amana amma take cutar kanta kullum abubuwan maza takeyi.
Ko gaisuwa Amana bata yi ba kawai sallama takeyi ita bata saba da gaida mutane ba,shima Alim bai damu ba yace kije kitchen ki hadawa Aabid abinci, kece kullum zaki Na dafa masa abinci,ki kaishi schl ki daukoshi ke da driver,
To kawai Amana ta furta tare da fadawa tunanin family dinta,jibi gata da son karatu, amma su iyayensu Sam ba ruwansu da ilimin yaransu,gashi suna son karatu ba dama,a fili kuwa cewa tayi master dan Allah ka sani a makarantar Aabid kaga ni a ss2 Na tsaya sai mu dinga zuwa muna dawowa tare,
Bazan saki ba cewar Alim,kafin ya rufe baki Amana tace master lada zaka samu Ina fada ma taimakon irinmu zai iya jefaka a aljanna,Fice min da gani cewar Alim, baki ta zumbura tare da ficewa tana kunkuni.Alim a ransa yace lallai yarinyar nan bata da kunya karshe,zan gyarata very soon.
Kitchen Amana ta shiga Wanda ke part din Alim,Dattijuwa Saude ta iske a ciki tana shiryawa Alim girki,ko sallama Amana batayi ba ta fara shiryawa Aabid da kanta abinci, minti kadan ta soya chips, da egg,sai tea me kauri,ta damawa Aabid oats da madara.
Saude sai kallon Amana takeyi tana dama haka take da kyau,lallai karfa yarinyar nan ta karbe gidan nan watarana, a fili Saude ta ce insha'allahu hakan ma baza ta faru ba,
Amana tana aikinta sai ji tayi Saude ta bangajeta, a zuciye Amana ta shaki wuyan Saude tare da makata jikin bango sannan ta dinga zagin Saude tare da kara makure Saude ta kwala mata ludayin miya a goshi kafin kace me goshin Saude ya kumbura ya fashe yayi wani sumtum,Amana kuwa ta gama aikinta ta jera komai a tire ta dauka ta haura saman Alim,
Ganin haka yasa Saude tace wlh baza ta kyale Amana ta mata illa ta tafi a banza ba,Saude Ce ta suri mubirgin miya tabi Amana a guje har Saman Alim,tunaninsu Alim bacci yakeyi,turus suka ja birki ganin Alim zaune cikin shiri da Alama fita zaiyi,Saude uwar makirci nan take ta fashe da kuka tace Alhaji kalli yanda wannan yarinyar tayi min duka a kitchen,ta fasa min kai akan kawai nayi mata nasihar gishirin zaman duniya,yar daba ta fara dukana harda cewa itace ajalina ta kara fashewa da kuka,Alim sarai yasan karyar Saude, Saude kuwa ganin Alim bashi da niyyar magana yasa ta kara bude baki zatayi magana,ji kake fafff Amana ta make mata baki tare da cewa ki kyale mana master dallah haka karki sa masa headache,
Bakin ciki yasa Saude shako wuyan Amana,Amana kuwa me karfin maaza Hannu tasa ta mirdewa Saude hannu, wayyooooo cewar Saude tana ta kara,Amana tace ina daga miki kafa Iya ke babbace kija girmanki kafin Na fara taka ki,wannan abin ba komai nayi miki ba wlh ki kiyayeni ko a garinmu Na kano bani da mutunci ki tambayi tarihina kiji,
Saude da kyar ta kwaci kanta ta arce da gudun tsiya,Alim Na kallonsu a ransa yace naga Alama yarinyar da ta ja da yan fashi ta fansheni ai ta kai karshe a duniyanci.
A fili kuwa tsaki yaja sannan a hankali yace idan Aabid yayi late a schl sai kin karbi punishment,da sauri ta zauna ta bawa Aabid yaci ya koshi itama taci sannan ta daukeshi ta wanke masa baki neat ita kuma ta dauko aswaki zurere Na itace ta sa abakinta sukayiwa Alim sallama driver ya daukesu a rantsatsiyar mota ta kai Aabid schl sannan suka dawo tare da driver,tana ta dirzar bakinta da itacen aswaki,Amana idan tayi brush da asuba to duk cin abinci ko sallah sai tayi aswaki haka tsarinta yake,har palon ta shigo tana aswakinta,
Alim taci karo dashi zai fita ba Wanda ya kula wani ta wuce dakinta ta kuskure bakinta ta kwanta sai bacci.
0 comments:
Post a Comment