_page→1_*
..........6urum aka turo k'ofar tamkar za'a cireta.
Zaune yake a bakin gado yana harhad'a wasu takardu, hankad'o k'ofar basashi ko gezauba barema ya d'ago Dan yasan bai wuce matarsace lubna ba, da wanan d'anyen aikin.
Ta huro hanci had'eda rik'e k'ugunta da hannu biyu, wata uwar harara ta watsa masa, wadda baimasan tanayiba.
*_Umar fharuq!!._* takira sunansa cikeda masifa.
Bai amsataba baikuma d'agoba, harkar gabansa kawai yakeyi.
Lubna dake tsaye tana karkad'a jiki takuma k'ufla, Dan haka tacigaba da magana cikeda tsiwa.......
Gsky nikam nagaji, kasan yadda zakayi dani wlhy, shekaranjiya kacire yara daga makaranta bance maka komaiba, yaukuma shine zakazo da mutane suna zazzagaye gida?, shin mikake nufu?, ko shima gidan saidashi zakayine?, to wlhy idanma tunanin haka kakeyi ka canja, Dan bazan rayu banida tsuntsu baniga tarkoba.
Aidama nasan tunda aka aura maka waccan 'Yar k'auyen, saimun shiga bala'i, gashinan tun ba'aje ko inaba komai yak'are, mayya mai farar k'afa tashigo rayuwarmu, saura kuma kurwarmu ake bibiya alashe yanzun...
d'an tsaki yaja idonsa akan takardun dayake zubawa acikin wata 'Yar jaka, saida yagama tsaf sannan yad'ago fararen idanunsa yana kallonta, yanunata da d'an yatsa lubna kishiga hankalinki, kinsan banason shirme ko?, gidakam zan saidashi idankuma nakine saiki hana, inama yimiki albishir daki fara shiri Dan nanda kwana biyu zamu barmusu gidansu.............
Jar ubannan kai, wlhy Umar baka isaba, ainima inada hak'k'i da gidan, tunda 'ya'yana sunada gado.
Kansa ya girgiza yana rataya jakar akafad'a, ya ce, "mahaukaciya kawai, saiki bari saina mutu kafin yazama gadon nasu mtsoww.
Umar nikake kira mahaukaciya?!.
Bai tanka mataba yatako cikin nutsuwa yanufi hanyar fita......
Da Sauri tasha gabansa tana huci, wlhy babu Inda zakaje saika sanar dani wacece mahaukaciyar?.
Kallon sama da k'asa yay mata, batareda yayi maganaba yaja tsaki tareda ra6awa ta gefenta zai wuce.
Da Sauri takuma shan gabansa.
Afusace ya ce, " wlhy koki tashimin a hanya, kokuma na kashe fuskaeki da mari......
Toka marenin mana, nagadai Nima ALLAH yabani hannun dazan rama.
Ya ce, "ko?.
"eh, kozaka gwadane?."
Wani k'asaitaccen murmushi yasaki, yara6a tad'ayan gefenta yafice yana cije le6ensa.
Binsa tayi da kallo tana girgiza jikinta alamar tsumuwar bala'i, saikuma ta rushe da kuka.
Na ce, "tofa, anayinta."
Shikam koda yafito d'ayan 6angaren ya Shiga, babu kowa a falon, sai sassanyan k'amshi dana AC dake tashi, TV ma a kashe take, hanyar wani d'aki yanufa.
Tana zaune abakin gadonta dayasha gyara, ananma k'amshine mai dad'i dasaka zuciya nutsuwa ke tashi, ta rabga tagumi, daga ganinta Kasan tana duniyar tunani.
Gyaran murya yayi had'eda sallama.
Firgigit tad'ago tana kallonsa, sai kuma tazamo daga gadon Baki narawa ta ce, "yaya ina yini.
Atak'aice ya amsa da lfy, yacigaba da fad'in kifara shirya kayanki nanda kwana biyu zamubar gidannan...... Baijira cewartaba yafito abinsa.
Wasu siraran hawaye suka zubo daga kumatunta, Afili ta ce, "na Shiga uku ni Asma'u, shima gidan ka saida ya Fharuq?!, nikam naga ta kaina, karfa maganar aunty Lubna yazama gsky, ta rushe da kuka maiban tausayi........
_nakalli zarah, Zarah takalli Xoxo, mukayi tsuru tsuru tamkar munafukai, Xoxo ta ce, " tawan ta'ina zamu fara?, na ce, "umm tawan tambayi Zarah kotanada idea nikam banida fus._
_Zarah ta gyara tsayuwarta, hannunta rik'eda Biro da 'Yar takardar d'aukar rahoto, ta ce, " bily nimafa na toshe Dan naga gidan kowa a rikice yake bansan wazamu tunkara yabamu labariba?, Xoxo kozakije wajen lubna?._
_Kam bala'i babu inda zani daga rakkiya?, agabankufa mijinta yakirata mahaukaciya, sannan kucemin naje tasaukemin na jaki._
_Dariya muka gumtse nida Zarah danjin zancen Xoxo, Zarah ta ce, "bily fa?._
_Na ce, " um um kodai ke ki gwada, nisainayima wannan magana?._
_Shiru Zarah tayi, Dan itama batason komawa wajen lubna........_
_Zuwacan Xoxo taja numfashi idonta akan Zarah, ta ce, "Zarah nibamfa gane mi tawan take nufiba?, catayifa murakota d'aukar rahoto, amma sai wani shirin lik'a mana aiki takeyi?._
_Harar Xoxo nayi, amma tawan idan kuntayani na buga labarinnan naga ba fad'uwa kukayiba ko?._
_Hakane, amma gsky nikam bazan iya da wannan iya bala'in matar tasaba, kumafa ni sonsama nakeyi, Dan guy d'in yahad'ufa._
_Dariya muka shek'e da ita nida Zarah, Zarah ta ce, " haba 'Yar uwa kice kishi bazai barkiba kawai, ammafa Nima bily bawai zan tayaki bane, namiki rakkiyane kawai, saidai mukoma gidan zan tayaki da shawarar yanda zaki d'auki wannan rahoto._
_To shikenen ngd Zarah muje, kekuma tawan dazanmiki hanya ki aureshi ammafa yanzu nafasa._
_Kai tawan nidakefa ba'a jin kammu?._
_Aikodai yau za'aji...........🤥😏._
*_tab masu karatu akwai aiki Dan bansan yanda zaku sami cikakken labarinba, tunda masu d'aukar Rahoton duk matsoratane._*
*_Daga miss xoxon Zarah Bukar, harni bilyn Abdul duk fararen kurayene_*
_amma ni bilyn Abdul zan kawo muku cikakken labarin, tunda su o e anji tsoro😏._
Kikasance dani danjin yadda zata kaya😻😘.
Bilyn AbDul ce👌🏼
*_luv you all_*
*_(((S))).....2017_*
[11/14/2017, 5:05 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻typing..........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
_Sadaukarwa_
*_miss Xoxo na_*
*_Zarah bukar_*
*_Ayusha muh'd_*
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._*
*_page→2_*
...........Tundaga k'ofar gida nafaracin karo da wasu manyan motoci akorikura har uku, duk an loda musu kaya, ra6awa nayi tagefensu nashiga cikin gidan, lallai tashi ya tabbata nafad'a azuciyata ina bin ko'ina nagidan da kallo.
Asma'u naga tafito da akwatuna biyu ahannu tanaja, Umar dake jingine da motarsa yana latsa waya yad'ago yana kallonta, d'an ta6e bakinsa yayi yana kauda kai daga kallonta, aransa ya ce, "yarinya tamkar mara laka ajiki?, komai nata salaf-salaf......
Maganartace ta katse masa tunaninsa ta ce, " yaya gasu.
Baiyi maganaba ya ajiye wayarsa saman motar, but yabud'e mata tasaka akwatunan, yarufe sannan yad'auki wayarsa yabud'e motar yashiga.
Asma'u tana tsaye sai faman bin gidan da kallo takeyi, kwata-kwata zuciyarta babu dad'i takeji, tasan yaya umar ma yana dakewane kawai kasancewarsa mutum jarumi mai dakiya da kawaici, duk 6acinran da Umar zai shiga mawuyacine kagansa shinfid'e afuskarsa, mutumne daya iya 6oye sirrin zuciya........
Ganin bata shigoba yay mata horn.
Da sauri tabud'e motar amma bata shigaba, tad'an sunkuyo ta ce, "ya Fharuk Anty Lubna fa?.
K'aramin tsaki yaja, yace batana canba tund'azu, kinafa 6atamin lokaci.
Jiki a sanyaye tashiga motar yaja yafice daga gidan zuciyarsa namasa zafi, amma sai ambatar innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un yakeyi.
Tuk'i yakeyi ahankali tamkar bayaso, dagashi har ita babu mai iya magana, lokaci-lokaci ita takan share hawaye, yana kallonta ta gefen ido.
Ak'ofar wani matsakaicin gida yay farking, koba'a fad'aba nanne gidan dazasu dawo, domin annan muka tadda motocin akoru kurarnan sunata aikin sauke kaya dashigar dasu cikin gidan.
Kad'an ya kalleta, kishiga ciki su Hasiya da Rafi'a da fatee duk sunanan sune zasu tayaki gyara kayanki, ni bara naje wani waje.
To ALLAH yatsare, saika dawo.
Ameen, yafad'a akan la66ansa.
Bud'e motar tayi tafita, harta d'an fara tafiya saikuma tajuyo, ya Fharuk kayanfa?.
Baitanka ba saida yatada motar, kije idan nadawo zan shigo dasu yanzu Sauri nakeyi, magana yakeyi amma ko Inda take baya kallo.
Itama kanta ta jinjina tajuya tashiga cikin gidan, abakin matsakaicin bak'in gate d'in sukai karo da matasan samarin dasuka gama Shiga da kayan nata.
Sannu tayi musu sannan tashige ciki.
Bin ko'ina takeyi da kallo, gidan k'aramine irin ginin talaka mai k'aramin k'arfi, ko'ina shage yake da siminti lumus, haka tak'arasa cikin gidan tana raba hanya.
Abakin fanfo taga Afrah da Amrah yaran Anty Lubna sunata wasa da ruwa, bata musu maganaba gudun kar cibi yazama k'ari Dan Anty lubna batason abinda zai ta6a 'ya'yanta ko kad'an.
K'ofar falon tatura tashiga, Rafi'a da fatee Hasiya sukazo da gudu suka rungumeta, itama rungumesu tayi sunamai murnar ganin juna.
Hasiya ta ce, "kai Anty Asma'u kinganki kuwa, wlhy kinyi bala'in k'yau, gidan ya Fharuk ya kar6eki.
Hararar hasiya tayi cikin sigar wasa, Hasiya kina nandai baki canja haliba wlhy.
Dariya sukayi suduka, Asma'u tabi falon da kallo, babbane sosai, sai kowace kusurwa da akwai k'ofa.
Ganin kallon da takema falon yasa Rafi'a fad'in wlhy Anty tsarin gidan yayi sosai, kinga nan family falone, wancan k'ofar shine naki, akwai falonki da bedroom sai bathroom, wancan kuma na Anty lubna ne, itama iri d'ayane da naki, wancan na tsakkiyar kuma na ya Umar ne.
Murmushi Asma'u tayi, tace ALLAH ya tabbatar da alkairi to.
Ameen suka fad'a suduka.
Kama hannunta fatee tayi, tana fad'in zomuje kigani harmun fara had'a miki bedroom d'inki.
d'akin daya kasance NATA suka nufa, tuk'uru suka Dage suna aiki, kafin k'arfe biyu sungama komai har babban falon sun saka kujerun dasuka kasance ada na 6angaren bak'i agidan dasu dasuka taso, d'akin Ya Umar suka shiga, shima tsaf suka gyara masashi ko'ina yad'auki haske.
Duk bidirinnan dasukeyi basuji motsin Lubna ba sai yanzu, duk sunzube a family falo suna maida numfashin Hajiya lubna tashigo itada Suhaima k'anwarta.
Suhaima tabi falon da kallo tana wani yatsine fuska, Anty lubna wai kina nufin anan ya Umar zai ajiyeki?, aiko 'yan aikin gidanmu sunfi k'arfin zama acikin wannan kangon?.
Baki lubna ta ta6e kibarsa kawai Suhaima Nima INA rakashine naga iya gudun ruwansa, amma wlhy bazan zauna awanan k'onannan gidanba saikace wata fak'ira, shima yasan bamu gaji tsiyaba wlhy.
A to yakamadai kid'auki mataki, wannan gidan saidai su o e wad'anda dama atsiya aka taso, shigarta wannan gidan ai ita k'arin cigabane.
Rafi'a tamik'e danufin maida murtani dantasan sarai da Asma'u suke.
Da Sauri Asma'u tarik'e hannunta tana girgiza mata kai alamar a'a kartacr komai.
Lubna ta gallama Rafi'a harara, to tabbatacciya da dakika tashi dukanmu zakiyi?.
Shiru Rafi'a Tamata Dan Asma'u tahanata magana.
Suhaima ta tuntsure da dariya Anty lubna kinga muje nifa kinganni bakowace bola bace abin kallo agareni.
Fatee ma tabud'e baki Zata maida murtani Asma'u ta harareta.
Daga k'arshema tashi tayi takad'a Kansu suka shige cikin falonta.
Daga Lubna har suhaima Bahaka sukasoba, sunso su Hasiya su kulasu ayi badad'i, dama Neman dalili sukeyi da dangin Umar d'in.
Suna Shiga Asma'u tarufesu da fad'a akan itafa batason tashin hankali, danhaka komi sukaimata karsuce zasu sake kulasu.
Shiru sukai mata kowa tana turo Baki, dansu hak'urin Asma'u haushi yake basu.
Sai magriba ya Umar yadawo gidan, suna zaune bayan sun idar da sallah yashigo.
Suduka rissinawa sukai suna gaisheshi, ya amsa babu yabo babu fallasa.
Ya ce, ''kutashi namaidaku gida.
To, suna fad'a kowa tana mik'ewa daneman mayafinta, kowa yashirya sukaima Asma'u sallama, hawaye tafara da rok'onsu Dan ALLAH su ringa zuwa mata akai-akai.
Hak'uri sukabata sukace zasuringa zuwa, dama makarantace take hanasu.
Ya Umar duk yana jinsu, ganin sunk'i tahowa yadoka musu tsawa, kai banason rainifa........
Bama su bari yak'arasaba suka fita dad'an gudunsu.
Asma'u tacusa kanta tsakanin cinyoyinta tana kuka saboda kewar 'yan uwan nata, koba komai yau taji dad'in ganinsu, sunyi hira taji farinciki aranta.
Bata kuma saka ya Umar a idontaba har wayewar gari, dama bazuwa kwana d'akinta yakeyiba, itakuma bata zuwa d'akinsa Dan duk hak'urinta tanada matuk'ar zuciya, dukda tasan basonta yakeyiba hasalima taimakonta yayi, amma ai baidace yarik'a mata hakaba kodan darajar zumincin dake tsakaninsu......
Share hawayenta tayi tamik'e zuwa kichin domin had'a breakfast.
Ruwan shayi kawai tadafa da Lipton da kayan k'amshi Dan bataga wani abuba a stor d'in gidan.
A tsakkiyar falon tazo ta ajiye kofuna da filas d'in shayin Dan ya Umar bayacin abinci akan dinning.
Tana cikin d'an gyara kayan yafito daga d'akinsa sanye cikin farar jallabiya.
Rissinawa tayi ta gaisheshi, saud'aya ya amsa yafice.
Mintuna kad'an yadawo d'aukeda bak'ar Leda ahannnusa, Asma'u na zaune a babban falon tana jiran dawowarsa danta tambayesa yanda za'ayi.
Ledar yamik'a mata, hannu biyu tasa takar6a tana masa sannu.
Kujera yasamu daga d'an nesa da ita yazauna, itakuma tabud'e ledar, biredine aciki sai madara irin 'Yar sacet d'innan guda uku, sai sukari da bota ta Leda.............
*_luv you oll_*
*_(((S))).......2017_*
[11/20/2017, 6:20 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻typing..........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
_Sadaukarwa_
*_miss Xoxo na_*
*_Zarah bukar_*
*_Ayusha muh'd_*
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._*
*_page→3_*
....... Ganin yanda kayan shayin yake yasata rarrabama kowa akofi ta ajiye, gamawarta babu dad'ewa saiga su Amrah sun fito da gudu.
Jikin babasu suka fad'a suna fad'in daddy?.
Ya ce, "na'am twin's d'ina kuntashi lfy?.
Lfy lau, daddy yaushe zamu koma gidanmu?, nan gidan babu dad'i sai zafi babu AC.
Murmushi kawai yamusu, yakama hannunsu suka sakko k'asa inda Asma'u tahad'ama kowa shayi.
Dai-dai nan Lubna tafito, taci kwalliyarta cikin pink d'in shadda sai zabga k'amshi takeyi.
Afrah data kur6i shayi tayi saurin zuboshi ak'asa tareda cillama Asma'u bread d'in data bata bayan tashafeshi da bota, nidai bazan sha tea d'innanba momy babu dad'ifa, ni dankali da kwai nakeso.
Galala Asma'u tayi tana kallonta, ganin haka itama Amrah tayi cilli da nata gefe.
Ya Umar duk yana jinsu amma yay kunnen uwar shegu dasu sai danna shayinsa da bread yakeyi hankali kwance.
Lubna ta harareshi, tokaji sufa bazasu iya shan wannan tea d'inba maikamada ruwan wankin kai, koni wlhy bangoyi bayan sushaba tundasu ba dabbobi bane.
d'ago idanunsa dasukayi d'anja yayi yana kallonta, baice komaiba yamaida kamsa yacigaba dayin break d'insa.
Asma'u ma tea d'inta taja tahausha batareda tasake kallon inda Lubna da yaranta sukeba.
Aiko ganin haka yasa Lubna fara zubar da ruwan masifa da tijara, sai zabgama Ya Umar gori takeyi.
Wai aii babantane dama silar arzik'in nasa, wlhy tayi nadamar aurensa Dan aurensa bai amfaneta da komaiba sai fad'awa tarkon wahala, dan haka dolene yasaketa ita bazata zauna dashiba taringa shan ruwan wankin kai amatsayin shayi.........
Haka taita zabga ruwan masifa babu Wanda ya kulata barema ya tanka mata, Asma'u tana gamawa ta tattara komai takoma d'akinta.
Shima mik'ewa yayi yashige nasa d'akin.
Itama ganin babu sarki sai ALLAH taja hannun Afrah da Amrah suka bar gidan.
Bayan wasu 'yan mintina Umar Fharuk yafito tsaf sanye cikin k'ananun kaya sai zabga k'amshi yakeyi.
Araina nace bawan ALLAHnnan ya iya d'aukar wanka wlhy.
d'akin Lubna yashiga, amma saiyaga wayam, baice komaiba yafito yashiga na Asma'u.
Tana falo kwance a doguwar kujera, chart takeyi abinta sai faman murmushi take zubawa.
Sallama yay mata sannan yazauna kujerar dake fuskantarta.
Itama tashi tayi zaune ta ce, "sannu.
Bai amsaba amma idonsa na kanta, Ita saima duk kunya takamata, ganin haka yasashi d'auke kai daga gareta, ya ce, " zanje shagunana Dan inaso afara gyaransa muga kuma abinda ALLAH zaiyi, idan kud'in sunkai angama gyaran to ko haya saina bada, idan kuma basu kaiba saimuga kuma abinda yadace ayi.
Jin yayi shiru tagane cewa yagama maganarsa, cikin sanyinta ta ce, "ALLAH ya tabbatar da alkairi aciki, Yakuma mayar da alkairi fiye da abinda aka rasa.
Yaji dad'in addu'arta danhaka ya amsa da ameen yana mik'ewa.
Saina dawo, yay maganar yana fita.
Itama tace ALLAH yatsare takoma ta kwanta.
%%%%%%%%%%%%
Umar nafita daga nan gidansu yanufa, gidan babu laifi mai k'yaune Dan tuni Umar yagyarashi tsaf, komai na more rayuwa saida yazubama iyayensa shi, horn yayi maigadi yabud'e masa gate, saida suka gaisa sannan ya ida shiga ciki, yasamu guri yay fakin.
Da sallama yashigo falon, Rafi'a ce kawai ta amsa cikeda farinciki, amma mama da Mufida da Harris sun amsane babu yabo babu fallasa.
Waje yasamu yazauna ak'asa yana gaida mama.
Dak'yar ta amsa masa, bai damuba yajuya yana amsa gaisuwar Rafi'a, harara ya gallama Harris da mufida Ku baku iya gaisuwa bane?, wai yaushe kuka rainanine?.......
Kafin suyi magana mama ta cafe, a'a yabazasu rainakaba? Tunda kagaza yimusu maganin abinda yadamesu.
Ajiyar zuciya yasauke, idanunsa harsun canja kala, ya ce, ''kiyi hak'uri mama abubuwane sai ahankali, kinsan dai halin Dana tsinci kaina aciki, inda Dane kobasu tambayaba zan basu, amma wlhy yanzu banida sh......
Kai dakatamin!!!, mama takatsesa cikeda tsawa, harni zaka bud'e baki kacema bakadashi, koma kunyar yin k'arya bakaji?, shekaranjiyafa kasiyar da gidanka miliyoyin kud'i amma har bakinka yafurta bakadashi, duk dai Wanda yagaza godema ALLAH to zai godema azabarsa.
Wani yawun 6acinrai ya had'iye, muryarsa cikeda girmamawa agareta ya ce, "kiyi hak'uri mama, wlhy kud'in gidannan acikinsu aka cire aka sayi gidan damuka koma, sauranne kuma zanje nayi gyaran shaguna nana, bammayi zaton kud'in zasu kaini ko inaba.
Hummm tonaji baban tsari tashi kabani guri, kama gyara duniya dasu ba shagunaba, itadai rayuwa duk Wanda yakedashi yagaza taimakon d'an uwansa aiyayi asara....
Da sauri Umar yad'ago yana kallon mahaifiyar tasu, idonsa yayi jajur, Rafi'a ma kuka takeyi, tana mamakin hali irinnan mahaifiyar tasu, kwatakwata mutumce dabata godiyar ALLAH, atunaninta ya Umar yafi k'arfin cin fuskarta kodan k'ok'arinsa nason k'yautata mata, duk cikinsu babu mai hak'urinsa dakuma kula da iyayensu, amma tunda iftila'in nan yasamesa 'yan gidan suka fara canja masa........
Maganar ya Umar ce takatse mata tunaninta, rissainawa yayi ya ce, " sai anjima, ALLAH ya huci zuciyarki, yakalli su Harris ya ce, "zantura muku insha ALLAH.
baki suka washe suduka harda mama, ko kaifa d'an nan to ALLAH yayi albarka kaji, ameen yafad'a ala6ansa.
Suma su mufida sai zabga godiya sukeyi, shidai ficewarsa yayi.
Koda yashiga mota saiya fice daga gidna, tafiya yakeyi amma zuciyarsa namasa zafi, gefen titi yasamu yay fakin, yakifa kansa jikin sitiyari yana duk addu'ar datazo bakinsa, wlhy yana mamakin hali irinna mahaifiyarsu, alokacin da yakedashi tafi kowa sonsa da tattalinsa, kullum addu'a take masa dafatan alkairi dagamawa da duniya lfy, amma abin mamaki tunda komai yak'are masa saita fara canjawa, yanzu babu Wanda tatsana samadashi, batada magana saita ya Abubakar da Anty Sa'a da Harris da mufida, suma Kansu 'yan uwansa sun canja masa gaba d'aya, anty sa'a ce kawai da Rafi'a suke sonsa, yasa handky yana share hawayen dake kwarara a kumatunsa.
Yakai tsawon lokaci awajen sannan yabirka motar yanufi kasuwa.
Alhmdllh aiki yayi nisa Dan anata kwashe tokar gobarar data k'ona shagunan, ganin komai natafiya dai-dai saiya shiga mota yanufi majalissar abokansu.
%%%%%%%%%%%%
Zazzaune suke sunata kwasar hira da dariya, motar Umar tatsaya.
Motsowwww ga k'aban nan cewar Hafiz.
Waye k'aba?, Salman yatambaya idonsa akan hafiz?.
Umar mana, kokai bakada ganewane, cewar Tasi'u.
Al'kasim yata6e baki kaini wlhy fa banason yana ra6armu karya goga mana talauci.
Ashe kagane d'an uwa, yanzufa d'angidan dayake mana tak'ama dashifa ya saidashi.
Kai Dan ALLAH kabeer dagaske kakeyi?.
Wlhy kuwa Hafiz da gsk, nima jafar take bani labari jiya, kunsan shi kunya bazata bari yafad'a manaba.
Tofa, yanzu to ina Yakoma?.
Wani kangon gida yasiya... Dariya suka shek'e da ita, Al'kasim ya ce, "su k'aba anji yaji........
Umar dake tsaye duk yana jinsu yagirgiza kansa tareda musu sallama............
Afurgice suke kallonsa, duksun tsargu kardai yaji firar tasu?, dansu basusan yama iso inda sukeba.
Kowa yakama 'yan kame-kame.
Hannu yamik'a musu suka gaggaisa fuskarsa d'aukeda murmushi, suna gama gaisawa ko zama baiyiba ya ce, " bara nawuce, Dama nabiyo gaishekune.......
*_(((S)))....2017_*
*_luv you all my fan's_*😻
[11/20/2017, 6:20 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻typing..........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
_Sadaukarwa_
*_miss Xoxo na_*
*_Zarah bukar_*
*_Ayusha muh'd_*
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._*
*_page→4_*
..........ah mungode angon Asma'u da uwargida Lubna.
Baice komaiba sai murmushin takaici dayayi yajuya yashiga motarsa, suduka binsa sukayi da kallo, kai jama'a Kodai yaji mimuke fad'a?.
Kai baiwani jimuba, idanma yaji saime kune kukejin tsoronsa.
Mtsowwww miye abin tsoro a can?, mutumin da duk talauci ya gwaguyeshi, ni gwarama dabai zaunaba......
Umar da takaici yacika yana shiga motarsa yabar wajen zuciyarsa namasa k'una, waishi kowa ke gudu tamkar wani mai mugun hali, babu komai yagodema ALLAH, komai na duniya fararrrene kuma k'ararrene, zaiyi hak'uri insha ALLAHU, hak'uri irinna bayin ALLAH, hakadai yayta tunani harya isa gidansa, tun ak'ofar gida yaga motar mahaifin Lubna, cikeda mamaki yake kallon motar, tokodai Lubnace tazo da ita?, yatambayi zuciyarsa.
Ajiyar zuciya yasauke tareda fitowa daga motarsa yashiga cikin gida, ganin takalma reras ak'ofar falon yatabbatar masa da babu lafiya.
K'uru yayi yashiga da sallama, abin mamaki mahaifin Lubna ne da Mahaifiyarta, sai yayunta biyu da suhaima k'anwarta, Asma'u na tsigunne agefe da'alama kuka takeyima.
Dukda babu Wanda ya amsa gaisuwarsa haka yak'arasa cikin falon, yarisina yana gaida iyayen nata, fuska babu yabo babu fallasa suka amsa, yad'ora dafad'in Abba lfy kuwa?.
Lfy lau sai alkairi, Ameer yayan Lubna yafad'a amasife.
Yawu Umar ya had'iye na 6acin rai, amma baice komaiba.
gyaran murya mahaifin Lubna yayi, ya ce, "Umar nasan zakayi mamakin ganina agidanka?, toba abin mamaki baneba, baby ce takai k'ara akan bazata iya zama awannan kangon gidan nakaba, shiyyasa nazo ni dakaina na shaida maka nima banyarda d'iyata ta zauna anan ba, alfarma d'aya zan maka shine nabaka d'aya daga cikin gidajena kakoma kaida baby amma banda waccan sai farar k'afar, yanuna Asma'u.
Sai yanzu Umar yad'ago yana kallonsa, yayi wani d'an murmushi sannan yamaida kansa k'asa.
Duk azatonsu yaji dad'in k'yautarne shiyyasa ya murmusa, amma sai furucinsa ya tabbatar musu da sa6anin haka.
Ya ce, " ngd sosai Abba da wannan k'yauta, saidai inamai baka hak'uri dabazan kar6aba, wannan shine gidan daya kasance dai-adai k'arfina, idan Lubna tana sona tayi hak'uri muzauna anan, danni gsky babu inda zan koma.....
To aiko wlhy Umar saidai kasakeni........
Maganar Lubna takatseshi.
Shiru yayi baice komaiba, Safwan ya ce, "tokaji fa, saika za6a sakinta kokuwa bin abinda takeso?.
Kuyi hak'uri ya Safwan bazan iya sakintaba, kuma bazan koma ko inaba.
To aikuwa zakaga sammaci, Dan yarinyata bazata zauna awannan kangonba tanacin gabza.
Mom Dan ALLAH kuyi hak'uri, kufa iyayenmune baikamata irin wad'an nan zantukan suna fitowa bakinkuba.
Mtsoww to ubana gayamin yanda zanyi?.
Shiru Umar yayi Dan yasan wacece Mahaifiyar Lubna, masifaffiyace dama tafad'a aji.
Mik'ewa sukayi suduka har Lubna d'in, kawai saiyajin anci kwalarsa.
Cikeda mamaki yake kallon Lubna daketa girgiza jiki, ta ce, " wlhy saika sakeni.
Tsawa yadaka mata ke banason iskanci sakemin Riga.
Bazan sakiba wlhy saika bani takardata, kuma saki uku nakeso.
Zuciyar 'yan mazan tazo kusa, aiko ya sharara mata mari..... Baisauke hannunsaba Mahaifinta shima yamareshi.
Umar kana haukane?, agabana zama mari yarinyata, wlhy saikayi nadamar hakan, baby sakesa idan bai bayar da arzik'iba, aizaibada datsiya akotu.
Sakinsa Lubna tayi suka fice suduka.
Binsu kawai da kallo Umar yayi.
Asma'u kuwa dama tun d'azu kuka takeyi, suna fita tashige d'akinta da gudu tana kuka.
Itama binta kawai yayi dakallo.
Zubewa yayi ak'asa yana sauke numfashi da hawaye, shikenan Dan *_KARAYAR ARZEEK'I_* tasamesa sai kowa yatsanesa?, shin shiya d'orama kansa?, miyasa mutane basa ganewa?, ya ALLAH kabani ikon cinye jarabawarka, ALLAH ka k'aramin hak'uri da Wuyan d'auka, yadad'e awajen zaune abin tausayi, dak'yar ya rarrafa yabar falon Yakoma d'akinsa.
%%%%%%%%%%%%
Bayan kwana biyu da faruwar hakan, ya Umar dukya k'ara ramewa yafita hayyacinsa, abincima sai Asma'u tasaka masa kuka yakeci, baya fita ko ina, yama tsaida aikin shagunan nasa, kud'in da k'annansa suka buk'ata yabasu.
Yauma haka yatashi yanajin jikinsa duk babu dad'i, yasan tabbas da likita zai gwadasa saiyaga jininsa yayi hauhawar farashi zuwa dubu k'arewa 180+, yanzuma zaune yake afalo Asma'u ta ajiye masa abinci amma yakasa ci.
Sallamar dasukajice tasakasu kallon k'ofar suduka, har Asma'u tamik'e ya ce, "tazauna yaje.
Hannu yabama bak'on nasa suka gaisa, Umar ya ce, " kayi hak'uri ban wayekaba.
Eh bazaka sannuba, sunana Ahmad ilyasu daga kotu aka aikoni nabaka wannan, yamik'a masa zungureriyar farar takarda.
Jiki asanyaye Umar yakar6a, sallama yamasa yatafi, shikuma yajuya cikin gidan.
Asma'u tabishi da kallo, tasan ko tambayarsa tayi dawuya ya amsa mata Dan haka taja bakinta tayi shiru.
Zama yayi ya warware takardar ya karanta, girgiza Kansa yayi yana cije le6ensa, waishi Lubna takai kotu akan ya saketa?, tamanta da alk'awarin dasukaima juna?, tamanta da soyayyar dasuka Gina atsakaninsu?, tamanta hidima da k'aunar daya Nuna mata?, tamanta?, tamanta?, dayawa.
Ninke takardar yayi yasaka aljihun jallabiyarsa.
Yasakko yazauna ak'asa yaci abincin sannan yatashi yakoma d'akinsa yakwanta.
Asma'u kam shiru tayi tana mamakin komi takardar ta k'unsa oho.
%%%%%%%%%%%%
Bayan kwana hud'u ya amsa kiran kotu.
Bayan kammala wata shari'a aka fara tasu.
Tashin farko lauyan Lubna yanemi takardar saki dabin kadin hak'in Marin da Umar yayma Lubna ranar.
Umar ya ce, "shifa bazai saketaba, mari kuma it's tajama kanta.
Alk'ali yaci kud'i, Dan haka yace tilas Umar yayi saki Dan Lubna tace yana barinta da yunwa, babu sittirar kirki, sharridai sosai suka shirya masa wad'anda dole suka tirsasashi yamata saki d'aya.
Tayi tsalle tadire ta ce, ''uku takeso, Alk'ali ya ce, " yacika biyun.
Ran Umar yakai k'ololuwar 6aci musamman da Lubna taci kwalarsa acikin kotu gaban d'unbin mutane, cikin 6acin rai yacikashe uku amma yace tabasa 'ya'yansa, nanma ta ce, "bai isaba tabada 'ya'yanta mayya tarainesu.
Indai tak'aice muku tilas Umar yahak'ura, alk'ali yasashi biyan Tatar Marin dayayma Lubna, dakuma kud'i milyoyi akan rainon yaransa.
Kukane kawai Umar baiba amma tuni duniyar tafara juya masa, a take anan yamata transpar d'in kaf kud'insa na Account zuwa Account d'inta, bai barma kansa ko nera d'yaba.
Suna fitowa daga kotu yashiga mota yay gida ransa a6ace.
Sukuwa su Lubna da 'yan uwanta sai farin cikin samun nasara sukeyi.
Umar natsaida motarsa yafito, dak'yar ya iya shiga cikin gidan yana dafeda k'irjinsa, dak'yar ya iya sallama yashiga falon, aiko yana shiga ya yanke jiki yafad'i...............
😕wayyo ya Umar Fharuk😥.
*_(((S)))....2017_*
*_luv you all my fan's_*
[11/21/2017, 4:33 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻typing..........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
_Sadaukarwa_
*_miss Xoxo na_*
*_Zarah bukar_*
*_Ayusha muh'd_*
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO....😜._*
*_page→5_*
........da sauri Asma'u da Rafi'a sukayo Kansa, jikinsu sai rawa yakeyi, summa rasa taimakon dazasu bashi, Rafi'a ce tai k'ok'arin fita waje da gudu, cikin sa'a tayi gamo da mak'ocin ya Umar d'in zai fita.
Kuka tasaka masa tana nuna masa cikin gidan, amma takasa magana.
Ya ce, "yammata lfy kuwa?, fad'amin mike faruwa ne?.
Dan ALLAH ka tai makemu ya Fharuk karya mutu....katai makem.....
Ai baima bari tak'arasaba ya afka cikin gidan.
ALLAH yasa ya iya mota, Dan danan suka taimaka masa suka d'akko ya Umar dayayi jagaf tamkar gawa.
Rafi'a tafad'a musu asibitin datasan ya Umar d'in yana zuwa shida iyalansa harma dasu yakansa akaisu idan basuda lfy.
Suna zuwa asibitin Rafi'a ta ce, " sukaishi office d'in Dr jafar.
Babu marasa lfy ak'ofar office d'in Dan haka suka sami damar Shiga kai tsaye, Dr Jafar nazaune yana rubuce-rubuce jin anshigo ko sallama babu yasakashi d'agowa yaga wanene.
Kafin yayi magana,... Rafi'a ta ce, "Ya Umar muka kawo Doctor pls ka taimakemu karya mut......
Kafin takai k'arshe anshigo da ya Umar, doctor yatashi ya taimaka musu aka d'orashi ad'an gadon da'ake d'ora marasa lfy.
'Dan duddubashi yayi sannan yadawo ya zauna yana kallonsu Rafi'a.
Ya ce, " miya sameshi?.
Fad'uwa yayi.
Numfashi doctor yasauke tareda fad'in ALLAH ya sawak'e.
Ameen, Asma'u da Rafi'a suka fad'a.
Doctor yacigaba da fad'in, gsky bazan 6oye mukuba Umar yana cikin matsala, yanzu haka sai mun kwantar dashi sannan musan taimakon dazamu basa, zakuje kubiya kud'in gado dasauran Mayan aiki.
Da sauri Asma'u ta ce, "doctor nawa ake buk'ata?.
Uhmm kamar 100k insha ALLAH zasu isheku komai harma da canji.
Idanu suka zaro waje harda had'a baki wajen fad'in 100k fa doctor?.
Eh, haka nafad'a, aikunsan asibitin kud'ine wannan.
Rafi'a ta ce, " to doctor tunda ya Umar abokinka ne kumasa duk abinda yadace idan yadawo hayyacinsa saiya Baku.
Kai yagirgiza mata, bazai yuwuba aii, shima yasan dokar asibitinmu aii, kuma ma idan nace zanyi k'uri namasa komai idan yatashi yanada abin biyanane?, kuma kunsan Umar bashida ko sisi yanzu saidai yazamemin kaya, so kuke kawai kunemo kud'i kunga yana cikin danja.
Wash hawayene masu zafi sukrbin kumatunsu Asma'u, sudai sunsan doctor Jafar aboki ya Umar ne nakusa, Wanda sunada tabbacin yana cikin jerin wad'anda sukaci gajiyarsa da dukiyarsa fiye da kowa, amma yau danyaga bayidashi shine yake furta wad'an nan kalamin akansa.
Asma'u tadurkushr masa yana kuka da rok'on doctor jafar, amma yay kunnen uwar shegu da ita, saga k'arshema masifa yahauyimusu, kai nifa kuna cikamin kunne da 6atamin lokaci, idan kunada kud'in daza'a lura da Mara lafiyarku kubada, idan bakudashi kud'aukeshi kukaisa asibitin gwamnati.
Ran Asma'u ya6aci sosai, dama ita akwai zuciyar tsiya, mik'ewa tayi fusace taja hannun Rafi'a suka fita.
Saida sukaje harabar asibitin Rafi'a ta tirje tana ad'in Anty Asma'u wai ina zamujene?.
Hawaye Asma'u tashare, ta ce, "Rafi'a kirakani inda ake sqida wayoyi, zansaida wayata, nasan insha ALLAH ko 25k zatayi.
Ajiyar zuciya Rafi'a tayi ta ce, "to kije shagon su labaran na anguwarku, nikuma sainaje nafad'ama su mama king a yakamata su sank ko?.
Eh hakanma yayi, saimun had'u to.
Saga nan kowa yanufi inda zashi, sukabar makwafcin nan nasu tareda ya Umar.
Shagonsu labaran Asma'u take, babban shagone da'ake saida wayoyi daduk abinda yashafi hakan, had gyara sunayi, matasane sunkai Bihar masu tsaron shagon, kowa da abinda take kula dashi.
Asma'u tashiga da sallama, wani matashin saurayi ya ce, ''yammata kina buk'atar wani abune?.
Fuskarta takuma tamkewa damage Asma'u babu damace wajen rashin walwala.
Ta ce, " inaso na said a wayane.
OK to naga wayar.
Wayarta taciro tamik'a masa.
Yakar6i wayar yana jujjuyawa tareda d'agowa yana kallonta.
Ganin kallon mamakin dayake binta dashi yasata fad'in malam lfy kuwa?.
Eh to Hajiya dadai sauk'i, amma tsakaninki da ALLAH wayarnan takice?.
Cikeda mamaki take kallonsa, tagyara tsayuwarta sannan ak'ufule ta ce, "namaka kama da a6rauniyane?.
A'a wlhy Hajiya ko d'aya, kinsandai rayuwarce sai'a hankali kawai, amma idan ranking ya6aci kiyi hak'uri.
Idanma ban hak'uraba dukanka zanyi, kashiga cikin wayar sosai insha ALLAHU zakagane idanma tawace ko akasin haka.
Shawararta yabi yashiga bincike awayar, tabbas tatace Dan hotunantama dake kai sun Isa shaida, yad'ago yana kallonta to Hajiya nawa zaki sayar?.
Kasiya yanda yadace, nidai ina rok'onka kamin adalci kawai, nima dolece tasakani saida wayar badan nasoba.
Jinjina kai yayi, ya ce, "nasiya 150k.
Idanunta tazaro waje, kai malam kallifa da k'yau kaga wayar dake hannunka.
Murmushi yayi Hajiya nagani sosai, wlhy nama saya da daraja aii.......
Kafin tayi magana wani dake kusadasu yana sayen waya ya ce, " gsky kacuceta Dan wayarnan bata sha wahalaba.
Asma'u da mamaki yakashe ta ce, nifa duk bamma fahimci inda kukadosaba, wayar dabata wuce 25k ba kuke kira mata 150k?, ahankama har ana fad'in an cuceni?.
Wanda yasaka musu bakin ya ce, "Hajiya amma dai bake kika sayi wayarnanba?.
Eh bani nasayaba, yayanane yasiyamin.
Haba shiyyasa bakisan kud'intaba, wannan wayar dakike gani, ana saidata 400k wlhy.
Idanu sosai Asma'u ta kwalalo waje, sai maimaita yawan kud'in take azuciyarta, dubu d'ari hud'ufa?, tabd'ijan, lallai ya Umar yayi k'ok'ari......
Tunaninta yakatse yayinda taji maganar labaran abayanta.
A'a Asma'u lfy kuwa?.
Lfy lau wlhy Labaran, nazo nasaida wayane.
Tofa ina wayar?.
Kaganta nan, tayi maganar tana nunama masa wayarta dake hannun saurayin.
Hannu yamik'ama saurayin yabashi wayar, saida ya rissina sannan yabashi alamar girmamawa.
Labaran yakar6i wayar ya jujjuya sannan ya ce, " nawa kasiya?.
In ina saurayin yafarayi alamar rashin gsky, labaran ya girgiza kai kawai danyasan halin yaran shagon dason zuciya.
Baice komaiba yak'irgo kud'i masu yawa yabata, Asma'u ga 330k kiyi hak'uri datayin farko dayayi mini.
Babu komai tafad'a tana murmushi, ngd sosai labaran, amma Dan ALLAH kozan samu memory nakwashe abin kan wayar?.
Babu damuwa, idan nakwashe zanbama Rafi'a takawo miki.
To ngd sosai labaran.
A babu damuwa Asma'u.
Agurguje tafice tasamu adaidaita cikeda kwarin guywa suka nufi asibitin..........
*_(((S))).......2017_*
*_luv you all my fan's_*
[11/21/2017, 4:33 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR AZEEK'I!!_*💎
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO......😜_*
*_page→6_*
.......Anshigar da ya Umar babu dad'ewa su mama suka iso, suduka sukai kan Asma'u suna tambayar jikin ya Umar d'in?.
Jikin Anty sa'a tafad'a tana kuka, wannan yasa suka k'ara rud'ewa.
Makwafcinsune yamatso, cikin hikima yamusu bayani.
Godiya sukai masa sosai, daganan aka koma zaman jigum-jigum.
*_3h...ago_*
Dr yafito shida Nurse's dasuka taimaka masa.
Shimadai rufuwa akansa sukayi suna tambayarsa jikin ya Umar.
Yabuk'aci ganin wasunsu a office d'insa, amma babu Wanda zaya iya hak'uri abarsa abaya, Dan haka suka tafi suduka.
Dr bai hanasuba saima gurin zama daya nuna musu.
Kowa yasamu waje yazauna yanajiran bayani, bayan Dr yagama 'yan rubuce- rucensa yad'ago yana kallonsu, ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce, "Alhmdllh, gsky Ku k'ara godema ALLAH akan taimakon daya bama Alhaji Umar danba kowane yake irin fad'uwarnan yatashi dai-daiba, amma shi Alhmdllh babu wata Marsala, saidai yana cikin matsannanciyar damuwa wadda saida taimakonku aikinmu zaikai ga nasara, yanzudai yasamu barci kuma bazai farkaba harsai nanda 24h Dan munaso zuciyarsa tasami Hutu sosai.
Yanzu ga wannan zakuje kubiya kud'ad'en sannan kuma asayi wad'annan magungunan kafin ya farka.
Atare sukace to Dr mungode sosaifa.
Karku damu aikinane.
Godiya suka masa sannan suka fita.
Suna fita Mama ta kalli ya Abubakar, ta ce, " Abubakar saika amshi takardun kaje kabiya kakuma sayo magungunan ko?.
Fuska ya murtike tamkar zai fasa kuka ya ce, "to kuzama shaida idan yatashi zai bani kud'ina Dan na kasuwane.
Asma'u da Anty sa'a, mufida, Rafi'a duk kallon mamaki suke masa, shikansa ya fahimci haka amma saiya basar yamik'ama Asma'u hannu alamar tabashi takardun.
Kanta ta girgiza ta ce, ''ya Abubakar kabarsa akwaima kud'i awajena kuma insha ALLAH zasu ishemu komai.
Babu kunya ya washe bani yana fad'i a to kinyi k'yankai Asma'u.
Babu Wanda yatanka masa acikinsu, Asma'u da Anty sa'a suka tafi wajen da Dr yafad'a musu.
Sunbiya kud'in komai sannan sun sayo duk magungunan da ake buk'ata, dawowarsu babu dad'ewa ya Abubakar yawuce kasuwa akabarsu mama anan.
Sumadai zuwa dare duk suka tafi akabar Asma'u kawai awajensa, da mamace zata tsaya Asma'u tace taje tahuta ita zata zauna dashi, dak'yar tayarda saida su Anty sa'a suka saka bakima.
Bayan tafiyarsu Asma'u tayo alwala tashimfid'a sallaya, sallar isha'i tagabatar tayi addu'a sosai darok'on ubangijin al'arshi akan yakawoma mijinta d'auki da sassaucin halin daya tsinci kansa aciki, tashafa addu'ar tanamai zubar da hawaye, bayan kammalawarta saman kujerar dake d'akin tadawo ta zauna ta talsurama k'yak'yk'yawar fuskar ya Umar idanu, duniyar tunani tafad'a wa rayuwarsu tabaya maicikeda abubuwa na ban mamaki, ban haushi, al'ajabi, tausayi, farinciki, da jarabawoyi kala-kala...........
*_SHEKARUN BAYA DASUKA SHU'DE_*🤔
Malam Tsalha baduku tsohon kirki mai mata d'aya da 'ya'ya uku aduniya.
Hajara tsohuwa mairan k'arfe uwargida kuma amarya agidan malam Tsalha baduku, ta haifamasa yara uku 2maza 1mace.
Usman, Kabiru, Binta.
Sun rasu suduka tun shekarun baya dasuka shud'e.
Usman yanada mata d'aya da yara Uku shima, Mero itace matarsa suna kiranta da mama, malam Usman mutumne mai hak'uri da kawaici, yanada son 'yan uwansa sosai dakuma iyayensa, bawani mai k'arfi banebashi amma mutumne mai Neman nakansa cikin tsaftatacciyar hanya, akwaishi da wadatar zuci dakuma Nuna godiyar ALLAH kan abinda yabashi walau kad'an kokuma mai yawa.
Saidai Bahaka bane ga matarsa Dan itakam akwai hange-hange da son kud'i damai kud'i, Indai Kanada naira tokuwa kai abokin tafiyane, idankuwa babu to kana gefene awajenta.
Yaransu uku Sa'adatu, Abubakar, Umar Fharuk.
Sai kuma Kabiru matarsa d'aya wasila amma basu ta6a haihuwaba.
Halin Kabiru shima yasha banban Dana malam Usman dankuwa shimadai akwai son 'yan canji, toshikam babu laifi yanada d'an hali danyafi malam Usman arzik'i.
Sai Binta itamadai tayi aure harda yaranta, halintakam irinna malam Usman ne dantanada hak'uri sosai da kuma zafi idan ka k'ureta.
Yaranta hud'u duk mata, Saratu, Asma'u, Fateema, Hasiya.
ALLAH yayima malam Usman rasuwa tunsu Umar suna k'anana danshi bama sosai yasanshiba, bashida wayo sanda yarasu.
Bayan Rasuwar malam Usman rik'on yaran yacigaba gudana hannun mahaifiyarsu mama, ta taka rawar gani sosai wajen kula dasu har bayan shekara uku da rasuwar malam Usman sai kawu Kabiru yazo da buk'atar auren mama abisa shawarar da inna binta k'anwarsu tabashi.
Dagudu kuwa mama ta yarda Dan tasan Kawu Kabiru yanada d'an abin hannunsa gashi kuma baita6a haihuwaba, ba'a wani 6ata lokaciba aka d'aura auren, anan gidan tacigaba da zama, cikin ikon ALLAH kuwa saiga ciki, wayyo zokaga murna wajen kawu kabiru da family gaba d'aya, tattali sosai yakema mama, ciki yanakai wata Tara da wasu kwanaki ta sunkuto d'anta Namiji Wanda yaci suna Usman suna cemasa Harris, shekarar Harris biyu mama takuma haihuwar mace Mufida, daganan sai Auta Rafi'a.
Rafi'a nada shekara biyar aduniya Anty sa'a tayi aure bayan ta kammala karatunta na Secondary, taso cigaba da karatu amma hakan bai samuba, shima Ya Abubakar a daddafe da buga-buga yakammala Diploma d'insa, daganan yay aure yanad'an sana'ar saida kayan provision awani shago dake k'ofar gidansu.
Bata sake zaniba akan Umar Fharuk dan shimadai duk ajirgi d'aya suka sauka, bayan kammala secondary yafara karatun nasa a B,U,K saboda k'yawun result d'insa kai tsaye degree suka basa, dahad'a gabas had'a yamma aka kammala, ALLAH yabashi nasarar fita da result mai k'yau, yayi farinciki sosai hakama 'yan uwansa musamman ma mama Dan aganinta itamafa karan 'ya'yanta yakai tsaiko yanzu.
Umar yadawo zaman gida babu aikinyi, tun zaman yana masa dad'i harya fara gundurarsa, tuna maganarnan ta hausawa dasukance babu maraya sai rago tamasa allurar tashi domin Neman abinyi, duk abinda yasan zai rufa asirinsa yinsa yakeyi babu sanya ko girmankai irinna 'yan bokon nan, ana haka wani abokinsa yay masa hanyar Babur na adaidaita sahu, sosai Umar yaji dad'in wannan taimako, cikin farin ciki yazoma mama da kawu Hamidan wannan labari.
Hummm, amma saisuka gwaleshi da nuna masa wannan k'ask'ancine, yaza'ayi kamarsa dayakeda kwalin degree yak'are da tuk'a babu, gsky yacanja shawara amma ba wannanba.
Wannan lamari ya6ata ran Umar sosai, Dan haka ransa a6ace yanifi gidan inna binta.
Tarba sosai yasamu agurinta Dan d'an gatantane.
Inna tasaka Fatee takawo masa abinci da ruwa, saida yaci yak'oshi sannan yakwashe komai yafad'a mata.
Itama ranta ya6aci sosai Dan haka taita fad'a kamarsu mama na gabanta, takuma kwantar masa da hankali akan zata samesu, shikuma yaje yakar6i adaidaita sahud'in yafara aikinsa.
Yaji dad'i sosai Dan haka yayta mata godiya, daganan hira maidad'i suka cigaba dayi Dan akwai shak'uwa tsakaninsu sosai.
Sallamar Asma'u da Hasiya ne yasakasu katse hirar suka amsa.
Asma'u tazube littatafanta na islamiyya tana fad'in wash inna wlhy nagaji yau.
Binna ta ce, "to sannu ragguwa, amma bakiga yayankiba.
Idanunta tad'ago ta kallesa, saikuma ta kauda kai tace ina yini.
Bai amsataba saima hararta dayakeyi, takuma fad'in inayini, Dan ita azatonta baijibane, d'an yatsine fuskarsa yayi sannan ya amsa, yamaida kallonsu ga Hasiya da itama take gaidashi, ya ce, " Autar inna ya islamiyyar?, kinadai yin k'ok'ari ko?.
Hasiya ta jinjina kai ta ce, "eh yaya munayi, yanzu hakama ina ajin sauka nida yaya fatee, yaya Asma'u kuwa sune manya Dan sune 'yan ajin hadda.
d'an satar kallon Asma'u yayi, suna had'a ido ya kauda kai.
Asma'u tad'an ta6e baki tareda mik'ewa tashige d'akinsu tana k'unk'unai Dan haushin ya Umar takeji saboda abinda yay mata shekaran jiya, tana hira da saurayinta ya koreshi, abin bak'aramin haushi yabataba.
Bata k'ara fitowa falonba saida taji yatafi sannan tafito.
Inna tabita da kallo, kekuwa Asma'u mikikeyi ad'aki tun d'azun?.
Kanta tad'an sosai ta ce, "inna ina wayane da Anty saratu fa.
Inna batace komaiba ta mik'e, saida takusa zuwa k'ofa sannan tajuyo tana kallon Asma'u, ta ce, "idanma laifi kikaima Umar to wlhy kiyi gaggawar bashi hak'uri Dan kinsan Sam banason raina nagaba.
Asma'u ta kwa6e fuska kamar zatayi kuka, nifa inma ban masa komaiba.
Ohodai nidai nafad'a miki, inna tafad'a tana ficewa daga falon........
*_(((S)))......2017_*
*_Luv you all_*
[11/22/2017, 1:23 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_*
*_page→7-8_*
......Umar kam tun aranar yaje yakar6i Babur d'in Adaidaita sahu, kuma aranar yafara aiki, ganin alkairin daya samu yasakashi farinciki sosai tareda samun kwarin guywa.
Bai sanarma kowa yafara aikiba agidansu saida inna tazo washe gari sukai magana dasu mama, badan mama tasoba ta amince, amma babu yanda zatayi Dan tanason inna binta sosai kodan k'aunar datake nunama 'yayanta, ta taka rawar gani sosai akan karatun Umar Dan d'an gidantane.
Tundaga ranar Umar yacigaba da hayar adaidaita sahunsa, dukda mama bata nuna farincikinta aikai hakan bai hanashi yimusu hidaimaba da d'an abinda yasamu, babu yabo babu fallasa suke kar6a, shikam Umar ko kad'an hakan baya damunsa harkokinsa kawai yakeyi.
Ana haka sai wani al'amari yafaru a wani daren Juma'a ranar alhamis kenan da daddare.
Bayan Umar yagama aikinsa misalin k'arfe 11 saiyayi harama tafiya gida.
Yana cikin tafiya saiyaga ana d'aga masa hannu tundaga nesa, lamarin yabashi tsoro Dan azatonsa 'yan fashine ko 6arayin Babur, haka yak'arasa wajen guywarsa asage yanata ambatar duk addu'ar datazo bakinsa.
Yataka birki agaban dattijo da wani matashi daketa k'ok'arin tsaidashi, matashin saurayinne yayma Umar magana.
Abokina Dan ALLAH kozaka kai alhaji gyad'i-gyad'i?.
Shiru Umar yayi na 'yan sakwanni zuwacan yasauke ajiyar zuciya tareda kallon agogon hannunsa, ya ce, "abokina darefa yayi duba kagani, gashi kasan akwai tazara daganan zuwa gyad'i-gyad'i.
Nasani abokina amma Dan ALLAH ka taimaka, wlhy daga airport na d'akko mai gidana saikuma mota tamana tsiya, tun d'azun muke tsumayen abin hawa amma bamu samuba.
Kafin Umar ya ce, " wani Abu dattijon Alhaji yalek'o yanafad'in yaro kadauro Dan ALLAH, wlhy nagaji sosai burina kawai nahuta.
Ajiyar zuciya Umar yasauke tareda gyad'a kai ya ce, "shikenan shigo mutafi baba.
Alhaji yaji dad'i sosai, Dan haka yashiga sakama Umar albarka, kayansa direban yakwaso zuwa adai-daitar sukaiyi sallama Umar yaja suka tafi.
Tunda suka tafi babu maima wani magana, Umar yana tuk'i yana tunanin rayuwa da yanda take tafiya, Alhaji kam yayi shiru abaya saboda gajiyar zaman jirgi dake nuk'urk'usarsa, saida suka isa gyad'i-gyad'i sannan Alhaji yanuma Umar layin dazasu shiga.
Ak'ofar wani katafaren gida suka tsaya, Umar yajinjina kai azuciyarsa yana fad'in wani kaya sai amale.....
Alhaji yakatse masa tunani da mik'a masa kud'i masu yawa Wanda shima baisan adadinsuba.
Umar ya yakalli kud'in ya kalli alhaji sannan ya ce, " baba 350 ne kud'inka aii.
Murmushi alhaji yayi ya ce, "d'ana karka damu kaidai kar6i.
A'a baba ngd kabani iya hak'k'ina kawai, girgiza kai Alhaji yayi dakuma ajiyema Umar kud'in akan cinyarsa, babu yanda Umar ya iya dole yakar6a yay godiya sannan yatafi gida da addu'ar ALLAH yakaisa lfy.
Inda yake kai adai-daitarsa yanufa, yasamu guri yay fakin, abinda yake lilli6eta yajawo zai rufe sai idanunsa suka sauka akan wani d'an k'aramin akwati, shiru yayi yana nazarin kowaye ya manta?.
Wata zuciya ta ce, " masa Alhajin Daka sauke yanzu.
Afili ya ce, "hakane kuma, ya kalli agogonsa saiyaga har 12:36, gsky yanzu yana tsoron sake hawa titin nan, kuma idanma ya iya komawa yanada tabbacin za'a barsa yashiga wannan gidan a irin wannan lokaci?, d'an tsaki yaja tareda d'aukar akwatin yana fad'in insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu da sassafe saina kai masa.
Da wannan shawarar yanufi gida, dama kullum shine k'arshen dawowa gida shiyyasa yake rik'eda key d'in gidan guda d'aya, bud'ewa yayi yashiga sannan yamaida yarufe tareda addu'ar rufe gida, d'akinsa yashiga yay wanka da shirin barci sannan yay nafilfilinsa kamar yanda yasaba ya kwanta.
_washe gari_
Tunda yatashi yay sallar asuba bai koma barciba dama shi haka yake bai iya barcin safeba kullum yana dawowa daga masallaci zai d'auki alkur'ani yahau karatu, saida gari yay sha sannan yay addu'oi yatashi, wanka yashiga.
Shigarsa babu dad'ewa mama ta shigo d'akin, idontane yasauka akan bak'uwar jakar mai k'yau, jikinta har rawa yakeyi tabud'e jakar, idanu tazaro amatuk'ar razane Dan ganin mak'udan kud'in dake cikeda d'an akwatin duk daloline sababbi k'ar.
Razanuwa da ganin kud'in yasa takasa aikata komai har Umar yafito daga wanka, shimadai bak'aramar razana yayi dagani kud'inba, Dan yauce rana ta farko daya fara ganin zunzurutun kud'i tsirara agabansa masu yawan haka.
Jikin mama amace ta ce, " Umaru INA kasamo wad'annan kud'in haka?.
Zama yayi abakin katifarsa, yajanyo jakar yana rufewa mama ba nawabeneba, wanine nad'auka jiya da daddare shine yamanta da jakar.
Mama ta washe baki tana fad'in Umaru aii yamzun sunzama naka tunda tsuntuwa kayi, lallai kagodema ALLAH da wannan arzik'i daya yimaka, dama masu iya magana necewa dare d'aya ALLAH kanyi bature.
Kallonta kawai yakeyi damamakin ganin rikicewar datayi Dan kawai taga kud'i, shi rabonma dayaga fara'ar mama agareshi harya manta wlhy, amma duba daga ganin kud'i dukta rikice, ya kauda Kansa saboda 6acin rai, amma kasancewarsa jarumin 6oye sirrin zuciya sai fuskarsa bata nunaba ko kad'an, cikeda ladabi ya ce, "mama zan maida MASA kud'insa ne, Dan zan gane gidan Dana saukesa insha ALLAHU.
6ata rai mama tayi, ta gallama Umar harara to Uban masana basaikaita maidawarba, idan banda ga6anci ALLAH yabaka irin wannan dukiyar har kayi tunanin maidama mai ita?, shi Kasan ta hanyar daya samu?, k'ilama 6arawon gwamnatine.
Kiyi hak'uri mama ALLAH ya huci zuciyarki, abinda zaki duba wannan kud'i ba hakkina bane, koma tayaya maisu yasamesu wannan shiyya d'aukarma Kansa kaya, inada damar maida masa kud'insa, to aii gara na maida domin ubangijinafa da barci ko gyangyad'i baya d'aukarsa yana kallona, kuma baya yafe hak'k'in wani akan wani face kanemi gafarar Wanda ka zalunta, tonikuwa mizaisani butulcema ni'imar da mahalliccina yay mini? na tsarkakakkiyar zuciya.
Mik'ewa mama tayi a fusace tafice tanata masifa.
Umar ya girgiza Kansa tareda sauke zazzafan huci, afili ya ce, " mama ALLAH ya shiryeki.
Niko bilyn Abdul sai na ce, "ameen ya Umar🤷🏽♀.
Koda Umar yagama shirinsa yanufi d'akin mama Dan mata sallama kamar yanda ya saba.
Da sallama yashiga falon, babu kowa sai Mufida da Rafi'a dake break fast kowanne sanye cikin kayan makaranta na gwamnati.
Gaisheshi sukayi, ya amsa yana tambayar ina mama?.
Mufida ta ce, "tafita makwafta yaya.
Makwafta kuma?, yanzu da sanyin safiyarnan?.
Shiru sukayi basuce komaiba, ya ce, " to kutashi mutafi idan kun gama?.
Rafi'a ta ce, "yaya bazakayi kari ba yau?.
A'a Rafi'a yau ina saurine, kudai kutashi muwuce, to suka fad'a suna mik'ewa, kowa yad'auki jakarsa ta makaranta suka fice.
Atsakar gida suka gamuda kawu, Umar yadurk'usa har k'asa yana gaida shi, Abba ina kwana.
Lfy lau Umaru anfito?, eh Abba mun fito, to wannan akwatinfa haka?, Abba wlhy wanine ya mantashi jiya dana d'akkoshi shine zanje na mayar masa, tofa yo kai Umaru banda abinka aii wannan tsintuwace, karik'e abinka kawai mana, nasandai bai wuce kaya bane aciki?, murmushi Umar yayi yanamai jinjina halin iyayen nasu aransa, ya ce, " karka damu abba nasan gidansa zankai masa dan takardune aciku, aikin 6ur inji tusa, a'a jeka kakaimasa abinsa, mizakayi dawasu tarkacen takardu dadai kud'ine ko kaya saika rik'e, nanma murmushi kawai Umar yayi harsu Mufida na tayashi.
Rafi'a da Mufida ma suka gaidashi, suma amsawa yayi cikeda fara'a.
Sallama sukai masa sannan suka fice, wajen adaidaitarsa sukaje, saida ya goge sannan suka shiga, makaranta yafara saukesu daganan yanufi gyad'i-gyad'i.
Da gyar ya iya gane layin, yatsaya adaidai inda yasauke dattijon Alhaji, gidan dayaga alhajin yashiga yake kallo, shi saima yanzu yaga gidan sosai, katafaren gidane na mai jida 'yan canji, komakaho yashafa katangar gidan yasan mai gidan ya shahara kuma yagama jik'ewa da data.
Yad'an dad'e atsaye yana tunanin yanda zai shiga gidan, baigama tunaniba yaga an wangale k'aton gate d'in gidan, wata dalleliyar motace tafito bak'a wulik sai d'aukar ido takeyi, k'arfin hali Umar yayi yamatsa kusada motar yana d'aga masa hannu.
Ahankali aka sauke bak'in Gila's d'in motar, wani matashin saurayi dabaifi sa'an Umarba ya bayyana.
Umar ya ce, "sorry Dan ALLAH inada tambayane?.
Inajinka saurayin yafad'a cikeda isa.
Umar ya ce, " jiya nakawo wani dattijo gidannan, to bayan mun rabu sainaga yayi mantuwa Dan haka nakawo masa abinda ya manta d'in.
Saurayi ya kashe motarsa sannan yacema Umar ya kamannin dattijon yake?, danshi ko kad'an baikawo dad d'insu bane.
Lissafa masa Umar yashigayi, cikeda mamaki Saurayin ya ce, "my dad, tomiya kaishi hawa adaidaita sahu?, bud'e motarsa yayi yafito, ya ce, " to muje cikidai.
Umar yad'auki d'an akwatin suka shiga cikin gidan, saurayi na baya Umar nabinsa abaya............
*_(((S)).....2017_*
*_Luv you all_*😻🤝.
[11/22/2017, 1:24 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_*
*_page→9-10_*
.........Wata had'ad'diyar k'ofar Gila's suka nufa, saurayin ya danna wani abu k'ofar tabud'e da kanta, Umar dai yanadaga baya yana kallon ikon ALLAH.
Bayan k'ofar tabud'e suka shiga k'aton falon dayagama k'awatuwa da kayan alatu, gurin zama saurayin ya nunama Umar sannan yashiga cikin gidan domin Neman iso.
Umar na zaune yanata Rarraba idanu tsakanin falon da kayan dasuke ciki saurayin yadawo.
Bismillah yafad'a yana nunama Umar hanya, mik'ewa yayi yad'auki jakar suka tafi, gaba da gabanta Umar yafad'a aransa yayinda suka shiga falo na biyu, saiyagama falon farko Ashe bai had'uba, yayinda suka shiga na Uku sai kan Umar yakusa kwancewa Dan maganama ta gagaresa, benen dake tsakkiyar falon suka hau anankam Umar yakasa daurewa saida ya ce, "masha ALLAH, falone nafad'a aji Wanda koda saga binnin sin kazo dolene ka yaba, nanma gurin zama ya nunama Umar.
Umar yazauna kad'an akujerar tamkar bayaso, sai 'yan kalle-kalle yakeyi.
Woow!!...... Yaji wata zazzak'ar murya yafad'a.
d'ago fararen idanunsa yayi ya sauke akan k'yak'yk'yawar fuskar mamallakiyar muryar, ya sauke numfashi ahankali tareda kauda idonsa akanta Dan itama nata icon nakansa kam ko k'yaftawa batayi.
Batasamu damar yin maganaba dad da Safwan suka fito.
Umar yamike domin nuna girmamawa ga dattijon, dattijo yay dariya tareda fad'in a'a saurayi kaine?.
Nine Alhaji, Umar yafad'a cikeda girmamawa.
Bismillah zauna mana, zama Umar yayi ak'asa, Alhaji ya ce, " a'a tashi ka koma saman kijera mana, nanma yayi wlhy Alhaji ngd.
Daganan Umar ya gaida Alhaji, cikin fara'a ya amsa masa, Umar yad'ora da fad'in Alhaji dama mantuwar sannan kayi, to jiyan naso dawowa na maida maka saikuma naga dare yayi shiyyasa nabari sai yau.
Tunda Alhaji yay tozali da akwatin kud'insa sai mamaki da al'ajabi ya lullu6esa, damage akwai sauran mutane nagari aduniya irin Umar?, Alhaji yajawo akwatinsa gabansa yabud'e, kud'insa na nan yanda ya shiryasu, yad'ago yana kallon Umar cikeda mamaki, Safwan ma dai kallon Umar yakeyi, hakama budurwarnan tad'azun.
Ajiyar zuciya Alhaji yasauke tareda fad'in yaron kirki kenan, nunama rasa abin fad'a saboda lunbin mamaki daya cikani, yaro yaya sunankane?.
Umar Fharuk!.
Masha ALLAH Umar Fharuk mai gaskiya da rik'on amana, lallai kadace da k'yak'yk'yawar zuciya maicikeda alkairi, ALLAH yasa kad'ore haka har karshen rayuwarka, wlhy bammasan namanta jakarnan awajenka ba, amma saboda adalcinka ka kawomini, kila dasai natashi amfani dakud'in naita bulayin Neman, kaidai ALLAH yayi maka albarka.
Gaba d'aya suka amsa da ameen har mom da Suhaima dake fitowa yanzun, Safwan yamik'ama Umar hannu sukayi musabaha sannan ya ce, "d'an uwa munfa gode sosai, nizan wuce abujane lokaci NATA tafiya, To ALLAH yatsare Nina ngd sosai.
Safwan yayma iyayrnsa da k'annensa sallama harya kama k'arfen bene zai sauka budurwar d'azu ta ce, " ya Safwan Dan ALLAH karma manta da sak'ona wajen Fidoo.
Karki damu baby zan fad'a mata insha ALLAH.
hannu tad'aga masa tana murmushi harya sauna.
Umar ya ce, "zaitafi wajen aiki, harya mik'e Alhaji ya ce, " Hana Umar Fharuk koma ka zauna aii alkairi dank'one baya fad'uwa k'asa banza, baby kusa kuku yashirya mana break fast.
To dad, Budurwar d'azu wadda suke kira baby ta amsa.
Babu yanda zaiyi dole yahak'ura ya zauna har aka gama shirya had'ad'd'en break fast a dinning.
d'unguma sukayi gaba d'aya zuwa dinning, Umar dukaya takura, musamman akan kallon k'urullah da baby ketamasa tun d'azun, dasun had'a ido saita sakar masa k'ayataccen murmushi, adaddafedai yakammala break d'in yamik'e, Alhaji yakama hannunsa har falonsa dashima ya amsa sunansa dankuwa komai yaji tamkar baza'a mutuba, zaunar dashi Alhaji yayi akan luntsumemiyar kujerar ta alfarma sannan shima ya zauna, idonsa akan Umar ya ce, "Umar Faharuk kayi karatu?.
Eh Alhaji nayi.
Wane mataki ka taka?.
Nahad'a degree d'ina Alhaji harda bautar k'asa.
Masha ALLAHU, ammafa kabirgeni wlhy, awannan zamanin bokowane matashine kamarka zai kammala karatun Degree ba yadawo tuk'a adaidaita sahu, Dan aganinsu hakan zubar da girmane, kuma bahaka baneba.
Umar dai kansa na k'asa yana murmushin jin dad'i.
Alhaji ya ce, " to yanzu insha ALLAHU zan taimakeka domin nima ka taimakeni taimakon dabazan ta6a mantawa dakaiba atarihin rayuwata, idan kanason aiki kakawo takardunka zan nema maka, idan kuma kasuwanci kakeso wannan mai sauk'ine daga gobe ma zaka fara insha ALLAHU?.
Wani dad'ine yatsarga zuciyar Umar, yad'ago yana kallon Alhaji, zamowa yayi k'asa ya tsigunna yana masa godiya, Alhaji yakamashi yamaida saman kujera yana fad'in karma damu Umar kaima kazama d'ana aii, yanzu wanne kaza6a?.
Alhaji naza6i kasuwanci Dan dama shine burina, nayi karatune Dan kare mutuncin kaina amma badan aikiba.
To Alhamdllh naji fad'in za6inka nima sosai, Alhaji yamik'e yana fad'in jirani ina zuwa.
Babu dad'ewa yafito, yazauna kusada Umar tareda mik'a masa makullin mota, Umar ga wannan tukuycin alkairinka gareni.
Idanu Umar yazaro bakinsa na rawa ya ce, "baba motacrfa?.
Dariya Alhaji yayi ya ce, " nasani Umar motace tana nan aharabar gidannan, zansa direba yakaimaka har gida, idankuma zaka d'auka da kankane babu laifi.
Hawayen farinciki Umar yakeyi, ya ce, "baba dakabarsa, wlhy ban kawo maka jakarnan danka sakamin dawani abuba, namaido maka da itane saboda tsoron ALLAH da cin hak'in saba nawaba.
Alhaji yakamo hannun Umar yasaka masa key d'in Hana fad'in nasani Umar, nima namakane badan na biyakaba aii.
Godiya sosai Umar yayma alhaji sannan yafito.
Afalo yatarar da baby da Suhaima, suna ganinsa baby tamik'e tsaye cikin fara'a ta ce, "ya Umar kafito?.
d'an murmushi yamata tareda jinjina Kansas.
Takashe masa ido d'aya tana wani far da idanu, tobara namaka rakkiya ko.
Baice komaiba Dan tafara gundurarsa, kusan at are suka sauka, ganin haka yasaka Suhaima bin bayansu da sauri danson ganin abinda zai faru.
Har wajen gate suka rakoshi, yashiga a adaidaitarsa yatada, baki Suhaima ta ta6e afili tace kambu tak'ashinnan, yanzunan duk had'uwar bawan ALLAHn Nan a adaidaita sahu yazo?.
Hararta Baby tayi sannan tak'arasa kusada Umar dake k'ok'arin tafiya, ta ce, " ya Umar mungodefa sosai, inafata zaka cigaba da ziyartarmu Dan sada zuminci?.
Kallonta kawai yayi baice komaiba ya kauda kai.
Murmushi tayi azuciyarta ta ce, "ka cancanta my guy, afili kuma ta ce, " I Love you so much.💋
Da sauri Umar yad'ago yakalleta amma tuni harta bar wajen ta isa inda Suhaima ke tsaye tana kallonsu.
Kasa tafiya yayi yatsaya binsu da kallo, harsaida suka isa gate sannan Baby tajuyo ta kanne masa ido d'aya tashige cikin.
Wata sassanyar ajiyar zuciya yasauke sannan yakuma tada baburd'in yafice daga anguwar cikeda farin ciki.
Tunanima yake wayakamata yafara fad'ama albishir d'innan, su mama ko inna ko Anty Sa'a?, baisan dawa zai faraba.
Daga k'arshedai ya yanke shawarar fara zuwa gidan inna, dankoba komai itace ta k'arfafa masa hayar adaidaita sahun, togashi tasilar hakan yayi gamon katar da tarin alkairi, kunga kuwa aii ita yafi cancanta tafara sani ko?.🤷🏽♀
Kai tsaye gidan inna yanufa kuwa........
*_(((S)))........2017_*
*_Luv you all_*
[11/23/2017, 4:57 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO......😜_*
*_page→11-12_*
........Tun'a k'ofar gida yaci karo da abinda yasaka farincikinsa rauni, wato ganin Asma'u da wani saurayin ranar, Asma'u na ganinsa ta 6ata fuska Dan gudun karya k'ara bata kunya kamar ranar, abisa tsautsayi suka had'a ido, yamaka mata wata uwar harara.
Kauda kanta tayi daga kallonsa, saurayin na gaisheshi amma ko kallon bai isheshiba yashige cikin gidan.
Asma'u tarakashi da harara.
Saurayin ya ce, "Asmy wanene wancan kuma?, nagafa sai hararmu yakeyi?.
Baki Asma'u ta ta6e ta ce, " yayanmune.
Kai Asmy shine baki fad'aminba na gaisheshi da k'yau?.
Uhmm kaga Zayyan share batunsa kawai, yanzu yaushene zaka dawo a tafiyar?.
Uhmm insha ALLAHU bazan wuce 2year's ba zan dawo.
Kai kana nufin bayan mun kammala s,s,c,e fa kenan?.
Eh hakane my Asmy, amma kiyi hak'uri nima Bahaka nasoba wlhy, kinsan karatunane yakawo haka, kuma umarnin Abba ne babu yanda na iya.
Shikenan ALLAH yatsaremin kai, yasa kaje a sa'a kadawo a sa'a.
To ameen my Asmy, shiyyasa nake k'ara sonki da k'yaunarki akowacce dak'ik'a ta rayuwata.
Murmushi Asma'u tayi, tareda fad'in nima ina sonka sosai zayyan, tayi maganar tana rufe fuskarta da hijjabi.
Dariya zayyan yayi yace Asmy sarkin kunya kenan......
A6angaren ya Umar kuwa ransa a6ace yashiga gidan, inna data fito daga d'akin baba mahaifinsu Asma'u ta ce, "a'a Umaru kaine agidan?.
Murya acinkushe ya ce, " nine Inna, sannu.
Yauwa Umaru, amma yanaga kamar Ranka a6ace yake?.
Da sauri ya saisaita nutsuwarsa, shikansa yana mamakin yanda baya iya 6oye Bacin ransa idan yaga Asma'u da saurayi, kuma aii hakan bata faruwa akan Mufida kosu fatee, wata zuciya ta ce, "aigara Mufida tayi girma tunda tana 100L a jami'a, amma Asma'u fa SS 1 take a secondary........
Innace ta ta6ashi, firgigit yadawo daga duniyar tunani, ta ce, " tunaninmi kuma kakeyi Umaru?.
Cikin inda-inda ya ce, "babu komai Inna wani albishir Nazo miki dashi, amma mi Asma'u yakeyi awaje da safennan?, mima yahanata zuwa makaranta.
Dariyace taso kufcema Inna saboda hango kishi k'uru-k'uru a idanun Umar, amma saita dake tace kasan suna Exam, toyau basuda ita shiyyasa, wancan kuma Zayyanne wai zaiyi tafiyane shine yazo suyi sallama.
Kansa kawai yagyad'a amma bai iya cewa komaiba yamik'e yana fad'in bara nagaida baba.
To kashiga yana ciki.
Ak'ofar d'aki yayi sallama, saida aka bashi izinin Shiga sannan yashiga.
Baba na zaune yana karin kumallo Umar yashiga, cikeda fara'a yataresa, Fharuku kaine agidan namu?.
Nine baba ina kwana?.
Lfy lau Umar ya hidimomin duniya?.
Alhmdllh baba.
To masha ALLAHU, kaga matso muci abinci ko?.
A'a wlhy baba nakarya nikam.
Kai Umaru karfa filako kakeyi?, a'a baba yazanyi filako agidanmu, nak'oshine kawai, to shikenan, yawajensu Maman taku?, lfy lau suke baba sunama gaisheku, a muna amsawa wlhy.
Umar yamik'e to baba bara naje mugaisa da Inna natafi wajen nema.
To Umaru ALLAH yabada sa'a kaji, ayitadai hak'uri da yanayin rayuwa, duk Wanda kaga yayi hak'uri baici ribaba to d'an kad'an yayi, duk abinda ALLAH ya albarkaci mutum dashi karya raina yace Alhmdllh, to insha ALLAHU ALLAH zaibasa mafiyinsa agaba kajiko?.
To baba ngd sosai, ALLAH yak'ara yawancin kwana.
Ameen Umaru ALLAH yayi albarka kuma.
Amen summa ameen baba, naira 500 ya ajiyema baba, baba ga wannan asha fura.
Kai a'a Umaru zoka d'auki kud'inka kaji, nikam bazan kar6aba, airik'e kankuma dakukeyi abin alfahirinmune basai kumbamu ko sisiba.
Hhh baba Dan ALLAH ka kar6a kasamusu albarka, nima banisu akayi.
To shikenan Umaru ALLAH yak'ara bud'i na alkairi ngd sosai.
Babu komai baba Umar yafad'a yana ficewa daga d'akin.
d'akin Inna yashiga, azaune yatadda ita tana jiransa, yasamu waje yazauna suka k'ara gaisawa da tambayar lfyar juna.
Alhmdllh Inna sai godiyar ALLAH.
To aii haka akesonji Umaru, wanekuma albishir aka kawo mini?.
Murmushi yayi tareda gyara zama yazayyane mata komai tundaga jiya har safiyar yau.
Farinciki sosai Inna ta Nuna harda kukan dad'i, tashi tayi tagad'oma baba shima yayi farinciki sosai, har d'akin inna yashigo yataya Umar murna da wanan k'yauta.
Suna cikin farincikinsu saiga Asma'u tadawo hannunta d'auke da Leda.
Itadai kallonsu kawai takeyi, data kasa jurewa saita ce inna wai miya farune kuketa murna haka?.
Inna ta zayyane mata komai, itama sosai tanuna farincikinta akai, ya Umar kam sai antaya mata haarar yakeyi, ko a jikinta wai antsikari kakkausa.
Bayan sun gama murnar yatashi yatafi akan zaidawo gobe yanuna musu motar.
To d'an Albarka, ALLAH yayi albarka kaji.
Ameen inna saina dawo.........
Daganan sai gidan Anty sa'a, ita kad'ai yatarrar agidan Dan yara suntafi makaranta, tamik'e da k'yar saboda tsohon cikin dake jikinta, oh ni Umar dama kana duniya?.
Dariya yayi ya ce, "Anty Sa'a ina zanje?, hidimomine kawai sukaimin yawa.
Haka kuka iya kullum kaida Abubakar da Harris bakwa rasa uzuri aii.
Tab Anty aii garani da wad'annan, kema kinsan ina k'ok'arin zuwa wajenki fiye dakowa agidanmu.
Eh to hakane kuma, amma aii kaima wani lokacin saika 6ace 6at.
'Yar dariya yayi ya ce, " hakadai kikace Anty sa'a.
Oh hakama zakace?, Anty sa'a tafad'a tana fita daga falon.
Babu dad'ewa tadawo d'aukeda tire shak'e da kayan ciye-ciye.
Da sauri Ya Umar yamik'e yatarota, kai Anty yakamata ki saukema kanji irin wad'annan aiyukan, ai kinyi nauyi dayawa.
Zama tayi da dabara, shima ya ajiye tiren sannan ya zauna.
Ta ce, "k'anina yazanyi, aii dole natashi nayima kaina, 'Yar mai aikin dake taimakamin kakarta tarasu taje gida tun shekaranjiya, jabeer da Laila kuma mizasu iyamin inbanda su 6ata.
To da wannan Dan wannan kuma, amma gsky mata kuna bani tausayi matuk'a, koda rainon cikinnan kad'ai akabarku aiba k'aramin k'ok'ari kukayiba, balle ga haihuwa, raino, tarbiyya dukfa suna kanku, kai ALLAH yasaka muku da aljannadai.
Amin d'an k'anina, Anty sa'a tafad'a tana dariya.
Shima dariyar yayi yana kai kofin zo6o bakinsa, saida yasha sosai saboda k'aunarsa da zo6o sanan ya ce, "big aunty dawani daddad'an albishirfa nazo miki.
Tofa k'anina ko ansami matar aurene?.
d'an tsaki yayi ya ce, " Anty wane matar aurefa, aii aurena banan kusaba kuma dainamin zancensa.
Umar kanka d'aya kuwa?, wai sokake saika tsofe agidane?, shekararka fa 28 yanzu, amma ace babu aure agabanka?.
Hummm Anty sa'a kenan, Ku kawai auren kuke ambata, amma bakwa tunanin inda mutum zai ajiye matar, abinda zataci, Wanda zai mata sittira dakuma matsalolin yauda kullum musamman na rashin lafiya dakanzo tamkar ha6o.
Hakane Umar amma aii duk ALLAH ne mai komai da kowa ko?.
Hakane Anty ALLAH yasa mudace to, dama albishird'in nawa shine..................tas ya zayyane mata komai.
Saboda farinciki jitake kamar tatashi taita tsalle, ta ce, "ALLAH sarki Umar kaga ribar hak'uri ko?, lallai yau nayi farinciki sosai, ALLAH yasa iyakar wahalar kenan.
Amen Anty sa'a ngd.
Sund'an dad'e suna hira sanan yatashi yaymata sallama yatafi.
Daga nan aikinsa yatafi, yau cikin d'unbin farinciki yakeyin komansa har zuwa dare daya koma gida.
Yaukam dawuri yakoma gidan Dan ana isha'i yakoma.
Afalo ya iske mutanen gidan suduka, har yaya Abubakar yazo, suka gaisa Harris da su mufidama suka gaisheshi, mamadai ta had'e masa gabas da gamma, amma wanan bai hanashi gaishetaba.
Kamar yafad'a musu saikuma yayi shiru da bakinsa, and'anyi hira ya Abubakar yatashi yatafi, shima Umar mik'ewa yayi yamusu sallama yatafi d'akinsa, ganin haka Harris ma yamik'e akabar mama da 'yan matanta..........
*_(((S)))........2017_*
*_luv you all_*🤝😻.
[11/23/2017, 4:57 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_*
*_Gaisuwa da fatan alkairi agareku, Action baby & Maman Khaleed, alkairin ALLAH yakai muku aduk Inda kuke, ALLAH yabar zuminci, INA alfahari daku😻😍❤👌🏼._*
*_page→13-14_*
........washe gari Umar yay shirinsa, kamar yanda yasaba yalek'a ya gaida mama, dukda bata wani amsa masa yanda yakamataba amma hakan bai damesaba yamik'e yashiga d'akin Abba shima ya gaisheshi, baisake bin takan kowaba yafice abinsa sai gidan Alhaji.
Yau har ciki mai gadi yabarsa yashiga da Babur d'insa, yananan tsaye saiga baby tafito yaudai tayi kwalliyarta sa6anin jiya dayasameta cikin kayan barci.
Cikeda rangwad'a tak'araso garesa, Umar yajanye idonsa daga kallonta, Hii my guy, tafad'a tana dafa adaidaita sahun.
d'aure fuska Umar yayi, ko kallonta baiyiba barema tasamu amsa.
Abin ya6ata mata rai, amma saita dake, ta ce, "sorry Assalamu alaika.
Sai yanzu Umar yajuyo fuskarsa babu yabo babu fallasa ya ce, " wa'alaikissalam.
Murmuahi tamasa tareda fad'in dama haka kake babu sauk'i?.
No bahaka bane, yadace duk inda d'iyan musulmi yashiga farko yafara sallama kafin yasamu damar aiwatar da Abu nagaba, ina fata daga yau zaki gane kuskurenki ki gyara.
Tayi far da idanunta, cikin sanyin murya ta ce, "kayi hak'uri zan gyara insha ALLAH.
Wani murmushin daya kasheta yamata, talumshe idanunta domin jin wani dad'i ya ratsa zuciyarta, bata dawo daga magagin shauk'in so ba muryarsa tadaki kunnenta.........
Wai miye cikakken sunankine?, nasandai baby ba suna baneba......
Da sauri taware idanunta akansa, cikeda salo ta ce, "sunan Lubna."
Shima maimaita sunan yayi a la66ansa, ya ce, "lubna!, nice name.
Cikeda jin dad'i ta ce, "da gsk?.
Kansa ya jinjina mata yana murmushi.
Wani uban tsalle tayi Wanda yasakashi tsayawa kallonta, ngd ya Umar I love you wlhy.
Umar kam yadaskare atsaye, mamakinta yakeyifa, tun jiya take ambatar kalmarnan akansa, amma yagaza gane inata dosa......... Muryar alhajice takatse masa tunaninsa, Umar kayi hak'urifa baby tacikaka da magana.
Murmushi Umar yayi ya ce, "babu komai Alhaji aii muna gaisawane.
Duk'awa yayi yana gaida Alhajin, Alhaji ya amsa yanamai kamasa ya tadashi tsaye, Lubna tazo saitin kunnen Dad d'inta tagaya masa wani Abu danima banjiba.
Dariya dad ya ce, " baby da gsk koda wasa?.
Dad serious wlhy, tarufe idonta.
Masha ALLAH babyna ALLAH yatabbatar mana da alkairi, kisa aranki kinsameshi kinji, kanta tagyad'a tanamai farinciki, shidai Umar dabaisan miye zancen nasuba kallonsu kawai yakeyi.
Tundaga Ranar Alhaji yad'ora Umar akan dukiyarsa, Umar ya ajiye daidaita sahu, yafara hawa motar da Alhaji yabasa, lokacin dayakaima su mama wannan zance mama tamkar zata goyashi Dan farinciki, tundaga ranar yazama d'an lelenta, komai Umar, duk wani motsinta Umar, abinci saiya za6a, idan yadawo daga kasuwa tayita nannan dashi tamkar wani jariri.
Shi Umar ma wani Abu dariya take bashi damamaki.
A6angaren kasuwa kuwa komai yaaa tafiya masa daidai saboda kasancewarsa mai ilimi, kullum cikin dabarar kasuwanci yakeyi Dan haka dukiyar Alhaji tak'ara bink'asa, ga Umar mutumne mai gsky da rik'on amana Dan haka Alhaji yake matuk'ar son Umar Fharuk.
Umar yazama d'an gida sosai, bashida wani shamaki agidan Alhaji, ko ina shiga yakeyi, ahaka kuma soyayaya mai k'arfi tak'ullu tsakaninsa da Lubna, soyayya mai tsafta suke nunama juna.
Umar kam komai yacanja masa yanzu, yafara zama babban mutum, ga d'inkuna na alfarma Alhaji namasa, duk motar dayaso hawa yake agidan Alhaji, gashi kowa sonsa yakeyi agidan.
Ganin yanda abubuwa suke tafiya daidai Alhaji yabama Umar jarin kansa ya ce, "shima yajuya, amma duk da haka yana kula masa datasa dukiyar.
Ubangiji mai hikima cikin k'ank'anin lokaci Umar yabunk'asa yazama babban d'ankasuwa abin kwatance, ga abokai masu kud'i daji da Kansu, kowa sonshi yakeyi, agidansu kam yazama shine babba, sai abinda yace, yamaida k'annensa makarantar kud'i, yagyara gidan tsaf tamkar bashiba, hakama inna binta bai mantataba, dakansa yacanjama Asma'u wata makaranta tafara zuwa, suma su Hasiya ya canja musu makaranta, dangi kowa yanacin amfanin Umar, mamako sai d'agawa da Nuna isa itama d'anta yazama wani Abu, zannuwa take sakawa masu tsadar gsk, harta canja k'awaye, komaidai zamzam.
Ana cikin haka Alhaji yabashi damar turo iyayensa domin Neman auren Lubna.
Sosai Umar yay murna da wanan batu Dan yana tsananin k'yaunar Lubna sosai, babu Wanda bai Santaba a family nasa, taje gidansu sau babu adadi domin gaida mama, har inna da Anty sa'a saida aka kaita ta gaida.
Manya sun shiga ansaka ranar auren Ya Umar da Lubna watanni kusa.
\\\\\\\\\\\\\\\\\\\\\\
Asma'u takalli 'yan uwannanta dasuka baje kayan alawa da biskit sunata rabo, baki ta ta6e tareda kauda kanta daga Kansu tacigaba dacin abincinta.
Antu Saratu ta harareta, kekuma miye kike wani ta6ema mutane bakine?.
Nifa yaya Saratu bance komaiba.
Fatee dake 6are cingam ta ce, "yaya Asma'u kodai kina kishine?, Dan sainaga kamar kinason ya Umar.
Kutttt, Asma'u tafad'a tareda jifan fatee da murfin kwano.
Kaucewa fatee tayi tana dariya, suma 'yan d'akin dariya sukeyi duka, Asma'u tayo kan Fatee tana masifa, da gudu Fatee tafito Asma'u ta biyota.
Gaf tayi karo da Abu, baya taja da sauri tareda dafe goshinta tana fad'in wash ALLAHna, abisa tsautsayi ta taka 6awon ayaba, aiko tazame suuuuu zata fad'i.
Da sauri yaruk'o hannunta ta fad'o jikinsa, daddad'an kamshin turarensa ta shak'a ta lumshe idonta, saikuma tabud'e da sauri danjin antureta gefe.
Ya harareta kewai bakida Kaine?.
Idanunta ta kwalalo waje, saikuma tahau kakka6e jikinta tana wani had'e fuska, yakatseta da fad'in ina hankalinki yatafi?.
Saida tad'an murgud'a bakinta amma bai ganiba sannan ta ce, " yana jikin......
Bata k'arasa fad'aba ta hango fatee, dagudu tawucesa tabi Fateen suka afka d'akin inna.
Girgiza kai Ya Umar yayi shima yanufi d'akin.
Afalon yatarar dasu suna zagaye kujeru, hasiya da Anty Saratu sunata tuntsura dariya, cikin dariya Anty Saratu ta ce, "wlhy Ma'u kifad'i gsky, Dan nima nadad'e ina zargin soyayya kukeyi da ya Umar, kumafa wlhy kun dace, kardai ki cuci kanki, kifad'a sai'a had'a masa biyu kawai.
Dan ALLAH Anty Saratu kibari, ALLAH zakusa nakuma TSA.......
Bata k'arasaba ta hangi ya Umar tsaye abakin k'ofa, mak'alewa maganarta tayi amak'oshi.
Suma duk kallonsu Yakoma kansa, yak'araso d'akin shima, guri yasamu ya zauna suka gaisa, ya ce, " innafa?.
Inna tana gidanku aii tunda safe.
Ayya aiban saniba, dayake badaga gidan nakeba.
Ruwa Hasiya takawo masa da zo6o, zo6on yasha Dan yanaso sosai, domin shima Inna takeyin zo6o ta ajiye .
Asma'u kam d'aki tashige, tana shiga hawaye suka fara bin kumatunta, tabbas son Yaya Umar na neman illata mata zuciya, tadad'e da d'umbin sonsa azuciyarta tun tana karama, haka taketa dakonsa, saboda alkunya irinta 'ya'ya mata Hausa Fulani dakuma tsoronsa Dan tuni ta lura ya Umar kam haushintama yakeji, wannan yasa take dannewa da k'ok'arin ciresa aranta, amma hakan na Neman gagara.
Ashe duk k'ok'arin danne zuciyarta da takeyi akan ya Umar 'yan uwanta harsun fara fahimtarta?, ya ALLAH ka kawomin agaji akan wannan lamari, idan ya Umar mijinane ALLAH ya karkato da hankalinsa kaina, idan kuma ba mijina bane ya ALLAH kaciremin sonsa azuciyata na hak'ura da zayyan d'ina, daya dawo muyi aurenmu.....
Share hawayen fuskarta tayi da sauri danjin muryar ya Umar na kwala mata kira.
"Husna!."
"Husna!!."
Lumshe idanunta tayi sannan ta amsa, shikad'aine yake kiranta da Husna, shiyyasa takanji sunan daban kamar ba nataba.
Asanyaye tafito, yana tsaye a bakin k'ofa da alama fitama zaiyi, kallo d'aya tamasa ta kauda kanta, tad'anje nesa dashi tashaya kamshin turarensa na bugun hancinta, shima idonsa akanta yamik'a mata kud'i yana fad'in da safe kije gidan matar Yousif kikaimata ta ajiye masa, saura kuma idan kinje ki kai dare.
Saida ta tura baki gaba sannan ta kar6a, yamik'a mata d'ari biyar na mashin, nanma kar6a tayi, baijira cewartaba yafice.
Da harara tarakashi, tajuyo cikin falon tana k'unk'uni.
Anty Saratu dasu Fatee suka shek'e da dariya harda tafawa suna fad'in soyayya ruwan Zuma.
Asma'u bata kulasuba tashige d'akin inna domin ajiye kud'in............
*_(((S))).......2017_*
*_Luv you all😻🤝 ._*
[11/25/2017, 5:37 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_*
*_masha ALLAH, ALLAH yasauki k'awata Ayusher Muh'd lfy, ya azurtata da samun haihuwar baby gal, Ubangiji ALLAH yaraya mana ita akan turbar musulinci, ALLAH yasa Bad'i mudawo sunan twin's kuma_*😻😜
*_page→15-16_*
............Shirye shiryen biki ya kankama sosai, ya Umar yagama gyaran gidansa tsaf, gidane na garari Wanda za'a iya kira namai kud'i, kowa yagani dolene ya yaba Dan gidan yaginu babu k'arya.
Agidansu amaryama shirin biki akeyi na 'Yar gata Dan wannan shine karo na farko dazasu aurar, komai na 'yan gata aka shirya, damma mahaifiyarta batason auren, Dan taso ace lubna ta auri d'an shahararren mai kud'i irinsu amma ba Umar ba, to amma babu yanda zatayi tunda takafe shitake so.
Mama kam wannan aure yamata dad'i d'anta zai auri d'iyar masu kud'i, sai d'agawa da fariyya takema 'yan anguwa.
Asma'u tunda aka fara shagalin bikinnan tashiga matsanan ciyar damuwa, amma haka tadage da addu'oi harda azumi tana addu'ar ALLAH ya danne zuciyarta tazama mai hak'uri, inna tana kula da duk halin da Asma'u tashiga amma babu yanda zatayi saidai ta taya d'iyar tata da addu'a tunda haka ALLAH yatsara lamarinsa.
*_biki buduri_*
Ansha biki na nunawa a duniya Dan taron d'aurin aurene daya halarci manya-manyan masu fad'a aji ak'asarnan, sarakuna, 'yan siyasa, 'yan kasuwa, harda shugaban k'asa, lamarin bak'aramin girgiza Ya Umar yayiba, Dan baita6a zaton ko kansilan anguwarsu zaizo d'aurin aurensaba bare shugaban k'asa gaba d'aya.
Biki kam saidai Sam barka Dan nera tayi kuka sosai.
Bayan biki amarya da ango ansha amarci babu k'arya, sosai suke zuba soyayya kamar babu gobe, saida ya Umar yay sati biyu baya fita kasuwa, koda yaushe yana gida manne da lubna, abinci saidai suje su sayo.
Tsawon wata d'aya ana kashe kan amarci, amarya babu abinda takeyi dagaci sai barci, komai saidai 'yan aiki, wani lokacinma ya Umar keyimata wankan, abinda yafara 6ata masa rai da ita shine son jiki, komai saidai ayi mata tana a kwance, daidai da ruwan dazaisha saidai tasaka 'yan aiki sukai masa, gyaran d'akinsama haka, wani abin k'arin haushinma shine duk sanda zaidawo gidan saidai ya Tatar da ita shame-shame kwance 'yan aiki namata tausa, wannan lamari na 6ata masa rai matuk'a.
Daya kasa daurewa yafad'ama mama saitace yacika k'orafi shikam, ya yarinya tatashi cikin Hutu yanzu zai k'ok'arin tsinke mata, itafa bata yarda ko fad'a yaringa yima Lubna ba, abin ya6ata masa rai, yarasa wane irin haline da mahaifiyarsu?, haka yabar gidan ransa a6ace.
////////////////+////////////
A6angaren Asma'u kuwa abubuwa sun mata sauk'i, tanata k'ok'arin cire ya Umar azuciyarta, tamaida hankalinta sosai akan karatu babu wasa, burinta bai wuce Zayyan d'inta yadawo suyi aureba.
Ana haka Lubna ta fara laulayin ciki, zazza6i da yawan amai sun addabeta Dan haka ya Umar yakaita asibiti, gwaji farko akace cikine.
Cikin tashin hankali lubna ta ce, "doctor jafar cikifa kace?".
Dariya Doctor jafar yayi, ya ce, " hakane lubna kina d'aukeda babynmu.
Afusace takalli ya Umar da farinciki yacika zuciyarsa shima zai zama baba, ta ce, "Umar kanajindai abinda doctor yafad'a aii?. Murmushi ya Umar yayi yarungumota zuwa jikinsa yana fad'in naji sweet d'ina, kuma inacikin farinciki......
Bai k'arasaba ta fisge jikinta daga nasa, ta6d'i jan Umar wlhy bazata sa6uba, yaza'ayo kamarni 24year's ace inad'aukeda ciki, lallai akwai lale awannan batun.
Cikin mamaki ya Umar ya ce, " Lubna akwai lale kamar yaya?, wannan ba abin farinciki bane?.
Abin farincikine agareka Umar, ammani abin kunyane da bak'inciki agareni, ace kamarni beby wata hud'u da aurena aganni da ciki, haba saikace dai wata akuya, asaima k'awayena sumin dariya wlhy.
Daga ya Umar har doctor jafar kallonta sukeyi cikeda mamaki, ya Umar ya kwantar da murya cikin Nuna damuwa ya ce, "haba Lubna miye abin kunya ga samun k'yautar ALLAH?, kitunafa akwai dubunmu dasuke nema amma ALLAHA bai basuba muyabamu, bakuma dan munfisu agurinsa bane, a'a ikonsane yasa yabamu sukuma baibasuba, amm.......
Hannu tad'aga MASA cikin masifa ta ce, " kaga Umar Dan ALLAH sauraramin da wannan wa'azin naka mana, nifa nace banason ciki yanzu, danhaka saikasan yanda zakayi dani, ban shirya rainon cikiba ayanzu kuma babu mai tursasani nayi.
Ran ya Umar yafara 6aci, Dan haka afusace shima ya ce, "to wlhy Lubna babu mai zubarmin da ciki, dukma abinda zakiyi saidai kiyi, yamik'ama doctor jafar hannu sukayi musabaha, abokina ngd, yadaka mata tsawa dallah malama tashi muwuce.
Mik'ewa Lubna tayi Dan tsawar Umar d'in ta razanata sosai
Tundaga wannan ranar zamansu yafara rawa, kullum cikin fad'a da tashin hankali, abin kamar wasa har yakaisu ga zuwa wajen iyaye, mahaifiyar Lubna ta goyi bayan lubna ta zubda ciki, amma mahaifinta ya hana, sosai lamarin ya6ata ran Lubna, tundaga wannan lokacin komai ya canja musu, shidai yana nuna mata kulawa sosai da tattali, duk abinda ta ce, "tanaso zai saya matashi, ga cikin NATA da saka shagwa6a, tattalin dayake nuna mata yasakata sakin jiki itama ta manta da komai suka koma zuba soyayyarsu, mama bata had'a sati d'aya batazo gidanba ganin Lubna.
Ahaka cikin lubna yashiga watan haihuwa, kuma Yakama lokacin hutunsu Asma'u suna gida.
Ya Umar yaje ga inna tabashi Asma'u danta taya Lubna zama tunda tace bataso akawo mata kowa, dayace to yad'akko Asma'u?, saitace ta amince zata zauna da Asma'u Dan mutuniyarta ce.
%-%-%-%-%-%
Tunda Asma'u tazo saita raina tsaftar matar gidan Dan bawani zuwa sukeyi sosaiba, batayi k'asa agwiwa ba tace duk 'yan aikin su huta tazage sosai tagyara gidan har d'akin ya Umar ko INA yad'au k'amshi, takuma shiga kichin tamusu abinci mairai da lafiya.
Lubna dakebin Asma'u da kallo ta ce, "lallai sunnunki da k'ok'ari, wai bak'yajin ciwon jikine?.
Dariya Asma'u tayi tareda fad'in wlhy aunty Lubna banajin komai, aiini ban d'auki aikin gidannan aikiba, idan dawani bayan wannan tom zanyi kuma natashi garau.
Baki luban ta ta6e tace lallai wahala da rai.
Asma'u batace komaiba saidai dariya.
Da ya Umar yadawo tun a harabar gidan yaga canji, yashigo falon shima cikeda mamaki yakebin ko ina da kallo, Asma'u dake zaune tana kallo tamik'e tana fad'in sannu da zuwa ya Fharuk.
Kallonta yayi ya ce, " yauwa Husna sannunki, Lubna kam ko kallo bai ishetaba tana zaune turus ak'asa, ya Umar yak'arasa gareta yana murmushi, rungumota yayi had'eda manna mata kiss akumatunta, Uwar biyu ykk?. Fuska ta yatsine masa tana wani kumbura Baki, kacefa yanake tunda kahad'ani da aiki, murmushi yayi acikin kunnenta ya ce, "aitare mukayi bani kad'aiba ko?, bare amin d'agwaiy, dukan wasa tamasa ak'irji, yatashi yana dariya, daidainan Asma'u tafito daga kichin d'aukeda k'aramin tire tad'ora ruwa da lemo da cup, ganin yamik'e ta ce, ''ya Fharuk ga ruwa.
Kallonta yayi acikin wani yanayi, tunda yay aure ba'a ta6a akawo masa ruwaba ayayin daya dawo gida, wani lokacinma saizaici abinci za'a bashi kokuma ya rok'a, kansa ya jinjina mata yakoma ya zauna, Asma'u ta tsiyaya ruwa ta mik'a masa, kar6a yayi tareda bismillah yasha, Lubna ta ce, " Asma'u kedai bakya gajiya, yanzunan k'ato dashi saikin kawo masa ruwansha?.
Kallonta kawai Asma'u tayi amma bata iya furta komaiba, shimadai ya Umar zuciyarsa ta sosu da maganar ta Lubna amma saiya share yamik'e bayan yagama sha, d'akinsa yashiga danya rage gajiya, Kallon ko ina yakeyi cikeda sha'awa, yasan wannan aikin Asma'u ne Dan matarsadai bata iya komaiba sai addabama 'yan aiki, dawad'annan tunane-tunanen yay wanka yashirya sannan yadawo falon, inda yabar Luban nan yasameta da wahalallun 'yan aikinta suna faman mata tausa, harya zauna Asma'u ta ce, "ya Fharuk ga abincifa.
Kallonta yayi saikuma ya kauda idonsa, ya ce, " yaushe kika iya abinci?, idanu Asma'u ta kwalalo danjin rainin hankalin mutuminnan, saikace yau yafara cin abincinta, tad'an murgud'a baki sannan ta ce, "aibani nayiba Anty Lubna CE.
Da sauri ya kalleta, saita kauda idonta, ya jinjina kansa Dan yagane bak'ar magana tamasa, itako Lubna saita washe baki tana fad'in a'a kedai kikayi abinki, ni inani ina aikin wahalarnan, my Honey kaje kaci wlhy akwai dad'i sosai dantafi kuku iyawa, nidama zata dawo nan gidan danaso haka..
Kallonta kawai yakeyi cikeda al'ajabi amma yagaza furta mata komai, saida ya mula Dan kansa harma Asma'u tayi fushi sannan yasakko k'asa Dan bayacin abinci a dinning, Asma'u tajere masa komai tazuba masa, aii mutuminku dayayi cokali d'aya saida ya lumshe idanu, sosai yakejin dad'in abincin, wannan yana d'aya daga cikin abinda yasa ya d'akko Asma'u ta zauna dasu.
Tundaga ranar komai Asma'u takeyi agidan, tazama tamkar itace matar gidan, kwananta takwas dazuwa Lubna ta haihu 'yan biyu duk mata, wayyo zokaga murna wajen ya Umar da sauran dangi harma da family d'in Lubna, ranar suna yara sunci sunan mama da momyn Lubna, wato Maryam da Haleematu, za'a ring a kiransu Amrah da Afrah.
Bayan suna dakamar sati biyu su Asma'u suka koma makaranta, Dan haka ta tattara ta koma gidan d'aukeda shatara ta arzik'i daga Lubna da Ya Umar...............
*_(((S))).....2017_*
*_Luv you all_*
[11/26/2017, 4:48 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_*💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO........😜_*
_masu karatu karfa Ku rikice, har yanzu muna cikin tunanin Asma'u ne_.
*_page→17-18_*
.........Shekaru sun shud'a sosai Dan su Asma'u harsun kammala s,s,c,e d'insu, amma haryau Zayyan bai dawoba, abin yana damunta, hakama iyayenta, gashi bata kula kowa Dama saishi, iyayenta sunso Sumata aure tunda ta kammala secondary amma hakan ya gagara, suna zaman jiran dawowar Zayyan, a haka Asma'u takusan cinye shekara agida.
Ranar ya Umar saiyazoma Inna da shawarar mizai hana Asma'u takoma makaranta da wannan zaman?, idan saurayin nata yadawo koda tana karatunne sai ayi auren tacigaba agidan mijinta.
Da farko inna da baba sunk'i, amma ya Umar yadage da nuna musu fa'idar karatun sai suka amince.
Babu 6ata lokaci yafara nema mata makaranta, dandanan kuwa aka samu Dan yanzu su Yaya Umar sunzama manya, komai shine yayi mata, tafara zuwa makaranta nan FCE kano.
___________________
Agidan ya Umar kam abubuwa na tafiya daidai, yaranshi sunyi girma ko ina zuwa sukeyi, ga surutun tsiya abakinsu, soyayakam shida matarsa sai abinda yay gaba, hakama danginsa kowa sonsa yakeyi tamkar ya goyasa musamman mama da kawu kabiru, ga abokaimadai hakane, abokai gareshi tamkar tsiya, shikansa yana mamakin wasuma a ina ya sansu?, 6angaren kasuwarsa saidai godiyar ALLAH, kullum k'ara cigaba yakeyi, yabud'e babban super market akasuwa, komai kashiga zaka samu awajen, tundaga suturu akwai 6angarensu, kayan kwalliya, kayan mak'ulashe, kayan abinci, kayan d'inki, kayan wuta, kai harsu wayoyi dukzaka samu, ya bunk'asa sosai, gashi yabuga musu wani k'aton gida na garari mai 6angare buyu, tuni Lubna tarud'e da tambayar d'ayan 6angaren nawaye?.
Ya ce, "mata na yarane, idan sunyi girma can zasu koma, hankalinta yad'an kwanta amma ba sosaiba Dan bata yarda dashiba ko kad'an.
Rayuwadai ta shud'a sosai, hargasu Asma'u sun kammala karatu na tsawon shekara uku, tafito da result mai k'yau, masha ALLAHU Asma'u tazama cikakkiyar budurwa mai kimanin shekaru 22 Aduniya, har yanzu bata kula kowa wai tana jiran Zayyan, amma k'ark'ashin ranta tana mak'ale da son ya Umar har yanzu dan dai babu yanda zatayine, ayanzuma ganin take yamata nisa fintin kau danya zama babban mai kud'i matashin maiji da kansa, tako ina ya Umar yagama had'ewa gashi da d'abi'u irin na manya wad'anda suke matuk'ar k'ara masa kwarjini a idon jama'a.
Ayanzukam bak'aramin bud'ema Asma'u wuta su inna sukayiba akan ta fidda miji, hankalinta yakai k'ololuwar tashi, idan tana kuka saidai su Fatee suyita lallashinta da bata baki.
Ana cikin haka saiga Zayyan tamkar an jehoshi, Asma'u tayi farinciki mai yawa, amma daga baya tayi kuka harya kaita ga kwanciya asibiti saka makon maganar da Zayyan yazo mata dashi mai ratsa zuciya.
Lokacin da Zayyan yazo Asma'u tafito bayan ya aika kiranta, batayi zaton shibane Dan haka tafito cikin fushi, yayinda tayi tozali da Zayyan yaci wani uban wanka yana jingine da motarsa saita rikice Dan farinciki, cikeda zumud'i tak'araso garesa tana fad'in zayyan da gsk Kaine?, kokuwa mafarkin Dana saba yine?.
Zayyan yad'ago yana kallonta babu yabo babu fallasa, tun anan jikin Asma'u yayi sanyi Dan ganin halin ko in kula da Zayyan ya nuna agareta, jiki a sanyaye tace sannu da zuwa, bai amsaba amma yamik'a mata IV.
Cikeda mamaki ta amsa tanamai Kallonsa, tayi k'arfin halin fad'in zayyan wannanfa?.
Yatsine fuska yayi ya ce, "IV d'in aurenane nanda kwana 30 kacal, kiyi hak'uri tunda natafi ban sake nemankiba, wlhy nayi gamon katarne da tsaleliyar budurwa a can yayin karatuna, gata 'Yar masu kud'i, ke idai tak'aice miki ta kereki a komai na rayuwa, tun shekara uku dasuka wuce nadawo k'asarnan ALLAH bai bani ikon zuwaba saiyau, naga kuma bai daceba ace ansha bikina baki saniba shiyasa nakawo miki katin gayyata, nabarki lfy...
Yana gama fad'a yashige motarsa yabar anguwar tareda bud'a mata k'asa.
Ai Asma'u saikawai tayanke jiki tafad'i, ya Umar ne dayazo gaida inna yaganta kwance ak'ofar gida, da farko masifa yafara mata amma dayaga bata koda motsi sai tsoro yakamasa, yagirgizata amma shiru kakeji, anahaka saiga baba dasu hasiya, arikice suma suke tambayar lfy kuwa?.
Nima wlhy baba ban saniba, a haka na Tatar da ita, dasukaga magana bazata musuba suka kwasheta sai asibitinsu Dr jafar.
Natak'aita muku zance saida Asma'u tayi kwanta biyu assume sannan ta farfad'o, tashin hankali kuwa ba'a maganarsa wajen family d'inta.
Bayan kamar sati d'aya Asma'u tadawo daidai aka tambayeta sanadi?, tafad'i yanda sukayi da Zayyan.
Ransu inna ya6aci matuk'a harya kai ga inna tasamu ciwon hawan jini itama, ga Asma'u jikinta yak'i dad'i yauda lfy gobe babu.
Wannan 6acin ran yasa ya Umar cewa ad'aura masa aure da Asma'u kafin ranar d'aurin Auren Zayyan.
Kowa yayi na'am da wannan batu a family, Dan haka bayan kwanta uku da faruwar haka aka d'aura auren Asma'u da ya Umar batareda tasaniba, saidaga bayan shima ba'a fad'a mata mijinba.
____________________
Hummm randa wannan lamari yafaru ya Umar yaga tsantsar tashin hankali agidansa, Dan Lubna tamkar zata kunna musu wuta su k'one, zage-zage da tsine-tsine dangin ya Umar sunshashi, tundaga ranar zaman lfy ya k'aura agidan, bayan kwana Uku Asma'u ta tatare agidan Dan ba'ayi wani shagalin bikiba, amma dukda haka saida abokansa suka shirya musu denner, bayan kawo Asma'u aka halarci wannan denner wadda ta tata hankalin Asma'u dataga waye aka aura mata amatsayin miji na har abada, shin murna zatayi kokuwa bak'inciki?, batada za6in ko d'aya sai aikin kuka a 6oye har aka tashi denner, daganan kowa yakama gabansa, ya Umar Yad'auki Asma'u suka tafi gida, har 6angarenta yarakata, suna shiga yajuyo batareda yace da ita uffanba.
6angaren Lubna yadawo Inda yatarar da shika-shikan bala'i Dan ranar kwana sukayi babu barci harya shashshek'a mata mari biyu, taci kuka sosai tamkar ranta zai fita.
A6angaren Asma'u ma bawai barcin tasamuba, kwana tayi kuka ita kad'ai.
____________________
Tsawon kwana uku Sam babu zaman lafiya agidan Yaya Umar, Lubna ta tada hankalin kowa agidan, adaren kwana na hud'u kuma wani tashin hankalin yazoga ya Umar customs suka rik'e masa kaya babu gaira babu dalili, ya Umar yarasa inda zai saka kansa, yabi duk wata hanyar daya dace kayansa su k'u6ta abin ya gagara, haka ya hak'ura, ba'a k'ulla wataba ranar aka wayi gari kuma wai shagonsa yayi gobara komai ya k'one ba a mori komaiba, wannan tashin hankalin ne yahad'u yayma ya Umar yawa, komai yazo yak'are, har aka koro masa yara daga makaranta, yazo ya saida gidansa, ga kowa ya gujesa ciki harda matarsa Lubna, ammasa k'arfa-k'arfa akan 'ya'yansa, hargashi da tsintar kansa agadon asibiti batareda ya shiryama kansa hakanba.
_______ _______ _____
*_Mun dawo labari_*
Firgigit Asma'u tadawo daga tafiya dogon tunaninta na tsawon shekaru dasuka shud'e abaya, takai dubanta ga agogon dake d'akin karfe 2:47am, idanunta tazaro tana mai mamakin doguwar tafiya datayi atunani batareda tasan dare yayi nisa hakaba, ahankali tasauke idonta akan ya Umar dake barci, fuskarsa tayi fayau, ya k'ara haske dukda kasancewarsa bak'i sosai, yarame sosai sai dogon hanci, tashare hawayen dasuka cika mata fuska sannan tamik'e, bayin dake d'akin tashiga kasancewar ya Umar kad'ai aka kwantar aciki Dan baya buk'atar hayaniya, alwala tayo tazo ta shimfid'a sallaya tayi nafilfilinta tareda karatun alkur'ani mai girma, tayi addu'oin samun lafiya ga mijinta sosai sanan tashafa ta kwanta awajen saman sallayar barci yay awon gaba da ita...........
0 comments:
Post a Comment