Washe gari.
Bayan sallah azahar sir Aliyu ne tsaye a waiting parlourn gidansu yana kallon Hafsat sun rungume juna da sa'ada suna ban kwana,Hafsat kamar tayi kuka sbd sabon datayi agidan dakuma batasan rabuwa da sa'ada.
Mommy ce tazo taja hannun Hafsat tasaka mata wata babbar Leda ahannunta ,hafsat zatayi magana mommy ta rufe mata baki,takalli sir Aliyu dake tsaye yana aikin kallonsu. Tace babana kuje dan Allah ka lallab'ata kaji?
"Yatsina fuska yyi yace haba mommy lallabata d'in me zanyi,ya kalli Hafsat yace oya muje."
"Turo baki tayi tabi bayansa."
Ya shige mota yabarta ,yak'i bud'e mata ,itakuma tak'i shiga sbd yasaba shike bud'e mata duk in zata shiga motarsa.
Shikuwa yana sane yyi hakan Dan yaji haushin yadda ta nuna damuwa kan zata rabu da sa'ada amma shi bata damu dan zasu rabuba.jin shirun yyi yawa yasa yafito ya kalleta fuska daure yace wai bazaki shi ga bane kome kkejira?
Kauda kanta tayi gefe tace cikin shagwaba tonika bud'e mun nashi ga. Kallonta yyi yace keko kin rainani kwa nannan ko? batace komaiba can yabud'e mata sannan ta shiga yaja motar ,saida yabiya yasiya mata su ice cream da ga sassun kaji dasu biscuits da chacoolat,sannan suka wuce anguwarsu.
Bayan yyi parking da sauri ta kai hannunta dan bude k'ofar ta jita yasa lock,shiru tayi dan dama tunda suka shiga motar batayi masa magana dan zama da shi yasa takoyi miskilanci.
Kallonta yyi murya k'asa k'asa yace wato dan zakiga baba ki koma gunsa shine kikemun haka ko?
[26/12, 8:27 pm] +234 703 230 7283: "Ahankali tace nifa ba haka bane bakaine kayita d'aure fuska ba k'ak'i yin dariya."
Kallonta yyi yace to kalleni,ba musu ta kallesa suka had'a ido murmushi yyi,turo baki tayi tace bemunba gsky ka canza wani.dariya yy yace aigarani Nayi murmushi keko murmushin bakiyiba .da sauri tayimasa murmushi har yar wushiryarta ta bayyana,tace to yaya nayimaka bud'e mun,bece komaiba yabud'e mata suka fito.
Dede bakin soron gidan suka had'u da baba da sauri sir Aliyu ya iso gunsa ya duk'a yana gaidashi, ya amsa cikin sakin fuska ,had'e da yimasa godiya da tambayarsa mutanan gida.Hafsat kuwa bayan baba yagama gaisawa da Sir Aliyu da sauri ta rungumesa tana masa shagwaba,shikuwa sir Aliyu se kallonsu yake azuciyarsa yana cewa oh anyi shagwab'ab'b'iyar yarinya.
Babane yace Aliyu inafatan dai bata yi muku wani shirmenba?murmushi sir Aliyu yyi yace ah ah baba .
Baba yace masha Allah ,azuciyarsa kuwa ca yake kaga yaro kamar balarabe ko bature ai ban dauka yanajin hausaba.
Sir Aliyu ne yakatsewa baba tunani gun cewa ni xan wuce baba sai munyi waya,da fara,a baba yace to Aliyu bazaka shiga ciki ba? Murmushi yyi yace zanshiga wani lokacin ,har mota baba yarakasa yana sa masa Albarka da yimasa godiya, sannan yadawo yasami Hafsat tsaye zaure yace muje ciki ko,ahankali tace lah baba na mance kayana amotarsa bara naje na d'auko.
"Nan ta wuce ,baba yashiga ciki."
Tana zuwa tasame sa cikin motar yad'ora goshinsa kan sitiyarin motar,ahankali tace yayanah nagode sosae Allah yabar zumunci Allah... Da sauri yadago yace ya,isa haka my Hafsat kinji bbu godiya atsakanun mu ko aike k'anwatace ko?
Murmushi tayi tace eh hakane wlh yaya dakai da familyn ka kunada kirki sosai amma mommy duk ta fiku kirki tafad'a hade da yimasa gwalo taja ledar tsarabarta ta gudu.
Dariya yyi yace haba yarinya zamu hadu askul nanda 5days,yafada had'e da Jan motar yabar anguwar da kewar Hafsat aransa.
Hafsat nashi ga gida tayi sallama Laure dake tsakar gida tayi salati had'e da cewa oh ni duniya ,ainad'auka gun yawan karuwancin zaki tabbata ,wlh anji haushi waya sani koma ciki yyimiki kuka je aka zubar shiyasa kika kwana biyu gunsa to allah yatoni asirinku,kuma deeni ma yayafeki ko kyauta aka bashike bazai karba kina kingin wani dan Wannan ba aurenki zaiyiba saidai ya lalataki.
Hafsat hawaye ne ke ta zuba akumatunta ,tanajin zafin maganganun Laure.
Babane ya fito afusace sbd yagaji da jin irin kalaman da Laure ke alak'anta Hafsat dasuba,beyi wata wataba ya wanke Laure da maruka2 lafiyayyu yanunata da yatsa yace wlh kinci albarkacin Hafsat dan inna rabu dake bbu dacewa in zauna dagani sai itada k'annantaba,da tuni na dad'e da rabuwa dake,amma inaso ki rubuta ki aje duk ranar danaga matata to wlh aranar zamana dake yak'are ,yafad'a azafafe tare da kallon Hafsat yace muje.
Su Laure saikaji tsit baki yamutu tana matsar hawayen munafunci.
Ko ad'aki baba yyita rarrashin Hafsat har tayi shiru ,tahaubasa labarin gidansu sir Aliyu da kirkinsu,kuma baba yaji Dadi sosai ,be fitaba saida aka kira la'asar sannan yace bara yaje yyi sallah .
Bayan ya fita ita Hafsat tayi tata sallar .
Bayan ta idar ba jimawa ,taji sallamar Fatima,nan tashigo d'akin,had'e rai Hafsat ta yi, tayima kamar bata gantaba.
Murmushi Fatima ta yi tace ayya sis dan Allah kiyimun uxuri kiji bayanina dan Allah ba fushi zakiyi daniba.
Harararta Hafsat ta yi tace hmm aini kin bani mamaki ace duk yadda muke dake har kije wani gun bansaniba.
Da sauri Fatima ta ce yi hakuri sis wlh dawiwarmu kenan,nace bari nazo na goge laifina.
Kinsan mahaifiyar ummanmu bata lfy tana asibitin abuja,to jikinta yyi tsanani,shine aka kira umma taxo 'sainabita da harda yaya Ahmed zamuje dan yazo gaidasu umma yatarar zamuje to sai daddy yace ah ah yazauna tunda shi angone shine Muka barsa gida mukatafi.
Ajiyar zuciya Hafsat ta yi tace ayya sis allah yabata lfy yanzun yajikin nata?
Fatima ta ce da sauki sosae
Nan Hafsat ta labar tawa Fatima abinda yafaru tsakaninta da deeni dakuma zuwanta gidansu sir Aliyu.
Sosai Fatima ta yi murna da yadda sir Aliyu yyi maganin deeni,sannan tak'ara
Yarda aranta cewa sir Aliyu yanason Hafsat.
Nan Hafsat ta nuna mata tsarabarta da mommyn sir Aliyu tabata da abinda sir Aliyu yasiya mata,nanta tayata murna ,suka raba kayan har Fatima tak'i karb'a amma ganin yadda Hafsat ta ji haushi yasa ta karba kasancewar komai suka samu tare suke rabawa.
Har soro Hafsat ta rako Fatima dazata tafi gida ,harta Fatima ta fita tadawo tace sis saurafa 5 days mukoma skul kizama cikin shiri.
Murmushi Hafsat ta yi tace eh ai nasani Allah yakaimu, Fatima ta ce ameen tareda tafiya,Hafsat takoma ciki.
Bayan kwana biyu....NIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story & written by mmn fareesa
🅿73&74
Bayan kwana biyu.
Gaba daya shire shiren komawa suke skul,baba yayiwa Hafsat siyayyar komai,itama tagama shirinta gobe sai skul.
Yanzun haka Hafsat ce zaune a d'akin ta suna fira da babanta,amma hankalinta baya gun firan sotake ta karb'i wayarsa takira sir Aliyu su gaisa rabon ta dashi tun ranar da ya maidota gida.
"Can wata dubara ta fad'oma ta."
Da sauri tace baba bani wayarka zanyi wani lissafi!bbu musu yabata tareda cewa Nina fita dan ukku tayi ankusa la'asar,inna dawo na karba.
"Ahankali tace to baba adawo lfy nan yafita .Hafsat cikin zumud'i ta shiga cikin contacts, cikin sa'a taga bbu number sir Aliyu. Shiru tayi,can kuma tashiga receive call ta duba rana da lokaci Atake tagane number dukda ba suna.";;
Atake tasaka kira,harta tsinke ba'a d'agaba,turo baki tayi cikin jin haushi kamar agabansa take,kawai taji wayar na ringing tana dubawa taga shine yakira,saida takusa tsinkewa ta d'aga batare da tayi magana ba.cikin girmama wa sir Aliyu yyi sallama had'e da cewa baba barka da rana,murmushi Hafsat ta yi me sauti atake yagane itace,cikin zumudi yace my Hafsat kece? Wani murmushin tasakeyi tace nice yayanah,kaga nadamu dakai ko amma kai baka damu dani ba gashi Nina fara kiranka.
" cikin marairai cewa had'e da rarrashi yace ayya my Hafsat bahaka bane, wlh inason muyi waya amma inajin nauyin cewa baba yabaki ne shiyasa,amma yanzun kin hakura?"
"Kamar yana ganinta ta d'aga kai had'e da cewa eh."
Murmushi yyi yace to nagode ai nasan kinada hakuri da sauri yafiya,amma kina yawan tunanina?
Yar dariya tayi tace ah ah.
Had'e rai yyi yace to shikenan tunda ma bakya tunani,nima zan dena tunaninki.
Cikin shagwaba ta ce, yaya dan Allah kada kadena tunani na nafison koda yaushe ina cikin ranka.
Lumshe idanunsa yyi yajin dadin sweet voice dinta hade da kalamanta.
"Ahankali yace um um kema ai bakya tuna ni ."
Dasauri tace ah ah wlh ina tunaka namaka dubarane dan inji kana tunani,shiyasa,ammafa ko yanxunfa tunanunka nikeyi ,nayiwa baba dubara na karbe wayarsa nakiraka.
Murmushi yyi yace Allah tawan.
Lumshe ido tayi tace eh mana,yanzun kana ina ?yace ina part dina, tace inasu mommy da sa'ada ?
Murmushi yyi yace sunyi kewarki sosai,dariya tayi tace nima haka.
Murya k'asa k'asa yace gobe sai skul ko?turo baki tayi tace eh yaya ni banso in koma gobe nafiso sai next week murmushi yyi yace gobe insha Allah zaki koma skul.mur gud'a baki tayi tace to sai anjima, dasauri yace kingaji da magana danine? Ahankali tace ah ah kawai dai banso baba yasameni ina waya Bacin ban fada masa ba.ajiyar zuciya yyi yace hmm wata ta koma mak'aryaciya ko?
Cikin shagwaba ta ce allah niba mak'aryaciya bace ni munbata dakai.
Dariya yyi yace dama rannan kinmun gwalo ko? To zamu hadu askul gobe saina saka mlm rabe yabani dorina na zabeki.cik in kukan shagwaba ta hau basa hkuri,shikuwa jin tana hakan yyi saurin k'ashe wayar sbd wani yanayi da bak'on al'amari da ya tsinci kansa aciki.ita kuwa Hafsat ta dauka da gaske yake tunda har yakashe kiran duk saita ji tsoron komawa skul gobe duk da wata zuciyar nacewa wasa yake miki.
Washe gari da misalin karfe 4:00harsu Hafsat sungama shirinsu ,baba yyi mata nasiha akan takulada kanta tayi kuma karatu tunda Wannan ce shekararsu ta karshe dazasuyi askul.har yan hawaye saida ta yi,Laure na kallabta tana tab'e baki had'e da hararanta,sarai Hafsat ta lura da ita tadai nuna kamar bata gani ba, kallon su hanifa da shamsu kannanta tayi tace suxo sutayata d'aukar kaya,kallonsu Laure kawai tayi suka gane meta ke nufi. Atake sukak'i zuwa ,baba da agabansa akayi ya kallesu yace kuje kutayata dauka ko ranku yab'aci,ganin ba wasa afuskarsa yasa sum sum suka bita, suna tayata.awaje taga Fatima da driver,nan akasaka komai aboot suka dauki hanyar skul dinsu.
****************
6angaren sir Aliyu kuwa, mommy ta yi masa miyar kaji da danbun naman rago had'e da provision tace yakaiwa Hafsat a skul.
Sir Aliyu yyi Dadi sosai yyi farin ciki da yadda mahaifiyarsa ke nuna k'auna da tausayawa ga Hafsat.
Haka yaci wankan sa,cikin kananun kaya, sai k'amshi yake,abin sai Wanda yagani yaja motarsa sai skul.
Koda ya isa, office dinsa ya bude yashiga ya zauna aciki,yabar windows abud'e dan yana hangen get dg office dinsa.
"Yafison da Hafsat ta dawo yaganta."
Befi15minit ba yahango Hafsat cikin pink checks na doguwar Riga idanunta sunyi d'an ja alamar tayi kuka kenan.
"Azuciyarsa yace yah salam me tayiwa kuka ne?"
Hangowa yyi sun gama shigowa da kayansu Fatima ta saka ana dauka ana kaimusu daki,su kuma sun biyo bayan su.
"""""Hafsat ta saci kallon office din sir Aliyu taganshi abude, kallon Fatima ta yi tace sis xomuje gun sir naga office insa abud'e yake!da sauri Fatima ta ce ah ah sis kedai kije bari ni naje najere mana kayanmu a laka.Hafsat tace ba damuwa,nan tanufi office din Sir Aliyu. Shikuwa yana hangota yafito dan bayason yawan ke b'ewa da ita dan gudun ajimasu wani zato.
Tana ganinsa ta tsaya,shikuwa kafeta yyi da mayun idanunsa yana kallonta, murya k'asa k'asa yace waya samun ke kuka gayamun kinji tawan?
Sunku yadda kanta k'asa tayi tace ba kowa kawaidai banson in rabu da babana.
Murmushi sir Aliyu yyi yace kada kidamu zan rik'a kira miki shi kuna gaisawa.
Murmushi tayi had'e da kallon sa tace yauwa yaya nagode sosae, harnaji Dadi wlh.
Murmushi yyi yace nima har naji Dadi da kika kasance cikin jin Dadi.
" ahankali yace ga kayanki can a office da mommy ta bani nakawomiki."
d'an zaro ido tayi tace oh wai yaya mommy bata gajiya da yimun hidima ai d'awainiyar tayi yawa dan Allah.
"Ahankali yace kada kidamu mommy haka take."
Nan yaje yad'auko mata kayan tayita masa godiya sukayi sallama, ta nufi hostel shikuma ya nufi step quarters.
________________
WAIWAYE.....
Mahaifiyar Hafsat tunda mlm aminu yasaketa yakwace y'arsa tarasa ina zata gashi batada ko sisi Balle ta tafi gombe garinsu,kuma rabontada garin tun sadda mlm amunu yadauko ta dg can yakawota Kaduna ko labarinsu bataji.haka tarik'a tafiya cikin bak'in ciki da b'acin rai. Bata auneba taji mota ta bangajeta ta fadi daga nan bata sake sanin inda kanta yakeba.
Shikuwa Alh suleman rabo wato mahaifin sir Aliyu da yabanketa,hankali tashe yyi hospital da ita.
Babu bata lokaci akayi emergency da ita.
Bayan awa3 wani doctor yafito yakalli alh suleman yace muje office dina inason magana dakai.
Bayan sun zauna doctor yyi ajiyar zuciya yace a gsky akwai matsala
"Da Sauri alh suleman yace tame?"
Doctor yace gsky brain d'inta tasami matsala dan kota farka bazata dawo hayya cintaba sbd brain dinta ta bugu sosai,saidai bazata dauwama ahaka ba ah ah zamu azata kan magani har Allah yasa ta warke brain dinta ta dawo normal.
Innalillahi wa inna ilaihir raju un kawai alh Suleiman yake maimai tawa.
Cikin tashin hankali yace wlh doctor bansantaba kuma da alama cikin damuwa take na kad'eta.
Amma bara naje nasanarwa da mata ta sainadawo.
Doctor yace babu damuwa."
Babu jimawa alh Suleiman yadawo da hjy Aisha ,kasancewarta mace mai fahimta ,ta fahimci komai takuma tausayawa marar lafiyar.
Saida tayi kusan wata daya a hospital sannan aka sallah meta,suka koma gida gashi ko magana batayi,mai aiki hjy Aisha ta dauka tana kula da ita.
Akuma lokacin sir Aliyu baya kasar yana karatu dashida kabeer.
sa'ada ce sai sadeek ita sa'ada alokacin tana yar8years shikuwa sadeek yana 13years duk da bawani lura suke da abinda ke faruwaba kasancewar part daban ake jinyarta.
Da alh Suleiman yaga har tayi shekara gashi bbu sauk'i kuma ba asamu danginta ba sai yaturata kasar waje yadauki wadda za ta je jinyarta.
Har akayi shekara 4tana can bbu sauki dai ga kuma lokacin har sir Aliyu yadawo yagama degree dinsa na biyu,kuma su mommy sun labarta masa abinda yafaru saidai betaba zuwa dubata ba saidai daddy ke xuwa duk karshen month.
Ko lokacin da Hafsat ta zo gidan baya kasar yanacan dubata.
Cigaban labarin...
Share plsNIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story & written by mmn fareesa
🅿75&76
cigaban labarin
Bayan Hafsat ta koma d'aki tasami har Fatima ta je re musu komai a laka.
Nan ta nuna mata kayan da mommyn sir Aliyu ta bata.
"Fatima tayi murna sosai da godiya, sannan suka sake shirya kayan ."
Washe gari byan sun dawo dg class Hafsat suna daki wata mate dinsu tazo tace mata sir Aliyu yana kiranta,bbu bata lokaci ta saka hijab ta fita.
"" tana fita dg get din area hostel ta gansa atsaye yyiwa hanyar kuri da ido alamar ita yake ji ra."ahankali ta isa gunsa,bayan sun gaisa ta kallesa taga kamar yana cikin damuwa.murya asark'e tace yaya naaaaaaaa! kallonta yyi da idanunsa dasuka fara ja ,murya k'asa k'asa yace I'm sorry to say Hafsat yanxun daddy nah yakirani kan naje Lagos zanyi 7or8days nakula da kayansa dake can shi aiki yyi masa yawa.nadamu sosai wlh nafison ina acikin skul din nan akoda yaushe ina kula dake ,amma kiyi hakuri kinji,yafad'a cikin damuwa.
"Ahankali Hafsat tace pls yaya kamayar dani gd inkadawo nadawo."
Girgiza kansa yyi yace hakan ba zai yuyuba my Hafsat karatunfa?
Turo baki tayi hade da fashewa da kuka!ai gaba d'aya saita rikitasa co's yatsani yaga tana kuka.
"cikin rarrashi yace haba mana pls kiyi shiru da me kikeso naji ne da kukanki ko da zafin rabuwarmu?"
Yi shiru kinji Hafsat dina goge hawayanki kimun mgn ko zanji dad'i.
Da sauri ta goge hawayenta ,tana kallonsa,tace nadena amma yaya wlh baxanji dadin skul din nan ba inbakanan.
Cikin rarrashi yace ai bazan dad'eba yafad'a had'e da mik'a mata keys yace gashi na office dinane nasa anmiki daya ni daya,duk sadda kika tunani kije kibud'e ki gyaramun kinji tawan?
Karba tayi ta lumshe idanunta had'e da waresu a fuskarsa ,tace to shikenan nagode.
Kallonta yyi yace kimun alk'awari bazakiyi ta kukannanba,
"Ahankali tace baxanyiba insha Allah zan dunga yima ka addua Allah yasa kadawo lfy".
Murmushi yyi yace yauwa kokefa tawan har naji Dadi wlh, muje ma kirakani get.
" ba musu ta bisa sukajera suna tafiya cike da burgewa da sha'awa."
Ahanyane yace my Hafsat zan dunga kiran mlm rabe yana banike muna gaisawa kinji ,kuma nabada not kuyi innadawo zanyi explanation.
"Ahankali tace to yaya nah,amma zanyi missing dinka sosai,kallonta yyi yace nima haka my Hafsat nunawa ne kawai banayi,amma me kikeso nasiya miki pls kinji tawan kada kice ah ah kifad'amun ?
Da Saudi tace duk abinda kaga yadace dani kasiyamun zanyi murna dashi,tafad'a had'e da tsayawa kasancewar sunzo bakin get gun motarsa.
Bud'e motar yyi had'e da kafeta da lumsassun idanunsa yace zantafi zo kimun addua.
Ba musu tazo gab dashi tayimasa,ta kallesa hawaye na zuba murya na rawa tace yaya ka kulamun da kanka sannan kaji tsoron Allah aduk inda kake kaji?
Yah salam yafada azuciyarsa ganin batadena hawayeba,ahankali yace insha Allah tawan matso kiji ba musu ta Dan matso yarad'a mata wata magana wadda nikaina banji komai yace ba sbd yyi maganar k'asa k'asa. Da sauri Hafsat ta fashe da dariya tana kallonsa tanacewa allah yaya,shima dariyar yake yi yace eh mana,murmushi tayi tace to shikuma kaje kada kayi latti.ba musu yashiga hade da Jan motar ,Hafsat dake tsaye tarika daga masa hannu harya fita get ta nufo hostel cike da kewar sir Aliyu.
Bayan ta dawone take labartawa Fatima sir baya gari yayitafiya ,Fatima tace allah yadawo miki dashi lfy dan wlh sis ko kiso ko kada kiso keda sir Aliyu kunason juna sbd alamomi sun nuna hakan.
Harararta Hafsat ta yi tace gsky sis ba kanki dayaba,malaminane.
Fatima tace hmm allah yabamu rai da lfy ko Ku menene amma dai kuna son juna.
Hafsat bata sake cewa komaiba ,amma maganar ta tsayamata arai da tunanin maganar ta kwana.
Washe gari haka ta yini sukuku,jira kawai take taga mlm rabe yakirata yace ga sir Aliyu yakira su gaisa amma shiru har dare.
*****************
Bayan kwana4 yakama sir Aliyu lwamansa 5da tafiya Lagos,Hafsat ce zaune a bed dinta tanata tunanin sir Aliyu, kodai ba lfy har yanzun shiru be kirataba.tunawa tayi da keys d'in da yabata da sauri taje ta d'auko taja Fatima suka wuce office dinsa,bayan sun bud'e suka shiga,suna shiga Hafsat ta ji gaba d'aya office din k'amshin sa yakeyi,jitarik'ayi kamar zata gansa ,duk abin nan Fatima na lura da ita sbd itama tayi nisa asonAl-ameen dinta dan jitake in akarabasu zata iya rasa ranta,Hafsat ce ta katse mata tunani da cewa sis ki gyara office nikuma na gyara bed room,ok Fatima ta ce ta koma office Hafsat ta cigaba da gyara bed room din cike da tunanin sir Aliyu had'e da kewarsa.
"Bayan sun gamasuka fito,Hafsat ji take kamar karta fito."
Nan suka koma hostel abinsu.
Bangaren sir Aliyu kuwa da gangan yak'i kiran Hafsat dan acewarsa soyake yagwada zuciyarsa kozai iya yin wasu kwanaki beji muryarta ba ko be ganta,sbd yasan SSCE zatayi ba jimawa dole yabar ganinta kullum,dan aganinsa yyi mugun sabo dakuma shak'uwa da ita, amma me?adaddafe yyi5days yaji bazai iya jurewaba sannan ga yawan mafarkinta dayake yawan yi,dan jiya da kyar yyi bacci sbd tunaninta,bbu shiri yakira mlm rabe yace yaje yabata wayar zai kira ne yabata wani sak'o bbu musu mlm rabe yace to nan yanufi hostel dan kiran Hafsat.
Hafsat kuwa dawowarsu kenan daga gyarama sir Aliyu office mlm rabe ya Aiko tazo,da sauri ta fita dan ranta yabata sir Aliyu ne keson magana da ita away a.
Tana isa taga mlm rabe tsaye bayan sun gaisa yace mata dama gashi yanzun mlm Aliyu zai kira suyi magana .
Nanta karb'a tadan matsa bayan staffroom, nanko wayar tayi ringing saida ta k'osa tsinkewa ta d'aga shikuwa bawan Allah jin ta d'aga wayar yyi wata ajiyar zuciya dabesan yyiba.
Hafsat najin haka tasaki kukan shagwaba kamar tana agabansa.
Shikuwa gaba daya ta susutashi da shagwaba rta,lumshe idanunsa yyi murya k'asa k'asa yace I'm sorry kinji yi shiru kifada mun me kikewa rigima ne?
Cikin turo baki tace bakaineba tunda ka tafi baka kiraba sai yanzun meyasa kayi hakan?
Cikin wata kasalallar murya yace my Hafsat bahaka bane wayana ta fadi saida na canxa layi Nayi welcome back shiyasa .
Murmushi tayi tace to nayarda bakada laifi to ina wuni?
Murmushi yyi dan yalura akwai k'uruciya da yarinta atare da ita,lfy ykk ya karatu?
Ahankali tace alhmdllh.
Nandai sukayi ta fira daga karshe sukayi sallama,taje taba mlm rabe wayarsa ta koma daki cike da farinciki.
____________________
Bari mu lekasu kamal muji awane babin suke........
Share plsNIDA D'ALIBATA
Story & written by mmn fareesa
🅿77&78
Bari mu lek'asu kamal muji awanne babi suke..
"" zazzaune suke bayan sun gama shan aiki sun gaji",kamal dake tsakiyarsu kallo daya zaka masa kasan yaji jiki duk yarame yyi bak'i sbd wahalar dasuke sha shi ne yyi gyaran murya yace wlh wlh naga rayuwa kuma na yarda duniya makaranta ce ,lallai xuwana gidan jarin nakoyi darasi.insha Allah aka sakemu zanje har gun mlm Aliyu na rok'i yafiyarsa dakuma yarinyarnan hafsat.
d'ayan dake gefensa yace nima haka na shiryu dama Kaine oganmu kuma ka shiryu,dayan dke gefe yace nima haka amma kai kamar basunsaka anbata maka ta karduba? Kamal yace eh Wannan ba matsala bane sbd abbana kamfaninsa yaso na zama manager amma naki na nuna ni sai teaching zanyi ,amma inmunfito zanje narok'esa gafara yamayardani a camfaninsa.baki dayansu sukace ameen Allah yashiryu masu Hali irin namu.
Bangaren su hafsat kuwa sundage da karatu ,kuma tunanin sir Aliyu yana nan dank'are axuciyarta,yanzun haka tunaninsa take tana tunanin yau ko gobe zai dawo.shiru tayi can kuma sai takama kuka sakamakon mahaifiyarta data rasa ina take tana Raye kota mutu? Fatima ce taji kukanta ta taso tana tambayarta lfy?nan cikin kuka tace mamana sis bansan inatakeba banson kowa nata ba yazanyi da rayuwata? Ahankali Fatima ta ce kada kidamu Allah yana tare da mai hakuri kuma duk tsanani yana tare da sauk'i ki dage kiciga ba dak'ara addu a insha allah za'a ganta dan inajin hakan ajikina kinji da haka dai Fatima ta rarrasheta da irin Wannan nasihar har tayi shiru.
**************
Sir Aliyu ne tsaye gaban mirror yana taje sumar kansa yyi wani kyau na musammun ,sai sauri yake sbd dawowarsa kenan dg Lagos yanaso yaje yaga hafsat dan bazai iya kwana be gantaba.
Yana gama kimtsawa yafito awaiting parlour yasami mommy zaune tana ganinsa tace baba ga abincinka can dining yana jiranka.
"Ahankali yace mommy na k'oshi".
Da sauri yyi waje ,murmushi mommy ta yi afili tace hmm tunda kana zumudin kaje kaga hafsat ai bazaka tsaya cin abincin.
" Sir Aliyu be tsaya ko inaba sai skul dinsu hafsat ko office be budeba straight area hostel yanufa."
Cikin sa'a Fatima zata skul shop ta hangosa ya nufo nan ,danshi bema lura da ita ba ,ai dagudu ta koma ta kaiwa hafsat labari.
Da gudu hafsat ta fito dan murna tanufi get ,tana fita get sir Aliyu yana kawowa zai shiga saura kad'an hafsat ta fad'a ajikinsa.
Cikin murna had'e da farincikin ganin juna suka tsurawa juna ido suna kallo ko k'iftawa bbu.
"Ahankali sir Aliyu yace my Hafsat nasameki lfy?"
Lumshe idanunta tayi tace lfy lau Yayana Nayi kewarka da yawa .
Murmushi yyi yace nima haka, amma ai gashi nadawo kinga mahakurci mawadaci ko?
Ahankali tace eh,inasu mommy da sa,ada ?
Murmushi yyi yace wato ni ba'a wani tambayata yanike ko wani abu saidai ki tambayi su mommy da sa'ada ko?
Marairaicewa tayi tace lah yaya ba haka bane ,ba yanzun nace Nayi kewarka ba kuma kasan ai nadamu dakai, amma tunda ma kishi kake dasu mommy da sa'ada shikenan ,zandunga yin mafarkinsu sai murika gaisawa cikin mafarki ko?
Yatsina fuska yyi yace eh naji ,ni kingama tafiyata ,murgud'a masa baki tayi had'e da masa gwalo .
Murmushi yyi nidaiko ?yanzun nazo shine kkemun haka ,kinsan dama inatara laifukanki ko gashi yanzun kin sake ,gobe zankarbi bulala gun mlm rabe na zaneki da ita.
Cikin shagwaba hade da marairacewa tahau basa hkuri,shikuwa kamar gaske sai yawani sake d'aure fuska, shi adole da gaske yake.
Ai tuni hafsat ta rud'e tafara zare ido dan ta dauka da gaske yake.
Shikuwa dama haka yake so sbd hafsat tafi masa kyau a haka in tana atsorace,shagala yyi da kallonta harta lura ga murmushi kwance a fuskarsa.
Turo baki tayi ta kafesa da ido tana kallo,cikin shagwaba tace shine ka tsoratani ko?
Murmushi yyi yace hafsat dina kenan aikinfi kyau ahakan ne shiyasa na tsorataki.
Yar dariya tayi tace yaya kaje kayi aski duk wannan kasumbar ta ragemaka kyau kaje agyara maka .
Murmushi yyi dayaji tace tarage masa kyau wato hafsat ta na ganin kyawunsa kenan,kallonta yyi yace to my Hafsat duk abinda kikeso shi za'ayi kinaso insaka a askemun ita duka?
Da sauri tace ah ah anbar sajenka kafumun kyau ahakan kawai dai agyaramaka naga duk fuskar ta cika.
Murmushi yyi yace hmm garin ne banyarda damasu gyaran fuskansu ,nabari sai nazo nan nagyara da kaina,kuma dawowata kenan nace sainazo naganki.
Murmushi tayi mai sauti tace hakane yaya nah wlh kana ji dani sosai nagode .
Ahankali yace kada kidamu kinfi haka aguna ,abinda nikeso dake ki maida hankali kiyi karatu kinga final year kuke kinjiko?
Ahankali tace insha Allah ,kallonta yyi yace ni zan wuce maraice yyi ,kije kiyi alwalla kiyi zikiri kafin magarib.
Ba musu ta ce to yaya jagaidamun dasu mommy.
Kallonta yyi yace nak'i bake kikace zaku gaisaba amafarki ,murmushi tayi tace eh ai namantane,batajira amsarsaba tayi cikin area hostel.
Shikuwa yar dariya yyi yawuce get yadauki motarsa yanufi gida.
_________________
Haka rayuwa taci gaba da kasan cewa ,inda shakuwa mai karfi ta sake shiga tsakani Sir Aliyu da Hafsat dakuma tsanani son junansu inda har yanzun bbu Wanda yasan yana son dan uwansa dan duk atunaninsu shakuwa ce sukayi da juna.
Kwanci tashi bbu wuya gun uban giji harsu hafsat sun kammala exams dinsu ta first term anbasu Hutu yau sun nifo gida cike da murna dukda wani gefen na zuciyar hafsat batason rabuwa da yayanta wato sir Aliyu dukda yace zai dinga xuwa yana kawo mata Sa,ada.
Washe garin dasuka koma gida Hutu Yakama satday ne ,tun safe hafsat ta keta aikatuwa kasancewar baba yana kasuwa gun aikinsa dan in gabansane bazai bariba yanzun haka uban wanki ne tasha na Laure da yaranta,ta zauna tana hutawa baba yashigo da ledar fura guda biyu hafsat daya Laure da yaranta daya .
Bayan hafsat ta yi masa sannu da zuwa yabata ya nufi dakinsa,bbu jima aka Aiko wai wasu mutane nayin sallama da Mlm aminu.
A k'ofar gida kuwa alh Suleiman rabone wato senator da body guards d'insa, governor yaturasa a anguwanni yasami me anguwa yaji matsalolin anguwarsa,shine suka shigo nan anguwar kasancewar gidan mlm aminu ne bakin hanya kuma farkon layin hakan yasa senator yace sutsaya nan akira me gidan yyimusu magana da mai anguwar ,anguwai.
Cikin gida kuwa mlm aminu yyi mamakin kiransa ,hakadai yafita dan ganin masu nemansa.
Yana zuwa da mamaki yakalli senator mutumin da sai a tb yake ganinsa ko ajarida amma shine k'ofar gidan sa allah yasa lfy .
Senator da yalura mlm aminu yadan tsorata daganinsu k'ofar gidan sa,nan yasaka akayima mlm aminu bayanin dalilin zuwansu.
Nan mlm.aminu yakawo gaisuwa gun senator tare da cewa bari akawo ta barma sai yaje yataho damai anguwa.
Nan yashiga ciki yadauko tabarmi,Laure na tambayarsa lfy?
Yace yyi bak'i ne k'ofar gida,bejira amsartaba yafita.
Shewa tayi dan dama sotake yafita ta kwace furar da hafsat ke damawa suhad'a da tasu itada y'ayanta su sha.
Yana fita tahau tsinewa hafsat ta karbe furar tace kuma in ta sanar da baba sai tajama ta Sharrin dahar ta mutu bata mantawa,sannan ta jefeta da bucket tace taje ta d'ebo mata ruwa.
Bbu musu hafsat ta dauka tana kuka tasaka hijab har kasa ta fito da bucket a hannunta.
Ak'ofar gida kuwa baba bayan ya shinfida musu tabarma sun zauna bbu wulakanci ko k'yama ,mutum daya yabisa dan kiran me anguwa,yabarsu senator zaune nan gun.
Hafsat na fitowa ta tsaya asoro tana goge hawayanta dan ta lura da mutane awaje.
Senator dake zaune yana fessin k'ofar gidan yana kallon Wanda ke zaure,a idonsa yaga hafsat tana hawaye yaga kuma ta goge su ka kakaro murmushi kamar batayiba ta na niyar fitowa da bucket a hannunta.
Tana fitowa ya gansu da sauri ta xube k'asa ta gaidasu ta tafiyarta.
Shikuwa senator se yaji yarinyar taba sa tausayi dan yalura tanada damuwa amma ta boye aranta sannan kuma uwa uba tanada kamun kai da tarbiyya,atake wani abu yad'arsu aransa.
Akuma lokacin mlm aminu yadawo da mai anguwa,bbu bata lokaci sukayi magana da senator akan abinda yakawosu.
Bayan sun gama magana senator, yacewa yaransa suje sujirasa ,yakira mlm aminu kasancewar dazasuyi magana da mai anguwa yabasu wuri.
Bayan mlm.aminu yazo senator yakallesa yace ...
Share pls[12/30, 9:37 AM] Ikhty Hafsat: NIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story & written by mmn fareesa
🅿79&80
"Bayan mlm aminu yazo senator yakallesa yace dalilin dayasa na kiraka shine inason inyimaka tambaya2 dan Allah inkabani dama?" Cikin mamakinsa mlm aminu yace to y'allab'ai ina sauraronka, senator yace na farko !wata yarinya nagani ta fito da bucket y'arkace?mlm aminu yace eh y'ata ce,senator yacigaba da cewa anyimata miji?mlm aminu yace ah ah gsky.
Senator yace inbazaka damuba inaso kabani dama na nemawa d'ana aurenta.zaro ido mlm aminu yyi yace gsky y'allabai kafi karfinmu ,mu talakawa ne ,murmushi senator yy yace kada kadamu Dame kud'i da talaka duk Allah yyi su inde zakaba d'ana aurenta bbu matsala. Ajiyar zuciya mlm aminu yyi yace gsky bata gama karatuba yanzun aji6 take a makaranta. Senator yace inna fahimceka befi saura wata 6tagama secondary skul din ta,mlm aminu yace eh hakane.senator yace bbu damuwa intagama sai ya aureta inma zataci gaba sai tayi agidansa.mlm aminu yace to y'allab'ai nagode sosae amma zan tuntubi yarin yar tukum.
"Wani kat senator yamik'a masa yace gashi address dina ne dakuma personal number ta,nabaka dama kaje kayi bincike akanmu dan shi aure yanason bincike sannan duk shawarar daka yanke ka kirani."
Baba yakarb'a yyi masa godiya ,senator yabada rafar yan1000guda2 yace akaiwa baba,amma baba yak'i karba yace suyi hkuri wataran ya karba,bbu yadda basuyiba yak'i karba har sai da senator yace ya karba had'e da cewa ba amaida kyau baya maida kyauta se shaidan sannan ya karba had'e da shigewa gida.
Shikuma senator ya yarda cewa inde sir Aliyu ya auri yarinyar nan to zaiyi suruka ta kirki dan yalura basuda kwad'ayin abin duniya dan inda wanine uban be wani shawara Atake zai yarda.
****************
Bangaren su kamal kuwa har ansakesu sati biyu da suka wuce.har yyi yar kiba haskensa yadawo,kuma iyayansa sunyafemasa yadawo da aiki a camfanin mahaifinsa.
Ayanxun haka tafe yake a motarsa zashi office d'in sir Aliyu dan yaje yyi bincike kansa yaga no office dinsa.
Bayan ya isa yyi magana akasanar da sir Aliyu yanada bako,nan akace yashiga.
Yana shiga yyi sallama sir Aliyu da kansa dake duke ya amsa yad'ago dan ganin wanene?
Atake ya hade rai sakamakon kamal dayagani,atsawace yace get out of my office .
Da sauri kamal yaduka harda yan kwallansa ya hauba sir Aliyu hakuri dan gani yake kamar zai sake suburbud'arsa.
Kallonsa sir Aliyu yyi bbu yabo bbu fallasa,yace meke tafe dakai?
Da sauri kamal yace pls katai makeni kayafemun da abinda na muku kaida kanwarka dan girman Allah badanniba.
Kallonsa sir Aliyu yyi yaga eh da alama yashiryu.
Nan yace bbu komai zaka iya tafiya Allah ya yafemana baki daya,nan kamal yyi masa godiya ya fita.
______________
Zakiyya ce tsaye bakin titi tun dazu ta ke jiran driver yaxo yamayar da ita gida ,tunda yakawota gun saloon tace bayan 50 minit yadawo amma shiru,kasancewar bbu waya gunta Balle ta kira dan tunda abbansu yasa sir Aliyu yadaketa,yakarb'e mata waya da mota itada Mubarak, yahana ta zuwa ko ina saidai inta kama driver yakaita.
"Har gyale da saka k'ananun kaya,duk yahanata saima yasakata islamiya,cikin ikon Allah tafara shiryuwa dan yanzun haka ma hijab ce ajikinta.
Kamal dake driving hankali kwance dan yaji Dadi da sir Aliyu ya yafemasa.har ya wuce yadawo sbd wata yarinya dayagani atake yaji tamasa."
"Ahankali yyi parking yafito yanufeta."
Zakiyya dake tsaye taji anyi mata sallama, juyowa tayi dan ganin waye?har cikin ranta kamal yamata amma afili sai ta wani d'aure fuska ta ce mlm lfy ?
Kallonta yyi yace dan Allah inbazaki damuba muje narage miki hanya.
Kauda kanta tayi tace nagode ,yanzun driver zaizo ya mayar dani gd ,murmushi yyi yace muje ki zauna baya sai in zauna gaba kinga nazama driver dinki ko? Yafad'a had'e da wani langabe kai.
Atake kamal yabata dariya nan ta bisa ,yabud'e mata gaba ta shiga yaja motar,nandai suka daidaita Kansu.
Bayan kwana2
Mlm aminu ne zaune da Hafsat suna fira ad'akinsa.kallonta yyi yace Hafsat!tace na'am .
"" ahankali baba yace ina Neman wa ta alfarma agunki !da sauri Hafsat ta zaro ido tace nikuma baba tana nuna kanta?yace kwarai kuwa.da sauri tace bbu alfarma atsakanunmu saidai kabani umarni kawai nikuma Nayi biyayya. murmushi baba yyi hade da saka mata albarka yace komene nabaki umarni zakiyimun?da sauri tace eh ko menene.baba yace Alhmdllh, abinda zanbaki umarni saikin gama makaranta ne ,kin amince ko nafad'amiki yanzun ko sai lokacin?kallonsa Hafsat ta yi tace komenene babana ashirye nake da Nayi maka biyayya.
"Cikin jin Dadi baba yace to shikenan."
Bayan kwana3
Duk binciken da baba zaiyi gameda alh Suleiman da zuri'arshi yyi kuma yadace,wato alh sulaiman da d'ansa sunkai yadda kowanne mutum nagari zaiso had'a xuri 'adasu.
Bbu bata lokaci baba yakirashi yace ya amince .
Nan senator yaji Dadi sosai, tareda cewa zasu zo gobe nemawa sir Aliyu auren Hafsat.
Haka kuwa akayi senator yaturo magabatan sir Aliyu, kuma baba yabada aurenta ga reshi,sannan ansaka auren dasunyi SSCE da sati4 za'ayi bikin.
Baba yyi shiru be fadawa laureba itada Hafsat yabari sai lokacin yyi.
6angaren senator ma hakan take besanar da sir Aliyu ba yabari sai Hafsat ta yi SSCE tukum sai ya sanardashi tukum.
Yau Yakama Friday duk yau sir Aliyu yatashi da kewar Hafsat,ana tashi dg masjid yawuce yyi mata shopping sannan ya nufo anguwarsu.
Bayan yyi parking agaban gdn su yafito,akuma lokacin baba zai fita dg gidan,sir Aliyu da sauri yarusuna yana gaidashi cikin sakin fuska.
Baba yace Muje ciki aliyu,murmushi yyi yabi bayan baba...
Share pls
[12/30, 6:25 PM] Ikhty Hafsat: NIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story & written by mmn fareesa
Ina godiya ga dukkan masoyana aduk inda kuke kuyi hakuri masu yimun magana ta PC ko ta grps bana reply muna hidimane wlh ina gani kuma inajin dadi,wannan page din nayisane sbd farin cikin Ku.love u all anamugun tare🤝🤝.
🅿81&82
Suna shiga suka had'u da Hafsat asoro da bucket a hannunta zata debowa Laure ruwa.kasancewar Laure taga lokacin da baba yafita,tadau ka bazai dawoba yanzun shine tasaka Hafsat adole ta debomata ruwa.
"Babane ya kalleta yace ina zaki da bucket?"
"Cikin jin kunyar sir Aliyu tace inna zan dibar wa ruwa." Afusace baba yace wuce ki mayar Naha na,sum sum Hafsat ta wuce ciki.
"Baba ya kalli sir Aliyu yace Aliyu ya mutanan gidan?sir aliyu dke jin haushin anmayar masa da Hafsat dinsa baiwa,yace suna nan lfy."
Baba yace masha Allah Dede nan Hafsat ta dawo da tabarma ta shimfidawa sir Aliyu.
"Baba yakallesu yace Nina wuce", Aliyu kagaida gida sir Aliyu yace to baba,nan yafita."
Hafsat kuwa kanta na duk'e akasa batace komaiba.
"Ahankali sir Aliyu yace waini laifin menayi ne da baza'amun maganaba?"
Kuma kinki ki kalleni,agayamun sai inbada hakuri.
"""" d'agowa tayi bata kallesaba tace, ah ah babu komai ai baka laifi aguna.ajiy ar zuciya yyi yace to kalleni mana,dan tura baki tayi tace ni kunya nikeji,dan tunda yaganta da bucket sai taji ba dadi bataso hakan ba.tashi yyi tsaye yace to ni na tafi tunda bazaki kalleniba,da sauri ta d'ago dan cewa kada yatafi caraf suka had'a ido da shi,wani killer smile yasakarmata,da sauri tasa hannayenta ta rufe fuskarta tana dariya k'uri yyi mata yana kallonta ,dg bisani yace to ni dai yau kuma ake jima kunya ko?batare da ta kallesaba tace kayi hkuri bansan meyasa nake jin kunyarkaba.""";;
Kafin sir Aliyu yace wani abu har sunga wata k'atuwar mage ta shigo soron ,shamsu yabiyota dan yasan Hafsat na mugun tsoronta.ai tana ganinta tayi wani uban ihu da gudu tanemi hanyar guduwa duk ta rude shikuwa sir Aliyu mamaki yake wai sbd magen ko me Hafsat keyin wannan ihun?be auneba tafad'a jikin sa du mammiyya,cikin tashin hankali yad'agota yaga bata numfashi da sauri ya kwantar da ita kan tabarma ya nufi cikin gidan.
Shikuwa shamsu da yakoro mage ,ganin Hafsat ta suma yasa yyita dariya hade da Jan magen sukayi cikin gidan.
Sir Aliyu yana shiga ko sallama bbu yawuce gun da ake aje ruwa ya debo ze fito kenan Laure ta fito a toilet, tawani kurma uban ihu hade da cewa kwart....maganarce ta mak'alemata sabida mugun kallon tsanar da sir Aliyu yajefeta dashi hade da Jan doguwar tsuka yabar gidan.
Ai Laure saitayi tsit dan tun sadda sir Aliyu yadaki deeni Laure ke shayinsa.
Yana zuwa soron yadinga yarfa mata ruwan afuska ,can ta tasaki wata nauyayyar ajiyar zuciya, tareda cewa yaya Aliyu dan Allah kada ka bari mage ta kamani tsoronta ni...rike mata hannu yyi yana girgizawa ssita bude idon ta,atake tadawo hayyacinta ta janye hannunta.
Kallonta yyi fuska cike da damuwa yace Hafsat dina haka kike tsoron mage dama?wane yarone yashigo da magen,?
Cikin marairai cewa tace pls yaya k'anina ne ,kada kayi masa komai kaji dan Allah.
Kafeta yyi da idanunsa yace kina nufin sumar min dake da yyi zaitashi a iska bazai yuyuba....
Kafin tace wani abu deeni yashigo soron,aiji yayi kamar yakoma sakamakon arba da yyi da sir Aliyu, amma da sauri deeni yaduk'a jade da cewa mai gida barka da rana.
Wani mugun kallo sir ya aika masa had'e da jin kishinsa yataso masa Wanda besan kishi bane atunaninsa tsanar deeni yyi.
Cikin bada order sir Aliyu yace dg yau kada kasake shigowa nan gidan,kaji ko baka jiba ?ya fad'a atsawace .
"Cikin ladabi deeni yace to bazan karya dokarkaba."
"Sum sum deeni yafice dg gidan."
Sir Aliyu ne yakalli Hafsat cikin tausayinta had'e da rarrashi yace muje kirakani mota ,ba musu ta tashi suka fito har bakin motarsa.
Gidan baya yabud'e yamiko mata tsarabarta, bbu musu ta karba had'e da godiya,bude gidan driver yayi zai shiga.
"Ahankali tace yaya!!!"
Kallonta yyi tasakarmasa murmushi ,shima yyi mata ,yace ki kulamun da kanki kinji tawan?
Murmushi tayi batace komaiba.
"Kallonta yyi yace koba tawan bace?"
Da sauri tace takace mana ,lumshe idanunsa yyi ya shige motar,itakuma tana masa addua.
***************
6angaren su Mubarak kuwa shima ba laifi ya shiryu dan saida abbansu yadage da tsayuwar dare Kansu.Allah majik'an bawansa yakarb'i addu ar sa.ita kuwa mommy n su kyaleta yyi yafita harkarta duk abun yadameta,ta yi masa mgana miyasayashareta?sai yace aure zai k'ara!aiduk saita rud'e,kasancewar yasan bata son kishiya.ai da kuka taje gun daddy wato senator takai k'ararsa nan senator yatarasu yyi musu nasiha,sannan duk tabada hkuri ta karbi laifinta tareda alk'arin zata gyara.shikuma abbansu Zakiyya ya janye maganar kara aure.
Ayaune mummunan kabari yazowa Fatima cewa 'al,ameen yarasu sakamakon accident, Fatima ta shiga tashin hankali tayi kuka kamar ranta zai fita.itama Hafsat kawa ba abarta abayaba dan itama ta damu da hakadai har Fatima ta dangana tacigaba da yimasa addu a.
Kwanci tashi bbu wuya gun uban giji su Hafsat har sun koma skul sun cigaba da karatunsu ,sir aliyu nacigaba da kula da ita.
BAYAN WATA6
Hafsat ce da sir Aliyu cikin mota guda sir Aliyu yana driving farinciki fal a fuskarsa.hakama Hafsat kasancewar yau suka kammala SSCE itada Fatima,ga kyaututtukan data samu abayan motar kasan cewarta gifted.shikuwa sir Aliyu yace shizai daukota, dukda taso tabi Fatima su shigo mota1,fatimarce tace taje ta bisa.
Shiru Hafsat ta yi axuciyarta kuwa kishine fal aranta sbd sunbar skul kuma zai cigaba da koyawa student tanajin haushin ayita kallensa ko ace ana sonsa. dan yanzun ta gane tana sonsa,kuma tayi alk'arin bazata tab'a nuna masa ba ko fad'a masa saidai inshi yanuna hakan.
Sir Aliyu ne yalura da yanayinta,murya k'asa k'asa yace ,Hafsat dina menene naga kamar kina cikin damuwa pls kigayamun kinsan bansan ganinki cikin damuwa?
Sunkuyadda da kanta tayi tace babu komai.
Hade rai yyi yace shikenan,tunda kinfison nima na zauna a damuwa,tunda kema kina cikinta.
Ganin yyi zuciya yasa ,tadan kauda kai ,murya na rawa kamar zatayi kuka tace,bakai bane ,zaka cigaba da koyawaba a skul din mu damuka bari,nikuma banason kana koyarwar.
Murmushi yyi jin shirmenta dan shi a shirme yadauki maganar,batare da yakalleta ba yace to naji tawan ai abinda kikeso shinike so ,kinfi so nadena koyarwar?
"Da sauri tace eh."
Yace to shikenan nida skul din Ku har abada da sunan koyarwa.
"Shikenan bbu wata damuwa yafad'a tareda yin parking kasancewar sunxo gida."
Wani farin ciki Hafsat ta ji jin kalaman sa.
"Ahankali tace bbu wata damuwa yayanah,amma nima meke bakaso kaga Nayi?"
Da sauri yace baniso ki kula ko wanne saurayi ,dan skul zaki cigaba kinajina?
Cikin murna tace to Yayana nagode sosae.
Nan ta fito ,yafito mata da kayanta Duka duk kyaututtukan data samu suka shige gidansu ,asoro suka had'u da baba,nan suka gaisa baba nata masa godiya da sakamasa albarka.
Nan Hafsat ta yi ciki da kayan,tadawo ta dau sauran ta koma ,baba kuwa yaraka sir Aliyu har mota,sannan yadawo gd.
Shikuwa sir Aliyu driving yake zuciyarsa cike da kewar Hafsat dinsa wani gefe kuma na xuciyarsa na fargabar maganar da daddy sa yace zaiyi dashi ,inyadawo daga Egypt dan yace mihimmiya ce,kuma k'ila gobe daddy nsa zai dawo.
Haka yyita tunani har ya isa gida yyi parking yafito ya nufi ciki....
Share plsNIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story &written by mmn fareesa
🅿83&84
Yana shiga, awaiting parlour yasami su sa'ada da mommy, nan ya zauna sukayita fira da bisani ya wuce part dinsa.
"Washe gari da misalin karfe 2:00pm daddy yadawo dg Egypt."
Bayan ya huta yaci abinci ,suna zaune shida mommy suna fira canyakalleta yace inaso muyi wata magana dke?mommy tace to alh inajinka.nan daddy yakoromata bayani akan auren da zaiyiwa sir Aliyu, dakuma cewa yau zai sanar dashi.ajiyar zuciya mommy ta yi cikin fad'uwar gaba tace amma shine alh har aka kai wannan lokacin baka fadaba.kumafa yaronnan yanada wadda yakeso.tsaki senator yaja yace kinsan bansan yawan Jan magana ko?nariga na yanke hukunci ,in yanada wadda yakeso meyasa be kawotaba?inma yanada ita to ya aureta dg baya amma nagama ,magana banason jin komai,kawai kiyi masa addua.shiru mommy ta yi ganin daddy zai dauki abin da zafi saitace Allah yazaba abinda yafi alkhairi. Amma a zuciyar ta tana tausayin sir Aliyu da Hafsat, dan talura suna son junansu.daddy ne yakatse mata tunani da cewa inyadawo kituromin shi nayimasa bayani.to mommy ta ce tafita.
****************
Babane zaune da Hafsat suna fira,adakinsa,can baba yakira sunanta har sau ukku tana amsawa ,sannan yyi gyaran murya, had'e da cewa kinsan abaya kinmun alk'awari kome nasakaki zakimun biyayya ko?jiki a sanyaye tace eh baba yace madallah.
"Nan baba yakora ma Hafsat bayanin nanda 4weeks za'ayi aurenta."
Cikin fad'uwar gaba tareda rawar jiki,had'e da tsoro Hafsat ta zaro idanu tace aure baba?
"Baba yace eh ,ko kinmanta kinmun alk'awari ko me na umarceki zakiyi biyayya."
Cikin dauriya hade da karanta inna lillahi wa inna lillahi raju un, tace to baba Allah yasa hakanne alkhairi.
"Ahankali yace ameen had'e da sakamata albarka."
Tashi yyi yace natafi masjid, bejira amsarta ba yafita,kamar jira take ta fad'a kan katifarta tasaki kuka me cin rai,afili tace yanzun yaya Aliyu wani zai rabani dakai bazan samekaba,dan Allah kazo kaceceni kabawa baba hkuri.
Haka tayita surutai da kuka har idanunta suka kumbura sbd kuka dg nan bacci yyi gaba da ita.
Bangaren sir Aliyu kuwa,bayan yadawo mommy ta ce yaje gun daddy yana son magana da shi.
Bayan yaci abinci, yanufi part dinya shiga.bayansun gaisa daddy yyi gyaran murya,yace da farko Allah yyimaka albarka ina alfahari dakai a y'ayaana sbd kanamun biyayya.
"Atake yaji fad'uwar gaba."
Daddy yacigaba da cewa, hakan yasa na yi bugun gaba dakai dan nasan bazaka watsamin kasa a idoba.
Nan daddy yazaiyane masa maganar aurensa nanda da4weeks.
Ai ji sir Aliyu yyi tamkar andasasa agun ga wani sarawa da kansa keyi kamar anbuga masa guduma,gabansa inbancin dukan Tara Tara babu abinda yake,ga wani jiri da yaji atake hade da bushewar makoshi sbd tsabar firgita da rudani,Dan besan daliliba ,anayimasa maganar yatuna Hafsat dinsa.
Daddy yace kobaka amince bane naji kayi shiru?
Murya a sarke yace na amince ,yafad'a cike da dauriya hade da mik'ewa tsaye yabar part din.
Part din sa yawuce ,ya kwanta sakamakon yadda kansa ke sarawa kamar zairabe ga xuciyarsa na bugawa da karfi,gefe guda kuma tunanin Hafsat ne fal aransa.
Gajiya yyi da juyawa a kan bed ,da sauri yatashi jiri na dibarsa yafita parking spaces yaja motarsa yyi gidansu Hafsat.
_________________
Hafsat kuwa bayan ta tashi tayi sallar la'asar ,mike rai adagule ta fito dan taje gun Fatima ta sanar da ita ko akwai shawarar dazata bata.
Shikuma sir Aliyu allane kawai yakawosa anguwarsu Hafsat lfy ,dan gudun da yakeyi ya wuce tunanin me karatu.
Yanayin parking ya fito ko rufe motar be yiba yashiga gidansu Hafsat ,idanun nan nasa sunyi jajir sai huci yake.
Asoro yahadu da Hafsat zata fita,aitana ganinsa da gudu ta fada jikin sa tasaki kuka me cin rai....NIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story & written by mmn fareesa
🅿85&86
"Yah salam kawai yake maimaitawa azuciyarsa" ganin yadda Hafsat ke kuka,hannunsa yasa yadago kanta yasa yatsansa yatsare mata hawayen,tared a kok'arin rabata da jikin sa amma tasak e manne masa tana kukan shagwaba. "
dama tarasa wazatayi mawa ,sai gashi yazo",cikin kasalallar murya yace yi shiru kinji Hafsat d'ina kidawo nan gun,yanuna mata gefensa.
Tare da cewa kinga in baba yasamemu ahaka bazaiji dadiba mutuncina zai xube agunsa.ai da sauri tabar jikin sa tadawo gefensa tana cigaba da kuka
"cikin damuwa yace me kikewa kuka waye yasaminke kuka yanzun yakarbi mummunan hukunci aguna??"
"cikin kuka tace babane."
da sauri ya maimata Kalmar babane!!
""" d'aga kanta tayi tareda cewa yaya dan Allah katemakeni baba zaimun aure yarinya dani!
Wani irin bugawa yaji xuciyarsa tayi hade da jin jiri da wani mugun ciwon kai,murya asarke yace aure kuma Hafsat wa baba zai auramiki?,yafada had'e da kafeta da jajayen idanunsa."""
Cikin kuka tace wlh bansanshiba nima pls kaje ka rokesa yyi hkuri wlh banason auren da kuma Wanda zai auramun ta fada hade da sakin sabon kukan.
"Cikin wani yanayi yace ke wa kikeso?"
K'uri yyi mata yana jiran tace k'ila koshi takeso, sai yaji tace bbu koma nidai kawai banson auren.
Tsakin dabesan yyiba yaja ,hade da tamke fuska yace k'ila dakin gayamun Wanda kikeso to danayiwa baba magana ,sai a auramiki shi"amma innace abarki kada ayi auren ,yace waKikeso ?nace masa me?
da sauri tace amma yaya kag......da sauri yace ki koma ciki anjima zamuyi waya bance kije ko inaba kina jina?kallonsa tayi hawaye na zuba tace gidansu Fatima zanje",cikin isa yace nace bazakiba yafad'a had'e da dafa bango sbd jirin dayakeji had'e da kunar zuci dan ji yake damuwarsa ta nunku akan wadda yake ciki,saidai wani gefen na zucoyarsa na tahumarsa dalilin damuwarsa dan ance Hafsat zatayi aure."";;
"Kallonsa tayi ganin yyshiru,tace natafi."
Cikin damuwa sir Aliyu yace dan Allah Hafsat dina kidena kukannan haka,nima wlh ina cikin damuwa yau ,zanyimana addu a kinji kema kiyimana.
" daga masa kai tayi hade da shigewa gida ",dan intayi magana kukane zaixomata.
Shikuwa sir Aliyu da sauri yafito dg gidan,kallo daya zaka masa kasan yanacikin tashin hankali da damuwa.idanunsa sunyi jajir ,jijiyoyin kansa duk sun tashi ga jiri na d'ibarsa,da sauri yabud'e mota yashiga ya axa kansa kan sitiyarin motar."
yaya Ahmed dake tafe a mota yahangi sir Aliyu cikin wannan yanayi atake yasan bbu lfy.
"da sauri yyi parking ya fito yana kiransa be jiba yashige motarsa" da sauri yy Ahmed yabisa.yabud'e gaban motar yashiga yasamesa kansa duk'e.da sauri Ahmed yace friend lfy meke faruwa ne??
"cikin damuwa sir Aliyu yadago,saida yy Ahmed yatsorata da yanda yaganshi." Cinkin damuwa ya sanarda shi halin da yake ciki.
Ahmad yyi ajiyar zuciya yace wannan ne abin damuwa! Aini nan banga abun damuwaba,tunda kak'i kayi aure ai gara suyima.tsaki sir Aliyu yaja hade da cewa ,aibansone shiyasa ,itama Hafsat dina ,za 'amata auren dole yafada kamar zai yi kuka.
Yy Ahmed yace banganeba?nan yabashi labarin itama Hafsat auren dole za'a mata.murmushi Ahmed yy yace tokai meye damuwarka? Wata harara sir Aliyu ya bankawa Ahmed yace ,my Hafsat ta na cikin damuwa ya za ai hankalina yakwanta.
"Girgiza kai Ahmed yy yace wlh ko kaso ko ,kada kaso kanason Hafsat so mai tsanani Wanda ko a idonka gashina kwance had'e da tsantsar kishinta".
Wlh kama farka in bacci kake tun kan sonta yyimaka illah ko lahani kasani ka bayyana mata.amma wannan ai kishinta kake,wlh duk wanda yasan so,indai yyi zaman minti biyar daku zai gane kana ma Hafsat wani irin zazzafan so hade da kishinta me tsanani ,nagane hakan tun a hidimar biki na,kuma nayiwa Fatima tambayoyi ta bani amsa anan na kara tabbatar wa kaina kanasonta,inhar baka zameta ba ko mai zai iya faruwa. Nan dai Ahmed yyita masa bayani hade da ankarar dashi cewa yyi zurfi ason Hafsat dakuma tamvayarsa kanajin kaza inka ganta ko kaganta da wani?me kakeji intana cikin damuwa ko Bacin rai?nan yacigaba da cewa zakaji kaza da kaza inkiuna tare kobakwa tare ko in kun gamu ko kaganta da wani nmji.
doguwar ajiyar zuciya sir Aliyu yyi hade da cewa na yadda abokina da maganarka dan duk abubuwan daka lissafamin irinsu nakeji game da ita.
Nayarda indai hakan shine so to lallai son Hafsat yamun illah ,muddin bansametaba komai zai iya faruwa dani yafad'a cikin damuwa.
" ahankali Ahmed yace friend kayi hkuri kaji kayi biyayya ga daddy sannan kayita adduar ai nmj mijin mace4 ne daga baya saika auri Hafsat din inrabonkace.
Batare da sir Aliyu yyi magana ba yatada motar.
Da sauri Ahmed yace wait,nan yakira driver na gidansu yace yazo yamayar masa da motarsa gida.kallon sir Aliyu yyi yace nizan kaika gida bazan bari katafi kai dayaba komai zai iya faruwa.
Bbu musu sir Aliyu yafita Ahmed yazauna amazaunin driver yajasu suka dauki hanyar gidansu sir Aliyu.
Bayan sunyi parking ko sallama sir Aliyu bebari sunyi ba yafito arikice yyi cikin gidan.
"Shikuwa Ahmed ya fito dg motar yyi waje,had'e da yiwa abokinsa adduar samun sassauci."
Yana shiga bbu ko sallama yanufi gun mommy dake zaune akushin kusada su sa'ada da kabeer,kamar wani yaro haka yafad'a kan cinyarta,yana Sabbatu cikin tashin hankali.
Mommy kuwa naganinsa tasan dama hakan zai faru tunda daddy yace zai sanar dashi maganar aurenshi.
Cikin tausayinsa tace baba na meke faruwa ne kke cikin wannan yanayi?
Arikice hade da rik'e mata hannuwa yace pls mommy kitaimakeni zanrasa Hafsat dina mommy itace bugun xuciyata mommy can iya rasa raina inbansametaba,mommy baban ta zai mata auren dole zai aura mata wani ba niba.
Wlhy matata ce duk Wanda yyi yunk'urin auranmun mata wlh zanyi ajalinsa domin dan ni akayita dani ta dace hafsat pls mommy kada kibari arabani da matata wlh zan iyayin komai akan hakan bazan sau....da sauri mommy ta rufe masa baki hade da cewa ya isa haka!
"Waya jamaka ?"
Kai kajawa kanka gudun hakan yasa na tambayi meke tsakanunku ?amma sai kacemun ai dalibarkace.
Sai yanzun dakaji za'amata aure zakace kanasonta.
Sukuwa su sa'ada da kabeer mamakin sir Aliyu suke dan tunda suke dashi yaune sukaji yace yanason wata mace.
Shikuwa kabeer azuciyarsa yace madallah anxo gurin ai dama duk masu cika bakin basayin soyayya duk ran da takamasu hmm basuji da daddy ji dai yaya ko ina ya aje miskilancin nasa duk yake wannan haukan akan mace?
Sir Aliyu ne yatashi dafe da xuciyarsa yana kiran Hafsat !Hafsat!! Hafsat!! Yana dafe bango dan gaba daya ya haukace musu,sai surutai yake musu,basu auneba sukaga ya fad'i kasa su mamme.
Share plsNIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story written by mmn fareesa
🅿87&88
"" da sauri mommy ta yi gunsa tana salati,sa'ada kuwa kuka ta saka."
Kabeer ne yyi hanxarin dakko swan mai sanyi yadunga kwaraya masa ,cikin ikon Allah yasa ki ajiyar zuciya hade da bude idonsa.
"Sannu kawai su mommy ke masa da su sa'ada ."
Ahankali yatashi zaune ya karbi sauran swan din yashanye sannan yatashi batare da yayi magana ba yyi part dinsa.
Kabeer ne yyi saurin cewa momm yko maje hospital adubasa dan Allah. Wani mugun kallo sir Aliyu yajuyo ya aikowa kabeer hade da cewa kai yaushe nafara wasa dakai?
Sunkuyadda kai kabeer yyi yace yi hakuri yaya.
"Tsaki sir Aliyu yyi yabar gun", mommy kuwa hararan kabeer tayi hade da nufa part dinta"".
Tana zuwa ta bincikowa sir Aliyu magunguna harda na bacci sannan ta wuce kitchen ya had'a masa tea mai kauri ta nufi part dinsa.
" shikuwa sir Aliyu kwance yake kan bed yyi rigingine idanunsa alumshe yana tunanin Hafsat dinsa mommy ta sh igo d'akin."
Saida tayi sallama sau3 tukum ya amsa yana dan Sosa kansa."ahankali mommy ta ce tashi zaune babana! Bbu musu yatashi ta bashi tea din ,bayan yasha tabasa magani ,hade' da yimai nasiha yyi biyayya ga daddynsa kuma yyita addua."
Bajimaba da shan tea din bacci mai nauyi yyi gaba dashi.mommy ta kallesa cike da tasayi tabar dakin.
******************
Hafsat kuwa tun bayan Sir Aliyu yatafi takoma dakinta ta cigaba da aikinta wato kuka.
Domin itadai kowama zata aura wlh tana tsoron sex dan tanaji in mate dinsu na bada labari in sun karanta a littafi ,cewa da wahala sosai,saitaji duk ta tsorata da aure to Balle batasan wanne marar imanin zaa aura mata ba.tana kukan da tunane tunane had'e da fushi da sir Aliyu bacci yyi gaba da ita, bata farkaba sai gab da sallar la'asar bayan tayi sallah ,tajima tana adduar allah yazaba mata abinda yafi alkhairi yakuma baiyana mata mahaifiyarta.
Cikin ikon Allah saitaji damuwarta ta rage ,nan taje tayi wankanta ta wuce islamiya kasa.cewar yanzun hadda take,amma fa tayi fushi da sir Aliyu sosai.
Bangaren sir Aliyu kuwa shima sai bayan laa'asar yatashi ,yyi wanka hade da sallah.
Cikin ikon Allah yaji duk wani k'unci da damuwarsa sun rage .
"Neman guri yyi ya zauna yafara tunani n Hafsat dinsa." mur mushi yyi daya tuna duk abinda yakeso matar dazai aura takasance dasu Hafsat tanadasu du ka.nafarko ya. Yana son wacce zai aura takasance yarinya danya sharaf,yadda zai raineta da kansa zai koya mata sonsa da kula da yaransu su zauna lfy.sannan kuma mai kunya ilimin addini da tarbiyyamai son danginsa,sai yaduba yaga Hafsat duk ta had'a wa inna abubuwan. Wata zuciyar ta ce kanada tabbas din zaka mallaketa?
Tunawa yyi kilama har yanzun batadena kukaba da sauri yazaro wayarsa yakira baba.
bbu bata lokaci baba yadaga had'e da sallama,Hafsat dke gefensa cikin sanyin muryarta tace baba waye yakiraka?
Baba dke cewa lfy lau aliyu ya gida?
Atake Hafsat ta gane cewa da sir Aliyu baba keyin waya,aisaita kwanta ta rufe ido kamar me bacci.
Shikuwa sir Aliyu tun sadda Hafsat ke tambayar baba yaji muryarta,dama dan ita yakira yanaso suyi magana.
"can yace baba ko Hafsat na kusa mu gaisa?"
Kallonta baba yyi ,yace aiko kamar tayi bacci Bari natasheta.
Da sauri sir Aliyu yace ah ah baba rabu da ita tayi baccinta.nandai sukayi sallamada baba,sir Aliyu kuwa yasan sarai Hafsat ba bacci takeba kwaidai fushi take dashi.
Murmushi yyi yace oh Hafsat akwai rigima da shagwaba ,nasan haka zanta fama da rigimarta inmukayi aur......da sauri yyi shiru sakamakon tunawa da yyi Hafsat wani za'a aurama ita.
" cikin jin haushi hade da wani kishi da yataso masa yatashi yafita dan xuwa masjid.
Koda dare Hafsat da sir Aliyu bbu Wanda yyi baccin kirki duk da damuwa suka kwana ,kowa na tunanin dan uwansa.
Washe gari haka sir Aliyu yatashi duk yad'an fad'a saidai fuskarsa tayi fiyau da shi,ko break beyiba yanufi gidansu hafsat ,dan hankalinsa yak'i kwanciya Hafsat tana fushi dashi.
Yana isa yyi parking yafito kaitsaye yakutsa kai cikin gidan ,asoro yasami Hafsat tana sharewa kallo daya zaka mata kasan tana cikin damuwa.
Ai tana ganinsa tasaki tsuntsiyar tayi cikin gidan aguje.
Murmushi sir Aliyu yyi dan yalura har yanzun fushi take dashi,dan haka shima yasaka kai cikin gidan...
Share plsNIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story & written by mmn fareesa
🅿89&90
"Yana shiga yasami bbu kowa tsakar gidan", kallon wani d'aki yyi yaga yan takalmi bakin k'ofar dakin atake jikin sa yabasa nan Hafsat ta shiga.
Beyi wata watab a yashiga had'e da sallama, da sauri Hafsat ta d'ago dan batayi tunanin zai biyota ." nan ta ammasa sallamar".
Ta juya masa baya batace komaiba,aha nkali yace my Hafsat duk fushinne har haka ,bazaki tausayamunba ki barni najida abinke damuna,sai kin karamun wata damuwar!yakikeso nayi da raina?
"Ahankali tace nidai yaya katafi ni bazan hakuraba ", Allah kuwa.
Shiru yyi yana tunani,can yace my Hafsat gidanku fa nazo,shine zakimun haka.
Kallonsa ta d'ago tayi hade da murguda baki tace eh din tun....shiru tayi ganin Laure a k'ofar dakin.
""" ckin masifa tace keko?kinanan kuna aikata masha,arku har cikin gd ko to asirinku yatonu wlh oh da rana Kiri k'iri bbu tsoron Allah ai.. Wata rikitacciyar tsawa sir Aliyu yadaka mata had'e da cewa ya isa haka wlh kinci darajar baba da wlh yau kinyi nadamar kalamanki,amma ko yanzun zan had'a ki da k'ananun yan sanda,yafad'a tareda da Jan doguwar tsuka yabar gidan. """;;
Hafsat kuwa shiru tayi kamar andasata agun tanajin ciwon maganganun Laure da haushin tafiyarda sir Aliyu yyi.
" Laure kuwa jiki amace ta nufi d'akinta".dan ta tsorata da maganar sir Aliyu.
Shikuwa sir Aliyu gida yanufa yanajin haushin kintsayawa da yyi ya rarrashi Hafsat.
****** ***** ******
bayan kwana biyu
Sir Aliyu ne zaune kan bed duk yyi yar fuska ga sajen fuskarsa yyi yawa baya gyarawa kwana2 sbd hankalinsa ba kwance ba sai Karen hancinsa dayyi siriri ya k'ara fito da ramarsa,sai tunani yake can wata dubara ta fad'o mishi da sauri ykira mommy yace ta turo masa sa'ada yanzun .
Bbu jimawa sa'ada ta shigo dakin ,bayan ta zauna ,cikin sakin fuska sir Aliyu yace y'ar autarmu wani aiki zakimun kinji ko?
"Ahankali tace wanne aiki?"
Kallonta yyi yace matso kiji bbu musu. Tamatsa kusa dashi yarad'a mata wata magana Shewa sa'ada ta yi had'e da cewa to yaya bara najira kashirya danni ashirye nake.
Murmushi yyi yace ammafa inaso abun yazama sirri kada ki nuna mata cewa inasonta,kin fahimta?
"d'aga kai tayi alamar eh."
Bece komai ba yashige bathroom itakuma sa'ada ta fito dg dakin.
Bayan yagama shiryawa sai wani fitinannan k'amshi yakeyi ya kalli kansa a mirror, yaga duk k'simba ta cika masa fuska.
Murmushi yyi daya tuna Hafsat ta tab'a cemasa yafi mata kyau inya gyara sajensa na fuska ai da sauri ya jawo wata lokar yafito da kayan gyarawar ya gyara abinsa yy kyau sosai,nan yasami mommy da sa'ada a waiting parlour a zaune.
Kallon sa'ada yyi yace Auta muje,na musu ta mik'e hade da kallon mommy ta ce muntafi da yaya zaimun shopping.
Murmushi mommy ta yi dan tasan bbu wani shopping dazasu.
"Ahankali tace kudawo lfy", sa'ada ta ce ameen hade da fita ta bisa .
Sa'ada da sir Aliyu bazu tsaya ko inaba sai gidansu Hafsat.nan sa'ada ta kalli sir Aliyu dke nuna mata gidan da hannu yace ga gidansu can yi gaba zan biyoki intsaya a soro sai kifitomun da ita.
Bbu musu sa'ada ta fito dg motar tayi cikin gidan,tana shiga tayi sallama Hafsat dke daki tanasaka kaya dan fitowarta kenan dg wanka,tanajin muryar sa'ada ta fito da gudu suka rungume juna ,cikin farin ciki Hafsat tace yau inada babbar bakuwa nan tajata dakinta.
Bayan tasaka kaya,suka dan fara fira Hafsat nason ta tambayi sir Aliyu amma tanajin nauyi,fan kwana biyu nan dabata gansaba adaddafe tayisu.
" sa'ada ce takatse mata tunani gun cewa pls muje gidansu Fatima naga tanada kirki."
Hafsat tace ok muje nan tasaka hijab suka fito,suna isowa asoro taji kamshin sir Aliyu da sauri ta d'ago kanta caraf suka yi 4eyes dashi. Sa'ada naganin haka ta maixa tayi tafiyarta gidansu Fatima dan dama haka suka tsara da sir Aliyu.
"Kallonta yyi yace my Hafsat kin huce ne?" Shiru tayi sai tura baki gaba take. Murmushi yyi yace duk Dan sabida kiyi farin cikin nakawo miki sa'ada ,kuma inji kindena fushin dani.
Cikin shagwaba ta ce ai yanzun na hakura ,amma pls kayimun murmushi yaufa kusan 4days rabon da inga murmushinka.
"Ahankali yakalleta yace nima haka Nayi missing smile naki amma kalleni,tsurrawa juna ido sukayi kowa na mamakin ramar da d'an uwansa yyi."
Sir Aliyu ne yafara mata murmushi itama tamaida masa,ahankali yace kinyi kyau bana gajiya da kallon wannan kyakkyawar furkar taki.
Murmushi tasake cikin yar shagwaba rta hade da yarinta tace kaima yaya kayi kyau banason in rabu dakai pls ta fad'a kamar zatayi kuka.
Kallonta yyi yace dakinyi kuka zamu bata ,mudage da addua kinji ko?
"To tace."
Ahankali yace abinda nibaki tab'a cewa ma Nayi kyauba kuma wannan gyaran fuskar danayi danke nayisa.
Da sauri ta kallesa axuciyarta tace kodai yana sona shima?
"Afili saitace Allah yaya kanamun kyau sosai ayanxun nikayiwa wannan kwalliyr taka?"
Kafin yace wani abu sa'ada ta shigo tace yaya muje dan Allah marece yyi bata jira amsarsaba tayi gaba.
Kallon Hafsat yyi yace my Hafsat zamu tafi,turbune fuska tayi kamar zatayi kuka ,cikin shagwaba ta ce nibanyatdaba dg xuwa sai tafiya.
Cikin rarrashi yace to ai gobe zanzo muje na kaiki amiki steaming kinjik..shiru yyi gani yadda take ta dire dire da bubbuga kafa kasa ita bata yardaba.
Lumshe idanunsa yyi dan in Hafsat ta yin irin wannan rigimar tata yana shiga wani yanayi.
Matsawa yyi gab da ita ,murya na rawa yace gayamun me kikeso kike wannan rigimar ,?
Cikin kukan shagwaba ta ce nibanason katafi kabarni dan bangaji da ganinkaba.
Murmushi yyi dan jin dadin kalamanta ya yadda kobata sonsa to tadamu dashi.
Rarrashinta yyitayi abu ga masoya saigashi yashawo kanta,hartahakura tamasa rakkiya hade da cewa sa'ada ta gaidamata mommy.
Sannan yaja motar suka bar anguwar.
Washe gari da misalin karfe 9:am sir Aliyu zaune kan carpet gaban daddy yazo gaidashi.bayan sun gaisa daddy yace kaga lokacin bikin nan yadan matso tunda saura3weeks yau xanje Dubai da mommy nku muhad'a lefe daganan muje Egypt mutaho da marar lafiyar nan a maodota gidan nan akwai wani doctor da zaixo yasake bincika rta. Shine nikeso ko inmuntafi ko bayan mundawo kaje gidansu yarinyar nan kuga juna kakuma gaida mahaifinta.
Wani fad'uwar gaba sir Aliyu yaji da Bacin rai jin maganar auran nan na nandai.
Jin yyi shiru daddy yace ina sauraronka ,inmuntafi zakaje ko kuwa sai bayan mundawo dg Dubai?.......
Share plsNIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story & written by mmn fareesa
Wannan page din nakune amintattun mata writer's association, tareda muhad'a kanmu writers, association.kuyi yadda kuke so dashi.. Kunfi kowa son nida dalibata nagode sosae da kaunarku agareni ,ana mugun tare.👏🏻😍😍
🅿91&92
cikin k'osawa da maganar yace daddy inkun dawo zanje tunda yau zaka tafi nikuma bansan gidanba.
"kuma suma ba su sanniba", murmushi daddy yy yace zasu sanka very soon Allah yakaimu sai insaka cikin body guards dina wani yyima ka jagora tunda sunsan gidan".
Atak'aice yace to had'e da barin part din,yanufi nasa part din.
Axuciyarsa kuw a cewa yake ko naje bazan sakan mata fuska ba dan kada yarinya ta kamun raini ,k'ila ma hafsat ta fita komai. Dukda nasan bazai zabamun marar tarbiyaba.
"" tsaki yaja hade da shigewa bath room dan yanason yaje ya kai Hafsat gun stea ming."cikin yan mintina yafito da kananun kaya sai k'amshi yake yanufi gun mota yashiga yabar gidan.
Ahanya kuwa sir Aliyu sai tunani yake ga wani kishin Hafsat dke tasomas a,yakudurta aransa duk ranar da yataradda wannan gajan da akace zata aura sai yamasa rashin mutunci k'ila ma yasuburbideshi saidai komai zai faru yafaru wlh.
"da wannan tunanin ya iso anguwar", fitowa yyi dan besan shiga cikin gidan sbd Laure kada wata rana taja masu sharri shida Hafsat dinsa."";;
" befi minti biyarba yaga Hafsat ta fito."
Kasancewar tun dazu ta ke jiranshi tunda jiya yace zaizo yau suje gun steaming din.
Tun kan ta ida isowa suke aikowa da juna sak'on mur mushi.harta ida isowa ,"ta kallesa hade da cewa Yayana ni kadai"!
dariya ta basa s hima yace Hafsat dina ni kad'ai.lumshe idanunta ta yi tace ina wuni?
"Ahankali yace lfy ." ina fatan bbu wata matsala ko damuwa ko?sunkuyadda da kanta tayi tace inada su Duka!cikin damuwa yace dan Allah kidena damuwa kibarwa Allah kinji?
Cikin shagwaba ta ce Aina hakura ya nxun Kaine damuwar banason inrabu dakai koda da minti dayane.tafad'a had'e da fashe masa da kuka .
Gaba daya ta d'aga masa hankali.
"Ahankali yaja hannunta yabud'e mota yasakata shima yaxagaya yashiga yatada motar",cikin rarrashi yace indai nine ba damuwa zandunga xuwa gidanki muna gaisawa kinji?yafad'ane dan tayi shiru amma bazai taba aikata hakan ba.
"da sauri tace dgaske kake yaya"?
" d'aga kansayy alamar eh."
Batare da yakalletaba yace muje yanzun agyaramiki gashinko tawan?
Murmushi tayi tace to Yayana ,dama inason ince kakaini sai gashi ka xoma da maganar ,murmushi yyi yace jikinane yabani kinason muje na kaiki.
"Ahankali tace duk lokacin damuke tare inajin kaina cikin farinciki ,pls yaya kada kak'i cikamun alkawarinka na xuwa gidana kullum had'e ransa yyi dan saiyaji koma tanason auren tunda har ta ke cewa wani gidanta. Fuska ad'aure yace yaron da akace zaki aura yafara xuwa kuna xance dashi ne?yafad'a had'e da kafeta da ido yanason jin amsarta cikin damuwa tace ah ah betaba xuwaba.
Wata ajiyar zuciya yasaki wadda besan ta fito filiba ." da sauri ta kallesa amma sai ya waske ."
Bayan sun iso da kansa yarakata yakoma mota ya jira har aka gama.sannan yabiya kud'in da besan adadinsuba yabiya mata,itakuwa matar ta karb'e tana godiya.
dg gun steaming suka wuce yyi mata shopping ,sannan suka dawo gida ,sai murna suke da farinciki, dan in suna tareda juna suna manta cewa wai sunada damuwa aduniya.
Nan sukayi sallama sir Aliyu yawuce gida cike da kewar hafsinshi.
****** ***** ******
bayan kwana ukku har daddy yadawo da mommy kuma sun dawo tareda mairo wato mahaifiyar Hafsat.
""" sun had'o kayan lefe nagani na fad'a anjeresu part din daddy washe gari zasukai gidansu amarya Hafsat."
Shikuwa uban gayyaar baya gidan lokacin da suka dawo ,yanzun haka shi ake jira yazo yaga kayan sannan daddy yasa guard dinsa yakaisa gidan mlm aminu.
Domin yagaidashi yaga kuma amarya Hafsat,dan har daddy yakirasa yashai da masa yau dansa zaixo yagaidashi.
"Mairo kuwa part daban akaware mata itada masu kula da ita."
Sir Aliyu bedawo gidanba sai bayan azahar,yasami su mommy a waiting parlour, bayan yyi mata sannu da zuwa ne .
"ta kallesa tace kaje kayan lefen na nan part din daddynku kagani sannan ka shirya da la'asar zakuje gun surikar tawa ,taf'ada cikin xolaya dan tasan ta k'ular dashi.
Yatsina fuska yyi yace haba mommy ni basai naganiba.sa'ada dke gefe tace eh wlh yaya kadama kagani tunda ba Anty Hafsat bace za'akaiwa lefen!da sauri mommy ta mata dakk'uwa ,sa'ada tayi shiru. Mommy ta kallesa fuska ad'aure tace wannan umarnin mahaifinkune banason musu maza kaje kagani kadawo ka shirya .yauwa inkadawo kuje Duka harda kabeer part din marar lfyar nan kuganta.
" to kawai sir Aliyu yace yanufi part din daddy. "
Fuska bbu yabo bbu fallasa yaga kayan ,sannan yafito dan shiryawa amma yanajin mugun fad'uwar gaba.
Bayan ya shirya cikin fararan suit fuskannan atamke bbu walwala ko fa'ara yafito yasami guard din zai kaisa a parking space. nan yashiga gidan baya shikuma guard din yaja motar.
"" tunda suka fara nufar anguwar kawo gabansa yacigaba da fad'uwa."
Bangaren su Hafsat kuwa adole baba yasa ta share soro ta shimfid'a tabarma babba ,sannan taje ta shirya rai bbu dad'i dan ta d'auniya niya saita masa rashin kunya kowane mugunne dakeson sanadin rabata da farin cikinta.
Haka ta shirya cikin arebiant gown dark blue, kuma sir Aliyu ne yasiya mata ita.
Shikuma baba hard a siyo swan water da exotic da za'a tari bak'o dashi.
Shikuwa sir Aliyu ganin sunshigo anguwarsu Hafsat yasa yakalli mutumin da sauri yace wai banganeba ina zamufara xuwane tukum?
Cikin girmamawa yace ranka yadade' ai nanne anguwarsu amaryar taka ga kwanar gidansu can,yafad'a yana nuna kwanar gdn su Hafsat.
Cikin kin yarda da maganar da yace wai ina wasa dakaine kafadamun yadda zan fahimta.
Cikin ladabi yace wlh nan anguwa r take,alokacin yyi parking agaban gdn, kuma Dede nan mlm aminu yafito da ga gidan.
Nuna masa mlm aminu yyi yace kaga mahaifinta can ma tsaye .....
Share plsNIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾
Story&written by mmn fareesa
Ina mika godiya ta ga dukkan masoya nida dalibata comments hade da sharhi na jiya yafi na kullum kuyi hkuri wad'anda banmusu reply ba a PC ,amma nagani inajin dadin hakan nagode inamugun jidaku. Anatare🤝🤝
Dedicate to all my fans
🅿93&94
Tsantsar mamaki yahana sir Aliyu magana ,saimurxa idanunsa yake yaga ba bacci yakeba .ha nnunsa yasa abaki ya gartsa,atake yagane ba mafarki bane d gaske ne.amma tambayar kansa yake yahakan ta faru?karar bud'e motar da guard din yyi yafita shiyadawo dashi dg tunaninsa."ahankali shima ya fito",,suka nufi gun baba,baba kuwa mamaki yake ganin sir Aliyu tareda guard din senator ,tambayar kansa yake to ina aliyu yasansu? Kafe aliyu yyi da ido atake yahango kamannin senator a fuskarsa.dan tundayake da sir Aliyu sai yanzun yyi masa kallon tsab."isowarsu tadawo dashi tunaninsa."guard dinne yafara gaida baba ,sannan yace dama y'allab'ai yaturoni nayiwa ogah jagora yazo ya gaidaku !kallon sir Aliyu yyi yace ogah inajiranka amota inkun gama."bejira amsarsaba yyi gaba cikin tsananin farin ciki had'e da murna sir Aliyu yaduk'a yakwashi gaisuwa gun baba.baba cikin al'ajabi had'e da mamaki ya amsa tare da cewa aliyu mushiga ciki muyi magana dan har yanzun ina cikin duhu maganar bata nan bace ." muje ciki",bbu musu sir Aliyu yabisa a soro. bayan sun zauna baba yyi gyaran murya had'e da cewa dan Allah aliyu yimun bayani yadda zan fahimta.sir aliyu da bakinsa yak'i rufuwa dan murna ."ahankali yace baba da farko wanene kabawa auren Hafsat."bbu boye boye baba yasanar dashi yadda sukayi da senator. "Murmushi sir Aliyu yyi yace to baba nine dai aliyu dansa kuma ni yanemawa auren Hafsat". Ajiyar zuciya baba yyi had'e da cewa alhmdllh ala kulli halin.
"" agaskiya Aliyu naji Dadi kuma Nayi farinciki daka kasance Kaine zaka auri Hafsat."domin kafin mahaifinka yaxo anguwarnan har yaga Hafsat yaso nema maka aurenta wlh kai nikeda niyar cemawa inba matsala xanbaka ita dan nayaba da hankalinka da tarbiyyarka d'ari bisa d'ari to sai haka ta faru ,ashekuma Kaine mijin ,ubangiji yasa alkhairi da albarka da aurenku.
"Cikin jin kunya sir Aliyu yace ameen."
Mik'ewa baba yyi yace bara na turomaka ita dan bazan sanar da itaba ,idonta yanuna mata, nan yyi cikin gidan.
Hafsat dke d'aki ranta adagule jira take baba yakirata taje taga Wanda akace zata aura tayimishi rashin mutunci.
Kawai saiga baba yashigo bakinsa kamar gonar auduga dan murna "kallon Hafsat yyi yace kije yana soro yanajiranki", bejira amsartaba yawuce yanufi d'akinsa dama Laure bata gidan tana yawonta.
Cikin jin haushi Hafsat ta nufi soro,tun kafin ta ida isa taji kamshin turaren sir Aliyu da sauri tasaka kai asoron.turus tayi ganin sir Aliyu tsaye yakafeta da mayun idanunsa yana kallo dan soyake yafahimci Hafsat zatayi farinciki da zai kasance mijinta dan inbata nuna hakan ba shima bazai nuna yanason aurenba.
Cikin sark'ewar murya ta ke kallonsa hade da nunasa tana cewa y..yay..yaya,baka ga waniba asoron han yaxo guna dan baba yace mun yana asoro?
Kallonta yyi yace bangansaba nidai kuma nine dai bak'on da baba yace d'in!so kinyarda?
Zaro idanu tayi tace yaya Kaine da..da..maa Kaine bata k'arasaba tayi cikin gida da gudu sai dakin baba tana haki take tambayarsa da gaske sir Aliyu shine bak'onta ?
Bbu wani boye boye baba yasanar da ita komai,had'e da cewa nima Nayi mamakin hakan saidai ikon Allah yafi da hakan Dan matsayinsa na d'an masu Hali had'e da mulki banyi tunanin zai iya hudda da talakawa kamarmuba.cikin tsantsar farinciki had'e da mancewa baba nagun Hafsat ta d'aga hannunta sama tana.hawayen farinci race alhmdllh allah nagode maka da kacikamun burina,yah allah kacikamun dayan burina naga mahaifiyata ameen.babama yyi saurin cewa ameen, Aida sauri Hafsat ta rufe fuskarta dan taji kunya da baba yajita da Dan gudunta ta fito ta nufi soro gun sir Aliyu, saidai tana xuwa tasami zai shiga motar tanason tsaidashi tanajin kunya,shima juyowa yyi cikin farinciki ya kalli gidan kawai yaga Hafsat suna had'a ido tayi saurin saka tafikan hannunta ta rufe fuskarta.murmushi yyi afili yace zanciremiki wannan kunyar nan yashige motar guard din yaja sukabar anguwar.
" itakuwa Hafsat ciki ta koma murna fal aranta ",tanashiga ciki tayi alwarla tafara jera nafila dan nuna godiyarta ga allah dayabata Wanda tacire rai dasamunshi,hade dayiwa mamanta adduar allah yabaiyanata.
Bangaren sir Aliyu kuwa suna isowa gida ko parking guard din be gamaba yafito cikin d'oki yashige cikin gidan.
Mommy! Mommy!! Mommy!!!
Kawai yake k'walama kira tareda da zama kan kujera ,mommy dke kitchen suna aiki tareda masu aiki taji sir Aliyu na k'wala mata kira da sauri ta fito dg kitchen din tana cewa babana lfy?
"Murmushi yyi cikin farin ciki yace wlh mommy itace!"
"cikin mamaki mommy ta ce menene itace"?
Cikin murna da zak'uwa yasanar da mommy cewa Hafsat ce wadda zai aura Ashe,be boye mata komaiba.
Cikin fara'a mommy ta ce to alhmdllh naji Dadi sosai dama wlh jikina yabani kanada rabon aurenta da jiya saida Nayi mafarkinku ,kuna tare kaida ita harda y'an yaranku.
Murmushi sir Aliyu yyi had'e da hugging dinta yace nagode sosae mummy nah kicigaba damun addua,dungure masa kai tayi tace to sai adena mun ihu da cewa sai kayi ajalin Wanda zai aure maka mata.
Yar dariya sir Aliyu yyi yace pls mommy abar tada zancen.
Dariya tayi tace bazan bariba mujema part din mejikinnan kadubata nima nasake ganinta.
Bbu musu yabi bayan mommy suka nufi part din.
Saidai besan daliliba yaji gabansa na faduwa har suka isa part din.
Suna shiga suka sami tana bacci ,mommy takalli me aikin dke gefenmarar lfyar tace mundawo inta farka.
Kallon sir Aliyu take dataga yyi kuri da ido yana kallon mairo dukda bacci take.
" ahankali tace muje ."
Sir Aliyu dabesan tanayiba dan matar Sak irin fuskar Hafsat dinsa gareta ,mamaki yake Wannan wace irin kamace.
Mommy ce tayi saurin tab'asa race wannan tunaninfa?muje ko.
"Kafin yace wani abu har mero ta bude idanuwanta ta tashi da sauri tana kalle d'akin tana cewa inna lillahi wa inna ilaihir raju un.
Kallonsu mommy take tana k'ara kalle dakin tanacewa ina nike nan bayin Allah Ku suwanene??
0 comments:
Post a Comment