Babu abinda sukeyi sai kukan zuci dana zahiri ga bak'in ciki da k'uncin rayuwa,,, saboda suna matuk'ar k'aunar d'iyansu da gaskiya basa son ko k'uda ne ya tab'asu idan da son ransu,,, haka dai suka cigaba da jinyar yaransu tareda da basu kulawa ta musamman,,,, batare da sanin iyayensu maza ba.
Ab'angaren gidansu Maryam itama ta kamu da tsananin rashin lafiya sosai,,, wato ciwon ciki mai tsananin gaske da hanasu barcin dare shine Iya Gwamma mayya ta tura mata,,, alokacin da ciwon cikin ya fara tashi Mama Sa'ima da Mubarak hankalinsu yayi k'ololuwar tashi sosai ga zuciyarsu sai bugawa takeyi da k'arfi da k'arfi! Kallo d'aya xaka yi musu kasan basa cikin kwanciyar hankali da jin dad'i,,,idan ciwon cikin Maryam ya taso har shure shure takeyi da kukan zafi da rad'ad'in ciwo,,,, su kuma su Mama Sa'ima babu mai kama wani akan hawaye kuka kawai sukeyi cike da tsananin damuwa da bak'in cikin rayuwa,,, wata rana idan ciwon ya lafa mata harda wasa takeyi da cin abinci sosai,,, idan ciwon ya tashi kuwa haka zata kama yin fisge fisge da shure shure kamar mai aljannu har kumfa ke fitowa daga cikin bakinta,,, saboda tsananin bala'in sihiri da magagin ciwo,, kunsan wani ikon Allah shine dukansu Allah ya mantar dasu su sanar da Alhaji Suleiman irin ciwon da yake damunta,,, domin shi bayada masaniya akan komai duk lokacin da baya nan gida to alokacin ne ciwon Maryam ke tashi..
Aranar nan suna zaune gefe saman tabarma sunyi tagumi,,, ga hawaye sai kwaranya yake daga idanun Mama Sa'ima,,, shi kuma Mubarak idanunsa sunyi jawur kamar barkono saboda damuwa da bak'in ciki,,, alokacin ne ya bud'i baki dak'yar yace mata "Mama inaga fa matsalar nan ya kamata asanar da Alhaji duk abinda ake ciki gameda ciwon Maryam,, idan muka sanardashi nasan zaice muje asibiti idan mukaje can duk abinda ake ciki gameda ciwon Maryam zasu sanar damu,,, ko mi ne ne shawararki? ".
Mama Sa'ima ta fyace majina sannan tace "haka za'ayi Mubarak domin barin kashi a a ciki baya maganin yunwa,,,, kuma ya zama dole babanku yasan wannan abu ".
"nima shine na gani amma munyi shiru munata b'oyon ciwo,,, kamar bamusan zafinta ba idan shiru yayi yawa gaskiya wani ciwon yana iya shigowa bamu sani ba ".Inji Mubarak cikeda jimamin rashin lafiyar k'anwarsa Maryam.
Mama Sa'ima ta nisa tace "duk abinda ka fad'a haka ne Mubarak,,, babu k'arya a cikin maganarka Allah ubangiji yaba Maryam lafiya da itada dukkan kullumin musulmi baki d'aya,,, amma ni agaskiya wannan ciwon nata yana matuk'ar bani tsoro da fargaba,,, sai ina ganin kamar ba ciwon Allah da annabi bane ".
"amin Mamanmu kiyi hak'uri karkice haka domin kada kiyi sab'on Allah,,, dukkan abinda kikaga ya samu bawa to muk'addari ne daga Allah,,, bawa bai isa ya cutar da d'an uwansa bawa ba sai yardar Allah mad'aukakin sarki,,, shiyasa akeson mutum ya kasance mai hak'uri da tawakalli akan lamuran duniya,,, da iznin ubangiji Allah Maryam zata samu lafiya ta warke garau kamar bata tab'a yin wannan cuta ba " .Cewar Mubarak cikeda da tunani da hangen nesa.
Mama Sa'ima tace "haka ne Mubarak Allah ubangiji ya k'ara mana juriya da hak'uri da kuma tawakalli da dukkan k'addarar da zata samemu,,, ita kuma Allah ya bata lafiya ".
Mubarak yace "Amin ya rabbi ".
Mubarak ya cigaba da kwantar mata da hankali,,, tareda bata hak'uri da kalamai masu sanyaya zuciyar mai sauraro..
*Allah ubangiji ya bamu d'iya nagari masu tausayinmu ,,,,da yi mana addu'a idan babu mu a duniya*.
*********************
**Ummaru da Kabiru ne zaune suna firar duniya data mayyu,,, cikeda matuk'ar natsuwa da kwanciyar hankali..
Kabiru ne ya dubi Ummaru yace masa "abokina kana fa k'ok'ari sosai sai rage mana mayyu kakeyi a cikin garin nan,, amma har yanzu ka kasa kashe Gwamma mayya wadda ta addabi rayuwar mutanen gari da k'auyukkan dake kewaye damu ".
Ummaru d'an Sala mafarauci yace "hmmm Kabiru abin ba'a cewa komai wlh,,, kadai sha kuruminka da yardar Allah k'arshen Gwamma mayya ya kusa zuwa,,,, ai komai b'oye b'oyenta na kusa kamata in kasheta ai jinin mahaifana bazai tab'a zuba a banza ba ".
Kabiru yace "haka ne gaskiya ai ka rage mana annoba cikin garin Gumi,,, saboda ka kashe mayyu fiyeda d'ari kaga kuwa sauran da suka rage nasan basuda yawa sosai,,, ai barin irinsu Gwamma acikin Al'umma bala'i ne da tashin hankali! ".
"wama zai barta a raye cikin duniya,, ai idona idonta k'aryarta ta k'are,,, sainayi mata kisan gillah saina banbance mata tsakanin wuta da ruwa,,,, har abada babu tausayi ko rahama atsakanina da ita ".Inji Ummaru d'an Sala mafarauci cikeda tunanin rayuwarsa ta baya tareda da iyayensa.
Kabiru ya dafa kafad'ar Ummaru cikeda tsananin tausayin abokinsa,,, domin shi har azuciya yana matuk'ar k'aunar Ummaru.
Sannan yace "kayi hak'uri Ummaru domin shi mai hak'uri wata rana zai cimma nasara da ribar hak'urinsa,,,,, sannan tabbas da yardar Allah zaka kashe Gwamma mayya kamar yadda ta kashe maka iyayenka! ".
Ummaru yace "na sani ai shiyasa kaga akullum akowane lokaci acikin shiri nake,,, domin bana fatar ranar ta riskeni ba ashirye ba saboda irinsu Gwamma shahararrun mayyu dole mutum yayi musu shirin tunkararsu na musamman ".
"wannan haka yake gaskiya ai rana dubu ta b'arawo rana d'aya tamai kaya ".Inji Kabiru.
Ummaru yace "haka ne tabbas ".
¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤
Ganin irin ciwonsu Fatima yak'i ci yak'i canyewa yasa,,, uwayen hankalinsu ya k'ara d'unguma sosai gabansu sai fad'uwa yakeyi yana bugawa rassssss! Rasssss!.
Umma Nusaiba ce ta dubi Mama Nafisa cikeda raunin zuciya da damuwa,, tace "Nafisa wannan ciwon yayi yawa fa ya kamata mu sanardasu baban Fadila domin akaisu asibiti da gaggawa,,, kada muyi shiru muzo mu rasa yaranmu akan zurfin ciki da gudun laifi wurin mazajenmu ".
Mama Nafisa ta d'ago idanunta da sukayi ja akan kuka da damuwa,,, tace "ai ya zama dole mu sanardasu komi domin gujewa afkawa cikin nadama da dana sani,,, ni wallahi yanzu k'irjina sai ciwo yakeyi ga wani abu daya tokare min k'irji mai nauyi,,, sai nake ganin kamar bazasu tashi ba mutuwa zasuyi! ".
"Subhanalillah! Nafisa ba'a yanke k'auna daga rahamar ubangiji kedai keyi fatar samun sauk'i da waraka,,,nima hankalina ba kwance yake ba amma ya zamuyi sai hak'uri da dangana,,, da kuma addu'ar Allah ubangiji ya basu lafiya ".Inji Umma Nusaiba cikeda matuk'ar sanyin jiki da damuwa.
Mama Nafisa tace "amin amin ya rabbi haka ne gaskiya lamarin duniya sai hak'uri da juriya ".
"bari adauko waya akira d'aya daga cikin mazajenmu ".Cewar Umma Nusaiba ,,,,, ta tashi tsaye ta shige cikin d'akinta,,ta jima kad'an tana waya da baba Nura tana sanardashi abubuwan dake faruwa,,, baba Nura yace mata gashinan nan zuwa yanzu yanzun nan karta damu,,, tace to sannan ya katse wayar ita kuma ta fito waje tace "Nafisa ga baban Fatima nan tafe yanzu je ki shirya ki fito kafin yazo,, yana zuwa wucewa kawai zamuyi ".
"to yaya Nusaiba ".Inji Nafisa ta tashi tsaye ta shige cikin d'akinta domin ta shirya.
Babu b'ata lokaci su dukansu suka shiryo cikin kayansu masu k'yau,,, suka tsaya jiran baba Nura bada jimawa ba saiga sallamarsa shida Fadil sun shigo kusan atare suka shigowa daga cikin gidan matan suka amsa musu sallama ,, babu b'ata lokaci aka kwashi su Fatima aka sanya cikin motar baba Nura,,,Fadil ya shiga gaban mota su kuma su Mama Nafisa a bayan mota,, baba Nura yaja motarsa ya nufi hanyar zuwa asibiti..
Suna zuwa asibitin aka amshi su Fatima domin afara basu taimakon gaggawa,,, gadajensu suna kusaga juna itama Maryam har babanta da mamanta sun kawota asibiti,, baba Nura yana ganin Alhaji Suleiman suka yi musabaha suka gaisa cikeda matuk'ar girmamawa da nishad'i sosai..
Umma Nusaiba ce ta dubi Mama Sa'ima tace"a'aaaa Sa'ima kece a cikin asibiti,,, wa ye ba lafiya? ".
"hmmm Maryam ce babu lafiya wlh ".Inji Mama Sa'ima.
Umma Nusaiba tace "to Allah ubangiji ya bata lafiya mu kuma su Fadila da Fatima muka kawo basuda lafiya sosai ".
Sai da gaban Mama Sa'ima ya buga da k'arfi d'immmmm sannan ta tattaro dauriya tace "to 'yan uku duk sun kamu da rashin lafiya alokaci guda,,, Allah ubangiji ya basu lafiya yasa kuma ba abinda nake tunani bane ya faru dasu ".....
[7/10, 12:17 AM] Mugiratmusa66: 🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*MAYYA CE*
🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*✍🏻
_[Onward together]_
*Written by Mugirat Musa*
*DEDICATED TO SIS NAJER'ART*
_Bismillahir rahamanir rahim_
*MAYYA CE FANS hak'ik'a ina godiya matuk'a da comment d'inku masu dad'i sosai,,, Allah ubangiji yabar k'auna da zumunci har abada nagode masoyana*
*PAGE 29*
Saida gaban Mama Nafisa ya buga da k'arfi rassssss! Hankalinta yayi k'ololuwar tashi sosai zuciyarta tana yimata k'una da tafasa,,,, ta mik'e tsaye cikeda matuk'ar fargaba da tashin hankali tace "ban gane mi kike nufi da Allah yasa ba abinda kike tunani bane ya faru? "."Nima kaina ya d'aure wlh,,, na kasa gane inda maganarki ta dosa ".Inji Umma Nusaiba cikin tsoro da fargaba akan rashin lafiyarsu Fadila. Mama Sa'ima tayi shiru na tsawon lokaci sannan can tayi doguwar ajiyar zuciya tace "yanzu kuwa zanyi muku bayani yadda zaku fahimta sosai,, ina nufin Allah yasa ba mayya ce ta kamesu ba saboda wannan lokaci na yanzu yanada hatsari sosai,,, musamman ga yara su rink'a fita yadda suka gadama batare da mayyu sun kamesu ba "."Hmmm Allah ubangiji yasa ba mayya ce ta kamasu ba,,, dako mun shiga uku mun lalace! Wayyo ni Allah kaiconmu da wannan mummunan al'amarin daya samemu ".Inji Mama Nafisa cikeda da tashin hankali da *RUD'ANI*,,,,Umma Nusaiba tayi matuk'ar ajiyar zuciya da k'arfi! Tace "ina lillahi wa inna ilaihirraji'un! Dako haka ne gaskiya muna cikin matsalar rayuwa,,, saboda yadda mayyu suke addabar mutane agarin nan ya wuce misali,,, su kashe mutum su cinye namansa ba'a bakin komai yake ba "."karku damu idan Allah ya yarda abin zai zo mana cikin sauk'i sosai,,, zasu samu lafiya insha Allahu ".Inji Mama Sa'ima cikeda matuk'ar sanyin jiki da zullumi,,, Umma Nusaiba tace "to Allah ubangiji ya basu lafiya,,, ya kuma yaye musu abinda ke damunsu "."Amin ya rabbi ".Cewar Mama Nafisa cikin fargaba da zullumi..
*BAYAN KWANA UKU*
Jikinsu Maryam baiyi wani sauk'i ba gaskiya,,, saboda ciwon ya k'ara tsananta sosai sun k'ara bak'i da ramewa k'warai da gaske,, duk mai imani idan yayima su Fadila kallo d'aya saiya tausaya musu,,, musamman akan yadda ciwon yake hanasu barcin dare da iyayensu,,,, idan ciwonsu ya tashi har kuwwa da kururuwar zafin ciwo da rad'ad'i sukeyi! Duk asibitin gaba d'aya saiya gameda kuwwarsu da ifface iffacensu,,, kowa da yake asibitin saiya tausaya musu har zuwa ganinsu akeyi akan matuk'ar tausayawa rayuwarsu Fadila,,, ni kaina ganin yadda suka k'anjame da ramewa saida suka bani tausayi sosai,,, an canza musu yanayin kamanni sun koma kamar skeleton babu k'yawon gani,,, ganin haka ne yasa hankalin iyayensu mata da maza ya k'ara tashi fiyeda misali.
Suna zaune duk sunyi jugum sun fad'a duniyar tunani! Tashin hankali da bak'in cikin ne bayyane afuskokinsu k'arara saboda rashin natsuwa da kwanciyar hankali duk sun rame sosai. Can saiga doctor Sageer ya fito daga cikin office d'insa,,, yazo wurinsu Alhaji Suleiman dasu baba Nazifi ya kallesu na tsawon lokaci yana nazari can ya bud'i baki yace "Alhaji kaine baban Maryam? "(dayake yasan Alhaji Suleiman tun dad'ewa ).Alhaji Suleiman yace "nine Likita bokan turai ".Sageer yayi murmushi sannan yace "to ina iyayensu Fatima Nura da Fadila Nazifi suke? ".Sukace"gamu nan "atare da juna.
"OK i want see you now all of you,,, muje office akwai maganar da nakeson in sanardaku mai muhimmanci ".Inji doctor Sageer bai tsaya jiran jin maganarsu ba,, ya k'ara gaba su baba Nura da Alhaji Suleiman suka mik'e tsaye sukace matansu su jirasu yanzu zasu fito,,,, su Mama Sa'ima sukace to babu matsala Allah yasa muji alkhairi,,, baba Nazifi yace "amin "suka nufi office d'in doctor Sageer da saurinsu.
Suna shiga suka iske doctor Sageer saman kujera ga takardu masu yawa asaman table,,, yana rubuce rubuce sallamar da sukayi ne yasa ya d'ago kansa ya amsa musu cikin sakin fuska da walwala,,, yayi musu bismillah dasu zauna saman kujerin dake cikin office d'insa suka zauna.
Yayi musu duba na fahimta da natsuwa sannan yayi ajiyar zuciya yace "Alhaji Suleiman ina fatar zaku saurareni da k'yau kuyimin fahimta na natsuwa da ganuwa,,, sannan kuyi hak'uri da irin kalaman da zasu fito daga bakina ".
Alhaji Suleiman ya dubi baba Nura,,, shima baba Nura ya dubi Alhaji Suleiman sannan sukace atare "insha Allahu zamu fahimceka sannan duk abinda Allah ya k'addara mai k'yau ne ".Shi dai baba Nazifi babu abinda yace kansa aduk'e yake,,, saboda k'irjinsa sai zafi yakeyi masa sosai ga wani irin zogi da rad'ad'i da zuciyarsa keyi masa.
Doctor Sageer ya numfasa yace "agaskiya ciwon yaranku bana asibiti bane,,, domin munyi bincike bincike ta hanyoyi da dama saboda mu gano kan matsalar ciwonsu ko bakin zaren,,, amma ciwonsu yak'i ci yak'i canyewa sai k'ara cigaba yakeyi saboda haka amatsayina na doctor ina baku shawarar,,, da kuje gida ku gwada na malamai ku gani ko za'a dace ".
"Alal hak'ik'a munji dad'in bayaninka da yardar Allah zamuje mu gwada na malamai ".Inji Alhaji Suleiman cikeda matuk'ar sanyin jiki da fargaba.
Baba Nazifi ya bud'i baki dak'yar cikin rashin kwanciyar hankali da tashin hankali! Yace "babu wani taimakon da zaka iya yi mana ayanzu ".
Baba Nura ya juyo ya dubi baba Nazifi yace "haba Nazifi miyasa bakada hak'uri ne,, bakaji bayanin da yayi mana bane ko baka gamsu da bayaninsa ba? ".
Doctor Sageer ya tari numfashinsu yace "kayi hak'uri Malam Nazifi insha Allahu idan kuka gwada na islamic za'a dace,,, kudai ku dage da yawan addu'a akan Allah ubangiji ya basu lafiya "."Amin amin doctor Sageer mun gode k'warai da gaske Allah ubangiji yabar zumunci ".Inji Alhaji Suleiman.
"Amin ".Cewar baba Nura doctor Sageer ya basu hannu d'aya bayan d'aya sukayi sallama da juna,,, sannan su baba Nura suka fice daga office d'insa.
Kai tsaye wurin matansu suka wuce direct batare da b'ata lokaci ba,, suka sanarda iyalansu an sallamesu daga asibiti sun fara had'a kayansu kenan saiga nurse Umaima ta kawo musu takardar sallama,,, daga wurin doctor Sageer itace ta tayasu suka gama had'a kayayyakinsu duka,,, sukayi mata godiya sosai sannan suka shige cikin motocinsu sunka nufi hanyar komawa gidajensu,,, cikin rashin kwanciyar hankali da jimamin ciwon yaransu.
¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤
Iya Gwamma ce ta aza tukunyar tsafinta tsakar gida,,,,tana ta tsubbace tsubbacenta ga wasu irin surutai da takeyi na sihiri marasa dad'in saurare da ji,,, wani irin tururin hayak'i da rugugin tsawa fasss fasss fasss! Ya bayyana da k'arfin gaske ga wata irin razananniyar guguwa ta taso da k'arfi ta game wurin yadda ko tafin hannu ba'a iya gani akan duhu! Idanun Iya Gwamma sukayi jawur kamar wuta halshenta ya zazzago ya k'ara tsawo kamar maciji,,, jikinta gaba d'ayansa gashi ya tsiro zago zago kamar dodanniya! Can dai guguwar ta tsaya cak ta daina yawo tsawa da hayak'i suka tsaya wuri d'aya,,, tayi nuni da hannunta zuwa cikin tukunyar wani irin bak'in abu ya shige cikin tukunyar batare da b'ata lokaci saiga photonsu Maryam ya bayyana k'arara acikin tukunyar,,, duk abinda ya faru dasu tun daga lokacin da ta tura musu ciwon da kuma kaisu asibiti da komai ma saida ta gani da idanunta!.
Wata irin mahaukaciyar dariya ce ta bushe da ita sannan tace"hhhhhhhh saini Gwamma d'iyar Talatu k'usurgumar mayya na rantse da jinin mahaifiyata da kuma gadon maita! Yara yanzu kuka fara wahalar ciwo akan rashin kunyarku,,, musamman ke Fadila babu uban da ya isa ya hana in kasheki! In kashe ki!! In kashe ki!!! ".
Ta sake karanta d'alamisai na tsafi da sihiri,,, gidan gaba d'ayansa da tukunyar suka kama rawa da girgiza da k'arfi! Ga wata irin wuta jawur da ta tsago akan tsakiyar tukunyar can batare da b'ata lokaci ba boka LOK'ORO ya bayyana acikin tukunyar yana k'yalk'yalar dariya sosai!.
Iya Gwamma ta dubesa tace "boka LOK'ORO jikina ya bani na kusa mutuwa,, ajalina ya kusa gabatowa gareni! Saboda haka saina kashe yaran nan guda uku kafin inbar duniya! ".
Boka LOK'ORO yace mata "tabbas haka ne gaskiya baki fad'i k'arya ba Gwamma,,, kin kusa mutuwa har abada nima nasan bazasu tab'a barina in rayu ba,,, saboda haka ki zama cikin shiri domin Ummaru d'an Sala mafarauci yana gab da tunkaroki domin ya kasheki ya d'auki fansar jinin mahaifansa! "Da wata shegiyar murya tasa kamar tusar kare.
"zan zama cikin shiri akodayaushe ya mai girma boka LOK'ORO,,, na rantse da gadon tsafi da maita! Shima Ummaru bazai tab'a iya kasheni cikin sauk'i ba saiya sha bak'ar wuya sosai a rayuwarsa wadda bai tab'a shan irinta ba! ".Inji Iya Gwamma mayya.
Boka LOK'ORO ya bushe da mahaukaciyar dariya yace "karki damu zaki basa bak'ar wahala kafin ya zamo ajalinki! Kedai kiyi taka tsan tsan da Ummaru d'an Sala mafarauci ".Yana rufe bakinsa photon dake cikin tukunya ya b'ace b'at kamar k'iftawa da bismillah.
"to ya mai girma boka LOK'ORO zanyi biyayya agareka zan kiyaye da duk irin abinda zai biyo baya ".Cewar Iya Gwamma cikeda shed'anci da ta'addanci.
**********************
Komawarsu Alhaji Suleiman gida yasa dole kowane daga cikinsu ya tashi tsaye,,, domin ganin sun nemawa 'ya'yansu magani saboda su samu waraka daga cutar,,, haka yasa sukayi ta kashin kud'i ana kawo musu magani na malamai iri iri daban daban,, to kunsan ciwo farat d'aya yake shiga samun sauk'i kuwa da sannu sannu yake shiga,, ganin haka ne yasa hankulan iyayen suka k'ara tashi sosai! Saboda ana shan magani amma ciwon sai k'ara anzama yakeyi,, su dukansu aman jini kawai sukeyi sannan basu iya tashi a tsaye a zaune suke kashi azaune suke fitsari babu k'yawon gani.
Haka iyayen nasu mata suke cigaba da kulawa dasu tareda zubar da hawayen bak'in ciki da k'uncin rayuwa,,, domin su kansu ciwon yaran har tsoro yake basu saboda aganinsu kamar ba zasu tashi ba mutuwa zasuyi,,, hmmm duniya ina zaki damu hak'ik'a ta'asar da mayyu sukeyi da kashe rayuka cikin Al'umma baki d'aya yayi yawa sosai,,, saboda su mayyu da kuke ganinsu basuda d'igon imani da tausayi ko kad'an a cikin zuciyarsu,,, komai suna iya aikatawa domin ganin burinsu ya cika,, jama'a mu kiyaye dan Allah mu yawaita karatun qur'ani da addu'a akan neman tsari daga shairin masu sharri,,, da iznin ubangiji Allah idan mutum ya kiyaye yawan addu'a da karatun qur'ani babu abinda mayyu ko aljannu zasu iya yiwa mutum da iznin Allah........
[7/10, 11:50 PM] Mugiratmusa66: 🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*MAYYA CE*
🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*✍🏻
_[Onward together]_
*Written by Mugirat Musa*
*DEDICATED TO SIS NAJER'ART*
_Bismillahir rahamanir rahim_
*PAGE 30*
Da iznin Allah ba zasu iya cutar da mutum da komai ba,,, saboda haka mu kiyaye mu tashi tsaye da dagewa da yawan yin azkar,,,, da yardar Allah babu abinda zai iya cutardamu komai tsafinsa da sihirinsa.
Ciwon Maryam ya tsananta sosai ayanzu,,, duk da yake magani kala kala iri iri daban daban ake bata domin samun dacewa da waraka,,,, duk ta k'ara lalacewa da k'anjamewa babu k'yawon gani,,, Mama Sa'ima da Mubarak hankalinsu ya k'ara tashi matuk'a saboda irin wahalar da Maryam kesha akan wannan ciwo!.
Mama Sa'ima ce zaune tana shafar kan Maryam tana zubar da hawayen bak'in ciki da takaici,,, domin aganinta kamar ba zata warke daga wannan mummunan ciwon ba,,, Mubarak agefe yana lallashinta shima kansa idanunsa sunyi jawur jijiyoyin kansa sun tashi rud'u rud'u! Saboda rashin kwanciyar hankali da tashin hankali,,, amma ganin mahaifiyarsa tana kuka dole yasa ya b'oye damuwarsa,,, ya tattaro natsuwarsa cikin dauriya yace "kiyi hak'uri Mama ki daina zubar da hawayenki,,, babu abinda Maryam ke buk'ata yanzu idan ba addu'arki ba,,, sannan cikin tsanani akwai sauk'i komai mai wucewa ne insha Allah ".
Mama Sa'ima ta d'ago jajayen idanunta,,, b'acin rai da bak'in ciki ne k'arara akan fuskarta tace "ya zama dole in yi kuka Mubarak,,, idan Maryam ta mutu bansan yadda rayuwata zata iya kasancewa ba,, duk nice silar faruwar hakan saboda ban hanata fita ba alokacin da zataje wasa ba ".Ta sake fashewa da wani irin rikitaccen kuka mai cike da k'unci da bak'in cikin rayuwa.
"bakida laifi Mama ina son ki sani komai ya samu bawa muk'addari ne daga Allah,,, sannan wannan ciwo da ya samu Maryam *K'ADDARA CE* bakida laifi ko kad'an,, ya kamata ki daure ki sassautawa zuciyarki domin ki samu sauk'in rad'ad'i da zugin da kikeji acikin zuciyarki ".Inji Mubarak cikeda matuk'ar tausayin kansu da Maryam.
Mama Sa'ima tace "bawai ban yarda da k'addara bane Mubarak,, wallahi na yarda da k'addararmu amma har cikin zuciyata ina jin tsoron mayyu saboda zasu iya aikata komai,,, domin babu imani acikin zuciyarsu ".
Mubarak ya dafa kafad'arta yana share mata hawayenta,,, shi kansa zuciyarsa sai tafasa takeyi da k'una amma ya zama dole ya b'oye damuwarsa,,, agaban mahaifiyarsa domin kada ya k'ara tayar mata da hankali,,, shi kansa yasha b'oyewa acikin d'akinsa yana zubar da hawayen bak'in ciki da k'uncin rayuwa,,, ga tunane tunane da fargaba akan ciwon Maryam!.
Ya numfasa sannan yace "ki daina cewa haka Mama mayyu basu isa cutar da d'an Adam ba saida yardar Allah mad'aukakin sarki,,,, sannan inason ki daure ki dinga hak'uri akan wannan lamari,,, tabbas zata samu waraka ta warke kamar bata tab'a yin wannan ciwo ba ".
"Mubarak kenan nasan kana cikin damuwa,,, amma kake daurewa kana bani hak'uri tabbas kai mai albarka ne a rayuwa,,, sannan Alhaji yace zaizo da wani shahararren Malami mai suna Malam Usama,,, domin shima yayi nasa maganin ko za'a dace ".Inji Mama Sa'ima cikeda matuk'ar fargaba da zullumi!.
Mubarak ya nisa yace "za ma adace da yardar Allah dama ciwo farat d'aya yake shiga acikin jiki,,, lafiya kuma da sannu sannu take shiga jiki saboda haka ki kwantar da hankalinki,,, babu abinda zai faru sai alkhairin Allah ".
Mama Sa'ima taja doguwar ajiyar zuciya da k'arfi! Tace "haka ne gaskiya amma zan daure inga idan zan iya,,, domin kasan tsakanin uwa da d'a sai Allah ".
"tabbas haka ne Mama amma zaki iya daurewa domin gujewa kamuwa da wani ciwon ".Cewar Mubarak cikeda tausayi da *SOYAYYAR GASKIYA* na tsakanin uwa da d'a.
Mama Sa'ima tace "to zan gwada Mubarak ".
"dako kin k'yautamin mahaifiyata ".Inji Mubarak.
Mubarak ya cigaba da kwantar mata da hankali,,, tareda lallashinta yana gaya mata maganganu masu dad'i matuk'a,,, ita kanta taji bak'in ciki da rad'ad'in da takeji acikin zuciyarta ya ragu sosai saboda Allah ya bata d'a nagari na kowa..
¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤
Suma Fatima da Fadila ciwonsu ya k'ara tsananta sosai,,, duk da yake suna nan suna shan magani iri iri daban daban daga malamai kala kala,,, amma ciwon sai k'ara cigaba yakeyi,,, k'urajen da suka fitowa Fadila ajiki sun k'ara girma sosai sai wani ruwa ruwa yake fitowa daga jikinta mai shegen wari da d'oyi! Bakinta har wani kumfa yake fitarwa akodayaushe akowane lokaci idan ciwonta ya tashi.
Ciwon Fatima da Maryam yanada sauk'i bisa ga na Fadila! Saboda ciwon Fadila yafi tsanani da firgitarwa!.
Ganin haka ne yasa hankalinsu Umma Nusaiba ya k'ara tashi matuk'a!.
Mama Nafisa ce take zubar da hawayen bak'in ciki da takaicin rayuwa,,, idanunta har sun kumbura sosai akan kuka! Ga wani irin abu da takeji daya tokare mata k'irji,,, gabanta sai yawan fad'uwa yakeyi da k'arfi da k'arfi! Zuciyarta sai zafi takeyi mata sosai.
Shesshekar kuka takeyi tana cewa "wayyo Allah ni Nafisa mun shiga uku mun lalace! Ya zanyi da rayuwata da wannan mummunan al'amarin daya samemu ".
Umma Nusaiba tana jiyo kukanta da maganganunta ta fito daga sauri cikin kitchen,,, ta nufi wurin Mama Nafisa tana cewa "haba Nafisa,, haba Nafisa miyasa bakida hak'uri ne,,, miyasa baki yarda k'addara ba? Ai komai na duniya hak'uri akeyi da kuma dauriya akan abinda Allah ya k'addari bawa dashi ".
"wallahi yaya Nusaiba ba haka bane,,, zuciyata zafi da rad'ad'in ciwo takeyimin,,, hankalina yak'i kwanciya gabana sai yawan fad'uwa yakeyi,,, sannan jikina ya bani akwai mummunan k'addarar da zata samemu! Dan Allah ki fahimceni laifin zuciyata da gangar jikina ce! ".Cewar Mama Nafisa ta sake fashewa da wani irin rikitaccen kuka,,, mai ban tausayi da tsuma zuciyar mai sauraro.
Umma Nusaiba jikinta yayi matuk'ar sanyi da fargaba akan kalaman Mama Nafisa,,, ta faikaci idon Mama Nafisa ta share hawayen da yake fita daga cikin idanunta!.
Sannan ta tattaro natsuwarta da dauriya tace "kiyi hak'uri Nafisa dukkan tsanani yana tare da sauk'i,,, komai na duniya yanada farko yanada k'arshe hak'uri da yarda da k'addara shine jigon zaman duniya,, da yardar Allah zasu samu lafiya ".
Mama Nafisa tasa hannu ta share hawayenta,, sannan tace "shikenan yaya na daina kuka Allah ubangiji ya basu lafi.........."Bata k'arasa maganar ba suka jiyo kuwwa da kururuwar Fadila mai matuk'ar tashin hankali! Suka shek'a da gudu suka nufi d'akin dasu Fadila ke kwance,,, suna zuwa suka iske sai kumfa da jini ke fita daga cikin idanunta,,, sannan idanunta sai k'ak'k'afewa da juyewa sukeyi akan rad'ad'i da zafin ciwo,,, can dai Fadila ta bud'i baki dak'yar tace "Umma,, Mama duk abinda nayi muku zamana na duniya ku yafemin,,, sannan ku rok'armin gafararsu baba su yafemin duk abinda nayi musu! ".Mama Nafisa ta saki wani irin gigitaccen kuka mai cike da k'unci da tarin damuwa,,, Umma Nusaiba ce ke zubar da hawayen bak'in ciki da k'uncin rayuwa ta matso kusaga Fadila ta rik'i hannunta tace "a'aaa Fadila ki daina fad'ar wannan magana bakiyi mana komai ba,, koda kinyi mun yafe miki cuta ba mutuwa bace "."dan Allah Fadila ki daina cewa zaki tafi ki barmu zaki warke da yardar Allah,, bakiyimin laifin komai Allah ubangiji ya tashi kafad'unki ".Cewar Mama Nafisa tana kuka sosai mai tarin yawa,, Fatima dake kwance tana kuka ta amsa ak'asan mak'oshinta "amin".Fadila ce ta juyo ta kalli Fatima tana murmushi sannan tace"ina sonki Fatima keda Maryam har abada kuna cikin zuciyata da ruhina,,, ku kasance masu biyayya da ladabi ga manyanku kada ku kasance masu rashin kunya da tsiwa nasan rashin kunyata ne yaja muku silar wannan ciwon,,, ku gafarceni ya k'awayena na tub......."Bata k'arasa maganarta ba tari ne ya sark'eta idanunta suka k'ak'k'afe suna rufewa da juyawa,,, can ta kama fisge fisgen fitar rai harta mutu Mama Nafisa tana ganin abinda ya faru ta fasa razananniyar k'ara da gigitacciyar kuwwa da k'arfi! Ta fad'i k'asa ta some Fatima dake cikin ciwo numfashinta ya d'auke da sauri akan tashin hankali da magagin ciwo!.
Umma Nusaiba ta saki gigitaccen kuka mai cike da rikicewa da d'imaucewa akan rashin kwanciyar hankali da masifa! Ta kama fad'ar kalmar "ina lillillahi wa inna ilaihirraji'un!! Na shiga uku ni Nusaiba wannan bala'in dami yayi kama?,,,, dan Allah ku tashi karku tafi ku barni cikin bak'in cikin rayuwa da k'unci ".Ta shek'a da gudu ta d'auko wayarta ta dialling numbar baba Nura cikin tashin hankali da rikicewa! Tana kuka ta sanardashi abinda yake faruwa cikin gidan yace mata gashi nan zuwa shida su baba Nazifi,, ya katse wayar ita kuma ta dawo wurinsu Mama Nafisa tana wani irin rikitaccen kuka jikinta sai rawa da makarkata yakeyi akan tsoro da fargaba!.
Babu jimawa sosai sai gasu baba Nura sun shigo cikin gidan cikeda matuk'ar sanyin jiki da tashin hankali,,, damuwa ce da bak'in cikin rayuwa da ya bayyana akan fuskokinsu suna zuwa wurin gawar Fadila sukace "ina lillillahi wa inna ilaihirraji'un Allahumma ajirni fi musibati wa'akhalufni khari minha!!.
Baba Nura ne yayi k'arfin halin d'ebo ruwa ya yayyafawa Mama Nafisa da Fatima,,, sannan ya umurci Fadil da yaje ya sanarda mutane da kuma maigari abinda yake faruwa,,, Fadil ya fice da saurinsa cikeda k'unar zuciya da tashin hankali!.
Baba Nazifi ya shiga cikin wani yanayi mai cikeda tashin hankali da rikicewa! Ya kasa koda k'wakk'waran motsi akan ya shiga cikin yanayi mai ban tsoro da tausayi,,, baba Nura yaja hannunsa ya zaunar dashi sannan su Mama Nafisa suka farfad'o daga suman da sukayi,,, babu abinda yake tashi sai shasshekar kukansu cikeda matuk'ar damuwa da bak'in ciki!.
Bada jimawa ba saiga Fadil ya dawo da mutane akayiwa Fadila wanka,,, sannan baba Nura da baba Nazifi sukayiwa gawar addu'a suna zubar da hawayen tausayin kansu,, Umma Nusaiba ma tayi mata addu'a itadasu Nabila amma Mama Nafisa kasawa tayi sai kuka takeyi mai cikeda bak'in ciki da k'uncin rayuwa,, haka dai aka sallaci gawar Fadila bayan angama sallar ne aka kaita makwancinta na gaskiya!.
Aranar nan iyalan gidansu Fadila sun kwana suna zubarda hawayen rashinta da bak'in ciki mara misaltuwa,,, ita kanta Fatima da batada lafiya sai kuka takeyi cikin k'unci da bak'in cikin rayuwa.
_Duniyar kenan Allah ubangiji yasa muyi k'yakk'yawan k'arshe yasa aljanna ce makomarmu_..
*********************
Duk abinda yake faruwa Iya Gwamma tana gani acikin madubin tsafinta,,, babu abinda takeyi sai k'yalk'yalar dariyar mugunta harda fad'uwa k'asa akan makirci da k'eta,,, saboda murnar ta kashe Fadila burinta ya cika wani irin farin ruwa ke fitowa daga cikin jikinta sosai ga wata sansanyar iska mai dad'i da take buso mata,,, babu abinda takeyi sai surutai da tsafe tsafenta can ta bud'i baki tace "dama na gaya maki ba'a ja da mayyu akwana lafiya,,, saboda haka yanzu na kasheki na kashe banza sauran k'awayenki suma na gama dasu saboda ni arayuwata babu tausayi ko sassauci acikinta !".
"amma bari yanzu inje insha iska in dawo sai inzo in d'ora daga inda na tsaya! In kashesu Fatima Hhhhhh hhhhhh".Inji Iya Gwamma tana gama fad'ar wannan maganar,,, ta b'ace b'at kamar bata tab'a wanzuwa awannan wurin ba......
[7/12, 1:17 PM] Mugiratmusa66: 🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*MAYYA CE*
🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*✍🏻
_[Onward together]_
*Written by Mugirat Musa*
*DEDICATED TO SIS NAJER'ART*
_Bismillahir rahamanir rahim_
*Maman Ummi ina godiya sosai da soyayyarki gareni matuk'a da kuma halaccinki,,, hak'ik'a ke masoyiyata ce ta gaskiya kin nunamin k'auna a zahiri,, Allah ubangiji ya saka miki da mafificin alkhairi kuma ya biya miki buk'atunki na alkhairi.*
*PAGE 31*
Tana b'acewa b'at bata sauka a ko'ina ba sai a can bayan gari cikin d'an daji,,, tana bayyana a cikin dajin tayita yawonta da shawagi tana d'ebo wasu itacen da zata had'a tayi wani maganin sihiri,,, bayan ta kamalla d'iban duk abinda takeso daga cikin dajin,,, saita juyo ta fara tafiya domin komawa gidanta,,, tayi tafiya mai nisa harta kusa shiga cikin gari kwatsam! Babu zato babu tsammani taga Ummaru d'an Sala mafarauci agabanta kamar an jefosa,,, ta murza idanunta domin tabbatarwa idan ba mafarki takeyi ba,,, gabanta ya buga da k'arfi rassssss! Hankalinta yayi k'ololuwar tashi sosai amma ko a fuskarta bata nuna masa ba,,, tayi tsaye tana jiran taga irin abinda zai faru atsakaninsu. Ummaru ya dubeta yayi murmushin mugunta da jin dad'i,,, sannan yayi mata walak'antaccen kallo yace "kin gama b'oye b'oyenki da guje gujenki Gwamma mayya,,, dama na gaya miki idan kere yana yawo zabo ma yana yawo wata rana dole su had'u,,, saboda haka yanzu nan zan gana miki azaba sannan in shiga dake cikin gari kowa ya ganki a walak'ance! Sannan in kasheki kamar yadda kike kashe wasu ".Iya Gwamma ta bushe da mahaukaciyar dariya sosai sannan tace "Ummaru kenan ka d'auka kasheni abu ne mai sauk'i awurinka,,,ko ubanka Sala mafarauci na kashesa cikin sauk'i bale kai! Saboda haka k'aryarka tasha k'arya ka kaini a walak'ance cikin mutane,,, saina gana maka azabar da baka tab'a shanta ba a rayuwarka! "."yimin shiru bak'ar annoba dangin tsiya,,,, idan kin saba kashe mutane acikin sauk'i,, toni naci dubu sai ceto ba zaki iya jadani ba Gwamma azzaluma macuciya mai cin naman mutane da aljannu! ".Cewar Ummaru d'an Sala mafarauci cikeda matuk'ar hasala,,, Iya Gwamma ta dubesa da idanunta jawur kamar barkono,, jijiyoyin kanta suka tashi tsaye rud'u rud'u akan b'acin rai k'arara tace "hak'ik'a ka tafka babban kuskure daka tunkareni gaba da gaba,, yau zan shayar dakai d'acin mutuwa ayau sai dai uwarka ta haifi wani amma ba kai ba! ".Ummaru ya harareta yace "sai an gwada akan san na k'warai,, saboda haka yau zan gabatar dake durk'ushe agaban mutane domin kowa yasan Gwamma mayya,, shahararra azzaluma mara imani azuciyarta ".Kai! Ya isheka ayau zakasan ka zageni saikabi ubanka acan lahira! In yaso ka iskosa acan barzahu! "Cewar Iya Gwamma cikeda hasala da jin haushi,,, Ummaru yace "karki kuskura ki gayamin maganar banza shegiyar karuwa! Annobar gari k'are dangi,,, wadda tayi abin kunya acikin gari ".
"yanzu kuwa zan nuna maka ainahin wa ce ce Gwamma ".Ta rufe bakinta ta afka masa suka rungutsume da azababban fad'a mai cikeda tashin hankali da bala'i! Naushin juna da bugun juna kawai sukeyi cikeda matuk'ar dauriya da zafin nama,,, Ummaru yana amfani da takobinsa domin ya kare kansa yayinda Gwamma ke jifarsa da ababen tsafi irinsu wuk'a,, mashi,, wuta,, kibiyoyi da dai sauran abubuwan mugunta iri iri daban daban,,, da bala'i yayi bala'i ta dinga feso masa wuta jawur yana kaucewa,, ta k'ara karanta d'alamisai na tsafi wata irin bak'ar guguwa ta bayyana,, ta d'auki Ummaru tana hajijiya dashi asama yasha wuya sosai sannan yayi wata addu'a,,, guguwar ta b'ace b'at kamar k'iftawa da bismillah,, ganin haka ne yasa ta k'ara yin wani sihirin k'aton rami da macizai ya bayyana a tsakiyarsu! Yana bayyana igiyar tsafi ta fito daga cikin ramin ta d'aure k'afafun Ummaru tana jansa da k'arfi,, yasha bak'ar wuya sosai sannan yayi wata addu'ar ramin ya b'ace b'at kamar bai tab'a wanzuwa ba! Iya Gwamma ganin ya tsira ne yasa ta k'ara harzuk'a da hasala ta feso masa ruwa tafasasshi suka zuba ajikinsa! Ummaru yayi kuwwa da kururuwar da k'arfi akan zafi da rad'ad'in ciwon ruwan zafi,, fatarsa jikinsa ta fara kwayewa akan masifa ganin ya fad'i d'immmmm ak'asa yasa Iya Gwamma ta bushe da mahaukaciyar dariya sosai tace "bazaka iya ja dani ba Ummaru,,, ubanka ma baisha d'a dad'i ba a wajena! ".Tana gama yin magana ya taso cikeda matuk'ar zafin nama ya naushi fuskar Iya Gwamma cikin shammata,, ai kuwa ta fasa gigitacciyar k'ara da kuwwa da k'arfi! Bakinta ya fashe da jini tasa hannunta ta lakato jinin dake zuba daga cikin bakinta,, tana ganin abinda ya faru da ita rayuwarta ta k'ara b'aci idanunta suka k'ara ja ta girgiza sannan ta rikid'a ta koma gwaggon biri,,, ta sake afkawa Ummaru suka sake rungutsumewa da wani rikitaccen fad'a cike da bak'in rai da mugun nufi! Dajin gaba d'aya ya kama girgiza da rawa tanbal tanbal kamar zai kife acikin k'asa,, masifa tayi masifa bala'i yayi bala'i dajin gaba d'ayansa ya kama da wuta yana k'onewa,,,tsuntsaye da dabbobi sai hijira sukeyi suna barin dajin baki d'ayansa.
Haka dai suka cigaba da azababben fad'a cikeda tashin hankali! Ummaru ganin wankin hulla zai kaishi dare yasa ya k'ara k'aimi,, tareda tattaro dauriya da zafin namansa ya chanza salon fad'ansa nan da nan ya rikita hankalin Iya Gwamma,, ya samu ya yanketa a cinyar k'afar dama ihu da kururuwar Gwamma kawai kakeji ta fad'i k'asa cikeda matuk'ar zafi da rad'ad'in ciwo! Ummaru yayi hanzari da sauri yasa igiya ya d'aure Gwamma,,,, ya d'auketa ya azata saman kafad'unsa ya nufi hanyar zuwa cikin gari fadar maigari Garba.
********************
Alhaji Suleiman da Mama Sa'ima sunje gaisuwar rasuwar Fadila cikeda jimamin mutuwa da sanyin jiki,, anan ne suke k'ara jajantawa juna hak'ik'a Mama Nafisa tayi matuk'ar basu tausayi sosai,,, saboda duk ta fita acikin hayyacinta kallo d'aya zaka yi mata kasan tana cikin rad'ad'in zafin mutuwar Fadila,, anan ne Alhaji Suleiman yake sanarda baba Nura akwai Malam Usama da zaizo gidansa yayiwa su Fatima magani,,, baba Nura ya nuna babu matsala ya umurci Fadil daya d'auki Fatima ya sanyata cikin motar Alhaji Suleiman,, Fadil ya d'auki fatima ya sanyata cikin motar baban Maryam,, shima ya zauna bayan motar rungume da Fatima Alhaji Suleiman yaja motarsa suka wuce direct zuwa gida.
Ya parker motarsa a waje sannan suka fito daga cikin motar gaba d'ayansu,, Fadil ya d'auko Fatima daga cikin motar suka nufi cikin gidan suna shiga suka iske Malam Usama zaune,, Alhaji Suleiman yayi murmushi tareda bayyanar da farin cikinsa da fara'arsa,, yaje wurin Malam Usama sukayi musabaha da sallama da juna,, Mama Sa'ima ta shige cikin d'akinta.
Malam Usama ya aje casbaharsa da qur'ani agefe,,, ya kalli Alhaji Suleiman yace "akawomin ruwa masu tsabta yanzun nan ".
Alhaji Suleiman yace" to Malam Fadil jeka ka kira Maman Maryam sannan kace tazo da ruwa masu k'yau".
Fadil yace "to baba ".Tareda mik'ewa tsaye ya nufi hanyar zuwa d'akin Mama Sa'ima,, babu jimawa sosai saiga Mama Sa'ima ta fito tareda Fadil d'auke da jug d'in ruwa a hannunta,, suna isowa ta aje ruwan agaban Malam Usama ta koma gefe ta zauna.
Malam Usama ya d'auki ruwan ya fara karatun qur'ani da addu'o'i na tsari da sihiri,, ya jima sosai yana yin addu'ar sannan daga baya ya tsaya ya d'auko gagarin maganin ya zuba acikin ruwan yana jijjigewa da sauri,,, yana gama jijjigar ruwan maganin ya watsasu ajikin Maryam da Fatima ,,,ai kuwa batare da b'ata lokaci ba sukayi wani irin gigitacciyar k'ara da kuwwa da k'arfi! Suka kama zabure zabure da shure shuren zafin magani,,, Malam Usama ya cigaba da yi musu karatun qur'ani da addu'o'i kala kala,,, kuwwa da kururuwarsu Maryam kawai ke tashi acikin parlourn su Mama Sa'ima jikinsu sai rawar tsoro yakeyi itada Fadil cikeda matuk'ar firgita da fargaba! Ya dad'e sosai yana yi musu karatu sannan daga baya kowacessu tayi atishawa da k'arfi sau uku nan da nan barci ya d'aukesu batare da b'ata lokaci ba.
Malam Usama yayi murmushi sannan yace "Alhmdlilah yaran sun samu lafiya Alhaji Suleiman dama mayya ce ta kamasu,,, sannan ta had'asu da miyagun aljanu domin kada suyi saurin samun waraka,, yanzu dai godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikkai wanda ya bani ikon k'ona aljannu da yardar Allah,,,, shikenan da sun tashi daga barci sun warke har abada,,, zan basu wani turare da garin maganin da zasu cigaba da shafawa garin kuma wanka akeyi dashi ".Yasa hannun cikin leda ya d'auko turare kwalba biyu garin magani leda biyu,,, kowacce su d'ai d'aya.
Tsananin farin ciki da murna ne suka bayyana a fuskokinsu k'arara mara misaltuwa,, Mama Sa'ima hawayen dad'i ne suka cigaba da kwaranya daga cikin idanunta,, Fadil ma sai kwallar murna yake fitarwa,, Mubarak daya shigo ayanzu cikin parlour amma yaji abinda Malam ya fad'a bakinsa yak'i rufawa akan murna da farin ciki sosai,, ya samu wuri kusa ga Fadil ya zauna fuskarsa d'auke da farin ciki da nishad'i sosai.
Alhaji Suleiman akan farin cikin dake d'auke afuskarsa har rungume Malam Usama yayi yanata zuba masa godiya,,, tareda da kwararo masa addu'o'i na gamawa lafiya. Can ya bud'i baki yace "hak'ik'a godiya ta tabbata ga Allah ubangijin sammai da k'assai wanda yake sanya ciwo alokacin da yaso,, sannan ya warkar da bawa aduk lokacin da yaga dama,, Malam Usama mun gode sosai Allah ubangiji ya saka maka da mafificin alkhairi yasa ka gama da duniya lafiya ".
Gaba d'ayansu yan parlourn sukace "amin amin ".Fuskokinsu d'auke da farin ciki da nishad'i sosai k'arara,, daga gani babu tambaya kasan suna cikin jin dad'i da farin ciki sosai.
"wannan ba wani abu bane Alhaji ai an zama d'aya,, Allah ubangiji dai ya tsare gaba ni yanzu zan wuce zuwa gida ".Ya aje ledar maganin ya tashi tsaye ya nufi hanyar fita daga cikin parlorn,, Alhaji Suleiman ne ya bisa a baya domin yayi masa rakiya,, bayan sunje waje ne Alhaji Suleiman ya bashi kud'i masu yawa wanda shi kansa baisan ko nawa bane,, dak'yar Malam Usama ya amsa sannan sukayi sallama da juna ya shige cikin motarsa,, Alhaji Suleiman shi ko ya juya zuwa cikin gidansa fuskarsa d'auke da farin ciki da annashuwa mara misaltuwa.
¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤
Ummaru d'an Sala mafarauci d'auke da Iya Gwamma akafad'arsa,, ya kawota ya ajeta saman k'asa agarkar maigari Garba cikin halin somewa,, jini sai zuba yakeyi daga cinyarta yana ajeta saman k'asa,, ya shiga cikin gidan maigari ya jima sosai sannan suka fito tareda da maigari da dogarawansa,, nan da nan maigari yasa akayi sanarwa acikin gari kowa da kowa ya taru mata da maza,,, yara da manya da tsofaffi,, bayan mutane gaba d'aya sun gama taruwa wani dogari ya ciko bokiti da ruwa aka juyesu ajikin Iya Gwamma mayya,,, batare da b'ata lokaci ba ta farfad'o daga suman da tayi jikinta d'aure da igiya,, kallon mutane kawai takeyi d'aya bayan d'aya,,,Maigari ne yayi gyaran murya sannan yace "muna godiya ga Allah daya bama Ummaru nasarar kama wannan k'usurgumar mayya wadda ta addabi rayuwar mutanen gari shekara da shekaru,, ta dad'e tana cin amana da zaluntar mutane da dama ta kashe mana iyaye,,mata,,,,'yan uwa,,, yara da abokan arzik'i,,,, dama duk abinda kakeyi wata rana sai dubunka ya cika komai yayi farko k'arshensa yana nan zuwa,,, mai hak'uri mawadaci ne saboda haka gashi yanxu Allah ya tona asirin Gwamma an kamata !Dama na gaya muku duk wadda /wanda aka kama yana yin maita hukuncin kisa shine ya kamacesa,,, saboda haka yanzu nan za'a yankewa Gwamma hukunci dai dai da abinda ta aikata,, ina dogari Tukur ne yake? ".
Tukur ya matso da sauri kusa ga maigari ya durk'usa yace "gani rankashi dad'e ".
"kaje cikin gida ka d'auko fetur da tayar mota yanzun nan ka kawomin ".Inji maigari. Tukur yace "angama ranka ya dad'e ".Ya mike zubur da saurinsa ya shige cikin gidan maigari Garba.
.
Maigari ne ya bada umurnin a d'auki Iya Gwamma amatsa da ita kusaga icce a d'aureta,, nan da nan aka cika umurnin maigari tareda daureta tamau ga icce,, Iya Gwamma sai kuwwa da kururuwa takeyi tana cewa "ku sakeni ku sakeni wallahi idan na kwance kaina duk saina kasheku,, saina kasheku ! Nayi alk'awarin bazan bar ko d'aya daga cikinku ya rayu yaji dad'i ba,, Garba tsohon munafiki dakai zan fara kaida shegen yaron nan Ummaru! ".Haka dai suka d'auketa d'aureta ga iccen,, bada jimawa ba saiga Tukur ya fito da tayar mota da fetur yana kawowa Ummaru ya amshi tayar da fetur,,, ya sanyawa Gwamma taya a wuya sannan ya dubeta yana murmushin mugunta yace"dama na gaya maki duk daren dad'ewa saina kamaki da hannuna,, shiyasa akeson mutum ya kasance mai aikata alkhairi akodayaushe akowane lokaci baki tab'a jin ance gaskiyarka ta k'are ba,, sai dai ace k'aryarka ta k'are saboda haka yanzu nan zan aikaki can inda kika saba aika mutane da dama ".Gwamma ta kama kuwwa da k'arfi tana kuka tana cewa "wallahi baka isa ba nice zan kasheka da hannuna,, saina kashe duka mutanen garin nan saboda su suka duka munafukan......... ".Bata k'arasa maganar ba ya kyasta ashana tareda zuba mata fetur ajiki,,, Iya Gwamma ta saki wani irin gigitaccen kuka tana cewa "kada ku kasheni wallahi duk sainaga bayanku,,, saina zare muku rai daga cikin gangar jikinku wayyo Allah ni Gwamma na shiga uku na lalace! ".....haka dai wuta ya cigaba da cin jikinta bal bal bal sosai sai kuwwa da kururuwar neman agajin gaggawa takeyi,, mutane sai kuwwace-kuwwace sukeyi na tsananin farin ciki da murna sosai,, kowanensu ka kalli fuskarsa farin ciki da murna ne bayyane afuskokinsu saboda ganin k'arshen Iya Gwamma,, Hassan ne na hango wani wuri zaune.......
[7/12, 1:46 PM] Mugiratmusa66: 🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*MAYYA CE*
🍥🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥🍥
🍥🍥🍥
🍥🍥
🍥
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*✍🏻
_[Onward together]_
*Written by Mugirat Musa*
*DEDICATED TO SIS NAJER'ART*
_Bismillahir rahamanir rahim_
*Ina godiya sosai matuk'a da soyayyarku da kuma k'aunarku gareni,, hak'ik'a ina matuk'ar farin ciki da kasancewarku acikin group d'ina saboda kuna sanyani cikin nishad'i da farin ciki mara misaltuwa.*
*Maman Haneef*
*Suwaiba Danabu*
*Maman twince*
*Ummu Shaheeda*
*Maman Hanifa*
*Ummu Usman*
*Maman baffa*
*Aishat Salisu*
*Ummeen Amatullah*
*His priceless jewel*
*Mom Hauwee*
*Khadijat Lookman*
*Hajja Saki*
*Ayshat*
*Firdausi Muhammad da duk sauran wad'anda ban ambata ba ina godiya sosai matuk'a sister's.*
*LAST PAGE*
*PAGE 32*
Hassan ne na tsinkayo yayi zaune yana tagumi,,, hawayen bak'in ciki da k'uncin rayuwa sai shatata yakeyi daga cikin fuskarsa,,, jijiyoyin kansa sun tashi rud'u rud'u idanunsa sunyi jawur kamar barkono,,, baba Labbo ma kwallar takaici da bak'in cikin rayuwa ne ke zuba daga cikin idanunsa,,, tausayin Iya Gwamma ne da takaici ya mamaye zuciyarsa ga wani abu ya tokare masa acikin k'irjinsa,, Suhaila tana ganin irin kisan gillah da walak'ancin da akayiwa mahaifiyarta ta fasa gigitacciyar k'ara da razananniyar kururuwa da kuwwa da k'arfi! Wani irin kukan bak'in ciki da k'uncin rayuwa takeyi da k'arfi nan da nan ta kama fisge fisge kamar mahaukaciya sabon kamu,, 'yan uwanta mata sukazo zasu rik'eta cak numfashinta ya d'auke ta fad'i k'asa d'immmmm ta some,,,, ina lillahi wa inna ilaihirraji'un!!! Kawai mutanen wurin suke fad'a tana fad'uwa mata 'yan uwanta suka d'auketa sukayi gidan mijinta da ita!..
Tokar gawar tana gama k'onewa,, wata irin mahaukaciyar guguwa da razananniyar tsawa suka bayyana k'arara atare,,, mutane da suketa kuwwace-kuwwace da yin farin ciki da murna akan mutuwar Gwamma mayya,,, guguwar ta fara d'iban mutane tana yassuwa k'asa rikcham da majinjiwa dasu,,, mutane suna ganin irin abinda ke faruwa kowa yace k'afa mi naci ban baki ba suka ranci na kare dimm dimm dimm,,, kawai ke tashi k'arar gudunsu!. Guguwar ta daina bin mutane ta tashi sama ta lulluk'a a cikin sararin samaniya ta nufi hanyar zuwa gidan boka LOK'ORO da saurinta!.
Boka LOK'ORO yana zaune kwatsam tokar gawar Iya Gwamma,,,tazo ta shige cikin jikinsa da sauri boka ya buga wata irin gigitacciyar k'ara da mahaukaciyar kuwwa! Yana cewa "ni boka LOK'ORO na shiga uku na lalace! Banyi kaina adalci ba saboda arayuwata ban aikata alkhairi ba,,, gashin tokar shegiyar nan Gwamma mayya tazo xata kasheni,, domin Ummaru ya k'oneta da ranta wayyo Allah wayyo Allah na tuba kiyimin rai! Baxan sake aikata mummunan dabi'a da kashe mutane ba,, yau ni boka LOK'ORO naga takaina yau nayi mugun gan..... ".Bai k'arasa maganar ba jini da mugun tari ne ya sark'esa ya fad'i kwance k'asa yana shure shuren mutuwa da kakarin fitar rai! Sai da jini gunduwa gunduwa ya zuba sosai acikin bakinsa sannan ya fad'i k'asa d'immmmm ya mutu,,, aikuwa nan da nan batare da b'ata lokaci ba gawarsa ta kama wuta bal bal bal tana ci! Sai da wutar ta k'onesa k'urumumus ya zama toka,,, acikin tokar kana hango macijizai da kunamai suna yawo wurin ya gameda wani irin mahaukacin wari da d'oyin masifa da bala'i!.
Wa iyazubillah ina lillillahi wa inna ilaihirraji'un!!! Allah ubangiji ya rabamu da aikata shirka ya kuma sa muyi k'yakk'yawan k'arshe.
********************
Bayan wani lokaci ne su Maryam da Fatima sun warke garau kamar basu tab'a yin irin wannan ciwo ba,,, suka cigaba da zuwa makaranta da kuma rage yawon banza,,, da sukaji cewa Fadila ta mutu ta barsu suka kama yin kuka babu mai kama wani,,, aranar sunyi kuka fiye da tunanin mai tunani idanunsu sukayi jawur akan bak'in ciki da rashin Fadila,, iyayensu ne suke lallashinsu tareda basu kalamai masu dad'i har suka dangana suka barwa Allah komai.
Mama Nafisa da baba Nazifi,, Fadil sun hak'ura da dangana akan rashin Fadila saboda sunsan Allah da yabasu ita yafisu sonta ya amshi ran abarsa,,, saboda haka ne suka cigaba da binta da addu'o'i da yawan karatun qur'ani domin ta samu rahamar ubangiji Allah..
Bayan mutuwar Iya Gwamma mutane suka cigaba da gudanar da rayuwarsu cikeda matuk'ar farin ciki da kwanciyar hankali,,, komai zasuyi cikin natsuwa sukeyinsa saboda sunsan an riga an kashe Gwamma mayya wadda ta addabi rayuwar mutane da aljannu! Sai godiya da addu'a sukayiwa Ummaru d'an Sala mafarauci akan irin k'ok'arin da yayi wurin kamata da hannunsa da kuma nuna matuk'ar jarumta,,, garin ya dawo dai dai farin ciki,, annashuwa,, jin dad'i,, walwala,, nishad'i,, da dai sauransu duk sun dawo cikin garin Gumi..
*ALHAMDULILLAHI.*
Duka anan ne na kawo k'arshen wannan littafi nawa mai suna *MAYYA CE*,,, da fatar mutane zasu d'auki darasin dake cikinsa su watsar da abinda nayi kuskure,,, sannan alal hak'ik'a maganar mayyu gaskiya ce bawai k'age ne nayi ba,, naman mutane sukeci dana aljannu babu k'arya.
Ina rok'on Allah ubangiji ya yafe mini kurakurren da nayi acikin wannan littafi,,, abinda nayi dai dai Allah ubangiji ya bani sakamako mai k'yau.
Godiya ta tabbata ga Allah mad'aukakin sarki wanda ya bani ikon gama wannan littafi lafiya,, ina mai numfashi da cikakkiyar lafiya sannan ina godiya ga dukkan masoyana masu bibiyar labarina da k'aunar wannan novel nawa.
*Ina godiya sosai da mik'a dubun gaisuwa ta ga wannan k'ungiya tamu mai tarin albarka,, INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION kungiya d'aya tamkar dubu wadda ta tara shahararrun marubuta masu matuk'ar ilmi,, hazak'a,, fasaha da kuma iya tsara labari mai fad'akarwa da nishad'antarwa,, ilimantarwa Allah ubangiji ya k'ara d'aukakaku yasa kufi haka shahara da d'aukaka har k'arshen rayuwarku,, ya kareku daga sharrin mahassada da mak'iya..*
_Ni Mugirat ina muku fatar alkhairi a rayuwa masoyana,,, sai kun jini asabon novel d'ina mai suna *SOYAYYAR GASKIYA* nan ba dad'ewa ba...._
Mugirat ce
0 comments:
Post a Comment