🖊Na marubuciya husna kabir zarewa (the mammah girl)
🖊Da sunan Allah mai rahma mai jinkai.......
Inama dukkanin masoya manzan allah (s.a.w) fatan alkhairi arayuwar Ku dafatan zaku bani hadin kai da goyan baya domin gani nakare wannan littafin nawa asa'a kuma Allah yabamu ikon aiki da abinda ke cikinsa na alkhairi ameen...
idan nayi kuskure ina fata zaku tunatar dani daga mai sanku ako da yaushe HUSNA ( the mammah girl)
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
1⃣⏭5⃣
Kuance take akan gado ta rufa da bargo baccinta take hankali kuance Wata kekkyawar mata ce tashigo dakin wadda akalla shekarunta baza su wuce 45 ba bargo ta janye tare dakiran sunanta Asma'u!!! ke Asma'u wai bazaki tashi bane baccin yasa isa haka rana fa tafito
Cikin muryar bacci take fadin
Umma Dan Allah kidan barni minti biyar kawai zan kara Umma tayi murmushi tace tun dazu kike fadin minti 5 dinnan kizo kikai mun nikan nan insamu inyi kosan nan kar Kuyi Lattin makaranta Asma'u bata ce komai kuma bata motsa ba ganin haka yasa Umma tanufi hanyar fita daga dakin tana fadin to bari ma kawai in tashi khadeeja ta yo mun nikan ai kafin Umma tarufe baki tuni Asma'u ta diro daga kan gadon a'a Umma base kin tashe taba zan je dakaina Umma tayi murmushi tafita daga dakin Asma'u bayi tawuce tana mutsitsike ido
Bayan kamar minti 10 tafito kitchen tanufa ta iske Umma ta ijeye mata robar nikan da kudin akai ta dauka ta wuce daga gidan Asma'u kenan kekkyawa ta bugawa ajarida shekarun baza su wuce 20 ba tana da tsayi daidai guarguado tana kyan jiki ta yadda ko mace takalleta se takara kallonta tanada far'a Da son mutane ba komai ne yake bata mata rai ba tana da hakuri da kaw dakai wannan kenan....
Daga wanka yafito da towel daure akugunsa da wani Dan karami akan sa yana goge gashin kansa wayarsa ce tayi kara bai kula ta ba se da takusa katsewa yana daga tare da amsa sallamar da aka mishi ban ji me aka ce tadayan ban garan ba naji yace mu hadu a office tare da ijiye wayar ya ci gaba da shirinsa yana gamawa ya fito daga bangaran sa ya sauko kasa se alokacin naga Ashe babban gida ne ba na wasa ba daga kasa akwai katon falon da girmansa ya kai na wani gidan tsayawa fadan tsaruwar falon bata lokaci ne akwai dakuna sunfi talatin akasa se matattakalai kuda biyu daya yayi dama daya kuma hagu acan sama ma dakuna barkatai abun dai sai Wanda ya gani da gani kai kasan dukiya ta yi kuka awurin domin idan baka fito za ka dauka akasar waje kake....
Yana saukowa kasa ba kowa afalon se masu aiki da suke kai kawo direct wani bangare yanufa anan kasan Shiva yayi tare dayin sallama wata dattijuwa ce zaune akasan kapet din falon tana cin abinci ta na ganinsa ta fadada far'arta ta amsa mishi sallama tare dafadin ABID katashi??
Karasowa yayi kusa da ita ya zauna tare dafin eh GRANY ina kuana tace lafiya kalau ga abincin ka can a dining kasan ni Nafi son kasan nan murmushi yayi tare da wucewa dining din yafara zuba abinci
ABID kenan wankan tarwada ne dogo mai dan matsakaicin jiki kyakkyawa bana wasa ba
yafara ci abinci kenan kenan wata matashiya ce da shekarunta bazasu wuce 22 tashigo falon tare da sallama grany ce ta amsa batare data dago takalleta ba itama yarinyar bata kalli grany tawuce direct zuwa dining tana sanye da farad doguwar riga tamata Kew sosai tana isa dining din taja kujere ta zauna tare da fadin good morning bro ABID yadago murmushi dauke afuskar shi ya amsa da morning KANWATA kin tashi?? murmushi tare da cewa yaya ina alkawari na yace name fan!!!?
Shagwabe fuska tayi tace yaya tafiyan dazamuyi ni da aysha mana
Yace to ai nace se kinfara girmama grany kuma ni banga kinfara ba
Yaya Allah nafara bakaga da nashigo namata sallama ba zai yi magana carab grany ta ce yo da kika mun sallama kin kalli inda nake ne bare ma ki gaidani sallaman ma daba Dan kinsan ABID na nan ba ai da bakiyi ta ba kuma ma wai uban me zaku je kuyi a London duka duka yaushe kuka dawo
ABID laifinka ne wallahi kai kasangarta SARAH abinda take so shi lake mata shi yasa kwata kwata bata ganin girmana
Sarah ta hade fuska takalli ABID tace yanzu yaya maganar nan se da kagayawa grant bayan kasan idan ta grany ne ko abincin gidan nan se naroka za'abani tana gama fadan haka ta fice daga palon grany tabita da harara
ABID ma tashi yayi ya dauki wayoyinsa yama grany sallama yana fita direct wurin motocinsa ya nufa motocin sun fi goma kowa da kalarta amma bakake sunfi yawa bodyguard dinsa suna gani ya fito suka mike suna mika gaisuwa sannan aka fito da motoci biyar bakake guda hudu sunsa fara daya atsakiya wurin farar yanufa aka bude mashi baya ya shiga suma suka shiga sauran aka wangale masu katon gate din gidan suka fice
ASM'U ce tadawo daga kai nikan a kitchen ta isko Umma tana dama koko Umma tace kindawo??
Eh Umma nadawo khadeeja ta tashi Umma tace a'a kema kinsan tashin khadeeja ai sai ke damma tace yau se 10 takeda lectures ai da tamakara
To ummah bari in tasheta dakin da khadeeja taken tanufa ta tura kufar tashiga tare da sallama tana kuance tana baccinta tsaye tayi tana kallonta tana murmushi ahankali takarasa ta zauna bakin gadon ta Dora hannunta akan khadija tana kiran sunanta khdy!!!
khadeeja takara gyara kuanciyanta taja bargo Asma'u tayi murmushi taje ta zuge labule rana ta haska fuskan khadeeja takara jan bargo ta rufe fuskanta cikin muryan shagwaba Ahmm Ahmm amma kibarni inyi bacci matsowa kusa da ita tayi tadagota tana fadin khdy zakiyi latti garama kitashi kafin Umma tazo da ruwan sanyi tashi tayi tana zumbure baki tashiga bayi Asma'u tabita da murmushi ta bude drowan khadeeja ta fito mata da uniform da jakanta ta dauko mata takalminta da safa ta ajiye mata kana tawuce kitchen tana taya Umma suyan kosai bayan sun gama ta zuba kosai a plate ta zuba kunu a cup ta koma dakin khadeeja ta iske khadeeja ta gama sa uniform ta na sa takalminta na makaranta Asma'u ta ijeyi plate din hannunta kan dressing mirror ta natso ta karba takalmin hannun hkadeeja ta tsugunna tafara saka mata khadeeja dai se binta take da ido har tagama saka mata ta dago suka hada ido Asma'u tace kallon fah khadeeja tai murmushi batace komai tadauki kosan da kunu tafara sha Umma tana zaune apalo suka fito khadeeja taje ta rugumeta tace Umma ina kuana Umma hmm ni dagani yanzu kuma ai saidai ai zancan wuni ina tunanin ranarda Asma'u zatayi aure bansan ya zakiyi ba khdeeja Ta shagwabe fuka tace ai tare zamu tafi ko yaya Asma'u tai murmushi sosai ma KANWATA khadeeja ta tashi ta musu sallama ta fita asma'u ma ta wuce dakinta ta shirya tama Umma sallama ta fita
Hkadeeja kanwa ce awurin Asma'u suna kama sosai sedai ita khadeeja wankan tarwada sabanin Asma'u fake fara shekarun khadeeja 17 tana ajin karshe a scndry school asma'u kuma level 200 a gwagwalada university fake nan abuja su biyu iyayensu suka Haifa asma'u tana bala'in son khadeeja tun tana karama tazama tamkar uwa agareta khadeeja tasha yin laifi amma Asma'u se tace ita tayi kawai dan kar adaki khadeeja zata iya yin komai AKAN khadeeja
baban su bakano ne se kuma mamansu bafulatanar Adamawa ce suna zaune a unguwar life camp dake abuja ba wasu masu hali bane se dai rufin asiri da wadatar zuci babansu Allah ya yimai rasuwa tun khadeeja tana Karama ada mamansu taso takoma garinsu dayaran amma yayan babansu yahana Wanda yake anan abujan shima dazama yana da mata da yara 2 nusaiba da fa'iz Se mamanshi datake zaune agidan shi wato kakar su asma'u kenan
To wannan dalilin ne yasa Umma take zaune a abuja saboda bazata iya Barin yaranta tatafi ba
Da yamma misalin karfe 5 Motocin ABID suka shigo haraban gidan ana gama parking dai daga cikin guards dinshi yazo yabude mashi baya yafito cikin takunshi na kasaita ya karasa cikin babban palon gidan yana shiga ya iske palon a cike da ain gidan kasancewar gidan family house ne duka aciki family suke
tuna baya!!!!!!
alh Kabiru hausaweee haifaffan garin yola ne su biyar ne awajan iyayan su maza 3 mata biyu amma biyu sun rasu su uku suka rage shine babba se kanin jamilu da kuma kanwarsa ladidi duk da cewa alh kabiru yayi karatu sosai amma harkar kasuwanci ya sama gaba tun yana karami haka yataso wannan dalilin ne yasa aminin mahaifinsa yadawko shi daga yola yadawo dashi Abuja Dan yarika taya shi harkar kasuwan cin sa ganin kwazo da kuma experience dinsa ne yasa ya Dora shi aharkar kasuwancin su inda yake tura shi kasashan waje kan harkar kasuwancin su wani zuwa da alh kabiru yayi kasar yaman ya shafe kimanin watanni 5 yahadu da hafsat diyar abokin kasuwancinsu suka kulla soyayya da yarinyar daga bisani maganar aure tashigo ciki sunsha gwagwar Maya ba kadan ba kafin iyayansu su yarda da zancan auran amma abunda Allah ya qaddara se ya faru
Haka akayi auran ya taho da ita Nigeria arzikinsa Yanata habaka sun samu karuwar da namiji inda aksamishi sunan baban Hafsat wato ABID bayan rasuwar mahaifin alh kabiru wata rana yaje gida ya isko kananshi ya saida gidan da suke ciki ya barnatar da kudin ganin haka ne yasa yadawko shi da mamansu suka dawo abuja ya maidashi makaranta dama ladidi tayi aure a can yola
Bayan wani lokaci alh kabiru suka sake samun karuwa ta ai mace inda taci sunan Sarah
Batare da sanin kowa ba alh kabiru yafara Gina wani katafaran gida da kyakkyawar niyyansa ta hada family dinshi wuri guda seda yakammala gidan sannan ya Sanar dasu suka tattara suka koma murna wurinsu ba magana se ma dasuka ga gidan aljannar duniya
Haka suka ci gaba dazama acikin wannan gidan cikin farin ciki da kaunar juna har kanin alh kabiru wato jamilu yayi aure ya auri sadiya wata diyar kawunsu itama aka kawota wannan gidan
Wata rana alh kabiru ya shirya tafiya yola ganin dangi shi da matarsa wato Hafsat akabar su ABID awurin hjy Maryam mamar alh kabiru ahanyar su tadawowa ne sukayi hatsari Wanda wannan shine dalilin rasuwarsu family ya girgiza da wannan al'amari kasancewar alh kabiru mutum me mai zumunci da son talakawa bayan rasuwar ne baban Hafsat ya zo yace abashi amma hjy Maryam tayi mirsisi tahana da kyar yasamu tabashi Sarah yatafi da ita ABID kuma ya zauna awurin hjy Maryam wato (grany) kenan
Haka taci gaba da kula dashi da karatunsa inda yagaji mahaifinsa wato kasuwanci haka yataso yana masifan son garny da kuma Sarah duk abunda suke so zai yi kokarin yaga ya musu indai baifi karfinsa ba
Ko bayan rasuwar alh kabiru family bai watse ba ABID yana iya kokarinsa wajan ganin yahada kan family din wannan dalilin ne yasa ya je yadawko ladidi da yaranta 5 kasacewar mijinta yarasu haka kuma yaje yaman yadawo da Sarah Nigeria
Cigaban labari!!!
karasawa yayi cikin palon ya zauna kusa da grany suka gaisa da sauran mutanan gidan Sarah ce tazo tazauna kusa dashi tace yaya yau ranar family meeting ne murmushi yayi yace nasani KANWATA ai dai kyabari inje inyi wanka inci abinci ko ?? Languabar da kai tayi tace to yaya tashi na kosa afara grany tamaka mata harara tace ai dama dole ki kosa tunda kina so kuje yawan gantali
Shuru tayi ta hade fuska batace komai ba
Daga nan kuma kowa yayi shuru a palon ABID ne ya katse shurun da cewa bari in je inshirya in fito nan fa kowa ya wangale baki tare da fadin to shi kuma ya haura sama yanufi bangaransa
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
🖊na marubuciya HUSNA kabir zarewa( the mammah girl)
🖊 da sunan Allah mai Rahma mai jinkai....
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
5⃣⏭1⃣0⃣
Ahankali yake takunsa har ya isa bangaran sa mamaki ne ya kamashi ganin palon shi abude can kuma yayi murmushi yace hmm nasan aikin Sarah ne
Yana shiga palon yaji anrufe mashi ido datafukan hannaye murmushi yayi yace
Aysha na ganoki Hannunta Yakama yazagayo da ita ta gabansa tare dasakar mata lallausan murmushi
Aysha kenan ya ce agurin uncle jamilu wato kanin baban ABID kyakkyawa ce daidai gwargwado Shekarunta zasu kai 20 Akwai soyayya mai karfi tsakaninta da ABID kuma suna fata ta kaisu ga aure
hura mashi iska tayi a fuska ahankali ya lumshe idanuwanshi Hannayanta ta sakalo abayan wuyanshi cikin muryanta mai Jan hankali tace kallon fan!!??
Ajiyar zuciya ya sauke tare da fadin nayi missing dinki ne banganki ba kuana biyu ina kika shiga!!?
Shagwabe fuska tayi
tace ai baka neme niba kuma dama nasan nice nake sonka kai ba ka sona
Zare jikinsa yayi daga nata yana fadin
Kullun haka kike cewa amma kema kinsan da bana sonki bazan tsaya bata lokacina akanki ba hangar dakin shi yanufa can kuma ya jiyo ya kalleta yace jike kasa yanzu zan shirya inzo
Murmushi tayi tace to se kazo ko in jiraka
dakin ya shiga yana fadin jeki kawai
Asma'u da khadeeja ne akan hanyar so ta dawowa daga islamiyya suna tafe suna fira
Sun wuce daidai masallacin unguwar su sukaji ana kiran Asma'u!!! gaba dayan su suka juya amma basu ga kowa ba suka ci gaba da tafiya aka ce khadeeja!!!!
suka kara juyawa basuga kowa ba khadeeja tace amma( sunan da take kiran Asma'u dashi kenan tun tana yarinya )
asma'u tace na'am
Tace amma ko munyi gamo ne
Asma'u tayi dariya tace haba khdy wane irin gamo?? Ni kamar ma nasan muryan nan
Ganin dagaske khadeeja tafara tsorata yasa taja hannunta suka fara tafiya suna cikin tafiya khadeeja taji anja hijabinta ta baya haba tafara ihu tana daka tsalle gashi tarufe idon ta Asma'u duk ta rikeci ta rirrike khadeeja can ta dago Dan ganin Wanda yaja hijabin fa'iz(yaron yayan babansu ) ta gani atsaye yana kwasan dariya harara ta makamai tace kaga abunda kaja ko??
Se alokacin khadeeja ta bude idonta ta kalli fa'iz
Har yanzu dariya yake yace ke wallahi khadeeja Allah yayi maki tsoron tsiya duk hijabin nan naki da islamiyyar maimaikon ki ambaci sunan Allah kin tsaya kina ihu kina amma!! Amma!!!
me amma zata iya yi maki bayan ita....
Ganin tamike tanufo shi yasa bai karasa maganar ba ya ruga aguje yanufi gida khadeeja tarufa mashi baya aguje
Asma'u tayi murmushi itama tabi bayansu
Aguje fa'iz ya shigo gidan Yana haki
Wajan yanufa Umma dake zaune akarkashin bishiya tana gyaran wake tace tsaya nan ni kar ka fado mun wakaje katsokano kuma daga zuwan ka?? Tana rufe baki khadeeja tashigo gidan rai ahade wurin fa'iz tanufa Umma tarike ta tana tasya me yahadaku??
Khadeeja bata ce komai se haki takeyi fa'iz yace
Umma wai Dan na jamata hijabi shine fah
Umma tace fa'iz kai dkasan halin khadeeja abun laifi baya mata kadan me yakaika tsokanarta murmushi yayi ya kalli khadeeja to yi hakuri bata ce komai tayi kwfa tare da wucewa daki Asma'u tashigo tazauna kusan Umma takarba wakyan tana gyarawa fa'iz ya matso kusa da ita yana tayata can ya dago yace AMMA saura kuana hudu fa !!
Tace name fahh???
Yace kituna mana
🤔 Tayi shuru can tace kai gaskiya ban tuna ba gira yafara daga mata yana cewa birthdayyyyyyyyy
dariya tayi itama tare da kwafan yanda yayi magar tace ohhhh na tunaaaaaaaa
Dariya sukayi su duka yace to me zaki bamu gift tace to ai ita gift ba'afada sedai kawai in ambaka kaga ko miye yace hakane khadeeja da fitowar ta kenan daga Palo tace dama tunda naganka nasan maula kazo yi Dan baka zuwa hakanan daure fuska yayi 😠yace to wa yakasa dake dazaki kwasa?? Ita ma fuska adaure tace tunda kakasa da amma ai kuwa dole in kuasa Asma'u ce ta katse fadan da cewa haba wai se yaushe zaku daina Abu kamar yara ne yanzu fa shekarun ku 17 amma har yanzu Baku girma ba
fa'iz ne yayi gyaran murya yace
😎 hmm hmm amma nifa 19 ne
tsaki tayi tace to miye maraban dambe da fada?? Umma ce tayi
dariya kana suma suka kwashe da dariya🤣
Bayan kaman minti talatin ABID ya sawko zuwa palon kasa yana sanye da 3quater da kuma jallabiyya milk color se kanshin turare ke tashi yayi kyaw sosai kamar black American tun da yafito suka kure shi da ido har ya iso ya zauna a dai daga kujerun palon sannan ya zaro check da bairo daga aljihun rigarsa yadora akan table din dake gabansa Sannan yadago ya kalle su daya bayan daya yayi gyaran murya yace to dafatan dai ba wata matsala babba dukansu suka ce a'a yace to alhamdu lillah kamar yanda muka saba zamu fara daga babba zuwa karami
Gaba dayansu kowa se washe baki yakeyi inkacire grany data hade girar sama da takasa
ABID ya kalli uncle jamilu
yace uncle bismillah uncle jamilu ya washe baki yace ni daman ba wani Abu bane kawai dai ciwon kafar nan na wane yadameni shine nakeso in fita Waje adubani yana magana yana kallon grany ganin yanda ta kafeshi da ido ko kiftawa bata yi ai kaman jira take yagamana tayi carab tace kai jamilu kaji tsoron allah yanzu fi sabilillahi duk asibitocin Nigeria basu isa suma maganin cewon Kafa harsai kafita waje ABID ne ya katseta da cewa ya isa haka grany wannan ba wani Abu bane duk kudin da nake nema ai saboda Ku ne So banga anfanin wannan dokiyar ba inhar bazan magance maku matsalolinku ba
Grany dai baki ya mutu se shuru da tai ta sa musu ido
Check din dayayi rubutu ya mikama uncle jamilu bansan konawa bane sedai naga yawashe baki yana godiya
ABID yajiyo ya kalli sadiya matar uncle jamilu yace
Aunt se ke
Baki ta washe tace dama jarina ne yayi yayi kasa shine nake so.....
Grany ce ta katseta da cewa ji wani jin dadi yo dan jarinki yayi kasa uban wa kike bi bashi anan??
ABID ne ya sake katseta da fadin
Grany please!!!!!
Saboda haka ta tashi azuciye ta nufi part dinta duk suka bita da kallon gwara da kika tafi Gyaran muryan da ABID yayi ne yasa suka dawo da dubansu gareshi nan ya mika mata check kowa ya cigaba da fadin nashi har akazo kan Sarah itama tafadi nata na fitan su London kuma ya amince aka zo kan aysha ita kuma tace tana so idan suka dawo daga London zata ji tayi degree dinta a abroad shima ya amince haka akacigaba har suka kare kowa yawatse cikin farin ciki da jin dadi
ABID yana tashi direct masallaci ya nufa kasancewar anata kiran sallah bayan yadawo ne ya wuce bangaran grany ahankali ya tura kofar tare dayin sallama sanyin AC da kuma daddadan kanshin turaran wuta ne sukamishi maraba
Zaune ya iskota kan sallaya tana lazimi kusa da yazo ya janyo pilo anan kasa ya kuanta ya dauki remote ya kamo tashar aljazeera yana kallon labarai se da yashafe kusan awa daya amma grany bata motsa ba sedai daga ya kalleta se ta kauda kai murmushi yayi yamatso ya dora kansa akan cinyarta yace grany nasan kin kare fa kawai shareni kikayi
Hannunta tadora akansa tana shafa suman kansa cikin sansanyar murya tafara magana kamar haka
ABID Nasha fada maka karage abunda kake ma yaran nan yayi yawa amma kakasa ganewa zaune yatashi yarike hannunta cikin nashi yace grany family nan sune rayuwata taya zan iya kuantawa inyi bacci mai dadi alhali family na suna cikin matsala na tabbata koda Abba yana raye da abunda yafi wannan ma zai iyayi grany tasauke ajiyar zuciya tace to shikenan Allah yasa albarka yace ameen ko kefa tace to ai bamu gama ba yace se kuma me zama ta gyara tace zancan iyali ABIDI anya kuwa lafiyanka kalau wajan shekara 30 amma baka zancan iyali
Dariya yayi yace grany kwantar da hankalin ki ankusa grany ta katse shi dacewa yo kai daga anyi magana se kace ankusa katsaya biye ma wannan shashan aysha ni kabani dama in zabo ma air mutunci mai tarbiyya kaki
Murmushi yayi yace grany ahalin danake ciki yanzu bakowace yarinya zan iya aure ba ina bukatar wadda tasanni da yanayin family na yarinya air baban gida wacce tasaba da rayuwar family house kinga seta taimakamun wajan kula da family na grany ni bawai macan dazatamun kwalliya ingani kawai nake bukata ba jarumar mace nake nema
To shiyasa kika ga ina bukatar lokaci
Grany ta sauke ajiyan zuciya tace
To banki ta taka sedai shekaru ja suke ABID ina so inga ya'yanka kafin lokaci na yayi ABID ya daure fuska yace ba nace idan muna magana kidaina kawo zancan mutuwa ba insha Allah har jikokina se kin gani Grany tayi saurin fadin
Um um daina mun fata ABID bana fata in kai lokacin da zan kasa tantance tsakanin gabas da yamma
Kiran sallan da ake ne ya katse masu firar ABID yatashi yana murmushi yace zanje masallaci daga can kuma zan wuce inkuanta nagaji dayawa
Grany tace yo ba dole ka gaji ba kazauna majalisar dinkin duniya
ABID yagane me take nufi shiyasa bai ce komai ba yanufi Hanyar fita har yakai bakin kofa ya jiyo yace grany kibada Lipton dina akamun tace to shi kuma ya fice
Misalin karfe 8 na dare Asma'u ce da hkadeeja zaune a Palo suna kallon shirin akushi da rufi Wanda ake atashar arewa24 can khadeeja ta waigo ta kalli Asma'u race amma alalan nan dagani zatayi dadi ko ??Asma'u tayi murmushi tace sosai ma ko kina sone ?
eh wallahi ina so zaki mun ne? Asma'u tace mezai hana khdy ko wannan din da suke girkawa yanzu in kina so se inje in karbo maki
Khadeeja ta shagwabe fuska tace uhm uhm nifa da gaske nake
Asma'u tayi dariya tace gobe zan maki naki khdy ta washe baki tace Allah ya kaimu Asma'u tace ameen suka ci gaba da kallon
Washegarin ranar ta kasance asabar misalin 10 nasafe Asma'u ta gyara wken alale tashirya ta tafi kai nika
ABID ne yafito daga bangaran sa cikin shiga ta kananan Maya wando light brown da faran riga ga fitinannan kanshi dake tashi daga jikinsa yayi kyau bakadan ba fitowarsa yayi daidai da fitowar Sarah daga nata part din da far'arta takaraso wurin shi tana gaida shi ya amsa shima dauke da murmushi afuskarsa yace bari inje ana jirana murmushi tayi tace AHMAD ko?? yace eh sannan yafara sauka har yakai kasa tace yaya kace mashi...se kuma tayi shuru kanshi ya dago ya kalleta yace ince mashi kina gaidashi ba??fuskanta ta rufe da tafukan hannayanta 🙈ta shige bangaranta shikuma ya wuce yama grany sallama daga nan ya nufi wajan motocinsa guards dinsa suna ganinsa suka tashi tsaye yadubi wani daga cikin su yace yahya bani makullin atare suka hada baki but sir !!!!
Fuska ya hade yace just give me the key Wanda aka kira da yahya ya mika mashi makullun ya karba naga ya nufi wata dakkareriyar Jeep baka se sheki takeyi ya fice daga gidan ahankali yake tukinsa kamar mai koyo har ya iso life camp akofar wani katafaran gida naga yayi parking mai gadin ne ya liko ya ganshi yace ah yallabai yafara kokarin bude get din ABID yace no barshi sauri nake yanzu zan fito kai tsaye cikin gidan ya nufa tare da sallama ya kutsa kanshi cikin palon wata matace ta amsa sallamar tana ta kokarin shirya abinci a dining Da murmushi ya karasa dining din yaja kujera ya zauna kana ya dago ya kalleta yace momy ina kuana bata dago ta kalleshi ba bare ta tankashi Shima kuma bai kara cewa komai ba Ya bude kula ya fara zuba soyayyan dankali da pepper soup yafara ci seda ya gama kana ya leka kitchen din ya iskota tana loda lemu a frig daga kofan kitchen din yace momy zan wuce se a lokacin tace toda wa yarikeka?? Murmushi yayi baice komai ba yafita daga palon wani bangare naga yanufa acikin gidan yana zuwa yatura kofar palon ya shiga babu kowa hakan yasa yawuce bedroom karasawa yayi kusan gadon tare da yaye bargon yana fadin AHMAD!! Ahmad ya gyara kuanciyarsa tare da Jan bargo ABID ya janye bargon gaba daya yace malan dallah tashi kai ko kunya baka ji tun baccin jiya har yanzu bai isheka ba Cikin murayan bacci Ahmad yace AK wai miye haka da sassafe kazo gidan mutum kahana shi hutawa ABID ya katse shi kai dallah tashi lokaci ya kure mukadai ake jira Tashi Ahmad yayi yana gunguni yanufi toilet ABID yace wai me kama Momy ne ?? Ya juyo ya harereshi da jajayan idon shi na bacci yace Ohoo!! meyasa baka tambaye taba yashige bayi ABID ya girgiza kai ya mike yaje drowan Ahmad ya Ciro masa kananan kaya wando baki da riga milk color bayan Ahmad yafito wanka ABID yace kashirya zan jiraka awaje kuma wallahi kadade kazo kaga bana nan Ahmad yace dadin abun dai Nima inada abun hawa ABID ya wuce ya barshi atsaye yana kallon kayan dake kan gadon
Asma'u ce tadawo daga kai nikan dataje tundazu tana tafe tana mitar dadewarta ita kadai shi yasa bataji horn da ake mata ba seda motan tazo kusa da ita Drivan yadaka mata tsawo afirgice tayi baya zata fadi Taji ta bige da wani har robar nikan ta karkace kadan ya zuba juyawan dazatai taga ashe mota ce ajiyan zuciya tayi tace kai amma Allah mai motanan albarka dayanzu nikan alalan khdy ya zube robar ta Dora akan motan tana gyara wanda yabata bakin robar tsawar da taji andaka mata ne yasata tajuya afirgice ABID tsaye abakin get Ya murtuke fuska kamar bai taba dariya ba ganin yana nufota gadan gadan yasa ta hadiye yawu tare da kura mashi ido tsabar tsoro yasa tama kasa motsa kafarta bare tayi yunkurin guduwa yana zuwa dap da ita bai yi watawata ba ya fisgota tare da zabgamata lafiyayyan mari a firgice ta dafe kuncanta 😨 Cikin Muryan kuka tace malam lafiya me namaka zaka mareni?? ABID da yagama hasala wato bata ma san abunda tayi bakenan cikin kakkausar murya yanuna motarshi da yatsa yana fadin
Dan ubanki nan yamaki kama da bola ko kwata dazaki zubamun wannan kazantar akai??
aranta tace ga mai mortar nan juyawa tayi takalli motar ita se a lokacin ma ta lura da Wanda ya zube akai maganar ABID ne yasa tamaido da dubanta garesa aranta take fadin hmm yanzu haka ma ita ce motar da yafara mallaka arayuwarsa shi yasa yaketa rawar kafa akanta ABID ne ya katseta da cewa ina magana kin wani kure in da ido sunkuy da kanta tayi kasa tace yi hakuri
What!!! apology dinki zai sa motata ta gyaru ne itama hade rai tayi dan abunshi yafara isarta kallonshi tayi tace inazuwa da Sauri ya sagabanta yana fadin ba inda zaki se kin... Bai karasa ba takatse shi dacewa dallah malam matsamun to in ban nemo abun gogewa ba da harshe na ka keso in llashe shi ko me ?? Tana gama fadan haka ta shiga gidan da ke kallon nasu Ahmad
ABID dai da kallo ya bita yana mamakin wai yau shine yake fada ana fada yayi danasanin rashin zuwa da guards dinshi da tuni sun tattaka wannan baby doll din ba Ba adau lokaci ba segata tafito daruwa aroba da wani dan karamun towel tazo tafara goge motar har tagama yana tsaye yana kallonta ko Inda yane bata kalla ba tadauki robar ta maida tadawo tadauki robar nikanta se alokacin ta kalleshi yana kokarin shiga mota tace Hey!!!
tsayawa yayi cike da mamaki yana kallonta matsowa tayi kusa dashi cikin sansanyar murya tace kasamu wani waje koda dan kadan ne acikin zuciyarka dazaka rika yafema Wanda yamaka laifi to gashi nagoge maka motar ka nikuma idan nace banyafe marin da kamun ba ya kenan tana kai tajuya tafara tafiya can kuma takara juyowa tace ohhh yes ina farin cikin sanar da kai
Kaine mutum na farko da yafara marina A tarihin rayuwata juyawa tayi tayi tafiyanta
Wani dogon tsaki ABID yaja se a lokacin ma yaji haushin kanshi da yatsaya sauraronta motan ya shiga ya zauna ba adau lokaci ba se ga Ahmad yafito yana daura agogo ahanunsa motar yabude ya shiga ya kalli ABID yace 😎AK nayi Sauri ko??
tsaki yaja baice komai ba ya tada motar suka wuce
Ahmad kenan yakasance aboki kuma amini awurin AK wato ABID tun suna yara suka taso tare koda wane lokaci suna tare Akwai shakuwa maikarfi atsakanisu Ahmad yakasance fari dogo mai dan matsakaicin jiki yanada surutu da barkuanci sabanin AK dabaicika yawan magana ba
Asma'u tana isa gida sukacikaro da khadeeja cikin muryar tausayi tace khdy yunwa ko ??
Khadeeja tace amma meya sami fuskar ki??
Asma'u ta kakalo murmushi tace ba komai muje in maki alalan rana tayi ko Umma ta aike ki ne
Khdy tace a'a wurinki naso inje naga kinjima Baki dawo ba batace komai ba taja hannun khdy suka karasa ciki..........
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧DOMUN KANWTA👩👧
🖊Na marubuciya Husnah kabir zarewa ( the mammah girl)
🖊dasunan Allah mai rahama mai jinkai ...
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
1⃣0⃣⏭1⃣5⃣
Bayan sati daya da faruwar hakan misalin 11 na rana Asma'u ce da khadeeja a kitchen suna girka abincin rana khadeeja tasa wakar harsashe awayanta suna aiki suna bin wakar idan anzo baitin da namiji keyi se khadeeja tabi na mace kuma se Asma'u tayi sundage se yi suke kai kace su suka rera wakar
Khadeeja har da kwaykwayon muryar maza ta nuna Asma'u da yasa tace " tadaban ce ke ta kadaban aciki ke nawware!!! Araba mu anyi....." har dai zuwa karshe tadake kuwa kamar da gaske
Asma'u ta kwashe da dariya ita ma ta karkace tana kikkifta ido tana kallon khadeeja irin na moyannan tace " niii taka tun asali ba mai kuacema!!!
Khadeeja ta kwashe da dariya tace ammah dazakiyi acting zaki samu kudi
Umma ce ta leko kitchen din tace kuna nan kuna shirman da kuka saba ko to nidai kuyi sauri ku gama Asma'u zan aikeki kasuwa daga nan kibiya wurin inna tana nemanki tana kai nan tafita
Asma'u ta juyo ta kalli khadeeja tace khdy zaki rakani ??
Khadeeja ta zaro ido ta dafe kirji tace wa?? Niii dama bazaki biyo wajan inna bane dana rakaki amma kinfi kowa sanin bama shiga inuwa daya da ita Asma'u tayi murmushi suka ci gaba da aikinsu....
sarah ce da aysha zaune suna shirya yanda tafiyan su zai kasance can aysha ta dago ta kalli sarah tace wai nikan sarah ina dan gidanki ne kwana biyu banga yazo gidan nan ba sarah tayi murmushi tace yana nan dazuma muka gama chart dashi he is just busy that's why aysha tace ahh ahh kice kun fara soyewa kenan ?? Sarah tayi fuskar tausayi tace wace soyewa kuma aysha bayan nikadai nake azabtuwa da sonsa shi bai ma San inayi ba aysha ta gyara zama tace to shin wai ke meyasa bazaki fadamasa halin da kike ciki bane nasan dai ko giyar wake ya sha baza yayi rejecting din ki ba Sarah ta saki baki tana kallonta se can ta yi dariya tace wa?? ni?? Da matsayina da Class dina kanwar the richest man in town inje insamu namiji ince ina sonsa never!!!
Aysha tadaga kafada tace nidai shawara nabaki kina nan sake da baki wata zata kwacemaki shi sarah tayi wani malalacin murmushi tace ai ba'a haifi macan da zata kuace AHMAD a hannuna ba wallahi ke ni maganar nan ma da mukayi kinsa naji ina son ganinshi bari inje company nasan zan same shi aysha ma tamike tace muje narakaki toh daga nan nima naga AK
suna fitowa suka hadu da grany itama tafito cikin shirin ta nafita cikin rada sarah tace ita kuma wannan tsohuwar ko ina zata ohoo aysha ta matsa kusan grany tace ahh ahh grany ina zuwa haka? Grany ta tsuke fuska tace inda kika aikeni aysha ma tahade fuska tace shi mutum ba'a iya mashi idan kashareshi yace ka raina shi in kuma kamai magana ya gaya ma nakar magana cikin fushi grany tace zan bige maki baki wato futsarar da kika ga waccan mai kama da kazar yan burin tanamun shi ne kema zaki soma ko to kufita a idona aysha ta wuce tana gunaguni grany tabita da harara tace mace kamar pal waya kome ma ABIDI yagane anan da har tabirge shi ohoo koda tafito su sarah sun tafi guards suna ganinta suka mike Driver yaje ya fito da dai daga cikin motocin gidan grany ta juyo ta kalli guards din da ke biye da ita ta kankance ido tana kallon su cikin masifa tace kai wai lafiya kuke biye dani kamar kaza da yan tsaki?? Sunkuy da kai sukayi basu ce komai ba tace toh Ku koma bazani da Ku ba daya daga cikin su ne yace sorry ma but umarnin yallabai ne kar mubar kowa na gidan ya rinka fita shi kadai Grany ta wuce tana fadin ai kuma se kuyi naga Wanda zai biyoni acikin Ku mota ta wuce tana waiwayo su tare da nuna su da yatsa har ta shiga driver yaja suka fita se da suka hau titi driver ya juyo yace grany ina muka nufa fuska ta daure tace baka iya gaisuwa bane ?? kai ya Sosa yace ina wuni tace lafiya kasuwa zaka kaini ...
asma'u ce a kasuwa tazo wucewa taga grany a tsaye se waige waige take ga tulun kaya agabanta har ta wuce se kuma ta dawo wurin grany tace ina wuni grany ta washe baki tace lafiya kalau yarnan sannu Asma'u tace kina son keke napep ne grany tace a'a da driver mukazo anan ya saukeni kuma kinga nafito ban ganshi ba Asma'u ta waiga ko ina bata ga mota ba ta kalli grany tace bari muje can bakin hanya muga ko yana nan grany ta washe baki tace to Asma'u tadauki kayan da kyar take tafiya har suka iso bakin hanya grany tace kinga kwa gashi can zo muje suna isa wurinsa grany ta haushi da fada baice komai ba se hakurin da yake bata ya karbi kayan ahannun Asma'u yasa a boot grany ta kalli Asma'u tace sannu yar albarka baki gayamun sunanki ba Asma'u tayi murmushi tace ASMA'U suna mai dadi ni kuma sunana... Asma'u tace grany ko?? Grany ta washe baki tace ina kikasan sunana Asma'u tayi murmushi tanuna driver tace damuka zo nan naji ya kiraki da sunan grany tayi murmushi tace eh hakane jika nane yake kirana da sunan shine ya Bini hannu tasa ajaka ta dunkulo kudi masu yawa tamikama Asma'u amma Sam taki karba se ma juyawa datayi ta tafiyanta grany tayi tsaye tana kallonta cike da sha'awa aranta kuma tana fadin inama ABIDI na yasamu irinki amtsayin mata da yamore har saida Asma'u tabace mata sannan ta shiga mota suka fice...
Daga kasuwa Asma'u direct gidan kawunsu tanufa tana isa ta tura kofar palon tare da yin sallama fa'iz ne kadai azaune yana duba wani magazine karasawa tayi ta zauna adai daga kujerun palo fa'iz ya ijiye magazine din hannunsa suka gaisa Asma'u ta mike ta nufi dining tana cewa bakowa agidan ne fa'iz yace Ummi taje barka nusaiba kuma tana ciki Asma'u tace inna fah yace tana Akurkinta Asma'u tayi dariya tace wallahi kai da khadeeja kunraina inna ranar da Abba ya kama Ku bazakuji da dadi ba abunci ta zuba tafara ci nusaiba tafito suka gaisa da Asma'u tace Asma'u inada dinki fah Asma'u tace to se ki kaimun shago Nusaiba tace tab!! Wannan shagon dinkin naku mai Nisan tsiya ina zan iya Asma'u tadaga kafada tace ba kishirya dinkin ba kenan nusaiba tahade fuska tanufi palo kusa da fa'iz ta zauna tana leka magazine din dake hannun shi baki ta washe tace kai ji wani gado kamar na sarauta fa'iz yayi murmushi yace Shi zan maki na auranki dukan shi tayi akafada tace Allah yaya bana so Wani page ya juyo sega photon AK yana sanye cikin shiga ta kananun kaya ga agogon Rolex daure ahannunsa yana murmushin da yake kara masa kyau nusaiba tace WOW!!! AK hausawee gayan nan yana bala'in birgeni fa'iz yace Ashe bani kadai ba ai gayan ya hadu ga gayu ga money
Daga can dining Asma'u tace waye ake cewa ya hadu fa'iz yace AK hausawee Asma'u takai loman tuwo bakinta tace waye kuma shi fa'iz yace ammah kina Abuja amma kanki na kauye to ai duk yan matan garinnan daya daya ne basu San shiba Wanda yakeda Hausawee interior decoration (HID) import company suna shigo da kayan gida irinsu Gado kujeru da sauran su tasowa tayi tana fadin ina jinshi abakin khdy Amma ni ban taba ganinshi ba murmushi yayi ya mika mata magazine din ta miko hannu zata karba kenan akaturo kofar palon tareda sallama wata dattijiwa ce tashigo palon kofar suka kalla suna Amsa sallamar tsaye tayi abakin kofar tarike haba tana zabga salati asma'u tanuna da yatsa fuska ahade tace ke yanzu asama'u dama nan kikazo wajan wa'innan sakarkarun kika shanyani ina jiranki? Asma'u tayi murmushi tace yi hakuri inna dama yanzu zanzo inna batace komai ba takada kai kafita Asma'u tabita da kallo fa'iz yace kin tsokano mana tsuliyar dodo hararar shi tayi tace ya isheka malam itama ta fita daga palon bangaran inna tanufa azaune ta iskota tana ninke kayanta da aka wanke da sallama takarasa cikin palon inna ta amsa sallamar ciki ciki ita adole tashaka kusa da ita Asma'u tazauna itama tafara ninke kayan kusan minti 10 bawanda yace wani Abu atsakanin su asma'u ce takatse shurun da cewa kince kina son ganina nazo kuma bakice komai ba inna tace yau wace rana?? Asma'u tace Dama dan kitambayeni hakan yasa kika kirani? inna tayi shuru batace komai ba Asma'u ta sauke ajiyar zuciya tace yau asabar menene inna tadago ta kalli Asma'u tace magani na yakare jibi ya kamata mu koma asibiti gashi abbanku bai dawoba kuma ni gaskiya ina jin kunyar inje ince ma Maman nusaiba tabani kudi inje asibiti Asma'u tayi shuru na dan lokaci can tadago tayi murmushi tace Karki damu inna Allah ya kaimu jibi kishirya da safe zan zo se mu wuce asibitin inna tayi fuskar tausayi tace asama'u ina ruwa yaci makadi ke kina ganga ta jiki yo dawane kudin zamuje asibiti? Asma'u tace Dama akwai dunkunan da nakare Se inkira a amsa kedai kawai kishirya da wuri Inna tawashe baki tace ai insha allahu tun asuba zan shirya Asma'u tace dakin kewta mun kuwa dan daga can shagon dinki nakeso in wuce Bazan samu damar zuwa makaranta ba inada aiki dayawa gaskiya inna tace to Allah ya taimaka amma asama'u kinaida wasa da karatunki kinje Asma'u batace komai ba tadauki kayan da suka gama ninkewa tashiga dasu ciki inna tabita da kallon tausayi tana fadin allah sarki Asma'u mace mai kamar maza kenan tana tsananin son yan uwanta da kishinsu tun tana Karama take zuwa gidan wata ameena makwabciyar su tana koyon dinki har ta kware aharkar dinki tana fitar da style masu kyau intayi dinki kai kace injin ne ya buga kayan ganin haka ne yasa lokacin da ameena ta bude shagon dinki tadauki Asma'u tana mata aiki Dawanan aikin Asma'u take rike da gidansu da kuma karatun khadeeja dawasu bukatun su kasacewar shi kanshi kawusu bawani karfi gareshi ba fitowar Asma'u daga daki ne ya katse ma inna tunaninta ledan da tashigo dashi daga kasuwa tabude ta Ciro wata Leda aciki tamika ma inna tana fadin inna ganshi ba yawa kidan yi brush inna takarba tana washe baki tabude gasashshiyan hanta ne Wanda bazasu wuce yanka 10 goma ba Inna anata lashe baki asma'u Tamata sallama tafita dayan bangaran Ta koma ta iske Ummi tadawo tana zaune a Palo wajanta ta karasa suka gaisa Ta kalli nusaiba dake gefe tana goge uniform tace ji ki kawo dinkin naki tashi tayi tanufi daki tana jin dadi Ummi tace Asma'u badai har zaki wuce ba murmushi tayi tace Ummi sauri nake yamma tayi Ummi tace namanta ban tambayi yar lelanki ba khadeeja it's dai bata zuwa nan gidan se in an aikota Asma'u tayi murmushi tace tana nan makaranta ne ya riketa nusaiba ce tafito dauke da turmin atanfa tamika ma asma'u tace buba nakeso Asma'u ta karba tare da fadin sedai singlet nusaiba tace kai ammah wane irin singlet kuma😧
Dariya suka sa Asma'u tamusu sallama tawuce
tafe take tana sauri ganin magariba ta gabato ta tsallako titi kenan ledan hannunta ta tsinke dogon tsaki taja ganin lemun da tasiyo ma khdy duk ya waste Hakanan ta tsugunna tafara tsincewa tanaji ana mata horn amma bata motsa ba AK dake bayan mota a zaune ya jingina kanshi akan kujera ya lumshe ido jin driver nata horn yasa yace menene? Driver yace wata yarinya ce a hanya Shiru yayi bai CE komai ba driver yakara danna horn Ita kuma haushi duk ya isheta ga karan horn duk ta rikice tarasa ma mezatayi jin shuru yasa Ak bude idonshi ya leko ta window ya ganta tana kokarin Gyara ledar da tayage komawa yayi yazauna yace ma driver taka motar driver yace sir???
tsaWa yadaka ma driver hakan yasa ba shiri ya taka motar suka nufota a guje duk dacewa Asma'u ta tsorata amma ko motsawa batayi ba bare tayi yunkurin guduwa seda motar tazo daf da ita har tana jin hucinta kana driver yaja birki mutanan dake wurin suka dau salati aka zagaye wurin AK kam yagama shaka a hasale ya fito daga mortar ya nufota yana zuwa ya fincikota ya daga hannu da nufin marinta se kuma yadakata yace you???Asma'u kuwa takafeshi da ido ko kiftawa batayi zuciyanta na azalzala aranta take fadin nufinshi da yakara marina ai kwa da na nuna mashi cewa ba kullum ake kuana agado ba ganin yadda take kallonshi babu ko alamar tsoro afuskarta yasa ya kalleta da mamaki yace ke anya bakyada tabin hankali kuwa?? Batace komai ba se hannunta da tafizge tadauki ledanta ta raba ta gefenshi ta wuce yana tsaye kamar Wanda aka dasa a gurin se binta yake da kallo aransa yana fadin anya kuwa wannan mutun ce tokodai gamo nayi ne ahankali ya furta (Wa innahu min sulaimana wa innahu bismillahi rahmani rahim) mota ya koma ya zauna driver yaja suka tafi yana karanta duk addu'ar data zomai Abaki...
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
🖊na marubuciya HUSNA kabir zarewa( the mammah girl)
🖊da sunan allah mai rahama mai jin kai....
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
1⃣5⃣⏭2⃣0⃣
AK yana isa unguwar su ana kiran sallah se da ya tsaya yayi sallah a masallacin unguwar su kana ya shiga gida yana isa ya iske mutanan gidan duka zaune a babban Palo suna fira kusa da grany yaje ya zauna bayan sungaisa da kowa na palon ya kalli inna ladidi yace ina su salma ne? Murmushi tayi tace sunje weekend gidan ameena uncle jamilu ne yace AK dama gobe nakeso nayi tafiyar da sassafe AK yace ok allah ya kaimu sarah ce ta zo tazauna kusa da shi tace yaya mu yaushe zamu tafi murmushi yayi yace sarah kinkasa ganewa ni bana so kiyi nesa da nine bana jin dadi idan bana ganinki
baki ta zunburo tace to amma yaya ai 1 week ne kawai fa kanta ya shafa yace to shi kenan next week se kuje tsalle tayi tace nagode yaya dagude ta wuce dakin aysha dan tasanar da ita AK ya bita da ido yana kallonta cike da so da kauna Bashir dan inna ladidi ne ya shigo palon ya zauna kasa kusa da kafan AK yana matsa kafan AK yayi murmushi yakalle shi yace kaga nagane wayon me kake so? murmushi yayi ya sosa kansa yace yaya dama account dina ne yayi low shine nake so adan taimaka murmushi AK yayi yace ba damuwa zan maka transfer grany ce ta daure fuska tace ABID abinda kake ba ka kyautawa yanzu kamar wannan gardin ace yagama karatu amma bazai nemi aikin yi ba sedai kullun yana yawan banza inyaso kudi kuma yazo yana Sosa gemu yana roko
Dariya suka sa apalon shi kuma ya zunbura baki yana gunaguni AK ya dafa kafadansa yace karka damu kabani takardunka inga wane aiki yadace da kai se insama maka baki yawashe yana dariya inna ladidi dake kusa dashi tasa kafa ta zungure shi da kafa ya waigo ya kalleta tamai alama da ido juyowa yayi yarike hannun AK yayi saurin cewa yaya ni a company dinka nake son aiki ?? murmushi yayi yace to komai yazo da sauki se kashirya munday kazo baki ya washe yana godiya inna ladidi na tayashi uncle jamilu ne ya buga tsaki ya tashi ya wuce bangaransu aunty sadiya tabi bayansa ladidi tabiso da harara bawanda ya lura da su kowa yana kallon AK da ke waya da Ahmad ta dayan bangaran Ahmad ya ce guy sakwaran Umma tayi dadi kayi santii AK yace kamar ya??
Ahmad yayi dariya yace kamanta file dinka anan tsaki yayi yace kataho mun dashi gobe Ahmad yace sarah tana nan Ak yace ya akayi?? Ahmad yace gaskiya bazan samu zuwa gobe ba kawai kazo ka karba yana kai nan ya kashe waya AK yayi tsaki aranshi yana fadin wai meyasa idan sarah tana nan Ahmad baya son zuwa gidan nan kiran sallah da ake ne ya katse mashi tunaninshi tashi sukayi shida bashir suka wuce masallaci matan kuma kowa tashige bangaranta...
Sarah ce adakin aysha bayan tafadamata zancan tafiyan suna ta murna aysha takalli sarah tace in baki shawara?? Sarah tace tame fah?
Aysha tace look sarah yakamata kafin mutafi kinsan matsayinki awurin Ahmad kobaki gayamasa kina sonsa ba to kinuna masa ko kisa ya soki bare ma nasan yana sonki kawaidai yana shakkar fada maki ne ? Sarah tayi ajiyar zuciya tace aysha bansan ya zanyi ba why can't u help me??
Aysha tayi murmushi tace zan taimake ki tunda nima kin tamakeni lokacin ina son AK yana shareni sarah tayi murmushi tace Ashe baki manta ba aysha tace ina fah!! yanzu dai yaushe rabon kuyi waya da shi ? Sarah tace bama waya sedai chart kuma tun ranan da nace maki munyi chart har yanzu daman gaisawa kawai mukeyi aysha tace bani wayanki sarah ta zaro ido tace me zakiyi?
Aysha tace kedai bani kawai asanyaye sarah ta mika mata wayar aysha ta karba ta shiga watsapp cikin Sa'a kuwa ta ganshi online yasaka photon AK a dp photon yayi kyau sosai aysha tayi murmushi aranta tace gaskiya ni mai Sa'a ce sako ta fara rubuta kamar haka
( amincin allah ya tabbata agareka Yayana dafatan kana cikin koshin lafiya yasu momy Da dady kuana biyu shuru kadaina zuwa gidan mu ko mun maka wani laifi ne to tuba muke ranka yadade kanmu bisa wuyanmu Idan kuma se munzo munsameka ne toh ni zan tarkato hausawee family gaba daya har da grany muzo mubaka hakuri
Fatan alkhairi daga your one and only sister se anjima....)
Tana gama rubuta sakon ta tura tana murmushi sarah ce tafizge wayan ta karanta sakon dariya tayi tace indai Ahmad ne allah sa ma ya karanta bare ya baki amsa Aysha tace ahab !! Kina wasa dani ne bari kiga ni nasan zai maido tana rufe baki kuwa suka ji karan text ya shigo da sauri sarah taduba wayan Ahmad ne ya turo sako kamar haka
( kema amincin allah ya tabbata agareki kanwata ya kike ya kowa na gidan ni har kin ma bani dariya wallahi ni na'isa kumun laifi nine ma da laifi kuma ina Baku hakurin rashin zuwana aiki ne yamun yawa amma insha allahu idan nasamu lokaci zan zo Nagode da kulawar ki se anjima..)
tsalle tayi data gama karantawa ta rugume aysha tana murna ayshi tace ni dagani kar ki karyani sarh ta tashi tana washe baki tace kai gaskiya aysha kin hadu dariya aysha tayi suka tafa aysha tace yanzu kicire duk wata kunyar da kike mashi kinuna ba komai aranki se yasaba da ke ina tabbatar maki shi da kanshi zai ce yana sonki sarah takara rugumeta tana murna
Asma'u ce zaune akan sallaya ta idar da sallar isha'i Umma tashigo ta zauna tace Asma'u wai kiran me inna tamaki ne ina ta jira kifada mun ke kuma kinyi shuru kuma ni naga yanda kika fita ba haka kika dawo ba kamar wani Abu na damunki khadeeja dake kuance kan gado tayi carab tace dama Umma ai duk Wanda yaje wurin inna dole yasamo damuwa in ma yanada hawan jini se yatashi Umma ta kaimata duka da bayan hannu ta kawce tana dariya Umma ta kalli Asma'u tace kinyi shuru Asma'u tayi murmushi tace Umma ba wani Abu bane asibiti takeso narakata ran munday Umma tace to allah ya kaimu Asma'u tace Umma inaso da safe zanje shago amma ba wuni zanyi ba saboda zanje islamiyya da yamma Umma tace to allah nuna mana goban lafiya duka suka amsa da ameen...
Washegari da yamma misalin karfe biyar Asma'u ce da khadeeja suke dawowa daga islamiyya sunzo daidai gidansu Ahmad dagowan da Asma'u zatayi taga motar AK akofar gidan murmushin keta tayi tafara waige waige can tahango wani bungun farar kasa taje ta Dauko shi dutse tasamo ta daka wanan farar kasar seda ya zama gari ta karbi ragowar ruwan dake hannun khadeeja tanasha tafara kwaba wannan farar kasar khadeeja tana biye da ita tana fadin ammah lafiya mezakiyi da wannan ido tazaro ganin Asma'u tanufi dankareriyar bakar motar dake gefe da gudu taje tasha gabanta tace ammah wai me kike shirin yi ne haka tsokana fa ba halinki bane daga ganin wannan motar ta mai kudi ce baki San mezai maki ba aa'u bata kulata ba tafara shafe motar da wannan farar kasar har wani Zane Zane takeyi amotar tsagayowa tayi ta gaban motar tayi rubutu da manyan haruffa kamar haka
(NEVER SLAP A WOMAN!!!)
Tana gamawa taja hannun khadeeja suka ruga aguje suka bar layin ahanya take ba ma khadeeja labarin abunda yafaru ranan tsakaninta da AK Khadeeja uwar fushi har idonta yayi ja cikin masifa tace Aida kingayamun tun acan wallahi da glass din zan fasa kuma najira se ya fito na rama maki marin Asma'u tayi dariya tace hakan ma ya isheshi ai khadeeja tayi kwapa tace wallahi duk ranar da nakara ganin shi se namai abunda se yasan yataba ki Asma'u tace um um khdy kibarshi kawai mutuminan baida imani ze iyayin komai akan motarnan khadeeja batace komai ba har suka isa gida
AK ne da Ahmad suka fito daga cikin gida da nufin shiga mota birki suka ci suna karema motar kallo ahmad yace AK wannan wane kalan painti kama motar Kane ko duk cikin gayun ne AK kuwa tsaye yake kamar guki yasaki baki da hanci yana kallon motar ko kftawa baya yi ahmad kuwa banda dariya ba abunda yake ya zagaye motar rubutun da tayi ya hango yayi saurin karasawa ya karanta kallon AK yayi yace toh!! Fah!!
Matso kagani da kyar AK yake Jan kafarshi ya karasa wurin da mamaki yace never slap a woman ??? Zancan banza kai Ahmad ya katse shi da cewa wa kamara kuma?? Ak ya zabgamai harara yace wako zan mara kawai dai inaga akwai mahaukata ne alayinku ahmad ya kara kallon motar ya kwashe da dariya har da rike ciki AK yakalle shi ahasale yace zaka sa agoge mun motata ne ko se kagama bata mun rai ahmad ya tsagaita dariyarsa yace ai bani nakar zomon ba AK yaja tsaki ya koma ya zauna akan dakalin kofar gidan ahmad ya leka ya kira mai wanke motocin gidan yasa shi ya wanke motar yaje kusa da AK ya zauna yana kunshe dariyarsa
Suna nan zaune akagama wanke motar suka shiga AK yaja suka tafi
Yana driving amma aransa yana maimaita never slap a woman dakarfi yaja birki harseda ahmada yabige kanshi goshi yadafe tare da fadin wane irin iskanci ne wannan zaka mun lahani AK yadaki sitiyarin motar tare dafadin baby doll !!! Yes ita na mara kenan itace zata mun hakan ahmad yaja tsaki yace waye kuma baby doll AK baice komai ba yatada motar seda suka hau titi yabama ahmad labarin abunda yafaru yakare da fadin ni tsoro ma naji inace ko nayi gamo ne ahmad ya kwashe da dariya yace AK har yanzu tsoronka tun na yarinta yana nan gaka da tsoro kuma kana son kallon horror films nan suka fara tuna yarintar su suna dariya har suka isa gidan su AK yana gama parking ya juyo ya kalli ahmad da nufin yin magana se kuma ya kwashe da dariya ahmad ma Yakama dariya yana fadin kai wai miye kake ma dariya AK ya janyo mashi madubin dake jikin motar yanuna mashi ahmad ya kalli fuskar shi yanda goshinshi yayi kululu inda yabige dazu fuska ya hade tare da fita daga motar masu aiki suna gaida shi ko kallonsu baiyiba ya wuce cikin gidan AK yabi bayanshi yana dariya palon yashiga tare da sallama aysha ce kawai apalon tana waya katse wayar tayi tana amsa sallamar ta gaishe shi ba yabo ba fallasa ya amsa ya wuce sashan grany AK ne ya Zo tabayanta ya rugumeta a tsorace ta juya tana ganin shine ta dake shi akirji tace kabani tsoro murmushi yayi yasake matseta a jikinsa yace naga kin kara wani fresh ne kuana biyu miye sirrin tureshi tayi tace miye sirrin kwa banda kai kara janyota yayi yace Dagaske ?? to me nake baki da har yakawo hakan ?Juya mishi baya tayi tace kawai ganinka da nake ne juyo da ita yayi cikin rada yace to bari nabaki wani abun kinga se kikara fresh kokarin hade bakinsu yake ta tureshi da gudu ta haye sama murmushi yayi yashafa kansa tare da cije lebensa nakasa ya wuce bangaran grany inna ladidi dake labe tun dazu tana kallonsu tayi tsaki tareda fadin akwai sauran aiki agabana
yana shiga bangaran grany ya isko ahmad kuance akan 3siter yana tattaba goshinshi da yakara girma zama yayi kusa dashi yace dazafi ne tsaki ahmad yayi yace se yanzu zaka wani shigo ai da kazauna acan AK yayi murmushi yace to bazan tsaya in gana da rabin raina ba kawai se in biyo wani gardi
Ahmad ya tashi zaune yace wallahi kana bata lokacin kane abanza nasha gayamaka ina yawan ganin aysha da wasu mazan a wurin shakatawa amma kaki yarda
AK yaja tsaki yace kai wallahi kacika abun haushi kawai dan kaganta to se me ai ba auranta nayi ba dazan hanata kula kowa kuma ita tace maka samarinta ne haka kawai se in takura air mutane ba gaira ba dalili kuma ma bandamu ba domun kai kanka shaidane aysha ni takeso so akan me zan damu kaina fitowan grany ne yakatse mashi maganar shi suka juya suna kallonta harara ta maka musu tace miye kuka wani kafeni da ido kunga air kekkyawa to kwalelanku dariya suka sa suna gaidata da fara'arta take amsa gaisuwar AK yatashi yanufi dining yazubo masu abinci ahmad ya kalli grany yace grany akwai fura? Kauda kai tayi tace sedai nono murmushi yayi yaci gaba da cin abincinsa frig tanufa ta dauko mashi fura ta kawo mashi karba yayi yana washe baki seda tazauna tace dawa kayi dambe yakara ma tsayin goshi AK ya kwashe da dariya ahmad ya harereshi yace grany waye kwa banda wannan grany tace subhanallahi garin yaya kuda tun kuna yara sedai kuyi cacan baki me ya kaiku ga dambe
Dariya kawai sukayi basu ce komai
Sarah ce tashigo palon Cikin wata dogur riga pink tayi rolling da farin gyale se farin takalmi tayi kyau sosai se kanshi take zubawa tana zuwa ta gaisa dasu takasa dauke idonta akan ahmad shiko sodaya yadago ya kalleta yaci gaba da cin abincinsa dining tawuce ta dauko spoon tazo tazauna a tsakiyansu itama ta fara cin abincin can ta dago takalli AK tace yaya kaga mun kusa tafiya inaso muje shopping kuma da kai nakeso muje Gashi yau kadai kakeda lokaci mushirya ka kaimu dagowa yayi yakalleta yace da magriban nan kike so muje shopping?? Shagwabe fuska tayi tace yaya please
Kamar daga sama taji ahmad yace ina zakije har aranta taji dadi murmushi tayi tace London yace keda wa?? tace aysha yace mezakuje yi kallon shi tayi da mamaki takasa magana bai ko kalleta ba yace kinyi shiru seda ta tattaro nutsuwarta cikin sanyin murya tace Hutu mikewa yayi yace kushirya idan mundawo masallashi zamu je yana kai nan yafita AK yabi bayanshi yana fadin ji wani karfin hali Dan allah
Da gudu sarah Tawuce wurin aysha tana murna tagayamata
Zasu je shopping kuma da ahmad za'aje aysha tace bana gayamaki ba yanda kike din nan wane namiji ne zai Ganki ya kauda kai
su Ak suna dawowa daga masallaci suka wuce shopping sarah nata kokarin shishshige ma ahmad tun baya kulata har yasake suna fira se da suka zagaya gari kafin suka dawo gida agidan ahmad ya kuana kasancewar dare yayi sosai dasafe ma tare suka yi breakfast su uku abangaran grany bayan sun gama cin abinci ne grany tafito cikin shirinta na fita Ahmad ya kalleta yace grany ina zuwa kuma grany tace asibiti zanje dazu yahya yake cemun matar shi ta haihu suna asibiti AK yace OK hakane ya gayamun kallon sarah yayi yace kuje kiraka grany mana baki ta zunburo tace yaya allah nagaji grany tayi tsaki tace kiyi zamanki dama bana so mikewa sukayi suduka sukafito suna isa guards suka mike AK yakalli yahya dake tsaye yana washe baki Yace yahya ya kuma naganka anan kaida yakamata ace kana wurin matarka yanzu ya sunky da kai kasa baice komai ba ahmad yamika mashi hannu yana mai barka grany takalli yahya tace asibitin zani yanzu wuce muje kabaro mata kazo nan kana washe baki kamar gonar auduga dariya suka sa duka banda sarah data kauda kai mota suka nufa shida grany se da yabude mata baya tazauna kana ya shiga gaba driver yaja suka Wuce suma su AK suka shiga mota Da sauran guards dinsa sarah ta leko ta window tace to yaya ahmad mun gode da kabamu lokacin ka murmushi yayi baice komai ba AK ne yabude motar ya kalli sarah yace shigo tace what??? Yace yes!! Naga bakida niyyar barinmu mutafi ne kuma we are getting late baki ta zunburo tace kai yaya!!!
murmushi yayi yace toh se mun dawo baya taja tana daga musu hannu har suka fita daga gidan sannan ta sauke ajiyar zuciya tare da lumshe ido ahankali ta furta ka kusa zama nawa Ahmad
asma'u ce da inna suka shigo asibiti tana tafe tana ma inna mitar ta tsaidasu yanzu ganshi har 11 tasan se la'asar zasu bar asibitin nan bazata samu daman zuwa shagon dinki ba inna dai tayi shuru dan tasan itace bata da gaskiya tundaga nesa Asma'u ta tsinkayo grany tana zuwa murmushi tayi ganin yadda grany tanufo su da sauri har tana hadawa da gudu inna takama hannun Asma'u tana fadin bismillahi ita kwa wannan lafiyanta Asma'u zatayi magana kenan taga inna taruga da gudu sun rungume juna Asma'u tayi tsaye sake da baki tana kallon ikon allah grany ta kalli inna tace hajiya Hadiza Ashe zan kara ganinki inna baki yaki rufuwa tace bari kedai hajiya maryam ai nadauka kin manta dani ina grany tace inafa zan manta da aminiyata guda kullun kina raina har kuka nasha ma ABIDI akan ya nemo mun ke se yace ina zai ganki acikin wannan babban birni Inna tace allah sarki ina yake jikana yana nan yayi aure ko inna tayi fuskar tausayi tace yana nan amma yaki yayi aure har yanzu inna tace hakane kinsan yaran zamani basa San aure da wuri muna nan dasu Asma'u ce takaraso wurin tace grany ina wuni grany ta juyo da mamaki ganin Asma'u yasa ta washe baki tace Asma'u ko ?? Asma'u tadaga kai tana murmushi da mamaki inna ta kalli Asma'u tace ina kika Santa?
grany takalli inna tace tare kuke ne inna tawashe baki tace ai jikata ce grany tace ikon allah a kasuwa muka hadu da ita ranan yarinyar akwai girmama manya tunda naganta naji ta kuanta mun arai Ashe jikata ce inna tace ai kuwa sannan takalli Asma'u tace wannan itace hajiya maryam aminiyata wadda nake Baku labarin mun hadu a aikin hajji da name Asma'u tadaga kai tace OK natuna ta sannan ta kalli grany tace grany muna shan labarin ki abakin inna kab yan gidanmu sunsan labarinki grany tawshe baki tace allah sarki mun tsaya arana waima me kuka zo yi asibiti ne waye ba lafiya inna tace nice nazo karban magani hawan jini ne yatasani Agaba kinsan jikin tsofa grany tace bari kedai nima ina nan ina fama dashi ni harda siga ma amma ina hadawa da maganin gargajiya yana anfani sosai inna tace hakane allah ya sawake kice kema maganin kika zo karba grany tace a'a matar yaron gidan mune ta haihu shine nazo barka inna tace oh toh allah yaraya suka ce ameen grany tace natsaidaku ko ? Inna tace a'a ba komai ai tunda mun hadu ai shikenan grany tace mukarasa mota na Baku number ABIDI inkunje gida Ku kira se kumasa kwatancan gidan yakawoni na wuni musha fira inna tace toh ba damuwa muje suna isa mota grany ta kalli driver tace kai bani numban ABIDI dagowa yayi ya kalleta yace sorry grany ba katinsa ne awurin mu kuma bama bada shi anyhow fuska ta daure tace kai wai meyasa kun raina nine yazance kabani number katsaya kanamun dogon turanci sunkuy da kai yayi yace sorry ma banada private number dinshi yahya ne kadai yakeda tsaki tayi tace kafadi haka tun dazu katsaya kana bata mun lokaci juyowa tayi takalli Asma'u tace jikata kije wurin yan haihuwa daki mai lamba 8 kice ana kiran yahya Asma'u ta amsa da to tawuce
Tana isa dakin ta shiga Gado biyu ne adakin inda taga wani namiji azaune takarasa bakin gadon tare da sallama juyowa yayi yana amsa sallamar Asma'u tayi saurin washe baki tare dacewa yaya dama Kaine shima da fara'arsa yace nine Asma'u kinga Zainab tasauka ko murmushi tayi ta zagayo inda Zainab din take kuance tace sannu Zainab allah ya raya Zainab din tarufe fuskanta da tafukan hannayanta tare da juya musu baya dariya suka sa mata Asma'u takarbi jaririn tana murmushi tace allah kenan har natuna lokacin da kukazo unguwar mu Zainab tana amarya se tayi ta kuka mune yan zaman daki kullum muna gidan har dare se ka koremu Muke tafiya dasafe kuma mu zamu tashe Ku dariya suka sa su duka harda Zainab Su inna ne suka shigo dakin Asma'u tazaro ido tace ya salam yaya kaga namanta cewa akayi inzo in kiraka inna ce takaraso wajan tana fadin yoke asama'u daga kizo kikira mutum se ki shanyamu awaje grany ce tace ko suma kinsansu ne yahya yayi murmushi yace grany Asma'u kamar kanwa take awurina Layin mu daya dasu grany tace allah sarki inna takarba jaririn tana musu barka grany takalli yahya tace yahya number din ABIDI zaka bamu dagowa yayi yakalleta yace grany me kuma zakuyi da numban yallabai dakuwa ta mashi tare dace gidanku zanyi da numbar Asma'u takalla tace bashi wayan yasamaki numban mika mashi wayan tayi ya karba yasa numban ya mikamata ta karba tayi saving da ABIDI fitowa sukayi daga dakin grany ta musu sallama ta wuce sukuma suka nufi wajan yankan kati
Basu suka bar asibitin ba se la'asar gidan su inna suka wuce suna shiga palon suka iske Abba yadawo daga tafiya dukansu suna zaune apalo bayan sungaisa fa'iz ya kalli inna yace kakus yau me aka muku a asibiti hararan shi tayi tace kai wallahi kafita a ido na in rufe wai meyasa kuka raina nine? yo inba iskanci ba makaranta katura nine dazaka tambayeni abunda akamana ??Dariya yayi yace allah baki hakuri daga tambaya to maida wukar Abba ne ya katse shi dacewa ya isa haka kai bamasan rashin kunya inna tajuyo takalli Abba tana washe baki tace Musa ina wannan aminiyar tawa danacemaka munhadu a aikin hajji ? Abba yace eh ina tune da ita inna tace yawwa to yau munhadu a asibiti abba yace ah toh madalla Abu yayi kyau fa'iz ne ya kwashe da dariya yace nifa nasan inna indai taje asibiti bata rasa kanun labarai abba yajefeshi da jaridar dake hannunsa yatashi yana dariya yabar palon inna tajuya takalli nusaiba taga tana kunshe dariya tace wai ni yaran nan meyasa kuka raina nine nusaiba tahade fuska tac ni kuma me nayi?? Abba yakalleta yace tashi kiba mutane waje zanyi maganin ku ne ai tashi tayi tana zubure baki tayi ciki Asma'u ta tashi tace nizan wuce gida abba allah ya huta gajiya har takai bakin kofa abba yakirata dawowa tayi tazo daga kasa kusan kafanshi tazauna ta sunkuy da kanta kasa tana wasa da zoban dake yatsanta abba ya kureta da ido shidai natsuwar yarinyar yana birgeshi yana jinta aransa fiye da yanda yake jin nusaiba bayan rasuwar kaninshi duk son da yake mashi se yadawo kanta ajiyar zuciya yasauke tareda kiran sunanta cikin sansanyar murya yace Asma'u!!!! Seda Asma'u taji gabanta yafadi da kyar ta amsa da na'am abba !! Abba yaci gaba da fadin Asma'u burin kowane uba nagarine yaga yarsa Takawo munzilin aure kuma ya aurar da ita ga miji nagari Tunda allah yakarbi ran kanina hakkinki na ya yadawo kaina to yanzu banada wani buri da yawuce naga na aurar fake ga mijin da yadace dake dama can harkokin ne suka tsaya shiyasa kikaga nasamaki ido amma yanzu alhamdu lillahi komai yayi daidai hausawee company zasu bamu sarin kaya afarashi mai rahusa to nasan insha allahu zamu dace to dama nagaya maki ne saboda idan kinada Wanda yake tsayayye kifada masa ina son ganinsa yana kai nan ya juyo ya kalli inna yace inna kome kikace inna tafashe da kuka tace me kwa zance banda allah shiyi albarka allah yajikan mahammadu abba yace a'ah inna miye abun kuka kuma Asma'u da tunda abba yafara magana take hawaye kanta akasa aranta tana fadin tofah !! ranar tazo kenan lokaci yayi dazan samu amsar tambayoyin danake yiwa kaina akowane lokaci kenan wane kalan muji zan aura ?? Yaya halinshi yake nagari ne ko akasin haka??dan nan garin ne kowani garin koma badan kasar bane gaba daya?? miye makomar rayuwar umma data KANWATA??ni miye makomar tawa rayuwar?? wasu irin mutane zanje nayi rayuwa dasu ?? shin zasu soni ko kuwa ?? allah kaine gatana!!! kukan inna dataji yasa tafashe da kuka mai ban tausayi abba yadora kanta akan kafanshi yana shafawa hawaye nagangarowa daga idonshi itama Ummi kukan takeyi sunkai kusan minti 10 ahaka palon yayi shiru sautin kukan matan kawai ke tashi abba ne ya rarrashi kanshi kana yararrashe su da hannayanshi biyu yaruqo kafadun Asma'u yatadata tsaye hannu yasa yadago fuskanta idonta alumshe amma hawaye na tsere afuskanta cikin muryan tsokana yace wacece wannan ?? Bude idonta tayi takalleshi Takara sunkuy da kai kara dago fuskanta yayi yace wannan ba asma'uta bace asma'uta jaruma ce batada saurin karaya bata barin wani yayi kuka bare har ita tayi amma ya naga wannan asma'un tana kuka?? Murmushi tayi har saida hakoranta suka fito abba ya goge mata hawaye yace Yawwa wannan murmushin shiyafi dacewa dake rugume shi tayi tace abba nagode hannunta yaja yana fadin muje nasama maki mashin karkiye dare yanzu muga wannan rigimammiyar tabiyoki Tanadai karatu ko? Asma'u tace eh abba Juyowa tayi tama su inna dasuka kafesu da ido sallama tabi bayan amma suka fita suna tafe suna fita yana rike da hannuta gwanin sha'awa seda yatare mata keke napep tashiga ya biya kudin sannan yaleko yace inkinje kicema auta nace tazo takarba tsarabanta Baki ta zunburo tace Abba nawa fah?? Dariya yayi yace har danaki zata kawo maki murmushi tayi tace mungode abba sannan tamishi se dasafe suka wuce suna dagama juna hannu
tana isa gida khadeeja ce kawai apalo tana kallo bayan sun gaisa khadeeja ta tashi takawo mata ruwa mai sanyi tasha sannan tace Umma fah ? Khadeeja tace dazu bayan kin fita aka aiko Zainab ta haihu suna asibiti shine tayi abinci takaimusu bata ma jima da fita ba
Asma'u tace hakane nama ga Zainab din a asibiti da danta kyakkyawa kamar yahya khadeeja tayi dariya tace kai ammah ina wani kyau a wurin yahya da zaki wani ce kyakkyawa? Asma'u tace kuma dai bazaki kirashi da mummunaba ba?
Khadeeja tayi dariya tace ni abun mamaki yake bani wai kaman ba Zainab dinda take guduwa ba lokacin da akawota tana amarya duk tadaga ma bawan allah hankali wai auran dole akamata bata sonshi to koh tayaya tasamu cikin ohooo !!
Asma'u tayi dariya tajefeta da pilo tana fadin allah ya shiryeki khadeeja tace ameen wallahi se kuma suka kwashe da dariya Umma ce tashigo da sallama suka amsa Asma'u ta mike takarbi kwanonin abincin dake hannunta ta kaisu kitchen ta dawo tazauna Umma tace firar me kuke tunda nashigo nakejin dariyarku ??
Khadeeja tace hmmm ba komai Umma kawai shirman Zainab din yahya muka tuna shine muke dariya Umma tayi dariya tace awho!!! ai kwa yanzu ma tagama wani shirman wai bazata ba jariri nono ba kunya takeji khadeeja tace wata sabuwa inji yancaca kuce wani sabon aikin ne Yakama yahya na koya mata yanda ake bada nono Asma'u ta harareta tana mata alama datayi shuru
Umma tace shibada nonon ne se yahya yakoya mata ??
Khadeeja ta kwashe da dariya tace toh ai tunda ya koya mata mai wuyan wannan mai sauki ne asma'u ta kara jifanta da wani pilon tace khdy wai bazakiyi shuru bane Umma ta tashi tana girgiza kai tana murmushi tace Ahab !! Indai khadeeja ce ai sedai shiriyar ubangiji bata jin kunyar fadan komai agabana sedai ni naji kunyarta khadeeja tayi dariya tace ai gaskiya nafada Umma banda iskanci taya bataji kunyar haihuwa ba zataji kunyar bada nono?? Umma tayi waje tana fadin ke kika sani ni kinfi karfina kiyita fadi allah sa Zainab din tajiki dama kun saba khadeeja tayi dariya tadawo kusa da Asma'u ta zauna tace Ammah kinyi kuka meke damunki?? Asma'u tadago takalle ta tace kuka kuma??
Khadeeja tace eh kuma karma kiyi tinanin yimun karya dan kinsan ba yarda zanyi ba ? Asma'u tasauke ajiyar zuciya kana taba khadeeja labarin yanda sukayi da Abba khadeeja ta dafa kafadanta tace karki damu Ammah everything will be fine kinada hali mai kyau so insha allahu zaki samu miji nagari kuma kiyi istihara kibama allah zabi se kiga andace nima zan tayaki
Asma'u tayi murmushi tace thank you yanzu natabbatar cewa KANWATA ta girma khadeeja ta turo dan kwali gaban goshi tace se ma kinji nasihar da zan maki ranar auranki zakisan na girma Asma'u tatashi tana dariya tace um um kirike nasihar ki ni tafi karfina je kima Zainab din yahya dariya suka sa Asma'u tajuyo takalli khadeeja tace ya akayi kikasan nayi kuka idona yayi ja ne?
Khadeeja tadauki remote tana canza chanel tace mutumin dabaya yawan kuka duk ranar da yayi se angane sannan takalli asma'u tace naga kina yawan sauke ajiyar zuciya ne Kuma naga kowace rana kina shigo mun da tsaraba yau naga kinshigo hannu rabbana shiyasa nabi diddigi na gano dalili
asma'u tagirgiza kai ta wuce tana fadin you can't be serious
Khadeeja tayi dariya tace I can but sometimes....
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
🖊na marubuciya Husna kabir zarewa( the mammah girl)
🖊da sunan allah mai rahama mai jinkai...
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
2⃣0⃣⏭2⃣5⃣
Bayan kuana biyu da faruwar hakan...
ranar laraba da safe
aysha ce adakin sarah suna breakfast sarah tadago ta kalli aysha tace idan mungama zaki rakani gidan su ahmad muyi ma Momy sallama tunda kinga gobe zamu wuce
aysha tadago tana murmushi tace Momy zakima sallama ko ahmad??
Sarah tayi murmushi tace dukansu
Aysha tace amma ai yau Wednesday kenan ahmad yana office sarah tace no munyi waya dazu yace yana gida se yamma zaije office aysha tayi murmushi tace hmmm kice dai yanzu kun shigo duniyar masoya sarah tayi yar dariya tace all thanks to u M's AK hausawee dariya suka sa tare da tafawa
Khadeeja!!! Khadeeja!!! wai bakya jina ne ? Khadeeja tafito tana daura dan kwali tace Umma sama zuciyar ki ruwan sanyi gani nafito
Umma tace tun dazu nake biye dake kizo kikaima Maman luka kunun ayar nan kar ya tsinke mun yau bansan meyasa bata aiko an karba ba khadeeja tace toh Umma kawo inkai daukan ruba tayi tana fadin Umma indauki daya Umma tace mezakiyi dashi bayan kuma ga naku nan? khadeeja tace Umma kedai kawai kice indauka Umma tace toh naji jike kina kaimata fa kidawo karki Dade khadeeja tanufi get tana fadin Umma zanje gidan Zainab din yahya Umma tace me kuma zakiyi acan bayan jiya ma kinje khadeeja har takai get tadawo tace Umma ingaya maki mezan je yi?? Umma tayi murmushi ta tashi tana girgiza kai tace um um jike abunki bansan ji allah taroki khadeeja tayi dariya tace ameen ta wuce daga gidan
tana isa daidai lokacin Maman luka tana bude shago khadeeja ta ijiye robar hannun ta bayan sun gaisa tace Maman luka yau lafiya baki fito da wuri ba Maman luka tayi fuskan tausayi cikin hausanta da bai fita tace deeja luka ne ba lafiya khadeeja tace ayyaaa ya jikinshi to Maman luka tace jiki ba sauki wooooo
Khadeeja ta kwashe da dariya Maman luka ta hade fuska tace deeja abunda kanayi ba caw fah na fadamaka yaro ba lafiya amma kana dariya khadeeja ta kunshe dariyarta tace sorry son kudinki ne naga yayi yawa kince jiki ba sauki amma kin bude shago Maman luka tace ha'an which can son kudi base mun bude sago zamu samu kudi magani ba yanzu dai tunda kinga I am busy kataimaka kasa mun kunu din a frig khadeeja taja dabaya tarike qugu tace iyeee dan ma kinsamu nakawo maki Maman luka tajuya takoma shago tana fadin deeja please naaaa khadeeja tace amma baban luka na gida ko?? Maman luka tace yes se kuma ta dawo wurin khadeeja tace why u de ask?? Khadeeja tayi murmushi tace nothing Maman luka takoma ciki shago khadeeja takara kallonta ta kwashe da dariya Maman luka bata kula taba dan tasan hali
Khadeeja tacire gyalenta ta daure aqugu tadawki robar da kunun ayan ke ciki ta nufi frig
Su sarah ne akan hanyar su ta zuwa gidan su ahmad cikin wata sabowar BMW fara se shiki take kana ganinsu kaga ya'yan manya aysha tana sanye da wata doguwar riga baka tayi roiling da milk color din gyale jaka da takalminta milk color ne sarah kuma wando ne da riga ajikinta wadon tight ne baki se rigar ja da adon baki ajiki ta roiling da bakin gyale sunyi kyew bakadan ba aysha ce ke driving sunzo daidai shagon Maman luka aysha taja birki ta tsaya sarah da ke charting awayarta iPhone 6 tadago takalleta tace yadai?? Aysha tanuna tanuna khadeeja dake tsaye tana kokarin bude frig tace kalla style din jikin yarinyar can sarah tamaida kallonta kan khadeeja tawani ya tsina fuska tace yana da kyew menene? Aysha tace ina sonshi sarah ta hade fuska tace haba aysha kar kijamana raini mana taya zakije wajan waccan karamar yarinyar kice tabaki style aysha tace come down bawai rokonta zanyi ba da kudina zan saya horn tafara dannawa khadeeja tana jinsu batago dago ba taci gaba da aikinta Maman luka kuma tashiga gida ta dawko sauran kayan sarah taja tsaki tace ji wani rainin hankali tana jin mu fah aysha takashe motar tafita tana fadin kibiyo da wayarki sarah taja tsaki tafito tana yatsina fuska
kusan khadeeja suka zo aysha tace ke!!! Ke!!! ba kya jine ? Maman luka da fitowarta kenan daga gida takalle su tace lafiya me kuna so ? basu ko kalleta ba aysha tasa hannu taja rigar khadeeja tabaya tace ke wai ko kurma ce khadeeja tamike tsaye ahasale tace malamai wai lafiya ko sallama babu kunzo Kun mun tsaye akai kuma ni ba ke sunana ba Sarah tace ke kar kiraina mana hankali basunan ni muka zo jiba style din jikin ki mukeso khadeeja ta kalli rigar dake jikinta wata doguwar riga ce mai shegen kyew da Asma'u tadinka mata ga salla baya tajuya ma sarah tace toh aunty zage mun zip din se nacire nabaki atare suka ce what??? khadeeja tace yesss to inba haka kwazo kusani agaba kuce nabaku style din jikina Maman luka da ke gefe ta kwashe da dariya sarah ta juya tamata wani irin kallo bashiri tafada shago
Sarah ta juyo ta saita khadeeja da wayanta tana fadin photon style din zamu dawka kuma saya zamuyi dama meza muyi da tsumman dake jikinki ahasale khadeeja tasa hannu tabige wayar tafadi kasa har saida tafashe sarah tadaga hannu da nufin marin khadeeja
Cikin zafin nama khadeeja tarike hannu tare da Nuna ta da dan yatsa cikin kakkawsar murya tace don't even try it sannan tasake mata hannu da karfi har saida tayi yar kara aysha tabude baki zatayi magana amma da suka hada ido da kadeeja seda taji hantar cikinta ta kada bashiri ta hadiye maganar ta tare da jan hannun sarah suka tafi har sun shiga mota khadeeja tadawko wayar sarah da tafadi tana fadin wakuka barma wannan Nokia din taku sarah taleko tace kinfimu bukatar ta aljana kawai aysha ce tayi saurin tada motar ganin khadeeja tanufo su har motar tafara tafiya khadeeja ta wurga wayar daidai setin kan sarah ji kake kwal sarah tafasa uban ihu tare da dafe kai ta window taleko taga khadeeja na dariyar keta cike da bakin ciki tace I HATE YOU!!!! Khadeeja ta kara kwashewa da dariya tace HATE YOU MORE sannan tajuya tanufi shago tana fadin Maman luka matsoraciya fito sun tafi Maman luka ta fito tana washe baki tace deeja bakada caw amma kamun daidai yara din basuda kunya khadeeja tadauki fanta daya afrig tace Maman luka nawa kike saida fanta Maman luka tahade fuska tace Dari khadeeja tace kunun aya gah Maman luka takara hade fuska tace sima Dari Khadeeja takama hanya tana fadin nadauki fanta amadadin kunun aya Maman luka tace ha'an deeja abunda kanayi ba caw khadeeja bata kulataba tawuce Maman luka tabita da kallo can tace toh dija kasa gyale din mana khadeeja bata juyo ba tayi murmushi ta kwance gyalen qugunta tana fadin kema ki gyara zip din rigarki
Maman luka tayi saurin kai hannu baya taji zip dinta abude ido tazaro tace cayyyy kenan shiyasa deeja ya tambayeni ko baban luka yana gida can kuma tayi dariya tace kai deeja wahala tajuya tana fadin yaya original kanwa jabu
Su sarah har sun kusa is a gidansu ahmad amma har yanzu tana dafe Dakai da kai tana hawaye aysha takalleta tace sorry duk ni naja haka tafaru sarah tayi tsaki takauda kai gefe tana fadin wallahi duk ranar da nakara ganinta se namata abunda se tamutu tana regreting aysha ta kunshe dariyarta tace yi hakuri kinga yanzu mukaje haka yakike tunanin ahmad zaiji sarah tayi murmushi tana gyara fuskanta
suna is a gidan suka iske Momy da ahmad zaune apalo suna fira da fara'a Momy ta tarbesu dams tajima da Sanin Sarah tana son ahmad bayan sungaisa Momy tace yanzu ahmad yake cemun zakuyi tafiya ko sarah ta sunkuy dakai irin kunyar nan tace eh momy shine nace bari nazo muyi sallama Momy tace kin kyewta kwa bari akawo maku abun sha ko tashi tayi tanufi kitchen sarah tasa kafa ta zuguri aysha ta dago ta kalleta alama Tamata da ido ta tashi tana fadin Momy bari natayaki suna fita tadawo kusan ahmad tazauna tana fadin yaya yagarin
remote ya dauka ya kunna TV yana fadin fine se tafiya ko? Murmushi tayi tace eh amma zanyi missing dinka dagowa yayi ya kalleta suka hada ido ta sauke kanta kauda kansa yayi yace sati daya kamar gobe ne kundawo kawai dai idan kunje kusan irin wuraran da yakamata Ku shiga dawowar su Momy ne ya katsemasu firansu bayan sunsha ruwa sukama Momy sallama suka fita har parkin space ahmad ya rakasu bayan sun sunshiga mota sarah tace yaya zaka rakamu airport gobe ko? Juyawa yayi ya koma yana fadin allah ya kaimu ...
washegari dasafe misalin karfe10 khadeeja ce akan hanyarta ta zuwa gidan Abba karbo tsarabarta
Tana isa gidan bangaran Ummi tanufa azaune ta isko su duka apalo nusaiba ce tazo dagudu suka rugume juna kusan Abba khadeeja taje ta zauna kamar zata shige jikinsa Abba ya shafa kanta yace auta yau kice agidan mu kin tuna dani kenan fa'iz dake gefe azaune yace Abba tsarabarta tazo karba khadeeja ta harareshi tace Abba manta dashi kar yahadamu fada Ummi tayi dariya tace ai gaskiyarsa khadeeja bakya son zuwa nangidan Asma'u tafiki zumunci baki tazunburo ta mike tsaye tace tunda hakanema ni tafiyata zanyi Abba ya riko hannunta yace a'a yi hakuri kyalesu kawai ni kinji nace wani Abu?
murmushi tayi tace Abba toh kabani tsarabar sauri nake Umma zata aykeni
Fa'iz ya kuashe da dariya yace aha'ap ai nasani ahasale khadeeja tanufi wurinshi mikewa yayi yana fadin in zaki tafi ki fadamun muje tare ina so inga ummana tsaki tayi tace ai kasan hanya base kajirani ba nusaiba ce Tamika mata ledar tsarabar takarba ta dawo wurin Abba tazauna tace Abba miye aciki murmushi yayi yace riguna ne guda biyu keda asm'u se gyalen shikuma na ummanku ne murmushi tayi tace Abba mungode kana ta tashi tamusu sallama tawuce har takai kofa Abba yace kifa biya kigaida inna nasan halinki dariya tayi tace toh Abba
tana fita bangaran inna tanufa bakowa apalon tawuce bedroom nan ma bakowa har ta juya se taji karan ruwa abayi dawowa tayi tastaya takure kofar bayin da ido
Inna ce tafito wanka birki taja ta tsaya tana kallon khdeeja da ta kafeta da ido tsaki tayi tace ke wallahi bakida hali haka kawai se kishigo mun daki ba sallama kuma kinganni ko gaisuwa babu to mekika zoyi nan khadeeja tagyara tsayuwarta tace ina kuana inna tanufi drowan kayanta tana fadin kirike kayanki bana so khadeeja tayi dariya tace inna mugyambo inna tajefeta da rigar hannunta tace wai ba narabaki da kirana da wannan sunan ba wallahi duk ke kikasa yaran gidan nan suka rainani khadeeja tayi dariya tace to yi hakuri bani kudin mashin inna ta kauda kai tace banda shi khadeeja ta juya tana fadin Wanda gareki subata inna tabiyota tana fadin bakinki yasari danyan kashi khadeeja tanufi har hanyar fita tana murmushi tace se anjima inna tace kigaida ummanku kuma kice ma Asma'u tazo ina kiranta
su ahmad ne da AK zaune a airport sun rako su sarah mikewa sukayi jin afara sanarwa AK yakalli aysha yace toh honey se munyi waya ko murmushi tayi tace OK suka maida kallonsu kan su sarah da tasa ahmad agaba kamar zatayi kuka ahmad yadago ya kalleta yace sarah tafiyar nan fah ba dole inkinga bazaki iya ba se kifasa murmushi tayi tace yaya zanyi kewarku kauda kai yayi baice komai ba kamar daga sama yaji ta rugume shi tsaye yayi kamar gunki aranshi yana fadin toh ita wannan miye nufinta janyeta yayi yana fadin is OK kuje karku rasa flight dagowa tayi ahankali tace I LOVE YOU!!! afirgice yadago yana kallonta sannan ya juya ya kalli AK yaga su yake kallo yana murmushi dawo da kallonsa yayi akanta ahankali shima yafurta LOVE YOU TOO!!! Murmushi tayi takoma wurin AK tarugume shi dariya yayi yace hmmm my little sis tafara soyayya ko
duka takaimasa a kirji tace um um yaya kadaina sani kunya dariya sukayi duka banda ahmad da yafada dogon tunani shi dai yasan ba soyayya tsakaninsa da sarah duk wani Abu da masoya keji atsakanin su shibaya jinsa akan sarah asali ma shi kallon kanwarsa yake mata amma yanda yaga farin ciki afuskar AK bazai iya kallon kwayar idonsa ba yace baya son kanwarsa ba sallamar dasuke masane takatse mishi tunanin shi hannu yadaga musu ya juya AK yabi bayansa suna fitowa ahmad yace AK bani makullin bakar motarka ni gida zan wuce AK yace haba Ahmad wane irin gida kuma bayan kasan munada aiki dayawa agaban mu Ahmad yakarba makullin yana fadin bajimawa zanyi ba muhadu a office motar yashiga yaja ya wuce yabar AK atsaye yana kallonsa kafin shima ya shiga dayar motar driver yaja suka wuce guards na rufa masa baya AK yalura da yanda jikin ahmad yayi sanyi amma shi atunanin shi tafiyar da sarah tayi ne toh amma shi meyasa baya jin komai dan aysha ta tafi???
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚👨👧DOMUN KANWATA👩👧
🖊na marubuciya Husna kabir zarewa( the mammah girl)
🖊da sunan allah mai rahama mai jinkai....
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
2⃣5⃣⏭3⃣0⃣
Khadeeja ce da fa'iz akan hanya suna tafe suna fira har suka iso unguwar su abakin hanya khadeeja taga wani mai agwalima wajanshi tanufa fa'iz yabi bayanta yana ina kuma zakije dama kinsan kinada kudi shine baki bari munshigo keke napep ba
Bata kulashi ba har ta isa gurin mai agwalima tace samun ta 50 fa'iz ya Sosa kai yace deeja nifah? Murmushi tayi tace kaima asamaka ta 50 baki yawashe yana fadin thank you sister mai agwalima yasama kowa tashi aleda ya mika mashi khadeeja takarba tata tajuya tana fadin yabaka kudinka fa'iz yazaro ido yabita da kallo aranshi yana fadin ji wani karfin hali yanzu da banada yan canji se tasa insha duka abanza maida kallonsa yayi wurin mai agwalima yaga ya miko mashi hannu yana murmushi fa'iz yayi yake 😁 ya mika ma mai Agwalima ledar dake hannunsa mai agwalima ya girgiza kai yana dariya yace kudin zaka ban fa'iz yasa hannu aljihu ya ciro yan hamsin guda biyu ya mika ma mai agwalima sannan yabi bayan khadeeja yana mita koda ya iso wajanta har tafara shan agwalimar kallonta yayi cike da takaici tsaki yayi yace toh yanzu da banada kudin fa?? Agwalima takai bakinta tana fadin nasan Kanada su ne fa'iz yace ehh dakika bani ba juyowa tayi takalleshi tace bani nabaka ba amma naga lokacinda Abba ya mikamaka Dari yace muhau mashin dama nazuba maka ido ne inga iya gudun ruwanka se naga har mun iso baka bakada niyyar tsaida mai mashin
fa'iz ya Sosa keya yana murmushin yake birki yaja ya tsaya yana fadin deeja ji wata zukekiyar mota dan allah khadeeja taja tsaki takalli inda yake nuna mata motar AK ta hango tana tafiya ahankali ido ta kankance tana nuna motar da yatsa fa'iz yamatso yana dariya yace kai deeja allah yamaki son abun duniya garama ni nayi magana ke kinma kasa bude baki hahahaha
ahankali ahmad ke driving jikinsa duk amace se yanzu yakejin haushin kanshi meyasa ma ya amsa ma sarah bayan yasan baya sonta anya kwa baiyi kuskure ba glass din motar ya sauke yana shakar iskan waje
kadeeja tana nan tsaye har motar ta iso wurin su tarasa mezatayi can ta jefi motar da agwalimar datafara sha kafin tafara Neman duwatsu
Ahmad ya lumshe ido yana shakar iska yaji fadowar wani Abu kusa dashi da sauri yaja burki yana dubawa baiyi aune ba yaji ruwan duwatsu da sauri ya zuge glass din motar ya fito
fa'iz ne yazo da gudu ya rike khadeeja yana fadin ke deeja bakida hankali ne anga yamaki hakan da kikayi shi zaisa ki mallaki irin motar ne ko me hannu tasa ta tureshi tana fadin dallah matsanan juyowa fa'iz yayi afirgice jin an rufe kofar mota da karfi yana ganin Wanda yafito daga motar yadora hannu biyu aka 🙆♂ yace cinekeee!!! Deeja u don kill us kin kosan wakika tsokano sir ahmad ne fah khadeeja ta karasa wurin ahmad takalleshi tace dama Kaine ni ina maka kallon mutumin kwarai ashe bahaka bane tanuna motar tace yanzu saboda wannan keke napep dince har zaka dauki hannu kamari mutum shidai ahmad yazama kamar gunki se binta yake da kallo kaman yasamu TV ko kiftawa bayayi
fa'iz ne yazo da gudu ya bangaje khadeeja ya tsaya gaban ahmad yayi fuskan tawsayi yace yallabai dan allah kayi hakuri kanwata ce tana dan fama da matsalan iskokai ne khadeeja tasa hannu taja wuyan rigan fa'iz ta maidashi bayanta matsowa tayi daf da ahmad tace ka kalleni sama da kasa kaga nama kama da mara hankali ahmad dai yazama kamar wawa kallonta yayi sama da kasa ya girgiza kai khadeeja tace yawwa so let me warn u nan gaba ko amafarki kaga kamari wata mai kama dani toh kayi gaggawan farkawa kayi addu'a bcz that will be your worst nightmare fa'iz ya kara matsowa yasa hannu yataba goshin khadeeja yalangwabar dakai yace deeja zazzabi ko?? Sannu hannunta yaja yana fadin zo muje gida kisha magani khadeeja tajiyo tana kallon ahmad daya jingina jikin mota yana kallon ikon allah lebenta nakasa ta cije tare dakarkada mashi dan yatsanta alaman kashidi kenan ahmad yakai hannu bayan wuyanshi yashafa tare da lumshe ido hangota yake lokacinda take motsa dan karamin bakinta tana masifa ahankali ya furta
Magical eyes!!!
softly lips!!!
Heart touching voice!!!
100% beautiful!!! yakai minti biyar ahaka hannunsa yakai yadan bubbuga gefan zuciyarsa tare da fadin wake up ahmad ahankali yabude idonsa tare da sauke wata nannauyar ajiyar zuciya motar yabude yashiga yana zama yaga agwalimar data jefo cikin motar agefen kujera dauka yayi yana murmushi yakai bakinsa daidai inda tasha tare da lumshe ido yakai Minti 10 kafin yatada motar yatafi yana jinsa cikin wani farin cikin da baisan dalilinsa ba se yaji duk yamanta damuwarsa
har suka isa gida fa'iz na rike da hannun khadeeja ita abun ma dariya yake bata suna shiga suka iske Asma'u na wanke gororin kunun aya fa'iz baibi takanta ba ya zaunar da khadeeja kan kujera yawuce daki Asma'u ta taso tazo kusan khadeeja tana fadin khdy lafiya menene fa'iz ne yafito da magani da ruwa ahannunsa yana fadin ammah dan allah barta batajin dadi maganin ya balla yamika ma khadeeja yana fadin karbi kisha kinji? Harara khadeeja ta maka mashi tace wai miye haka dan allah Asma'u takarba maganin tana taba goshin khadeeja tace khdy ba kya jin dadi ne karba maganin kisha kinji koza muje asibiti ne? Khadeeja ta zunburo baki tace nifa ammah lafiyata kalau Asma'u takalli fa'iz tace kai wai miye ne?
zauna yana fadin ammah yau deeja tayi abunda sabon kamun hauka kawai keyi khadeeja ta zunguri fa'iz tana keftamashi ido alaman yayi shuru
Asma'u takallesu tace meke faruwa ne??
fa'iz ya hadiye yawu yace kinsan sir ahmad na white house? Asma'u ta gyada kaialaman eh fa'iz ya gyara zama yace toh yau shi kadeeja tama ruwan duwatsu yanda kikasan tasamu shedan ke saura kadan tazabga mai mari badan nariketa ba karkiso kiga wani irin kallo dayake mata badan allah yasa nayi dabaran fakewa da zazzabi najanyota bako? Hmmm da ba abunda zai hanashi babbalata awurin Asma'u takalli khadeeja tace khdy dagaske hakan tafaru ? Khadeeja ta zunburo baki tace toh bashine yamare kiba ai dama nace duk ranarda nagansa se yagane kuransa Sa'a ma yaci Umma na mutunci da momynsa da har Marin se narama maki asma'u tazaro ido tana salati tace khdy yaushe nagayamaki cewa ahmad yamareni ? Kawai dan ranan kinga motar akofar gidansu shine zakimai tijara khadeeja tafara tsorata cikin rawar murya tace amma....ai.. acikin.. Motar nagansa fa'iz yace toh kawai dan kingansa amotar kika San ko tasa ce ? Dariya yafara ganin idon khadeeja ya cicciko Asma'u tace khdy bashine ya mareni ba ni Wanda yamarenin ma tun ranar bansake ganinsa anan layin ba kuma ni nayafe masa khadeeja tayi fuskan tawsayi tace to ni yanzu ammah yazanyi fa'iz ya kwashe da dariya yace ya kwa zakiyi yarinya bayan kindibo ruwan dafa kanki kwaniki ma aka watsa ma wata yarinya asid abayan layinmu da akayi bincike akagano wani saurayi tama wulakanci shine yawatsa mata Asma'u tasa hannu ta tallabin kan fa'iz tace kai dallah yima mutane shuru hantar khadeeja kam banda kadawa ba abunda take zufa tafara keto mata ba shiri tawarci maganin hannun Asma'u takai baki ta kora ruwa tana zare ido get sukaji anbude atsorace khadeeja ta waiga ganin umma ce yasa tasauke ajiyar zuciya fa'iz yakalleta yana kunshe dariyarsa harara ta maka mai amma ba bakin magana Umma takaraso suka Gaisheta fa'iz yakarbi ledar mongwaron data shigo dashi yana washe baki asma'u kuma taje takamata ruwa Umma tazauna tana kallon khadeeja tace waya taba mun auta ne naganta haka Asma'u tace ba komai
Umma takamo khadeeja tana fadin yazakice ba komai bayan baka nasaba ganinta ba tsarabar ma datake zuwa da gudu takarba yau ko kallonta batayiba fa'z yayi dariya yace ai Umma yau ruwa ne yadaki babban zakara Umma tace kamarya basu ce komaiba khadeeja tatashi jiki asanyaye tana Jan kafa tanufi ciki
fa'iz yabita da kallo yana dariya yace deeja kinganki kuwa?? Yasin kamar ankwara ma salad ruwan zafi khadeeja bata kulashi ba tashige Palo Asma'u ta mikama fa'iz mangwaron da tawanke tana fadin dan allah fa'iz kyaleta hakanan Umma tace shine ya tsokaneta ko?? Asma'u tace umm
Seda fa'iz ya gutsura mangwaro kana yadago yakalli Asma'u yace yawwa ammah ni nama manta inna tace wai gobe kije tana son ganinki Asma'u ta langwabar dakai tace me kuma zan mata fa'iz yayi dariya yace ohoo inna tana rasa abunyi ne
Umma takalli yanda fa'iz ke gaptar mangwaro tayi murmushi tace ko mangwaro zaki tsinkomata fa'iz yace mangwaro kuma? ganin umma da Asma'u na murmushi yasa yakalli mangwaron hannunsa yayi dariya yace kai Umma bafa santi nayi bafa kawaidai namanta ne Umma tace ai dama bance santi kayi ba khadeeja ce tafito tadauki ragowar mangwaron ta juya dariya suka sa kasaksa fa'iz yakalli khadeeja yace afito lafiya mai jigo azabure yamike ganin ta ijiye mangwaron ta wawuro icce aguje tabishi har get yafita yana fadin se dasafe Umma
wunin ranar dai haka ahmad yayishi cike da fariciki daga yarufe ido khadeeja yake gani shikadai inyatuna abunda yafaru se yayita murmushi har dare yayi daga yarufe idonsa ita yake gani
Washegari tunsafe yake zaune akan dakalin kofar gida wai ko zai ganta ta wuce amma har 8 tayi yawuce office baiga wucewanta ba
asma'u ce zaune adakin inna bayan sungaisa tace inna kince akirani lafiya inna tazauna kusa da Asma'u yo ke ranan kintafi munata kokekoke muka manta bamu kira lambar da hajiya maryam tabamu ba shine nace kizo mukira muji kinga saba alkawari ba kyew asma'u tayi murmushi taciro wayarta cikin post ta nemo numbar datayi saving da ABIDI tadanna kira Tamika ma inna tana fadin gashi nakira gaisawa kawai zakuyi dan ba kati inna taki karba tana fadin yo ke kya bani ni mezan cemasa ke kiyi magana in ya kaima hajiya maryam wayar se kibani asma'u tace to inna ni mezan cemasa?? wacece ni?kuma daga ina ?
AK yafito wanka kenan yaji wayarsa na ringing mamaki yayi ganin sabuwar number Da kamar kar yadaga seda takusa tsinkewa se kuma yadaga tare dazama bakin gado
asma'u tana jin alamun andaga kiran takara wayan akunne batace komai ba sun jima ahaka asma'u tadago wayarta taga har yanzu kiran bai katseba gashi katin bayawa
AK yana shirin aje wayar yaji wata siriruwa murya tamishi sallama wayar yamaida akunne tare da lumshe ido ya amsa sallamar shuru suka karayi na yan mintuna
Asma'u haushi duk yacikata ga katinta natafiya ga inna takafeta da ido bare takatse kiran tsaki tayi aranta tana fadin wannan wane irin mutum ne afili kuma ahasale tace ABIDI ne
tadayan bangaran azabure AK yamike yana fadin how dare you call me by that name who the hell are you??
afirgice Asma'u takatse wayar tsaki AK yayi ya ijiye wayar har yajuya sekuma yatuna grany ke kiransa da wannan sunan to ko itace tasa takira dawowa yayi ya dauki wayar yakira asma'u naganin kiran Tamikama inna wayar inna hannunta har rawa yake takarba asma'u ta daidaita mata ita tasa akunne tamike tsaye ta kalli gabas kamar mai Shirin kiran sallah moryarta gaba daya taware ta zabga sallama Seda asma'u ta zabura
AK nashirin magana kenan yaji an kwararo wata doguwar sallama
Assalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu
Seda AK yacire wayar akunne ya duba numban yakara maida wayan akunne ya amsa sallama
Inna tagyara tsayuwa tarike qugu tareda da gyaran murya tace kagane mai magana ? ahankali AK yace a'a aransa kuma yana fadin yau naga takaina shi duk atunaninsa ma ya'uwansa ne na yola murmushi yayi jin inna namai bayanin ko ita wacece dan yaganeta akan dresing mirror yadaura wayar suna fira yana shirinsa dan yanda inna ke magana ba bukatar handsfree asma'u tayi dariyar har tagaji inna namata alama tayi shuru amma takasa sedai inna tafita tabar mata dakin ta koma palo tacigaba da wayarta tun tanajiran inna tagama tabata wayarta har bacci ya dauketa
har AK yagama shirinsa inna nasurutu wayar yadauka yafita yna fadin inna bari nakaiki wurin kawarki yana zuwa ya mika ma grany wayar nanfah yaga cabta dan grany wani dan karamin aikin hajji tayi safa da marwa ta dinga yi daga wannan kujerar zuwa waccan fallon kwa tazagaye shi yafi so ashirin tun AK na kallonta yana dariya har yagaji ya kunna tv yana kallo
fa'iz ne yaleko palon inna ya iskota tanawa grany sallama akan se taganta goben kwashewa yayi da dariya yace wai dama inna waya kikeyi ni har nabiyo da Igiya inace ko kinzauce ne mudaureki Inna dai ba baKin magana se zare ido take tana shafa saman makogwaronta da da yabushe fa'iz yakara kwashewa da dariya yamatso kusa da ita yana fadin gaskiya inna irinku ake bukata awajan da'awa wai wannan murya haka tundaga get nake jiyoki
Inna Tamaka mai harara cikin dasashshiyar muryarta tafara fadin wallahi kafita a ido...... bata karasaba tari ya sarketa da gudu fa'iz yanufi frig ya dawko mata Goran ruwa inna takarba takafa kai seda tayi Rabi ta aje gorar banda dariya ba abunda fa'iz keyi harda rike ciki inna dai ba bakin magana se harare harare
abangaran grany ma haka abun yake koda tagama wayar tayi sharkaf da gumi akan kujera tazube ragwazab tana maida nunfashi Ak yatintsire da dariya yace grany Ashe haka kike waya awahale shiyasa kikace ba kya son rike waya grany dai se binshi take da ido dan har wani jiri jiri takeji shi kanshi AK biyu biyu take ganinsa bashiri tamike tanufi bayi dan watsa ruwa AK ya kwashe da dariya ganin yanda take rangaji kamar mai jin bacci
da yamma misalin karfe 5 ahmad ne zauna akan dakalin kofar gidansu yana waigen waigen ta inda zaiga bullowan khadeeja kamar daga Sama yaganta tashayo kwana cikin uniform dinta na islamiyya wani murmushin farin ciki yasaki khadeeja kamar ance tadaga kanta ta hangeshi azaune gabanta ne yafadi jitayi kamar ta koma se kuma tadake taci gaba da tafiya Ahmad naganin ta kusa isowa yatashi yanufeta yana murmushi ai khadeeja naganin ya nufota ba shiri ta fada wani gida ta turo kofar tana maida nunfashi ahmad yayi tsaye yana mamaki kamar ba ita bace jiya tasa shi agaba tana mai fitsara ba to kodai gaskiyar yayanta ne tanada iskokai
Murmushi yayi Yakoma yazauna yana jiran fitowarta amma har aka kira sallar magriba bata fito ba hakanan yatashi yashiga gida dan yin alwala yana shiga khadeeja tafito dama tana lekenshi ta jikin get din gidan asukwane tabar layin kamar zata tashi sama dan gani take kamar yana binta abaya
koda ahmad yafito kofar gidan ya kalla ya ganta abude murmushi dan dama yaga lokacinda tayi fitar harsashe daga gidan ahankali ya furta
I will find u my flying Bird!!!
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
🖊na marubuciya Husna kabir zarewa( the mammah girl)
🖊dasunan allah mai rahama mai jinkai......
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
3⃣0⃣⏭3⃣5⃣
aguje khadeeja banke kofa tashiga gida ta maida kofar ta rufe tasa sakata ta sulale akasa tana maida nunfashi asma'u ce tafito da hijab ahannunta da nufin fita tadubo ko lafiya yau khadeeja bata dawo ba da gudu takaraso wurin khadeeja tana fadin khdy lafiya ? Menene? Waya biyoki ? Meya tsaidaki baki dawoba har ana kiran magriba?
Khadeeja tamike tana fadin ammah wannan tambayoyi haka ajere wacce zan amsa maki bari muyi sallah sena fadamaki amma yau allah ne yamun alam nasharaha da sedai kiga nadawo fuska akone asma'u tace subhananllahi garin yaya kenan? Khadeeja bata kulata ba tashiga ciki tana fadin ammah biyomun da jakata asma'u tadauki jakar jiki asanyaye tabi bayan khadeeja
Seda suga gama sallah suna cin abinci khadeeja keba asma'u labarin abinda yafaru asma'u tayi dariya tace to waike gudun da kikayi kina tunanin nufokin da yayi asid zai watsa maki kenan ? Khadeeja takai lomar tuwo bakinta tace to inba haka ba hakuri kike tunanin yazo yabani kome asma'u tayi dariya batace komai ba dan tagane maganan fa'iz ta jiya ita ta tsorata khadeeja
Washegarin ranan da safe AK ne zaune apalon grany yana breakfast grany na gefe tana kokarin tura wani Abu jikanta AK yadago ya kalleta yace wai ni grany ina zakije ne tundazu kike kukarin hada kaya grany tazuge Jakarta tana fadin gidan hajiya Hadiza zanje badan ma zaka fita ba Aida tare zamu tafi ka gaisheta AK yayi murmushi yace a'a kije kawai grany Idan nasamu lokaci zamuje nida ahmad mugaisheta yanagama fadin haka yamike ya dauki wayoyinsa yayi gaba har yakai kofa grany takirashi dawowa yayi yazauna yana fadin gani grany ya akayi grany ta gyara zama tace ABID dagowa yayi ya kalleta saboda idan har yaji takirashi da wannan sunan yasan Abu mai mahinmanci zata gayamai
Grany tadago ta kalleshi tace agaskiya hakurina ya kusa karewa nagaji da ganinka haka ba aure kuma naga Alana bakada niyyar yinsa saboda nace kabani dama inzaba Maka mata kaki kace aysha kake so toh ita dinma nace ka aureta amma katsaya kana bata lokaci ko so kake se na mutu zakayi auren ne?? Dagowa yayi ya kalleta yana murmushi hawayen da yagani a idon grany yasa yamike da sauri ya Matso kusa da ita ya kama hannunta shima kamar zai yi kuka yace haba grany meye abun kuka kuma kina so kidaga mun hankali ne kinsan ba abunda natsana kamar ganin keda sarah adamuwa kuma kinsman kinada hawan jini so kike yatashi dan allah grany kiyi shuru wallahi idan wani Abu yasameki mutuwa zanyi grany tayi murmushi tashare hawayenta tace ABIDI bazaka gane yanda nakeji bane idan na tuna cewa har yanzu bakada aure nakosa naga kaima ka ijiye iyali ABIDI wa'yannan mutanan da kagani agidannan kake wahala akansu yau dazaran akace anwayi gari Baka raye suna gama cinye dukiyar Daka tara watsewa zasuyi su manta dakai iyalinka ne kawai zasu rika maka addu'a akoda yaushe abunda nake ganemaka kenan amma kai ka kasa ganewa
Jikin AK yayi sanyi da bayanan grany ajiyar zuciya ya sauke yadago ya kalleta yace nafahimce ki grany kuma insha allahu namaki alkawarin aysha tana dawowa za'ayi maganar bikin mu amma dan allah kidaina damun kanki da yawa grany tace to shikenan allah ya kaimu
AK ya kureta da ido cikin sigar zolaya yace ha'an yanaga ba kya farin ciki ne ko kishin ne yamotsa grany tayi murmushi tace a'a nida wata yarinya nagani namaka sha'awarta ga hankali ga nutsuwa ga girmama manya gata kekkyawa kamar yar India ina son yariyar jikar hajiya Hadiza ce yarinyar yar gidan mutunci ce babanta malan mahammadu ana cemashi magaji har yarasu kowa yana yabonsa a unguwar kaga gata marainiya tun tana Karama babanta yarasu kuma.........AK ne yakatseta da fadin ya isa haka grany wannan campaign haka to kiyi hakuri ta makaro ni aysha nakeso grany ta kauda kai tana fadin ni banga abun so awajan aysha ba mace kamar allo AK ya mike yana murmushi yafita yana fadin badai auren kikace kinaso ba to zanyi grany ta dauki Jakarta tabi bayansa tana fadin da dai ka daure kaga yarinyar nasan zaka sota
AK bai kulata yanufi wajan motocinsa grany ma wata motar tashiga tama driver kwatancan da inna tamata
Agidan inna grany ta wuni sunsha fira har sun gaji bacci ya kwashesu se bayan la'asar tadawo gida
Bayan kuana biyu ana jibi su sarah zasu dawo tama kasa hakura suyi sati dayan duk ta kosa tadawo taga ahmad dinta kullun seta kirashi awaya wani lokaci yadaga wani lokacin kuma har tagama ringing dinta yana gani baidaga ba ita kuma bata damu ba duk abunda tagani na maza mai kyew sai tasayama ahmad da AK har dariya takeba aysha wani lokacin kuma tabata haushi
Bangaran ahmad kuwa gaba daya yakasa sukuni shikadai sekaga yana murmushi tun Momy na shareshi har tafara tambayan shi amma se yace ba komai Momy tayi dariya tace zauna nan badai kunki aure ba ai dama gwowranci inyayi yawa yana taba kwakwalwa toh naga alama shine yafara zautar da kai saura abokin naka shi bamusan taya zai zomashi ba sedai yayi murmushi ya Sosa kai yace momy lokaci ne momy tace kanku akeji mudai namu ido nayi fadan har nagaji nayi fushin banza se kununa baku masan inayi ba
Ahmad kullun yana kan dakalin kofar gida yana jiran khadeeja ita kuma tun ranan ta sauya hanyar zuwa islamiyya setayi uban zagaye kullun cikin latti take ga Umma namata fadan kuana biyu bata dawowa da wuri
Umma ce zaune akarkashin bishiya ta hura wutan murhu tana hada turaran wuta asma'u tafito ciikin shirinta nafita kusan Umma tazauna tace wai umma har yanzu khdy bata dawo ba?? Umma zatayi magana kenan suka ji anturo kofa khadeeja ce tashigo tana rangaji tana zuwa tazauna ragwazab akan tabarma tana nufashi asma'u tamika mata ruwa tana fadin sannu Umma tace wai khadeeja ina kike tsayawa kwana biyu bakya dawowa da wuri ne ? Khadeeja takauda zancan dafadin haba tunda nashigo Layin nan nakejin kanshin turaran wuta ashe Umma ke hadawa namu ne???
Umma tace na momyn Ahmad ne ta iko dashi dazu na hadamata khadeeja bata gama jiba tafada daki
asma'u tayi murmushi tamike tana fadin Umma ni natafi se nadawo Umma tace to adawo lafiya kinga dana gama hadawa da nabaki kinbiya mata dashi amma jiki kawai naba khadeeja takai mata aguje khadeeja tafito daga daki har Zane na kwancewa tasha gaban asm'u tana fadin ammah dan allah kidan jira minti biyu Umma tagama se kikai mata kinga yanzu nadawo nagaji asma'u tagane khadeeja tsoron haduwa da ahmad takeyi murmushi tayi tace khdy sauri nakeyi kije kikaimata kimanta da maganar fa'iz ba abunda zai maki kinga daganan ma inkingansa se kibasa hakuri hakuri tayi fuskar tausayi ta langwabar dakai asma'u tayi dariya taja kuncan khadeeja tace wai khdy ce nake ganin tsoro a idonta khadeeja ta zun bura baki tace niba tsoro nakeji ba Umma tace wai gulmar me kuke ne asma'u bazaki wuce ba kintsaya biye ma wannan Mara aikinyi ko asma'u tayi murmushi ta wuce tana fadin senadawo
Khadeeja ce tsaye akofar gidansu ahmad takai minti goma atsaye tana shawarar tashiga ko kar tashiga can dai tayi shahada ta kwankwasa kofar mai gadi yaleko yana nan ganin khadeeja yabude kofar dama yasanta tana zuwa gidan wani lokaci ahankali khadeeja tasa kai cikin gidan tagaida mai gadi kamar ta tambayeshi ahmad na nan sekuma tace kar yayi tunanin ko wurinshi take zuwa da sanda tafara tafiya tanayi tana waiwaye kamar mara gaskiya ahmad da fitowansa kenan daga bangaransa ya hangi kamar wulgawar mutun haka yaji yana son ganin kowaye
Da sallama khadeeja tashiga palon ajiyar zuciya tasauke ganin Momy ce kadai a dining tana cin abinci Momy tadago tana amsa sallamar murmushi tayi tace auta yau kece agidanmu kodai batan kai kikayi ne khadeeja takarasa wurin momy tana gaisheta sannan ta mika mata robar turaran wutar tana fadin gashi inji Umma Momy tayi murmushi tace nifa nasan ba banza ba naganki agidan nan ina asma'u khadeeja tace tanan nan lafiya kana ta juya tana fadin Momy natafi se anjima Momy ta riko hannunta tana fadin wai lafiya kike sauri kamar ana koranki khadeeja tayi murmushin yake aranta tana fadin Momy bazaki gane bane
Momy ta janyota ta zaunar da ita kan kujera tana fadin zauna bari nazuba maki abinci khadeeja ta zaro ido tace Momy allah akoshe nake Momy tafara zuba mata sakwara da miyar agusi tana fadin se kinci zaki tafi khadeeja badan taso ba ta zauna tafara cin abincin tana kalalo murmushin dole amma ayanda take dinnan dan karamin motsi zaisa taruga da gudu
ninfashinta ne yakusan daukewa ganin ahmad ya turo kofar tsaye yayi daga bakin kofa yana mitsitsike ido dan ganin dagaske itace kodai gizo take mai ne Momy ce tadago tagansa atsaye murmushi tayi tace karaso mana ahmad baka santa bako khadeeja ce diyar Umma danake baka labari muna mutunci da ita tana zuwa nan gidan bakudai taba haduwa bane se yau
Kadeeja ta zaro ido😳 ganin ahmad yanufosu Yana murmushin gefe
Momy ta tashi tana fadin bari nashiga da turaran ciki khadeeja taji kamar tabita amma ba hali
Ahmad yakaraso yaja kujerar kusa da khadeeja yazauna yana kallonta
Khadeeja ta sunkuyar da kai kasa gabanta na dukan uku uku
Ahmad yagane ta tsorata murmushi yayi yace shekaranjiyar nan naganki kinata vibration yanzu kuma naganki so silent lafiya ??khadeeja dai ba baki se ido abincinma takasa ci se juya cokalin take ahmad yayi kasa da murya yace tsorona kike ne ? nan ma dai shuru ba magana aranta take fadin khadeeja karki nuna kina tsoransa lokacin ne zai samu damar cimma nufinsa akanki ajiyar zuciya ta sauke cikin karfin hali ta tsakuri sakwara takai bakinta ahmad dai yakafeta da ido dagowa tayi tasaci kallonsa ai kwa carab suka hada ido atake suduka biyun suka ji gabansu yafadi
lomar da khadeeja ta hadiye ce ta tsaya mata awuya ba shiri tafara shakuwa da sauri ahmad ya zuba ruwa akofi yamika mata yana fadin yi ahankali my flying Bird khadeeja tazun buro baki aranta tana fadin badai niba ruwan takarba takai baki afili ta furta thank u TARZAN saurin dafe baki tayi tare da zaro ido ahmad ya tintsire da dariya yace ke dan nakiraki da flying Bird shene kirasa sunan dazaki kirani dashi se Tarzan?? wayarshi dake aljihu yaji tana vibration hannu yakai aljihu yana kallon khadeeja ya hade fuska yana fadin bakinki bai mutu ba Ashe
Khadeeja tazaro ido ganin yakai hannu aljihu ita duk atunaninta asid zai dawko daga aljihun bashiri tayi wata irin supa tacapke hannun ahmad ahmad cikin muryar kuka take fadin dan allah da annabi kayi hakuri wallahi wallahi subutar baki nayi Dan allah karka watsa mun bazan sake ba i promise Umma da ammah duk zasu zo subaka hakuri wayyo na shiga uku momyyyyy!!!!
Ahmad dai yayi tsaye yana kallon ikon allah banda dariya ba abunda yake sam ta hana yafito dawayar
Da kyar yasamu ya kwace hannunsa ya riketa yana fadin ke wai mezan watsa maki wayata fah zan Ciro daga aljihu
Khadeeja tayi shuru ta sadda kai banda kadawa ba abunda cikinta keyi
Hannu ahmad yasa yadago fuskarta idon khadeeja alumshe kawai jira take taji asid afuska
Shikuma ahmad ido yakuramata yakasa dauke idonsa daga kanta jiyake kamar yarugumeta amma bahali jin shuru yasa khadeeja tabude idonta ahankali tasauke su cikin nasa wani Abu sukaji yana ratsa tundaga Kansu har tafin kafa sunkai Minti 2 ahaka jin motsin fitowar Momy ne yadawo dasu daga duniyar dasuka fada khadeeja taja baya adabirce tafara soshe soshe Momy takaraso tana fadin ya kuma naganku atsaitsaye lafiya ahmad ya Sosa kai baice komai ba khadeeja tayi murmushin dole tace Momy zan wuce yanzu Umma takirani tace naje Momy tayi murmushi tace kodai ahmad ne ya koreki nasan halinsa baya son baki khadeeja tanufi hanyar fita tana fadin shine Momy ahmad yazaro ido yana kallon khadeeja data fita dasauri har tana tuntube Momy tayi dariya takalli ahmad tace mekamata ? Kallon momy yayi yace to ni kwa mezan mata? Momy tace tunda naji tafadi haka to tabbas kamata wani abun ahmad yanufi hanyar fita yana fadin momy bari infita senadawo
Momy tabishi da murmushi dan tasan wurin khadeeja zaije saboda dazu agabanta komai yafaru tunda khadeeja takira sunanta momyyyy tafito dan ganin ko lafiya
khadeeja tana tafiya tana waiwaye har tafita get waigowa takara yi taga ahmad abayanta yana fadin my flying Bird dan tsaya mana ai bai gama rufe baki ba taruga aguje tasha kuana
ahmad ya tsaya yana dariya har da rike ciki ....
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
🖊na marubuciya Husna kabir zarewa( the mammah girl)
🖊dasunan allah mai rahama mai jinkai....
👨👧DOMUN KANWATA👩👧
3⃣5⃣⏭4⃣0⃣
Cikin kuana biyu soyayya da shakuwa mai karfi tashiga tsakanin khadeeja da ahmad tun tana tsoron shi intaganshi tana guduwa har tagaji tasaki jiki suna soyayyarsu mai ban sha'awa wani lokaci kagansu kamar abokai ko yan uwa amma har yanzu taki bari yazo gidansu asma'u ce kawai tasan da soyayyar su
Abangaran AK kuwa yagama yanke shawara da zaran su aysha sun dawo za'ahada bikinshi da na Ahmad ayi gaba daya kowa ya huta
ayau ne ake saran dawowar sarah da aysha AK yarasa inda zai saka kansa da murna har wani kara gyara akayi na musamman domun su
yau ko office baijeba yana gida wurin grany ana girke girke
ahmad ne yashigo bangaran grany da sallama dawke abakin sa grany ya isko apalo tana zaune AK kuma ya zage yanata shirya abinci a dining dariya ahmad yayi yana nuna AK da hannu yace
wanake gani haka kaman AK grany??
yau kuma sarautar kice ta motsa kika hana AK zuwa office kika tura bawan allah kitchen??
Grany ta tabe baki tace babu sa hannuna awannan rashin aikin yi waifa yaran nan yazage yana ma hidima ga masu aiki yabarsu suyi wai shi yafiso yayi dakanshi se kace wani kuku
Ahmad yazauna yana fadin wa'yanne yara kuma grany ? Grany Tamaka mai harara tace kai karka rainamun hankali mana ayshan ce baka sani ba ko kwa ita budurwan taka sarah nasan zakayi mamakin ya akayi nasani ko
To dazu AK yake gayamun kuma yace wai tare zaku hada bikinku shine nace Abu yayi kyew ai gara kuyi auran kowa ma yahuta
Ahmad dai tunda grany tafara magana idonshi ne kawai akanta amma hankalinsa na wani wurin tunani yake na gaskiya fa akwai babban aiki agabansa yanzu ya zaiyi da Sarah taya zaima AK bayani yasan ayanda AK ke bala'in son Sarah ba lallene ya fahimce shiba
shi kuma ko Ana ha maza ha mata bazai rabu da fliyng Bird dinshi ba
maganar grany ne tadawo dashi hayyacin sa kallon ta yayi yace na'am grany
Grany tatafa hannu tana salati tace badai kana nufin duk surutun nan nikadai nayi shi ba ahmadi
Ahmad yamike yana murmushi yace najiki mana grany kidai tanadi maganin hawan jini Dan naga abun zai maki yawa kishiyoyi biyu lokaci guda
Grany ta tabe baki tace Allah na tuba dawa zanyi kishin
Mata kamar asuwaki ni wallahi kunma bani kunya duk gayun nan naku da haduwar Ku amma kukare akan wa'incan sandunan Ku gaku da kumari amma matan kamar masu ciwon kanjamau
AK ne yafito daga kitchen rike da jug din Ginger jus yanufi dining yana fadin ya isa haka grany tunda kikaji zancan auran nan kika tasa yaran nan agaba se figesu kike inace dai mu muka gani munaso kuma mu zamu zauna dasu ke naki ido ne se kuma addu'ar zaman lafiya dazaki rika yimana
Grany tamike tanufi daki tana fadin a'ah ABIDI yi hakuri abun baikai haka ba nayi shuru daga fadan gaskiya ai su Kansu matan sunsan kunfi karfinsu Dan Sam Baku dace ba Mata sekace ........
AK yabuga kafa da kasa kamar zaiyi kuka yace Gany please!!!
grany tasa hannu ta toshe baki tare da wucewa ciki Ahmad dai banda dariya ba abunda yake
AK yaja tsaki yace Kai har kaga abun dariya anan Allah intana fadan haka se duk inji badadi dama can bason auren nan nake ba ni bansan meyasa ba duk zumudin da akefadin angwaye nayi ni Sam bana jinshi
Ahmad yamatso kusan AK cikin sanyin murya yace AK inaso zamuyi wata magana Mai mahimmanci dakai kuma.....
AK yakatse shi tare da fadin no Ahmad bamada lokacin magana yanzu jirgin su ya kusa sauka kabari daga baya zamuyi maganar wata kula yanuna mashi yana fadin bani kular can naga miye aciki? Ahmad yadawko kulan yana fadin bakai zuba abincin bane AK yasosa Kai yace nine amma namanta mena saka aciki
Ahmad yabude kular tare da tintsirewa da dariya🤣 yace Kai waya gayamaka anasa salad a kula AK ya hade fuska yakwace kular yana😠 fadin to a ina ake sakawa
Ahmad ya kalli salad din yakara sa dariya yace wai yanaga yazama hakane kodai dafashi kayi ne
AK yafara cire kwan dake ciki yana fadin bandafashi ba inaga zafin kwan ne yasashi yazama haka can kuma yadago ya kalli Ahmad yace Kai Kama raina mun hankali to ai ko Dan kawye yasan ba'adafa salad Ahmad ya tsiyayi jus akofi yasha sannan yace kaidai Ina rabaka da aikin daba nakaba abun ai ba daga waye bane kofin ya ijiye sannan ya kwalama Mai aiki Kira tanazuwa yace am... Rebeka kidan kwashe kayan nan ki gyara zamuje mudawo yanzu ta amsa DA yes sir
Shidai AK yana tsaye baice komai ba Ahmad yaja hannunsa yana fadin muje mushirya se muje mudawko su AK yabi bayansa kamar wani karamin yaro wayar shima yaketa dannawa har saida sukaje bangaran shi sannan Ahmad yasakemai hannu ya wuce toilet koda yafito AK yaciro musu kayan dazasu sa kananun kaya ne masu tsada Ahmad nafitowa AK yashiga kayan sukasa sunyi masifan kyaw kaman yan biyu haka suka sawko kasa uncle jamilu ne kawai akasa yana karanta jarida bayan sungaidashi kasakasa ya amsa gaisuwar Ahmad
Suna wucewa Ahmad ya matso kusan AK cikin rada yake fadin wai shi wannan tsohon kuana biyu bana ganinsa a company konaje office dinsa arufe yana bala'in wasa da aiki amma wata nakarewa shi kake fara ba albashi ashekarunsa yanzu yaci ace ya daina aiki amma wai.......
AK ya katseshi dafadin Ahmad shut up!!
Ahmad yayi shuru tare da juyowa yakalli uncle jamilu carab suka hada ido dama suna wucewa ya sauke glass dinsa yabi Ahmad da kallo
Murmushin yake Ahmad yamishi tare da daga Mai hannu shidai uncle jamilu se binsa yake da kallo har suka fita kana yamaida idonsa kan jaridar dake hannunsa
Suna isa jirgin su Sarah nasauka dagudu suka zo suka rungume AK rumgume su yayi yana dariya Sarah ta juyo da nufin rugume Ahmad yayin saurin jan trolley dinta yana fadin kuzo muje nasan kun gaji Sarah bata damu ba suka bi bayansa suna tafe suna fira banda Ahmad da se ba'a rasa ba yakesa baki
Suna isa bangaran grany suka nufah bayan sun gaisa grany tawuce daki Dan ba inuwa daya suke shigaba
Wurin dining suka nufa suka AK yaja ma aysha kujera tazauna tare da fadin thank u Sarah tayi tsaye tana jira Ahmad yaja mata kujera taga yazauna baida niyyan kallon inda take baki ta zuburo taja kujera tazauna suka fara cin abinci
AK ne yadago yakalli aysha sukayi ido biyu murmushi yayi yakashe mata ido tare dafadin miss you baby
Murmushi tayi itama tace miss you too duk abunda suke Sarah DA Ahmad na kallonsu Ahmad naganin Sarah tajuyo zata kalleshi yayi saurin sadda Kai
baki ta zunburo cikin muryar shagwaba tace wai ni kan yaya kayi missing dina kuwa AK yayi saurin juyowa yace nayi missing dinki mana kallonshi tayi ta nuna Ahmad tace bakai ba shi AK yayi murmushi ya kauda kai yana fadin ok to kirinka banbanta sunan tunda shi sauranyiki ne kisa masa wani sunan
Ahmad yamike tare da fadin nizan wuce Allah huta gajiya ganin Sarah tamike da nufin binsa yayi saurin am...AK muje kadan rakani mana AK yadago da loman abinci abakinsa yace ban gane in raka kaba kai bako ne Ahmad ya langwaba Kai yace kazo mana akwai maganar dazamuyi AK yatashi yana fadin Kai wallahi ka iya katsema mutun jin dadinshi
suna fita aysha ta kalli Sarah da mamaki afuskanta tace wai ya naga kaman Ahmad yana avoiding dinki ne Sarah ta zauna jiki asanyaye tace Ashe kema kin Lura ko?
aysha ta tabe baki taci gaba da cin abincinta
Seda Ahmad yashiga mota yadago yakalli AK yace AK gobe muhadu a office Ina so mu tattauna wata magana AK yaleko ta window yace haba Ahmad be a man mana nasan akan zancan auren nan ne duk kadaga hankalinka don't worry ni zanyi komai kuma ba dogwon lokaci za adauka ba yana kainan yajuya yana fadin se munyi waya
Ahmad yadaki stiyarin motar da karfi ya dafe Kai shi yanzu ya zaiyi afili ya furta Kai Ina!!! dasake wayanshi yadauka ya lalubo numban khadeeja bugu biyu ta daga tare da fadin Tarzan ya akayi Ahmad ya jingina jikin kujera ya lumshe ido yana fadin flying Bird kina Ina ne khadeeja takalli Asma'u da takafeta da ido tace Ina gida lafiya ?? Ahmad yatada motar tare da fadin gani nan zuwa khadeeja ta tashi azabure tana fadin gaka nan zuwa Ina? mema zakazo yi ?
Ahmad bai jira tagama magana ba yakatse wayar khadeeja ta juyo ta kalli Asma'u tana murmushin yake Asma'u takauda Kai taci gaba da aikinta khadeeja tazo kusanta ta zugunna tace ammah yazanyi tunda naji yace zaizo to Abu Mai mahinmanci zai kawoshi gashi Umma bata nan bata Masan da alakar muba
Asma'u tamike tana fadin idan yazo kije in Umma tadawo Zan Mata bayani amma kiyi ahankali ni soyayyar nan taku tsoro take bani duka duka KO sati bakuyi ba da haduwa amma kamar kun shekara tare kuma tun rashin kunyar da kika mishi yafara binki ni hankalina ya ki kunciya Anya bayada wata boyayyar manufa akanki kuwa khadeeja kinsan masu kudin nan basuda tabbas juyowa tayi tadawo wurin khadeeja tare da rike hannayanta duka biyu cikin sanyin murya tace khdy dan Allah ki kula da kanki ki tsare mutuncin ki kar kudi yarude ki kiyada tarbiyar da Umma Tasha wahala tabamu ba wai ban yarda dake bane a'a nasan kinada hankali kinsan Abu Mai kyew DA mara kyew amma shi Dan Adam Tara yake bai cika goma ba hawaye ne suka zubo a idonta tace khadeeja idan wani Abu yasameki mutuwa zanyi zuciyata bazata iya dauka ba
Da sauri khadeeja
tafada jikin Asma'u tafashe da kuka mai sauti Asma'u ta rungumeta tana shafa kanta cikin sheshshekar kuka khadeeja kefadin shi kenan ammah Allah nabari bazan Kara kulashi ba koda sonshi zaikasheni idan kikace bai maki ba Allah bazan aure shiba Asma'u ta dagota tana goge Mata hawaye tayi murmushi tace khdy bance bana son Ahmad ba duk abunda kike so nima Ina sonshi kawaidai Ina jin tsoro ne amma Zan sameshi muyi magana nakara bashi hakuri akan abunda kika masa kinga daganan se hankalina ya kuanta karar wayan khadeeja ce takatsesu
jiki asanyaye khadeeja tadaga Ahmad yacemata gashi akofan gida Asma'u tayi murmushi tace tashi kije amma karki dade kinga Umma batanan tashi tayi ta fita bata ce komai ba
akofar gida ta iskoshi karkashin bishiya ya jingina da mota yanda taganshi cikin damuwa yasa taboye tata damuwar takaraso tana kakalo murmushi tamai sallama shima murmushin yayi ya amsa bayan sun gaisa yabude motar yanuna Mata kujera ido tazaro tace menene ? Murmushi yayi yace kin cika tsoro zama zakiyi Ina so muyi wata magana khadeeja tayi murmushi tazauna tana fadin thanks
Ahmad yasauke ajiyar zuciya yakalleta yace khadeeja kinsan nataba gayamaki cewa AK hausawee abokina ne ko ? Khadeeja tadaga Kai alamar eh Ahmad ya zugunna ya jingina jikin bishiyar da suke karkashi sannan yabama khadeeja labarin duk abunda yafaru tsakaninsa da Sarah da shirin aurensu da AK keyi ayanzu
khadeeja tayi Shuru na Dan lokaci tace gaskiya tun daga farko kayi kuskure duk dacewa awancan lokacin bakada wacce kakeso bai kamata kamata kamata karyan kana sonta ba amma nidai da nice a matsayinta daga reactions dinka ya'isa nagane baka sona sedai shi so makaho ne tunda tana sonka bazata kula da wannan ba
Kuma ni banga abunda zaisa kadamu kanka akan wannan ba after all he is just a friend not a father kome takai takawo dai bazai aura maka kanwansa dole ba
Ahmad ya girgiza Kai yace khadeeja bazaki gane bane AK ba babana bane amma wani bangarene na rayuwata tare muka taso dashi tun muna primary muka shaku da juna takai har idan dayanmu yake makaranta zai tsaya abakin get har said Dan uwansa yaje sushiga tare dayawa mutane sun dauka gidan mu daya duk ranar da banada lafiya banje makaranta ba AK gidan mu yake dawowa har sai nawarke mutafi tare duk abunda aka sayamasa se ansayamun in ba haka ba kwa to bazai yi anfani da nashi ba
Muna scdry school dadyna yarasu alokacin shima abbanshi yajima da rasuwa AK shi yadawki nauyin karatu na har muka gama lokacinda zai je America karatunshi tare muka tafi lokacinda yabude companynsa ni yafara dauka aiki kuma yabani babban matsayi na mataimakinshi khadeeja AK yazama tamkar babban yaya awurina bansan da wane ido zai kalleni ba idan har nace bana son kanwarsa
cikin sanyin murya khadeeja tace to ka aureta mana
Ahmad yadago dasauri yace aure kuma khadeeja ?taya Zan aureta bayan bana Sonta ni ke nakeso khadeeja kuma ke zan aura baya cikin tsarina zama damace biyu kuma ko na aureta banajin Zan iya adalci atsakaninku so waht is the use of marrying her tunda daga ni har ita bazamu ji dadin auren ba
Khadeeja taji wani sanyi aranta dama can karfin hali kawai tayi na cewa ya aureta murmushi tayi tace to tunda hakane ba AK yakamata kagayama cewa baka son sarah ba ita yakamata kagayama kuma kabata hakuri akan wasa da emotions dinta da kayi nacewa kana Sonta alhali bahaka bane
ajiyar zuciya ya sauke tare da fadin hakane khadeeja naji dadi kuma nagode da shawarar da kika bani
khadeeja tayi murmushi tace bakomai nima nagode daka zabeni amatsayin wacce zaka fadama damuwarka kuma kanemi shawarata hakan yanuna mun cewa inada matsayi arayuwarka
Ahmad yamike yana fadin flying Bird Bari na wuce yamma tayi tunda ko ruwan gidanku baki bani ba dariya tayi tace laaaaa Allah namanta duk arude nake kasan bantaba tsayawa da saurayi ba murmushi yayi yace dagaske? kice nidin na daban ne kenan dariya tayi tare da rufe fuskanta da gyale tace u are my first love dariya yayi yace nagode da wannan matsayin and u are Mine too
baki ta zunburo tace kaifa second hand ne Ahmad yace kamar ya second hand sekace waya
murmushi tayi tace baka riga cema Sarah kana sonta kafin ni ba dariya yayi yashiga mota yana fadin wannan ai iya lebe ya tsaya ke kuma ko yanzu za'a tsaga zuciyata za'aganki aciki tada motar yayi yana fadin Zan tafi badan nagaji da ganinki ba murmushi tayi tana daga mai hannu har yatafi se kuma yayo rebas yadawo khadeeja tace lafiya kankance ido yayi yana kallonta yace wai ma yanaga baki Nuna kishinki akan maganar nan bane harma kike cewa in aureta khade Anya kwa kina sona murmushi tayi tace kazo mun da maganar ne dan kaga kishina Kodan nabaka shawara
Ahmad yasosa Kai yace Dan kibani shawara amma kinsan mu maza muna so muga Ana kishinmu ke intakai ma har dambe ayi dariya tayi tace to bada khadeeja za'ayi damben ba
yanda kazomun da damuwarka bai kamata na Nuna tawa damuwar ba se abun yama yawa shi yasa kaga na waske amma azuciyata yanda kasan Ana buga ball haka nakeji
Dariya Ahmad yake sosai har yatada motar yayi gaba yana fadin I can't leave without you my flying Bird !!! Khadeeja tayi murmushi ta koma cikin gida.....
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧 _DOMUN KANWATA_ 👩👧
Na ( Maryam Muhammad jibril)
Dasunan Allah mai rahama mai jinkai....✍
5⃣0⃣
Yana shiga bangaran Ahmad yatura kofar yashiga
Ahmad dake zaune da laptop agabansa at the same time yana waya da khadeeja ganin AK yasa yayi saurin katse kiran yana fadin call u back flying Bird
Sannan yadago yakalli AK yana fadin ina kabar wayanka ina kiranka baka dagawa
karasowa AK yayi yanufi Dan karamin frig din dake palon yana fadin waye kuma flying Bird?
Dasauri Ahmad yadago yakallesa Dan baitaba tunanin yaji abunda yace ba
murmushin yake yayi yace 😁tsuntsuwata ce
Goran ruwa yadauka afrig din ya zauna adaya daga kujerun Palon sannan yadago yakalli Ahmad yace se yanzu nayarda da zancan momy idan gwabranci yama mutum yawa yana zarewa gashi kafara tabuwa dariya yasa yana fadin inaga Inaga 1 week din danadauka yayi yawa yakamata narage idan ba hakaba naga alamun firstnight dinka a mental hospital zaka yishi yakarashe maganar yana kwashewa da dariya
Hade fuska Ahmad yayi baice komai ba yaturama AK laptop din yace duba kaga collection din wannan karon tun dazu ina kiranka bana samu
munyi
magana da zaid yace mun maybe zuwa yamma zasu iso Lagos
Karban laptop din AK yayi yaduba sannan yace sunyi kyew amma yau kaje office ne
Gyada kai Ahmad yayi yace eh naje banjima da dawowa ba
su mannir ma sun gama bedsheets din sun bala'in kyew se kagani
Murmushi AK yayi yace ai nasan mannir baya wasa da aikinsa amma yakaga aikin bashir yana tafiya daidai kuwa
Tsaki ahmad yayi yace Dan Allah daina zancan wannan banda wasa da tarin yan mata ba abunda ya ajiye
Tashi AK yayi yana fadin muje wurin Momy tace tana son ganin mu
hannunsa Ahmad yariko yana fadin come on friend ina kuma zakaje bayan baka gayamun abunda kazo fadamun ba
Mezan fadamaka kuma...AK yafada yana kokarin boye damuwar fuskarsa
Mikewa Ahmad yayi yashiga gabansa yana fadin haba AK nafasanka fiye da yadda nasan kaina u can hide ur sadness from everyone with ur fake smile but u can't hide it from me coz I know u in and out
So please don't waste my time
Tell me what is bothering u and let me do my job
Zama AK yayi yana sauke ajiyar zuciya
Kusa dashi Ahmad yazauna yana kafeshi da ido
Wani dogon tsaki Ahmad yaja da yagama jin labarin da AK yabashi mikewa yayi yana fadin wallahi kabani mamaki AK yanzu akan aysha ne ka daga hankalinka so what idan tayi rejecting dinka who the hell is she mata nawa ne agari suke Neman koda pics ne sudauka dakai Wanda ma sunfita komai
Dawowa yayi kusa da AK yazauna tare da dafa kafadansa yace AK please be ur self nasan dalilin dayasa kake son auren Aisha sedan kana ganin itace zata zauna da family dinka lafiya saboda ita ma nata ne kuma itace kasan halinta tasan naka
Amma shi rayuwar aure ba ruwansa da wannan kamar yanda kukai da grany kabarta tazaba maka kasan bazata zaba maka abunda zai cutar dakaiba I know one day u will thank her for that
Harara AK yawatsamai ba shiri yaja bakinsa yayi shuru yana danne dariyarsa
Mikewa AK yayi baice komai ba yawuce yana kada key din motar dake hannunsa
Bin bayansa Ahmad yayi yana fadin bamu gama maganar ba kuma katafi
Bangaran momy suka nufa
Tana zaune apalo suka iskota kusan kafanta AK yazauna yana fadin da girman kujeranki momy Allah sadai ba laifi mukayi ba
Kauda kai tayi tana fadin laifi kuma ai saidai kar akara
Dayan gefenta Ahmad yazauna yana sha sajen fuskarsa yana murmushi
Daure fuska tayi tace Ku yanzu saboda Allah kunfiso kuyita gantali agari da girmanku bazaku ma kanku karatun tanatsu ba wai ni idan kunsan bakuda lafiya ne kugayamun insan nayi amma nagaji daganinku haka
Dagowa sukayi suka kalli juna sukayi murmushi
Kara tamke fuska Momy tayi tace aw dariya ma kuke wato gani mahaukaciya ko
AK yace Yi hakuri Momy insha Allah mun kusa nadauka ma Ahmad yagayamaki zancan auren na dasati daya insha allah
Tafa hannu tayi tace yaw naji zancan banza shi auren angayamuku wasa ne kai karfa kurainamun hankali
Ak yace
Momy Allah dagaske to me muke jira tunda ko mata hudu mukace muna so zamu iya aurosu ayau base gobe ba
Baki Momy tawashe tana fadin kuma fa hakane amma ai duk dahaka yakamata ace mun fara shiri
Murmushi AK yayi yace abunda yakawoni kenan Momy se kije wajan grany zakiji bayanin komai daga gareta
Yana kai nan yamike yana fadin mom bari naje sena sake dawowa
Ahmad da tunda aka fara magana ya sadda kai sai yanzu
Yamike jiki asanyaye yabi bayan AK har yakai kofa momy tace Ahmad idan kadawo kazo inasan ganinka
To yafada yana fita daga palon
Amota ya isko AK zaune yana jiransa Shiga yayi suka bar gidan
Ahankali AK ke driving sunyi shuru ba mai cewa kala
kowa ya tsunduma cikin tunani shi ahmad yana tunanin taya zai gayama AK cewa bazai iya auren kanwarsa ba
Yayinda shi kuma AK yake tunanin wace yarinya ce grany ta zabamasa wace irin rayuwa zai yi da ita anya kwa baiyi gangancin yanke hukunci cikin fushi ba kuwa
Suna isa company office din AK suka wuce gaba daya
Mamaki ne yakamasu ganin aysha da sarah a office din
Daure fuska AK yayi Yana fadin me kuka zoyi nan
Langwabar da kai sarah tayi tace Yaya please give us a chance to explain
Kujeransa yanufa Ya zauna yana fadin banada lokacinda zan bata wajan sauraron tatsuniya
Cikin muryar kuka aysha tace AK wai meyasa kake mun hakane you've change completely I said I'm sorry kuka ne yahanata karasa maganarta
Ahmad da tunda suka shigo ya wuce Drowan dake gefe yana duba wasu files
Dogon tsaki yaja tare dazaran wani file yayi waje yana fadin aikin banza bin bayasa sarah tayi tana fadin bari nabaku space
Suna fita aysha tafada Jikinsa tafashe da kuka mai ban tawsayi tana fadin AK Dan Allah kayi hakuri komai yawuce Allah nafasa aikin banaso ni kai nakeso bandawka abun zaikai haka ba ko yaune nashirya zan aureka kuka ne yaci karfinta
Jiyayi yakasa jure kukanta hannunsa yadawra akanta yana fadin it's ok hanunta Yakama yazaunar da ita kan kujera sannan yazaro farin handkerchief a alijunsa ya mika mata Karba tayi tashare hawayenta cikin rawar murya take fadin ka... Ka hakura...? Kai ya gyada alamar eh
Murmushi tayi tace yanzu zamuyi aure ko ?
No way yafada yana zama akn kujerarsa
Dip murmushin fuskarta yadauke cike da mamaki tace bangane ba
Hannanyansa ya ware yana fadin nariga nasamu wacce zan aura kuma awannan satin
Afirgice tamike daga kan kujera Tanufesa tana fadin u most be joking right?
Kai ya girgiza yace kodaya and don't blame anyone u r responsible for it
Kara fashewa tayi da kuka tace ai nabaka hakuri AK why did u do that to me kawai saboda kaga INA sonka kamanta ni shekara nawa nayi ina jiranka shine.... Kukan dayaci karfinta shi yahata karasa maganarta
Tawsayinta ne Yakama AK Dan shi kanshi shaidane akan irin sonda aysha kemasa
Tasowa yayi yazo kusa da ita ya tsaya kauda kai tayi tana share hawayan fuskarta
Kafadunta Yakama yazaunar da ita yana fadin zauna muyi magana
zama tayi tana sauke nunfashi idonta har ya kunbura saboda kukan da tawuni tanayi
Hannunta yakama cikin muryan lallashi yace aysha I'm sorry nasan ban kyewta ba danayanke hukunci cikin fushi amma zanje insamu grany nabata hakuri ajanye maganar dama itace tazaba mun yarinyar ke kuma se ki kiyaye
Nan gaba u need to think twice before u speak
Murmushi tayi tarungume shi tana fadin thank u sweetheart Dan Allah kar kace zaka barni bazan iya rayuwa batare dakai ba
Kanta yashafa yana fadin I know tashi tayi tace to tunda komai yawuce let's have some fun Ak yace no I am busy
Langwabar dakai tayi cikin muryan shagwaba tace kenan baka hakura ba mikewa yayi yadauki jacket dinsa yana fadin let's go
Cike da farin ciki tabi bayansa
Office din ahmad yaleka azaune yake haushi duk yacikashi ga sarah Tasashi agaba se zancan bikinsu take mishi jiyake kamar ya bibbige mata baki
Jin anturo kofa yasa duka suka juya
Murmushi AK yayi yana fadin to Mr Romeo se kazo mutafi
ai zunbur ahmad yamike yana fadin thank god dama zafi ya isheni
Shi duk atunaninsa yadauka shida AK zasu fita ganin sarah tashiga mota yasa ya hade fuska bai gama shan mamaki ba seda yaga aysha ma tabude tashiga AK yatashi motar yana fadin babe se ina?
Wani irin kallon
kabada maza ya watsama AK tare dajan tsaki
Aysha tace wonder life
Sarah takatseta dafadin no shopping Yaya yakamata mufara shiri fa basauaran lokaci
Ko haka ba D ... Tafada tana kallon ahmad
Banza yayi da ita kamar baijita ba
Bata damu ba taci gaba da surutunta da AK
Dan itama aysha takaici ya isheta itada taso sufita daga ita sai AK
Sheraton suka nufa suna isa aysha taja AK sukayi wani gurin
ahmad ma kan wani guri yasamu yazauna yaciro wayarsa aljihu ya lalubo wayar khadeeja bugu biyu tadawka tareda sallama lumshe jingina yayi jikin kujera hade da lumshe ido yana amsa sallamarta
Shuru sukayi nadan lokaci tadayan bangaran khadeeja tace malam idan bakada abun fada hang up inada abunyi
Murmushi yayi yace yaw yan tsiyarne akai kenan Dan ma kinsamu na kiraki
Dariya tayi tace to ba dole ka kiraba kana so kaji zazzakar muryar khadeeja ba
Dariya yayi yace yabon kai bacinsa
Baki tazunburo kamar yana kallonta cikin muryan shagwaba tace to ai kai dayakamata kafada baka fada ba shiyasa natuna maka wai ni kwa Tarzan anya ma kuwa ka iya soyayya
Kwashewa yayi da dariya yace taya za'ayi insani bayan bantaba yiba amma aduk lokacinda nake tare dake se inji tamkar awata duniyar nake rayuwa banjima da haduwa dakeba amma se nakejin kamar tunda aka haifemu tare muka taso lokaci guda kika shigo rayuwata amma ayanzu rayuwata batada wani anfani idan har bake
Khadeeja tace hmmm ragamun hakanan Tarzan zaka kasheni da lubayya
Cikin muryan tsokana yace kufa mata ba'a iya muku kince ban iya soyayya ba yanzu kuma nazage na kwararomaki kalamai maimakon kiyaba sekuma kice ya isa hakanan dariya ta sa tana fadin to yi hakuri kalaman naka ne naji yayi iri daya dana mawakin Indian nan acikin wakar ishq vala
Kai yasosa yana fadin ai ina bala'in son wakan ne shiyasa na haddace amma karkidamu indai soyayya ce to ko sharukhan albarka
Dariya tayi tace to Allah sa idan baka cikin masu tashin matansu abacci da kafa ko adana musu dundu
Dariya yayi yace haba wuce nan yarinya se kin shigo zakiga nawa salon
Katse maganar tayi dafadin wai ya kunyi magana da sarah kuwa
Nan take fuskarshi tacanza cikin sanyin murya yace a'a tukkuna dai ni bansan ta inda zan fara bane
tadayan bangaran khadeeja tace haba Tarzan kar kabada maza mana kaifa namiji ne bai kamata wannan Dan karamin abun yadameka ba
Katseta yayi dafadin wannan ba karamun abu bane flying Bird bakaramun karfin hali zanyiba wajan gayama AK bana son kanwarsa
Ahasale khadeeja tace to kai ka aureta mana
Shuru yayi baice komai ba
Cikin sanyin murya tace sorry tarzan inajin haushin kaina ne dakashiga matsala kuma nakasa taimaka maka amma koda ta text ne base kagaya mata ba
Murmushi yayi yace nice idea I will try it shiyasa nake sonki akwaiki da brain....jin karan fashewar Abu abayansa da yayi shi yakatsemai maganarsa katse kiran yayi tare da juyowa
Sarah yagani atsaye fuskanta sharkaf da hawaye idonta yakade yayi ja ga kwalbar jus nan datafashe akasa jikinta har rawa yake bata damu ba tabi takan kualbar ta wuce harsaida tayanketa akafa amma bata ma san ta taka wani Abu ba saboda tsaban tashin hankalin datake ciki
Kusan Ahmad taje tatsaya kallonsa take da rinannun idanuwanta ko kiftawa batayi
Cikin sanyin murya ahmad yace sarah I'm sorry I know I hurt u by playing with ur emotions kibani dama namaki bayani
Bai yi auneba yaji saukar mari akuncinsa tuni hankalin mutanan wajan yakarkato wajansu
dafe kuncinsa yayi cike da mamaki yace kika mareni
Cikin rawar murya tace kozaka ramane kabani mamaki ahmad Ashe dama haka kake bansaniba kai wane irin butule ne
Rintse ido ahmad yayi hade da dunkule hannu zuciyarsa na tafarfasa wai yau shi aka mara in public kuma wai mace yatabba yau daba sarah bace tamareshi da Allah kadai zai kwaci koma waye ganin mutane na kallonsu yasa ya raba tagefenta yawuce batare da ya kalleta ba
Durkushewa tayi awajan tare dasakin wani irin kuka wanda dagaci kasan nabakin ciki ne seda tayi mai isarta sannan ta tashi tana jan kafa da gyalenta ahannu ita tafice basu bi takan su AK kowa ya wuce gida ataxi
Seda su AK suka fito basu gansu ba kuma yana kiran wayoyinsu basa dagawa
Janshi aysha tayi tana fadin muje mana AK tunda kaga basanan kenan suntafi
Aranan sarah wuni tayi adaki banda kuka ba abunda take aysha tayi tambayar duniyan nan amma taki gayamata se fadin take
impossible wallahi bazai yiwu ba he is mine and he only belong to me no one can never separate us .....
muryanta harta disashe saboda kuka har banci yadauketa
Washegari tunda safe grany tashirya tasami inna da maganar tana so suhada auren zumunci tsakanin Abid da Asma'u
Bakaramun farin ciki inna tayi ba nantake ta'aika kiran Abba bayan yazo tazayyane masa komai yayi murna sosai kuma yabada goyon baya saboda yasan AK kuma ya yaba da halayansa na taimakon talakawa da matasa
Yabasu tabbacin cewa da yamma zaije yasamu Umma da maganar duk yanda sukayi zasu ji ""''"""
Ur's.........✍
👩💻Maryam Mhd
[18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: afirgice tadago tana kallonsa da mamaki tace ahmad nizaka mara
Wani malalcin murmushi yasaki yace idan har zaki iya sa hannu kimareni to banga dalilin dazaisa nakasa marinki ba
Nunata yayi da yatsa yace and let me worn u
This isn't ur bedroom so wannan yazama karo nakarshe dazaki shigomun office without my permission
Sannan waccan yarinyar da kika kira da karuwa to bari kiji tafiki matsayi da daraja awurina idan har kika kara bude kazamin bakinki kikayi wata maganr banza akanta to wallahi zan baki mamaki ahaka kike so na aureki
Hannunsa tarike tana kuka tace ahmad please try to understand my love for u dagaske nake sonka zan iya mutuwa akanka daga ganin wannan yarinyar irin mayaudaran yan matan nan ne she is just after ur money
Fisge hannunsa yayi yana fadin get out of my office
Kara matsowa kusa dashi tayi tana fadin ahmad listen
I said out !!! Yafada yana daka mata tsawa
Dagudu tafita daga office nin tana rera kuka mai ban tawsayi
Komawa yayi yazauna kan kujera hade da lushe ido
Asma'u ce zaune agaban abba ta sunkuy dakai kasa tana wasa da yan yatsunta
Ga inna da Ummi agefe sunkafeta da ido
Kanta abba yadafa yace asma'u kinyi shiru kenake sawrare idan kinada Wanda kikeso kifadamun banaso namaki abunda zai takura rayuwarki
Carab inna takarbe dafadin yo ina taga Wanda takeso yarinyar dako samari batada
Kunyace kawai irin ta asma'u
Kafadanta abba yadafa yana fadin a'a nasan halin asma'u akwaita da zurfin ciki kibari kawai muji tabakinta
Itadai asma'u tunda abba yacemata jikan grany tayi shiru tana tunanin to wanne kenan amma dai tasan ba abidi bane tunda taji grany tace yanada wacce zai aura
Ummi ce takatsemata tunaninta dafadin kinga asma'u keba TV ba kinsa munfakeki da ido idan ba kyaso kifada mu gyara mukeso muyi wa rayuwarki ba takura ba
Hannu abba yadaga mata yana fadin a'a Ku sawrara mata mana ina anfanin gaggawa tashi kije har kiyi shawara kinji
Zunbur inna tamike tana fadin yo wace shawara kwa zatayi bayan kaji sunce da wuri sukeson ayi komai wai ke asma'u wace irin yarinya ce haka kike so kitsofe ba aure ne gashi allah yamaki gyadan dogo yabaki mijin son kowa shine se kiwani yi shawara
Kuka tasa tana fadin Allah jikanka magaji nasan dayana raye da tuni kina dakin mijinki
Tashi asma'u tayi takamo hannunta tana fadin a'a inna dan Allah kidaina kuka nayarda zan aureshi amma kidaina fadan haka
Rungumeta inna tayi cike da farin ciki tace haba asama'u ko ke fa insha Allah zakiji dadin zaman aure nasan abidi zai kula dake yanda yadace
Afirgice asma'u tace 😨ABIDI kuma??
meyasa sai shi
😧ba grany tace yanada wadda zai aura ba
Tabe baki inna tayi tace to ai shi aure nufine na Allah Allah yayi ba matarsa bace
Sunyi farin ciki sosai aranan bakamar abba dayake ganin burinsa yakusa cika na ganin ya aurar da ya'yan kaninsa ga mazaje nagari
Asma'u dai shiru tayi tana tunanin wayar dasukayi da abidi aranan idan har haka yake dazafin kai ya zatayi dashi
Kuka sarh take kaman ranta zai fita wannan karon ba idonta kadaiba hatta kanta da fuskarta sun kunbura ikon Allah ne kawai ya kaita gida batako gama yin parking ba tafito daga motar bangaran AK tanufa direct tana isa ta banka kofar tashiga hade da zubewa abakin kofa takara fashewa da kuka
AK dake kuance akan gado ya lumshe ido kamar mai bacci
Jin anturo kofa yasa yayi saurin dago kai ya kalla
Ganin sarah awannanhalin yasa afirgice ya diro daga kan gado har yana hardewa yanufota yana fadin subhanallahi sarah menene meyafaru daga ina kike
Rungumeshi tayi tacigaba da kukanta kamar karamar yarinya
Duk yarude yarasa yadda zai yi jiyake kamar shima yasa kukan
Kanta yafara shafawa cikin sigar lallashi saida ta zagaita kukanta sannan yace menene
Cikin dasashshiyar muryanta tace Yaya wai miye laifina miye bana dashi mmeye gareni Wanda ba'aso ajikin mutum
hawauenta yashiga share mata yana fadin ba kyada wani aibu kanwata kinada duk wani abunda za'aso mutun saboda shi
To meyasa ahmad baya sona !!!
Tafada tana rike hannun dayake share mata hawaye dashi
Da mamaki yace ban ganeba
Kai ta gyada tace eh cewa yayi baya sona kuma bazai aureni saboda yanada wacce yakeso
Murmushin gefe AK yayi yakama hannunta yazaunar da ita bakin gado seda ya tsiyaya mata ruwa yabata karba tayi tasha tana mamakin ya akayi bai nuna damuwarsa akan zancan ba
Seda yakarbi sauran ruwa ya ijiye sannan yazauna kusa da ita yace
Sonawa zan gayamaki idan zaki kuanta kirika yin addu'a amma ba kyaji yanzu gashi kinfara mungun mafarki yakarashe maganar yana kuashewa da dariya
Baki da hanci tasaki tana kallonsa ahasale tace wai Yaya kana nufin abunda nafadamaka mafarki
Murmushi yayi yace to ai sarah abunne yayi kama da mafarki taya mutumin da kuke soyayya har na saura sati daya aurenku kuma kice wai yace baya sonki yana da wacce kikeso
Murmushin dayafi kuka ciwo tayi tanuna masa fuskarta tana fadin Yaya wannan ma mafarkine
Dago fuskarta yayi yana kallon shatan yatsun da suka kuanta baro baro akuncinta abunka da faran fata
Nan take fuskarsa tacanza dan yatsani yaga abunda yataba lafiyar kanwarsa
Cike da mamaki yace sarah tell me what is happening
Muryanta na rawa tabashi labarin duk abunda yafaru tsakaninta da ahmad amma taboye zancan marin da tama ahmad
In shock yagama sauraren labarin
Makullin motanshi yadauka da wayoyinsa yanufi haryanr fita batare da yace kala ba
Har yakai kofa yasake dawowa yafizgi hannun sarah yatafi da ita
gudu gudu haka yake sakkowa kan stairs sarah dake biyedashi har tana neman faduwa
Karo sukaci da aysha zata haura sama shan gabansu tayi tana fadin AK lafiya meyafaru ina zakuje haka
Dayan hannunsa yasa yamatsar da ita gefe yawuce baice uffan ba
Baki bude tabisu da kallo har suka fita
Yana isa mota yabude gidan gaba ya wurgata sannan yazaga yashiga mazaunin driver yatashi motar aguje suka bar gida se company""""""
Ur's ....✍
0 comments:
Post a Comment