Dedicated to all Victims of Rape, never give up, fight for your right, this is not something to be ashamed of your self. Make the guilty ones feel ashamed of themselves* 🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾
"Garin Dukku jihar Gombe, gari ne wanda akasarin mutanen dake zaune wajen fulbe ne, ma'ana fulani ne. Ni Sameena tafe nake cikin garin ina bin tsarin garin da kallo yayinda zuciyata ta cika da nishad'i. Can na hangi wata matashiyar budurwa wacce ak'alla bazata gaza shekaru goma sha shida 16 a duniya ba. Daga yanayin halittarta zaka fahimci cewa bafulatana ce ta usul. Bata da matsanancin tsayi snn bata a layin gajeru, farinta irin mai d'auke idon nan ne don saida ta matso kusa sosai na fahimci hakan. Yanayin suturan dake jikinta zai tabbatar maka iyayenta talakawa ne sosai. Silipas din dake k'afufunta kuwa duk ya b'ule yaji jiki.
"Sauri take tamkar mai shirin tashi sama, yanayin tsoro da firgici da ya wanzu a fuskarta zai tabbatar maka cikin matsanancin tashin hankali take. Kaman ta zunduma a guje haka take tafiyar, Yar da d'an karan dake hannunta tayi ta soma sassarfa hadi da gudu gudu sakamakon jiyo muryar dake sata firgici koda a mafarkinta ne tana k'walla mata kira har waje ake jiyowa,. *ZUBAIDAH! ZUBAIDAH, ZUBAIDAH!!!
"Ni kuwa Queen Samy nace " Bari na bi wann yarinya na rubuto wa d'inbin masoyana labarinta mai cikeda tausayi, Al'ajabi da kuma ban mamaki had'i da darrusa masu girgiza zukata.
"Dan ubanki sai yanzu kika daman dawowa daga karuwancin naki? Macen dake tsaye tsakar gidan rik 'e da guga ta fad ' tana watsa wa Zubaida mugun kallo me nuni da cewa zaki yaba wa aya zak'inta.
"Bakinta na rawa take fad 'in Yaya Hadiza wllhi ban sami Yayan a kasuwa bane shine na k'arasa bakin tasha..... Ai bata gama cewa tasaha ba Yaya Hadiza ta jefa mata gugan dake hannunta ji kake tum ya fad 'I a tsakar kanta.
"Durk'usawa Zubaidah tayi tana rik'e da tsakar kanta hawaye na zuba bisa k'uncinta.
Hadiza ta k'araso gamida mak'urota tana fad'in" Dan ubanki ni na aikeki bakin tasha, wani munafurcin ne ya kaiki bakin tasha, auho kice mun karuwanci kika tafi, shegiya Me suffan mayu da aljanai. Rankwashin da ta sake mata a tsakar ka yasa Zubaidah sakin k'ara sabida azaban dataji.
"Hadiza ta shiga janta a k'asa tana fad'in" Au kuka ma zakiyi shegiya munafuka saikace wacce na bugeki toh bari kiga na tapkeki sosai sai kiyi mai dalili.
"Duk kukan da Zubaidah take tana rok 'on Hadiza tayi hak 'uri ko gizau bata fasa jibgangta ba kaman Allah ne ya aikota.
"Inna Furera mak'ociyarsu ce ta shigo a guje don ceton Zubaidah dama mak'ota sun saba shigowa kawo mata d'auki, tunda Hadiza ta tsefe ido taci mutuncinsu tsaf suka daina, saiko Inna Furera ce kawai bata fasa ba.
"Da sauri tayi tsalle ta kwace Itacen da Hadiza ke jibgan Zubaidah dashi, dama Jadiza irin ingarman matan nanne.
"Ta shige tsakani tana fad'in" Haba, haba Hadiza, anya kina kuwa tuna mutuwa, kullum sai ki kama wann 'yar marainiya kita jibga ke ko tsoron kamuwar Allah bakya yi. Cewar Inna Furera .
"Galala take Kallon Inna Fure kafin ta gyara tsayuwa ta soma fad'in" Fure! Fure!! Fure!!? Billahilazim hawainiyarki ta kiyayi ramata, banda munafunci irin taki ina ruwanki da ita, ci kike bata ko sha, cikin biyu babu d'aya. Toh wllhi wllhi ki fice a idanu na.
"Inna Fure tai murmushin takaici kafin tace " Lokaci ne, da zaran lokacin da Zubaidah zata sami kulawata yazo zata samu kuma ke baki isa kiyi komai ba.
"Shewa Hadiza ta kwashe dashi kafin tace " Ai dama nasan wajen munafukin wann d'an naki me matse yaran mutane a lungu take zuwa, bacin haka babu abinda zai kaita bakin tasha, Toh wllhi idan ni Hadiza ina numfashi Zubaidah bazata auri Ummaru dreban tanka ba. Ke na tak'sita maki zance Zubaidaha bazata tan's aure a rayuwarta ba, makarantar data samu na bari tayi ya isheta, amma aure kam saidai tayitaji k'annen bayanta suna tafiya d'akin miji amma banda ita, tunda dama sa 'anninta Sun k'are k'annenma sun kusa k'arewa. Ta juyo ta narkawa Zubaidah da har lokacin kukan zuci take hawaye na bin k'umcinta tace " Ke kuma bak'ar munafuka ki tashi ki min wanke wanke kafin ki d'aura sanwa don yau islamiyar ma ba zuwanta zakiyi ba. Daga haka ta wuce d'aki fuuu kamar me shirin tashi sama.
"Inna Fure ta girgiza kai ta k'arasa ga Zibaidah wacce ke faman mik'ewa da k'yar sabida raunin da Hadiza taji mata da itace, tsugunawa Inna Fure tayi tausayin yarinyar ya cika zuciyarta, a hankali tasa hannu ta goge k'wallan da ya zubo mata. Hannu tasa ta shiga sunce d'aurin da Hadiza tai ma Zubaidah da igiyan guga.
"Suna had'a ido Zubaida taji wani sabon kuka na shirin kufce mata, ........
[1/23, 22:07] +234 803 619 0581: 😭😭😭ZUBAIDAH😭😭😭
02
*©Sameena Aleeyou... ✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum.... 📖📚_
*Dedicated to all victims of rape, never keep silence, keep fighting for your right, this is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves*🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾
"Murya na rawa Zubaidah take fad 'in" Inna meyasa iyayenmu suka mutu suka barni dagani sai yaya na, meyasa Yaya na ya kasance haka, meyasa bai zama kaman ko wani d'an Adam ba...... " Tausayin kalamanta sun cika zuciyar Inna Fure, a hankali ta kwance bakin zaninta ta goge wa Zubaidah hawayen dake kwaranya a fuskarta. Hannayenta ta rik 'e suna fuskantar juna kafin ta soma fad 'in" Zubaidah kar ki bijire wa ubangijin ki, kar ki bari shedan ya rinjayi zuciyarki, har yake kawo maki ire iren wad'an nan tunani. Mutuwa dole ce kan ko wani mahaluk'i, snn kasancewar yayanki cikin mutane marrasa k'oshin lafiyan k'wak'walwa jarabawace daga Allah, wanda kema jarabawar ya shafeki. Shi kansa Habibu baijin dadin abinda Hadiza ke maki, amma babu yanda ya iya, bazai iya k'watan 'yancin kansa ba balle naki daga hannun Hadiza, hak'uri shine zakici gaba da yi.
"Goge hawayen tayi kafin ta furta a hankali " Kenan shikenan ni bazan tab'a jin dad'in rayuwa ba kenn, bazan rayu kaman yanda ko wani d'an adam yake rayuwa cikin 'yanci ba. ...."Kasa jure saurarenta Inna Fure tayi sabida tausayi, mik 'ewa tayi kafin tace "Tashi ki soma ayyukanki kafin ta fito ta sameki. Jiki a sanyaye Zubaidah ta mik 'e daidai lokacin " Kamalu d'an Yaya Hadiza ya fito cikin shirin tafiya islamiya fuskarsa da alamun bacci ya tashi, yaro d'an shekaru bakwai a duniya. Rungume Zubaidah ya k'araso yayi yana mata magiyan ta shirya su tafi islamiya, itama rungumesa tayi tana k'k'arin lalumo k'aryar da zata shata masa, don tasan yau kam babu ita babu islamiya. Inna Fure ta fice tana sak'sak'en lamarin Zubaidah a zuciyarta.
"Kamalu ya lura da hawayen dake bisa fuskan Zubaidah, Ya kalli gwiwar hannunta yaga jini, shiru yayi kaman bazaice komai ba kafin yace " Na sani yauma Umma tace ta dakeki ta hanaki zuwa makaranta ko Anty. Kame kame Zubaidah ta soma yi don yaron akwaishi da wayo da kaifin basira, daidai nan Yaya Habibu yayi sallama ya shigo cikin yanayin tafiyarsa na sokaye _Phsycos_ da maganansu.
Kamalu ne kawai ya tafi ya masa oyoyo Zubaidah kam wucewa tayi bakin rijiya don taran ruwan wanke wanke, tabbas tasan Yaya Habibu ya ganta a haka toh fah haka zai wuni yana kuka.
"Inna Fure tana shiga gida ta tarar da Umar dawowarsa kenan. Koda ya gaisheta sama sama ta amsa, Umar ya lura da yanayinta, don ko tambayarsa ko yaci abinci batayi ba, kaman yanda take a kullum. don haka zama yayi bisa gefen tabarman da take zaune " Sadda murya yayi kafin yace Innata meke faruwa ya tambaya yana kallon Inna Fure. Sauk 'e ajiyan zuciya tayi kafin ta soma fad'in" Umar shin da gaske kake son Zubaidah.
"Kallon mamaki yayiwa mahaifiyar tasa kafin yace "Haba Inna wann wace irin tambaya ne, Kowa ya sani duk fad 'in garin nan Zubaidah kadai nake so, nake burin mallaka, bansan meyasa Zubaidah tak'i barina na kai tambaya gidansu ba. Don wllhi Inna na k'agu na rabata da wann muguwar matan yayan nata.
"Inna ta sauk 'e ajiyan zuciya kafin tace " A gaskiya Hadiza bata da imani Ummaru....... "Ganin yanayinta yasa mik 'ewa zuciyarsa na bugawa yake fad'in" Inna ki fad 'a mun me tayi mata, ta kuma dukanta kaman yanda ta saba ko..
"Gjrgiza kai Inna ta soma tana fad'in a'a Umar don Allah ka zauna, zauna nace ba dukanta tayi ba, kawai dai so nake ayi maganar aurenku, da zaran malam ya dawo zan masa batun insha Allah, take farin ciki ya mamaye zuciyarsa nan ya shagala da zancen......Inna ta bisa da ido yanda yake murna kaman an masa alk'awarin hajji, gwara da ta kawo masa wnn zancen don tasan kalan zuciyar d'anta yanzu sai yaje yayi ma Hadiza kaca kaca.
**********************
*Abuja, Maitama*
"Wasu tagwayen gidaje na hango masu d'an karen kyau, exactly babu abinda ya raba da na gefe, komai iri guda. Wadan nan gidaje gidajen Yaya ne da kuma k'ani, Alhaji Kasim Dasuki shine Babba, yayinda Alhj Jamil Dasuki shine k'ani. Alhj Kasim da k'aninsa sunyi kaurin suna wajen hold'an kasuwanci ta yanda k'asashen duniya da dama suke hold'a dasu, tareda shahararriyar Company dinsu mai suna *Dasuki Holders*, Ko wannensu Allah Ya albarkacesa da yaro namiji k'wara dad'd'daya,.
SALIM KASIM DASUKI, da kuma LABIB KASIM DASUKI, tsakanin Salim da Labib shekara gudane cal, haka nan yaran suka taso cikin sangarci da rashin tarbiya, saboda so da iyayensu ke nuna masu, wanda a nasu tunanin gata ne. Babu mai taba masu 'Ya'ya Ya zauna lafiya sai sun ga k'arshensa, musamman Alhj Kasim shi yafi k'aninsa bak'in zuciya, wani sa'in Alhj Jamil dinne ke nusar dashi hanya. Haka zai balbalesa tsaf da masifa, uwa uba WA'azin da Alhj Jamil ke masa kan su guje dukiyar haramun cikin kasuwamcinsu, wann dalili Ya soma sakawa Alhj Kasim tsanar Dan'uwarsa har yake tunanin tabbas zasu iya samun sab'ani koma takaisu ga raba dukiyarasu.
[1/23, 22:07] +234 803 619 0581: 😭🙍🏻ZUBAIDAH🙍🏻😭
03
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum..📖📚_
*Dedicated to all victims of rape, never keep silence, fight for your right,... This is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves 🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾*
"Salim ne kwance saman coach a bakin pool dake a cikin gidansu, da gani daga ruwan ya fito don daga shi sai gajeren wando. Idonsa manne da bak'in sunshade ya k'ura wa rana ido, gefe dashi k'aramar table ne wanda wayoyinsa ne da kuma Chapman akai.
"A hankali ya kai hannunsa kan table din gamida daukar d'aya daga cikin wayoyin nasa nan ya shiga dialling lambar budurwarsa KAUSAR wacce ake batun saka masu rana. Sosai suke hiran soyayya daga ji kasan suna tsananin son junansu.
"Daga can bayansa yanda Labeeb ke tsaye ya k'urawa cousin d'in nasa ido, shakka babu su duka biyu sunyi tarayya wajen son mace guda, zuciyarsa yaci gaba da tafarfasa, da sauri ya juya ba tareda yayiwa d'an uwan nasa magana ba.
"KAUSAR TAHIR MARAFA, shine asalin sunanta, mahaifin Kausar abokin kasuwancin iyayen Labeeb da Salim ne, musamman Mahaifin Salim Alhj Kasim Dasuki, Shima Alhj Tahir Marafa dan asalin garin Dukku ne, Kausar basu jima da dawowa Nigeria ba daga k'asar Holland dalilin dawowarsu ma sabida neman muk'akin kujeran Shugaban k'asa da mahifinta zai fara ne, farkon dawowarsu sabo mai tsanani ya shiga tsakaninta da Labeeb a lokacin Salim yana can Scotland yana k'arasa wani course dinsa shi, koda Salim ya dawo Labeeb shi yayi masa introducing Kausar, tunda Kausar da Salim suka k'yalla ido akan juna soyayya mai tsanani ta shige tsakaninsu, toh fah run daga wann lokaci Labeeb ya rasa sukuni, a ganinsa cin amana ce wnn k'wace Salim yayi masa.
"Iyayensu gaba d'aya sunyi farin cikin wann Al'amari tun basu hadasu ba gashi sun hada kansu, babu kaman Alhj Kasim Dasuki wanda dama shi Money hungry, baya rab'an mutum sai zai sami alkhairi. Dukda tarin dukiyar da yake dashi baya hanasa hangar na wani. Yasan muddin tilon d'ansa Salim ya auri tilon 'yar Alhj Marafa wataran zasu mallaki gaba d'aya dukiyar Alhj Marafa.
"JALAL! Na'am Anna ya amsa gamida ajiye takalmimsa da yake faman gogewa, fitowa yayi ya tarar da Annah zaune tana stincen wake
. Kallonsa tayi yanda ya shirya tsaf cikin kaya masu kyau da tsada kaman wani d'an hamshak'i.
"Jalal ina zaka, Jalal farin saurayi dogo mai cikar zati kyakkyawa ya murmusa kafin yace "Annah birthday d'in abokinmu TARIQ zamuje su Salim suna waje suna jira na.
"Fuskar Annah tamau dama tasan zancen bazai wuce haka ba, tasha raba Jalal dasu Salim amma baya ji, yak'i yarda ya tsaya a matsayinsa na talaka bashi da aiki kullum sai k'ok'arin had'a kansa da sangartattun yaran masu kud'i musamman su Labeeb.
"Gyaran murya Annah tayi kafin ta soma fad 'in" Jalal har yaushe zan maka magana kaji, ka sani kai maraya ne kuma talaka, idan baka tashi ka tsaya ma rayuwarka ba babu wanda zai maka, kai kullum bakada aiki se biyewa su Salim ko, toh ka sani su sunada masu masu, sunada gatansu kaifah, baka dashi , tunda ka gama jami 'a ka'ki neman aiki ka tsaya kana biye masu, yau kune wancan club din gobe wancan, kune bin 'yanmata kune shaye shaye...... "Jalal yayi saurin d'ago kai yana kallon Annah, haba Annah shaye shaye fah kikace nasan dai su Salim suna yi amma ni banayi, ina dai da 'yammata banyi musu ba amma wllhi bana shan komai tunda kika hanani....... "Rufe mun baki Annah, ta dakatar dashi kafin taci gaba da fad'in" Da da kakeyi na maka uzuri don na d'auka yarinta ne zaka daina amma yanzu na gane shashanci ne kawai ke damunka, shekaranka 25 ace bakasan abu me kyau ba toh wllhi ka kiyayeni..... "Sallaman Labeeb ya katsesu.
"Gaisar da Annah Labeeb yayi, ta amsa masa babu yabo babu fallasa, kafin ya d'an daki kafad 'un Jalal yace Guy let's get going.. Jalal ya mike yana satan kallon Annah kafin yace Annah sai mun dawo, kallo tabisu dashi har suka fice, girgiza kai tayi kafin tace bazan fasa maka addu'an shiriya ba.
Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:07] +234 803 619 0581: 😭🙍🏻ZUBAIDAH🙍🏻😭
04
*©Sameena Aleeyou..✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_
*Dedicated to all Victims of rape, never keep silence. Fight for your right, this is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾*
"JALAL, abokin su Saleem ne wanda tun tasowarsu tare suka taso, Jalal maraya ne wanda bashida kowa sai mahaifiyarsa Annah, Annah tayi komai a rayuwarta don ganin ta inganta rayuwar Jalal tun yana yaro, kama daga karatunsa har zuwa girmansa, haka nan ya tashi ba tareda yasan mahaifinsa ba, don Annah ta sanar dashi cewa mahaifinsa ya rasu tun yana k'arami. Annah ta jima tana yiwa matar Alhj Kasim aiki wato mahaifiyar Salim, tun wani lokaci da suka zauna a Gombe, tun yaran gaba d'aya suna k'anana, Annah ita ta rainesu gaba d'aya, Salim Labeeb da kuma Jalal d'inta, wann dalili yasa lokacin da zasu komo Abuja suka taho tareda ita don tun a lokacin bata da miji ya rasu. Ta zauna da d'anta a nan BQ din gidan Alhj Kasim.
"Tunda yaran suka taso iyayen ke k'ok'arin rabasu da Jalal, suna nuna masu cewa shi ba daidai dasu bane, babu yanda basuyi ba don ganin sun rabasu amma abu yaci tura dole suka hak 'ura suka k'yalesu, amma ko kid'an babu wani abu na arziki da suke masa.
"Shi kuwa Jalal babban abun da ke masa dad'i shine yanda emmata da samaruka yaran masu kud'u suke zaton shima DASUKI'S ne, ma'ana shima dan familyn Dasuki ne, ko ina tare dasu Salim suke zuwa party shisha spot da dai sauransu. Allah ya masa kyaun hallita gabba d'aya yafisu kyau 'yanmata suna rubibinsa shiko na ja masu class kaman wani d'an hamshak"i ko kad'an bakace Jalal ya had'a jini da talaka ba...wann kenan.
*Gombe, Dukku*
"Huci take kaman wata kububuwa tana watsawa malam Habu mahaifin Umar da abokinsa malam Tanko harara, Malam Habu suka saki baki suna kallon ikon Allah sanda Yaya Habibu ya mik'e ya rusuna gaban Hadiza yana tambayanga shin ta amince a karb 'I baikon Zubaidah, .... Mikewa Hadiza tayi kafin ta d'ibi 'yan goron da malam Habu suka shigo dashi ta shiga juye masu a tsakar kansu, tana balbala wutan bala 'i da masifa, ta yanda take shiga bata nan take fita ba.
"Malam Tanko ya mik'e yana fad'in subuhanallah, Malam Habu ya baka fad 'a mun haka lamarin yake ba, Malam Habu da kunyar abokinsa mutum mai muhimmaci a gari irin Malam Tanko ya baibayesa, dama yasan haka ka iya faruwa, shiyasa tun farko bai so Ummaru ya nemi Zubaidah ba dukda ya aminta daehankali yarinyar kuma na tausayinta, amma ko kad'an bashi fatan abinda zai hadasa da dilalliya Hadiza,.....
"Zubaidah dake mak 'ale bayan k'yaure bata san sanda ta sulale gwiwoyinta a k'asa ba tana hawaye sanda ta jiyo irin fatattakan da Yaya Hadiza tayima iyayen Umar, shikenan itakam tasan bazata tab'a aure ba, bazata tab'a jin dad'in rayuwarta ba, mafarkin ta bazai tab'a tabbata ba, takaicin yayanta da tausayin kansu shida ita ya lullub'e zuciyarta. A hankali ta k'arasa kan tabarman da ya kasance makwancinta ta kwanta tana kuka mai tsuma zuciya.
"Malam Habu jiki a sanyaye ya shiga bawa Malam Tanko hak'uri, Malam Tanko yace a'a abokina baza 'a bar wann magana ba tunda yaran suna son junansu ni nasan yanda za'ayi, ka shige gida zan nemeka zuwa gobe, Malam Habu ya masa godiya sukayi sallama kafin malam Tanko ya hau babur dinsa ya wuce.
*******************
*Abuja*
"Suna isa wajen partyn pili ya dauki shewa da ihu, manyan yara wanda duk gabaki d'aya Abuja sunansu yayi k'auri Sun samu halarta, Tariq ya k'araso yana welcoming nasu sai wani tafe hannaye suke yanda niggas keyi. Tariq shine cikon na hud 'u a clik d'insu, shima mahaifinsa nada shears a companyn *Dasuki Holdings* kampanin mahaifan Salim da Labib, ..
*Zubaidah, Jalal, Umar, Salim, Labib da kuma Tariq*
*Ku biyo Sameena don jin labarin gumurzumon da wad'annan matasa suka fuskanta.......... 👌🏾*
[1/23, 22:08] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
05
*©Sameena Aleeyou.....✍🏾*
_Queen Same Novels Forum...📖📚_
"Alhj Kasim Dasuki, Alhj Jamil Dasuki da kuma Alhj Yusuf Maina mahaifin Tariq sai Barrister Munir Malami lawyer na company ɗinsu *Dasuki Holdings* kuma yaya ga mahaifiyar Salim Haj Farha Dasuki.
"Zaune suke gaba ɗaya a babban parlorn taraban baƙin Alhj Tahir, magana suke na tsaida ranar auren Salim da Kausar, an tsayar sati mai zuwa za a yi bikin saka rana. Daga nan suka ɓuge da hiran kasuwanci da siyayasa. Tunda dama Alhj Tahir na neman tsayawa takaran shugaban ƙasa, nan Barr Munir ya bada shawarin a tafi chan Dukku ayi bikin saka rana hakan ba ƙaramin nasara zai kawo wa neman takaransa ba, gaba ɗaya sukayi na'am da batun Barr Munir snn ƴan garinsu zasu tabbatar shi ɗin mai ƙaunar mahaifarsa ne..... Har farfajiyar gidan Alhj Tahir ya rakosu yanda bodyguards ɗinsu suke... Daga nan ya wuce ɓangaren matarsa uwar ƴarsa Hajiya Raliya don sanar da ita yanda suka tsai da batun auren yaran.
"Kausar da Asmah ya samu a parlorn ƙasa suna playin PSP, gaba ɗaya suka soma gaidashi... Papa sannu da shigowa amsawa yayi da sakin fuska kafin yace ina momman taku, har suna haɗe baki wajen cewa she's upstirs, ƙarasawa yayi ya nufi stirs ɗin.
"Kausar da Asmah suka ci gaba da game ɗinsu. Asmah cousin ɗin Kausar ce wacce a shekare baifi ta girme wa Kausar da shekera guda ba, tun dawowarsu Nigeria Asmah take gidansu daga zuwa kwana biyu Kausar taƙi barinta ta koma dole Aunty Miemie mahaifiyar Asmah ta haƙura da zancen don tasan halin Kausar da kafiya.
"Momma na zaune gaban dressing mirror tana gyaran fuska as usual don itakam taƙi yarda ta tsufa at her late 40s bats sahun matan nan masu barin gyaran jiki da zaran sunga shekaru ya soma ja masu,... Murmushi Papa yayi gamida rungumota ta baya, murmushi itama ta sakar masa kafin tace" Papa how do i look like, ɗan jan hancinta yayi kafin yace as always my one you look so gorgeous manna mata peck yayi a goshi kafin suka zauna bakin gado ya soma faɗa mata yanda suka tsai da maganan bikin Kausar, nan da nan idon momma yayi raurau Kausar is her only daughter ƙaunar ranar rabuwarsu tazo dukda tasan dole wata rana hakan ta kasance.... Papa yasan kwanan zancen don haka rungumota cikin jikinsa yayi ya soma lallashinta da kalamai masu taushi, "Haba first lady you need to be very strong you know, sooner or later zaki zama mother of the country insha Allah, bama Kausar kawai ba, the whole country will be yours, and for now akwai Asmah though nasan itama tana samu miji zamu aurarta but atleast zata ɗauke mana kewar Kausar.... Jin yanda mijin nata keta faman riritata yana shagwaɓata yasata sakin murmishi gamida goge guntun hawayenta tace" Pappy you ƙnow what made me cry...." Ɗan girgiza kai yayi har lokacin tana cikin jikinsa kafin taci gaba da faɗin" I dont know why, but har raina banjin son auren Kausar da Salim duk da ɗan aminiyata ne, quite alright nasan gidan girma arziki da mutunci zata but.... Kasan yaran zamani kar Salim ya hurting mana baby girl ɗinmu...."Papa yayi murmushi gamida shafa goshinta zuwa gashinta kafin yace" Raliya insha Allah we won't regret it, bazamuyi danasanin aurar da Kausar wa Salim ba, besides they both love each other wanda kinga hakan akeso ya kasance. Yanzu abunda nake so dake, you shud start preparing we leaving in a couple of days gwara mu mu fara isa tunda mune iyayen bride, I'll make sure the house is ready from now to tomrrw, ki kira su Kausar ɗin ki sanar dasu su fara shiri, barin ƙarasa parlor inada wasu baƙin.. Gyada kai kawai momma tayi da ƙyar kafin ya manna mata kiss a chick ɗinta ya fice.
"Wann shine rayuwar gidan Alhj Tahir, mutane ne masu Dattako da sanin ya kamata, ko kaɗan basuda ƙyamar talaka kaman Dasuki family, snn abin hannunsu sam bai rufe masu ido ba, da wann dalili yasa akasarin mutane suke mara masa baya a siyaysarsa, yayinda wasu ke ganin The Dasuki family ks iya ja masa cikas a siyasarsa sabida izzan su da ƙyamar talaka ds suke dashi.
"Kausar da Asmah sai murna suke zasu Dukku dukda kakanninsu gaba ɗaya sun rasu amma skwai sauran dangi, Momsy ya maganar kayan gaskiya ki sake masu waya we need them this week, they shud make it possible this week. Momsy ta ɗan sakar mata harara kafin tace" Kausar this is not Holland fah, na faɗa maki ki rage wann rawar kan taki, ba irin auren da kika saba gani bane na turawa, wann auren fulani ne wanda aka san sansu da kunya so be careful,... Momsy tana ficewa Asmah da Kausar suka kalli junah, suna daroya ƙasa ƙasa don suma har sun ɗagota bata son Kausar ta bar gidan ne Asmah ta ɗau waya tace bari kiga na kira *Mamza beauty* (makeup artist) na sanar mata, ke kuma pls ki kira Sarah fashion ( Fashion stylist ne a Dubai wanda zasu ɗinka kayyaykin Kausar da zatayi amfani dasu a events) ɗin ki sanar dasu.
"Rungume pillow tayi gamida lumewa cikin hashaƙin gadon tana tuno farin cikinta Salim, ya kusa zama *Mallakinta* Asmah na mata magana ko saurara batayi ba tayi nisa wata duniyar, girgiza kai kawai Asmah tayi ganida jifar ta da pillow kafin ta fice.
"Tafe suke suna tangaɗi da gani kasan sun bugu da giya, da ƙyar suka iya fitowa daga motan ,Alhj Kasim da har loƙacin idanunsa biyu baiyi barci ba ya dubi agogon bango dake maƙale a ɗakin ya nuna ƙarfe uku na talatainin dare, yasan ba kowa bane zai shigo gidan a yanzu sai Salim, kai tsaye down stirs ya sauƙo ya buɗe ƙofar parlor, chan ya hangesu suna tafe suna tangaɗi gaba ɗayansu, Jalal na riƙe dasu don dama duk randa suka je party suka shawu toh shi ke driving nasu da shike shi bai sha yanda za'a gane sama sama yake kora wine maras bugarwa sosai shide barshi da harƙan bin mata, shiɗinma da yawa ƴan matan ke kawo kansu wasu na zaton shi ɗin ɗan Dasuki Family ne yayinda wasu ke sonsa sabida kyaun da Allah ya masa.
"Wani mugun kallo kawai Alhj Kasim ke binsu dashi musamman Jalal, shikan ya tsana ganin yaransu da sidecake ɗin,..... "
"ƴan kame kame Jalal ya soma, tuni Alhk Kasim y dakatar dashi da faɗin" meyas baka kai shi gidansu ba ya ƙarashe maganar yana nuni da Labib, Jalal da tuni ya shaƙi kallon ƙasƙancin da Alhj Kasim ke masa, a daƙile yace " Gani nayi nan ma gidansu ne......"Jar ubancan haka Alhj Kasim yace a zuciyarsa lallai wnn talakan raini na neman shiga tsakaninsu, baiga laifinsa ba lafin su Salim ne,... Securities ne suka ƙaraso suka shiga taimaka wa Jalal, ɗaya security ɗin daga gidansu Labib yake yazo tafiya dashi don hankali mom ɗinsa ba ƙaramin tashi yake ba duk randa yayi dare a waje, duk da hakan ba sabo bane amma she couldnt get used to it har yanzu. Haka aka wuce da Salim da Labib kaman wasu mutattu don tuni bacci yayi awon gabadasu.
"Jalal ya ɗaga gira sama kafin ya dubi Alhj Kasim yace" Have a good evening Sir , daga nan yayi wucewarsa can sashensu. Kallo Alhj Kasim yabisa dashi kafin yayi ƙwafa ya shige cikin gida.
"Washe gari zaune suke gaba ɗaya a babban parlorn Alhj Kasim, Ya kuma duban Hajiya Farha dake zaune gefen Hajiya Nurah mahaifiyar Labib yace" Farha jeki taho min da yaran nan Labib da Salim suna sashen Salim, babu musu Hajiya Farha tabi umarnin mijinta ta fice kiransu.
"Sai ihu suke suna buga game na ƙwallo ko saurarenta basuyi ba, da takaici ya isheta batasan sanda ta fincike socket ɗinba....."Whatttt!!!!! Suka fadi a tare, Salim yayi jifa path ɗin hannunsa gamida faɗin " Shitttt, why mum haba haba mum.... Rufe mun baki marassa hankali kawai Mum ta ƙasesu, Labib ya ɗan langɓe kai kana yace" We are sorry favorite Aunty, Kunnens ta janyo kafin tace" Daga yau zaka tashi daga fav son idan baku zama good boys ba, Dad na kiranku bata jira cewarsu ba tayi ficewsrta. Labib yace nasan Uncle ne dama zai sa Fav Aunt ta mana haka he will never change. Salim ya watsa masa mugun kallo kafin ya fice ba tareda yace komai ba.
" Cikin tafiyarsu na samarin da tarbiya bai ishesu ba suka ƙaraso parlorn, gamida tsayuwa ma iyayayen tsegehe akai.
"Alhj Jamil, ya sauƙe ajiyan zuciya kafin yace" Seat down boys, zama suƙayi da ƙyar saman carpet Alhj Kasim kuwa banda hararsu babu abinda yake. Kaman jira yake nan ya soma surfa masu masifa " When are you boys going to start acting like real Dasuki's huh?Har yaushene zaku daina alaƙa da wann matsiyacin yaron, he's not one of you ba daidai ku bane get this to your heads..... " Alhj Jamil da mamaki yake kallon ɗan uwan nasa ko kaɗan baisan kan hulɗa da Jalal zai masu faɗa ba, a'a ya ɗauka kan ɗabi'u marassa kayu da suke zai masu faɗa, to his gretest surprised sai jin akasin haka yayi, lallai yayansa yayi nisa.
"Labib ne ya ɗago kai yanai ma uncle ɗin nasa mugun kallo ƙafin yace" Pls uncle will give us break, idan dai akan Jalal zaka mana faɗa you can keep on doing it but bazamu taɓa rabuwa dashi ba he's our childhood friend a brother from another mother....."Enough Labiiiib! Daddƴnsa ya daka masa tsawa, kafin yaci gaba da faɗin " Ma ucle ɗin naka kake faɗun magana haka, be careful kana jina, Labib yana wani hure huren hanci yake watsa wa uncle ɗin nasa mugun kallo, Barr Munir ya sako baki da faɗin" Ni kawai a kori ysron da mahaifiyarsa kowa ya huta. Wata harara Labib ya watsa masa kafin yace" Malam ka mana shiru dalla this is family issue who invited you..." Salim ya caƙumo wuyar Labib yana huci yake faɗin " First kayi rashin kunya wa Dad ɗin second kanayi wa Uncle ɗina, Brothern mahaifiyata how dare you Labib.... Saida aka shiga tsakanin Labib da Salim don kaɗan ya rage basu kaure da faɗa ba.
" Alhj Kasim ya goge zufar data keto masa dukda ac dake busawa a parlorn, iyayensu matan su suka lallashesu kafin suk sanar ɗasu maƙasudin haɗuwarsu.
"Take annuri ya cika fuskat Salim tuni ya mance wani baƙin ciki ya soma farin ciki, Yayinda zuciyar Labib taci gaɓa da tafarfasa, a cikin ransa yake furta " _no way it can't be happening, Kausar is mine not yours Salim Dasuki_
"ƙarasawa yayi ya ɗan daki kafaɗan Salim yayi con granulating nasa kafin ya fice cikin sauri.zuciyarsa naci gaba da tafarfasa
*****************************
"Mai anguwa yaci gaba da faɗin' ni mai anguwa ni na karɓi baikon Zubaidah kina jina ya ƙarashe maganar yana duban Hadiza data sadda kai a gabansa ta cika tayi fam. Ƙiris ya rage bata fashe ba.
"Hamma Habibu kuwa sai wsge baki yake kaman gonar audiga yanai wa mai anguwa godiya, banda hararsa babu abinda Hadiza keyi tanai masa kallon zaka shigi hannu ne. Mai anguwa yaci gaba da faɗin ya ysai da aure nan da wata mai kamawa kowa yaje yaci gaba da shirye shiryensa, kuma uffan Hadiza tayiwa Zubaidah za'a mata hukunci mai tsanani koma ya miƙa case ɗin gaban sarki, daga nan ya sallami Hadiza da Habibu suka wuce.
"Malam Tanko da mlam Habu sukayi godiya sukayiwa mai unguwa suka ɗan tattauna kafin ya sallalmesu.
"Tsakanin Ummaru da Inna an rasa wayafi farin ciki, tuni ya ficr ganin masoyiyarsa, mai shirin kasancewa amaryarsa......
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:08] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
06
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
"Zubaidah zaune bakin murhu tana kan hura wutan girki, ko kaɗan yau bata jin zafin duk tulin aikin da zatayi, snn ko kusa masifan Yaya Hadiza bai ɗaga mata hankali ba, jinta take tamkar sallah, muddin zata bar wann kurkukun dole taji farin ciki a zuciyarta, uwa uba zata ci gaba da karatunta saidai zatayi kewan Kamalu da Hammanta.
"Wani yaro ne yayi sallama snn yace wai ana sallama da Zubaidah...... "Wulli wulli tai da idanu tana kallon yaya Hadiza dake zaune bakin ƙofar ɗaki ta cika tayi fam ƙiris ya rage ta fashe.
"Meye kike mun kallon ƙurilla mayya jarababbiya, ai shikenan hankalinki ya kwanta za'a maki auren abinda kike so, ƙaramar karuwa kodayake ba laifinki bane kin riga kin san namiji tun a gantalinki na karuwanci......."ƙwalla suks ciko idanunta kanta na sunkuye a ƙasa, wann mummunar kalma na karuwanci da Hadiza ke jifarta dashi sosai yake ɗaga mata hankali.... Bata gama tunanin da take ba sai ji tayi yaya Hadiza ta janyo wuyarta ta jefata bakin ƙyaure tana faɗin "Wuce kije shegiya mayya kafin ki cinyeni, maza kije yaci gaba da mammatse a lungu yanda ya saba...."
" Ko ɗan kwalliya da ƴammata keyi idan zasu wajen saurayi Hadiza bata bar Zubaidah tayi ba, haka nan yanda ta tashi daga bakin murhu da warin hayaƙin da komai ta turata waje....
"Daga can bakin bishiyar da yake tsaye ya hangeta tana goge hawayen da ya jiƙa mata fuska.. Cikin sauri Umar ya ƙaraso yanda take, tuni ta soma matsawa da baya don bata so yaji ƙaurin hayaƙin da take, gashi shi yayi tsaf ya sha gayu abinsa irin na samari daidai da ajinsa.
" Harɗe hannaye yayi a ƙirjinsa yana kallonta, tausayinta da ƙaunarta na daɗa ratsa ɓargo da tsokarsa,.. Saida ya bari ta gama ƴan goge gogen hawayen kafin ya ɗanyi gyaran murya cikin tattausar murya ya soma faɗi" Zuɓaidah, shiru bata amsa ba har lokacin kanta na kallon ƙasa, kafe ta idanu yayi kafin ya kuma kiran sunan nata, sai snn ta ɗago koɗaɗɗun idanunta ta mar duba guda, Umar yanada ƙwarjini ta yanda duk budurwar da tayi ido huɗu dashi sai ta tsinci kanta da faɗuwar gaba, gashi a yau yafi kullum mata kyau, shi ba fari bane snn ba baƙi can bane, kallo guda zaka masa ka gane asalin bafulatani ne haɗi da kwantattun sumanss da sajensa da suks ƙara masa kyau da ƙwarjini...."Muryarsa ya katseta sanda yayi mata nuni da wani kututturen dabino yace" Mu karasa ki zauna, babu musu tabi umarninsa......" Har sun soma tafiya suka jiyo muryar Hadiza ashe tana laɓe jikin ƙyaure tana saurarensu nan ta soma faɗin "Ku ƙarasa ina, kai wani irin jarabebbe ne, baka jira akai maka ita ba sai kazo har ƙofar gidansu kana matseta, auho ashema kun saba kinji kunya Zubaidah tuna kika zaɓi zama karuwa, toh ni dai kar ki kawo min abin kunya kafin wata gudan da aka ɗiba maku ya cika taƙarashe maganar tana watsa masu mugun kallo.
"Umar yabits da kallon mamaki, ƙarasowa gabanta yayi yanda take tsaye kafin yace" Dillaliya kike ko wa? Galala take dubansa cike da mamaki kodashike tasan Ummaru da wann taurin ran nasa zaiyi fin haka, muryarsa ya katse mata tunaninta yanda yaci gaba da faɗin" Yau ta kasance rana ta ƙarshe da zaki saka masoyita kuka, don wllhi kinji na rantse kika kuma kiranta karuwa kotu zan maka ki sai munyi shari'a daga nan har birnin tarayya, kuma da kike cewa ni jarabebbe, naji na yarda idan dai akan Zubaidah ne sai nafi jaraba ma naci, don nasan bazan taɓa ƙosawa da ita ba, ki kalleta da kyau mana, ke ai kina ganinta kinga mace ba irinki ba, nasan hassada ce tsan tsa kike da ita ba wani abu, yayi wata murmushi mai cike da nishaɗi da gargaɗi kafin yace" This should be the last warning idan kunne yaji toh fah jiki ya tsira, daga haka ya dubi Zubaidah da ƙiris ya rage bata saki fitsari a jikinta ba don tsoro kana yace" Amaryata lets go, dont mind this witch, don yasan Hadiza dai ba turanci take ji ba......"Kallon Yays Hadiza tayi alamun tana jiran umarninta" Haba tuni ta soma bambami tana kunfan baki, yo har ni za'a yi ma turanci, ke Zubaida har kinyi kaurin da zaki biyewa saurayi inji ni nayi ɗawainiyar karatun naki, har shine zaki zaɓi saurayi akaina ya zageni da kalman turanci kina tsaye kina biyesa yayi maki kyau, idan dai namiji ne kije gaki gashi ..... Daga haka tasa kai ta wuce cikin gida fuu zuciyarta naci gaba da tafarfasa....
"Juyowa tayi tana duban Umar, murmushi ya sakar mata kafin suka ƙarasa suka zauna.
"cikin tattausar muryarta ta gaidashi, ya amsa yana wani kasheta da mayen kallo, ita kiwa duk kunyarsa ya rufeta musamman cewa da yayi, idan dai akanta ne sai yafi jaraba naci, wann kalmomi sun matuƙar mata nauyi, kaman yasan hakan kuwa nan yasa hannu ya karɓi ɗan karan da take wasa dashi aiko nan ta ɗago ido suka kalli juna, tai saurin sadda nata idon,
"Zubaidah, ki sani ina sonki ina ƙaunarki sann zanyi komai a sabida ke, nasan kalan rayuwar da kike da wann matar, daga rana mai kaman ta yau ki sani bazan sake barinta taci zarafinki ba.
"Ɗan murmusawa tayi kafin tace" Na gode, cikin muryarta mai daɗin saurare, kaman waccd aka zabura ta miƙe tsaye, ɗan dubanta yayi kafin yace" Yaya dai ko har mun gama hiran ne, ɗan girgiza kai tai kanta na ƙasa kafin tace" A'a gani nayi kaman ƙaurin dake jikina ya dameka.
"Tsuke fuska yayi ya kira sunanta da dakakkiyar murya, ɗago ki kalleni Zubaidah, ta ɗago tana dubansa, Umar yaci gaba da fadin" Nida ke mun zama ɗaya, bana jin ƙauri ajikinki, akasin haka nike ji, ma'ana ƙamshi nake ji, kasancewa taredake yafiye mun komai ina sonki a duk yanda kike. Murmushi tayi harda ɗan rufe fuska alamun taji kunya,.. Dariya ya ɗanyi mai bayyanar da hƙwara kafin yaxe" Oya faɗa mun kina sona... Ware idanu tayi alamun bazata iya ba, Umar yayi murmushi kafin yace" Surbajo na nasan kinayi koh... Kasa cewa komai tayi sai murmushi.... Hira sosai suka sha a wann rana kamsr karsu rabu da juna, basu taɓa hira irin haka ba, kullum saidai su haɗu a bakin rafi taje ɗibo ruws ko kuma ta kai saniyar yaya Hadiza kiwo.
*********************
" Salim ne tafe waya manne a kunnensa yayinda hannunsa ɗaya ke riƙe da coffee cup, "What com'on Tariq pls ka shirya yanzu yanzu, we will fetched you up sai mu wuce airport ɗin... Yeah right , see you soon. Yayi hanging up kafin ya tura ƙofar ɗakin da hannu guda.
"Cak ya tsaya yana kallon Labib dake baccinsa hankali kwance. Kan gadon ya ƙarasa ya ɗauki pillow ya shiga dukan Labib dashi yana faɗin" Will you get your lazy ass out of bed,...
"Labib, yayi miƙa gamida cusa kansa cikin bedcover yana faɗin" Shitt, pls mana Salim, kasan ba'a tashina a bacci i'll fall sick.
"Salim ya shiga yaye blancket ɗin yana faɗin whatever, You know we cant miss this flight, tun jiya Daddy ya mana bucking flight ɗin Gombe mukayi missing still yauma muyi missing what will u expect, they'll get mad ai.
"Gajeren tsaki Labib yayi kafin yace" Does it really has to be now, " Labib ya miƙe yana wangale labulayen tapƙa tapkan windunan ɗakin kafin yace" The flight is 10am and yet is almost 30mins pass 9.. Tsaki Labib ya kumayi babu salati yake hamma kafin yace" waima ina private jet ɗin Dasuki Holdings ne ba sai mu tafi dashi ba, Salim yace gaba ɗaya Jets ukun suna da prob, Daddy yace zaiyi firing masu maintenance ɗinsu, kaga idan mukayi missing wann flight ɗin tofa saidai mu tafi Gombe by road, kai ina I cnat afford to miss this flight ma, i'm dying ti see my Kausar,.. "Galala Labib ke kallonsa kafin yace" Waye ma kake tunanin zaiyi tafiya mai nisa haka by road, haba ba dai ni Labib Dasuki ba.
"Salim yayi dariya kafin yace" Freaking Dude sai ka tashi ka shirya ai na masu Tariq da Jalal magana suna shiryaw Ya ƙarashe maganar yana jifan Labib da towel.
Ba don yaso ba ya miƙe ya nufi bathroom..
"Gaba ɗaya Annah bataso tafiyar Jalal Dukku ba, don tun yana ƙarami data taho dashi Abuja basu kuma leƙawa ba, tana tunanin abinda ka iya zuwa yazo, kar wata rana daɗeɗɗiyar sirrinta data ɓoye masa ya bayyana. Haka tai kusan kwana zullimi......
*Gombe, Dukku*
_Toh fah readers gasu Jalal, Labib, Salim, da kuma Tariq a garin Dukku, shin me zai faru. Shin me Annah take ɓoyewa Jalal tsawon rayuwarsa. Ku biyo Sameena don jin yanda zata kasance_
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:09] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
07
*©Sameena Aleeyou.... ✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
"Drivers ɗin da suka ɗibo su daga airport suka soma paka luxurious cars ɗin a farfajiyan tangamemen gidan wanda yasha tsari da kayan alatu, idan ka shiga gidan sai ka ranste ba'a Dukku kake ba.
"Kai ysaye cikin gidan suka nufa yayinda gurds suka shiga firfito da luggage ɗinsu.
"Iyayen nasu ne zaune a babban parlorn, ciki harda iyayen Tariq.
"Tun daga nesa Alhj Kasim ya haɗe giran sama da ƙasa sakamakon abinda ya gani, wayo wann tsinannen mayen yaron saida ya biyosu...... Ko saurarensu baiyi ba sanda iyayayen keta faman hugging yaran suna masu sannu da zuwa, rai ɓace ko kulasu baiyi ba yayi ficewarsa, Labib ya rakasa da harara har ya fice. Cikin sauri Barr.Munir ya miƙe yabi bayan uban gidan nasa.
"Da yamma lis hadari ne sosai a garin already dama an idda wani ruwan don haka garin yayi sanyi weather yayi dadɗi. Samarukan guda huɗu suka shirya cikin ƙanan kaya kafin suka shige motarsu mai buɗeɗɗen sama don zagaya gari.
"Mutumina na maka murna fah ka kusa zama ango, cewar Balele dake zaune saman mota a bakin tasha, Umar yayi wani murmushin jin daɗi kafin yace insha Allah abokina, Balele ya kashe masa ido guda kafin yace" Ina tausayin yarinyar nan duk randa aka kulleta a ɗaki daga kai sai ita mutumina nasanka fah babu ɗaga ƙafa ranar..."Wata dariya Umar yayi kafin ya dubi Balele ya soma faɗin" Naji tunda nayi haƙuri ban taɓa bin ko wata mace ba, ban taɓa danne ƴar kowa ba ko ƙanwar kowa, kaga dole duk randa na sami nawa nayi budurina, babban farin cikina shine zan kasance da macen da nake so....."Balele ya busa sigarinsa a daidai fuskan Umar yana murmushi gamida jinjina kai.... Wani mugun kallo Ummaru ya watsa masa kafin yace waikai baka gajjiya da kayan maye ne? Murmushi Balele yayi kafin yace tuƙa manyan motoci ai saida kayan maye, gaskiya Ummaru ina gani ƙoƙarinka da ko karar sigari baka sha, Umar ya girgiza kai ba tareda yace komai ba ya soma ƙoƙarin miƙewa.
"Ina kuma zaka Balele ya biɗa,
"Bakin Rafi zanje munyi da Zubaidah zamu haɗu can, Balele ya murmusa kafin yace" Zubaidah tsokale idon samarin Dukku, gaskiya kayi sa'a da har ake ƙoƙarin maganar aurenku su Gwatse basu taɓa kai mata hari ba.
"Umar yayu wata murmushi mai cike da ma'anoni kafin yace" Balele kasanni akan abinda nike so, wallhi duk garin nan babu wanda ya isa ya taƙura Zubaidah muddin ina numfashi matar yayanta ma data tashi gabanta ban ragar mata idan dai akan sanyin idaniyana Zubaidah ne balle wasu ƙananun tsageru su Gwaste, wani murmushin ya kuma kafin yace "Shege ka fasa gasu ga ita......"Balele ya bushe da dariya kafin yace" Kai mutumina daɗina da kai akwai zuciya.... "Ba tareda ya kallesa ba yace" Kaga ni zan wuce idan Oga Kabiru ya iso ka basa uzurina dan Allah.
"Aff ai yau bazamuga Oga KB ba cewar Balele.
"Umar ya jiyo gamida mada kallon meyasa.
"Bakada labarin zuwansu Alhj Dasuki da ƙaninsa da kuma Alhj Tahir Marafa na unguwar dutse, mai neman tsayawa takaran shugaban ƙasa..... "Ɗaga kafaɗu Umar yayu kafin yace" Toh ni ina ruwana da zuwansu, Balele ya sake baki yana kallonsa kafin yace" Toh bikin saka ranar auren ƴaƴansu za'ayi jibi jibin nan kuma ƙofa a buɗe take ga dukk mai niyan zuwa kasan dai yanda suke neman muƙamin nan dile suja talakawa jiki. Na tabbata Oga yana can ana yana neman ganin Su.
"Gajerwn tsaki Ummaru yayi kafin ya miƙe gamida ɗaukat hankacip ɗinsa da yake riƙe kan starry dashi idan zai tuƙi musamman mai nisa kafin ya wuce ya bar Balele a nan zaune yana shaƙan kayan mayensa, Balele na masa sallama ko kulasa baiyi ba don baiso ya bar masoyiyarsa tayita jira.
"Wow.... This is so woow I just cant believe it yau gani a mother land ɗina, infact motherland ɗinmu dukanmu cewar Salim dake kwance bayar convertible ɗin shida Tariq yayinda Jalal ke driving Labib ke zaune mazaunin me zamar banza.
"Salim yaci gaba da faɗin" Guys mu ɗan bi ta gefen can rafin I knw it will be awesome....."Gajeren tsaki Labib yayu sanda Jalal ya karyi kwanan rafin da gudun gaske..... Ihu Tariq da Salim sukayi suna shewa alamun suna cikin farin ciki yayinda Jalal ke tayasu....."Will shut up for heavens sake, haba... Cewar Labib da gaba ɗaya ransa a jagule yake sabida gani yake shikenan bazai samu Kausar ba ta kufce masa.
"Guy chill up muna celebrating ne, cewar Salim. Tsaki Labib ya kumayi kafin yace" What's even awesome in this place, this place is sucks dont you see it. Ever since I came to this town nake fama da rashes a jikina for heavens sake i dont even knw who the heck came with the idea a zo nan garin ayi engagement..... Ni idande a nan garin za'ayi ɗaurin aurenka believe me I wont attend your wedding don wllhi na gama zuwa garin nan.
"Tariq yace" Guy chill pills we wunt stay long here, besides nan shine mahaifarku...."Ɗan tsaki Labib yayi kafin yace" Meyasa tuntuni basa zuwa garin sai yanzu sabida suna neman wani abi a wajen ƴan garin sabida a nuna a Network labarun tara cewa Alhj Tahir Marafah yazo garinsu yayi engagement ɗin tilon ƴarsa, people will be thinking sabida Allah yayi hakan amma mu munsan sabida buƙatarsa yayi don yaci takaran shugaban ƙasa....."Enougj of this Labib, Salim ya dakatar dashi kafin yaci gaba da faɗin" Inlawn nawa kake faɗin horrible things akansa you need to watch your mouth buddy.
"Murmushi Labib yagi a daƙile kafin yace" And who cared if he's your inlaw, gaskiya ne dole a faɗe ta, nasan Uncle shi ya ya basa wann shawaran don nasan Alhj Tahir is a responsible mutum bai iya ƙaryar ƴan siyasa ba....." Kan yayi shiru saiji yayi Salim ya cakumu wuyarsa yana faɗin" How dare you say those things to my very own father,..... Kan kace me faɗa na ƙoƙarin kufcewa ysakanin Labib da Salim..... Sai sn Jalal da tun fara cecekucensu bai tofah uffan ba dama sun san miskilancinsa sun san bazai ce dasu komai ba don ya saba, burki yaja ya tsaya tsakiyan hanya ƙiiiiiiiiiiiiiiittttttttt" Gaba ɗaya saida suka jirkita. Juyows yayi yana watsa masu kallo kafin yace" Let me know if u done... Daga haka bai kuma cewa komai ba. Tariq ya fuzar da iska kafin yace" Guys pls lets not ruin our day, besides bai kamata kuna haka ba, this is childishness you're all matured enough, snn abinda gayika Labib shi yayi Salim, we are all here because of you guys, what will you expect us to feel idan kuna abu makamancin wann a gabanmu nida Jalal, ku tuna we arr all friends and we love each other like brothers, pls lets not ruin this special moment especially you Salim this part of your wedding the beginning of your happiness lts chirrr it pls.
"Murmushi Salim yayi kafin yace" Yeah Buddy you right i shoudnt hve done that, ya kalle Labib kafin yace I knw why my cousin is acting this way sabida nan babu ƴan matansa i'm right.... "Sai snn sukayi murmushi su duka gaba ɗaya harda Labib ɗin ya ɗan daki kfaɗun Salim yace" Sorry Bro for been mean to you...." Its okay Buddy Salim ya faɗi da murmushi saman fuskarsa. Sai snn Jalal yaci gaba da Driving.
"Tsaye take bakin rafi saniyarta tana shan ruwa yayinda ita kuma Zubaidar keta faman tsane rigarta da ya jiƙe shaƙaf da ruwa sakamakon ruwan da aka tsulala, tafiya mai ɗan nisa ne daga wajen rafin zuwa cikin gari shiyasa har ƴanzu Umar bai zo ba, so take ta tafi amma tana tunanin kar ta tafi yazo bai sameta ba ransa ya ɓaci, don ita kanta tsoron ɓacin ransa take sabida zuciya da yake dashi, don haka dole ba don taso ba taci gaba da tsane kayan duk ya kakkame jikinta shape ɗinta ya fito sosai.
"Gama parking ɗinsa keda wuya idanunsa suka sauƙa kanta, baiga fuskarta ba sai bayanta, shi tunda Allah ya haliccess zaice bai taɓa ganin mace mai kyawun sura irin ta wnn yarinya ba, haka kurum yaji ya ƙagu ta juyo yaga fuskarta, Su Labib daketa faman selfie basu ko lura dashi ba, Saida Salim ya taɓosa kafin suka hangi abinda ya hango, sai faman tsane rigarta take ko kaɗan batasan akwai wasu halittu a wajen ba bayan ita da saniyarta......" *God have Mercy* Cewar Labib cikin sandarewar murya yayinda su Salim da Tariq suka kasa furta koda kalma guda,.. Haka kurum Jalal yaji baison kallonta dasuke, dukda shi tantirin ɗan iska ne wajen hulɗa da mata amma ko kaɗan yau ji yayi bai son su kalle wann yarinya da har lokacin bai ga fuskarta ba......
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:09] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
08
*©Sameena Aleeyou....✍🏾
_Queen Samy Novels Forum.... 📖📚_
"Cikin sauri Jalal ya tada motan ganin abokan nasa basu da niyyan daina kallon budurwan nan, jin ƙaran mota yasata juyowa babu shiri cike da firgici da tsoro...."
"Gaba ɗaya suka bi kyakkyawan fuskarta da kallo, Zubaidah ta razana matuƙa da ganin irin waɗan nan samari, bata taɓa ganin mota irin tasu ba snn yanayinsu yasha banban da samarukan garinsu, sunfi kama da taurarin cikin shirin wasan kwaikwayo wato film.... Cike da tsoro da firgici ta shiga tare jikinta da hannayenta....." Kaman wanda aka tsinkara haka Jalal yaja motar da ƙarfin gaske suka bar wajen, gaba ɗaya sai chaaa suka masa meyasa zai masu haka, meyasa bai bari sunyiwa yarinyar chan magana ba.. Salim ya murmusa a fili yace *"Cow Girl"* She's very beautiful I've never seen a beautiful girl like her before my whole life, cewar Tariq... Labib kuwa cewa yayi " I already have that imagination me and her on my bed making love together...... " Bai gama rufe baki ba Jalal yaja wata shegiyar burki a tsakiyar titi, sa'an su ɗaya babu mota a bayansu dan kuwa shakka babu da sun bigi juna.
"Mugun kallo Jalal ke watsa masu yayinda suma suka bisa da kallon mamaki, yana huci yake faɗin"
" Dont mess with her, I perfectly well know you guys, dont you dare hurt her....."Dariya Labib ya kwashe dashi kafin yace" Man nasan fah duk cikinmu nan babu wanda ya kaika son morewa da mace so I believe kaima da zaka samu mace kamar wancan yarinyar ta ringa ɗebe maka kewa I'm sure da garin nan yafi maka daɗi.....Salim yayi saurin cewa " Wait why you do you even care? Naga baka taɓa yin irin haka ba koda ƴammatan ka muka nema.
"Jalal ya ɗago ido yana dibansu one by one kafin yaci gaba da faɗin" Salim you are getting married soon ya juyo ya dubi Labib da Tariq kafin yace ku kuma I'm quite sure babu me sonta tsakani da Allah cikinku....." Bai ida ba Labib ya tuntsure da wata dariya kafin yace" For Gods sake Jalal ya kake haɗamu da wann low class chick ɗin kiwo fa take could you even imaging. Com'on Dude a bar wann zancen dukanmu dai muna son jikinta ƙuma kaima nasan kana so...." Wani mugun kallo Jalal ya watsa masa kafin yace" Kaima kasan duk neman matana bana neman yara kaman wann yarinyar don bazan taɓa lalata rayuwar ƴar kowa ba, duk ƴammatan da nake hulɗa dasu kasan matured babes ne daga waɗan da suka girmeni ne sai sa'anni na I see no reason da zai sa na lalata rayuwar ƙaramar yarinya wanda kamata yayi ace tana school kaman wann yarinyar. Nidai na faɗa maku dont mess with that girl, daga haka ya fincike mota suka ci gaba da tafiya.
"Har lokacin jikinta rawa yake don tana tuno sautinsu sanda suke faɗin " Hi chick, you beaitiful kasancewar tayi karatu har zuwa aji uku na matakin sakandare yasa ta gane wasu dga cikin kalmomin da suke faɗi da harshen turanci, haka kurum taji ta tsnesu ko kaɗan bata taɓa ganin mutanen da ta tsana irinsu ba dukda kyawun hallita da suke dashi... Babu shiri ta kaɗa saniyarta ta soma tafiya don gani take kaman zasu dawo.
"A daidai bakin kwalta ta haɗu da Ummaru, ganin yanayinta yasa shi ɗan razana, don gaba ɗaya a figice take.
" Surbajo na yaya dai lafiya ya tambaya yana ƙoƙarin kota maya saniyar, ɗan langaɓe kai tayi cike da yarinta take faɗin" Ba kaine kaƙi zuwa ba gashi ruwa ya min duka.
"Ɗan murmushi Ummaru yayi dama yasan hakan ka iya kasancewa. Haƙuri ya soma bata yana lallashinta har ta haƙura kafin ya sako zancen tafoyar da zaiyi nan da kwana biyu.
"Take idanun Zubaidah suka yi raurau, ƙwalla ya ciko idanunta, kaman me shirin kuka take faɗin" Yanzu shikenan tafiya zakayi ka barni...." Nan da nan yaji babu daɗi rausayinta ya cikasa, sandar hannunta ya karɓa kafin yace" Zubaidah ɗago ki kalleni, da ƙyar ta iya ɗagowa tana dubansa, Ummaru yaci gaba da faɗin" Ba jimawa zanyi ba sayi guda kacal zanyi, Shanu zamu kao chan jihar Lagos, na maki alƙawarin bazan wuce sati gudan nan ba. "Turi baki ta kumayi cikin harshenta na fullanci take faɗin" Nide da ka bar wann tofiya mu zauna kawai abinmu. "Umar yayi murmushi yana jin daɗin zance da ita yarintarta da ƙuriciyarta na birgesa, "
"Kinga kuɗin aurenmu zanje nemowa, ko bakiso ayi auren ne....."Tuni tasa tafin hannunta ta rufe fuskarta dashi alamun kunya, mirmushi kawai yayi kana suka ci gaba da tafiyansu suna hiransu gwanin ban sha'awa..
***************************
"Hankalin Annah ya gaza kwanciya, haka kurum take jin mummunar faɗuwan gaba, tana jin gwara ta kasance da Jalal ɗinta don kuwa ziciyarta tana raya mata mummunan tunani sarara, tasan tabbas taje Dukku da yawa daga danginta zasu gujeta, don haka bazata je wajensu ba ko taje, toh wajen wa zataje ta tambayi kanta, take tunanin ƙawarta Inna Wuro ya faɗo mata hakan kuwa za'ayi don tabbas su Lado sukayi ido huɗu da Jalal zasu iya ganesa kuma zasu faɗa masa komai.. Babu shiri Annah ta hau shiri ta nufi Dukku.
"Yaya Hadiza ce zaune saman tabarma sai karyan loman tuwo take tana jefawa baki kaman bata taɓa cin abinci ba, dama wann ɗabi'arta ce idan tana cin abinci kai kace wani zai wabce ne, jin sallamar aminiyarta Iyalle yasata saurin wurga kwanon tuwon bayan ƙyaure, nan ta shiga shage miyar kukan jikin rigarga kafin ta amsa sallaman Iyalle, tsegege Iyalle ke kallonta kafin ta taɓe baki tace" Meye kike ɓoye mun.
"Hadiza ta haɗe gira tace ban gane ba, kaman yaya me zan ɓoge maki, abinci na ida ci yanzun nan.....
"Taɓe baki Iyalle tayi kafin tace" Umhm ƙawata kenan sekace bansanki ba, keni ba wann ba labari nazo maki dashi na arziki da ɗumi ɗuminta. Tuni Hadiza ta kaɗe bujenta ta gyara zama, ina saurarenki.
" Iyalle ta zauna da ƙyar kafin ta ciro gudan ƴan dubu dubu cikin pose ɗinta ta goga su idanun Hadiza......
" Aiko baki sake Hadiza ke faɗin" Ƙawata ina kikayi babban kamu haka, " Iyalle ta murmusa kafin tace" umhm toh ki zauna a nan ke anayi banda ke.
"Ban gane anayi vanda ni ba, cewar Hadiza,
" Iyalle ta gyara zama kafin tace" Albishirinki idan kinson waɗan nan bugun habujan kema kina iya samu.
"Hadiza anji zancen arziki tuni ta miƙe ƙafafu tana faɗin ƙawata ina daurafenki wazaiƙi masu gidan rana ai sede bai samu ba.
" Iyalle ta mutmusa kafin tace" Ai kindaiji labarin zuwan su Alhj Dasuki da Alhj Marafa me neman kujeran shugaban ƙasa,.... Hadiza ta gyaɗa kai da sauri kafin tace" Ai ancema layin anguwan ba'abi duk sojojine a wajen suke tsaro. Wai idan muyum yabi wajen ke ko ƙwaronr yabi wajen sai an harbe sa
" Iyalle tace" Toh barikiji na faɗa maki sojoji dai suna tsaron anguwar amma basu hana mutane zuwa ba, ke yau na taƙaice maki ƙofar gidan tamkar kasuwa , a nan aka raba mana dubu biyar biyar duk wanda yaje babu babba babu yaro, inaga dai da ingin buga kuɗi ma suka taho don kuɗin baya ƙarewa.
" Haba idanun Hadiza sukayi wulli wulli taji kuɗi tuni ta wawuro ƙafar silipers ɗinta tana faɗin " Ƙawata tashi ki rakani, ... " Iyalle ta sheƙe da dariya kafin ta jawo Hadiza ta zaunar kana tace" Ƙawata ai kin makara na yau kam an gama. Hadiza rai ɓace take faɗin amma ƙawata baki kyauta min ba, ai aminta batace haka ba, ni duk yanda naga kaya mai kyau kafin wata dilalliya a garin nan ta sani sai na sanar dake ...."
" Iyalle tayi dariya kafin tace" Nima yau na sani da ƙyar su Dije suka yarda suka tafi dani kinsan suke aiki a gidan, toh a daƙilin haka na samu, sann da naji sunce suna neman ƙarin ma'aikata sabida hidiman da zasuyi na bikin ƴaƴansu nace bara na sanar dake kema ki samu, kinga sai ki tafi da wnn aljanar ƙanwar mijin taki tunda naga ta iya kala kalan abinci ko yaya kikace.
" Hadiza harza buga tsalle don murna kafin tace" Kai gaskiga ƙawata kin burge, kin kyauta min, aiko dolenta ma taje kinga nayi riba biyu ga kuɗinta ga nawa...... Dariya sukayi gamida tafe hannaye suka ci gaba da hiransu, kafin Iyalle ta tafi akan sai sun Haɗu.......
" Momyn Salim ce keta faman kaikomo yayinda ma'aikata suke take mata baya sai nuna yanda take so wajen da za'ayi event ɗin tsarin ya kasance, mussaman suka taho da masu tsara wajen daga Abuja, Annah ta dubi momy tace" Hajiya idan babu wani aikin zan wuce masauƙi. Momy ta murmusa kafin tace" Haba Annah ai gwara ki zauna a nan, ni banyi zaton jikin naki zai sakeki ki samu zuwa ba, snn wann biki fah na Salim ne kinga kuwa ai yakamata a soma komai dake.
" Annah ta murmusa kafin tace toh shikenan Hajiya yanda kikace.
"Isowan su Zubaidah kenan cikin kataparen gidan, daga ita har Yaya Hadiza kallo suka bi gidan dashi ko a mafarki basu taɓa shigowa gida irinsa ba, nan da nan Iyalle ta gabatar dasu ma Dije, Dije sai wani yauƙi take tana masu tambayoyin ƙaƙa uwaka ta haifeka irin ta smi matsayin nan, da ƙyar da roƙo dai ta yarda ta amince ta kaisu gaban momy a matsayin extra ma'aikata da aka ɗauka. Daga nan kitchen suka wuce suka soma aiki babu kama ƙafan yaro.
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:09] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
09
*©Sameena Aleeyou....✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
"Balele nifa kaga irin abinda bana so muzo muna ƙoƙarin kutsawa da ƙyar ɓa don Zubaidah na wajen nan ba wlhi babu abinda zai kawo ni, Cewar Umar dake tsaye gefen Balele suna ƙoƙarin kutsawa cikin gidan da ƙyar.
"Ko saurarensa Balele beyi ba sai fizgo hannunsa da ya samu yayi suka shige daga kansu kuwa aka kulle gate.
"Can gefe suka samu suka zauna sai kalle kalle suke irin ƙyale kyalen dake a wann gida, darene amma tamkar rana sabida yanda wutan lantarki ya gewaye ko ina, mutane sai kai komo ake.
"Momy da Mamin Labib ne tafe suna haƴewa bene yanda baƙinsu suke yayinda Zubaidah ke take masu baya hannunta ɗauke da tray, sai kalle kalle take tana mamakin dama akwai gidaje masu kyau da tsari irin wann a garinsu, kai idan aka ce zata taɓa shiga gida irin haka a rayuwarta zata musa.
"Suna Mami ta mata umarni ta ajiye. Nan tabi umarnin Mami ta ajiye ta nufi ƙasa, nan ne fah ta ɓata a hanya, don kuwa wann girma gida dole ma mutum ya ɓata musamman irinta da bata taɓa shiga irin gidan ba.
"Hanyar da ta miƙe dama nan tabi, sai wage waige take, gashi abinda yafi bata mamaki shine wann hanyar yayi shiru da yawa, anya nan suka biyo dasu Hajiya kuwa, haka dai taci gaba da tafiya har ta hangi stirs da sauri tayi wajen ta soma sauƙowa.....
" Bata ankara ba saiji tayi ta bugi jikin mutum, kallon kallo suka shiga yima juna, haka kueum taji gabanta yayi mugun faduwa snn ta rasa a ina tasan wann fuska, shi kuwa Jalal kasa daina kallonta yayi, haka kurum yaji ya tsinci kansa cikin farin ciki,.... Murya na rawa ta soma basa haƙuri.
"Dan Allah kayi haƙuri wllhi bansan da mutum bane, kayi haƙuri kaji yallaɓai kar ka sa sojojinku su harbeni......" Jalal kam dariya taso basa ganin duk yanda ta daburce, is Okay is Okay... Ya faɗi fuskarsa ɗauke da murmushi kafin yace zo ki wuce, da sauri ta raɓa ta gefensa ta nufi downstirs,
"Har ta kusa sauƙa Jalal yace" Emm ina zakije.
" Cikin sauri tace dashi sashen ma'aikata. Ɗan murmushi yayi mai bayyana dimpls ɗinsa kafin yace" I think Ƴou miss the way, kallonsa tayi ba tareda tace komai ba don kyaun halittarsa na firgita ta tamjar ba mutum ba haka take dubansa musamman da yayi murmishi.
"Ganin tayi sakare tana dubansa yasa yin wani murmushin kafin yace "muje na nuna maki, babu musu tabi bayansa, har ƙofan da zai fitar da kai BQ ya fito da ita,.... Da sauri ta nufi ƙofan ba tareda tace dashi komai ba, "Jiyo daddaɗan muryarsa tayi yana faɗin" Baki min godiya ba.
"Ɗan juyowa tayi gamida masa godiya cikin harshen fillanci, Shima murmushin yayi ya amsa mata cikin harshen fillanci... Jin yayi mata fillanci yasata ficewa da sauri tana ƙunshe dariyan da yazo bakinta da hannunta don kuwa da kalman tsokana ta masa godiya shima kuma da hakan ya amsa. Itakam tafi bashi balarabe ko bature kwata kwata bata kawo bafilatani bane.... Har ta isa kitchen murmushi take....
" Wani uwar harara Hadiza ta watsa mata kafin tace" Ke murmushin me kike, snn meyasa kika jima daga kai abu kinsan aiki na jiranki. Kinje kin saki baki da hanci kina masu kallon ƙurillan da kika saba koh.
" A'a emm dama..... bata gama faɗin abinda zata faɗa ba Hadiza ta jawota da niyan jibganta.... Sauran ma'aikata sai ƴan gulmammaki suke, Annah ce ta shigo dama itace incharge na ma'aikatan tunda ta taho, da sauri ta ƙwaci Zubaidah daga hannun Hadiza tace" Haba baiwar Allah, ko me ta maki ai bai kamata kina dukan budurwa kaman wann ba, Hadiza dai bata ce komai ba sai hararan Zubaidah da take.
"Annah ta kalli Zubaidah gamida sakar mata murmushi kafin tace " Ɗauko karas ɗin chan kin fere min babu musu Zubaidah tayi yanda tace cike da girmamawa. Haka kurum Annah taji yarinyar ya burgeta ta shiga ranta lokaci guda...
" Tun shigowarsa ɗakin yake murmushi ya kasa ce masu komai sai murmushi. Salim dake tsaye cikin closet ɗinsa na shiryawa ango to be, ya kalli Jalal ta jikin mirror kaɗin yace" Whats up with you Buddy, you seems very happy, Murmushi Jalal ya kumayi gamida zama tsakanin Tariq da Labib da suke kan buga PS5..... Ɗaura hannayensa yayi bisa kafaɗunsu yana duban Salim dake tsaye closet kafin yace" Guys I just saw her, I saw her......
" Da mamaki suke kallonsa har suna haɗa baki wajen cewa" sawWho"???
" Kaman wanda ya tuna abu, murmushi yayi ya miƙe ya nufi ƙaramin fridge ɗin dake ɗakin ya ɗauko kwalban wine ya tsiyaya a cup ya kurɓa, Labib ya dara kafin yace" Guy wacece ka gani.
" Jalal yayi murmushi ya kuma kurɓan wine ɗin kafin yace "Never mind its just my imagination... "Dariya kawai sukayi sanda Salim ya ƙarasa shirinsa suka fito gaba ɗayansu suka nufi filin event wanda aka tsara shi kai kace a turai ne, .....
"Isowar su Kausar kenan fili ya kacame, Salim ya shagala da kallonta don kuwa tayi kyau har ta gaji, wata arniyar silver gown ta saka kai komai nata silver ne sai ta fito tamkar wata me zuwa gasar sarauniyar kyau.
"Idon Labib ya sauƙa kan Asmah wacce itama tasha gayunta cikin red gown tayi ɗauri irin na yayi da royal blue vail a kanta tayi kyau matuƙa, duk haɗuwan da suke bata taɓa masa kyau irin ta yau ba.
"Taro yayi taro nan da nan aka soma gudanar da Event.
"Zubaidah sai leƙe take ta windon kitchen tanason fita taga amaryar don taji anyi annoucing isowarta. Ta ɗan saci kallon yaya Hadiza kana tace" Yaya don Allah naje na kalli amaryar.....Wani uwar harara Hadiza ta watsa mata kafin tace" Bazakije ba don uwarki, shegiya me shegen son kallon tsiya, wann abu duk a kunnen Annah ya faru. Ɗan girgiza kai tayi dukda batasan alaƙan dake tsakanin Hadiza da Zubaidah ba ta tabbata Zubaidah tana shan wuya wajen Hadiza, ƙarasowa cikin tangamemen Kitchen ɗin Annah tayi ta dubi Zubaidah dake ɗaman leƙe ta window tace" Zubaidah kina son kallo ne.
" Da sauri Zubaidah ta juyo ta dubi Annah gamida kallon yaya Hadiza data sakar mata harara. Annah tayi murmushi don kuwa taga irin kallon da Hadiza tayima Zubaidah..... Baki na rawa Zubaidah tace " a'a Annah ban ƙarasa haɗa waɗan nan parantan ba.
"Annah ta murmusa kafin tace kar ki damu zo muje ki kalla, juyawa Annah tayi ta dubi Elizabeth ɗaya daga cikin ma'aikatan da suka taho dasu daga Abuja masu uniform kana tace" Elizabeth continue with the plates arrangement" Elizabeth ta amsa da Okay Ma.
"Duk sunsha mamakin jin Annah na turanci harta Zubaidah saida tayi mamakin jin Annah tana turanci... "Hannunta Annah ta riƙe suka nufi farfajiyan gidan yanda ake gudnar da shagalin.
"Tun fitowarsu idanun Jalal ya sauƙa kansu, yasha mamaki sosai ganin Annah tare da Zubaida riƙe da hanun juna har suna magana. Toh dama Annah tasanta ne, toh a ina tasan ta??? Kasa samo amsar tambayoyin nasa yayi.
"Salim dake rawa da bride to be ɗinsa idanunsa suka sauƙa kan Zubaidah, kallon ta yake da mamaki, a hankali ya furta *"Cow Girl"* me take yi a nan.???
" Ɗan sunkuyowa yayi saitin kunnen Kausar kana yace" Sweetheart barin je wajen su Labib I'll back in some minutes.
" Kausar ta murmusa kafin tace" No prblm Dear take ur time. Satan idon mutane yayu gamida manna mata kiss a kumatu...."Zari ido waje Kausar tayi tana dubansa, harda wani kashe mata ido guda kafin ya wuce.
" Asmah ta taso da sauri tana dariya, a daidai saitin kunnen Kausar take faɗin " Girl I saw that, lallai wann angi naki za'a sha fama, nide kar aje ana kiran mumsy da Papy suzo su kawo.ɗauki, Hararan wasa Kausar ta watsa mata gamida riƙo hannayen Asmah suka soma yin rawan a tare.....
"Salim yana ƙarasowa table ɗinsu ya samu zancen cow girl suke dun babu wanda yasan sunanta cikn su, as usual Jalal yana warning nasu. Caraf idanun Jalal suka haɗu dana Annah, alama ta masa da hannu kan yazo.
"Su Salim suka dubesa suna murmushi ƙasa ƙasa suke faɗin yaje ƙila Annah tasnta ne. Zubaidah kuwa tana ganinsu a tare a haka, ta tunosu ta tuno yanda ta gansu bakin rafi, faɗuwar gaba ta tsinci kanta dashi..... Tana cikin tunanin ta jiyo nuryar Annah tana faɗin" Zubaidah barin yi magana da yarona, gyaɗa mata kai kawai Zubaidh tayi ba tare da tace komai ba, har lokacin ƙirjinta na bugawa musamman da Labib ya ɗago mata hannu tare da kashe mata ido guda.
"Ɗan matsawa gefe Annah tayi itada Jalal tana masa magana amma idonsa da hankalinsa gaba ɗaya suna kan Zubaidah......
" Daga yanda suke zaune can baya shida Balele ya hangeta sai faman rarraba ido take, ya kuma duban Jalal daya kafe ta da idanu, yaga sanda suka sakar wa junansu murmushi..." Take gabansa yayi mugun faɗuwa Da sauri ya miƙe ya nufi yanda take.
" Saida ta razana da ganin Umar don batayi zaton zata gansa a nan ba.... Juyawa yayi sukayi ido huɗu da Jalal, Jalal yayi saurin kauda nasa kan gefe.
" Fuska a tamke tana gaishesa ko amsawa baiyi ba ya soma faɗin" Wanene wancan saurayin da kike masa murmushi.
"Ido ta zari tana dubansa kafin tayi magana a zuciye yake faɗin" Naga irin kallon da yake maki, ke bakisan yaran masu kuɗin nan ba koh, waima har yanzu aikin uwar me kike da bazaki tafi gida ba,..." Kasa cemasa komai tayi sai kallon data busa dashi, kishinsa yayi yawa bacin bata ga laifin datayi a nan ba ko ƙwara.... " Umar ya kuma hasaƙa ganin tai masa biris,...." Bata gama tunanin da take ba ta jiyo muryarsa naci gaba da faɗin" Wani gulmar ne ma ya fito dake nan keda kike aiki a kitchen, Okay dama kallon maza kikazo yi, fine kici gaba. Yayi maki kyau, ni zan wuce lagos gobe da asubahin fari. Idan kinga dama ki bar wajen nan as soon as u can. Daga haka bai kuma cewa komai ba ya wuce fuuuu, Ko sallama da Balele bai samu zarafin yi ba ya fice abinsa.
" Labib ya dubi Salim da Tariq kafin yace guys ku kwantar da hankalinku ni nasan maganin Jalal, kan wann ƙazamar talakan yarinyar zai nemi raina mana hankali, muna buƙatan jikinta kuma dole mu samu bamu taɓa neman abu mun rasa ba so bazamu fara yau ba.
"Jalal na isowa suka sakar ma juna murmushi, farin ciki yakeji na ganin wann yarinyar, baisan me yakr ji gameda ita ba amma tabbas yana jin wani abu.
"Labib ya sunkuya ƙasan table ya ciro waɓi ƙwaya a aljihinsa ya tsiyayi drink a cup ya jefa a ciki. Hankalin Jalal gaba ɗaya naga neman ta ina ,ubaidah ta koma don bai ganta ba kuma. Be kawo komai a ransa ba ya karɓi drink ɗɗin ya soma sha, nan ya soma jinsa a sama, nan suma suka biyesa kaman suma a bugen suke, Salim ya miƙe ya nufi yanda Kausar da ƙawayenta suke yace mata " bara suje su ɗanyi freshing up dasu Labib, Kausar bata kawo komai ba tace dashi sai sun dawo take care. Kiss ya hura mata kan tafin hannunsa kafin ya wuce" ƴammata ƙawayenta suka ɗauki shewa, cewa suke wow Kausy tayi sa'an miji mai sonta snn romantic guy. Kausar kuwa sai jin kanta take mai sa'a a cikin mata.
"Zubaidah kuwa sauri sauri ta nufi hanyar fita amma bata cimma Umar ba, ko kaɗan bata son fushinsa, gashi tafiya zaiyi gobe gobe kuma gari mai nisa, itakam bazata so suyi irin wann sallama ba, cikin sauri ta nufi titi tana nemansa, abinka da yarinta ko tunawa da darene batayi ba ga yanayin anguwar babu mutane sosai gini ma can ɗaiɗaiya kake hangowa.snn ko tunawa ta faɗawa Annah batayi ba. Haka Annah tayi neman duniya bata ganta wajen taron ba eata zuciya tace ƙila ta koma kitchen.
"Haka su Labib suka ja Jalal suka nufi cikin mota dashi, suka fice.... " Zubaidah sai faman shate hawayen fuskarta take tana bin salɓalelen titin nan ƙarshe har ta ƙarasa ƙarshen layin yanda babu kwalta, nan ta soma tunanin anya ma ba ɓata tayi ba, tsoro dafirgici suka shigeta, nan take ta soma ƙwalla kiran sunan Umar tana wani sabon kuka,... Daga yanda suke suka jiyo sautin ta, tuni Labib ya karya kan mota suka nufi wajen.... Zubaidah na hango fitilan mota ta nufota ta soma ja da baya, tuni Labib yayi parking suka fito gaba ɗayansu.... Kan kace me sun gewayeta, kallonsu take tana ƙoƙarin ja da baya amma sai taga wani a bayan nata, idan rayi nan gefen sai wani ma ya tarota.... Duk wani addu'an da ya,o bakinta yinsa take, cike da tsoro da firgici cikin murya irinta me kuka take faɗin" Don Allah kar ku cutar dani, su waye ku meyasa kuke bibiyata......" Bata gama yin shiru ba taji Jalal ya rungumota cikin muryar maye yake faɗin" here she is......" Wani irin ihu Zibaidah ta sake tana mai ƙanƙame jikints, Jalal kuwa da su Labib dariya suka fashe dashi, Jalal yana dariya yana tangaɗi ya ɗora ɗan yatsansa akan bakin Zubaidah yana faɗin" Shiiiiiii, har loƙacin tana rungume cikin hannayensa, Kuka take kaman ranta zai fita, Labib ya ƙaraso gamida fizgeta hannun Jalal.......
" Dukda ba a cikin hankalinsa take va da ƙyar Labib ya iya fincike Zubaidah daga hannunsa, cikin muryar maye yake faɗin" Don't Labib dont you date think of doing that,........" Yana faɗuwa yana tashiwa da ƙyar, su kuwa su Salim da Tariq me zasuyi banda dariya,.........
"Ihu Zubaidah tayi sanda su duka uku suka nufota, Saalim Labib da kuma Tariq, Labib ya basu umarni dasu banƙare masa ita, hakan kuwa akayi, Jalal babu yanda ya iya ƙwayan da Labib ya basa ya hanasa taɓuƙa komi k motsi me kyau ya kasa balle ya tashi,
"Allah sarki, haka tanaji tana gani tana roƙonsu tana kuka basu fasa ƙudirin da sukayi niyya akanta ba, Tariq da Salim suka banƙareta ta hanyar rirriƙe mata hannaye, Labib yasa hannu ya kama tun daga wuyar rigarta ya keta daga sama har ƙasa, gaba ɗaya ruɗewa suka yi sanda na shanunta suka bayyana wanda suke a cike manya manya a tsartsaye, tuni Labib yakai masu capka kaman tsohon haka ya ringa wasa da albarkatun ƙirjinta su Salim na tayasa ƙarshe chaa suka mata akai su duka uku kowa nason ya fara biyan buƙatansa, ta yunƙura zata tashi Labib ya kifa mata mari. Bige bige take kamar mahaukaciya ta kuma yunƙura Salim ya danneta, Labib ya jawo wani duysi ya buga mata a ƙafa, tuni ta saki ƙaran azaba, haka su Tariq da Salim suka banƙare ƙafafunta suka rabata da suturanta,.....Wani ihu mai ƙarfin gaske ta sake sanda Labib ya shigeta, gaba ɗaya ba zuwan wasa ya mata ba, tunda Zubaidh tayi wann ƙaran bata kuma sanin yanda kanta yake ba.
"Haka Labib yayita gurzanta babu tausayi balle imani, saida yayi mai isansa kafin ya miƙe Salim ya soma, shima saida yayi iyaka yinsa kafin Tariq ma ɗora da nasa, haka sukayi ma baiwar Allah nan kaca kaca babu imani babu tausayi valle tuna mahaliccinsu 😭......
Sameena.ce👌🏾
[1/23, 22:10] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
10
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
" Komawa gefe sukayi suna maida numfashi, Tariq ya dubi Jalal dake kwance gefe alamun bacci yayi gaba dashi tuntuni, Dariya ya fashe dashi kafin yace" Guys lets get going kafin wani ya ganmu.
"Salim ya busar da iska kafin yace" Ban taɓa jin mace me daɗinta ba, shes so sweet I wish I could have her everyday...." Labib ya miƙe da ƙyar yana maida belt ɗin wandonsa kafin ya nufi mota ba tareda yace komai ba, jin har ya tada mota yasasu saurin ɗauko Jalal suka saka sa cikin motan, Tariq yakai dubaɓsa ga Zubaidah wscce ke kwsnce lifeless tamkar maras numfashi kafin ya dubi abokansa yace" What about her? Are we gonna leave her here???
"Tsaki Labib ya buga kafin yace" Dude idan zaka shiga mota mu tafi ka shiga what next, badai ka biya buƙanta ka ba me kuma yayi saura..." Tariq ya ɗanyi jimm kafin yace" Com'on guys we can leave her here lifeless she almost died...." Cike da ƙosawa Labib yace" If you cant leave fine, ka tsaya idan police suka kama ka da dead body sai ka masu bayani, kokuma Dad ɗinka ya ganka da ita kaga he'll definitely be proud of you huh??
" Salim ne ya riƙo Tsriq suka wuce mota yana faɗin" lets go Buddy I dont think that girl is still alive.
"Labib kuwa kaman jira yake suna shiga ya fincike motar......
" Har aka gama event babu Zubaidah babu dalilinta , Neman duniyar nan sunyi basuga Zubaidah ba, Ƙarshe dai Hadiza ta wuce gida da tƴnanin ko Zubaidah ta koma gida..
"Hadiza ta cika tayi fam sai banbamin masifa da bala'i take" wllhi yau Zubaiidah sai na kusan kasheki a gidan nn..." Hamma Habibu sai faman bata haƙuri yake yana faɗin" Kiyi haƙuri Hadiza zata dawo ne, Kamalu ya ƙaraso ya rungume babansa yana kuka yana faɗin shidai yana son ganin Didinsa.. Rungumesa Habibu yayi suka soma kuka a tare. Wani takaicin ya kuma tokaran Hadiza, ficewa tayi waje ta barsu sunata sharɓan kuka.
"Mami ta kuma kallon momy datayi jugum duk suna jiran dawowan ƴaƴansu kafin tace" Anya Farha bazamu sa securities neman yaran nan ba, what if simething bad happens to them, nan ƙaramin gari ne ba kaman Abuja ba da suka saba fita suyi dare, nan babu wani wajen zuwan da har zasuyi dare a wajen, they should be home by now...."Momy ta matso ta rungume Mami kafin tace" Its Okay Mami I know they'll be home soon,.....
"Dammit dammit those boys will never change... Cewan Alhj Kasim cike da ɓacin rai, duban Barr Munir yayi kana yace" Keep on trying their numbers, daga haka miƙewa yayi ya fice zuwa waje...
"Su Salim kuwa basu suka shigo gidan ba saida suks tabbata kows yayi bacci, cikin sanɗa suka wuce sashensu, gaba ɗaya suka zube a parlor suna maida numfashi.
"Kaman daga sama sukaji an banko ƙofan an shigo... Daddy ne tsaye yana binsu da mugun kallo,
"Salim da Tariq kam tsoro ne ƙarara ya nuna a fuskarsu yayinda Labib ke binsa da mugun kallo shima.
"Where the hell have you guys been??? Dady ya tambaya fuska babu alamun wasa,...
"Labib ya miƙe yana ɓalle buttens ɗin rigarsa kafin yace" Uncle would ƴou pls stop, why ate you asking us like we are still kids, ya kamata ka gane mun girmafah yanzu we can decide our life.
"Daddy ya fuzar da iska kafin yace" I see, I see. Ya sauƙe dubansa kan Salim da yayi zuru kamanai tunani kafin ysce" And where is your engagement ring. Sai snn Salim ya duba yatsan sa yaga tabbas babu zoben da Kausar ta saka masa ɗazu wajen engagement. Ɗan shafa kai yayi kafin yace" Com'on Dad I lost it. I'll by another one.
" We must talk gobe kunaji na, cewar Dad, daga haka sa kai yayi ya fice zuciyarsa na ci gaba da tafarfasa...
*Washe gari*
" Asubahin fari Hadiza ta fice ta nufi gidan Alhj Kasim, don izuwa lokacin itama ta soma shiga damuwa,. Hamma Habibu kam ko bacci bai sami zarafin yi ba haka ya kwana kuka, idan Kalmalu ya farka a bacci ya tayasa
"Securities kuwa sam sunƙi barinta ta shiga gidan, sai faman bambamin masifa take...."Anna dake tsaye ta back yard ta jiyo sautin Hadiza, aje bokitin hannunta tayi da sauri ta nufi gate..
"Hadiza na hangota ta nufota itama cikin sauri tana huci take faɗin" Wllhi kece, kece kikace tazo ki kaita ganin amarya, yun daga lokacin ban kuma ganinta ba. Annah ta riƙo hannunts kafin tace karkiyi magana haka, nida ke duk munsan tun jiya muka nemi Zubaidah wajen bikin nan, keda bakinki kikace gida ta tafi anyi haka ko ba'ayi ba. Snn naga kalan taƙura yarinyar da kikeyi, wnn kaɗai kan iya sa yarinyar ta tsere ma azabarki ƙila ta gaji da wahala da azabtar da ita da kike ne, ko gaban hukuma akaje dole ki bada wann statement ɗin... Haba nan fah Hadiza ta soma borin kunya musman dataji Annah na mata turanci,... Can kuma hawaye suka ciko idanunta ta dubi Annah tace don Allah ki taimaka min bansan yanda zan sameta ba.
" Annah ta sauƙe ajiyan zuciya kafin tace" Kinga yanzu ƙarfe shidan safiya masu gidan nan basu tashi ba balle nakai ƙoƙon taimakona garesu, Amma yanzu abinda zamuyi mubi layin nan muna tambaya muna nemanta wataƙila Allah zaisa mu dace. Babu musu Hadiza tabi bayanta suka bazama neman Zubaidah.
"Har ƙarshen layin suka isa babu ita babu alamunta, gashi basu haɗu da mahaluƙi ko guda ba balle su tambaya.
"Har zasu juya Annah taji kaman tayi tuntuɓe da mutum cikin ciyawa, aiko tana sunkayawa ta ganta kwance cikin bushesshen jini kaman an yanka dabba, gwiwoyin hannayenta da ƙafafunta gaba ɗaya ta kukkuje kai kace da kate tayi faɗa, ƙofan hancinta jini ne shima ya bushe, haka nan an ɗaure bakinta da farin ƙyalle, goshinta ma jini ya bushe alamun anji mata ciwo.....
"Annah bata san sanda ta durƙushe a wajen ba gamida fashewa da wani irin kuka wanda hakan yaja hankalin Hadiza,... Tana isowa wajen taga abinda Annah ta gani.
" Tsugunawa tayi a wajen dirshan, duk rashin imanin Hadiza da wulaƙanta Zubaidah da take yau saida taji tausayin Zubaidah...."Baki na rawa Hadiza ke faɗin " Fyaɗe aka mata, sun mata fyaɗe.... Wani sabon kuka ya kufce mata.
"Annah tayi saurin saita kanta kafin ta cicciɓi Zubaidah da ƙyar, ta dubi Hadiza tace" Maza ki koma can gidan kice ni na aikoki ki kira min ɗana Jalal kinga ban fito da wayata ba,shi zai taimaka ya taho mana da ƴan sanda don nasan da ƙyar asibiti su karɓemu babu jami'an tsaro, amma yanzu barin fara kaita asibiti don ceto rayuwarta. Gyaɗa jai jawai Hadiza keyi hawaye na zuba idanunta, tana tunanin yau Habibu yaji ko yaga wann zance tabbas sai ya kusa mutuwa, cikin sauri ta juya yayinda Annah ta wuce bakin titi neman adaidaita.
" juyawan da Hadiza zatayi taji ta taka wani abu kan ƙarfe, sunkuyawa tayi ta ɗauko abin, shakka babu zobene size ɗin hanun namiji, kuma da gani yaji kuɗi zai tsada, sakawa bakin zaninta tayi ta ƙulle kafin ta soma tafiya.....
"A hankali ya sima buɗe idanunsa da suka masa nauyi, da ƙyar ya iya moƙewa zaune gamida dafe kansa da hannayensa guda biyu yana son tuno me ya faru a daren jiya.
" Juyawa yayi ya kalli abokansa da suke kan sharan bacci babu sallah balle salati...."A hankali komai ya soma dawo wa Jalal....a fili ya furta *"Zubaidah"* Kaman wanda aka zabura ya miƙe abubuwan da suka faru suka shiga dawo masa kwanyansa, ya tuno sanda ya riƙota, ya tuno shi ya fara kamata, ya tuno sanda Labib ya fizgeta daga hannunsa, ya tuna sanda Labib ya keta mata rigarta, ya tuno sanda suke wawa akanta kaman almajiri yaga abinci....." Jiri ya soma kwasan sa, Wani wawan ƙara ya sake wanda saida ya tashi duk wani mahaluƙin dake barci cikin gida.....
*"NOOOOOOOOOOOO"*
"Ya faɗi da ƙarfin gaske, gaba ɗaya suka miƙe babu shiri suna dubansa, Jalal ya ɗago rinannun idanunsa yana dubansu ɗaya bayan ɗaya, fuskan Labib yake kallo yana tuna sanda ya fara raba Zubaidah da mutuncinta dukda a lokacin yana ckin maye amma hakan bai hanasa ganin komai da fahimtar komai ba.... Tsalle yayu ya cikumo wuyan Labib ya shiga dukansa a ciki kaman Allah ne ya aikosa...yana faɗin" You raped her didn't you, you started it, you imbecile how dare you...... Da ƙyar Salim da Tariq suka ƙwaci Labib. Kukan kura ya kuma ya jawo Salim da hannu guda snnTariq da hannu guda ya daki ƙofar ɗakin ta buɗe ya nufo downstirs dasu haka ya ringa jansu a ƙasa kan stirs har saida ya fito waje........ Labib ya goge jinin da ya ɓata masa hanci kafin ya biyo bayansu a guje, daidai lokacin dasu Daddy su momy suka fito.......
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:10] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
11
*©Sameena Aleeyou....✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
*Shout Out to all the readers....😘😻*
"Cikin sauri Labib ya miƙe yabi bayansu. Momy da Mami a balcony suka haɗu kowa ta fito daga ɓangaren mijinta don suma sunji ƙaran da Jalal yayi, a tare suka nufo downstirs... Curus suka tsaya suna bin Labib dake sauƙowa daga ɓangarensu wanda gaban singlet ɗinsa gaba ɗaya jini ya ɓata.... Mami ta nufesa a kiɗime tana faɗin" Baby me ya sameka, ina ja samo jini haka. Ɗan tareta da hannu Labib yayi sai sauri yake ya nufi parlor yana faɗin" Mami its nothing pls ku koma baccinku we can handle this, pls kar ku faɗawa wasu Dad...."Muryasa ya carke sanda ya jiyo muryar Dad daga waje yana falfawa Jalal ruwan ashariya da masifa, Ai Labib kaman zai kife ƙasa haka ya fice daga parlorn ya nufi waje don sauri. A tare Momy da Mami suka rufa mai baya.
" Barr Munir ya cafe zancen da faɗin" Ai dama tsiyan ka sake wa talaka kenan, yanzu Alhj ka duba yanda yaron nan yayiwa yaran nan snn kaji yanda yake mayar maka da magana tamkar wani sa'ansa..... Shiru yayi sanda ya hangi ƙanwarsa Hajiya Farha na fitowa waje,... Ƙarasow Momy tayi taga fuskan Salim duk a daddauje alamun an lakaɗɗesa.
"Boy who did this to you, Momy ta biɗa sanda take shafa fuskar Salim. Alhj Kasim ya dubesu itada Mami kana yace" Farha ku shige gida....." Idanun Momy ya sauƙa kan Jalal dake riƙe da sanda alamun shi ya jibga masu yara, ai a tamanin tayi kansa tana faɗin "Dama wnn shegen ne ya dakeku kuka ƙyalesa dashike ku saunaye ne....." Da sauri Dad da Barr Munir suka riƙota suka hanata ƙarasawa ga Jalal dake tsaye a wajen ko gizau baijiba da alama, banda huci babu abinda yake...
" Barr Munir ya jiyo ya dubi Jalal kana yace" Yanzu kai Jalal abinda zakayi kenan, mutanen da suka ɗaukeka tamkar ɗan uwa shine ka rasa sharrin da zaka laƙaba masu sai na fyaɗe, toh da kasan son yarinyar kake ai ba sai ka mata fyaɗe ba da nemanta da aure kayi da yafi maka.
"Jalal yayi murmushin takaici yana duban Barr Munir a hankali ya tako ya ƙaraso hat gabansa" Ido cikin ido suke duban juna kafin ya soma faɗin" Barrister bari kaji na faɗa maka, nafi ƙarfin na ɗaurawa su Salim sharri wllhi snn idanakwai waɗanda zan ƙulla masu sharri a wann rayuwa toh badai su Salim ba, sabida ƴan uwa na ɗaukesu inaga dukda dangantakar dake tsakaninku dasu nafika sonsu snn duk neman matan da mukeyi bazan musa maka ba a tare mukeyi snn da kake cewa son yarinyar nake shiyasa na mata fyaɗe kayi kiskure Barr sabida ni a tsarin bin mata na babu fyaɗe gasu nan ka tambayesu, snn koda zanyi fyaɗe ma bazanyiwa ƙaramar yarinya kamar Zubaidah ba, don haka Barr a matsayinka na mai hidima da kotu nasan kafini sanin hukuncin fyaɗe a ƙasar nan, kar ka dubi dangantakar ku kar ka dubi maysayin aikinka a companin iyaƴensu, ka dubi girman laifin a ƙundin tsarin mulkin ƙasa snn ka dubi girman laifin a al'adance snn ka duba a musulunce tunda nasan kai musulmi ne, ka shigar da waɗan nan azzalumai kotu ka ƙwato wa yarinya hakkinta, wnn shine kawai zai proving mana You are not a coward snn kasan aikinka snn kana hukunci da gaskiya......"Enough Barr ya daka masa tsawa kafin yaci gaba da faɗin" How dare kai har ka isa ka faɗa min abinda zanyi, wnn shi yake nuna dafinitely kai kayi raping nata....." Bai gama yin shiru ba suka jiyo muryar Salim yana faɗin"
"Toh kai Jalal da kake ta faman zare kanka kasan dai wann laifi tate mukayi sa, dukanmu huɗu mukayi raping nata so idan ma hukunci za'a mana harda kai....."Bai gama yin shiru ba su momy suka shiga tafe hannaye suna salati, Mami ta rungumo Labib ɗinta tana faɗin" wllhi bazai taɓa sakuwa ɗana ya karashe rayuwarsa a gidan yari ba, wllhi baku aikata ba, son pls tell me you are not involve..... "Barr ya fashe da dariya kafin yace" Hajiya pls kima daina ɓata hawayenki babu wanda ya isa ya ɗauresu don mune da ƙasa, idan kana kuɗi toh fah sai abinda kaga dama zakayi. Kan wata kucakar yarinya ƴar talakawa baƙauyiya kike tunanin za'a rufe yaran nan, ai hakan ba mai yuwuwa vane.... Ya ƙarashe maganar yana wani shafa haɓarsa.
"Jalal kuwa gyaɗa kai yayi kafin yace we shall see ya ƙarasa gabansu Labib ya dube fuskokin abokan nada kafin yaci gaba da faɗin" Da biyu kuka bani abinda zai bugar dani, kunyi hakan ne intentionally don ku aiwatar da mummunar kudirinku akanta, toh wllhi wllhi ku sani each and every one of you must pay..... Daga haka ya nufi hanyat fita......
"Cak yaja ya tsaya ganin mace ingarmiya wacce a tsaye ta kaisa tsaho tsaye a gabansa ga hawaye na bin ƙuncinta..... Su Dad ma gaba ɗaya suka maida dubansu ga matar. Yaya Hadiza kuwa kaman jira take tuni ta soma cire takalman ƙafafunta tana ƙoƙarin shan ɗammara take faɗin" Kune, wllhi kune ku kuka mata fyaɗe duk sau kunyi bayani...... Ta sunkuya tamkar taɓeɓɓiya tana shirin wawuran duwatsun dake a tsakiyar gidan cikin wani ruwa mai zubowa daga sama zuwa ƙasa.... "
"Oh my Lord! Shes crazy cewa Alhj Kasim, ya dubi Barr ya ce , Barr take care of her, kar a barta ta fice kasa gurd su kamata sƴ rufeta don wann matar ta fita da wann zance shukeɓan sunanmu ya ɓaci a duniya,... Barr ya gyaɗa kai yana murmushi kafin ya nufi kiran gurds, Alhj Kasim ya dubi Jalal dake shirin fita kafin yace" Dont do anything foolish boy ir you'll live to regret it, ya dubi su Salim kana yace ku wuce muje, babu musu suka bi bayansa kana ganin su kaga sangartattatun yara wanda basu san neman komai ba sede a basu.
"Kafin Jalal ya karasa wajen matar nan gurds sun kameta, yana da tabbacin matar nan tasan Zubaidah tunda gashi tana faɗi. Cikin sauri ya nufi gate, kai tsaye wajen da suka aiwatar da laifin ya nufa.
"Tsugunawa yayi a wajen sanda yayi tozali da bushesshen jinin dake malale kan ciyawar, take ya ringa tuno komai, komai ya shiga dawo masa, ji yayi ya kasa jure tsayuwar da yake tuni ya tsuguna a wajen zuciyarda na masa wani irin raɗaɗi tamkar zata fito waje, tunda yake a rayuwarsa bai taɓa nadama irin ta yau ba, bai taɓa danasanin shan giya ba sai yau, bai taɓa jin ya tsana kansa irin ta yau ba, yana wajen suka rabata da mutuncin ta and he didn't do anything to pretect her against them, infact shi ya fara riƙota ma ya damƙamasu ita..... Wani ƙara ya sake gamida kama gashin kansa kamar zai cizge, yasan bazai taɓa yafewa kansa ba, yanzu ina take ina zai ganta. Take matar ɗazu ta faɗo masa, miƙewa yayi cikin sauri, jin ya taka wani abu yasa sa tsayuwa, tsugunawa yayi ya ɗauka abin yana bi da kallo, ɗan hankacif ne data saƙawa Umar me flawowi a jiki, ..
"Jalal yabi Hankacif ɗin da kallo, a hankali ya manna hankacif ɗin a fuskarsa zuciyar sa naci gaba da zogi. Kaman wanda aka zabura ya soma tafiya....
"Likita ya dubi Ammi a karo na biyu kafin yace" Baiwar Allah magana ta gaskiya sede fah kiyi haƙuri don babu yanda za'ayi mu karɓi wann case ɗin ba tareda hukuma ba, kinsan yanzu laifin fyaɗe ya zama ruwan dare snn an saka tsattsauran mataki akan irin wnn case ɗin, a gaskiya kije kizo da hukuma don kinga dole a saka a cikin file na asibiti kuma gwamnati ta gani ni za'a kama tunda nine da duty.
"Ammi ta yarfe zufan da ya keto mata kafin tace" Haba likita taimako fa zakayi snn ka duba fah ka gani yarinyar nan tamkar bata numfashi don Allah ka taimaka idan yaso kar kasa case ɗinta cikin report ɗinku na yau har sai an san su waye masu laifin. Ka taimaka likita ka tuna idan ƙanwarka ce ko ɗiyarka a wan condition ɗin yaya zaka ji, nasan kai musulmi ne don Allah ka taimaka kar mu bari rayuwarta ta salwanta haka nan tunda su waɗan da sukayi laifin abinda suke so kenan, kaga hakan na nufin kaima ka goyi bayan ɓarna.
"Jikin Dr yayi sanyi da jin kalaman Ammi, fuzar da iska yayi kafin yace" Shikenan Hajiya zan taimaka mata, Godiya Ammi ta soma masa tana hamdala, tuni Dr yasa Nurses su shigo da Zubaidah ɗakin tiyata,
"Saida ya girgiza da ganin irin cin zarafin da akayiwa Zubaidah, tabbas wann ba don kwananta na gaba ba data tuni ta mace, Allah shi kaɗai yasan dalilinsa na barin yarinyar nan a raye, idan aka ce masa maza goma ne sukayi amfani da ita bazai musa ba, don kuwa sun mata kaca kaca, ta yanda ko dabba bazaiyi irin haka ba. A ƙalla ya samu ciwo a privaye part ɗinta sama da bakwai snn jini ya zuba sosao a jikinta. Tuni ya soma gudanar da aikinsa da taimakon nurses ɗinsa.
" Gaba ɗaya hankalinsa a tashe yake,shi yama rasa wanne zaiyi sashen da yake tunani nan aka sauƙi Amminsa ya nufa, yana isa ya tarar bata nan ɗaki ya shige ya kulle kansa cike da naɗamar rayuwa.
"Hadiza sai wage baki take taji kuɗaɗen da ko a mafarki bata taɓa jin labarin irinsu ba, ta kuma duban Alhj Kasim dake hankince saman kujera kafin tace" Alhj barinyi sauri na ƙarasa asibitin kafin matar nan ta kira ƴansanda.
"Alhj Kasim yayi murmushin cin nasara kafin ya jawo drwer ɗin dake gefensa ya ciro bandir ɗin ƴan ɗari biƴar ya miƙawa Hadiza yace, ki fars taɓa wann, hannu na rawa Hadiza ta amshe kuɗin ta shiga sunsunawa tana wani lumshe idanu, a sittin ta miƙe ta nufi waje tana yashe baki kaman gonar audiga....
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:11] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
12
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
*In Dedication to All Victims Of Rape. Never Keep Silence, Fight for Your Right. This is Not Something To Be Ashamed Of Your Self, Let the Guilty Ones Feel Ashamed Of Them Selves..... 🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾*
_Wannan Shafin naku ne Barr Asmie n Zainab ina ƙaunarku yanda kuke ƙaunata da labarai na, Allah shi bar ƙauna #1Luv...😘😍_
"Alhj Jamil ya rapka uban tagumi yana kallon yayan nasa, ɗan gyaran murya yayi kafin ya soma faɗin" Yaya kana ganin abinda muka yi munyi daidai, anya Yaya bazamu miƙa yaran nan ga hukuma ba......" Bai kai aya ba Alhj Kasim ya katse sa,...
"Jamilu kai har sai yaushe zaka soma tunanin irin ƴan adam, akan wata yarinya ɗiyar talakawa kake magana muyi risking rayuwar yaranmu, ka faɗa mun idan muddin muka bari maganar nan ta fito media shikenan sunan mi ya ɓaci, reputation ɗinmu ya ɓaci snn wa kake so ya gaje mu idan mu muka miƙa tilon yaran mu ga hukuma snn kana tunani Alhj Tahir zai yarda ya aurawa Salim ƴarsa Kausar ne, kai ƙarewa ma duk abokan hulɗanmu na kasuwanci sai sun guje mu, our company will go bankrupt (Kampaninmu zata samu kariyan tattalin arziki) dan haka bana sonjin wani magana daga gareka.
"Shiru Alhj Jamil kawai yayi yana duban ɗan uwan nasa wanda bashida abinda yafi masa kuɗi a rayuwarsa da kuma tilon ɗansa Salim.
"Barr Munir yayi wata murmushi kafin yace" S gaskiya Mr President shawarinka yayi daidai yanzu sai musan yanda za'ayi da wann yaro Jalal don nasan definitely yaron ka iya kawo mana cikas tunda dai mun gama da iyaƴen yarinyar. (Alhj Kasim Dasuki shine President na *Dasuki Holdings Of Company*)
"Alhj Kasim ya murmusa kafin yace ku bar min wann ni nadan yanda zanyi, Ya juyo ya dubi Mami da Momy da sukayi jugum suna kallonsu kafon yace" Farha kusan yanda za'ayi Kausar da Hajiya Raliya su rigamu isa Abuja...." Momy ta sauƙe ajiyar zuciya kafin tace " Dama Haj Raliya ta faɗa mun washi garin sakun rana zasu koma gaba ɗaya harda Alhj Tahir kasan very busy mutum ne, yau idan yayi sadaka a ƙofar gidansa gobe zasu wuce.
"Daddy ya jinjina kai amma har cikin ransa mamaki yake ya akayi Alhj Tahir bai sanar ɗashi ba, shashantar da zancen yayi dan yanzu babban ƙalubalen dake gabansa shine ya kuɓutar da ysransa. Jinjina kai yayi kafin ya dubi momy yace " Whete are the boys?? " Momy ta amsa masa da suna sama, kai tsaye stirs ya nufa Barr Munir na taka masa baya, Dad ɗin Labib kuwa ficewa waje yayi yana amsa call....
"Suna zazzaune kowa da abinda yake saƙawa Daddy ya turo ƙofa suka shigo hida Barr Munir, Kallo ɗaya Labib ya masu ya watsar yaci gaba da ɗunduma gefen fuskarsa yanda Jalal ya ji mai ciwo.
"Kallonsu One by one yayi kafin yace" Gobe gobe zaku bi jirgin safe ku wuce Abuja, babu wanda ya amsa sa duk cikinsu, ya dubi Tariq da har lokacin hancinsa bai daina zuban jini ba yace" Na kira Dad ɗinka nayi briefing nasa komai a waya don ya riga ya wuce Abuja yau da safen nan, kundai jini kar ku bari kuyi missing flight ɗin safiya, daga haka suka sa kai zasu fice Salim ya katse su da faɗin " Daddy what about Jalal,....." Bai gama rufe baki ba Barr Munir ya katse sa da faɗin " Kaci gidanku Salim, na maganar kuɓutar da rayuwarku kana maganan wani Jalal...." Baki Sal ya turo gaba like a spoiled kid kafin yace" But Uncle we cant leave without him, hes onr of us..... " Wata ashar Daddy ya watsa masa kafin yaci gaba da faɗin" Idan Jalal ɗin ƙanin ubanka ne sai ka jirasa ka tafi dashi, snn ku buɗe kunnuwanku da kyau kujini, babu ku babu Jalal, inace don kunga kuna rayuwa gida ɗaya ne dashi shiyasa kuke ganin kaman ku dashi ate equal ko, toh wllhi kukayi wasa koransu zanyi daga gidana daga shi har uwsrsa...Barr munir yayi saurin cews shikenn kuwa Mr Ptesident kaga kowa ya huta...
" Labib ya miƙe yana watsa masu mugun kallo mussaman Barr Munir don ya tsane sa ba kaɗan ba, don yana ganin shi yake saka Uncle ɗinsa yin wasu abubuwan snn yaga alama ƙoƙarin raba uncle ɗinsa da ɗinsa yake. cikin dakakkiyar murya yake faɗin " Uncle Idan ka kori su Jalal a gidanka zasu dawo gidanmu. So ba matsala bane....." Cike da mamaki Daddy ke kallonsu, anya Jalal bai asirce masu yara ba, bai kuma cewa komai ba sai karya babban gyaransa da yayi ya fice fuuuu Brr ma yabi bayansa da saurin gaske...
" Kasa zama yayi a ɗakin sabida ƙuna da ƙirjinsa ke masa, tausayin yarinyar ya saka gaba, ko runtse ido yayi sai ya tuno sanda suke rabata da mutuncinta, quiet alright ba sonta yake ba but tausayinta ya hanasa sukuni, jinta yake tamkar ƙanwarsa ji yake da ma ƙanwarsa akayi haka tabbas da sai yanda ƙarfinsa ya ƙare, mussaman kasancewarsa shi kaɗai wajarn mahaifiyarsa, tafiya yake baima san yanda zaije ba, shi dai yasan yana bin titi, hankacif ɗinta da ya tsinta kuwa yana nan damƙe hannunsa kaman mai tsoron kar wani ya wupce, duka lungun da Jalal yabi sai kaji ana yaba kyaun halittarsa babu mata babu maza, kar kuji nace haka, Jalal mutum ne wanda Allah yayi masa halittan kyau wanda harta ƴan uwansa maza suna yaba kyaun halittar sa.
"Ammi tana ganin fitowsr likita daga ɗakin tiyata yana share zifa tayi saurin miƙewa ta nufesa tana tambayarsa,
"Ɗan goge zufar goshinsa yayi kafin yace" Hajiya a gaskiya bazan ɓoye maki ba yarinyar nan ta sami mummunar rauni, sauƙin abin guda shine bata kamu da yoyon fitsari ba, amma tana tsananin buƙatar jini, yanzu abinda nake so dake kije ki nemo wani ɗan uwanta ko kuma kuɗin da za'a nemi jini a ƙara mata ....
" Ammi ta sauƙe ajiyan zuciya kafin tace" Toh likita ko za'a auna nawa. Ɗan jimm yayi kafin yace toh bbabu matsala idan kince haka, amma koda mun auna naki yayi daidai sai kinada wadataccen jinin da zaki iya ba wa wani kafin mu ɗiba, Ammi tace ta amkce, nan aka shiga ɗakin aunin jini da ita, unfortunately jinin Ammi baiyi matching na Zubaidah.
"Tagumi Ammi tayi tana tunanin ina Hadiza ta tafi, gashi batasan gidanta ba, bata san ina zata sameta ba, wata zuciya tace ki fita ki neme ta tunda ƴar uwarta ce ƙila a sami wanda jininsu zaizo daidai. Haka Ammi ta fice tana tunanin me ya hana Hadiza dawowa.
"Chan tsalleken titi ta hangesa sai faman tafiya yake, shaff ta mance da Jalal ma gaba ɗaya, hankalinta ya kaikaita wajen ceto rayuwar Zubaidah. Da sauri ta nufesa cike da mamKi take tambayarsa ina zaije haka.
"Ɗan shafa kai Jalal yayi kafin yace" Kawai dai ina kallon yanayin garin ne...... Zuciyar Ammi ya buga tayi saurin riƙo hannunsa suka tsallaka titi, Jalal dai sai kallonta yake gaba ɗaya da ganin Ammin tasa tana cikin damuwa....... Murya na rawa Ammi take faɗin Jalal babu dai wanda ya ganka ko, Jalal ka faɗa mun....."Da mamaki yake kallonta kafin yace" Ammi are you alright, meke faruwa, waima me kike yi a nan a daidai wnn lokaci.
"Sauƙeajiyan zuciya tayi kafin tace ba komai Jalal mije cikin asibitin sai na faɗa maka abinda ya fari,
"Asibiti kuma??? Ya maimaita a zuciyarsa, haka yabi Ammi kaman raƙumi da akala har suka shige cikin asibitin zuciyarsa na ci gaba da bugawa da sauri ɗa sauri.
"Cak ya tsaya yana kallonta sanda Ammi ta buɗe kofar ɗakin da take, itace dai ba gizo take masa ba, fuskanta na fiskantar sama, idanunta a lumshe tamkar mai bacci gashin kanta ya rufe pillow ɗin da aka mata mayashi dashi, hancinta pointed yana kallon sama ɗan lips ɗinta kaman wacce ta shafa jan baki, ga bandage ta ko ina duk yanda taji ciwo an rurrufe. Take yaji jiri na neman ɗibarsa, Ammi sai faman masa bayanin yanda ta sameta da abunda aka mata take Jalal kam ko saurarenta bai yi, abu guda da yaji shine shigowar likita da tambayar jinin da yayi.
"Juyowa yayi ya dubi Dr ɗin kafin yace" Dr ka yake my blood..... Kallonsa sukayi daga Dr ɗin har Ammi, Dr ya ɗanyi jim kafin yace " Amma sai mun auna munga ko........" Bai kai aya ba Jalal da tuni jijiyoyinsa sun tashi cikin ysananin ɗaga murya yace" *I said take mine,*
"Jiki na ɓari Dr Garkuwa yace Okay muje muje, Ammi kuwa kallo tabisu dashi har suka fice.
"Cikin sa'a jinin Jalal yayi daidai wa Zubaidah nan da nan aka ɗibi har leda biyu aka saka mata.
"Ammi ta shigo ɗakin da Jalal yake yanda aka ɗibi jininsa yana ƙoƙarin maida rigarsa, nan ta hangi tabon dake a bayan kafaɗansa wanda da gani ba sai ance maka shaida bace, ƙirjinta ya buga da ƙarfi, anya duk ranan da Jalal yasan ba ita ta haifesa ba anya bazai tsaneta ba, Juyiwan da zaiyi suka haɗa ido, murmushin ƙarfin hali ta sakar masa kafin tace "Son sannu da aikin alkhairi Allah ya biyaka.
"Ɗan mirmushi yayi ba yareda yace komai ba, su duka biyu kana ganinsu kasan akwai abinda ke damunsu,....
"Iyalle ta dubi Hadiza baki sake kafin tace" Ashe ke shasha ce, yanzu ɗan wann kuɗin har ya isa ya rufe bakinki, ai baki sani ba hanyar arziki ne Allah ya kawo maki a sauwaƙe, yanzu abinda za'ayi tashi zakiyi kije ki sami wann saunan mijin naki kita shera kuka ki faɗa masa abinda akayi wa ƙanwarsa daga nan ki ɗaukesa kuje asibitin ki koma can gidan kiyita masu bore da hauka, kinsan masu kuɗin nan basu fatan abinda zai ɓata masu suna, Snn kinsan anƴi baikon Zubaidah ce masu zakiƴi a al'adan garin nan duk macen da aka sameta ba budurwa ba tofah maido da sadakinta ake snn sunanta da na iyayenta ya ɓaci snn har ta mutu babu me aurenta, ce masu zakiyi saidai su aurawa yaransu ita, nasan bazasu yarda ba kinga dole su ksra maki kudi mai tsoka snn kice dede ku bisu Habuja don a nan tsangwamanku mutane zasuyi. Kinga idan kiks tafi Habuja kya min hanya nima na tafi, kinga muafah shikenn zamu fara neman kuɗi da gaske a can har muzo mu gine gida kalan nasu....... Hadiza tayi shewa ta miƙa wa Iyalle hannu suka tafe kafin tacr" Ƙawata shiyasa nake sonki yanzu bari kiga da zafi zafi ake dukan ƙarfe. Yawwa ƙawata cewsr Iyalle maza lalumo nawa kasoɓ ki bani ke ai tanzu kin zama hajiya.
"Hadiza ta zaro kuɗi ta danƙawa Iyalle kafin ta fice.
"Yanda Iyalle ta tsara mata kuwa hakan akayi, Hamma Habibu yasha kuka shaɓe shaɓe harda majina, tabbas yasan iyayensa bazasu taɓa yafe masa ba ya kasa riƙe masu amanar tilon ƙanwarsa, Hadiza harda hawayen munafunci take basa baki, kayi haƙuri Habibu ina nan tare da kai snn duk wanda yayi wann abu wa Zubaidah bazmu taɓa barinsa ba ko ɗan uban waye, sai an bi mana kadinmu, maza shirya muje asibitin, babu musu ya shirya suka nufi asibiti.
""Labib ne ya soma ƙarasowa yanda Jalal ke zaune kafin su Salim.suka karaso, murya kalan na masu nadama suka soma magana dashi, ko kallo basu ishesa ba ƙarshe ma tashi yayi ya bar masu wajen, ya ɗau aƙwashin ko yau ya koma Abuja bazai ci gaba da zama da Dasuki family ba, ya koyi darussa a rayuwa snn zai tashi ya nemi abun kansa duk wuya duk rintsi.
**************************
*Gombe Fada*
Wata matashiyar mata ce zaune saman Kujeru na alfarma, a shekare bazata gaza shekaru 40 ba, tana sanye cikin kaya na alfarma, fuskan nan nata ko kaɗan babu annuri, ido ta kafe hoton jariri dake manne a tangamemen parlron dashi, wani katutun baƙin cini ya kuma tokare mata maƙoshi, Idan akwai abinda tafi tsana a rayuwarta toh wann tangamemwn hoton ne wanda yake kaman ruhin mijinta Mai marta sarkin Gombe MODIBBO ALIYU MU'ALLAYIƊI.
Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:11] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
13
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
"Gimbiya Zahida ce ta shigo parlorn cikin shiga shiga ta alfarma Alkebba fara ƙal sai ɗauke ido yake, daka ganta basai ance maka ga jinin sarauta ba, gefe da mahaifiyarta ta zauna fuskarta ɗauke da murmurshi kana tace" Barka da Hantsi Ummi na, da fatan kin tashi lafiya.
"Murmushi matar data kira da Ummi tayi kafin ta shafi gefen fuskar Zahida tace " Barka ɗiyar saraki jikar saraki da fatan kin wayi gari lafiya.
"Murmushi bai bayyana haƙwara Zahida tayi kafin ta riƙo hannun Ummi tace " Ummi kina sani naji kamar watarana zanyi sarauta idan kina koɗa ni haka.
"Ummi ta jawo Zahida cikin jikinta ta rungume kafin tace" Mai Martaba baida wani ɗa ko jika a doron ƙasa face ke, baida gudan jininsa a duniyan nan face ke ƴar lele na, meyasa kike tunani wataran bazaki mulki garin nan ba.
"Rausayar daidanu Zahida tayi kafin tace" Ummi a ina kika taɓa jin mace tayi sarauta a ƙasar nan, burina dai kawai shine na auri saraki nima don gaskiya idan ba jinin sarauta ba bazan yi aure ba.
" Ummi tayi wani dariya mai cike da ma'anoni idanunta suka sauƙa kan tangamemen hoton jaririn dake manne a tampatsetsen parlor kafin tace" Maza tashi muje mu gaida kakarki kafin ta fara mita.
"Babu musu Zahida ta miƙe Ummi na riƙe da hannunta bayi guda biyu ne ciki harda Jakadiya suka take masu baya snn suka nufi sashen "Madaki wato mahaifiyar mai Martaba.......
"Tunda ta buɗe ido tayi ido huɗu da lkitan ta ringa mimmiƙewa tana wani irin ƙara haɗi da ƙanƙame jikinta dukda azaban ciwon da takeji, babu yanda likita baiyi ba ya dubata amma abu yaci tura, kai duk wani mutum idan ya shigo muddin na mijini ne to ta rinƙa figita kenan tana wanu irin kuka mai wani irin sauti tana ƙanƙanme jikinta.....
"Daga can nesa ya tsaya yana kallonta sanda aka kira nurses sukai mata alluran bacci, wani irin tausayinta ne ya cika zuciyarsa, take yaji bazai iya kallon wann hali na ƙunci da wahala da take ciki ba, kaman wanda kwai ya fashe ma a ciki haka ya fito reception.
"Zama yayi a reception yana kallon Hamma Habibu dake ta faman share hawayen da ya wanke fuskarda gaba ɗaya, Jalal ya kuma jin tausayin waɗan nan bayin Allah sanda yaga Hamma Habibu ya kama wuyar rigarsa yana sharan majina dashi a hankali ya ƙarasa ga Hamma Habibu gamida da dafe kafaɗansa Habibu ya ɗago rinannun idanunsa da suka jiƙe da hawayr yana kallon Jalal kana ya soma faɗin"
"Bata da kowa sai ni, iyayenmu sun rasu sun bar min amanarta, gashi na kasa cika masu burinsu, na kasa riƙe amanar tilon ƙanwata, idan ta mutu bazan taɓa yafr ws kaina ba.... Kuka mai ƙarfi ya kufce masa sanda yake dukan kansa da duka hannayensa biyu yana faɗin" Bani da amfani, gaskiyar Hadiza ne banida amfani, banida amfanin komai.... Kalmar da ya ringa nanataw knn yana dukan kansa da ƙarfin gaske.
"Jalal da tuni hawaye sun ciko idanunsa, tausayin Zubaidah da Hamman ta ya cika zuciyar sa, Allaj sarki ashe marainiya ce babu uwa babu uba babu dangi sai Hamman ta wanda yake irin mitanen nanne masu maysalar ƙwaƙwalwa. Abu mai kaman wuya ne ke sa Jalal kuks, zai iya cewa tun yana yaro kai koda yakr yarinta duk tsananin abu bai yin kuka amma wann karan sai ji yayi ya kasa controlling kansa, tuni idanunsa sunyi jazur haka nan farin fatar sa ta koma ja, tsanar aminan sa ne ya cika zuciyar sa haɗi da tausayin Zubaidah da rayuwar da zata fuskanta...
"Annah ce ta bawa Jalal kuɗi ya sayo allura don babu wanda ake buƙata za'a mata a asibitin, cikin sauri ya amsa ya nufi waje, Annah ta karaso ga Hammah Habibu tana basa baki cike da tausayawa.
"A daidai ƙofa ya haɗu dasu, sun ɓadda kama basu ɗauko luxurious cars ɗinsu ba, Daddy ne sai Barr Munir... "Cikin sauri Jalal yayi niyyan wucewa Barr Munir yayi alama wa Gurd ɗinsu guda ɗaya da hannu, kan kace me an janye Jalal zuwa cikin wata mota mai baƙar glass.
"Fuzgewa Jalal ya shiga yu da iya ƙarfinsa daidai lokacin da Barr Munir da Daddy suka shigo, banda harara babu abinda Jalal ke masu, a hasale yake faɗin" Me kuke yi a nan marassa imani.
"Daddy yayi wata murmushi kafin yace" Relax boy, dont di anything foolish, magana ɗaya zuwa biyu zamuyi da kai, if you cooperate fine ka tsira, idan kuma ka ƙi..... Wata murmushi yayi jafin ya kalli Barrister.
"Barrister yayi gyaran murya kafin yace" Jalal, shin kana da shaida cewa su Salim su suka raping yarinyar nan, shin idan kana tunanin idan kayi gigin sbigar da ƙara kai zaka tsira ne, bazaka tsira ba , tunda dukanku kuna wajen sanda incidence ɗin ya faru, tabbas yarinyar ta ganku gaba ɗaya, babu mai cire ka cikin wnn mess ɗin, she'll admit dukanku ne kukayi raping nata, snn boy ina gani daga idanunka you are madly in love with her....."Da mamki kurum Jalal ke kallonsa.
"Barr yayi wata murmushi kafin yaxi gaba da zayanno kalamai masu ɓadda tunanin mutum irin nasu na lawyoyi " Ka sake tunani da kyau yaro, idan kayi confessing laifinku zaka tafi prison for the rest of your life don bakada mai tsaya maka, kar ka mance ƙasar nan idan kana da kuɗi babu mai ja da kai, su salim will be free kai ɗaya za'a bar cikin wann mess ɗin don kaine talaka, and poor mum ɗinka da bata da kowa saiki, ƙunci zai kasheta, snn wann yarinya bazaka taɓa kasancewa da ita ba, wataƙila itama depression ya kasheta, kaga ashe tainakon da kayi niyyan yi baiyi rana ba.
"Jalal ya zuciye tamkar zai jai mai naushi yake faɗin" Stop involving me a cikin mess ɗinsu, ban aikata ba n no one will force me to confrss something I never did, not even you Alhj Kasim.
"Murmushi sukayi su duka biyi, kafin Barr yace" I like your courage boy, amma dai ka duba maganar da nayi maka, and abu na karshe idan kana so kayi saving life ɗin yarinya ka aureta....
"Mun riga mun gama magana da likita gibe za'ayi discharging nata kai tsaye kuma Abuja zamu wuce gaba ɗaya including her and her family. So dabara ya rage naka Jalal, ka sani kai za'a bari a rana don mun sami amincewar uwar goyonta da likitan ta, kaga baka da shaida... Daga haka suka buɗe masa marfin mota ya fice jikin sa a sanyaƴe.
"Wai shin haka duniya ta koma, wai shin shi talaka bashida ikon gudanar da rayuwarsa yanda yake so, shin mutane haka suka zama, abin duniya ya gama rufe idanun kowa, kaico irin wann rayuewa da muke cikinta a yau.....
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:11] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
14
*©Sameena Aleeyou....✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
" Jiki a sanyaye ya tare mai mashin yana tambayarsa ina zai sami chemist mafi kusa don ba sanin garin yayi ba, basu wani tafiya mai nisa ba suka samu, nan ya sai alluran ya koma asibiti.
"To his greatest surprise wulgawan motar compnayn *Dasuki Hodlings* ya gani, kuma tabbas ɗazu cikin ta su Daddy suka zo. Toh me ya dawo dasu tambayar da yayi ma kansa kenn, sann babu mai basa amsar wann tambayar nasa yasa ya nufi asibitin kai tsaye.
"Shaye da mamaki Jalal ke kallon su Mommy da Mami, Annah ce ta hango shi tsaye ya kafe su da idanu,
"Jalal ƙaraso mana , Allah dai yasa an sami alluran, Annah ta faɗi daidau lokacin da gaba ɗaya suka maida kallonsu ƙofa, Mami Momy da kuma Yaya Hadiza.
"Momy ce ta miƙe gamida karɓan alluran hannun Jalal wanda ya koma tamkar gunki bai gama shan mamakin ɗan adam ba saida yaji momy na faɗin" Jalal abokan ka sun wuce sun barka har ina masu faɗan ina suka bari ka, ashe kai kam taimako ka tsaya... Da mugun mamaki kurum yaje binta da kallo sanda taci gaba da faɗin "
" Allah sarki Jalal yaron arziki, Allah dai ya biyaka kaida mahaifiyarka, irin wann raimako da kukayi ai mu ya kamata mu ringa yin irinsa, ta maida duvanta ga Annah daketa faman murmushi kafin tace" Habs Annah ai irin haka da wuri ake faɗi sai mubada kalan namu gudumawar, ƴanmatan da kaddara da tsautsayi na fyaɗe a auka masu haƙiƙa suna buƙatar taimako da kulawa don haka ne ma Alhj ya yanke shawarin taimaka masu itada familynta, gobe insha Allah zamu tafi Abuja baki ɗaya don hakan ne kurum zai mantar da ita wann mummunar ƙaddara da sameta, zamanta a nan zai ringa tuna mata abin, snn cannin wajen zama zai mantar da ita komai.
"Mami dai kallon Mommy kawai tayi tana mamakin yanda halin momy da Daddyn Salim yazo daidai, banda lugude da ƙirjinta keyi bata komai sau kallo, dan kuwa saida mijinta ya mata kashedi babu ruwanta a wann zalunci, toh ya zata yu tuɓda ɗanta na ciki, data rasa tilon ɗanta gwara ta biye masu kida hakan ka iya kawo matsala ga aurenta.
"Annah da yaya Hadiza godiya suka shiga, yaya Hadiza harda share hawayen munafunci tuni ta kaɗo kan Hamma Habibu yazo yayi godiya, bai kawo komai a ransa ba ya ringa masu godiya...
"Takaici da tausayi ya hanasa ci gaba da tsayƴwa a wajen, tuni ya fice zuwa farfajiayan asibitin.... Ƙasar wata bishiya a samu ya zauna gamida haɗe kansa da gwiwarsa, maganganun Alhj Kasim da Barr suka shiga dawo masa,
"Kalaman da yafi nanatawa shine *"You are in love with her, Ka aureta shine maka mafita...*
"Girgiza kai ya soma tamkar zararre, ko ɗaya ko kaɗan baijin abinda yake ji game da ita So ne ,shi bai taɓa yin soyayya ba balle yasan yaya take, abunda ya sani shine yana jinta tamkar ƙanwarsa snn yana tsananin tausayinta, snn ya ɗau alwashin tamaika mata har iya rayuwarsa.... A gigice ya miƙe ya nufi cikin asibitin sanda yajiyo wani irin karan da ta saki.....
" Mami dai jigum tayi a mota har suka isa gida, tana shiga parlon su ta tarar da Daddyn Labib zaune yana karanta jarida da alama isowarta yake jira.
"Kamar wacce ƙwai ya fashe ma a ciki ta nufesa tanai masa sannu da gida, ko kallo bata ishe sa ba baƙƙe ya tanka ta. Sanin bazai mata magana ba yasata nufi sama.
"Daidai step na biyu taji ya kira sunanta, cak ta tsaya ba tare da ta jiyo ba.
"Saboda kin raina ni shine saida kika biƴewa Yaya da matar sa kuka je ha'intar waɗan nan bayin Allahn ko, kina cikin hankalinki kuwa Salma, na saka maki doka ki take......."Kamar me shirin kuka ta soma faɗin" Haba haba Jamil, me kake tunani, na bari inaji ina gani tilon ɗan nawa ya tafi gidan yari, bazan iya rasa sa ba idan kai baka damu dashi ba...."Mikewa yayi gamida ajjiye jaridar dake hannunsa kafin yace " Shi ya janyo ma kansa, shi ya saka kansa a ciki don haka babu hanuna a kare shi, kuma a yau na isa Abuja zan miƙa sa ma hukuma....."Ihun da Mami ta saki ne ya kaɗo hankulan sauran mutanen dake gida, kuka take kan rusawa tana fadin " Ita babu mai kai mata ɗata kurkuku....
"Alhj Kasim da Hajiya Farha a tare suja shigo, Mami ta karasa gabansu tana kuka take roƙon Daddy, Yaya dan Allh ka masa magana cewa yayi zai miƙa Labib ga hukuma, Yaya ka taimaka min ka hana sa....."Momy ta riƙo Mami tana lallashinta suka nufi upstirs....
"Wani mugun kallo Alhj Kasim ke waysa wa ƙanin nasa kafin yace" Jamilu wato baka daina maganar nan ba koh, bari kaji na faɗa maka dukda cewa kai ka haifi Labib baka isa ka min iko akansa ba, bari kaji na sake faɗa maka in case u forgotten "Wllhi wllhi babu mahaluƙin da ya isa ya shigar da ɗana prison muddin Naira na aiki a kasar nan, Jamil ga fili ga doki idan kayi shirin yin faɗa dani yayan ka. Kayi abunda kaga dama tunda yanzu har ni nake faɗa kake faɗa.... "Daga haka yasa kai ya fice fuuuu...
"Kallo Alhj Jamil yabi ɗan uwan nasa dashi, jikinsa yayi sanyi tabbas bazai so yaga rugujewar family ɗinsu ba hankali ya sulale gamida zama bisa sofa haɗi da zare faran tabarau na ƙarin ƙarfin gani dake idanunsa.....
*Washe gari*
"Tunda aka sallame ta bara ɗago ido ta kalli kowa ba, snn bata san duniyar take ko akasin haka ba, iyakacin abinda take tunawa shine dariyar su da shewan su sanda zasu rabata da mutuncin ta, haka nan idan ta buɗe idanun ta fuskokinsu take gani, motsi kaɗan idan tayi takan ji zafi zogo haɗi raɗaɗi daga ƙasanta, hakiƙa a galin yanzu tafu shiga sahun marassa ganjali, don kuwa tabbas bata san yanda hankalin nata yake ba, iyaka abinda ta sani shine duk na mijin da yazo kusa da ita takan fita hayyacinta takan koma tamkar mai ciwin hauka....
*Abuja*
"Batasan a ina take ba, itadai buɗe ido tayi ta ganta a wani gida na daban, mafarki take waɗann samaruka sun nufota da wuƙa tana ihu tana gudu, gabanta kuma Umar ne ya buɗe hannu alamun ta ƙaraso garesa, fuskarsa kaman ba nasa ba ashe shima wuƙar ne a hannu sa.. Da tsoro ta isa gareshi yana ƙoƙarin burma mata wuƙar knn ɗaya daga cikin samarukan nan ya ture Umar ya rungumeta.........
"A gigice ta saki wani irin ƙara gamida taƙurewa waje guda, .. Hadiza ce ta shigo gamida jan dogon tsaki jin Zubaidah na kiran sunan Umar,......Yaya na kazo ka ceceni kashe ni zasuyi,
"Ruwa cikin kopi Hadiza ta ɗebo gamida sheƙa mata..... Babu shiri ta buɗe ido firgit, ta yunƙura zata tashi taɓi zafi, hannunta dake ɗaure da bendeji yanda ta gurɗe taji ya shiga mata zogi alamun ta fama, a gigice ta fito daga ɗakin tana kallon yanagin yanda take, wani ƙara ta saki gamida durƙusawa waje...
"Labib dake tsaye ta windown ɗakinsa yake hangota, wayarsa ya ciro ya shiga neman layin Salim.....
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:12] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
15
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
"Hello guy kana ina ne? Daga ɗaya ɓangaren Salim ya amsa
"Gidan su Kausar, what akwai wani abu ne.
"Okay mu haɗu a company things are getting outta control...
"Dont get u buddy, wau meke faruwa ne.
"Gajeren tsaki Labib yayu kafin yace" Salim its about that girl....
"You mean the Cow girl.
"Dama wacce yarinya nake maka magana aside from her, ka gane Uncle cant tackle this issue alone, we need to talk kafin abubuwa su caɓe wann matan yayan nata zata zame mana sabon matsala, nu banma san meyasa Uncle ya kwaso su ya taho dasu ba,..... "
"Miƙewa Salim yayi kana yace "Okay fine ka kira Taruq kace masa mu haɗu a company.. Daga haka yayi hanging.
"Fuzar da iska yayi gamida furta "Dmn dammit..!!!!
'Daidai nan Kausar ta ƙaraso riƙe ƙaramar tray a hannun ta... Da mamaki take binsa da kallo ganin ya miƙe ya ɗauki car keys ɗinsa.
"Ajiye tray ɗin tayi saman tabƙe kafin ta bisa da kallo.
"Ɗan murmushi yayi kafin yace" Sweetheart I'm so sorry but I really need to go.
"Ɓata fuska sosai Kausar tayi kafin tace" I dont get u, you mean you leaving right now, haba Salim wai meke damunka ne, this days you acting very strange, tun jiya fah ka dawo bakazo ka ganni ba as your fiancee na ɗauka ma da zaran ka iso zaka zo ka ganni, ko waya mukayi da kai bana gane kanka kwana biyun nan, tell ne pls is something bordering you???
"Ƙaƙaro murmushi yayi gamida ƙarasowa daf da ita hannayenta ya riƙe kafin yace" Sweetheart don't let those ideas to ur head pls. Babu abinda ke faruwa sai zallan soyayyar ki, Daddy ne ya kirani and its urgent, you know how business men are, always busy,
"Hannunsa Kausar ta kalla bataga zobensa ba, ɗago ido ta kuma yi tana masa kallon tuhuma kafun tace "And where is your ring.
"Ƙirjinsa yabada rasss, cikin sauri ya saita kansa kafin yace " Em na cire shi lukacin da zanyi wanka but ina zuwa guda zan saka.
"Cikin rashin gamsuwa da excuse ɗinsa tace " But that ring is a promise bazaka taɓa cire shi ko yaya,
"Ɗan fuzar da iska yayi sanda wayarsa ta soma ƙara, da sauri ya saka a silent kafin ya kalleta yace " For Allah's sake Kausar its just a ring, besides mu a nan ƙasar ba auren zobe muke ba, its obvious kin saba ɗabi'un turawan yamma, but its diff here kin gane, whats important is that I love you with all of my heart and I mean it, Ɗan kallan agogon hannunsa yayi kafin yace" Daddy is waiting for me, I'll give you a call, luv u take care daga haka ya fice sai sauri yake kaman zai kifa...
"Kallo ta bisa dashi har ya fice......
"Cikin gida Kausar ta wuce jiki a sanyaye, haka kurum take ji wani abu na shirin faruwa tsakaninta da Salim.
"Ƙura ma Yaya Hadiza ido tayi tana binta da kallon mamaki, she couldn't believe what shes hearing, hawayae na bin ƙuncinta ta sa bayan hannunta maras ciwon ta ɗan goge kafin ta soma faɗin"
"Meyasa, meyasa kika ɗauko ni daga mahaifata kika kawo nan wajen, meyasa baki bari na mutu ba, meyasa baki bari an bisneni gefen iyaye na ba, meyasa kika rabo ni da garin masoyi na, shin kina tunanin zanci gaba da rayuwa ne, shin kina tunanin ni Zubaida har akwai sauran rayuwa a gaba na, babu ita. Mutuwa a wnn lokacin yafiye mun komai....
"Tsawan da Hadiza ta daka mata ya jawo hankalin su Momy da Annah gaba ɗaya suka nufo sashen da aka sauƙe su Zubaidah. Janta Hadiza ta shiga yi tana faɗin babu yanda zaki tafi a nan zaki tsaya a nan zaki ci gaba da rayuwa.......
"A zuciye Zubaidah ta fizge hannunta daga riƙon da Hadiza ta mata, babu alamun tsoro a tattare da ita take kallonta, cikin ɗaga murya take faɗin"
"Is this all you can do for me, iyakacin abunda zaki iya min kenn? Ki amimce ki biyo waɗanda suka lalata min rayuwa suka durƙusar da rayuwar yarinyar da bata ci masu ba bata sha ba, shin idan kece Zubaidah hakan ta faru dake shin yaya zakiji,..
"For years kina azabtar dani kina wulaƙanta Hamma na sabida lalura na rayuwa da yake dashi, daidai da rana guda ban taɓa saɓa maki ba, shin abinda zaki saka min dashi knn....
"Da mugun mamaki Hadiza ke kallon Zubaidah ta canza gaba ɗaya ta koma tamkar ba ita ba lokaci guda, Huci ta soma tana bƙrin kunya....
"Ɗaga mata hannu Zubaidah tayi kafin taci gaba da faɗin" Kin kula.dani tun ina yarinya Allah saka maki da alkhairi da abubuwan da kika min, Allah ya biyaki na sani nida Hamma na duk muna ƙarƙashin kulawarki ne, Allah ya biyaki. Amma ki sani mutuwata a yanzu tafiye mun komai..... Da ɗingishi ta juya ta koma cikin ɗakin gamida rufe ƙofar.....
"Bugun duniya Hadiza tayi Zubaidah taƙi buɗewa. "Taƙurewa tayi can ƙuryan ɗakin tana kuka mai tsuma rai.
"Momy jiki a sanyaye ta koma sashen ta yayinda Annah ke tsaye a wajen tamkar gunki, abu guda da Zubaidah ta faɗi yayi muguɓ ɗaga mata hankali, *Kika kawoni wajen waɗanda suka lalata min rayuw* kalmar da Annah tayita nanatawa kenn, abinda ya ƙulle mata kai ta kasa fahimta. Jiki a sanyaye ta wuce ɓangarensu tana tunanin lamarin......
"Daga yanda yake tsaye ya gama jin komai yaga komai a gabansa komai ya faru, Zuciyarsa taci gaba da zogi da raɗaɗi, shin haka zai tsaya yanaji yana gani rayuwarta ta ƙarasa lalacewa,..."A fili ya furta no, no no cikin sauri ya juya ya nufi gate ya fice......
"A ƙofar *Dasuki Holding* suka haɗu su duka uku. Salim ne ya soma fitowa daga motarsa kafin su Labib da Tariq suka fito dama tare suke Labib ya biya ya ɗauki Tariq, Securities ne suka ƙaraso suka karɓi keys ɗin motocinsu suka ƙarasa da motocin parking space snn su kuma suka shige cikin companƴ ɗin wanda yake ko ta ina glass ne tamkar a turai kake.
"Guys gaskiya nifa na fara nadamar abinda mukayi don wllhi my Dad is totally mad at me, cewar Tariq yayinda suke ƙoƙarin shigewa cikin lift, Salim ya ɗanyi gajeren tsaki kafin yace nima dai abin ya soma damuna don Kausar ta fara tunanin I'm hidding something from het. Tsaki Labib yayi sanda suka isa floor ɗin Daddy kafin ya juyo ya dubesu yace" Thats precisely why we are here, to talk with our parents, they shouldnt have brought that girl here in the first place. Gaba ɗaya suka kaɗa kansu suka ce haka ne.
"Duk yanda suka wuce gaushe su ake *The Dasuki's* ba yara masu ji da kansu da ƙarfin arzikin iyayensu......
"Sakatariyan Daddy ta ɗan dubesu cike da rusunawa tace " Am sorry but Mr president is at the middle of a meeting right now, you cant see him now....
"Dmmit!!!!! Labib ya faɗi da karfi gamida buga tabƙe ɗinta wanda yasata zabura.
"kwanto da kansa saitin fuskarta yayi fuska a tamke yake faɗin " If you dont want to get self fired then go in right a way, and tell him we wanna see him right now.
"Da sauri ta miƙe kafin tace Ok ok sir right a way sir,ta wuce ta nufi Conference hall .....
"Ana tsakiya da meeting sakayariyar sa ta kawo masa saƙon, fuzsr da iska yayi cikin ransa yace " Those boys wunt kill me, excusing kansa yayi kana yayi alama ma Lauyan sa Barr Munir kan cewa ya biyo bayansa, babu musu Barr ya miƙe yabi bayansa...
"Babban parlon dake cikin Office ɗin suka ƙarasa, shigarsu yayi daidai da banko ƙofar wanda hakan ya ja hankalinsu gaba ɗaya suka kalli ƙofan. Cikin wani irin yanayi suke dubansa.
"Barr yayi saurin faɗin " How dare you barge in here, ku talakawa really have no manners.
"Daddy ya girgiza kai kafin yaci it is not his fault, I have to make it clear to those stupids securities that this filthy jark isnt my son, he cant just come in here inti this very company.....
"Alhj Kasim we need to talk for the sake of these spoiled brats ya ƙarashe maganar yana nuna su Salim da tuni sun sha jinin jikinsu....
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:12] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
16
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum....📖📚_
"Kallon mamaki suka bisa dashi, Alhj Kasim ya dubesu kafin yace "Excuse us, Labib ya kalli Uncle ɗin nasa kaman me son yin magana sai kuma yabi bayansu ya fice.
"Jalal ya dubi Barr Munir dake zaune saman ɗaya daga cikin royal chairs ɗin da aka ƙawata parlorn dasu kafin yace" Kaifa Barr aren't gonna excuse us...."Dakatar dashi Alhj Kasim yayi ta hanyar ɗaga masa hannu kafin yace " Boy ko me zaka faɗa min ka faɗa min gaban lawyer na, nida shi babu wani shamaƙi a tsakanin mu so just go ahead and talk.
"Ƙarasowa cikin parlorn yayi gamida zama bisa kujera mai kallon na Alhj Kasim tuni idanunsa sun rine zuciyarsa ta shiga masa zafi sabida abinda zai faɗi, bashi da wani choice rather than it..."Barr ne ya katse masa shirunsa da faɗin " Jalal we don't have the whole day, Mr President is a busy man so kayi abinda ya kawo ka.
"Fuzar da iska yayi kafin ya ɗago ido ƴana dubansu kana yace" *Zan aureta* daga nan shiru yayi bai kuma cewa komai ba, sai faman murza hannunsa yake jijiyoyin jikinsa sunyi ruɗuruɗu haka nan idanun sa sun koma jawur....
"Surprisedly suke kallonsa...
"Fari'a ne ya cika fuskokinsu mission ɗinsu goes well wann na ɗaya daga cikin dalilin da yasa suka taho dasu, don sun san muddin Jalal ya aureta toh magana ta ruhu har abada babu abinda zai kuma tono ta.
" Kafaɗan Jalal Alhj Kasim ya shiga bubbugawa a hankali kafin yace" Now you proved to us you are capable of helping her, da kayi gigin kai report da shine ka cuceta ka kuma cuci kanka, don bazaku taɓa kancewa tare ba, you'll endup in jell and ita kuma she might commit suicide ko depression ya karta gaba ɗaya, and ƴour poor mother will loose her only son, Jalal you did the best thing.
"Har lokacin dai Jalal bai ce masu komai sai kallon gefe da yake yi.
"Alhj Kasim yayi ma Barr ido, check Brr ya ɗauko ya rubata mar kuɗi kafin ya miƙa masa yace" Ka je ka nemi hida sai ku yare gaba ɗayanku a can....." Bai gama rufe baki ba Jalal ya miƙe yana masa mugun kallo kafin yace" Bana son komai daga gareku, auren Zubaidah sji kaɗai na tambayeku sabida a halin yanzu ku kuke iko da ita tunda kuke iko da wicked sister inlaw ɗinta......
"Murmushin bossawa sukayi baki ɗaya kafin Alhj Kasim ya dubi Barr ya masa ido, Kallo suka bi Jalal dashi wanda tuni ya fice....
"A first parlor ya hangu su Salim suna zazzaune, Harara yabisu dashi ɗaya bayan ɗaya, Labib ne ya miƙe da sauri ya nufesa, saidai kafin ya iskesa ya tura sliding door ɗin ya fice.....
"Alhj Jamil da Alhj Maina Dad ɗin Tariq suka ƙaraso parlorn after the meeting don jin me ake ciki, Alhj Kasim yace kar su damu he can take care if everything.... "Kallonsa dai kawai sukayi amma sunsan Alhj Kasim zai iya yin komai to get rid of his problems.
"Alhj Jamil ya ajiye masa wasu documents saman table ɗinsa kafin yace
" Yaya our company its at risk of going bankrupt, we might loose some of our employees sabida fake golds da aka fitar zuwa NewZeeland,...
"A zabure ya miƙe yana kallon ƙanin nasa, tunu ya cire hular kansa ya shiga fifita duk da sanyin AC ɗin dake parlorn "
"Jamil yaya akayi suka gane Zinaren bogi ne, Jamil we can't go bankrupt you need to do something.... Gaba ɗaya kaman zaucecce yake maganar, Waya ya ɗaga ya kira sakatariyarsa yace ta masa scheduling meeting da *Marafa Group Of Companies* Barr da Alhj Jamil sai kallonsa suke yanda ya zauce lokaci guda.
"Kallon Alhj Jamil ya kumayi kafin yace " Ka kira duk wani bankin da ka sani ka karɓo aron kuɗi kafin business venture ɗinmu da Marafa group of companies ya bunƙasa, we cant loose our company brother, do as I said pls,...
"Alhj Jamil ya dubesa da mamaki kafin yace" Yaya bashin banki fah kake magana, kasan....." Bai ƙarasa rufe baki ba Alhj Kasim yace " Haba Jamil so kake mu rasa company ɗinmu, ko billion nawa ne kasa hannu ka karɓa idan yaso daga baya sai mu wanye dasu, amma yaya kake gani yau udan baba ya taso yaga company ɗin da yasha wuya akansa ƴaƴan sa his very own children sun kasa maintaining, pls brother just do as I said for the sake of our company, for the sake of *Dasuki Holdings* Fuzar da iska Alhj Jamiƙ yayi kafin ya riƙo hannun ɗan uwan nasa yace " Yaya zanyi yanda kace, daga haka ya miƙe ya nufi Office ɗinsa.....
"Yana ficewa Alhj Kasim da Barr Munir suka kwashe da dariya harda tafe hannu,.
"Barr yace " Mr president baka da kyau, Alhj Kasim ya murmusa yana karkaɗa pen kafin yace" Let him borrow the Money, with that I'll ruin him completely dariya suka kuma yi hadi da tafe hannu...
¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤
*A Dukku fah*
"Inna wai har yau babu wanda zaice min ha yanda Zubaidah take, ya kuma tambaya a karo na biyu.
"Ajiye rariyan tankaɗen dake hannunta tayi fuska a tamke kafin tace" Baba Wuro (Haka take kiran Umar) Har sau nawa zan faɗa maka nima bani da taƙamammen masniyar yanda suka tafi, iyakacin jitajitan danaji cikin gari shi na faɗa maka, Zubaidah bada kanta tayi ma ɗaya daga cikin yaran masu kuɗin nan da suka zo, bayan sun gama lalatan su, suka tattara suka bisu garinsu wasu ma cewa suke da maƙudan kuɗi suka sayesu.....
"Girgiza kai ya shiga yi idanunsa jazur yake faɗin" Inna ni nasan ƙarya ake mata sharri ne, Zubadah na bazata taɓa bada kanta ma wani ba, bazata taɓa bin masu kuɗi ta barni ba, nasan tana sona......" Baffah ne ya fito daga kewaye ya tarar suna zancen....
"Ajiye butar hanunsa yayi gamida zubar da ruwan dake bakinsa kafin ya juyo yana ma Umar mugun kallo kana yace " Wato har yanzu bazaka daina maganar wann yarinyar ba ko, toh idan baka sani ba ka sani, maganar da mahaifiyarka ta faɗa maka gaskiya ne, idan da ba gaskiya bane ai da sun mana sallama kafin su tafi musamman ita Zubaidar tunda akwai baikon ta akan ka...
"Idanuwansa suka ciko ƙwalla, da sauri ya miƙe ya shige ɗaki gamida kulle kansa, da gaske ne Zubaidah ta barsa sabida wani, take ya yuna sanda tayi aikin wuni guda gidan Alhj Dasuki, ya tuna irin kallon da wani saurayi ne kyau yake mata, ya tuna yanda itama ta masa murmushi, tabbas ko wata mace zata iya barin masoyinta akan wann saurayin sabkda ya haɗa komai na rayuwa, ka kuɗi ga kyau,....."Share hawayen da suka zubo masa yayi yana jin zuciyarsa na masa ƙuna, bazai iya barin Zubaidah ba, bazai iya rayuwa babu ita ba, dole ya fice ya neme ta dole ya dawo da ita gareshi don kuwa tabbas Zubaidah *Mallakin sa* ne......
"Iyalle ta dubi ƙanwarta shafa wacce ke mutuwar son Umar amma besan tanayi ba, tayi murmushi kafin tace" Shafah ki kwantar da hankalinki Ummaru kaman kin samu an gama, ni nan da kike gani ni na kitsa wa Hadiza yanda zata yi, bacin haka ina taga kwanyar yin wnn tunani, ni dai abinda nake so dake kisan yanda zaki saye zuciyarsa tunda naga har kusan mutuwa nikayi sanda yakai baikon Zubaidah.
"Shafa tayi wani murmushin jin dɗi, don yanzu jinta take tamkar sarauniyar mata tunda Zubaidah ta tafi kafin tace" Ai wllhi bakiji wani daɗin da nake ji ba, yanzu kika tabbatar min ke ɗin yayata ce, Umar kuma dole yaso ni tunda wancan me kama da aljanai ɗin tayi gaba.. Dariya suka kuma yi a tare harda kashe hannu....
*Gombe, Fada*
" Abba barka da war haka , cewar Zahida yayinda take ƙarasawa kusan mahaifin nata,
"Murmushi yayi mai fitar da ƙwarjininsa kafin yace "Barka Gimbiya ƙarasi mana, ya matsa mata gefe da tumtim ɗin da yaɗan kishingiɗa akai ta ƙaraso gamida zama daf dashi. Hannayenta ya riƙo gamida sunbatar su kafin yace" Allah ya miki albarka ɗiyata. Murmushi tayi tana mai kallon mahaifin nata wanda a kullum cikin tausayin sa take sabida damuwan da bar yau ya kasa mance ta sama da shekaru ashirin da huɗu.
"Ɗan gyaran murya Zahida tagi kafin ta kalli tapkeken hoton jaririn da duk wani parlor a gidan akwai hoton kafin tace " Abba meyasa baza a cire hotunan ba tunda naga ɗaga maku hankula yake musamman kai da Madaki, snn ya mutu Abba inaga ajiye hotonsa a parlor haka babu wani alfanu
"Girgiza mata kai yayi idanunsa naga hoton kafin yace "Zahida Yayanki bai mutu ba, ni inaji a cikin jikina bai mutu ba, nasan watarana Allah zai haɗani dashi, ina ganinsa kullum cikin mafarkina, snn Suhaima tana faɗa min cikin mafarki na ɗanmu yanada rai, snn ta bar min amanarsa duk randa na hafu dashi......."Baki Zahida ta saki tana kallon mahaifinta wanda ba don jinin sarauta dake yawo a jikinsa ba da sai tace tabbas kwanyarsa ta kusan samin matsala, a hankali ta miƙe da zummar barin wajen, don tasan mai martaba muddin ya soma waɗan nan batu toh a ranar haka zai wuni bai fita fada ba..
"Ummi dake maƙale jikin labule tana kallonsu, take taji zuciyarta na mata zafi, shin wnn wani irin yaro ne, shekara da shekaru yaci ace mai martaba ya mance sa shida uwarsa gashi har yau yana tunasu, gashi har yau bata cimma burinta na mallakan ɗa namiji ba wanda zai kasance magajin sarki.... Da wnn ƙunci ya juya ta nufi sashenta ba yateda ta shiga sashen mai martaba.
"Zahida kuwa tana komawa ɗaki wayatya ta kunna ta hau facebook don abokin hitarta knn sai amintattun bayinta guda biyu, kasancewar kullum a killace take a guda bata fita ko ƙofa.
"Hira ta soma yi da kawarta wanda basufi kwana biyu da haɗuwa ba, hura da yayi dadi sai aka koma waya daga chating...
*Abuja*
[1/23, 22:12] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
17
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
*"Dasuki Mansion"*
"Matashin saurayi ne wanda aƙalla bazai haura shekaru 35 ba zuwa da shida ya shigo cikin parlorn cikin shiga irinta guards, baƙaƙen kaya daga sama har ƙasa, idanunsa manne da ɓaƙar tabarau.
"Cike da rusunawa ya miƙa wa ogan nasa saƙon dake hannunsa. Alhj Kasim ya murmusa kafin yace " Good job Faisal, I trust you, I know I can always count on you, kaci gaba da aiki me kyau.
"Faisal ya kuma rusunawa haɗi da yin gajeren murmushi kafin yace " At your service Sir,
"Daddy yace " You can leave now,.
"Kuɗaɗene shirye cikin babban jakar wasu in dollars wasu kuma Naira, murmushi yayi sanda suka kalli juna shida Barr Munir.
"Barr ya shafi haɓarsa yana murmushi kafin ya jawo jakar ya buɗe, ..
"Documents ɗin dasuke cikin first folder ya ɗauko ya shiga buɗewa,.
"Murmushi yake yana kallon takardun kafin ya kalli Alhj Kasim yace" Everything perfect, gaskiya yaron nan bazamuyi wasa dashi ba yasan kan aikinsa, ka duba kaga yanda yayi copying signature ɗin Alhj Jamil tamkar shi yayi,....
"Alhj Kasim yayi wata murmushi kafin yace" Barr I know what I'm doing nasan irin mutanen da nake aiki dasu, Wann yaro Faisal is very talented bazamu barsa ya tafi haka nan ba, dole naja sa sosai a jikina, yanzu abinda nake so da kai yanzu kayi attaching attaching waɗan nan documents ɗin da wanda yayi signing na karɓan bashin banki, kaga idan akayi presenting a conference meeting babu wanda bazai yarda sa hanunsa bane, daga nan mission dina na mallakan *Dasuki Holding* ya kusa zama sucessesful... Dariya suka fashe dashi kaman ba manyan mutane ba....
"A tare suka miƙe suka nufi waje Barr na biye bayansa ɗauke da rapan en ɗari biyar rufe cikin envelop kai tsaye sashen su Jalal suka nufa...
"Annah na tsaye tana kwasan shanya taji sallaman su, cike da tsananin mamaki ta bar abinda take ta ƙaraso tana amsa sallaman, mamaki ma ya hanata gaishesu, da ƙyar ta lalumu kalamai tai masu sannu, suma sun lura da hakan.
"Har Annah tai masu iso suka shigo ta shimfiɗa masu darduma bata daina mamaki ba.
"Bayan sun gaisa ne Daddy yai gyaran murya kafin ya soma magana.
" Hannatu nasan zakiyi mamakin ganinmu a ɓangaren ki, Toh magana ta gaskiya its about your Son Jalal.....
"Ɗago ido Annah tayi tana dubansu kafin tace" Lafiya Alhj me ya sami Jalal.?
"Daddy ya ɗanja fasali kafin yaci gaba da faɗin" Jalal was at my office earlier, Yaje shi office ɗina on an a serious matter, bansan ko kin sani sabida naga tun da incidence ɗin ya faru kin yi iya ƙoƙarinki wajen kula da yarinyar, in short ke kikayi saving life ɗinta......
"Gaba ɗaya ya ƙulle kan Annah, ko kaɗan bata gane me yake nufi ba kokuma ina ya dosa.... "Murya cike da damuwa tace " Alhj saidai ban gane me kake nufi ba, what did this had to do with my son.
"Ko yayi maka wani abin ne....
"Daddy da Barr suka kalli juna kafin Barr yayi gyaran murya yaci gaba da faɗin"
"Tabbas bakida masaniya akan abinda ke faruwa amma yanzu ya zama dole ki sani tunda abin yakai ga aure, da alama Jalal ya ɓoye maki amma gaskiyan magana Jalal shi yayi ma yarinyar nan Zubaidah fyaɗe wanda hakan yasa Alhj taimaka masu tunda basuda kowa snn Jalal ma bashida kowa sai shi.......
"Kaman almara haka Annah take jin maganar, ƙirjinta ya buga da ƙarfin gaske tasan Jalal manemin mata ne amma bata taɓa kawo zai iya yiwa wata yarinya fyaɗe ba..... Take hawaye ya shiga zarya a fuskar Annah.
"Alhj Kasim da damuwan munafunci ya nuna a fuskar sa yaci gaba da faɗin" Hannatu keda Jalal duka ƴan uwa muka ɗauke ku mussaman Jalal na ɗauke sa tamkar ɗa bazan gansa cikin matsala na ƙyalesa ba dan kuwa shida su Salim daidai na ɗauke su. Snn laifin da ya aikata yayi nada wann dalili ne yasa amincewa zai auri yarinyar su rufa wa junan su asiri.
"Barr ya ajiye kudin gabanta kafin Daddy yaci gaba da faɗin" Yau da dare insha Allah zamu ɗaura auren snn ga wann Jalal yayi amfani dashi don neman muhalli,..... "Kasa magana tayi har suka fice bata san sun fice ba.....
" Ido ta ƙura wa kuɗin har lokacin idanunta na hawaye, "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un " Fyaɗe, Fyaɗe Jalal, Jalal, ɗinta shi yayi raping Zubaidah.... Hannu tasa ta goge hawayen, dukda ba ita ta haifi Jalal ba tana masa so irin wanda uwa keyi wa ɗanta, her whole life burinta Jalal ya zama ɗa na gari, amma sai ya kasance akasin haka, kaico kaicon irin wann rayuwa.
"Sai yanzu komai ya shiga dawo mata daki daki tun ranar bikin sakun rana Salim, ta tuna Jalal ya tambayeta sunan yarinyar da suke tare, ta tuna irin kallon da taga yana mata ta tuna yanda hankalin sa ya tashi lokacin da Zubaida ke asibiti wann a dalilin haka har rana me kaman ta yau bata gane kansa ba, ta tuna yanda yayi donating jininsa ma Zubaidah, ashe dama sabida yasan laifinsa ne dole ya damu..... Maganar Zubaidah na ɗazu ya dawo mata kwanyar ta yanda take faɗi wa Hadiza *"Kika kawo ni wajen waɗanda suka lalalta min rayuwa* tabbas da Jalal take, shine ma komai ya tabbatar mata shine tunda gashi su Alhj har sun sani, no wonder bai mata maganar ba, no wonder ya tafu kai tsaye ya sami Alhj ba tare da saninta ba. Durusawa tayi wajen zuciyarta na mata ɗaci......
" Suna fita daga sashen su Jalal suka nufi sashen da aka ba wasu Zubaidah su zauna.
"Har lokacin bata buɗe ƙofa ba tana rufe ƙuryar ɗaki tana kuka.
"Hadiza tana ganinsu ta miƙe tana washe baki tana gyara ɗaurin kwali, gaishe su ta soma yi har tana tuntuɓe wajen ɗaga masu kayan da Zubaida ta ringa watsi dasu.
"Gaba ɗaya suka sakar mata murmushi kaɗin suka tambayeta Zubaidah...
"Nan ta soma jero masu ƙarya da gaskiya na abinda Zubaida tayi da wanda bata yi ba. Barr ya fuzar da iska dan bai zaci yarinyar zata zame masu matsala har haka ba, Barr ya kuma tambayar Hadiza ina mijinta, ta bashi amsa da fadin" Sun fice ganin gari shida Kamalu
"Alhj Kasim ya murmusa kafin ya ciro wayar sa yayi dialing wani lamba ya ƙara a kunne. "Hello James ya kashigo cikin guda ina neman ka, Barr zaizo ya directing naka yanda nake, daga gaka ya kayse wayan.
"Jim kaɗan Barr da wani murtuƙeƙen mutumi sanye cikin baƙin kaya da baƙin tabarau , da gani basai ance maka guard dinsa bane suka shigo a tareda Barr.
"Daddy ya dubesa kafin yace " James nasan kanada makullin duka ɗakunan gidan nan, I want you to open this door right a way.
"Kames ƴa rusuna kafin yace " Considered it done sir.
"Kan kace me James ya buɗe ƙofar ɗakin da Zubaida ke ciki.....
"Aikuwa tana ganinsu ta saki wani ƙara ta shiga tattaro gaba ɗaya kayan jikinta tana rufe jikinta, manne wa sosai tayi ta taƙure can ƙuryan ɗakin jikin garu, banda rawa da jikinta keyi bata komai, sai faman cije bakinta take tana kuka maras sauti.
"Alhj Kasim yayima James Ido. Take James ya ciro ƙaramar bindiga a cikin suite ɗinsa yayi pointing bindigar a kanta cikin miryarsa mai cike da tsoro yace " Quittttttt....!
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:13] : 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
18
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
"Daɗa mannewa tayi jikin garu gamida runtse idanunta wanda suke a jiƙe da hawaye,
"Alhj Kasim ya durƙusa a gabanta gamida ƙura mata ido, hannu yasa ya ɗago fuskarta......
"Wani irin kyarma jikinta keyi jin hannunsa a jikinta, tamkar garwashin wuta aka ɗora mata haka take ji, ƙara ta saki gamida ƙanƙamewa waje guda,...." Murya a dake yace " Kalle ni nan...
"Bata kallesa ba sai runtse idanunta da tayi.
" James ya kwaɗa mata ƙasar bindigan a keyar wanda yasata buɗe ido babu shiri, da ƙarfin gaske James ya ɗago ta gamida riƙe hannayenta, jin bazata daina kuka ba yasa James ɗaure bakinta da wani farin ƙyalƙe, yana riƙe da ita ya ɗago ta tana facing Alhj Kasim...."
"Barr yayi wata silent murmushi kafin yace " Yarinya ki bada haɗin kai ki sami tsira, bata kallesu ba sai hawayen dake zuba daga idanun ta....
"A zuciye Daddy ya pinciko gashinta da ƙarfin gaske gamkda ɗago kanta, kallonsa kawai take da idanun tsana hawaƴe na bin idanunta.
"Daddy yaci gaba da faɗin" Idan kika bi umarni na kin tsira Shashan yayanki wanda ya kasa kula da rayuwarki ya tsira, ki buɗe kunnuwanki da kyau kiji abubuwan da zan faɗa maki.
"Kukan azaba kwai Zubaida keyi riƙon gashinta da Daddy yayi na mata ciwo, haka nan raunukan dake jikinta basu gama warkewa ba.... "Daddy yaci gaba da faɗin
"Idan kika ƙi yin abu guda da zan umarce ki zan kashe ki snn na kashe ɗan Hamman ki kinga na tabbata wann sokon yayan naki wanda hankali bai ishe sa ba, idan ya rasa ki ya rasa ɗansa nasan baƙin cikin duniya zai taru ya masa yawa, bayan na gama azabtar dashi snn na kashe shi,..."Wani irin runtse idanunta tayi hawaye na bin ƙuncinta jin irin kalaman da yake faɗa mata.
"Zan aurar dake a yau ɗin nan ma wanda naga dama, snn wllhi wllhi kinji na rantse naji wann magana ya fita waje zanyi yanda na faɗa maki zan kashe ki na kashe ɗan Hamman ki na kuma azabtar da Hammanki, don haka kar naji kar na gani bakin ki ƙanin ƙafarki, maganan fyaɗen da aka maki ya zama tarihi... Kina jina ya ƙarashe maganar yana zungurin kanta da bakin bindiga.
"James ya kifa mata wani gigitaceccen mari kafin yace " Answer!!!!! Da ƙarfin gaske...
"Daɗa runtse idanunta tayi kafin ta gyaɗa kanta da ƙyar sabida azaba.
"Barr ya ajiye mata kuɗi bandir ƴan ɗari biyar a gabanta kafin yace " Amarya wann kiyi anfani dashi wajen sayayya don nasan amare ba a rabasu da sayayya.... Daga haka James ya suce mata baki gamida yin wurgi da ita tsakiyar ɗakin kafin suka fice.
"Yaya Hadiza dake laɓe bakin window ta gama ganin komai, dariya tayi a hankali gamida watsa wa Zubaida dake kwance helpless a ƙasa wani uwar harara kafin tayi saurin ƙarasawa yanda su Daddy suke.
"Murmushi suka sakar ma juna kafin Daddy yace " Kar ki damu kaman yanda na faɗa maki aurenta yau da daddare a parlor na ina fata yayan nata bazai zame mana matsala ba.
"Hadiza ta kuma murmusawa kafin tace" Yo ai Alhk kar kaji komai tunda kanada ni, wann shashashan kuma ai ba mutum bane don sai abunda nasa sa shi zaiyi,..
"Barr da Daddy suka kalli juna kafin suka sakar ma juna murmushi.
"Barr yasa hannu cikin jakar ya ciro rapan ƴan ɗari biyu ya miƙawa Hadiza baki har kunne tasa hannu ta amshe. Barr ya kalleta xike da jin daɗin yanda Hadiza ta kasance mace mai son kuɗi babu wuya yanzu sai ka saye imaninta.
"Hadiza sai ysallen murna take ta nufi cikin gidan, ɗakin da Zubaidah ke yashe a ƙasa ta shige...
"Tana nan kwance a kasa kukan ma baya fita, Allah sarki ƴar marainiyar Allah.😭.
"Harara Hadiza ta watsa mata gamida zama gefenta, ɗaukan kuɗin tayi ta maƙe a hammatar ta, take ta canza fuska zuwa kalan damuwa sai ka rantse har ranta ne.
"Tallafo Zubaidah tayi ta rungume gamkda goge hawayen munafinci kafin ta soma faɗin" Kiyi haƙuri Zubaidah ki amince ki auri wanda ya aminta da aurenki ki sani taimaka maki zaiyi don wllhi yanzu babu me yarda ya aureki ko Ummarun da yake waƙar soyayyarki muddin yaji abinda ya sameki ba aurenki zaiyi ba. Kuma bari na faɗa maki babban rufin asirinki shine rufuwar maganar nan din kuwa muddin kowa yasan abinda ya sameki haka za'a keta zancen ki ana nuna ki da yatsa, mutane zasu ƙyamace ki haka nan babu mai kallon da wata daraja baƙƙe kima.....
Sameeena ce👌🏾
[1/23, 22:13] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
19
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
"Toshe kunnuwanta tayi da ƙarfin gaske alamun bata son jin kalaman Hadiza, wani uban tsaki Hadiza ta buga kafin ta tureta daga jikinta ta faɗi ƙasa, idan kin ga dama kiyi yanda kika so tunda ke ba'a maki abin arziki, ai ba akan ki aka fara fyaɗe ba kuma wanda aka masu ma suna ci gaba da rayuwa, idan kin gama kukan munafurcin kinya iya tashi kizo ki min aiki don ba baiwar gidan ubanki bane...."Daga haka ta kaɗe sawayenta tayi ficewarta..
"Asmah ce ta shigo tapkeken parlorn da sallama cikin shiga irinta lauyoyi wato cooperate, har ta cire belt ɗin dogon takalminta Kausar dake zaune a parlorn bata sani ba, da alama tayi nisa duniyar tunani...
"Ɗago kai Asmah tayi tana dubanta kafin ta ƙaraso daf da ita ta dafata....
"A ɗan zabure Kausar ta kalleta kafin ta sakar mata murmushi...
"Ah Attorney yau har kun taso daga sch ɗin ne.
"Asmah ta murmusa tana mai ajiye tapkeken littafin ta saman tabƙe kafin tace" Ai na faɗa maki Law School ba kaman degree program bane ba lalle mu ringa jimawa ba... Asmah ta canza zancen da faɗin
"Ehen wai meke damunki ne, kwana biyu nan you dont seems your self, is anything bothering you?...
"Shiru Kausar tayi gamida ƙurawa Tv dake kan faman aiki idanu..
"Asmah ta matso daf da ita gamida dafa kafaɗunta kafin tace " Sis I'm here for you, you can talk to me may be I can help.
"Kallonta Kausar tayi still damuwa ne a face ɗinta kafin tace " Cousin bazan ɓoye maki ba its about Salim.
"Asmah ta gyara zama kafin tace " Ehen me ya sami Salim ɗin.
"Kausar ta ɗan rausayar da idanu wanda ɗabi'arta ne kafin tace " These days he's been acting very strange, gaba ɗaya tamkar bashi ba, I'm afraid he might be hidden something from me, and ɗazu yazo ya tafi sauri sauri wai Daddy na kiransa, ni the most abinda ya ƙuƙƙen kai ma shine rashin ganin engagement ring ɗinsa da banyi ba a hannunsa.......
"Dariyar da Asmah ta fashe dashi ne yasata cin birki, wani mugun kallo take watsa mata kaɗin tace " What, is it funny?
"Asmah ta ɗan tsaigata dariyar nata kafin tace" Wait hold on Kausar, you mean akan rashin ganin ring a hannunsa kika shiga damuwa haka, tabbdijam toh ai mu musulmai ba auren zobe muke ba, ke bari kiga naje na faɗawa Mumsy islamiya zamu shiga don wllhi turawan nan sun juyar maki da tunani...
"Harara Kausar ta kuma watsa mata har lokacin Asmah bata daina dariya ba kafin tace"
"Look at you jor, ce maki akayi ban sani bane, well I'm only used to it ne nothing more, nasan musulmai basa auren zobe you dont have to inmply anything, besides ni jikina ne ke bani something drastic is about to happen.... Miƙewa tayi ta suri car key ɗin Asmah gamida jan mayafi ta yafa."Asmah baki sake take kallonta.. "Wait ina kuma zaki.
"Kausar ta gama saka takalminta kafin ta juyo ta kalli Asmah tacd" Kinsan tunda aka sa rana na Mumsy bata so ina fita, so thats why zan fita da motarki don nasan bazata gane na fita, so kindly ina si ki miƙe ki wuce ɗakin ki, and help me close my door kafin one of those maids masu neman gidin zama wajen Mumsy su kai mata rahoton na fice.
"Asmah ta kalleta galala kafin tace" Aiko basu faɗa mata ba ni zan faɗa mata...
"Pls mana Attorney ,
"Murmushi Asmah ta ɗanyi kafin tace " But you've to be fast, sai kin dawi Allah ya tsare, hugging juna sukayi kafin Kausar ta fice cikin sauri.....
"Hamma Habibu yayi shiru yana duban Hadiza, harara ta kuma galla masa a kari na biyu kafin tace" Meye kake kallona haka, kamata yayi kamin godiya ba ka tsaya kana kallona haka nan ba tunda da taimakona ta sami mijin aure, bacin haka waye kake tunanin zai kwashi wnn ƙanwar taka sauran kan layi...
"Kallon Zubaidah dake matse cikin garu yayi har lokacin bata dawo daidak ba kafin ya maido da dubansa ga Hadiza, murmushi ya ƙaƙaro kana yace" Eh eh haka ne haka ne Hadiza, mun gode maki daba don ke ba da yanzu muna can garinmu anata zagar min ƙanwa.
"Ya kuma duban Zubaidah kafin yace " Kiyi haƙuri kiyi haƙuri ƙanwata kin sami me auren ki...... "
"Miƙewa tayi tana cije baki kallon tausayi tabi Hamman ta dashi kafin ta juyo tana duvan Hadiza,
"Murya na rawa take faɗin" Bazan aure sa ba wllhi ko waye bazan aure sa ba, bazan taɓa aure ba bazan ci gaba da wann rayuwar ba, da na auri wani ba Umar ba gwara mutuwa na, snn a halin yanzu banjin zan iya auren nasa,... Ta ƙarasa ta riƙe hannun Hamanta kafin tace " Hamma ka yafe min, ta shafi kan Kamalu dake bacci bisa tabarman kafin ta soma tafiya da baya da baya... Kan kace me ta fice a guje dukda ciwo da azaban da take fama dasu...
"A guje suka bi bayanta suna kiran sunanta, har suka fito haraban gidan wanda hakan yaja hankaƙin illahirin mutanen gidan...
"Daidai lokacin aka buɗe wa Kausar tangamemen gate ɗin ta kuwa shigo a guje wanda ita kanta bata san dalilinta na shigiwa a guje ba, kodayake tunanin da take ciki yasata yin hakan.... " Kowa dake wajen runtse idanunsa yay don kuwa daidai ƙarasawan Zubaidah wajen knnn.....
"Shigowarsa gudan knn yayi jifa da abinda ke hannuna ya nufeta gamida ƙwalla mata kira.....
"ZUBAIDAHHH..... Daidai lokacin da Kausar ta danna wani uban birki babu shiri, Jalal kuma ya rungumota suka zube ƙasa suka shiga juyi a ƙasa, ya tareta ta ko ina yanda bazata ji ciwo ba...
"Salim dake tsaye balcony ƙirjinsa ya buga da ƙarfin gaske ganin Kausar ce ta shigo, ai a talatin ya zura shkrt ɗinsa ya nufi downstirs...
"Buɗe idon da zatayi tayi ido huɗu dashi, fuskan da bazata taɓa mancewa ba, fuskan da shine mutum na farko da ya kai mata sura, ɗaya daga cikin fuskoki huɗu da bazata taɓa mantawa a tarihin rayuwarta ba, ɗaya daga cikin mutane huɗu da suka lalata mata rayuwa, farin fuskan da ya koma mata tamkar baƙin kumarci......."Wani irin kara ta saki don kuwa gaba ɗaya abinda ya faru da ita ya shiga yawo a kwanyanta...
"Tunda tayi wann ƙaran bata kuma motsi ba,... Hankali tashe ya shiga jijjigata yana kiran sunanta,.. Kausar ma hankali tashe ta shiga taya Jalal, gaba ɗaya sauran mutanen suka karaso Hammah Habibu kam durƙusawa yayi a wajen ya shiga shera kuka...
"Hadiza ta yaɓe baki take da baeinta kukayi ta mutu tunda abinda tafi so kenan, sekace akanta aka soma fyaɗe..... "Kausar ta ɗago tana duban matar dake magana kaɗin tace " You mean Rape???
"Daidai lokacin da Salim ya fito farfajiyan gidan... Dafe kansa yayi a hankali ya furta "Shitttttt! Cikin sauri ya juya ya koma cikin gidan.
"Mummy tayi saurin ƙarasawa ta riƙo Kausar ta faɗin " Daughter taso mu shige ciki...
"Kausar ta ɗan kalleta kafin tace " Mummy bari a sa mata ruwa ta farka, she panic nd then fainted......"Ido Mummy tayiwa Hadiza alamun su shige ciki....
"Kan su ankara Jalal ya sureta ya nufi ciki da ita, gaba ɗaya suka bisa da kallo.
"Hadiza ta gallawa Hamma Habibu harara kafin tace" Sai ka taso mu shige ciki ai me ƙanwa,... Kausar ta bisu da kallo har suka shige
Kafin ta juyo ta dubi mummy wacce itama kallon tabisu dashi.
"Suna haɗa idanu Kausar ta sakar mata murmushi da iayakacinsa fatar baki. Mummy ta rungumo kafaɗun Kausar kafin tace mu karasa Daughter.....
sameeena ce👌🏾
[1/23, 22:13] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
20
*©Sameena Aleeyou... ✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_
*Dedicated To All Victims Of Rape*
"Shiru Kausar tayi tana duban Mummy, a hankali ta furta "Jalal, so Jalal can rape someone....
"Mummy ta matso gamida rik'e hannun Kausar cikin nata kafin tace " Daughter ki bar D'anAdam yanda kika gansa, muma bamuyi zaton Jalal can do such thing ba, anyway they are getting married, at least sun rufa asirin junansu......
"Kallon Mummy ta kumayi da mamaki kafin tace " Mummy this is a very serious crime, why would you cover-up for him, let him pay for his crime, bai kamata a k'yalesa haka nan ba.
"K'irjin mummy ya bada dummm! Tamkar Wanda aka sauk'e mata guduma.
"K'ak'aro murmushi tayi kafin tace " Kausar the girl refused to talk, tak'i to shigar da k'ara tace duk wanda ya dameta da maganar shigar da k'ara zata kashe kanta, snn Jalal yayi nadaman abinda yayi ya nemi yafiyarta snn ya amince zai aureta so kinga gwara a barsu su sami Chance na kasancewa tare.....
"Jinjina kai Kausar tayi da jin hujjojin Mummy, on the other hand ta tsinci kanta cikin rashin gamsuwa da labarin da Mummy ta bata gameda Zubaidah, haka kurum taji tana son jin gaskiyar labarin, snn tana son kasancewa da Zubaidah don akwai abinda take so taji daga gareta.... bata kuma cewa komai ba har Mummy ta mik'e tana rangad'a kira wa Cook Jane don tazo tayi serving Kausar...
"Dafe kansa ya kuma yi a Karo na biyu yana hangen k'ofar parlorn....
"Ganin Mummy ta fito yasa sa k'arasasa da sauri... Wani uwar harara Mummy ta watsa masa kafin tace " Ni na gama nawa part d'in I made her believed Jalal was the one who raped the girl... Yanzu saura ya rage naku kai da Daddynka, yasan yanda za'ayi su bar gidan nan zuwa gobe kai kuma ka fara tunanin zama namiji for once, and stop being so Mama Boy...... Daga haka tasa kai ta wuce......
"Sauk'e ajiyan zuciya yayi kafin ya murd'a marfin k'ofan a hankali, zaune ya hangeta da gani tunanin wani abin take..
"Yayi saurin saita kansa kafin ya k'arasa yana fad'in " Baby kece a gidan namu, what a surprise..
"Mik'ewa tsaye tayi fuska babu walwala kafin tace " Mummy nazo gaisarwa don tun dawowarsu daga Dukku bamu gaisa ba ko a phone ne, and I'm leaving right now....
"Ohhh com'on baby so soon, at least mud'an gaisa mana...
"Hararansa take ba tare da tace komai ba ta suri Jakarta...
"Da sauri yasa hannu ya rik'e jakar kafin yace " What why the face, wai make damunki me huhm Sweetheart.
"Kallonsa take ido cikin ido kafin tace " Salim duk yanda akaga guda d'aya dole aga sauran ukun, what I Mean duk yanda aka ga Jalal dole a ganku kai, Labib and Tariq, don kuwa nasan bakwa rabuwa, Salim I perfectly well know you and your friends, nasan all of you are womanizers, now tell me the truth and when I said the truth I mean only truth, are you involved in that horrible crime?????
"Da mugun mamaki yake kallonta da k'yar ya iya lalumo kalamai saman harshensa kafin yace " Sweetheart I don't get you..... Which... Which crime are you talking about.
"Huci kawai Kausar keyi kafin tace " The crime your very own friend your childhood friend Jalal had committed, and still ka b'oye min baka dad's mun ba.
"Tattare naman goshinsa yayi gamida fuzar da iska kafin yace" For God's sake Kausar stop talking ridiculous, I swear to you I had nothing to do with that, Why must you accused me of such dirty crime, haba haba sweetheart I tought kinmin farin sani by now kinsan abinda zanyi kinsan wanda bazanyi ba, wllhi tun ranar da na d'aura idaniyana akanki ban sake kula ko wata mace ba, If I want zuwa zanyi na kama hotel na shek'e ayata da iya adadin 'yammatan da nake so without you knowing it ba wai na tsaya ina raping mere girl irin wann yarinyar ba, rashin fad'a maki kuma da banyi ba gani nayi wann ba abun fad'a bane abin takaici ne da Allah wadai... Jalal is my very good friend but believe me wllhi banda hannu kan abunda ya aikata, hasalima nida Daddy taimakonsu muke shida yarinyar su gina sabon rayuwa amma idan baki yarda dani ba fine banida choice..... Ya k'arashe maganar yana ware hannaye sai ka rantse gaskiya ya gama fad'i....
"Jikinta ya d'anyi sanyi amma har yanzu ba wai ta aminta bane. Gyara mayafinta tayi kafin ta d'ago kai tana dubansa snn ta soma fad'in" Salim zan iya zama da kowani irin mutmun a duniyar nan amma banda *Rapist* if I finds out kanada hannu ciki believe me I will not marry you and you can forget about me, excuse me.... Daga haka tasa kai ta soma tafiya....
"Dammit, dmmitttt, Ya fad'i gamida murza duka hannayensa biyu cikin gashinsa, da sauri ya bud'e k'ofar ya shiga kiranta yana binta da sauri......
"Daidai K'ofar da zai sadaka da haraban gidan ta had'u da Labib, kallo d'aya ta masa ta watsar don kuwa gaba d'aya haushinsu take ji...
"Ohhh our bride to be yau kece a gidan namu, Labib ya fad'i yana wani shi'umin murmushi....
"Gajeren murmushi tayi snn suka gaisa a tsaitsaye kana tace "Ita zata wuce gida,
"Labib ya kalli Salim dake tsaye bayansu yana muzurai kaman munafuki kafin ya ware idanu yace " Aww this is so soon though bansan time d'in da kikazo ba, gashi inaso muyi 'yar wata magana about your cousin Asmah, but anyway zamu zo gida nida abokina then we talk....
"D'an yak'e tayi kafin tace " That wud be much better, bye for now...... Wucewa tayi ta nufi motar, Labib yayi ma Salim ido alamun meke faruwa, ido ya masa kawai kafin yabi bayan Kausar da sauri.....
"D'an tab'e baki Labib yayi kafin ya nufi cikin gidan.....
"Har lokacin ya kasa motsa koda d'an yatsansa ne sai hawaye dake neman kufce masa....... Baki ya bud'e da k'yar da niyyan magana tayi saurin dakatar dashi ta hanyar d'aga masa hannu kafin taci gaba da fad'in
. "Jalaluddeeen, ban tayar da kai ta hanyar banza ba, Allah shine shaida na, my whole life I've been struggling for you to have a better future, Why Why Jalal, meyasa ka zab'i ganin kukana, meyasa ka kasa rik'e amanar da Allah ya d'aura maka a matsayinka na d'an Adam. Meyasa ka lalata rayuwar innocent girl irin Zubaidah. Idan ka kubce wa Shari'an duniya ka sani bazaka kubcewa Shari'an mahaliccinka ba......
"I zuwa lokacin ya kasa rik'e hawayensa..... A hankali ya k'araso gamida d'aura kansa bisa cinyarsa ta, kuka yake kaman k'aramin yaro, babu yanda ya iya bashida wani zab'in da ya wuce d'aukan laifin da ba nasa ba, Alhj Kasim is very rich and powerful Man, he can destroy Zubaidah and her family muddin ya fad'i gaskiya so as Annah too, he needs to this for Zubaidah and Annah, take yaji zuciyarsa tana dad'a basa k'arfin gwiwa.....
"Kuka Annah keyi har lokacin kansa na bisa cinyarta, hannayenta ya rik'o a hankali yayi kissing nasu kafin ya soma fad'in"
"I hope one day you'll forgive me my Annah, yeah I was stupid and also a coward, I was drunk that I couldn't stop...."Burki yaja cikin ransa kuwa k'arasawa yayi da fad'in "I couldn't stop them, na kasa hanasu cin zarafinta......
"D'ago ido yayi yana kallon Annah kafin yace " I'll never ever forgive my self for what I did...... Wayarsa ne tayi k'ara gabansa yayi mugun fad'uwa ganin me kiran "Alh Kasim Dasuki ne. Jiki a sanyaye ya d'ago ido yana dubanta kafin yace " I'll Marry her Annah, I'll help her to live again, I'll stand by her to overcome this horrible experience, I'll help her to heel all the damages I caused her...... Daga haka ya fice cikin tafiyar da tafi kama da sassarfa.
"Annah ta bisa da kallo har ya fice, wani ikon Allah sanyi ne taji ya ziyarci zuciyarta, hak'ik'a Jalal yanada baiwa da wani babban Al'amari a tattare dashi wanda ita kanta bata isa tace ga abun ba......
Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:14] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
21
*©Sameena Aleeyou.... ✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
*Dedicated To All Victims Of Rape*
*How painful it is... 😭😭😭 I barely slept well last night when I received the saddest story. Three girls were raped at a University in one night, and you know what frightens me the most, one of the victims was raped by three men just like ZUBAIDAH, she's now receiving treatments at a hospital ..... 😭😭😭*
*Shin har yaushene za'a daina yiwa mata cin zarafi ta hanyar fyad'e a k'asar nan, shin shuwagabannin mu basu ganin abinda ke faruwa ne, shin wai shi talaka bashida ikon rayuwa ne, Hak'ka yanzu nake jin k'warin gwiwar rubuta wann littafi kuma ina fata sak'ona zai isa ga jama'a mussam THE RAPISTS AND THE VICTIMS da kuma shuwagannimu, Dan Allah matasa aji tsoron Allah kar ka b'ata rayuwar da baka san yanda aka jima ana ginata ba Ka tuna idan baka haifah ba meyuwa ka haifa a gaba idan Allah beyi zaka haifah ba toh bazaka rasa 'yan uwa wanda nasan bazaka tab's so kaga wani yayiwa naka wann cin zarafi ba, Oh my Brother in Islam ka tuna whatever goes around comes around Dan Allah mu kiyaye......... , 'Yar uwa wanda wann mummunar tsautsauyi da k'addara ya apka maki kar kiyi fushi da lamarin ubangiji kar kice shikenan baza kicigaba da rayuwa ba kaman da although it's very difficult but don't worry Allah is with you, you'll never be alone, give your self a chance to live.. And Don Allah a ringayin gaggawar Sanar da hukuma idan irin haka ta faru don taimakwa wajen tsayar da b'arna....... "Ku kuma jami'an tsaro kuji tsoron Allah ku ringa hukunta masu irin wann aiki da irin hukunci da aka tanadar domin su, idan kun tawye hakkin 'yar wani ku sani Allah bazai barku ba don baya hukunci da zalunci....... Allah Ya kawo mana k'arshen wann musiba a doron k'asa.. Ameen*
"Jiki a sanyaye ya k'arasa cikin parlorn, ga mamakinsa Hamma Habibu ya gani zaune k'asa gefen Alh Kasim, daga gefe kuma saman kujera Lamin masallacin Alh Kasim ne gefe dashi kad'an Alh Jamil ne, d'aya kujera me kallon tangamemen glass door d'in dake parlorn kuwa Alh Maina ne Dad d'in Tariq da Barr Munir ne suke zaune akai...... Jalal yabisu da kallo One by one kafin ya k'arasa shigowa, Hamma Habibu kasa rufe baki yayi sai murmushi yake, gefensa ya muskuta yabawa Jalal,
"Jalal ya d'an sakar masa murmushi kafin ya zauna.....
"Zamansa keda wuya suka soma gudanar da abinda ya tarasu, Hamma Habibu shi yayi alwali wa k'anwarsa Zubaidah yayinda Jalal ya wakilta Alhj Jamil ya karb'a masa auren Zubaidah....!
"Cikin mintuna da basufi biyar zuwa goma ba aka d'aura auren *Jalal da Zubaidah* kan sadaki Naira dubu talatin tare da shaidu kaman yanda yake a tsarin musulunci....
"Hammah Habibu ya kamo bakin rigarsa yana share k'wallan da suka ciko idanunsa, tausayinsa ya hana Jalal motsawa daga yanda yake, kamo hannun Jalal yayi har lokacin na sharan k'walla kafin yace " Ka kulamin da ita bata da kowa a duniyan nan sai ni sai kuma kai a yanzu......"Bai iya ci gaba da maganar ba sakamakon rushewa da kuka da yayi..... "duk wani mai imani a wajen saida ya tausaya wa Hamma Habibu.
"Alh Jamil da Jalal suka rik'osa har haraban gidan, har lokacin Jalal kasa cewa komai yayi ba, dukda ba auren soyayya yayi da Zubaidah ba saida yaji canji a yanayinsa, har Hamma Habibu ya wuce sashensu bai sani ba.
"Kafad'unsa da yaji an dafa ne yasa juyowa da sauri, Alhj Jamil ya gani fuskarsa cike da damuwa.... "D'an bubbuga kafad'un Jalal yayi kafin yace "Jalal Allah ya saka maka da mafificin Alkhairi..... Jalal bai iya cewa komai ba sai kallon da ya bisa dashi.... Har Alh Jamil ya wuce gidansa dake manne dana d'an uwan nasa Jalal bai daina kallonsa ba, A hankali kuma ya maida dubansa ga sashen su, Jiki a mace ya soma tafiya zuciyarsa ta shiga tambayarsa "Anya hukuncin da ka yanke kayi daidai, wata zuciyar ta shiga k'arfafa masa gwiwa kan cewa wann shine hukunci mafi kyau, Allah yaga niyan ka bazai barka haka nan ba , da wann tunani ya isa sashensu wato BQ..
"Zaune ya taddata ta had'a tagumi komai ya faru kaman a mafarki, komai ya faru all of a sudden, ta kasa gasgata lamarin wai Jalal d'inta yau yayi aure, tabbas abinda ta jima tana son gani kenn dukda ba wani girma can yayi ba.. Saidai auren yazo ba ta yanda tayi zato ba, snn a halin da ake ciki a yanzu batasan makomar auren ba....."Zaman da yayi gefenta ne ya katse mata tunaninta......
"D'ago ido tayi tabb k'walla tana kallonsa shima k'wallan ne a idanunsa..... "Bud'e baki yayi zaiyi magana Annah tayi saurin rungumesa, rungumeta shima yayi sosai gaba d'aya suka soma hawaye...
"You did the right thing son, Allah albarkaci rayuwar aurenku, maza tashi kaje kaci abinci....
"Mik'ewa yayi da k'yar tamkar maras laka a jiki da k'yar ya iya furta na k'oshi Annah wanka zanyi yanzu daga haka bai kuma cewa komai ba ya shige d'akinsa.......
"Yana tsaye jikin mirror bayan ya fito daga wanka , ya k'urawa tabon dake gefen cikinsa ido tunani iri da kala suna yawo a kwanyarsa, kaman daga sama ya soma jiyo hayaniyar mutane, babu shiri ya k'arasa jikin window ya d'an jaye labule kadan yana lek'ewa......
"Mummy da Hadiza ne rik'e da ita, Fuskarta a kod'e alamun taci kuka, da gani basai an fad'a maka dole aka mata ba, k'irjinsa ya shiga bugawa da sauri da sauri, juyawa yayi babu shiri gamida zama bisa katifarsa. Har lokacin k'irjinsa bata daina luguden da take ba......
"Annah ta fito domin tarbansu, Hadiza kuwa sai yab'a mata habaici da mugun kallo take, Mummy tayi saurin jan Annah uwar d'aki don tattaunawa.
"Ina d'an naki yake, ya fito ya kaimu gidan da zamu zauna, don nauyi ne sosai ya hau kansa, tunda ya iya danne d'yar mutane ya keta mata haddi na tabbata yayi girman ya d'auki d'awainiyar mutane da yawa....... "Jin wann kalamai na Hadiza yasa Zubaidah sakin wani k'ara gamida kame kanta, tak'urewa tayi can k'arshen garu tana kuka gamida k'ank'ame jikinta sosai, duk k'ok'arin dasu Annah suke abu na neman fin k'arfinsu, duk wanda ya nufota ihu take sakewa tana matsewa cikin garu..
"Daga d'akinsa yake jiyo kukan nata, dafe kansa yayi sabida zogi da yaji zuciyarsa na masa, cikin sauri ya fice daga gidan dukda dare ya d'an soma ja......
"Suna tsaye gate din gidansu Labib suna shirin tafiya gidansu Kausar suka hangosa, shima kallonsu yake daga yanda yake tsaye.......
Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:14] +234 803 619 0581: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*
22
*©Sameena Aleeyou.... ✍🏾*
_Queen Samy Novels Forum...📖📚_
*Dedicated To All Victims Of Rape*
"Cikin sauri Labib yabi bayansa...
"Jalal pls mana let's talk Buddy, I promise I won't take much Of your time....."Hannunsa yasa ya rik'o hannun Jalal guda d'aya wanda ya hanasa ci gaba da tafiya....
"Kallon hannunsa yayi yanda Labib ya rik'e gam kafin ya d'ago rinannun idanunsa yana duban Labib, a hankali ya furta "Let go of my hand......
"Girgiza kai Labib yayi kafin yace " No Jalal, I won't let you go until we finally talk, for goodness sake Jalal we can't go on like this, I.....I know bamuyi daidai ba but please let's reconcile our friendship....."D'aga masa hannu yayi alamun dakatarwa, murmushin takaici yayi kafin ya soma fad'in"
"Labib Dasuki, You and I have nothing to talk about, I already made my decision and I didn't ask for Opinion.
"Kunyi abinda kuke so sabida kunada masu tsaya maku a wann rayuwar, kunyi destroying innocent soul, kun b'ata mata rayuwarta sabida bata da mai tsaya mata a rayuwa, kunyi amfani da k'arfin dukiyar da kuke dashi kun rufe bakin kowa, even the girl who's suffering right now bata da ikon kare kanta, sabida nasan Alh Kasim bazai tab'a bari tayi magana ba fine... Amma ka sani baku k'arfin Allah ba, And let make this clear to you,...."Dafa kafad'an Labib yayi kafin yaci gaba da fad'in" I didn't marry her because I wanna cover up for You, No! Na aureta ne to save her life, to help her continue living, and also to PROTECT her, Snn na rantse da Allah I'll never leave her side for as long as I will live.... Da d'an yatsansa yake nuni kan k'irjin Labib kafin yaci gaba da fad'in
"And let me give you this message ka isar ma sauran abokan naka da kai kanka and also to your so called uncle, Zubaidah is now mine, she's now my wife,....."Ya d'an ja fasali kafin yayi wata murmushi da bazakace ga nufinsa ba kafin yace " You don't Owe me any Explanation... Daga haka ya wuce ba tareda ya kuma cewa komai ba....
"Shafe fuskarsa Labib yayi da hannunsa gamida fuzar da iska.
"Sai sann Salim ya k'araso yana masa alama da ido kan me ya faru. Gajeren tsaki Labib yayi kafin yace " Let's get going Salim,...
"Kallonsa Salim yayi kafin yace " Wait just wait Labib, tell me what exactly you guys discussed, and... And ka fad'a masa kar yacewa Kausar komai gameda wann mess d'in in case she ask him? Huh? Com'on Salim say something.......
"Foz kawai Labib yayi yana kallon Salim cikin zafin nama yake bud'e hannayensa yake fad'in " Enough, enough of this Salim,, for God's sake be a man for the first time, haba haba I can't stand your attitude of always being Mama boy, be responsible for once, kai da anyi magana Kausar Kausar, Baka tunanin wann abun can also ruin our reputation so as our parents, you always think of your relationship with kausar, enough of this, kai wllhi na fasa raka ka ma, inaga nan gaba hiranma ni zan ringa maka...... A zuciye ya wuce ya nufi k'ofar gidansu.....
"Gajeren tsaki Salim yayi gamida dukan tayan motarsa da k'afa yana first shitt!!! Cikin gida ya nufa gamida cilla wa security guda d'aya car keys d'insa yace " Get my car in.....
"Sashen mummy ya nufa sai ture turen baki yake kaman.... Sak spoiled child.
*************************
"Gida ne d'an madaidaici mai d'auke da d'akuna hud'u sai brander a tsakiya, daga can gefe kuwa kitchen. D'aya d'akin daga can gefe yake tamkar d'akin samari.....
"Tun daga waje yake jiyo hayaniyar Hadiza ta yanda take shiga bata nan take fita ba,....
"Ke ki bud'e kunnuwanki da kyau kijini wllhi tallahi sai kinyi k'aura zuwa d'akin mijinki, uban me zaki zauna ki mana, kokuma raba yayan naki zamuyi nida ke,...... Iyakacin abinda ya iya jure ji kenn cikin sauri ya nufi d'akin Annah....
"Zaune ya tadda ta da alama taji komai itama, murmushi ta sakar masa kafin tace " Shigo Son. Babu musu ya shigo gamida zama gefenta. ....
*Manage this, zakujini later insha Allah...*
0 comments:
Post a Comment