AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
Bismillahirahmanurrahim
Aysha A bagudo
Page 1-2
Lekki Unguwace mai dauke da karancin mutane da suke rayuwa acikinta ,a silent place, saboda bata cika hayaniya mutane ba , dauke da tarin sanyin ni'ima mai dadi sakamakon kusancinsu da ruwan teku" unguwace da tattara kan manya ma'aikata da kusoshin gwanati, hade da manyan masu kudi ,ga tarin yan yahoo boy'z domin mafi yawancisu sunfi sha'awar zama acikinta. rayuwar mutane unguwar abin sha'awa bbu ruwan wani da wani domin suna rayuwasu ne tamkar a kasar waje .
PLASNUW ROWS FAMILY ESTATE
Estate ne mai dauke da tarin dangi acikinta , hadin kai tattare da zaman lfy, Sam bbu hayaniya acikin wannan family kowa kagani cikin nishadi da farinciki zaka gansa ,ga tsantsar fahimtar juna dake tsakanin wannan family. kwakkywan family ne masu matukar kaunar junansu .
Let alh Muhammed bello khaliyal ,haifafen garin Lagos ne ,Amman asalinsa fulanin khaliyal ne dake jahar kebbi. sananne mai kudi ne yayi tashe tun alokacin da duniya ke kwance. sannan kuma take zaman lfy, marigayi Muhammed bello soldier ne daya taka rawar Gani a kasar nan .
ya rike mukamai da dama a wancan lokacin. ya rasu yabar tarin dukiya da da ya'ya da jikoki bila adade.
gabadaya family Muhammed bello bbu talaka aciki domin sun gaji dukiya mai tarin yawa daga mahaifinsu .
kafin rasuwarsa dake shine babba a dakinsu kuma Allah yabashi tarin dukiya da en'uwan , dan ganin ya inganta rayuwar kannensa kafin daga baya ya Gina wannan katanfarin estate din mai mazan kanta.
ya tattara kan yan'uwasa suna zaune a ciki ,yana da mata hudu hjy shema'u wacce aka musu aure tun saurayi da budurwa tana da ya'ya goma Sha biyu, mata takwas maza hudu sai hjy hauwa mai dauke da ya'ya goma maza biyar mata biyar ,sai hajiya rabi mai ya'ya takwas maza biyar mata uku sai hajiya Fatima wacce suke kira da hjy shuwa itama tana da yaya takwas mata bakwai namiji daya .
bbu abinda bbu acikin wannan estate din kama daga makarantar islamiyya wajen wasa buga kwallo wajajen exercise wajen swimming pool library Sannan ga wani katanfarin Holl dake gefe wanda aka shiryashi da kayan kyale kyale zagaye da kujerun zama . an ginashine saboda taron sada zumunci , wanda zasu dinga yi a duk karshen wata .
haka suka taso har zuwa girmansu cike da son junansu .
anan cikin dangi mazan suka zabi matan suma matan suka zaba akayi bikinsu anan cikin estate din suka zauna tare da iyalinsu har zuwa sanda tsufa yacima marigayi Muhammed bello yayi retire.
yayinda ya'yansa da ya'yan en uwa suka cigaba da kula da estate din .
a lokacin aliyu da habib ne kadai suka rage da basuyi aure ba saboda karatu .
Byn rasuwar marigayi bello ne aka raba gado aliyu ya dukufa gurin juya dukiyarsa ,ba abinda yasaka a gaba sai neman kudi wanda acikin kankani lokaci ya gawurta yayi fice yayi suna a duniya, yayiwa sauran yan'uwansa zarra aliyu ya mallaki tarin dukiya da shi kansa bai san iyakarta ba. hade da tarin compenis a Lagos da kudancin Nigeria yana da gidajen saida man petir Bila adadi shine mallakin aliyu airlines yana da hannu jari da dama a compenis na kasashen duniya yana da gidaje a abuja da sauran garuruwa .
tsananin neman kudinsa ne yasa bai ajiye iyali da wuri ba ,burinsa bai wuce ya auri mace mai matukar kyau da tarin illimi ba .
Garin neman kudinsa ne ya hadu da fadila a india tun daga lokacin da aliyu ya daura idanunshi akanta "ya dauki son duniya ya daura mata kasancewarta kyakkywa gaske ga tarin illimi . fadila itace Diya ta biyu a gurin iyayenta su uku ne , ahmed ne babba sai ita sai farida , kin amincewa iyayenta sukayi da auren shi a cewarsu bako ne sannan kuma bakin fata. sai da aka kai ruwa rana dasu sannan suka amince da auren .
koda yazo daita Nigeria ma bata wani sha wuyan zama cikin family dinsa ba .
kasancewarta mace mai tsananin son jama'a da son yara cikin lokaci kadan tashaku da sulaiman da mahamud ya'ya ne ga yayyen aliyu sun shaku matuka da yaran ta daukesu tamkar ya'yan data haifa acikinta .
suma kuma suna maseefar kaunarta dan haka suke kiranta da ummi ,duk abinda suke so itace take musu bata ragesu da komai ba saboda bata da rowa hakan ne yasa ta sake janyo mata soyayya ta daban a gurin iyayensu.
shekarata biyar da aure mutuwar mahaifiyar ta risketa ,zuwan datayi indiya ne dazata dawo tazo da kanwarta fadila ta hada dasu Mahmoud tacigaba da rikonsu .
sai da fadila ta dauki sama da shekara takwas da aure sannan tasamu cikin murna a wajen wannan family bai faduwa .
cikinta na da wata tara cif ta haifi NASURUDEEN daga ita har aliyu suna matukar son DEENI tamkar numfashinsu DEENI yataso cikin gata da kulawar iyayensa, da dangi gabadaya suna nuna masa tsansar gata da soyayya fiyye da tunanin mai karatu .
shiyasa yataso a shagwabe a sangartacce saboda kaf estate din kowa yasan da zaman DEENI babbar matsalar da suka fara fuskanta da deeni , shine rashin magana da bai yi ,da farko fadila ta dauka ko kurma ne sai daga baya tagane tsabar miskilanci ne kawai yayi masa yawa .
duk tarin ya'yan dake cikin wannan estate din DEENI yafita dabam acikinsu, bashida aboki ,.
gabadaya baya yarda da kowa koda yaushe yana tare da umminsa ko farida ko su Mahmoud tun tasowarsa yake da burin son zama soldier yayinda ummi take bashi goyon baya wajen kiransa soja .
Domin wani lokacin zai je yatasa hotonta marigayi kakansa dake manne a falonsu gaba yayi ta kallo yana shafa fuskar tsohon yana murmushin ,Sam shi bashi da fara'a ballanantana sakin fuska koda yaushe fuska nan tashi a hade take tamkar hadari , .DEENI Nada shekara takwas byn yakare primary school aka sai mishi form din shiga makarantar sojoji ba'awani samu wata matsala ba yasamu sakamakon matsayin mahaifinsa da kakansa. sabanin wayanda basu da gata.
domin a wanan lokacin idan dai kai bawani bane ko dan wani ba ko bakada hanya a military school ,sunanka sorry.
Domin kuwa kana ji kana Gani military school zai gareka shiga .
byn wani lokacin farida ta samu miji anan cikin estate din wanda shima yakasance "Da"ne ga marigayi Muhammad bello wato habibu ubansu daya da aliyu mahaifin ga DEENI .
duk da fadila ta nuna rashin amincewarta matuka , da nuna wa er'uwartata illar aurenta da Habib Amman sai taga yarinya ta nuna tana so abunta ,dan haka ta kyaleta kuma da kunya dai ta fito fili tace batason jinin aliyu ,wanda itama kanta tasan hakan ba mai yiwu bane . itama ba wai shi din ne bataso ba ,halinsa ta tsana ,
Amman shi babban ma'aikace gwanati ne, director of land and housing & same na Lagos state gabadaya. yana da mata biyu da yaya bakwai farida ce ta uku .
Ko alokaci daya auri farida takasance mace ce mai tsananin hakuri .
duk da mijin nata Vai kasance mutun mai adalci ga iyalansa ba. Amman bata taba kawo kararshi ga ummi ba domin tasan halin ummi Sam bata son raini .
Shekarar da aka yiwa sulaiman da mahamud aure shekarace Allah yayiwa mijin ummi rasuwa wato alh aliyu Muhammad bello sunji matuwar farar daya , mutuwar tayi matukar gigita ummi dan byn ya dawo daga sallah asuba ne yayi irin kishingide nan yana lazimi koda ummi taji shiru shiru bai sake fitowa ba Sannan bai nemeta ba kmr yadda ya saba , wanda aldarsa ce da zarar gari yayi sha ...yake fitowa ko yakirata a waya Amman taji shr .
tashiga dakin nasa ta tarar dashi kishingide da carbi a hannunsa .
da fari ta dauka ko bacci yakeyi sai tayi nufin ta tasheshi yakoma kan gado.
Ammai sai taga alamun rashin motse atare dashi takai hannuta wajen hancinsa da karjinsa a lokacin daya taji baya numfashi.
take ta zube anan ta sume.
har a kashare zaman makoki ummi batasan a wani hali take ba ,dan bata cikin haiyacinta' koda ta farfado ma sai da akayi ta hadawa da addu'a Sannan aka samu kanta ta dawo daidai , dan mutuwar ta girgiza har ta kusan zarar daita .
Byn wani lokacin su sulaiman suka cigaba da tallafawa ummi da DEENI a lokacin farida na dauke da tsohon ciki duk da itama ta dan jima bata haihuwa ba, kuma har lokacin ummi bata san er'uwarta tana cikin matsala ba ,sai byn data haihu" lokacin ne ummi taga komai bbu alhalin ga tarin dukiya kmr zai kashe habibu , gashi yasake kara wani sabon auren matansa sun cike hudu cif .
ummi tayi kuka kmr may gashi tana cikin danginsu da suke tamkar tsiya madauri daya.
ba daman tace zata dauki wani mataki akan haka .
dan tasan yadda kansu yake a hade .
dan haka taci kukanta takoshi ita da er uwarta ahankali take furta kalmar shiyasa tun farko naki amincewa da auren nan naki da habibu ,ba dan komai ba sai dan irin haka Amman kika nace ,ga irin abinda nake gudar miki kennan Amman kika kiji , sai kuma ta tsagaita da kukanta ahankali tace ba yadda zamuyi da ikon Allah ,sannan ga rabo a tsakani.
Amman duk da haka sai da ummi tayi masa tatas saboda daman ita bawani sakar masa fuska take ba kuma yana shakkata.
kullum ummi acan take wuni har ranar suna yarinya tace sunan mahaifiyarsu ummi wato muzeenat , shima habibu yayi hakan ne saboda ya wanke kansa a wajen ummi,kuma yayi nasara domin hakan da yayi yasa ummi taji dadi Sosai aranta har ta dan rage jin zafinsa .
sannan bakaramin kudi ummi takashewa bby ba. haka ma ranar suna ummi Tayi rawar Gani sosai .
byn anyi suna ne ummi tasamu habibu akan dan Allah ya dinga kula da farida dan ita kadai gareta bata da kowa duk fadin Nigeria sai ita, idan ma bazai damu ba, zata bashi Rabin dukiyarta yakara akan nashi da duk wani abinda yake so, ita dai burinta kawai ya kular mata da er,uwa ,yayi murmushi kawai hade da ce mata yaji .
Byn wani lokacin farida ta kuma samun wani ciki wanda tun yana karami take fama da laulayi tun lokacin ummi tadawo da zeenat wajenta ,
a kwana a tashi bbu wuya a gurin Allah har cikin farida ya isa haihuwa gurin haihuwar ne taji jiki sosai .
koda ta haifi yaron ma bbu rai sannan itama tace ga garinku .
mutuwar ta shigi habibu matuka yayi kuka tamkar ransa zai fita ,dan shi kansa yasan yayi babbar rashin da ba zai taba maida irinsa ba.
yayi rashin mata mai tsananin kirki da hakuri da sanin darajar miji . Allah sarki ummi kusan har tafi habibu jin mutuwar tilon er'uwarta ta ,.
a wannan Lokacin ne rikon zeenat ya dawo dindindin gurin ummi ta dauki soyayyar duniya ta daurawa zeenat tana mugun ji da Yarinyar tamkar ranta kwata kwata bata son abinda zai rabata da zeenat Sannan kuma tana debe mata kewar er'uwarta .
lokacin shi DEENI na ss1 a NMS, Nigeria military school dake zariya.
yayinda DEENI Sam ba halinsu daya da ummi ba koda yaushe kagansa fuskar nan tasa a daure a cunkushi bbu wani fara'a ga shegen miskilanci tsiya sai dai mugun kyakkyawa ne na karshe . ajin farko, wato first class ,gashi da maseefar iya sa kaya kallo daya zaka masa ya gigitaka kaji yashiga ranka farar daya saboda tsabar kyawunsa sai shegen shiga ran mutane domin kusan yan'mata cikin estate din suna maseefar son sa yayinda yake girma kyawunsa na sake bayyana hade da miskilancinsa .
Tunda zeenat ta dawo gidan magana bata taba hadasu ba ko gaisheshi Tayi baya amsawa in dai bayaga idanun ummi ba yana da matsanancin tsafta wanda kusan a wajen ummi yagada .
Cikin haka ya kammala karatunsa na secondary school ya wuce NDA burinsa kennan nason zama cikakken soja itama ummi kuwa nasake karfafamasa gwiwa da bashi goyon baya yana karantar science ne ,wato likitan soja .
bansan yadda zan kwatanta muka halinsa ba Amman yakasance mutun ne shi mai bambanci ra,ayi.
byn yakare karatunsa ya fito da mukami second lieutenant star biyu kennan .
Zaune zeenat take a falo tana kallon wani serisfilm a zeeword my let home Tayi zurfi cikin kallon film din gabadaya attention dinta naga kallon ita kadai ce ummi tashiga cikin estate din yin barka taji karar Bell wanda shine kusan karo na hudu da taji ana dannawa. cikin jin haushi ta mike dan bata son abinda zai dagata daga kallon datakeyi , tana bude door din bata tsaya ganin kowaye ba ta juya abinta takoma mazauninta sallama taji hade da shigowa ta dago kanta kennan da niyar amsa sallama sai taga mutun tsaye kikam sanye da sabon kayansu na sojoji gabadaya zeenat ta gigice hade da rikicewa tsabar tsoro dan ita Allah yayita da maseefar jin tsoron soja take cikinta ya dauki kugi Amman still idanunta na kansa ta tsaresa da kallo .
in ina tasoma yi wa..wa.. waalai....ya dakatar daita da hannushi, yana zabga mata wata uwar harara muryasa a kwasashe yace yau ne kika fara ganina da har zaki wani tsareni da idanu Kona canza miki ne ?da sauri tasoma girgiza masa kai. Kai tsaye dakin ummi ya nufa tunda bai ganta a parlour ba yasan tana dakinta tana kallonsa ta kasa dauke idanunta daga garesa har sanda ya dawo fuskar nan tasa a hade yace ke.....dan iskanci kina kallon mutune bazaki iya cewa ummi bata nan ba kin wani tsare mutun da idanuwa tamkar na maciji ,dayake bawani manyan idanu gareta , da sauri bakinta na rawa tace dan Allah kayi hakuri mantawa nayi ko kallonta bai sake yi ba yaja tsarki yayi hanyar dakinsa ta tabe baki hade dacewa jarababbe kawai ai yadawo kennan, itama taja tsaki ta juya tacigaba da kallonta ..
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
Aysha A bagudo
Page 3-4
Sai da tagama kallonta tsab Sannan ta canza Chennal hade da tashige kitchen dan daura abinci abincin dare
bakin kofar kitchen din ta dawo Tayi tsaye abunta tana cigaba da kallonta Chennal data canza, ajima ajima tana zuwa tana duba abinda ta daura.
Karar bell taji ba kaukautawa shiyasa da sauri taje ta bude gudun maseefar DEENi dan tasan muddin yana gida baya son yawan hayaniya , yanzu ne zai gama daita, Maryam tagani tsaye da wasu en school dinsu su biyu tuni murna yakama zeenat ,ta rungume su daya bayan daya tana musu sannu da zuwa hade da basu hanya "suka shigo har cikin main parlour din hade da Sallamar su .
waje ta nuna musu da hunnu kuzauna mana suka zauna ita kuma takoma kitchen ta duba abinda ta daura taga yayi ta kashe gas din sannan ta dawo inda tabarsu hade da kawo musu drunks mai tsanyi da snacks ta ajiye agabasun .
gabadaya hayaniyya ce ta barke a atsakaninsu da murna ganin juna ,zeenat ta kalli su Sumy hade dayin kasa kasa da muryata tace kuyi magana ahankali fa sannan tace kun kyauta sai yau kuka ga damar zuwar mana , Sumy tace ba gara mu ba muna zuwa time to time.
kufa sai aikin sa rana kullum, hira suka shiga .
a inda Maryam ta dube zeenat tace wai nan fa IV suka kawo mana na birth din rukky, zeenat ta zaro idanu waje I ....me Maryam tace IV .
zeenat Tayi dariya hade da cewa uhmm badani ba" kema kinsa sarai baza'a taba barinmu zuwa wani birthday party ba " Sumy Tayi murmushi sannan tace ai sai da nagaya rukky Amman tace ga zance ga magana " gashi nan, ni ai nasan bazakuyi attending birthday party dinta ba ,da day itace sarkin shishigi da neman suna , zeenat tace kmr kinsani ,duk abinda ya wuce cikin gidan nan namu "ta girgiza kanta baza'a taba barinmu ba ,ki bata hakuri kawai Amman wlh har ga Allah naso zuwa ko dan rukky Sumy tace to why nut ku sace hanya kuje a boye batare da kowa yasani ba ... zeenat ta kalli Sumy fuskarta a hade tace kefa kin cika matsala fa wlh.
kmr bada hausa nake miki magana ba.
ta bude bakinta kennan da niyar sake balbale summy.
sai ga DEENi ya sake fitowa parlour jikinsa sanye da jallabiya marun colour may maseefar kyau sai kyalli take zuwa ga kamshin turarensa mai mugun sanyi dadi wanda tun tasowar zeenat ta sanshi da auren Hamilton har yanzu fuskarsa a daure take tam .. kmr koda yaushe " take ta hadiye maganarta batare da tasan Tayi hakan ba ,ta zuba masa idanu tana kallon kwayar idanunshi, sai data ya hararata, sannan ta dauke idanunta ,ta maida kallonta da hankalinta kacukam a kansu Sumy dake zaune surusuru. Yayinda gabadaya Maryam duk ta fisu tsurewa ko dan ita Yar gidan ce oho..
cikin wata irin murya mai sanyi dadi tamkar ba soja ba yace ke......ta juyo ta ahankali ta sake zuba masa idanunta dan tasan dai daita yake dan haka tabada duk attention dinta garesa.
bakisan kibawa mutun abinci bane ? Dan iskanci sai an roka ,zatayi magana ya katseta a fusace , ai ba tun yanzu nasan ke muguwar rowa ce dake ba Tayi surusuru da idanu ,da sauri tace kayi hakuri dan Allah nayi zaton ko kana azumi ne "naga kullum kana yi "
yace "oh "dama kinsa min ido ne har kinsa cewa azumi nake kullum ?
Jikin Maryam har rawa yake ,a hankali tace wayoo Allah ashe ya dawo ,bari in gudu tun bai gama daita ya da kanmu ba , zeenat tayi shr har sanda ya sake maimaita tambayarsa hade da cewa dan ubanki bada ke nake ba kike bina da idanu kmr zaki cinyeni" ta sake girgiza masa kai,. Tana bashi hakuri
marowaciyace banza kawai mai mugun gado. shiru yayi na dan wani lokaci hade da sauke numfashi .
Sannan can kuma yace ai idan bakiyi rowa ba sai Allah ya tambayeki" km baza'asan ke...Yar uncle Habib bace .
kin taba ganin barewa Tayi gudu danta yakasa rarrafe" zeenat ta sake girgiza kai da sauri ,yace OK ashe dai kema kinsa gaskiya dole kiyi gadon rowa.
Ganin haka yasa su sumy suka nemi sulalewa duk yana kallonsu sai daya ga Maryam na shirin gudu itama dan har summy ta daura hannuta kan handle din kofar ,ya dakatar dasu da hannusa , sannan yacigaba duban zeenat yace barikiji da kyau yana mai nuna da yatsansa" nan ba gidan marowata bane gidan masu bayarwa ne aci . yace menace ? Da sauri tace gidan masu bayarwa ne.
yace gud daga yau bama ni ba ,ko wani ki kaga yazo gidan nan ki bashi ruwa da abinci yaci dan ba naki bane.
ya sake jiho mata wata tambayar yace ko abincin naki ne?, da sauri ta girgiza masa kai dan gabadaya ta sure ta kasa kwakwaran motsi sai ajiye zuciya kawai take yi , yace" baki da baki ne kike kadawa mutane kai , tace naji kayi hakuri dan Allah. Sannan ya juya kan Maryam da kadan ya rage ta fashe da kuka , ya zuba musu ritattun idanunsa da suka fi kama da mage masu saurin raunana mutun kai tsaye , yace ku kuma en iskanci banza kun wani cikawa mutane kunne da hayaniya tamkar kuna club ,kallo daya yayi musu kowace tabawa kafarta iska yaja tsaki ya juya ya nufi dakinsa.
ahankali zeenat take sauke ajiyar zuciya hade da dafe kirjinta , batasan meyasa ba ,idan har Yaya DEENI yana guri Sam bata samun cikakkiyar natsuwa "sai tarinka ganin duk yacika guri ga tsananin tsoransa da take ji yana mamaye zuciyarta . Maryam har da kuka tayi byn sun fita dan daman can ita haka take ,shegen tsoro gareta aiko, su sumy suka ce mezasu ba dariya ba dariya suka dinga yi har da rike ciki suna nuna ta aiko tace yau sai da suyi ta zama a estate din dan bazata rakasu gun securities ba sai da sukayi ta bata hakuri sannan suka jera suna hirar abunda ya faru.
Ko lokacin da ummi tadawo tuni murna da farinciki Ganin tilon "dan " nata yamamayeta zuciyarta nan suka zauna a parlour suna hira cikin hirar ne ummi take masa maganar aure in da tace masa yakamata yanemi mata yayi aure kasan shekararka nawa kuwa yanzu ?yayi murmushi ai dole nasan shekaruna ,muke nan kullum cikin rubuta date of birth ,talatin da biyu ne kawai fa ummi Tayi dariya 32 din ne kawai kusan duk sa'annin haihuwar ka duk sunyi aure acikin estate din nan gasu yasir nan ma duk ansa musu rana dan haka kaima ka fidda mata kafin azumi DEENI yazaro idannu yana bin ummi da kallo a shagwabe yace haba first love dan sunan da yake kiranta dashi kennan tun tasowarsa .... ni din guda nawa nake da zakice inyi wani aure yanzu. Dan Allah kiyi hakuri my first lov zuwa wani lokaci ,duk hirar da suke zeenat na zaune tana jinsu haka kawai taji gabanta na faduwa lokacin da taji abinda ummi tace ,Amma jin amsar da yaya DEENI yabata yasa taji wani irin sanyi na ratsa zuciyarta .
kmr ance ya dago idanunsa suka sauka cikin nata harararta yayi yace kallon fa kin wani tsare mutun da idanu, ummi tace uhmm kafa dawo kennan karka takuramin yarinya ,
ya langwabar da kansa yana maida idanunsa kan ummi cikin sanyi murya yace haba first lov baki ga irin kallon da take bin mutune dashi bane, kmr bata san mutun ba , ummi tace kai da wani idanu ka kalleta har kasan tana kallonka. kuma ma ni banga komai ba kai dai ta kurace kawai dakai indai kana gida baka barin yarinya nan ta huta ta sarara , ya dubi ummi ya tabe baki , Sannan yace ke....kawo min coffee ,ta mike taje ta hado coffee din takawo masa gabanta na wani irin faduwa ta durkusa har kasa ta ajiye masa .
Adaidai wannan lokacin ne zeenat ta kammala karatunta na secondary school , ta fito da sakamakon mai kyau domin tasamu almost 7 credit masu kyau .
shi kansa DEENI yaji dadi Sosai sanda ummi ta nuna masa Amman dayake miskili ne, sai cewa yayi Sam shi bai ga wani kokari da Tayi ba tunda bata cinye duka ba .
ummi Tayi murmushin tace kai ne dai bakaga kokarin ta ba. Amman ni nagani km nasan Tayi kokarin Sosai .
Ina laifi duk cikin wayanda suka rubuta jarabawa tare bbu wanda yakaita marks ,.
yace ok inda ta cinye duka ne zan iya cewa Tayi kokarin ai wayanda suke cinye 9 credit ba finta brain sukayi ba.
Ita dai wasa da kallace kallacen banza tasa a gaba.
ummi ta hade fuska tana harararsa yacigaba da zagin zeenat ganin yadda ummi Ta canza fuska ne ,yasa yabar maganar , ummi ta sake duba result din tana shafawa hade da kwallawa zeenat data tashi tun sanda taji DEENi yasoma zaginta kira ,takaraso tazo ta tsaya kusa da ummi DEENi ya dauki wayarsa yana daddannawa ba ko kalli inda take ba ummi ta mika mata slip din tana murmushin tace kinyi kokari sosai , zeenat ta karba ta juya ta bar gurin dan bazata iya zama a duk inda yake ba .
ummi ta dubi DEENI tace yanzu kuma sai aure zanwa zanwa yarinyata .
DEENI ya juyo a sukwane yace wani irin aure kuma first lov da rana tsaka , kudai Bari yarinya tacigaba da karatu kawai" dan yanzu kai yawaye , an daina irin wannan auren, ballanantana mata marasa illimi "ummi ta dubesa da kyau ta numfasa Sannan tace ni tawa iya secondary zan aurar daita dan ma taki sauraran masu sonta . itama shegen iyayi ne daita kuma dai kasan matan wannan family din basa wuce secondary ake musu aure .
kuma kasan baza'a fara karatun jami'a daga kanta ba, uhm nima nafi son na aurar da abita. DEENI ya tabe baki Sannan yace Allah ya kyauta ni ko zanyi aure bazan auren Yar secondary ba wlh sai wacce tagama jami'a mai tarin illimi ,kuma ba auren family zanyi ba dan baya birgeni. yakarasa maganar yana dan murmushi ,ummi tace to Allah yabaka sa'a. amman ni tawa aure zan mata da wuri .
kai kasan halin big dady bazai taba barinka kayi aure a waje ba .
Wlh nasoma a hada aurenka dana su yasir yace uhmmmm su dai yi nasu ni sai nan gaba .
A wata yammacin DEENI zaune akan dadduma awajen shakatawa shi da abokansa wayanda duk kusan , family ne zagaye dashi gefe guda kuma flasks ne cike da ruwan zafi da kananan cups , hira suke sosai atsakaninsu Amman banda DEENI dan gabadaya daukar hirar tasu yake shirme dan duk zance nasu akan maganar aurene wanda shi kuma Sam baya kaunar ji , dan haka ya sharesu yacigaba da lasalasar wayarsa ya yinda ya kai hannunsa daya ya dauki cup din coffee wanda orready fk ya tsiyaya masa ya kai bakinsa yasha hade da rufe rikitattun idanunshi wanda yazame masa jiki fk ya kalli yasir da faysal dake tawowa inda suke, ya kwashe da dariya har suka karaso bai bar musu dariya ba fk yace sannuku da karasowa Mayan angwane kunsha kamshin kunsha kamshin ,faysal yace kai dai anyi dan iskan yaro , kai baka tsaya ruwan ido ba kana biyewa wannan ya nuna DEENI da yatsa fk yayi murmushi yace yayi an gwanen bana wannan karon gabadaya suka dara hannu suka bawa juna suka gaigaisa har DEENI.
yasir ya dube fk yace ai gara muyi aurenmu tunda muna son juna kai ka zauna kar kayi har mahdi ya bayyana ,fk yace A'a nifa bance saboda me zakuyi aurenku ba . Amman gaskiya zaku takura kanku ne kawai yanzu da wani aure wayannan kananan bbys din.
DEENI ya tabe baki Sannan ya dube fk yace shiyasa rawar kan yaran ke kara yawa ba . dukkansu suka sa dariya suna cikin dariyar ne fk har da rike ciki sai gasu zeenat da suka taso daga islamiyya su biyar suka jero kowace sanye da hijab dinta raudat da shemah da samiha da Maryam sai zeenat dake tsakiyar su dukkansu kyawawane .
da hannut fk yake nuna musu inda suke Sannan ya dakata dariyarsa ya kalli inda DEENi ke zaune tamkar bai san abinda ake ciki ba , ko kallon inda suke bai yi ba, yacigaba daddannawa da sarrafa wayarsa .
fk yace kai gaskiya bbys din nan fa su hadu dayawa fa , nima ko zan dan shiga daga ciki ne.
yasir yace dako ka huta , kabar wannan ya nuna DEENi fk ya cigaba A'a ina ai bazan barsa ba tare zamuyi namu auren , ko yakace mutumina kaga Shikenan mun huta da surutu jama'a DEENi ya kallesa a kaikaice yace A'a ku dai da kuka ji zaku iya kuje kuyi Tayi .
Amman ni ya nuna kansa da yatsansa hade da tabe baki, ba yanzu ba" har sanda su zeenat suka zo suka wuce . Suna hirarsu suna dariya Maryam ce ke basu labarin abinda ya faru jiya bbu wanda bai dara ba har ita zeenat din raudat tacewa zeenat ai ke kika daukar masa wlh kuma yarinka yi miki kennan ina ma nice daya gane kuresan suka sake yin dariya .
Tun lokacin daya dawo zance sa da ummi bai wuce DEENI kayi aure fito da mata cikin yan,uwanka kayi aure hirar kennan sai dai idan basu zauna ba .
Yau takama walimarsu zeenat ta saukar alqur'ani mai girma wanda aka shirya musu anan islamiyyarsu dake cikin estate din ,su kusan goma anyi taro walima lfy yayinda zeenat ta karbi kyaututtuka da dama saboda kokarinta har kuka ummi Tayi sakamakon tunowa datayi da er'uwarta taro ya watse lfy kowa yakama gabansa ,byn sun gama hirarsu da ya zame musu jiki suka fara hada kujerun da akayi walimar dasu . sun fito kennan suka ga Yaya DEENI da wani abokinsa zaune akan kujera biyu suna hira ,take suka ja birki samiha tacewa zeenat jeki amso wadan can kujerun, cikin zolaya tayi mata maganar dan tasan yadda take jin tsoronsa zeenat tace uhmmmm ku dai kuje "suka sa mata dariya ke wlh muguwar matsoraciyace wlh ki rage tsoransa shiyasa yabi duk ya renaki ,Tayi sororo tana kallonsu , Sannan tace to bari naje amso Tayi tafiya kmr zata isa gurinsa sai kuna ta juyo da sauri" aiko suka sake kwashe mata da dariya .
muryashi ce ta katse musu dariyar tasu lokacin daya suke kallonsa a frigice" yayinda gaban zeenat yasoma faduwa yace ke....da hannu ya nuna musu alamun suzo 's suka nufo inda
Yake cike da tsoro ya zuba musu rikitattun idanunsa yana kallonsu daya byn daya yana nazarinsu Sannan yace da ganinku akwai alamun rashin gaskiya atare daku ? ya nuna su da dan yatsansa zeenat Tayi saurin cewa A'a cikin inda inda uhm bbu komai fa Tayi gudun Kar wata cikinsu tafada masa shiyasa Tayi saurin yin magana ,to menene na inda inda wama ya tambayeki ?Tayi shiru tamkar ruwa yacinyeta. Sannan ya juya ya kalli abokin nasa da ya zubawa zeenat idanu yana kallonta kafarsa yasa ya take kafar manir dashi ,sannan ya dawo natsuwarsa ya mai da hankalinsa kan DEENi , DEENi ya nuna su zeenat da samiha hade da shemah da Maryam yace gasu nan bansa inda sauran suka nufa ba, manir yace ina tayaku murna walima saukar alqur'ani mai girma, Allah yasa na tsoron Allah ne ,suka hada baki wajen cewa Ameen , kallonsu kawai DEENi yayi jikinsu har rawa yake suka bar wajen.
manir yabi bayansu da kallo yace kai sisters din nan naka fa akwai kyau DEENi ya kallesa yana watsa masa harara ok iskancin naka kuma yau agidanmu zai Kare.
manir yayi murmushi yace Allah barin ma wace ta tsakiyarsu gaskiya duk tafiso haduwa DEENi ya kalli inda ya nuna sai yaga zeenat yake nufi take yaja tsaki manir yace dama ita ka zaba wlh dan nasan karshe ma auren zumunci za'a maka DEENi ya sake jan tsaki dan Allah malam karka dameni da wannan shirme bazan ,manir bai daddara ba ya sake cewa Allah dama tsayawa kayi akayi Yar gida tunda duk tarin matan dake sonka baka kallonsu , a fusace DEENi yayi magana dan me zan kallesu alhalin banda abinyi dasu.
manir yayi murmushi ina ma ni ne kai wlh tsayawa zanyi na kwashi gara son raina har sai nagaji in more kuriciyata , DEENi yace ai kai dan iskanci ne lamba daya , wlh ka guji abinda kakewa ya'yan mutane "ko dan gaba .
ka dauki neman mata tamkar wani abinci, manir ya dan daki kafadar DEENi yace ai sun fi abinci dadi ,.
Amman Allah koni ina son na daina bin matan bazan ,wlh abun ne da kmr wuya Amma kacigaba da yimin addu'a . DEENi ya nuna sa kai zanwa addu'a saboda banda abinda zan roka Allah , manir ya dage masa gira daya yes meye dan kamin addu'a kaga idan Allah ya shiryani sai kabani wacce Yar dimadimar sister din taka na aura , bai kulasa ba sai canza zance da yayi nan dai suka cigaba da hirarsu har zuwa sanda sukayi sallama da juna .
Abinda zai daure maka kai bai wuce yadda ummi ke sake bawa zeenat kulawa ta musamman ba ,ta kowani part tana iya kokarin ganin ta fito da diyarta ta tsab, zeenat bata rasa komai ba tun daga dangin sutura da mayuka shafe masu tsada zuwa kayan kwalliya ana cikin haka tafiya takama ummi zuwa India dan haka ta tasa diyarta gaba suka tafi zeenat taji dadin zuwansu India tamkar karta dawo ,watan su daya suka tattaro suka diro Nigeria saboda bikin family dinsu yakusa koda ta dawo ma su Maryam sun dinka mata duk anco din da aka fidda tunda damar suna da telarsu ce da yake zuwa har gida ya karba dinki,.
biki akayi sosai bakama hannu yaro an kashe kudi tamkar ba'asan ciwonsu ba bidia iri kuma a duk anan cikin estate din akayi komai, daga karshe akayi walima washegari ranar Sunday aka daura auren en mata biyar haka ma samarin aka dan kowace gidan mijinta, ya saura mutun uku ne cal suka rage da basu aure ba, Maryam da shemah sai zeena amaza kuma fk da DEENi sai kamil .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
Aysha A bagudo
Page 5-6
Zeenat na da kyau sai dai ba can ba" fara ce Sol Amman batada dagon hanci wannan bai sa fuskarta muni ba" haka idanunta matsakaita ne ita mutun ce mai tsananin son kwalliya wanda ko alwala Tayi sai ta sake yin wata sabuwar kwalliya, haka nan ummi bata gajiya da siya mata kayan kwalliya iri iri sannan bata ganin aibunta a duk lokacin da zata bata a gurin yin kwalliyar .
abinda kawai bata so kuma bata yarda dashi ba, shine a yimata dinkin da zai bayyana surar jikinta ,nan nefa tace bazata bada goyon baya gurin bata kamasho yada zina ba , dan a cewarta shigar da yawancin ena'mata keyi a wannan zamani itace ke sake haifar da fashadi a doron kasa.
zeenat akwaita da saurin sabo da mutane sannan km tana da son kawaye ita da Maryam dan ko yanzu suka san mutun ko km kuka hadu dasu sanadin wata kawar, Shikenan sun zama kawaye , shiyasa suka fi dukkan sauran en'uwansu jama'a dan daga waje ma zuwa ake gurinsu sabanin sauran" kullum kaga ana rikinci a bakin get da sune , gurin shigo da baki most especially ma na school dinsu. abinda ummi tafi tsana kennan daga gareta yawan tara kawaye gata da matukar son gayu ,da son kallace kallacen film muddin tana gida kuwa bata da aikin yi sai na kallo ,daga wannan Chennal zuwa wata ,sai dai duk da wannan halin nata Allah yabata illimi sosai both arabic & school.
Daidai misali Allah yayi mata farin jinin samari masu sonta daga waje ma biyota akeyi, sai dai bata fita dan ma ummi taki yarda tafara zance da wuri sai data kai ss2 kuma duk masu zuwa gurinta da aure suke sonta "amman matsalar dai daya ce family dinsu basa yarda da macce Tayi auren wajen Amman sukan bar namiji.
kana duk masu son nata bataji son su har cikin ranta 'har wani lokacin ummi kesata gaba da fada "tace maza ki tsaya ruwan ido daga karshe kirasa kowa kizo kina nema yawan yi mata fadan da ummi keyi ne yasa ta tsaida kamil dan gwaggonta" yayar mahaifinta da suke uwa guda uba guda .
shima bakowa yasan suna tare dashi ba , dan bata gama tantancewa aurensa ba" kuma shi bai fiyye zama a garin ba yana aiki ne a abuja ". haka kawai taji idan bata samu wanda yafi ba , zata iya aurensa dan shima ba laifi .
Jiki da jini wata safiya ummi ta tashi da ciwon ciki , wasa wasa tun tana daurewa har abun yafi karfinta gabadaya tafita haiyacinta' hankalin zeenat yayi mugun tashi dan bazata manta yawan labarin da ummi ke yawan bata na mahaifiyarta da irin wahalar da batasha kafin mutuwarta ,ciki har da cewa mata Tayi ta bude ido ta zabi miji wanda zai san mutuncinta kar taje gurin ruwan idonta ta kwashi gaibu ,shiyasa take massefar jin tsoron haihuwa da mutuwa dan ta kudircewa ranta, ta amince da mutuwa tunda tasan muddin kwanakinta suka Kare Shikenan "amman ita kam bazata yarda da haihuwa ba ganinta garata tasha wahala daya .
wunin ranar da ciwo ummi ta wuni can kuma tasamu sauki dare nayi ciwo ya sake dawo zeenat taso zuwa ta sanar da DEENi Amman ummi taki .
washegari DEENi yashigo da shirin fita aiki dan bai san bata da lafiya ba koda yashigo dakin yayi matukar girgiza da ganinta kwance cikin bargo da kyar take iya magana a rude yakaraso inda take ya tambayar ba lafiya ne ? Ummi tace eh tun jiya yace meyasa baki sa an tashe ni ba ,ya kalli inda zeenat ke rukube kusa da ummi duk tazama wata kalar tausayi.
ke....Wace irin" sakariyace da baza ki iya zuwa kisanar min ba da kyar ummi ta iya bude baki ,tace ni na hanata ya furzar da huci ta bakinsa hade da cire hular kansa yayi wurgi dashi gefe ,take ya Ciro waya cikin aljihun bayan wandonsa yakira family doctor dinsu wanda side dinsu kawai yake dubawa.
mintina kadan sai gashi likinta dayake bai da Nisa dasu cikin sauri yashiga duba ummi sosai har drip aka sawa ummi a ranar DEENi kasa fita yayi koina byn likinta ya wuce ne, ya kirasu ya Mahmoud ya sanar masu da ummi fa ba lfy , idanunta ta zuba mashi tana kallon bakinsa yadda yake maganar ne tamkar wata mace shi yafi daukar hankalinta,
ba taba jin DEENi ya birgeta ba irin na yau.
duk wunin ranar kusan shi yayiwa ummi komai hatta magani da abinci a baki yabata sai gurin la'asar su Yaya Mahmood sukazo tare da matansu sai zuwansu ne ma yasa mutane cikin estate din suka sani dan DEENi bai sanar da kowa ba, shi dai ta mahaifiyarsa kawai yake.
Ai kafin kace me tuni side din ummi yacika da jama'a, haka suka dinga shigowa duba ummi har dare DEENi na tare da ummi yana bata kulawa. duk yayi wani iri cikin lokaci kadan yafita haiyacinsa zeenat na zaune a gefe guda tana jiyo hirarsu rokonsa ummi take akan yayi aure ahankali takira sunansa NASURULDEEN ....abinda yasake tada ma DEENi hankali kennan yaushe rabon dayaji ummi takira complete name dinsa , tacigaba ban rasa komai na rayuwar duniya ba inada tarin dukiya da kadaroro wanda ni kaina basan iyakarsu ba ,burina da muradina ahalin yanzu bai wuce inga aurenka ba, Amman na fuskanci kafi son sai na mutu sannan zakayi aure . Jikin DEENi ya dauki rawa hankalinsa ya sake tashi matuka ta sake kiransa cikin tattausar muryar hade da rarrashi DEENi banida kowa daga kai sai zeenat sai kuma dan uwana wanda yake wata uwa duniya ,idan bakayi aure ka taramin jikoki masu albarka ba mezakayi min naji dadi , ina ji ajikina sai na mutu zakayi aure a rude yace first lov ki daina cewa haka zanyi inshallahu kina raye Tayi murmushin karfin hali tace kullun haka kake cewa, ni tuni na fidda raina ka tashi katafi Allah ya maka albarka ... Amman yarinyar nan zeenat na rokeka dan Allah ko ban tashi ba kada kabari ta koma hannun mahaifinta, na damka amanarta a hannunka ,bata da kowa duk duniyar nan daga ni sai kai ,karikemin ita a hannunka har zuwa lokacin da zata samu miji . DEENi yakamo tafin hannun ummi cikin nasa ahankali yasoma magana muryasa cike da rauni da fargaba, yace haba first lov ki daina maganar mutuwa nan kece zaki aurar daita da hannuki kuma kina raye inshallahu ta girgiza kai ita kadai tasan abinda take ji cikin muryarta irinta marasa lfy tace Shikenan tashi kaje ka kwanta , hankalinsa a tashe ya fice daga dakin..
zeenat ta mike daga inda take idanunta na zubda hawaye ta taimaka mata suka kwanta tana kuka kasa kasa ummi tace lfy zeenat ummi . .... ummi..... cikin sheshekar kuka tace banason naji kina cewa zaki mutu kibarni dan Allah ,ummi tace nafa da kar na fada mutuwa ta zamemin dole sai dai idan ajalina bai zo ba . zeenat ta saki kuka hade da kamkameta ummi a jikinta , tacigaba da kuka mai cin rai hade da cewa ummi bazaki mutu ba inshallahu da kanki zaki aurar dani ni ga duk wanda kike so da kyar bacci ya dauketa yayinda ummi Tayi nisa a bacci .
Shi kuwa DEENi tunda ya koma dakinsa ya kasa zaune ya kasa tsaye sai zariya yake daga farkon dakin zuwa karshe kafin daga baya ya nemi gurin ya zauna.
yayi tagumi da duka hannuwansa yayi zurfi cikin tunanin yadda zai yi lallai ya zama dole ya nemo mata domin cikawa umminsa burinta. sai dai shi matsalar sa bai san ta ina zai fara ba ? Bai taba yin buduwar ba ballanantana wata aba soyayya, shi duk a tunaninsa raini hakan zai jawo masa idan yaje yace yana son budurwar .
ya kamo gefen lips dinsa ya dan cizawa a hankali har daga karshe ya yanke shawara zai nemi fk da zance anan ya sulale ya kwanta rigingine idanunsa na kallon celling dakin .
yayinda ya rungume hannushi a saman kirjinsa yana aiyana irin type din maccen dayake son ta mallakesa,kuma wacce ya dace ya aura cikin sanyi ya runtse idanunsa gam take yasoma zaiyano irin type dinsa kyakkyawa dogowa mai dirin jiki , choculate colour, mai dara daran idanu sannan educated mai wushiryar haka dai ya rinka yi har dare ya sula bai samu wani ishashen bacci ba. koda asuba kafin ya tafi masallaci sai da ya fara shiga Bedroom din ummi ya sameta tana sallah ya sauke ajiyar zuciya sannan ya wuce ganinta tsaye tana sallah yasan Allah yakawo mata sauki .
A masallaci DEENi suka hadu da fk byn an idar da sallah "yajashi gefe guda da idanu fk yake binsa da kallo "abinda bai taba faruwa ba saboda DEENi daya idar da sallah yayi yan addu'oinsa yake wuce wa gida .
fk ya dube sa da kyau yana nazarinsa kafin daga baya yace lfy kuwa naganka haka ? Gabadaya fk yagama tsurewa da ganin yanayinsa sai da ya sake maimaita tambayarsa sannan DEENi yace ina fa lfy jiya ummi kwana Tayi ba lfy har tana barmin wasiya burinta da muradinta yanzu bai wuce nayi aure ba.
fk yayi shr yana jin DEENi har sanda yagama bayaninsa sannan yace baita kadai ba har big dady ma burinsa kennan dan ko jiya sai daya min maganar nida kai Amman tunda kai ummi ta damu ta tsananta gara kayi kawai kurabu lfy .
DEENi yace ai bakasan inda zan nemi matar ba nifa gabadaya en,mata family din nan basu min ba sannan kuma sun min kankanta da aure ,fk yace A'a bawani kankanta" mace na kankanta da aure ne ? kaine dai kawai kake ganin haka ,ni yanzu na yanke shawarar zan tsaida shemah kawai tunda na dade ina sonta nida zakaji shawarata ma da zeenat ka aura DEENi ya mishi wani irin kallon bakada hankali sannan yaja tsaki yace haba dai zeenat , fk yacigaba yarinyar akwai hankali wlh ,ba kmr wancan banzar ubannata ba, dayake duk sun tsani halinsa.
kaga kawai sai a hada bikinka da nawa kawai kaga zeenat batada matsalar, km ko bakomai ummi zata ji dadin Sosai da wannan hadin.
DEENi yace Amma ban taba jin koda alamar digon sonta ba, kuma ni gaskiya ina ganin tamin yarinta dayawa duk fa shekarunta sha tara zuwa sha ashirin ne fa. nafison mutual girl wace ta mallaki hankalin kanta tasan yadda zata kula dani akan bed ,amman wannan Yar bbyn maimakon ta kula dani ,ni ne zan koma renonta.
fk ya dubesa a kaikaice yace lallai yaran zamanin da kasani Amman banda na yanzu, sai su maka abinda manyan matan baza su iya ba, kana rai nata ne kawai , sai kaga mararta ta daukeka tsab, DEENi yaja tsarki kai ban son iskanci shawara nake so, ba wani shirme ka can na bazan ba .
fk ya kada kafada yace well tunda kaga bata maka ba kana iya duba wasu acikin gari .
DEENi ya kalleshi yana watsamasa harara "kaifa dan iskane dan kaga nazo maka da maganata shine zaka rainawa kanka hankali " sai kuma yayi kasa kasa da murya yace kasan Allah ni fa ko a waje ba wai ina kallon mata bane, fk yace to katsaya akan zeenat din kawai, duk inda ake neman macce mai natsuwa yarinyar nan takai ,DEENi ya sake jan tsaki yace ai inda takaicin yake kennan sai kuma nakirata ince ina sonta ...ya fada yana tabe baki "hade jin takaici da haushin shawarar da fk yakawo masa " fk yace inda bazaka iya ba kabi ta sama , ma'ana kasamu big dady da maganar kawai, kasanar dashi kana sonta nasan zai ji dadi Sosai .
DEENi ya sake watsamasa wata harara yace dan Allah malam ka dameni , ina ganin fa kmr kafara samun tabin hankali , wa yace dakai ina sonta "zan dai yi aure badan ina so ba ,ya juya yabar fk nan tsaye yana binsa da kallon mamaki sannan kuma yace ai kaine babban mahaukacin dan iskan kawai , sai iskanci fall ciki ,shi bai ga laifinsa da yace bazata ya saukarsa a bed sai nawa sai kuma ya kwashe da dariya .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 7-8
Har DEENi yazo gida tunanin yake akan shawarar da fk ya bashi" anya kuwa zai iya amince da auren zeenat ?
Lokacin da yashigo yayi daidai da zeenat ta tabare magani tana mikawa ummi ,ta amsa ta apa zeenat ta Mika mata ruwa ,yayinda shi km yake tsaye jingine da jikin kofa rungume da hannuwansa duka a kirjinsa yana kallonsu, take zuciyarsa ta dinga ingizashi akan lallai bbu wace ta dace ya aura sama da zeenat bisa ga hujarsa tacewa ,bazai taba samun matsala daita gurin kula da mahaifinsa saboda irin soyayyar dake tsakaninsu "
yasan ko yana nan ko baya nan zata kula daita, umminsa zata zamo a karkashin kukawarta tunda zeenat bata da wata uwar da wuce ummi tunaninsa ya katse lokacin da ummi takira sunansa' tace son karaso mana yayi frigigit ya dawo natsuwarsa ahankali yashiga takowa har inda ummi take ,ya zauna zeenat ta gaidashi ta mike zata fice daga dakin bai amsa mata gaisuwar data masa sai dai yabi bayanta da kallo" ummi ta kalleshi ta kauda kanta, yace first lov yajikin naki ummi ta danyi murmushi hade daura hannuta kan sumar kansa tace naji sauki sosai , ahankali sauke ajiyar zuciya ko bai ce komai ummi ta fahimci yaji dadin yadda yaganta ,yana nan zaune , Sam yakasa yiwa ummi zance yana ya auren zeenat din ,daga karshe ma tunani yayi kawai gara yasamu ya mahamud da zance dan gaskiya kunya yake ji yayiwa ummi maganar da kansa .
Da yammacin ranar byn ya dawo daga office yaje har gida yasamu ya mahamud da maganar ya ji dadi kwarai da gaske, har yarasa inda zai sa DEENi dan farinciki dan shima da kansa ya matsu yaga DEENi ya ajiye iyali kmr kowani magidanci , yace Shikenan sai kasamu yarinyar da zance, ku daidaita kanku DEENi yace A'a ina ganin basai na sameta ba in dai first lov ta amince ai Shikenan .
yaya mahamud yace ummi bazata taki ba Amman dai kasan kaidar auren gidanmu kennan bbu dole a ciki "muddin kuka daidaita kanku na iyayenmu may sauki ne idan Kuma ita ummi ta amince ita yarinyar tace bata sonka fa? DEENi yaji haushi da takaici sunkamasa alokaci guda yace ai nima ba wai ina sonta bane kawai dai zan aureta ne.
Yaya mahamud yace shirme bazan kennan kai yanzu idan anzo meeting cewa zakayi basonta kake yi ba ,zadai ka aureta ne ?DEENi yayi murmushin gefen baki har dimple dinsa ya lotsa sannan yace cewa kurum zanyi ina son zan aure zeenat ne ' Yaya mahamud yace to Allah ya mana zabi na alkhari kabari zanje gurin ummi tukun duk yadda mukayi daita zakaji DEENi yace Shikenan ya mike fice ,a office ma koda yaje aikinsa kawai yasa gaba .
dan shi gabadaya ya manta da wani zance aure can .
Mahamud yasamu ummi cike da karfin gwiwa" ganinsa ba wanda zai kai ummi murna tunda daman burinta kennan naganin auren DEENi, Amman ga mamakinsa yana gama labarta mata abinda yakawo shi, sai yaga ummi tayi kicin kicni da ranta tamkar bata taba sanin wani abu farinciki ba "sai da gaban Yaya mahamud ya fadi dan ganin yadda ummi tayi da fuska tamkar yazo mata da zance mugun abu " tace kai ne kaga sun dace kaba shi shawara ya nemi aurenta ko Kuma shi da kansa ya sameka da zance ?
Da sauri yaya mahamud yace A'a shine dai yazo min da zance ummi ta sake daure fuska, sannan tace ka koma ka fada masa ban amince ba ,kace masa akwai sauran mata a gidan nan yana da damar zabar duk wacce tayi masa, idan ma ya canza ra,ayinsa nakin auren family' to yaje waje ya nemi matarsa can itama Allah zai bata nata mijin, Amman Sam ni ban yarda da wannan hadin ba " tayi shiru na wani lokacin kana zubawa Mahmud idanunta tana kallon yanayin daya shiga ,ahankali ta numfasa sannan tace kana iya wucewa idan kana da abinyi ka manta da wannan shirme na DEENi .
Yaya mahamud yayi kasa da kansa Sosai cikin muryasa can kasa kasa da alamun km rarrashi yace dan Allah ummi ki amince da auren nan bazan iya tunkarar DEENi da maganar ba.
duk da bansa dalilinki nakin amincewa ba" ummi ta dan saki fuskanta ba kmr dazu ba tana mugun son mahamud tamkar dan da ta haifa acikinta tana jinsa har cikin zuciyarta .
tace bawai ina kin hadin bane duk duniya idan akwai wanda zai so auren DEENi da zeenat a bayana yake ,na farko dai kaima kasan halin DEENi da dan bazar zuciya , ga saurin fushi ga maseefar miskilanci tsiya ga jin kai sannan da bakinsa yasha gayamin cewar shi bazai taba yin auren family ba sannan shi mai digiri yake so ya aura ,shine km yanzu zai zowa mutane da wani salo.
ni da tawa iya secondary kadai ta tsaya" ai kai da jin zancensa ma kasan akwai wani makirci daya shirya "dan nace yayi aure ai bance lallai sai ya aure tawa yarinyar ba , Muhamud yace ummi ki duba lamarin abun tunda shi da kansa ya furta cewa ita ta masa ba za'a samu wata matsala ba ,.
ummi tace Sam bata yarda da wannan tsarin ba " ita dai yaje gaba ya nema hakurin duniya nan bbu wanda yaya Muhamud bai bawa ummi ba amman taki amincewa ,duk ta inda ya bullo mata sai itama tabiyo masa ta wata hanyar, har ran yaya mahamud yasoma baci ,yaji haushin abinda ummi tayi dan haka ya hakura ya fice ransa abace .
DEENi zaune a office dinsa ya dukufa wajen tura sakwanni a yanar gizo ,hankalinsa kwance yake bin komai daki daki , yaji daya daga cikin wayoyinsa ,daya ta dauki karar sauti mai dadi ,ya dauke idanunsa daga kallon system din yasa hannu ya dauki wayar yana dubawa ganin sunan dake yawo akan screen din ne" yasa yayi sauri dagawa yakara a kunnenshi hade da yin sallama" kana ina muryar Yaya mahamud yaji ta daki dodon kunnenshi cikin sanyi murya DEENi yace ina office yace ok idan katashi kabiyo inason ganinka sannan ya kashe wayar .
DEENi zaune a gaban Yaya mahamud kansa sunkuye a kasa yayinda idanunshi ke kallon zarazaran yatsun kafafunsa yana sauraron sakonshi da ummi tabayar a sanar dashi.
a gurin Yaya mahamud sam bai tsammaci jin haka daga umminsa ba ,ga mamakin Yaya mahamud sai yaji deeni yace Shikenan babu komai Allah yasa haka shine mafi alkhari .
ya mahamud yace ka hakura kennan? Nashi ganin bazai damu dan ummi ta hanashi auren zeenat , dan haka Yace eh "tunda daman ba wai yana sonta bane" nan dai suka bar zance aure suka shiga wata hirar daban a inda Yaya mahamud ya tashi yaje ya kwaso wasu takardu da file files ya zubesu nan a gaban DEENi yace yasa masa hannu ciki " kai tsaye DEENi ya zaro wani hadadden Biro daga gaban aljihun rigarsa yasoma cike gurraren da akeso yayi sign, dan gabadaya dukiyar DEENi , sulaiman da Muhamud ne akai su suke kula daita kuma komai na tafiya daidai " domin dukkannisu abu guda ne a gurin ummi dan ma idan ba'agaya maka ba…
zaka dauka duk ummi ce ta haife su .
Sai da DEENi yagama sign din ,sannan yaya mahamud hada da mishi bayanin companies din da suke son budewa a kasar American, sun turo musu da sako akan suna da bukatar mutun daya daga cikin masu company din " yazo interview dan haka shi ya wakilta sulaiman yaje , DEENi yayi murmushin yace Shikenan bbu komai duk yadda kukayi ,daidai ne Allah ya taimaka .
To byn DEENi yakoma gida ya dingawa ummi wani irin kallon, wanda shi kansa yakasa gane dalilin yin haka, yana son yi mata magana Amman yayi shr ,yayinda zuciyarsa ke kwabarsa akan ya share kawai ai baita kadai bace mace a duniya" daman ai dan ita yake son ya aure zeenat din ,da yaje waje ya aure wata wacce bai san halinta na boye ba ai gara zeenat din Amman tunda bata so shima ya hakura .
Da misalin karfe goma na dare DEENi sanye da rigar wanka dan fitawarsa kennan daga bathroom ,ya tsaya gaban dress mirrow yana karewa jikinsa hade da zare rigar wanka dake jikinsa" ya saura daga shi sai boxer , yabi koina a jikinsa da turaren Hamilton 27, sai daya kammala da komai na al'adarsa da yasaba yi kafin ya kwanta sannan ya hau kan royal bed din ya lumshe rikitattun idanunshi, alamun yana son yayi bacci' sai dai baccin yaki zuwa kawai ya tsinci kansa da tunanin zeenat.ya rinka jinta ajikinsa , yadda yake jinta a halin yanzu bai tsammaci abin har ya zai haka ba ,,
Sosai ya tsinci kansa cikin damuwa ko baya son yarinyar hakika ya tsananta da son aurenta yayi shr yana tambayar kansa abinda ummi take nufi da kin amincewa datayi,shi ya guji big dady da maganar a tunaninsa sai umminsa tafi kowa murna da jin dadi 'ya dauki tsawon lokacin kwance kafin bacci barawo yayi gaba dashi .
Byn kwanaki , DEENi yakasa hakuri da maganar zeenat din kmr yadda yaso shima ta share da zance kawai ya manta dasu "
Amman yakasa, ya samu ummi da kansa a wata safiya dayazo gaisheta byn yayi shirinsa na zuwa aiki cikin kakinsa dake kara masa kyau tamkar dan shi kadai akayi" sai kamshin yake zubawa ta koina "gashin kan nan nasa kwance luf luf luf dasu , duk da bacika yawa sukayi ba ,saboda yanayin aiki "Amman dayake Allah yayi mishi suma takoina ajikinsa ko yayi askin ma baya wani dadewa" gashin zai sake fitowa" sosai yayi kyau matuka ,ita kanta ummi satar kallonsa take har ya tagota ya sakar mata murmushi tace son kayi kyau sosai fa, uniform din nan nakara maka kyau ,ya dage mata girarsa daya yace Allah first lov yace ai daman can nj may kyau ne sannan duk maccen datayi dacen samuna , ta gama samun duniyarta sai dai ta nemi lahirarta kawai " ummi tayi dariya sosai ya kamo hannun umminsa cikin nasa muryasa a shagwabe hade da dan karyar da wuyansa, yace first lov da kanki ma kin yaba dani "tace uhmm yabon gwani yazama dole "yace to meyasa bazaki bani auren zeenat ba ?
Ta lissafomasa dalilinta kmr yadda ta sanarwa Muhammad ta Kuma sake jaddada masa yaje gaba ya nemi mata Amman banda diyarta ranshi ya baci Amman ya share take Yar fara'a dake fuskarsa ta dauke " sai dai bai nuna ba , cikin sanyi murya yace to Shikenan ummi na hakura" Amman bazan taba zuwa koina neman aure ba" saboda banida nagartar daza'a soni Kuma bani aure" ummi tace ba fa haka nake nufi ba yace haka ne mana first lov" ina da munanan halayen da ban cancanci abani mata aure ba. ummi tayi murmushi tace nifa bance haka ba yace haba first lov kince mana gashin nan kema da kanki kin hanani taki Yar , to waye zai amince yabani yana kaiwa nan ya cire hannun umminsa cikin nasa ya mike cikin sanyi jiki tamkar bai damu ba ,.
gabadaya jikin ummi yayi tsanyi ita bawai auren ne bata so ba halinsa take gudu ta yaya zata yarda ta aura masa marainiyar Allah yazo yana cutar mata da yarinya .
Abin mamaki duk a tunanin DEENi na bazai shiga damuwa ba akan kin amincewar ummi ,
sai gashi dumu dumu cikin tashin hankali kullun sai yayiwa umminsa naci da magiya akan tabashi auren zeenat ,ita kuwa ummi duk lokacin dataga ya dauko mata zance sai share hade da bata fuska .
Please kumin uziri , may be zaku dan jini shiri sakamakon matsalar rashin wuta naso narinka muku type akai akai batare da westing time ba Amman kuyi hakuri ana kyawun tare🤝🏻🤝🏻
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 9-10
Zeenat kwance a bedroom din ummi hannuta rike da wani English novel face to face tayi zurfi cikin karatun novel din saboda yadda take enjoy din novel din ya .
Yaya DEENI ne yashigo gaishe da ummi kafin yafita aiki ,byn sun gaisa ne ummi tace har ka shirya fita kennan ? Yace mata eh sannan yaja ya tsaya yayi shr ya zubawa ummi idanunshi .
ummi ta dubeshi tace da magana ne ? Tunda tarigada tasan muddin yayi shr irin haka to da magana a bakinsa.
koda yake tasan dai zance nasa bai wuce maganar zeenat bane " Kuma daman tana son zeenat din tajima kunneta idan ta amince ruwanta "
dan haka ummi kalleshi da kyau tana nazarinsa ta numfasa sannan tace masa kayi shr alhalin nasan da magana abakinka .
, muryasa a shagwabe yace first lov kan dai maganar zeenat ne ,dan Allah first lov, ba yabon kai ba "ina da qualities din da za'a bani auren kowace irin mata nake so" Kuma ko Yar gidan waye ,.
Yar taki ma daba wani kyau ne daita ba" dan ma zan taimaka mata "ya fadi haka fuskarsa a hade ,.
ummi tace duk da haka day bazan bada diyata ba kaje waje ka gwada sa'a r ka" wai ma in tambayeka DEENi yamaida hankalinsa sosai ga umminsa" tace kai da kake ta damun kanka da zance nan kullum. kasamu ita yarinya da maganar ,kun daidaita kanku ne ?
DEENI yace uhmm kece dai zaki sanar mata, ummi ta nuna kanta da dan yatsanta, nice ma zan tayaka yakin nemar maka soyayyarta" lallai ma bason auren nata kakeyi ba" kashare zance kawai tunda baka shiriya neman aure ba. yace to ni first lov in na fada sai naga tamkar Raina ne zatayi, ummi tace kunji girman kan ba a hassale ummi tace dan Allah kayi hakuri kabar zance nan. haba duk kabi katadda hankalinka da nawa. yarda ne dai bazanyi .
dan haka kayi hakuri kabar zancen nan kwata kwata dan ba yarda zanyi ba .
DEENI daya gaji dayiwa ummi magiya ya hakura ya ficewarsa ,yana jin takaici kansa, tunda daga lokacin da zeenat taji DEENi ya ambaci sunanta ta mike zubur zaune daga kwanciyar datayi, hankalinta a tashe jikinta har rawa yake tsabar rudewa" ita zeenat din yaya DEENi yake nufi ko wata daban.
ahankali ta furta in ko ita yake nufi dakuwa ta more a rayuwarta, dan gaskiya yaya DEENi ba irin namijin da mace zatace bataso bane , ahankali ta sake furta A'a dan Allah ummi kada kimin bakinciki mana.
tana jin fitarsa ta fito da sauri daga dakin tana kallon ummi dake zaune tana jan carbi, zatonta ko ummi zata mata maganar ne. Amman sai taga sabanin haka .
dan kuwa ummi ko kallon inda zeena take tsaye batayi ba.
dan tarigada tasan taji komai" to Kuma bayanin me zata tsaya yi mata. Ta dai yi shr ne taga yadda zata dauki lamarin .
Can kuma, ummi ta dago tana duban zeenat din tana nazarinta" yayinda zeenat din itama ummi take kallo" har zuwa lokacin ummi batace komai ba .
sai ma kau da kanta gefe datayi , ganin ummi bada niyyar ce mata komai ,yasa zeenat kira sunan ummi" ta juyo tana duban zeenat din da kyau".
ahankali cikin sanyi murya tace ummi wai wata zeenat din yaya DEENi keso ?
Ummi ta dan tabe baki sannan tace dan Allah rabu dashi wai ke yake nufi "da sauri zeenat tasa hannuwanta duka ta dafe kirjinta dasu tana zaro idanu waje "tace da gaske ni yake so ?
ummi tace zan miki karya ne" zeenat ta marairaice murya tace shine Kuma ummi zakice masa baki yarda ba.
ummi tace to may kike nufi ,kina son kice min kina son DEENi kennan ? Zeenat Tayi shr dan bata da amsar bawa ummi dan gabadaya ilahirin jikinta bbu inda bai dauki rawa ba.
ummi ta sake yin magana daman kina son DEENi ne naga duk kin tada hankalinki haka ?zeenat tace nifa bance ina son shi ba Amman ke meyasa zakice A'a Kuma ma mayye dalilin dayasa kika ki amincewa ,ummi tace ok tutseni zakiyi" kan naki yarda ko yaya , zeenat tace ba haka bane" ummi tace tsaya ma kiji abinda yasa naki yarda, DEENi "da" nane' ni haife shi da cikina sannan ke ma kinsa halinsa sarai da shege miskilanci da saurin jin haushi mutun ,abu kankani ke hassalashi ga tarin girman kan tsiya, zeenat ta tsugunna nan gaban ummi hade kamo hannuwan ummi duka cikin nata muryarta sanyaye tace haba ummi dan day kawai saboda wannan halin nasa ne "zai sa kike amincewa , in dai dan haka ne' ni na amince da aurensa kinji .
ummi tace duk kinbi kin koma kalar tausayi wai ma meyye birgeki da DEENi ne naga duk jikinki ya dauki rawa haka ?.
Zeenat tace ai gaskiya yaya ba irin mutunmin da za'a tsaya cewa ba,aso bane ni dai na amince ,ummi tace ko kin amince, ni nace A'a ban yarda ba ,.
Zeenat ta mike cikin fushi tayi bedroom din ummi .
da kallo ummi tabi bayanta dashi ummi taji matukar mamakin ganin reaction dinta musamman da tasan zeenat din ,bata fiyye nuna fushinta akan abu ba .
Koda tashiga dakin ma waje tasamu ta zauna abunta tayi tagumi batayi aune ba, kawai taji hawaye na silalowa mata.
ita kanta tasha mamakin ganin hawayen na zuba a idanunta "ta tambayi kanta to daman can tana son DEENI ko yaya? domin abun itama yayi maseefar daure mata kai ".
kuka takeyi " iya karfinta hade da ganin laifin ummi din ,to meyyesa ummi zatace batason aurenta da ya'ya DEENi byn ita tasha kisma haka a ranta .
taci kukanta sosai har sai da taji alamun kanta ya fara mata ciwo ta runtse idanunta sannan ta kwanta "nan a gefen bed din ummi tacigaba rera kukanta kasa kasa .
Yinin ranar tayi shi ne cikin daki hade da tunanin DEENi da kitsima kalar rayuwar da zatayi a gidan DEENi.
Da zarar taga ummi kuwa take hade fuskarta saboda jin haushin abinda tayi " .
kusan zuwa Maryam uku gidan "Amman zeenat taki saukowa kasa" dan gabadaya takasa samun sukuni gabadaya haushin kowa take ji.
,ita kuwa ummi sai binta take da idanu dan ma kasa magana tayi , gashi ranar Sam DEENi ma kin dawowa yayi da wuri sai wajen shabiyu , .
haka ma washegari tun asubar fari yabar gida ya dai shigo ya gaida umminsa a tsaitsaye.
,byn ummi ta idar da sallah ne kafin ta soma lazimi , yayinda zeenat ke kwance akan bed , idanunta a runtse tamkar may bacci Amman Kuma ba baccin take ba .
ummi takira sunanta kusan sau uku Amman tayi mata shr alhalin tana jinta.
ummi ta sake kiran sunanta tace zeenat nasan kina jina Kuma idanunki biyu Amman kika min banza , hade da ganin laifina .
bakomai yasa kika ga naki yarda da maganarki da DEENi ba" nasan halin DEENi ciki da bai bashida dadin sha'ani kwata kwata gashi da bakar zuciya tsiya azo ayi auren nan yazo yana gana miki azaba, .
ni.. nasan abinda nake gudar miki Amman inda kinkiji ke kika sani , kije Allah yabada sa'a .
Amman ki sani idan akwai wanda zai ji dadin aurenki da DEENi a bayana yake, Amman duk da hakan bazai hanani fadar gaskiya ba idan tazo.
Kuma shawarata gareki ki rage rawar kai dan idan ya fahimci haka zaki sha wulakancin, da karshe km mutuncinki ya zube a gurinsa.
ga zaton ummi zata ji zeenat din tace ta hakura da auren DEENi din ne Amman sai ganinta tayi ta duro daga kan gado ta zube gabanta durkushe.
, taji tace idan dai har kin amince ummi inshallahu bbu abinda zai faru .
Ummi tayi shr ta tsura mata idanu tana kallonta ummi tace kina nufin kin amince zaki auri DEENi kennan ? Zeenat tayi shi shr takasa cewa komai ba sai karyar da wuya datayi , ummi ta sake duban tace ke..bafa zan yarda da auren nan ba . take zeenat ta fashe da wani irin kuka tana bawa ummi hakuri ta amince dan Allah abin ma ya daina bawa ummi mamaki , yadawo bata tsoro ,.
Cikin kuka zeenat ,tace ai shi yace yana sona " to ta yaya ke zakice A'a ummi tabita da wani irin kallo tausayi , aranta kuma tace ya'yan yanzu sam basu da kunya . wani irin son zeenat din ne taji yana ratsa ko wani part na jikinta.
ga tarin tausayin yarinyar dake matukar damunta ,Amman hakan ba zai sa taji zata iya amincewa da muradinsu ba .
ta kau da tausayin yarinyar a ranta ta hade fuskarta tamau ,sannan tace ke dan ubanki akan na hana aurenki DEENi ne zaki ,ta sani gaba da kuka "dan bakisan ciwon kakin ba ,danma ke shashace ko shi dayace yana son naki" bawai damuwa yayi dake ba.
tunda har zuwa yanzu bai kawo kansa gareki ba.
sai kece zaki wani damu mutane da kuka akanshi ,cikin wani irin sabon kukan zeenat tace bagashi ke yayi miki maganar ba .
Ummi tace OK dan yayi min maganar shine may . ni zai aura ko ke ,da kyar ta iya sausauta kukanta sannan tace ummi dan Allah ki amince mana tunda day har shi ya furta da kanshi".
ummi taja tsaki ta mike tsaye tace ni masa, ban waje tun banyi ball dake ba shashar bazan kawai.ta wuce parlour
tavarta zeenat nan durkushe.
aiko zeenat naganin haka ta fashe da wani kukan har da shesheka .
Da daddare misalin karfe tara ,DEENi zaune a parlour shida ummi suna kallo Amman jifa jifa take sako masa hirar duniya " shi dai jinta kawai yake , yayi tamkar bbu abinda ke damunsa Amman shi kadai yasan abinda yake ji aransa' zeenat ta hado masa coffee tazo har inda yake zaune ta ajiye masa nan kusa dashi ta juya zata bar gurin ko kallo bata ishe shi ba ballanantana yasan ko ita wacce, hakan da yayi ne yasa ummi taji ba'adadi aranta . muryasa a kwasashe yace ke.....ta juyo ahankali hade da zuba masa idanunta shima ita yake kallo da ritattun idanunsa ,yace dawo ki dauki abinki konace miki ina bukatane" da sauri ta zeenat ta girgiza kai, ya kau fuskarsa kmr bashi yayi maganar ba .
bai sake cewa komai ba ,km bai kalli inda ummi ke zaune ba, ya mike kan three site yayi kwanciyarsa " aransa yace akanki zan dinga huci takaici abinda ummi tamin" tunda tace bazata auramin ke ba.
nima na hakura da auren naki" sai ta jikaki tay tasha .
kunya ne hade da tsoro suka taru sukama zeenat rubdugu , taji gabadaya kakafunta sun Gaza daukarta " ana cikin haka shemah tashigo da sallamarta "kai tsaye wajen ummi ta nufa ta zauna tana gaishe da ummi "ta amsata cikin sakin fuska , .
,sai sannan ta juyo tana kallon inda zeenat ke tsaye kikam tamkar an dasata' km sai a lokacin idanun shemah yaKai ga DEENi,dake kwance idanunshi a lumshe. itama idanu ta zuba masa tana kallonsa , tana jin wani irin ajikinta yayinda gefe daya zuciyarta ke wani irin dokawa da sau da sauri " shi km kwata kwata bai ma san Allah yayi ruwan mutun a gurinba " ahankali ya mike tsaye yana wa ummi sai da safe "a ciki ta amsa masa dan takaici abinda yayiwa zeenat " suna hada ido da ummi yasakar mata murmushin gefen baki hade da yakashe mata idanunsa daya wanda ita kadai tagani " da sauri ya haye step ,.
yana barin wajen atare suka sauke ajiyar zuciya daga zeenat din har shemah " .
dan har gara shemah ma akan zeenat din dan ita gabadaya a frigice take "idanunta ta dan juya da niyar satar kallon inda ummi take , ai ko take suka hada ido daita ummi kalli zeenat din tana watsa mata harara dan gabadaya tagama bata haushi .
yana shiga dakinsa ya fada kan bed dinsa ya jawo system dinsa kennan idanunsa yaKai ga phone dinshi dayaga almost 12 miss cul da sauri yasa hannu ya dauki wayar yayi dealing number daya Gani bugu daya biyu "fk ya dauka yace ka kyauta angon zeenat" bukatarka ,ta biya ai dole kashare mutane. DEENi yaja tsaki mtssss sannan yace dan Allah ni rabani da wannan zancen naka na banza" haka kurum kasa mutun a one chance,.
gashi kaja wa mutun wulakancin kawai ,fk yace wulakancin Kuma a gurinwa DEENi ya tabe baki tamkar fk din na ganinsa sannan yace a gurin ummi mana.
to meyya faru inji cewar fk.
sai da DEENi ya jima bai yi magana ba kafin daga baya ,yaja wani irin numfashi yace ummi fa taki amincewa da shawarka ,sai ma wani yawo ake min da hankali kmr za'a bani gold.
fk ya kwashe da dariya yace mutumina kodai ka zurma ne, irin wannan jin haushi haka.
DEENi yace kai nifa na hakura da yarinyar nan wlh ,dan gaskiya bazan jura wannan wulakancin ba .
ga mata nan dayawa a waje suna bina kmr su lashe ne " fk yace tsaya ranka ya dade ba haka za'a yi ba, bari zamu samu big dady da zance nasan komai zaizo da sauki .
ko Kuma kai me zai hana kasa zeenat din da kanka.
DEENi ya sake jan tsaki yace maganar bazan kennan ai inda takaicin yake kennan haba ai kauyancine a wajena na tsaya ina gayawa wannan yar karamar yarinyar kalmar so .
fk yace kaji irin ta ko kana son yarinya Amman girman kanka na neman cutar dakai "DEENi ya katseshi " hade da cewa kai fa dan matsala ne , nasha gaya maka ka daina cewa ina son yarinyar nan, zan dai aureta ne kawai fk yace Shikenan ajiye wannan zance.
bari gobe inshaallahu zanzo muje gurin big dady DEENi baice komai ba ya katse wayarsa .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 11-12
Washegari bai tashi da wuri ba sai wajejen shabiyu na safe yatashi. yashiga, bathroom byn ya fito ne yayi tsaye gaban mirrow yana kallon every part of him ,tsawon lokacin yana tsaye yana kallon kansa ta mirrow kafin daga baya ya janyo wata karamar stood dake gefe ya zauna .
hannushi ya dora a saman fadaden kirjinsa yana shafa kwantaccen gashin kirjinsa hade da lumshe idanunsa "shi kansa yasan duk matar data mallakesa matsayin mijinta bakaramin Lucky Tayi ba .
cikin sanyi jiki tamkar macce yasoma shafe jikinsa da body lotion " DEENi na kashewa kanshi kudi fiyye da tunanin may karatu ,
mikewa yayi cikin tafiyarsa ta kasaita ya nufi cikin bedroom din shi dan saka kayan " har ya nufi kofar dazata kaishi parlour" sai ya tuna ana jiransa dan haka yaja tsaki mtssss sannan ya nufe kofar bedroom dinshi byn yashige tare da cewa koma waye zai tafi idan yagaji da zama dan yanzu baida lokacin kowa .
Shiryawa yayi cikin wasu hadadun kananan kaya wando blue jeans da riga longslive" wani irin kyau Allah yayi masa na daukar hankali" ya isa kan durowa ya kwashi wayoyinsa ya zuba cikin aljihun wandonsa "ya sanya takalmansa mai sawun ciki ya zura hannushi daya cikin dayan aljihun .
Shemah ce zaune a parlour DEENi take zaman jiransa "wacce tun karfe tara na safiyar ranar ta dako samamko son ganin DEENI din.
da farko bedroom din ummi ta nufa , sanin datayi dole zai shigo gurin ummi ,ganin har ummi tagama abinda take tadawo main parlour dinta yasa itama tabiyo bayanta , .
Ganin tagaji da zama kusan 1 hour tana zaune zaman jiransa Amman bata ga alamun. fitowarsa ba yasa tacewa ummi dan Allah takira mata shi .
Ummi takirasa tasanar dashi bai ce da ummi komai ba dan kusan da haushi yatashi . Ita Kuma ganin yayi shr yasa tace mata taje part dinsa .
Koda ya yafito falonsa yaga mutun zaune shi duk tunaninsa FK ne ko cikin abokan aikinsa kallo daya Yayi mata ya dauke idanunsa daga kanta "yi yayi tamkar bai ganta ya nufi hanyar fita. ta taso da sauri tana kiran sunanshi " cigaba yayi da tafiyarsa danshi a ganinsa bai ga abinda zai sa ya tsaya ba ,.
ganin saurin bazai mata ba , dan haka ta kara da dan gudu da sassarfa har ta cimmasa ,a daidai cona da zata kai mutun main parlour din gidan tasha gabansa da sauri tana sauke ajiyar zuciya hade da cewa dan Allah yaya katsaya magana nake son yi dakai .
dubanta yayi tamkar bazaiyi magana sai Kuma yace meyye matsalarki dani ? Dan ji Yayi kmr ya dauketa da maruka " Kalmar daya fada ne yasa taji zuciyarta ta tsinke " Tayi wani irin tsalle kmr zata tafasa kirjinta ,.
Tayi shiru tana tattaro kalmar dazatayi amfani wajen fahimtar dashi abinda ke ranta .
cikin sanyi murya yace ina zaton kin manta ko ni wanene shiyasa kika tareni , sai da ta saita kanta sosai, ta'aro jarumta takara akan wanda take da" sannan tasamu kwarin gwiwa. cikin marairaicewa murya irin ta masu neman taimako tace dan Allah yaya" kadan bani aron lokacin uziri ne dani.
yamata wani irin duban dayasa yanhanji cikinta kadawa sannan yace uhmm ina jinki kuma ki tabbatar da uzirinnaki mai ma'ana ne .
"da idanunta ta amsa masa dan gabadaya ilahirin jikinta kirma yake tsabar rudewa datayi har wani gumi take fitarwa na wahala.
tun ba yau ba DEENi yasan shemah nason furta wani abu gareshi Amman rashin ganin fuskarsa yasa taki tunkarsa shi bema san dalilinsa na tsayawa ba .
Shi kansa yasan dole wannan ranar zata zo komai daren dadewa ".
ahankali take sauke ajiyar zuciya saboda fargaban da tashin hankali , abinda zai biyo baya " numfashi taja hade dayin kasa da kanta dan sam bazata iya kallon kwayar idanunshi a wannan lokacin .
Ahankali tasoma magana muryata kasa kasa cikin in...inna ,tace daman ..daman..ina son sanar dakai " ina..ina so.....da hannushi ya dakatar daita" tun bata kai ga karasa maganarta ba tare da buga mata wata irin razananniyar tsawa wanda yasa ba shemah ba ,har zeenat dake kokarin fitowa daga dakin ummi zuwa parlour "ta koma cikin daki da sauri " ta manne da jikin kofar hade da cewa wayyo... Allahna me Kuma yasame sa haka cikin tashin hankali ta sake mannewa da jikin kofar . , hatta ummi dake zaune a falo say da taji amon muryasa ,wani irin kallo yake jifarta dashi yace kina.... me uhmm repeat what u say , lip's dinshi cikin bakinsa yana cizawa sannna yace what ar u try to say ,ya sake jiho mata wata tambaya, still shr kake jin shemah ba bakin magana Amman gabadaya ilahirin jikinta ya dauki kirma .
Cikin isa da takama yace u better keep what'ever you won't say before I sikater you now jikin shemah yacigaba rawa kafafuwanta suka Gaza daukarta dana sani kuwa tayishi yafi cikin buhu , ya tsareta da mayatattun idanunsa " murya a kwasashe yace na sake jin kin Kuma furtamin wannan bazar kalmar wlh azim zakiga yadda zanyi da namanki stupid girl kawai.
ya ja tsaki ya wuce abinsa ta tsaya nan tana bin bayansa da kallo ranta a bace batasan lokacin da Hawaye yasoma zubo mata tana tunanin yaushe ne zata daina kuka akan son DEENi mutumin da take matukar so tamkar ranta mutumin da mata ke rububin son shi mutumin dayake jama mata aji ga shegen kyau da kwarjini " nan ta zube kasa ta risgar kuka ahankali hade da sa hunnta duka ta toshe bakinta dasu .
Zeenat dake tsaye jikin byn kofar dakin ,banda kirma bbu abinda jikinta keyi , tsabar frigice jin abinda shemah ke kokarin yi' domin taji duk abinda ya faru tsakanin yaya DEENi da shemah tsabar tsoro ne ya hanata fitowa ,wani irin kishi ne taji yana taso mata tun daga kan tsintsiyar kafarta yana bin ilahirin jikinta hade da kashe mata duk wani gabobin dake jikinta , taji a ranta da tana iya fitowa,. tabbas da ita kadai tasan yadda zatayi da shemah, tsinuwa kuwa iri iri bbu wanda zeenat bata aikawa shemah ba .
, ahankali zeenat ta sulale kasa ta dora hannuwanta duka bisa kanta.cikin kuka take cewa Shikenan ummi tacuce ni zata kai ni tabaro "gashi taki yarda da aurena ,da yaya DEENi ga wasu can suna neman farautarsa .
,ba tasan tana shirin jefa diyarta cikin halaka bane akan tilon danta.
dan ita yanzu ji take zata iya yin komai akan DEENI .
Ahankali Tace ita yanzu yazatayi da ranta , idan Kuma yace hakura daita fa ? Taji gabanta fadi
Da sauri tasoma girgiza kanta tace hakan ma bazai taba faruwa ba inshallahu sai ta aure yaya DEENi mijinta ne ita kadai , .
dan ita yanzu wani irin son DEENi din ne yashigeta na farat daya ,kmr kar taji ya furta yana sonta ...itama taji tana maseefar kaunarsa , Ita taji ta Gani zata iya rayuwa dashi akowani irin hali.
kawai,a hankali ta sake ta saki wani irin marayar kuka mai ban tausayi tana furta ummi karkimin haka dan Allah ..kar min haka ummi ke uwace gareni har da rabi .
dan Allah karki rabani yaya DEENi wlh zan iya zama dashi a haka , duk munin halinsa ina son shi " tunda harshi ne ya furta yana sona ...
gabadaya ta rikece da wani sabon kuka tana sambatu .
kuka tayi sosai har da shesheka ahankali ta sauko da hannuta bisa kirjinta" ta dafe kirjinta dataji yana mata wani irin ciwo zuciyarta na dokowa da sauri da sauri zeenat ta runtse idanunta dan ita kadai tasan yadda take ji.....
ta ciki dakin zeenat ke rizgar nata kukan ,yayinda shemah da ke waje durkushe ta nata .
Taku yake cikin izza da jin kai da jin shi wani ne yake takunsa har yakaraso ya zauna kujerar da umminsa ke zaune ya dora kansa kan cinyarta "ita Kuma ta'ajiye jaridar dake hannuta tun soma jin amon muryasa ta daina karatu datake "ya sakar mata murmushi gafen baki tamkar bbu abinda ke damunsa ,yace gud morning my first lov ....
ta daura hannuta bisa sumar kansa tare da fadin morning my son yakatashi lfy , ya dan tabe baki sannan yace nut bad ....
tace ya'akayi ne son me kakeson cine akwai dinshi iri iri akan darning wanda orready zeenat tashirya komai .
turo baki yayi cike shagwaba har zaiyi magana " kome ya tuna sai Kuma ya fasa cewa komai " ummi ta tsurawa fusharshi idanu tace kayi shr ya lumshe idanunsa muje kayi breakfast din ina lura da kai tunda kasoma zancen yarinyar nan bakason zama ma a gidan ballanantana Kaci abinci ahankali ya ware idanunshi akan umminsa sannan yace first lov na koshi fita ma zanyi yanzu ....
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 13-14
Bangane fita zakayi ba byn ko breakfast bakayi ba ina fa hankalce dakai fa duk kwanakin nan bakason cin abinci,
ina zaka ma tukun danaji kace fita zakayi naga week end ce yau .ta hade fuska ta mau hade da zuba masa idanunta.
Ya dan yi murmushi gefen baki har dimple dinsa ya lotsa" kyaunsa ya sake bayyana" ya mike daga kan cinyarta ya zauna sosai shima yana kallon yanayin umminsa" yana jin yadda soyayyar Ummi nasa fiyye da komai nasa "yana sonta baya son damuwarta itace duniyarsa sannan itace ke tattare da duk wani farincikinsa tana tsantsar " son shi da nuna masa duk wata kulawar da uwa kadai zata iya yin haka .
Hannuta yakamo duka cikin nasa ganin yadda ta damu muryasa a sanyaye kmr koda yaushe yace am so sorry my first lov muje zanci tayi murmushi tace kai ko hade da dan dungure masa kai "dan bazata iya fushi dashi "shi kadai Allah yabata " batada. Kmr sa duk duniya . Cikin dan daga murya Ummi tayi kiran zeenat .
DEENi ya yamutsa fuskar sannan ya langwabar da kai yace kibarta kawai "first lov .
ki zuba min da kanki nafi son naci dagareki dan ma banson wahalar dake ne ma da sabon girki zaki min yakarasa fadar maganar cike da shagwaba " ummi ta dubesa ta sake yin dariya tace Allah yashirya min kai yace Ameen yana kashe mata idansa .
byn yagama cin abinci duk da bawani abin kirki yaci ba "Amman hakan yatiwa ummi dadi ko bakomai ya dan saki ranshi ba kmr kwanaki ba" wayarsa ce ta sake karade parlour da kara wanda tun soma cin abincinsa yake jin kukanta "Amma ya" share.
ahankali yasa hannu ya dauki wayar yana kallon screen din " sunan FK yagani rubuce yana wayo "tabe baki Yayi kana ya manna wayar da kunnenshi , , FK najin alamun an daga wayar yace Yayi angon zeenat da girma "kujerarka . DEENi yaja tsaki yace ya'akayi ne" sarkin matsala.
bangaren FK kuwa shekewa Yayi da dariya sannan yace ina waje ina jiranka fa dan banson nashigo muyi westing time dan nasan halinka da son jikin tsiya " shima DEENi bay wani damu da shigorwasa ba dan baya son ummi tasan inda zashi ,
'Umminsa yake kallo har sanda yagama" waya sannan yace mata shi zai fita sai ya dawo tayi masa a dawo lfy " mikewa Yayi tsam cikin tafiyarsa ta kaisata ya nufi hanyar kofar fita ya daura hannushi kan handle ummi takira sunansa ya juyo yana dubanta tace kar kade fa yayi murmushi yace love you mum ya murda kofar ya fice .
Tsaye ya iske FK shi kadai jingine da jikin motar DEENI hannuwansa rungumeta da kirjinsa DEENi ya Mika masa suka gaisa sannan suka wuce kai tsaye gidan big dady.
FK na gaba DEENi na biye dashi a baya har suka karasa cikin gidan suka nufin inda suka san zasu tarar da big dady .
zaune suka hango tsohon mai tarin shekaru da dattako,sai dai" ya dan manyanta kadan domin shine "dan" Muhammad bello khaliyal na farko Kuma shi ke yanke hukunci ga duk abinda yataso dangane da komai" na cikin family .
Zaune yake idanunshi manner da medical glass "da Gani kasan nakara lafiyar ido ne.
suka karaso inda yake da sallarmasu ,da fararsa yake dubansu.
ya ajiye jaridar daily trust din dake hannushi gefe cikin sakin" fuskarsa dauke da murmushi ya amsa sallamar sannan suka gaidashi ya amsa yana tambaye aikinsu" suka ce alhmd .
shr yabiyo baya tsawon lokacin kafin da tsohon ya dago ya sake dubansu.
da fk, suka hada ido dan DEENi tun byn gaisuwar da Yayi masa Yayi kasa da kansa yana kallon yatsun kafarsa" tsai Yayi yana nazarinsu duka sannan yace lfy dai naganku haka duk da yana ganinsu koda yaushe "amman wannan zuwan nasu da dan banbanci "sai daya sake maimaitawa, tambayarsa sannan fk Yayi gyaran murya yasoma yi masa bayanin abinda ke tafi dasu.
Sannan yakara danashi maganar tsakaninsa shemah .
big dady yaji dadi Sosai matuka da jin haka duk da yasan kusan irin aure da akeyi kennan a family din .
Amman duk da haka yaji dadi fiyye da kowani aure da'akeyi family din.
Yana murmushi yace har kun daidaita junan ku kennan ?
fk Yayi tsuru tsuru yana kallon big dady" yayinda shi DEENi har zuwa yanzu kansa na soke a kasa" yana jin duk abinda big dady ke cewa. take yaji karfin gwiwarsa tayi kasa big dady yace uhmm kun gama daidaita kanku ?
still fk ne ya sake bashi amsa yace A'a sai dai shi DEENi ya sanarwa umminsa" amman bata amince da abun ba.
big dady ya kira sunansu daya byn daya, a tare suka dago, suka zubawa masa ido.
big dady yace kuje ku nemi amincewarsu ku daidaita tsakaninku inyaso sai asan abin yi
DEENi zaune tamkar an dasa shi ji yayi kmr kasa ya tsage ya shige ciki haka yaji " dan wani irin kunya yaji tamasa rubdugu dan haka da kyar yasamu ya iya Mikewa tsaye suka bar part din jikisu duk a sanyaye barin ma fk da bai taba tunanin haka ba .
Suna fitowa daga part din big dady" DEENi yasoma zagin fk yana bude masa wuta , yace daman ka kawo ne a sake nuna min iyakata ?
,fk yace haba DEENi ka natsu mana musan abinyi "wlh ko ni kaina bansa haka zata faru ba dan Allah kayi hakuri ka sausauta wlh na dauka komai zai zo da sauki shiya gaji nace muje . wani irin duba DEENi ke jifansa dashi " DEENI yace ok wani sabon rainin wayon zaka sake kawo min .
gabadaya fk yakasa cigaba da magana illa idanu daya zubawa DEENi yanzu yace son zeenat yake" yace masa sam ba haka ba .
DEENi ya tsaya sosai suna kallon juna shi da kf .
a fusace yace kasan Allah kasan yadda zakayi da haukar, damuwar da kaman nami dan ban ai keka kabani irin wannan gurbataccen shawar ba.
Gabada ka rusa min komai , fk dayaga hassala shima jin zantuttukan da DEENi ke furtawa .
A harzuke yace ai bani nace kazo min da shawarar taka ba " iya abinda naga zan iyayi ne" na sanar maka.
Kai tsaye ka fito kace daman can kana son yarinyar" bancin haka daga baka shawarar , meye naka na damuwa daita .
DEENi bai san sanda ya dunkule hannushi" zai kaiwa fk naushi a baki ba.
Take fk ya goce yana kallonsa gabadaya yanayinsa yagama canzawa sai huci yake kmr mayuncin zaki .
Fk yace wai meke samunka ne ?
kodai kasha wani abu ne yau , a fusace DEENi yace wuta nasha ba wani abu .
Sai daya furzar da huci mai zafi sannan yace kasan Allah sai dai kasan yadda zakayi da tashin hankali daka jefani ciki .
fk yace idan ba haka ba Kuma fa "DEENi Yayi kyacci yace I will finish you.... ya wuce fuuuuuu kmr wani zaki .fk yabi bayansa da sauri yana kiran sunanshi yayi banza dashi yacigaba da tafiyarsa da sassarfa har yacimasa ya ruko hannushi "da sauri DEENi ya juyo, ya bige masa hannu " fk yace haba DEENi meyasa kake daukar komai da zafi ? DEENi yace da fetir ne kasan Allah idan har kana son zaman lafiyarka dani " wlh ka nemo solution ya wuce nan yabashi .
Cikin tsanyi jiki zeenat ta mike tsaye byn taci kukanta ta koshi . bathroom tashiga ta wanke fuskarta tukun sannan ta fito' ta murda handle din kofar ' daidai lokacin da shemah ta mike tsaye itama " tasa byn hannuta tana goge fuskarta " yayinda wasu ke sake silalowa" wani irin kallon zeenat ke binta dashi ,kmr takasheta haka take ji wanda kallo daya shemah tayi mata "tarasa dalilin dayasa zeenat ke mata irin wannan kallon haka .
Zeenat tace munafuka ashe zuwan dakike mana gidan" ba dan Allah kikeyi ba.
Shemah tace lfyr kuwa , bangane nufinki ba.
zeenat tace zaki gane manufakar banza kawai daga karki sake shigo mana gida tunda kinada manufarki ta zuwa .
jin haka yayi mugun hassala shemah, gashi daman tana tare da haushin abinda DEENi Yayi mata , hannuta tacire ta dauke zeenat da wani mari wanda ya frigita zeenat .
ai kafin ta sauke hannun zeenat bata tsaya wata wata ba" ta damki makonshi shemah tace ni kika mara.. kika mareni daga bazaki sake marin wata ba ,wani irin nishi shemah ke fitarwa tana mutsu mutsun kwatar kanta har hawayen wahala take fitarwa ,zeenat tace ba kukan soyayya kikeyi ba zan aikaki abarzahu inyaso kya ji dadi yin kukan da tushe .
Km still tana damke da makoshinta " tace nufinki kice kina son yaya DEENi ko .
Wlh yarinya karyar tasha karya " da kyar shemah tasamu tasa iya karfinta ta kwace kanta daga rikon da zeenat ta mata .
Take suka suma kwokuwa da juna gabadaya hayaniryasu ta cika gidan ,a tsorace ummi takaraso gurinsu ta shiga tsakanin" zeenat da shemah wacce har shedewa take saboda kukan dayaci karfinta gabadayansu fuskarsu tayi jazir,.
zeenat na kuka shemah na kuka cikin fushi da bacin rai ummi ke tambayar su abinda ya hadasu fada amman cikin bbu wanda yabata amsa har sanda " DEENi yashigo gidan ya samesu tsaye cirko cirko , yaja ya tsaya yana jan tsaki dan tun shigowarsa yake jin hayaniryasu yanzu ma ganin ummi ne yasa ya tsaya , da kallo yabisu dashi " ummi na ganinsa tace yauwa gara ma daka shigo , ta sanar masa abinda faru ummi nagama fada masa takama gabanta .
ai yana gama jin abinda umminsa tace ya fara dauke zeenat da wani mahaukacin ,mari dayasa taji dan guntun fitsarin dake makale da mararta zubowa , itama shemah bata nata sannan ya gwara kansu gabadaya waje daya jikake gum....... Bbu wacce tayi kokarin yin kuka cikinsu dan sunan halinsa sarai bakaramin aikinsa bane ya hada musu da punishment.
tsawa ya daka musu yace kowace ta takama gabanta tun bai sabauta musu jiki ba , hade da cewa yan iskan yaran kawai .
Dakinsa ya wuce yasoma zariya daga farkon daki zuwa karshe hannuwansa duka yasa yana balbale botura rigarsa" wani irin zafi yake ji a zuciyarsa tamkar ana zuba masa barkono , gumi ke tsatsafo masa takoina kmr ba dazu yayi wanka ba " sai daya balle botura rigar ya cire yayi jifa daita ya fada kan bed idanunshi na kallon sama celling dakin ahankali .
Ahankali yasoma runtse idanunshi har ya rufesu ruf gabadaya tunani mafuta kawai yake tabbas indai sai ya tunkari yarinyar nan da sunan yana sonta to wlh ya hakura daita har abada kai auran ma yafasa gabadaya .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 15-16
Tare zeenat suka jero da shemah" suna kuka saboda marin da yaya DEENi yayi musu yashigi kowannesu" amman hakan bai hana zeenat aikawa shemah da zagi iri iri ba" har suka karaso parlour" inda ummi ke zaune tayi xuru ...hade da zubawa sarautar Allah ido abin ya faru Yayi maseefar girgiza zuciyarta . kirasu ummi tayi tana sake tambayar su" abinda ya hada su fada haka" alhalin da can ba haka sukeyi ba,.
shemah ce tasoma magana cikin kuka Allah ummi ni bansan nayi mata wanj abu ba" kawai ganinta nayi tafito daga daki" tana wasu abubuwa ,daga nan Kuma sai ta hau ni da zagi ,.
zeenat zatayi magana ummi "ta katseta tace ya isa banson jin komai daga bakinki .
dan ta fara zargin wani abu dangane da abinda ya faru yanzu " ummi tayi musu fada sosai da nasiha mai ratsa jiki .
tace karta sake ganin sunyi fada da juna , shemah ce kawai ta iya amsawa tayi wa Ummi sallama ta wuce Amman it's zeenat kishi tattare da kunar zuci suka taru suka tsaya mata a kirjinta hakan yasa takasa cewa komai .
Ko byn fitar shemah ma "zeenat tsaye tayi tacigaba da kukanta tana jin haushin ummi data hanata yin magana ,alhalin gaskiya tana Gani .
yatsun DEENI ne kwance a gefen fuskarta wanda ya haddasa wajen dan tasawa , dan gabadaya fuskarta ta canza kala tayi jazir ".
tun Ummi naji haushin kukanta nata har ta dawo tausaya mata dan tasan , ta daukar kanta wahala ne in dai akan DEENi ne .
Ummi na kallon yatsun DEENi kwance a fuskarta take taji wani abu ya tsarga mata " har cikin zuciyarta taji kmr ta zubda hawayen takaici kiran sunanta tayi hade da nuna mata guri zama kusa daita.
cikin sanyi jiki zeenat ke daga kafafunta inda take tsaye har ta isa inda Ummi ke zaune ta zauna "kmr yadda ummi ta umarceta ,
Ummi ta zuba mata idanu kawai tana kallonta dan abun nata na neman fin karfinta "tsawon lokacin zeenat tana risgar kukanta ,batare da ummi tace mata komai ba ,
sai da ummi ta gama nazarinta tsab sannan tace duk wannan kukan na meye haka ?
Kar kice min duk akan son DEENI kike neman yin fada da er'uwarki . Saboda Allah Ke ko kunya abinda kika aikata baki ji ba .
" zeenat tayi shr takasa cewa komai dan ita kadai tasan yadda take jin zuciyarta, .
Ummi tace meyasa zeenat , meyasa bakya jin maganata ne ,irin abinda zaki min kennan ko wannan shine kalar tarbiyar dana baki uhmm ?
kina ganin haka kawai zanki amincewa da auranki da DEENI " kiyi tunanin mana .
koda yake baki san ciwon kanki ba shiyasa.
' ballanantana" kisan gata neke miki .
mutumin da bai san da zamanki ba, bai damu dake ba" ko kallon arziki baki isheshi ba" shine zaki zauna kina westing din hawayenki akansa takarasa fadar maganar tana takaicin zeenat,.
" Ummi ta sake maida dubanta sosai gareta tana mamakin yadda zeenat din ta canza cikin lokacin kadan . Alhalin ita duk iya lokacin ta dauka tare da yarinyar bata taba ganin irin haka atattare daita ba
cikin kuka zeenat tace ummi kinki amincewa da aurenmu yaya DEENi .
ai gashi nan ai ...... sai km tayi shr" dan jin kunyar abinda take kokarin son fadi "dan haka tacigaba da sheshekar kukanta,.
" Ummi tace uhm Ina jinki kikarasa mana , tace wlh wlh idan kika kuskura" kika bari yasan kina wannan" haukar akansa " kin shiga uku da wulakanciinsa " .
zeenat ta zube nan kasa tana kuka hade da kamo kafafun Ummi .
tace dan Allah Ummi ki Amince da maganar yaya kinji "wlh ni Ina sonshi a haka " kiyi mana addu'a kawai" bbu abinda zai faru inshallahu .
Ummi ta sake zuba mata idanun tana kallon sarautar Allah, da rashin kunya irin ta Zeenat , su fa daman yayan zamanin nan ba wata kunyace ta ishe su ba .
,ummi tace" da bai ce yana sonki ba fa ?
Ta jeho mata tmyr " data girgiza zuciyar Zeenat " din" tayi kasa da kanta tana zubda kwalla ita fa ganinta bbu abinda tayi .
a ranta ko cewa tayi ai shima yana sona tunda ya iya furtawa .
Ummi ta sake kiran sunanta tace zeenat idan bakiji kunyata" ta matsayina ta mahaifiyarki ba " ,
Ai kya ji kunyata ta ummin DEENI .
amman tunda kin nacewa auren DEENi km kinji" kin Gani to wlh duk abinda kika Gani Shikenan , .
da ma sharadi kozan amince da auranki dashi .
Banda zuwa kawo kara kum duk abinda yabiyo baya babu ruwana ciki sai dai ki haye abinki tunda shi kika zaba .
da sauri zeenat tace to....ummin indai kin amince bbu ma abinda zai faru sai alkhari .
Wani irin kallo Ummi tabita dashi wanda da Gani kasan na tausayi ne.
Dan yanzu ta daina mamakin duk abinda zatayi .
da murna ta tashi ta koma bedroom tayi kwanciyarta tana jin dadi Ummi ta amince da aurenta da yaya DEENi . idanunta ta lumshe" tana jin Yadda soyayyar DEENi ke sake huda zuciyarta .
Yinin ranar da murna zeenat tayi shi cike da tsantsar farinciki ga tarin tunanin DEENi dake sake mamaye kowane part na jikinta yau tazo mata da abubuwa masu yawa bacin rai da farinciki .
duk abinda takeyi Ummi na hankalce daita . kallonta kawai take tana binta da idanu .
Washegari zeenat" ta zaci ummi zata sanarwa yaya DEENi cewa ta amince" sai kurum taji ummi ta share da zance gabadaya , koda dai da wuri yake fita ,.
wasa wasa ummin ta share da maganar kwata kwata garakar gabanta kawai take , .
tana jin lokacin da dama idan yaya DEENi ya dauko mata maganar zata katse shi tace kar ya dameta ya rabu daita .
sai dai abun yana damun zeenat matuka yadda kullum yaya DEENi ke sake daure mata fuska da wulakanci iri iri. Amman takan masa uziri ganinta killa sai lokacin da ummi ta amince masa ' sannan zai daina nuna ko in kula dayake ,mata.
shi kansa yaya DEENi baisan cewar zeenat din tasan da zance ba. kullum dai ya shigo wajen ummi sai yayi mata nacin ,shifa yana nan yana Jirata.
ita km tace kar ya dameta bayace yafi son Yar jami'a ba .
"to yaje ya nema Amman ita sam bazata bashi diyarta ba , .
yana fita zeenat ta matso sosai kusa da ummi tace ummi dan Allah bakince ,kin hakura ki amince tunda na yarda ba .
sai ummi ta dube tana watsa mata harara tace sakariya bazan kawai".
kalli fa ko kallo arziki baki isheshi ba .Amman duk kinbi jin tsamgwami kanki .dan fitina tsiya da jaraba , .
ni duk abinda nake Ina yi ne "dan Kare matuncinki , ba dan Ina kin aurenki da DEENi bane .
tunda yashiga dakinsa bai sake fitowa ba" sai dai yatashi" yayi sallah kawai yakoma gado .
yasawa ranshi, cewa ya hakura daita kwata kwata dan baiga dalilin da zai sa shi ya dinga batawa kansa lokaci ba .
Kwance yake akan makeken royal bed dinshi ya rufe kanshi cikin alky blanket mai matukar taushi ,.
bacci yake Sosai hankalinsa kwance ya rufe koina na jikinsa banda fuskarsa saboda yanayin unguwar su mai dauke da sanyin ni'ima ,.
ahankali ta bude Kofar dakin" kwance ta ganshi, yana sharar baccinsa ,sai yanzu hankalinta ya kwanta gangar jikinta yasamu natsuwa , kusan kwana biyu kennnn rabon data sashi a idanunta,.
ahankali take daga kafafunta har ta isa inda yake,. kwance
idanunta ta zuba masa" tana kare ma kwakkywan fuskasa kallo yadda tayi kyau tana fidda annuri na musamman .
Ahankali ta lumshe idanunta " tana jin wani irin tsanyi nabi jijiyoyon jikinta.
Ahankali ta bude idannuta suka sake sauka akan beautiful face dinshi ,.
fuskarsa ta kurawa ido har wani kyalli kyallin kyauwu take fitarwa , cikin rawar hannu takai hannuta gefen fuskasa ta dan tashafo . wani irin taushi taji wanda ya sake dulmiyar daita a duniyar kaunarsa .
Take taji koina na jikinta ya mutu sai wani yammmmuu take ji.
ita kanta tarasa dalilin dayasa take jin haka ajikinta .
ganin bacci yake sosai yasa ta juya ahankali tabar dakin cike da shaukin soyayyar DEENi dama Ummi ce "tace ta dubashi dan har lokacin fitarsa aiki na neman wuce .
Koda ta sanar da Ummi cewar bacci yake har yanzu, yasa ummi ta nufi dakin" dakanta kusa dashi taje" kai DEENI sai data kira sunanshi" kusan sau biyu" sannan ya dan bude gengerous eyes dinshi ya kalleta dashi "tace lafiyarka da har yanzu dabaka tashi ba , .
tacikin blanket din ya dan yi Mika hade da salati sannna ya dan gyara kwanciyarsa yace lfy first lov ,natashi har nayi sallah " to bazaka aiki bane yace zani.
Ummi tace Ina jiranka idan kagama.
ya amsa mata da kai kawai .
a hankali ya zame jikinsa daga cikin blanket din , daga sai dan gareni wando Mika ya sake yi yasa hannunsa ya gyara jijiyarsa dake mike .
Sannan ya shiga bathroom,.
duk da yamakara hakan bai sashin yin sauri ba, wanda normally haka yake da sanyi jiki .
wanka yayi, ya fito. ya shirya cikin kakinsa da suka dace da surar jikinsa, har ya murda handle din kofar "dazata Kai shi parlour ya tuna Yayi mantuwar wasu files a dakin baccins" dan haka yakoma ciki daukowa .
Tsaye take a bakin kofar dakinsa tafi kusan minti biyar a wajen tana saka dawarwara yadda zata sake shiga Bedroom din sa.
ummi ce tasake aikota .
Ta dubashi dan taji shr har yanzu .
tana son tayi nocking Amman tsoro da fargabane suka hanata .
daidai wannan lokacin DEENI ke shirin fitowa daga part dinsa . ta daura hannuta kan handle din kofar.
ai agigice cikin matsanancin tsoro tasaki wani irin kara da tasa DEENI , tushe kunnuwanshi " da duka hannushi "ai batasan sanda ta fada saman fadaden kirjinsa ba .
hade da runtse idanunta gam dan tsabar jin tsoro , batasa abinda zai mata ba Jira kawai take taji saukar mari dan gabadaya tagama frigicewa.
Amman abin mamaki sai taji sabanin haka.s shiyasa tasaki jiki ta sake narkewa a fadadden kirjinsa tana shakar dadeden kamshin turarenn jikinsa mai birkita mata tunani "a duk sanda ta Shaka .
wani irin ya dinga ji ajikinsa, yrrrrrrrrrrrrr.... yrrrrrrrrrrrrr abinda bai taba faruwa dashi ba kennan" jikinsa ya hadu da wata macce" shi tunda yake ma ko hannun macce bai ta ba rikewa ba ballanantana yakai ga hada jiki .
Ya dinga jin wani irin wani irin a gangar ajikinsa.
gabadaya tsigar jikinsa suka mike tsaye , yaji da zai iya " rungume zai yi kawai zaiyi .
ko zai ragewa zuciyarsa radadi da ciwon dayake ji.
Amman Ina... Sam bazai taba iya aikata hakan ba .
ganin yadda tayi lamo ajikinsa ne yasa, cikin takaici ya bambareta daga kirjinsa cikin tsanyi jiki,
tsayuwa ce ta gareta , zuciyarta ke neman tarwatse tsabar tsoro da rikincin data tsinci kanta ciki.
,ko ta kanta bai bi ba ya tsuke fuska yana kallonta ,itama idannuta ta zuba masa ko kiftawa batayi.
ga wani irin tsoransa dake lugudar zuciyarta.
ahankali muryasa a sanyaye yace malama ki daina min "irin wannan kallon na munafurci .
in ba haka na kwakule idanun rashin kunya tsaki yaja hade da bin gefenta yazagayeta ya wuce kai tsaye part din umminsa yashiga" sai dai bai ganta ba,.
dan haka ya wuce main parlour 'dan yasan tunda bata dakinta, tana can .
zaune yasameta tana yin breakfast fuskarsa a dan sake yakarasa har kusa daita ya zauna yace gud morning my first lov, ta dubeshi fuskarta dauke da murmushi tace morning dear ,kata tashi lfy girarsa ya dage mata.
cikin tsnayin jiki zeenat takaraso wajen, kallo daya DEENi Yayi mata yasa ta canza hanya batare da ta sake kallonsa , kan wasu kujeru dake ajiye a gefe ummi tabishi da kallo batare da tace masa komai ba " da kanta tayi savice , din shi ,shi km sai wani zuba mata shawaba yake , .
coffee kawai ya iya yasha, ya mike tsaye cikin hanzari sakamakon wayarsa data dauki kara yana dubawa yaga ogansa ne daga wajen aiki .
dan haka yayiwa umminsa sallama da hannushi ya fice wayar manne da kunnenshi .
Zeenat data zuba tagumi ,Da hannu biyu tabi bayansa da kallo har yabar gurin idanunta na kansa , itama ummi data dauke idanunta daga kan DEENI "zuru tayi tana kallon Zeenat din , tana girgiza kanta .
waskewa zeenat tayi hade da sakarwa ummi murmushin dole ummi tayi mata dakuwa da hannu .
Byn DEENi ya gama amsa wayar oganshi ne yana zaune cikin mota wayar fk yashigo " yasa hannu ya dauki wayar ya duba ganin fk ne yasa ya maida wayar ,mazauninta .
Yakirasa yafi sau gomasha daya Amman yaki pic sai a karo na shabiyu ne ya danna wani abu "sai ga muryar fk radau yakarade koina a motar , hello.... hello DEENi kana jina ....
Yayi shr yaki yin magana,sai ma cigaba da yayi " da direving dinshi .
fk yace haba DEENi ya kana jin zaka min shr. "duk fa" maganar bata kai haka.
afusace DEENi ya katse shi yace maganar tafi haka har ta zarce haka a waje na.
km wlh wlh karka kuskura, ka tako inda nake da sunan kasan ni ai bansa cewar da kungurumin ,dan iska nake zaune ba.
fk yayi murmushi yace Allah dai ya huci zuciyarka ,dan shi.
bai fiyye fushi ba" kwata kwata ma bayason duk wani abinda zai kawo masa tashin hankali .
dan haka yayi tabawa DEENi hakuri hade da bashi baki .
DEENi yaja numfashi ya sauke ajiyar zuciya . hakan yasa fk ya gane cewar ya sauko kennan fk yace to yanzu yazamuyi da maganar da big dady yace.
DEENi ya tabe baki yace ya dai zakayi dan ni tuni na hakura da wannan yarinyar , karma ka km yimin wannan bazar zance.
daidai da yakaraso wajen aiki ,ya katse wayar fk batare daya tsaya ji mai fk din zai km ce masa ba .
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 17-18
Wata daya kennan fk yaji "shiru DEENi bai km yimasa zance maganarsa da Zeenat ba musamman" yazo gurinsa dan zance daman Kuma sun dade basu ga juna ba" sai dai sukan yi waya lokaci zuwa , lokaci dama ya kirashi a waya cewa yana nan zuwa .
Byn sun gaisa fk yace friend har yanzu ban sake jin batunka da yarinyar nan ba .
deeni ya gyara zama ,hade da yaja tsaki sannan ya lumshe idanunsa dan takaici da Haushi maganar .
ya zubawa fk ido yana kallonsa kawai domin rasa me zaice masa Yayi ,tsawon lokacin suna zaune a haka sannan fk yace friend hakuri zakayi dan Allah ba wai Ina son dawo maka da hannun agogo baya bane .
Amman idan maganar danayi akan Zeenat ya bata maka rai, kayi hakuri.
ahankali deeni ya furzar da iska mai dumi ya miko hannushi ya dafa gwiwar fk , Friend ban tasamun abinda ya bani matsala kmr maganar yarinyar nan" abin haushi duk lokacin da nayi kudirin hakura daita sai nakasa .
Kullum addu'a ta Allah yaye min ita daga raina Amman abin ya faskara ko son yarinyar ne yakamani "oho " fk yayi murmushi yace lallai sonta kakeyi Allah yasa itama ta soka haka .
DEENi ya gintse fuska yace Ina ruwana daita first lov ce kawai damuwata ,data amince da yanzu an wuce gurin Amman tsohuwar nan sai cewa take zan cuci Yar mutane ita bazata bani Yarinyar karama ba inzo Ina bata wahala fk yace sanin halin ka tayi dan kai din bana wasa bane kana raina yarinyar ne dayawa shiyasa ummi batason aura maka ita wani lokacin sai inga kmr da gaskiya ummi DEENI yayi masa wani kallo dan ni bason iskanci idan abinda yakawo kennan kana iya tafiya .
Fk yace zanje in sameta da kaina kar damu .
deeni yace dama kabar ta kawai dan ko kaje ba amincewa zatayi ba.
nasan halin first lov , da zata yarda da tunin ta amince .
na dai fada mata cewar ni na hakura dayin auren gabadaya" inda tagaji da zamana haka tasan abinyi .
Fk yayi ta dariya tare da xolayar DEENI" friend ka dai shiga da yawa da ka'ajiye duk wani girman kai ,ka dinga kiran yarinyar kana janta ajiki ,idan ummi taga haka zatafi yarda da gaske kakeyi "Amman kai kullum fuskarka a hade kmr hadari .
DEENi ya tabe baki, kasan Allah bazan taba iya kiran ko wace irin yarinyar bace, da sunnan zance koba Zeenat ba. kai ma abinda kariga kasani ne "bansa ta Ina zan soma ba ,nifa bana kawo Zeenat a raina ,in dai first lov ta yarda " to tayi hakuri ta aureni kawai dan ni banda wani lokacin ya mace . dan ma taji dadi ta samu miji irina ,yakarasa fadar maganar yana jan tsaki fk yayi dariya yace friend banda yabon kai fa , DEENI ya dan yi murmushi gefen baki har dimple dinsa ya lotsa kai ma kasan gaskiya fada ne dai kawai bazakayi cikin "nida ita wazai taimaka wani ?
Bbu abinda zata nuna min " fari ne kawaiya ceceta " wanda kai kasan ko man bleaching takara bazata taba kamo nawa ba "fk yace ai shiyasa ka daurawa kanka girman kai al'amarin mata" km duk da kafita kyau ita zuciyarka ta zaba ,ta zama abokiyar rayuwarka " zanyi maka iya bakin kokarina ,.
DEENi yabishi da kallo yace sannan ya maida bayansa ya jingina da kujera , dama kabar, damun kanka akan zance yarinyar nan , wai dole ne sai na aureta ,fk yace tunda nace zanyi kabarni mana ,na gwada sa'a ta ko ummi zata yarda . DEENi ya daga kafadarsa alamun shi yasani ,sannan yace tunda ka nace kaje din Amman idan labarin ba may dadi bane ,karka zomin dashi ba ,.
Kmr yadda fk yayi alkawari haka ce takasance yasamu ummi da zance byn sun gaisa ne yace daman akan zance deeni ne da Zeenat" ummi najin haka ta canza fuska " har tasa karfin gwiwar da fk yazo dashi " yayi kasa.
Ahankali yacigaba" dan girman Allah ummi kiyi hakuri ki amince da auren nan "saboda dukkansu naki ne a ganina wannan abin farin ciki ne .
Ummi ta sake tamke fuskarta Sosai tace faruk Ina matukar ganin kimarka da mutuncinka zai fi kyau kabar zance nan" bana jin cewar zan iya amincewa .
fk yayi shr yana tunanin yadda zai bullo mata can dabara tazo masa yace to Shikenan Amman naso ki Amince domin deeni yana cikin wani hali nason yarinyar nan. daidai lokacin da Zeenat ta dawo daga gidansu Maryam tanac kokarin shigowa parlour ummi .
,karaf zance ya fada cikin kunneta cak taja ta tsaya jikinta ya dauki kirma .
Fk yace ummi kin san halinshi baya daga cikin mutane masu magana biyu ,ya min ransuwa ba zai tabayin aure ba ,in ba Zeenat ba ,km duk duniya ita ya Gani yake so.
zamanshi haka nasan yana damunki ummi tace in duk duniya Zeenat yagani yake so ita Zeenat din ya sameta yaji ko tana son shi ? Ko haka kawai dan shi yana sonta" zan dauke diyata ta nabashi batare da ya nemi amincewarta ba.
Nifa bazanyiwa diyata auren dole ba dan kawai Ina son na faranta masa rai ba .
Daga inda Zeenat ke tsaye tana jin komai" take jikinta ya dauki yacigaba wara har wani zazzabi zazzabi taji yana neman rufeta , kafafunta suka Gaza daukarta sakamakon kirmar da suke , nan ta sulale kasa tana jin yadda gabanta yashiga faduwa da sauri da sauri , tarasa dalilin ummin nakin aurenta da yaya DEENi .
alhalin tasan yana sonta har haka .
,to hakan na nufin ummi tafison yaya yaje waje ya aure wata , sabanin ita kennan .
kawai batayi aune ba taji saukar hawaye nabin kuncinta .
Da sauri tasa Hannuta ta dangwalo hawayen dake bin fuskarta, tana kallo ta girgiza kai kawai tana jin tamkar an diga mata dalma ne zuciya ,.
Ta runtse idanunta ahankali muryarta cike da rauni tace meyasa ...
Meyasa ummi kike son ki ruguzamin rayuwa please ummi ki amince na auri yaya DEENi , Ina sonshi har bansan iya kar kaunarsa a zuciyata ba " bazan iya rayuwa in bashi ba
Fk ya fahimci abinda ummi take nufi shiyasa yace ma DEENi ya dinga kiran yarinyar suna hira. ko km yajata ajikinsa . Ta hakan ne komai zai zo da sauki , fuskasa dauke da murmushi yace ummi idan dan wannan ne ,karki damu , duk wannan me sauki ne zamu tuntubi yarinyar muji , idan bata amince ba Shikenan .
Ummi tace da dai yafiye muku" ba ku tsaya girman kai ba, fk ya sake yin dariya yana girgiza kai yayi mata godiya ya mike .
Jin da Zeenat tayi fk yayiwa ummi sallama ne yasa tayi hanzari mikewa da sauri tashige bathroom din parlour din dake manne da falon nan ta fashe da wani irin kuka ita kam zuwa yanzu tafara jin haushin ummu .
Fk na fita yakira deeni bugu biyu ya dauki wayar , fk yace friend kafara da bani goron albishir ,cikin yanayi na ko in kula deeni yace kada kace min first lov ta saurareka ?
Fk yace ta saurareni km inshallahu zamuyi nasara da alamun ummi ta amince ,.
duk yayi masa bayanin yadda suka yi da ummi ,
yakarasa zance da ummu ta nuna tanason asamu yarinyar a nemi amincewarta .....
DEENi yayi shr sannan yace to ai wannan shine mai wahalar dan bazan taba iyawa ba , fk yace wai kai tsorota kake jine ko yaya ?
,ai take deeni ya hassala a fusace ya aiko masa da wata irin uwar ashariya " wanda yasa fk yayi sauri cire wayar daga kunnenshi ,ya dan duba sai daya tabbatar daya yana kan layi. sannan ya mayar yacigaba magana" haba friend meyasa kake saurin daukar zafi akan abinda bai yakawo ba .
bance dole sai kasameta da kankaba ,ni dakaina zanyi komai.
sai Kuma ya sausauta yana jan numfashi yace ai kai ne da wani zancen baza.
naji tsorota akan me ,raini ne kawai banaso , yanzun dai kai kaje kasameta kuyi magana da in ni nakirata bafa ra'ayinta zanjira ba. umarni kawai zan bata fk yace Shikenan sai na nemeka .
Zeenat zaune gaban TV dake manne a parlour su ta hada uban tagumi ,hade da zubawa TV idanun . Kallo daya zaka mata , kasan kwata kwata hankalinta bai kan shirin da'ake gabatarwa .
gabadaya tunaninta ya kashi gida biyu .
ga tashin hankali ummi taki amince wa da aurenta da yaya DEENi. ga kamil da yasako, gaba da zance yanason kai maganarsu gurin big dady, .
hankalinta a matukar tashe yake .
har ummi takaraso inda take zaune taba tasani ba".
ummi ta zuba mata idanu kawai tana nazarinta sannan ta numfasa sai data kira sunanta tukun , Zeenat tayi saurin juyo a frigice tayi firgigib tana duban ummi .
idanunta ta zubawa ummi kmr wata mara gaskiya " ummi tace wai ke wace irin sakarriyar yarinyar ce" da kwata kwata baki san ciwon kanki ba "kalli ummi ta nuna jikin Zeenat da dan yatsanta , dube yadda kika dawo ,duk kinbi kin sakama kanki tunanin banza ji yadda kika koma duk kin tsotse kin rame dan jarabar tsiya ,anason a karemiki mutuncinki ,kinki natsuwa, kisan haka .
sai kiyi tayi ai.
cikin haka fk yayi sallama yashigo ya zauna akan kujerar one site yana gaida ummi
Ta amsa masa fuskarta a gimtse da tasan kwanan zance " Zeenat ma ta gaisheshi tsam mike taje takawo masa abin sha .
,ummi ta tabe baki tana hararata dan takaici sannan ta sake kai dubanta ga fk din" tace DEENI fa yana dakinsa .
Fk yayi murmushi yace ai ba gurinsa nazo ba ,jin haka yasa ummi tashare , ta cigaba da kallonta , gabadaya parlour ya dauki shr tamkar babu mutane a cikinsa baka jin motsen komai sai karar TV .
Zeenat kam kamewa tayi tashiga hankalita dan motsi kadan , ummi zatace tafiye rawar kai .
ganin shr yayi yawa yasa ummi ta mike tabar gurin ta nufi dakinta . Parlour ya saura daga Zeenat sai fk .
yana Ganin ummi tashiga dakinta yasa ya juyo yana fuskantar Zeenat yace sister wajenki nazo fa . tace to Allah yasa dai lfy yace lafiya nasan zakiyi mamakin zuwa na ?
Tace bawani mamaki killa akwai abinda kake son nayi maka ne .
yace ba wannan bane nazo ne dan nasanar miki da wani abun alkhari koda yake bansan yadda zaki dauki abun ba.
tsab Zeenat tagane abinda yakawo shi gabanta taji ya tsananta faduwa ,.
fk yace deeni ya duba duk cikin en'mata dake cikin family din nan.
yaga bbu wacce tayi masa km tadace dashi sai ke .
Zeenat ta zaro idanu waje kmr da gaske ta nuna kanta tace ni fa kace yana so...
Fk yace bawani abin mamaki bane , Dami kika tsinta a kala ,a ranta tace maganar ka gaskiya.
fk yace yanzu me kika gani idan kin amince , magana zata wuce gurin big dady kai tsaye batare da bata lokacin ba .
ta tabe bakinta kmr batayi murna dajin zance ba , sannan tace gaskiya kagaya masa kawai yayi hakuri dan ni narigada na tsaida wanda zan aura ,.
fk yace waye shi km a ina yake km kin kai maganar wajen big dady ne ? Duk alokaci yajero mata tambayar ,tace Ko daya muna dai shirin yin haka fk yace yace shi din wanene tace wani ne acikin family dinmu yake humm yace inbaki shawara ta daga masa kanta" zan so ki dakatar da koma waye.
dan kowa zaki aura ina tabbatar miki ba zai taba kai kmr DEENI ba .
ke kanki kinsa samun irin su DEENi sai an tona. zakiyi alfahari samun mijin kmr sa "mata dayawa suna ,sonshi ban sani ba kodan sun fahimci qualities dinsa ne .
sai km yace amman bazan takura miki ba in kinga bakison shi Shikenan .
ta kalleshi a shashance hade da wani irin salo sannan tace nifa bance maka bana son shi ba na dai kawai kace masa na tsaida wanda zan aura .
Kaga yanzu idan na canza raayina da sauri haka shi saurayin nawa bazai dadi ba .
ka dai bashi hakuri Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhari .
fk yayi shiru yana cizan yatsa hankalinsa yasoma tashi "karfa yarinyar nan ta kwafsa masa yazaci yana mata zance zata amsa da murna ya fadi haka a kasan ranshi.
can km yace to ni yanzu mekike son nace masa ?
Ta sake tabe baki yace Kafada masa gaskiya kawai , yace ba za kiyi tunani akai ba kafin ki yanke hukunci ,ko km kuje kisamu wanda kika san kin amince mata km tasan deeni din sosai tabaki shawara akai, Zeenat tace naji zanyi tunanin .
Fk Yace Shikenan zan sake nemeki zuwa gobe naji abinda kika yanke akai , tace badamuwa .
Byn ya tafi, ne tashiga dakin ummi tana murna cike da farincikin burinta yakusan cika ,fitowar ummi kennan daga bathroom aiko tana ganin yanayinta da alamun tace musu ta amince ,take ta sake daure fuskarta , ta rufeta ta fada, ai gashi nan saboda baisan darajarki ,da kimarki ba sannan bai dauke ki da mahimmanci ba ,yakasa zuwa da kansa sai abokinsa ya turo miki nasan jikinki na rawa kika amincewa ko ?.
Zeenat taaba fuska tamkar zata saki kuka tace nifa ba wani rawar jikin danayi .
ummi tace wlh kiyiwa kanki fada, akan sakarcin da kikeyi ke kmr ba macce ba .
sam bawani jan aji irin na sauran mata .
Zeenat ta sake bata rai sosai .
ummi tace gaki nan ga deeni ,inda shine nabarki dashi ya isheki wando da riga .
A waya DEENi yaji duk yadda sukayi ya dinga mamaki wai wannan yar yarinyar ce zata ce sai tayi shawara to dawa zatayi ? Km ita ce wa ?
Fk yace itace mace deeni yace dan Allah malam imin shiru shiya sa fa kaga bazan iya kai kaina gareta da sunan Ina sonta ba bare tamin salo . Nan km yau zazzagawa fk maseefa yana Ai shi yaja masa duk wulakancin da'aka masa fk yace kwanta da hankalinka kavarni daita kawai nasan zata yarda ma kawai dai itama so take ta nuna mana itama macce .
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 19-20
Shiyasa kaga bazan iya kai" kaina gareta ba da sunan Ina sonta , bare tamin salo .
Nan km yayi ta zazzagawa Fk maseefa hade da cewa ai shi yaja masa duk wulakancin da'aka masa .
Fk yace kwantar da hankalinka kabarni daita kawai ,nasan zata yarda ma ,.
kawai dai itama so take ta nuna mana ,itama macece , nasan jan aji ne kawai na mata Amman ita din wa dazatace bata sonka ,Ina rai inshallahu zamuyi nasara.
Cikin fushi da jin haushi deeni Yace in taki yarda ka kyaleta kawai , yarinya sai kace wata gold sai wani yawo akamin da hankali akanta, yaja tsaki hade da kashe wayar batare daya sake jin abinda fk zai ce ba .
Kwana deeni yayi da tunanin hade da zullumi halin da zai tsinci kansa idan yarinyar nan taki yarda dashi, duk shi Gani yake ba sonta yake ba. zai dai yi aure ne kawai saboda umarnin umminsa, bugu da Kari ma, bazai iya kaskantar da kansa wajen mace ba ballanantana har ya kai shi ga furta kalmar so.
Har zuwa wayewar garin ya cigaban mamakinta ganinta yake , tamkar yau aka haifeta, sannan har zuwa yanzu kallon karamar yarinya yake mata, ashe tasan abinda take yi ,uhmmmm uhmmmm ahankali ya dinga sauke ajiyar zuciya, wai zatayi tunani akai ya sake tunawa da kalmar data fadawa fk to da ko da uban wa zatayi tunani ya furta hakan a kasan rashi .
kwance take akan bed din ummi Amman ba bacci takeyi ba ,hannuta rike da wani English novel mai suna ,mumy why sanye take cikin kananan kaya, pencil jeans da riga iya gwiwa a natse take karatunta dan tana jin dadi labarin yarinyar ciki litattafin ta birgeta kwaira ,ta yadda take kokarin kwatarwa kanta enci saboda mahaifiyarta ta hanata auren saurayin da take son ..
Cikin isa da kasaita yashigo dakin , tana jin motsen bude kofa Amman tashare dan batason abinda zai katse mata karatunta .
Jin kamshin turarensa yasa ta dan dago idanunta suka sauka akansa , ganinsa yasa ta dan mike daga kwanciyar datayi, tasha jinin jikinta bata san meke sata jin yawan faduwar gaba ba, a duk sanda taga yaya DEENi .
ta gaidashi batare daya kalli inda take ba , ya amsa mata a ciki ,km cikin isa da takama sannan a takaice , tamkar dai yadda yasaba dan baya son duk abinda zai sa magana tayi tsawo atsakaninsu .
sai dai ita kam tsintar kanta tayi da zuba masa idanunta, tana binsa da wani irin mayyen kallo , cikakken namiji ne sosai mai ji da kansa , ko a tafiyarsa zaka shida haka. gabadaya bbu wata alamun ragwanta atare dashi .kana ganinsa zakaji ya birgeka ,daman aikin da yakace shi kennan wato jami'in tsaro .
Har suka gaisa da ummi dake tsaye fitowarta kennan daga bathroom ya juya da niyar barin dakin, idanun Zeenat na kansa tamkar zata ya dawo ya zauna kada ya fita saboda tsoron masu farautarsa ,takasa dauke idanunta daga kallonsa take taji wani irin masefaffen kishinsa ya diram mata zuciyarta ta dinga rawa bata idanunta a kansa ba sai data daina ganinsa .
Ummi tabita da kallo tausayi tace inkin gama kallon nashi sai ki tashi ki hado masa abinsa ko kawai soyayya aka iya ba'asan tattali ba , Zeenat ta dan turo baki tace ni dai ummi kwanan bansa abinda na miki ba komai nayi sai kin min fada, ki dinga ganin laifina , nifa bashi nake kallo ba , ummi tace eh ai nasan bashi kike kallo ba kuruwarsa kike kallo jairar yarinya kawai ni tashi ban guri .
Washegari
Zeenat tarasa dawa zatayi zance yaya DEENi taji dadi kuma yaba shawara tamkar yadda zuciyarta ta aminta dashi ,ganinta duk wanda ta nufa da maganar baza tasamu goyon baya ba ,kmr dai yadda ummi tayi ,
Maryam ce ta fado mata a rai ,dan haka tashirya taje har part din su.
Tana shiga part din idanunta sukaci karo da fuskar data tsana a halin yanzun arayuwarta ,kmr ta juya ta koma haka taji , shemah ta hango zaune akan three site suna hira da Maryam take taji wani iri abu ya caki zuciyarta .
ganinta yasa taji tamkar an soka mata kibiya ne a kahon zuciya taja ta tsaya takasa karasawa inda suke dan baza juri zama a duk inda take ba , ganin haka yasa itama shemah ta mike ta fice Tama bar part din gabadaya . Da kallo Maryam tabi kowanne su
Ahankali Zeenat takaraso tasamu waje kusa da Maryam din ta zauna zuciyarta a cunkushe , tsawon lokacin takasa cewa komai , Maryam tace wai yana ganki haka ne ? Cikin nishadi Maryam ta soma janta hira har Zeenat ta sake Sosai
Daga nan ta labarta mata duk halin da'ake ciki ,.
Maryam ta zaro idanu waje tana mamaki tace kai da gaske kike ,to Ina girman kan nasa km?
Zeenat tace yana nan bai je koina ba" sai ma abinda yakaru ,
Maryam tace in fada miki gaskiya,zeenat ta daga mata kai alamun eh "ki amince kawai" karkiyi wasa da damarki domin mata dayawa suna can suna neman miji irin yaya DEENi
basu samu ba.
amman idan kin yi saken da kika tsaya yauki ,wai ke jan aji ,kya zo daga baya kina nadama dan irinsu tsada ne dasu ,.
kin dai san halinsa da maseefar zuciyar tsiya.
maryam takarasa zance da
Uhmmmm .. Ina ma ni Yace yana so ......
jin haka yasa take Zeenat ta hade fuskarta tamau , hade da zabgawa Maryam din wata uwar harara tace kefa Yar wulakanci ce bangane dama ke yace yana so ba Maryam tace ke nifa da wasa nake dan baga kmr kin fara hassala Zeenat tace ,wani irin wasa wannan, nifa banson shirme bazan.
Ko kema zaki shiga layin shemah ne?
Maryam tayi murmushi tace bada dai Ai tsakaninmu bbu haka yauwa naji ance ma kunyi fada da shemah Kwanaki ?
wai may ya hadaku fada ne , Zeenat ta tabe baki tana sauke ajiyar zuciya sannan tace shirme tamin irin naki .
nan dai ta zaiyanewa Maryam komai ,suka tafa suna kyalkyale dariya Maryam tace kai tawan kina wuta , Zeenat tace Ai ni bata wasa bace ban daukar raini tuni nagama daita duk da batasan abinda tamin ba har yanzu.
Maryam ta sake bata hannu suka taba, tace baki da kyau fa" sai dai idan ba'a tabo ki ba.
Maryam tacigaba tawan ki Amince kawai da auren nan musha biki amman fa zakisha fama da wannan miskililin ,Zeenat ta sake yin murmushi tace indai zai cigaba da sona kmr yadda yake yi yanzu Ina ruwana da wani miskilancinsa can yakarata , ai abinda yafi ma birgeni dashi kennan.
Amman nasan wuyarta dai ayi auren da sannu zai rage duk wannan jin kan nasa .
Zeena ta kagu dare yayi saboda cewar da yaya faruk yayi zai dawo .
,tun tana Jiran zuwansa har ta fida tsammani dan tara tayi gabadaya hankalinta a matukar tashe yake,t unaninta kar dai ya deeni ya hakura daita kmr yadda tace abashi hakuri.
zuciyar tashiga rawa tamkar zata tsinke ta mike tsaye cikin sanyi jiki tasoma zariya duk dai ummi biye daita da kallo can Ganin goma tayi yasa ta nufi dakin ummi tana shiga ta fada kan gadon tana zubda kwalla,.
ahankali tace Allah Allah kasa ba hakura yaya DEENi yayi ba ,.
dako na cuci kaina da kaina tashiga zubda hawaye baji ba Gani tana jin zuciyarta na neman taewatsewa tace Allah ka tausayin ka jin kai na ka mallakamin abin kaunarta deeni ina sonka deeni tunda ka furta kana sona nakasa samun sukuni dan karkace ka fasa kuka take sosai hade da sambatu ,,.
Shadaya daidai ummi tashigo ta dubi inda Zeenat take kwance taga alamun kmr bata jin dadi karasowa yayi tace ke lafiyarki kuwa da kyar Zeenat ta iya bude bakinta,t ace kaina ke min ciwo ummi tace shine zaki zauna kina kuka ,tayi mata sannu taje takawo mata magani .
Wasa wasa sai da Zeenat tayi kwana biyar cur batare da taga zuwan yaya faruk ba.h hakan yasa hankalinta sake tashi fiyye da koda yaushe .
cikin lokacin kadan ta zabge ta sake ragewa zazzabi may zafi ya rufeta, jikinta ya dauki zafi gwau , hankalin ummi yatashi , da Ganin halin da Zeenat take ciki kmr zatayi kuka.
Ummi ta kira likitan dake duba su, wato family doctor dinsu , byn yazo ne yasoma aikinsa cikin sauri ganin yadda Zeenat din takeyi taki magana sai zubda hawaye kawai take ga zuciyarta na buguwa da sauri da sauri Ganin haka yasa doctor din ya dauko abin awo ,ya auna BP dinta ,cikin mintina da basu wace ashirin ba ya gano abinda yake damunta sannan ya daura ma drip hade da sanya allurar bacci ciki take ko bacci yayi awon gaba daita .
Gabadaya hankalin Ummi ya sake tashi wani irin tsoro ne yashigeta lokacin daya ,da sauri tace doctor meke damunta ?
doctor yayi shiru yana nazarin abinda zai cewa Ummi kafin daga bisani ya numfasa ,sannan Yace akwai abinda tasa aranta wanda shine yayi dalilin haddasa mata damuwa har takai jinita ya hau sosai , Ummi ta sake maimaita abinda doctor yace , doctor yace Amman inshallahu bbu da damuwa zata samu lfy da zarar ta tashi komai zai yi dade, ummi tace to doctor na gode yayi mata sallama tare da gayamata yadda zata bata magani.duk wannan drama da akeyi deeni bai sani ba dan ko yashiga gaida Ummi baya damuwa daita ballantana yasan ko bata da lfy ne ,ita Kuma da haushi taki sanar masa Ai shi ba makaho bane
Kwata kwata Fk bai samu damar zuwa ba sai acikon kwana na bakwai tukun yazo ,yasamu Zeenat din bayadda take yayi mamakin , yadda DEENi bai sanar masa ba gashi kusan kullum sai sun hadu .
byn sun gaisa da ummi ne ,ya fita Yace Zeenat din ta same shi a parlour .
Cikin tsanyi jiki ta mike tasoma daga karta da kyar, cikin gimtsewar fuska ummi tace Ina km zaki kefa bakida lfy ?
Zeenat tabata fuska dan kada ummi ta hanata zuwa tace ummi sako zan karbo gurin Yaya faruk ,yanzu zan dawo , Ummi ta bita da idanu kawai Zeenat tace ummi sai nadawo cikin jin haushi da akaici Ummi tace kada ma ki dawo ki kwana a can .
Da sallamarta tashigo parlour "Zaune ta same yaya faruk din suka gaisa ya sake yi mata ya jiki sannan Yace sister kiyi hakuri dan girman da rashin zuwana kmr yadda nace, wasu abubuwa ne suka sha kaina wlh, dan haka yanzun naxo naji abinda kika yanke,zeenat ta danyi shr kmr mai nazari Yace kada ki damu idan har baki son shi , kisanar dani ,danshi yace idan baki amince ba, kada atakura miki shi ya hakura, a dan frigice tace Ai yaya kaima kasan bazan iya cewa banason shi ba, ko dan ummi dan haka kace masa kawai na amince .
Fk ya saki murmushi murna yayi hamdala a zuciyarsa hade da godiyar cin nasara yace Shikenan ni zan wuce sai kin jimu .
A ranar ummi ta nemi ciwon Zeenat ,tarasa duk tana zargin ciwan nata bazai wuce akan DEENi bane ,da daddare har nafila Zeenat tayi dan Mika godiyar ga Allah. ummi tayi murmushi tace yau km ibadar ce ta motsa har da sallar dare ?
Zeenat tayi mata banza kmr bataji ba tacigaba da sallarta, Ummi ta sake cewa Allah yasa a dore in km nasamun NASURULDEENI ne nasan daga yau Shikenan .
Abinda ke sake bawa Zeenat mamaki bai wuce Ganin yadda kullum yaya DEENi ke nuna ko in kula akanta ba gabadaya ma Gani take kmr baisan da zamanta ba .
ko magana ta fatar baki bata hadu su, idan ma yana guri kennan ita kanta batason zama in da yake yanzu ,Allah Allah take tabar wanje dan juriyarta takusan karewa .
Fk bai samu ganin deeni ba, sakamakon wani aiki daya taso masa ,Amman Yace masa yabari zuwa weekend ,ya same shi a gida .sai da fk yakirasa a waya ya tabbatar masa da yana gida sannan yazo .
zaune suke cikin parlour deeni byn sun gaisa fk yayi masa bayani duk yadda suka yi da Zeenat a boye DEENi ya sauke ajiyar zuciya ,sannan Yace ta taimaki kanta da kanta , kennan , fk yabishi da wani irin kallo sannan yace kai fa dan rainin wayo ne abinda yakamata kace kennan, deeni Yace nifa bawai na matsu dole sai ta amince da aurena bane .
asalima ita din ba irin kalar type dina bace zan dai aureta ne kawai ,a rashi samun choice dina fk ya saki baki yana kallon deeni ,Yace Amman friend kasan itama tana kyawunta daidaina , sai da ya dauki lokacin sannan yace ni nace maka dan kyawunta zan aureta?
Ai bata da kyawun da zai rudeni ,km wlh har ga Allah da bata amince ba na hakura , har zuwa sanda zansamu type dina.
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 21-22
Wani irin kallon mamaki fk yake masa , ,gabadaya ya zamo tamkar mutun mutimi a zaune a gurin ,
Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa " wai shi DEENi wani irin bahagon mutun ne ?
Shi sam bbu ruwan shi da fadar duk magana da tazo bakinsa .
In a low voice fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?
A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita " fk ya sake dubanshi sannan yace dan rainin wayo kawai kar mai dani kmr wanda bai san komai ba mana .
,tunda har zuciyarka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta definitely kana sonta" ko yaya ne" ,.
deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" matsala dakai kennan rashin saurin fahimta fk yace idan son da kake mata ne ,na fahimta ,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba , DEENI ya sake first da huci may zafi ranshi tasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son musamu matsala dakai fa" muddin baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .
Idan km kafin son haka ya daga kafadarsa alamun Shikenan , parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci yayinda deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da runtse idanunshi ya dan jin daci maganar fk 'ta yaya ma " zai nace akan yana son yarinyar byn shi yasan aure kawai yake da bukatar yi bawata ,aba soyayya ba ...
maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution tunda yarinya ta rigada ta amince ?
Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai kagama may wuyar "ya maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu .
girgiza kai kawai fk yayi uhmm shi wannan bazai taba canzawa zai ba .
halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso " shi komai baya so matsawar ba ra'ayin sa bane" duk yayi magana ne akasan ransa,,.
Ganin ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama .
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi yaja ya tsaya byn ya tura ayi masa kiranta fk tafito sanye da doguwar rigar material puppy colour mai shegen kyau hade yane kanta da karamin mayafe baki ahankali take isowa gareshi duk step daya Sai kirjinta ya motsa tun fitowarta ya zubawa kirjinta ido kyam yana kallon yadda kirjinta ke motsawa lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin sannan ya sake budesu ahankali mutuwar tsaye a gurin har takaraso inda yake ta gaisheshi cikin sanyi jiki bai dauke idanunshi akanta ba yacigaba da da binta mayataccen kallo da sallamarta iso inda yake ta gaisheshi ya amsa yana sake bin koina na jikinta da kallo cikin sanyi tace yaya faruk Gani Yace Ai naganki ,daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki ,nan dai yasanar mata koma , tunda yasoma magana tayi shr kawai hade da sunkuyar da kanta badan tana jin dadin abinda yake kokarin fahimtar dai ba ahankali ta dago ta zuba masa idanunta Sai data tabbatar ya gama fadar abinda yakawoshi sannan tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina Gaza bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya hakura dake ba Amman zan baki lokaci yi tunani akai tace nifa bawani tunanin dazanyi akai ka dai yi hakuri ka nemi wata ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye ,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunta ahankali tafe yake yana saka da warwara da tunanin malomasarsa a gurinsa ,a fusace shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace matabakomai.
Byn kwana biyu
Da misalin karfe takwas na dare fk ya km samu shemah da zance shi fa ba zai iya wani hakura daita ba kawai tayi hakuri ta amincewa da bukatar domin shi yana matukar son ta km aurenta yake son yi ,tace dan Allah yaya kayi hakuri wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya soka dan kaima baka rasa komai da zankika ba , kadai yi hakuri kawai .
al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa yadda zanyi daita yayi can dabara tazo masa,ya tsareta da idanunshi Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa ni zaki cewa kina da wanda zaki kike so byn Banga uban da kike saurara ba ,lafazinsa yayi mugun bata mata rai dan haka a ranta abace tace to dole ne Sai na aurenka kaje Kanemi wata mana ko ana soyayya dole ? ta juya a fusace zata bar guri ,ya fizgota hannuta , gabadayanta ta fado jikinsa , idanun ta zaro a tsorace, ,take taji wani irin faduwar gaba , .
Hannuwansa dukka yasa rungumeta tsam ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya daidai kunneta ya kai bakinsa Yace maimaita abinda kikace Ina jinki cikin tsiwa tace wannan wani irin iskanci dazaka wani rungume mutun ? Ok nine ma nake miki iskanci ?
Uhmmmm fa shemah karkibari muyi haka dake zaki amince ta girma da arziki ne ko km na jawo soyayyata ta karfin tsiya ,.batare da na wahalar da kaina ba muryarta na rawa tace anki a amince da soyayyarka .
ko ana so dole ne ?
, dan Allah ni kasake ni ,ya zuba mata manyan idanunshi kawai ,yasoma yawo da hannushi a jikinta gabadaya jikinta ya dauki kirma abinda bai taba faruwa daita ba kennan tunda take arayuwar ta ,wai namiji ya rabi jikinta har takaita ga runguma ,dan takaici ma batasan sanda , kwalla ta cicciko a idanunta ba , hawaye yaga yana silalowa daga idanunta ahankali ya sauke ajiyar zuciya, ya dan sausauta rungumar da yayi mata yasa yatsansa ya dangwalo hawayen dake bin fuskarta yana kallo Yace duk wannan kukan akan nace Ina sonki ne kike zubda hawayen ki?
,tayi shr taki cewa komai dan haushi ji tayi kmr ta daura hannuta akanta ta kurma ihu , ahankali ya sake maida ita jikinsa ya rungumeta yana shinshina wuyanta daidai nan Sai ga big dady dake dawo daga masallaci , a tsorace yake binsu da kallo cike da mamaki da alajabi abinda yagani , meke shirin faruwa km yau acikin zuri'arsu ,fk yacigaba manneta da jikinsa yana rarrashi ta amincewa aurensa , dagowar nan da zai lyi karaf idanunsa suka sauka kan big dady dake tsaye duk da duhu ne hakan bai hana gareshi ba gabansa yaji yayi muguwar faduwa jikinsa ya dauki kirma duk da ya tsorata Amman yaji dadi Ganin da big dady yayi musu ,yasan hakan zai sa a aura masa shemah batare da bata lokaci ba tsabar frigice yasa yakasa rabata da jikinsa gabadaya jikinsu rawa yake shemah da batasan wainar da'ake tuyawa ba sake lafewa tayi ajikinsa saboda irin rungumar dayayi mata ba wacce zata iya kwacewa bace har big dady ya wuce su a gurin shemah batasa big dady yagansu , ahankali fk yasoma rabata da jikinsa har zuwa yanzu hawaye bai daina bin fuskarta ba hannuta yakamo yasoma tafiya ita kum tana biye dashi bbu wanda ya iya cewa dan'uwansa komai har yakawo part dinsu yaja ya tsaya ahankali Yace shemah kiyi hakuri dan Allah kibar kuka ba nufi na kuraki ba Ina matukar kaunarki bansan lokacin dana fara sonki ba Amman zan baki lokacin kiyi tunani akai ,zan dawo zuwa jibi yana gama fadar haka ya juya da kyar yake iya daga kafafunsa tsabar frigice da nauyin da suka masa zuciyarsa tamkar zata buga , dan fargaba haduwarsu da big dady shi yasan ba makuwa tunda har big dady yagansu aure kmr anyi an gama Amman kunya fa ,har ya iso part dinsu wanda kusan nan samari suke zaune wayanda basuyi aure ,
Itama tana shiga dakisu ta wuce kai tsaye tana kuka , mamanta dake zaune a parlour tace ke lafiyarki Amman ko juyo batayi ba fadawa tayi kan gado tana risgar kuka to meye yaya faruk yake nufi daya sonta alhalin ita DEENi take mutuwar so ..... Dan haka bata taba aurensa ba ,tunawa datayi ba'a musu auren dole a family dinsu sai sun amince da juna yasa taji hankalinta ya kwanta Amman gabadaya jikinta yayi bala'in sanyi haka ta wuni a daki batare data sake fita ko parlour ba ,fk bai dawo ba kmr yadda Yace mata kusan sati tsakani shiyasa tayi tunanin ko yayi wa kansa fada ne ya hakura daita dan haka ta sake abinta kwasam Sai gashi a wani daren lahadi byn tagaishi a dage ,yayi murmushi yace yazo ne akan maganar su ,a fusace tace wata magana kennan i tough mun gama da wannan zance tunda nace ban sonka , Yace haka kika ce ,tace eh ko dole soyyaya dakai ,Yace uhmm Amman dolenki ki aureni ya wuce batare da damuwa ,
DEENi yasamu yaya mahamud yayi masa bayanin shi kuma ya samu big dady da zance tsohon yaji dadi Sosai jin sun hada kansu yace Shikenan bbu damu zai tuntubi yarinyan tukun asan abinyi .
Nan dai aka saka ranar aure tare da yanka sadaki yaya mahamud ne yayi komai ko sisin Kobo bata fita daga aljihun ogo deeni ba ko mahaifin zeenat yayi murna sosai da jin DEENi ne zai aure diyarsa
Anyaka sadaki da dukiyar aure naira duba dari biyar wanda duk a aljihun yaya mahamud suka fita .
Da kyar big dady yashawo kan Ummi dan tuburewa tayi ita sam bata yarda da wannan aure ba big dady yace Ai tunda dai yara sun hada kansu km suna juna Ai Ina Gani magana takare fatanmu Allah ya zaunar dasu lfy .
Lokacin da aka sanar da DEENi ansa ranar wata biyar deeni Yace wa yaya mahamud lokacin nan bai yi yawa ba kuwa ?
Dan akwai aiki da zai kaini akwaibon Ina Ganin zaifi kyau a takaita lokacin koma ba dan haka anawa raayin nafi son ayi nan da wata uku yaya mahamud yace Shikenan kabari dai zan samu Ummi da maganar .
Zaune take a cikin extra room dinsu wanda kusan yanzu can tafi zama tunda aka sa musu rana da yaya DEENi ta zabga uban tagumi tana mamakin hali irin na yaya DEENi yau kusan wata biyu Keenan dasamusu rana Amman ko sau daya bai taba kiranta da sunan zance ba haka nan ko cikin part din Ummi yashigo bata ishe shi kallo ba takan ji tsoro da frigice sun shigeta a duk sanda taga yaya DEENi nuna rashin damuwarsa akanta ,a kasan ranta tace, anya kuwa banyi kuskure da wautaba wajen saurin amincewa aurensa ba domin fa zuwa yanzu tasoma sarewa anya kuwa yaya DEENi yana sonta ?
kullum miskilancinsa sake gaba yake har zuwa yanzu dabatason cikakken matsayin ta a gurinsa ba ,son auren yasoma fice mata arai domin ita kadai tasan fargaban da take cikin zuciyarta ga ,gorin da Ummi kebinta dashi kullun garin Allah ya waye , dan haka ta yanke hukunci samun yaya faruk dan ta inda aka hau tanan ake sauka .ta shirya taje har part dinsu tace daman tazo ne akan maganar mu da yaya DEENi idan fa abin nan bazai yiwu ba gara tun yanzu abarshi .
Fk ya gyara tsayuwa sannan yace wani abu ne ya faru ? Tace to yaya faruk a haka ne zamu fahimci juna in San abinda yake so shima yasan wanda banaso shi fa aure ba banza bane kmr yadda ya dauki komai tacigaba bai taba kirana ba km ko gida yashigo ban ishe shi kallo ba shi bashi da lokacin kowa sai na kansa fk yace kiyi hakuri bawai zangoyi bayansa ba aikine yayimasa yawa kiyi nasa uziri Amman kina ranshi zeenat ta tabe baki dan tasan karya ne yace wai tana ran yaya DEENi Ai abinda kake son baka sakaci dashi fk yacigaba komai yakusan zuwa karshe da zarar kin zama a gidansa nasan dole ya baki dukkan lokacin sa ,zeenat tayi shr ne kawai ba wai dan maganar tashigeta ba , fk yace tayi hakuri zai masa magana da sauri ,zeenat ta dago tace dan Allah yaya kar kace ni nayi maka maganar ya sake dubanta sosai yaga duk ta wani frigice yace karki damu ni nasan abinda zanyi .
Fk yakira deeni a waya Amman ba'a daga ba
Da misalin karfe goma na dare fk ya amsa kiran DEENi tare da yin sallama byn sun gaisa yace friend dazo inata kira baka daga ba DEENi ya runtse ritattun idanunshi tamkar na may jin bacci sannan yace wlh aiki ne yasha kaina lafiya dai ko ya fadi cikin kasala dan duk a gajiye yake fk yace lfy dama akan maganar yarinyar nan ne yakama mushirya muje zance gurinta , ,anhakali DEENi ya bude idanunshi jin abinda fk yace muryasa a sarke yace wacce yarinyar km?
Fk yace sai karinka yin kmr baka san da zance ba ,byn nasan tana ranka DEENi yace dan malam karkadameni go to the point dan bangane wacce yarinyar kake nufi ba fk yace Ai dole ka manta da ko wacce yarinya ce tunda kaga kasameta cikin kwanciyar hankali km Ummi ta amince ,tsaki yaja kana yace wai zeenat kake nufi ?
Yasake jan wani tsakin mtssss wani irin hira kum kmr muna kauye byn angama magana sai jiran lokacin fk yace kai mugun dan iska ne Ai duk da haka yakamata muje dan ita yarinyar tasan raayinka kai ma haka ku samu fahimtar juna DEENi ya katse shi da itace Keenan ta aiko ka fk yace ko daya ni dai naga dacewar haka DEENi yace to baza'aje ba ... Kar Allah yasa mu fahimci juna, ita tun tasowarta, bata san abinda nake so da wanda ba,fk yace idan ita tasan abinda kake so da wanda baka so kai kasan nata ?
DEENi ya sake jan tsaki hade da kamo lip's dinshi na kasa yana dan ciccizawa sannan ahankali yace to sarkin yakinta ni ba haka taarina da raayina yake ba Ina tunanin in har zanje zance gurin budurwar ,zanje ne dan tallar kaina in samu gindin zama to ni narigada na samu shigar ,bbu dalilin da zai sa na takurawa kaina me kadauki ni ,nafa san irin son da yarinyar nan take min ,kawai dai ni banda lokacin wannan shirme dakace km nasan ita ta aiko ka fitowa ne kawai bazakayi kafada ba .
Fk yaja tsaki shima yace kai ,dan Allah wani irin bahagon mutun ne?
To wlh ka canza wannan budadden halin naka, to ko waya ce ka tsiya mata ,DEENi yace shima din baza'a tsiya ba ,duk abinda zai faru ya faru ciki har da fasa aurena ,fk yace kai fa kafiyye kafiya ,da maida karamar magana tazama babba ,. yace sake cewa yanzu dai kayi hakuri dan girman Allah ka Sai mata ko karamar waya ce.
DEENi yace kasan Allah ko game bazan Sai mata ba , ballanantana waya , tunda har taiya zuwa ta sameka da maganar bana kiranta fk yace kadaina cewa tasameni ni kawai Gani nayi ya dace muje DEENi ya tabe baki tamkar fk din na ganinsa Shikenan kai ka sani ni km kar ka sake damuna da maganar wata yarinya ya kashe wayarsa batare da ya tsaya jin abinda fk zai ce ba .
Wasa wasa lokacin bikin ya dinga karatowa da kwanaki ya wattani har zuwa yanzu dayayi sauran wata cif cif ayi daurin aure to Ganin kurewar lokaci yasa DEENi yasamu Ummi da maganar shifa baya son zamansa cikin estate din taje Ummi tayi kicin kicin da ranta sannan ta dago tana dubansa tace bangane abinda kake nufi ?
Sai da ya sake maimaita mata tukun Ummi tace sam ita bata yarda ba salon yaje yana dinga cin amanar Yar marainiyar Allah ga babbin gurin bid dady yasa an Gina musu shida sauran enuwansa shine kai dan iyayi zaka ce bazaka zauna ba ,to wlh kaji na rantse anan zaku zauna Sai naga yana yin zaman naku cikin yin kasa da murya yace Shikenan first lov na hakura duk abinda kika ce shi za'a yi tace da dai yafiye ma a yi mutun Sai girman tsiya da iyayi yace to kiyi hakuri .
Zeenat dake sauransu ta lumshe idanunta jin Ummi bata amince ba dan tana matukar jin tsoro zaman daga ita Sai shi ahankali cikin sanyi jiki ya mike idanunshi suka sauka akan inda zeenat ke kwance suka hada ido da sauri ta gaidashi hade da dauke idanunta ,bai sake kallonta ba bare ya amsa gaisuwar ta .
Shirye shiryen biki ya tashi gadan gadan enmata duka a tare suke shirinsu dan yanzu zeenat ta saki da shemah sun koma kmr da ganin da tayi wanda ma take haukar akansa bai san da zamanta ba wata safiya suka shirya zuwa siyayar su irinta amare mutun biyu ne abayanta mota Maryam da shemah yayinda zeenat ke gaba kai tsaye kasuwar Lagos suka nufa sukace derive yayi parking a idimota su kum suka shiga cikin market din
Derive yaja ya tsaya suna fitowa da yaya kamil suka soma cin karo tun shigowar motar dayaga hango zeenat zaune ya zubawa motar ido har sanda ta fito ahankali suka jiro suna hira Amman banda zeenat dataji gabanta ya yanke ya fadi dan tun lokacin da aka mata rana ,rabonta dashi dai dai sun kusan geftashi yakira sunnanta zeenat..... tacigaba da tafiyarta dan batason abinda zai km hada ta dashi cikin sassarfa ya biyo bayanta yasha gabanta cak taja ta tsaya suna kallon junansu,yayinda su Maryam suka cigaba da tafiyarsu suna tsaye batare da dukkansu suyi yunkurin yin magana ba kamil ya gyara tsayuwa ya tura hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa ya kafeta da idanunshi ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace lfy yaya ka tsayar dani muryasa a dashi yace lfyr ce takowa haka yanzu zeenat kin kyauta kennan ki zabi wani kibarni byn duk lokacin dana dauka Ina fama da soyayyarki ,a she kinsa bakya sona kibarni inata faman hauka akanki tace Allah yaya ba haka bane Amman kayi hakuri dan Allah, ya sake gyara tsayursa , yayinda idanunshi ke kanta har yanzu yace iya hakuri ne kawai zai wadatar da zuciyar da tayi sama shekara biyu tana mata da miki so.... yace Shikenan bbu komai Nagode Kwarai da abinda kika saka min tace ka dauka haka Allah yaso ni din ba matar ka bace yayi murmushin karfin hali sannan yace haka ne fa al'amarin ubgj Amman agaskiya DEENi ya cuceni ,tace kabar cewa ,tayi ta dago suna kallon juna fuskarta dauke da murmushi ta bude baki kennan Sai ga motar DEENI ta kuno kai cikin compound din km shi suke facin Ai take maganar ta ta tsaya sakamakon DEENi data Gani zaune a mota yana kallonsu duk kasancewar akwai dan duhun magariba hakan ba zai sa takasa gane bscin ransa ba , gabanta ya yanke ya fadi , ,shima kamil din shr yayi bai sake yin magana va kusan minti goma yayi yana kallonsu koda bata ga fuskasa sosai ba tasan a daure take ,har sanda DEENi ya fito yayi matarsa key idanunshi na kansu ,cikin tsoro da frigice zeenat tace ni zanshiga ciki ,kamil yace Shikenan Allah yabaki zaman lfy ta gefensu yazo yazo ya gifta hade da jan tsaki sannan ya wuce . a filli ta furta wayo Allahna nashi uku kamil ya sake yin murmushi dole sannan yace da'aka me,da kika shiga uku, nifa Banga abinda ya birgeki a DEENi ba,har da kika iya zabarsa , kalli fa yadda jikinki ke rawa saboda Allah tamkar kinga wani malaika tsaki taja hade da zabga masa harara dan Allah kabarni naji da damuwa Ai duk kai kaja min matsala Ina zaman zamana da yanzu Ina cikin gida💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 21-22
Wani irin kallon mamaki fk yake masa , ,gabadaya ya zamo tamkar mutun mutumi ,a zaune a gurin ,
Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa ,fk ya dinga masa kallon bahagon mutun wanda
Shi sam bbu ruwan shi da fadar duk magana da tazo bakinsa .
In a low voice fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?
DEENi ya tabe bakinsa hade da cewa A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita "alhalin bata sonta nake yi ba .
fk ya sake dubanshi sannan yace dan rainin wayo kawai "kar ka mai dani tamkar wanda bai san komai ba mana .
,tunda har ita zuciyartaka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta definitely kana sonta" ko yaya ne" ,. Amman maganar kace baka sonta,wannan ma ba gaskiya bane .
deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" sannan yace matsalata dakai kennan rashin saurin fahimta .
fk yace ta yaya kake so na fahimta ?
Alhalin ga zahirin gaskiya nan" idan son da kake mata ne ,na fahimta wannan.
,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba.sai dai kayi hakuri ,
DEENI ya sake furzar da huci may zafi ranshi yasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son mu samu matsala dakai fa" muddin baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .
Idan km kafin son haka ya daga kafadarsa alamun Shikenan ,.
parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci, yayinda deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da soma jijiga kafarsa daya a tile's dakin " runtse idanunshi Yayi dan jin daci abinda fk din yace"
'ta yaya ma " zai nace akan lallai yana son yarinyar byn shi yasan auren kawai yake da bukatar yi" bawata ,aba soyayya ba ...
maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution akan maganar, tunda yarinya ta rigada ta amince ?
Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa dole. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai kagama may wuyar " tare da maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu .
girgiza kai kawai fk yayi. uhmm shi wannan bazai taba canzawa ba .
halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso da murdanden raayi " shi komai baya so matsawar ba ra'ayin sa bane"fk yayi magana ne akasan ransa,,.
Ganin da yayi DEENi ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama yayi ficewarsa .
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi ,ba bata lokaci yasamu yaro ya tura ayi masa kiranta dan ya kudirtawa ransa ,yau ce, ranar da zai isar da sakon zuciyarsa gareta domin yagaji da cutar da kansa .
tafito sanye cikin doguwar rigar material puppy colour mai shegen kyau hade da yane kanta da karamin mayafe baki,
ahankali take isowa gareshi duk step daya datayi Sai kirjinta ya motsa sakamakon dukiyar fulani dake gareta.
tun fitowarta ya zubawa kirjinta idanunshi kyam ko kyafta ido bai yi yana kallon yadda albarkatun kirjinta ke motsawa, lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin ,sannan ya sake budesu ahankali. mutuwar tsaye yayi a gurin " har takaraso inda yake tayi sallama.
bai dauke idanunshi "akanta ba .Sai ma cigaba da yayi" da binta da wani irin mayataccen kallo wanda yasa shemah tasha jinin jikinta.
Ganin irin duban da take masa ne yayi saurin ,sauke idanunshi,tare da sakin ajiyar zuciya, ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska, yana sake bin koina na jikinta da kallo dan tayi masa kyau matuka ,rigar jikinta irin mai flay akasa ce Sai dai taka mata a sama sosai. cikin sanyi murya tace yaya faruk Gani , Yace Ai naganki .
,yayi shr yana tunanin ta inda zai soma ,itama shr tayi Sai dai,haka kawai ta tsinci kanta da jin ,faduwar gaba. haka nan kallon da yaya faruk din kema ,yasa taji wani iri ajikinta ,dan haka ,ta sunkuyar da kanta kasa tana Jira daga gareshi.
,can numfasa,hade da jin kwarin gwiwa yazo masa ,ya danyi gyaran murya" yace daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki , taji gabanta yashiga faduwa ,ta dan dago kadan ,taga ita yake kallo , ahankali tace na mefa? Sannan ta km maida kanta kasa tana jin yadda gabanta ke lugude faduwa.
Yayi murmushi yana cigaba da kallonta, cikin natsuwa da jarumta.
yasanar mata koma .
tun da yasoma magana tayi shr kawai hade da sake sunkuyar da kanta kasa, sosai badan tana jin dadin sauraron abinda yake kokarin fahimtar din bane ,taji hankalinta ya yayi matukar tashi dan haka , ahankali ta dago kanta , ta zuba masa idanunta , Sai data tabbatar daya gama fadar abinda yakawoshi a dan frigice tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina fa za bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya wannan hakura dake bani ba Sai d zan baki lokaci kiyi tunani akai , tace tunanin me km zanyi? nifa bawani tunanin dazanyi ka dai yi hakuri kawai ka nemi wata ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye .
,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare da yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunsa da suka masa nauyi, ahankali yake daga kafafunsa yana saka da warwara" da tunanin makomasarsa a gurinta .
,a fusace shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace mata bakomai.
Byn kwana biyu
Da misalin karfe takwas na dare fk ya km samu shemah da zance ,shi fa bai ji zai iya wani hakura daita ka " kawai tayi hakuri ta amincewa da aurensa , domin shi yana matukar sonta ,tace ni dai dan Allah yaya kayi hakuri wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya aurenka dan kaima baka rasa komai da zankika ba . kadai yi hakuri kawai .
al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa " yatasa yadda zaiyi daita, can dabara tazo masa, dan haka ya tsareta da idanunshi Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa" ni zaki cewa kina da wanda zaki kike so byn Banga uban da kike saurara ba.
,lafazinsa yayi, matukar bata haushi da mugun bata mata rai" dan haka ranta a bace tace to dole ne Sai na aurenka kaje Kanemi wata mana ko ana soyayya dole ? ta juya a fusace zata bar guri ,ba zato ba tsammani taji ya fizgo hannuta , gabadayanta ta fado jikinsa , idanunta "zaro a tsorace, ,take taji wani irin faduwar gaba fiyye da wanda taji dazu , .
Hannuwansa dukka yasa ,ya rungumeta tsam ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya "daidai kunneta ya kai bakinsa Yace uhmmm maimaita abinda kikace Ina jinki?
cikin tsiwa tace wannan wani irin iskanci ne dazaka wani rungume mutun ?
Ok nine ma nake miki iskanci ?
Uhmmmm fa shemah karkibari muyi haka dake ,tace muyima mana ,dan Allah ni malam kasake ni ,yayi murmushin karfin hali sannan yace zaki amince ta girma da arziki ne.
ko km na" jawo soyayyartawa " ta karfin tsiya ,.batare da na wahalar da kaina ba. muryarta na rawa ta sake cewa anki a amince da soyayyarka .
ko ana so dole ne ?
, dan Allah ni kasake ni , tun ban saka maka ihu ba ,ya zuba mata manyan idanunshi kawai yana kallonta. ahankali ,yasoma yawo da hannushi a sansar jikinta " gabadaya jikinta ya dauki kirma " abinda bai taba faruwa daita ba kennan" tunda take arayuwarta ,wai namiji ya rabi jikinta har takaita ga runguma ,dan takaici ma batasan sanda ta saki kara ba , kwalla ce cicciko a idanunta . Ya dan sausauta
Rungumar da , yayi mata ya zubawa fuskarta ido hawaye yaga yana silalowa daga idanunta ahankali ya sauke ajiyar zuciya,yasa yatsansa ya dangwalo hawayen dake bin fuskarta yana kallo Yace duk wannan kukan akan nace Ina sonki ne kike zubda hawayen ki?
,tayi shr taki cewa komai dan haushi , ji tayi kmr ta daura hannuta akanta ta sake , kurma ihu , ahankali ya sake maida ita jikinsa ya rungumeta yana shinshina wuyanta Yace please kidaina zubda hawayenki, Akan nace Ina sonki wlh duk ma wanda kike tunanin zaki aura nafi shi sonki , yasoma shafa bayanta da hannushi daya , daidai nan Sai ga big dady dake dawo daga masallaci take yaja birki , a tsorace yake binsu da kallo cike da mamaki da alajabi abinda yagani , meke shirin faruwa km yau acikin zuri'arsu ,fk yacigaba shafa bayanta tare da sake manneta da jikinsa yana rarrashita tayi hakuri ta amincewa aurensa .
dagowar nan da zai yi da niyar rabata da jikinsa karaf idanunsa suka sauka cikin na big dady dake tsaye ,gurin da Yar sandarsa yana kallonsu. "duk da duhu ne hakan bai hana ganeshi ba gabansa yaji yayi muguwar faduwa"take jikinsa ya dauki kirma duk da ya tsorata ,hakan bai sa ya saketa ba Sai dai yaji dadi Ganin da big dady din yayi musu .
yasan hakan zai sa a aura masa shemah batare da wani bata lokaci ba "tsabar frigice da yake ciki Ne yasa yakasa rabata da jikinsa gabadaya jikinsu rawa yake shemah da batasan wainar da'ake tuyawa ba .
sake lafewa tayi ajikinsa saboda irin rungumar dayayi mata ba wacce zata iya kwacewa bace" har big sanda big dady ya wuce su a gurin shemah batasa big dady yagansu ba , ahankali fk yasoma rabata daga jikinsa " har zuwa yanzu " hawaye bai daina bin fuskarta ba. Bai tsaya Ganin yanayin datake ciki ba hannuta ya damko yasoma tafiya.
ita kum tana biye dashi a baya , bbu wanda ya iya cewa dan'uwansa komai ,har yakawo part dinsu yaja ya tsaya , sannan ahankali Yace please... shemah kiyi hakuri dan girman Allah kibar kuka nan haka ba nufi na ta kuraki ba .
Ina matukar kaunarki" Ina miki son da ko ni kaina bansan lokacin dana fara ba Amman zan baki lokacin ki sake yi tunani ,zan dawo zuwa jibi yana gama fadar haka ya juya ,da kyar yake iya daga kafafunsa tsabar frigice da nauyin da suka masa zuciyarsa tamkar zata buga , dan fargaba haduwarsu da big dady "shi yasan ba makawa" tunda har big dady yagansu" aure kmr anyi an gama Amman kunya fa? Tana nan har abada .
,har ya iso part dinsu wanda kusan nan samari suke zaune wayanda basuyi aure gumi ke tsatsafo masa,
Itama shemah da kuka ta shiga part dinsu , mamanta dake zaune a parlour tace ke lafiyarki kike kuka ?
ko juyo batayi ba daki ta wuce ,ta fada kan gado ta cigaba da risgar kuka to yaya faruk yake nufi da yana sonta alhalin ita DEENi take mutuwar so ..... Dan haka tace wlh bazata taba aurensa ba ,tunawa datayi ba'a musu auren dole a family dinsu sai sun amince da juna yasa taji hankalinta ya kwanta Amman gabadaya jikinta yayi bala'in yi sanyi, haka ta kwanta da tunanin abinda fk yayi mata Ta dinga jinsa ajikinta tsagar jikinta suka mike ga kamshi turarensa daya fureera ,ko ta juya kamshinsa da hannushi ke yawo a koina na jikinta,.
Washegari ma kin fitowa tayi daga daki ,gabadaya
Yinin ranar a kwance tayi shi batare data fita ko parlour ba .
,fk bai dawo gurinta ba kmr yadda Yace mata kusan sati kennan tsakani ,shiyasa hankalinta ya kwanta Sosai tayi tunanin ko ya janye ne Tare da yiwa kansa fada ya hakura daita ,dan haka ta sake abinta.
kwatsam Sai gashi a wani daren lahadi byn ta gaisheshi, a dage ,yayi murmushi yace shifa yazo ne akan maganar su ,a fusace tace wata magana kennan?
i tough mun gama da wannan zance tunda nace ban sonka , Yace haka kika ce ,tace eh ko dole sai anyi soyyaya dakai?
,Yace ba dole kiyi soyayya dani ba ,Amman Ina son in tabbatar miki da aurena yazame miki dole ,yakamo hannuta ya sumbaci tafin hannuta sannan wuce ya yabar nan tare da damuwa ,
DEENi yasamu yaya mahamud yayi masa bayanin shi kuma ya samu big dady da zance tsohon yaji dadi Sosai jin sun hada kansu yace Shikenan bbu damuwa zai tuntubi yarinyan tukun yaji kafin yaasan abinyi .
Bayan wata daya
A wata lahadi da takasance ta karshen wata wanda sukeyi taronsu na family.
Holl din cike da yaya da jikoki tare da iyaye kowa kagani cike yake da tsantsar murna sabanin shemah da jikinta ke a tsanyaye sakamakon jin rade radin datayi na DEENi ne zai aure zeenat km Sai lokacin tasan dalilin dayasa zeenat ta mata wulakanci kwanaki
Byn wani lokacin gaishe gaishe ne yasoma biyu baya.
Takan shemah big dady yasoma, bai tsaya jin tabakinta ba yace akwai wanda taKe so ne ? Tace A'a yace shikennan yabawa faruk aurenta Take hawaye wanke mata fuska baita ba ko fk dake kokarin kiran DEENi wanda shi kadai bai iso ba , duk da hukunci big dady yayi masa dadi hakan bai hana jin gabansa faduwa ba daidai lokacin DEENI ya dau waya yaakayi ne mlm zaka dameni da kira fk yace angama dani fa sauran kai DEENI yace mezanzo yi km ? Fk yace kai fa dan rainin hankali ne zaka ce bakasan abinda akayi ba yau , uhmmmm tare da katse kiran Yama kashe wayar gabadaya dan bai son damuwa ,.
Kuka sosai shemah takeyi ta dinga datasanin cewa bata kowa gashi an kasaba mata auren fk nan Aka kira zeenat itama big dady yayi mata Mata tmbyrta ta Amince Sai sanda akazo neman su fk aka nemi DEENI akarasa kiran duniya akayiwa wayarsa taki shiga ,daga karshe big dady yace tunda yaji raayin zeenat din Ai aishikenan.
Nan dai aka saka ranar auren DEENi da fk tare da yanka sadaki, yaya mahamud ne yayi komai na DEENi ko sisin Kobo bata bai fita daga aljihun ogo deeni ba, ko mahaifin zeenat ma yayi murna sosai da jin DEENi ne zai aure diyarsa.
Anyaka sadakin zeenat tare da dukiyar aure naira duba dari biyar wanda duk a aljihun yaya mahamud suka fita .
Da kyar big dady yashawo kan Ummi dan tuburewa tayi ita fa sam bata yarda da wannan aure ba , big dady ne yace Ai tunda dai yara sun hada kansu km suna so junansu Ai Ina Gani magana takare fatanmu Allah ya zaunar dasu lfy .
Tace Ameen.
Lokacin da aka sanar da DEENi ansa ranar auren wata biyar , Yace wa yaya mahamud anya kuwa lokacin nan bai yi yawa ba kuwa ?
,Dan akwai aiki da zai kaini akwaibon Ina Ganin zaifi kyau a takaita lokacin koma ba dan haka ba ,anawa ra'ayin nafi son ayi komai nan da wata uku yaya mahamud yace Shikenan kabari dai zan samu Ummi da maganar .
Zaune take a cikin extra room dinsu wanda kusan yanzu can tafi zama tunda aka sa musu rana da yaya DEENi ta zabga uban tagumi tana mamakin hali irin na yaya DEENi yau kusan wata biyu Keenan dasamusu rana Amman ko sau daya bai taba kiranta da sunan zance ba haka nan ko cikin part din Ummi yashigo, bata ishe shi kallo ba takan ji tsoro da frigice sun shigeta a duk sanda taga yaya DEENi nuna rashin damuwarsa akanta ,a kasan ranta tace, anya kuwa banyi kuskure da wautaba wajen saurin amincewa aurensa ba domin fa zuwa yanzu tasoma sarewa anya kuwa yaya DEENi yana sonta ?
kullum miskilancinsa sake gaba yake har zuwa yanzu dabatason cikakken matsayin ta a gurinsa ba ,son auren yasoma fice mata arai domin ita kadai tasan fargaban da take cikin zuciyarta ga ,gorin da Ummi kebinta dashi kullun garin Allah ya waye , dan haka ta yanke hukunci samun yaya faruk dan ta inda aka hau tanan ake sauka .ta shirya taje har part dinsu tace daman tazo ne akan maganar mu da yaya DEENi idan fa abin nan bazai yiwu ba gara tun yanzu abarshi .
Fk ya gyara tsayuwa sannan yace wani abu ne ya faru ? Tace to yaya faruk a haka ne zamu fahimci juna in San abinda yake so shima yasan wanda banaso shi fa aure ba banza bane kmr yadda ya dauki komai tacigaba bai taba kirana ba km ko gida yashigo ban ishe shi kallo ba shi bashi da lokacin kowa sai na kansa fk yace kiyi hakuri bawai zangoyi bayansa ba aikine yayimasa yawa kiyi nasa uziri Amman kina ranshi zeenat ta tabe baki dan tasan karya ne yace wai tana ran yaya DEENi Ai abinda kake son baka sakaci dashi fk yacigaba komai yakusan zuwa karshe da zarar kin zama a gidansa nasan dole ya baki dukkan lokacin sa ,zeenat tayi shr ne kawai ba wai dan maganar tashigeta ba , fk yace tayi hakuri zai masa magana da sauri ,zeenat ta dago tace dan Allah yaya kar kace ni nayi maka maganar ya sake dubanta sosai yaga duk ta wani frigice yace karki damu ni nasan abinda zanyi .
Fk yakira deeni a waya Amman ba'a daga ba
Da misalin karfe goma na dare fk ya amsa kiran DEENi tare da yin sallama byn sun gaisa yace friend dazo inata kira baka daga ba DEENi ya runtse ritattun idanunshi tamkar na may jin bacci sannan yace wlh aiki ne yasha kaina lafiya dai ko ya fadi cikin kasala dan duk a gajiye yake fk yace lfy dama akan maganar yarinyar nan ne yakama mushirya muje zance gurinta , ,anhakali DEENi ya bude idanunshi jin abinda fk yace muryasa a sarke yace wacce yarinyar km?
Fk yace sai karinka yin kmr baka san da zance ba ,byn nasan tana ranka DEENi yace dan malam karkadameni go to the point dan bangane wacce yarinyar kake nufi ba fk yace Ai dole ka manta da ko wacce yarinya ce tunda kaga kasameta cikin kwanciyar hankali km Ummi ta amince ,tsaki yaja kana yace wai zeenat kake nufi ?
Yasake jan wani tsakin mtssss wani irin hira kum kmr muna kauye byn angama magana sai jiran lokacin fk yace kai mugun dan iska ne Ai duk da haka yakamata muje dan ita yarinyar tasan raayinka kai ma haka ku samu fahimtar juna DEENi ya katse shi da itace Keenan ta aiko ka fk yace ko daya ni dai naga dacewar haka DEENi yace to baza'aje ba ... Kar Allah yasa mu fahimci juna, ita tun tasowarta, bata san abinda nake so da wanda ba,fk yace idan ita tasan abinda kake so da wanda baka so kai kasan nata ?
DEENi ya sake jan tsaki hade da kamo lip's dinshi na kasa yana dan ciccizawa sannan ahankali yace to sarkin yakinta ni ba haka taarina da raayina yake ba Ina tunanin in har zanje zance gurin budurwar ,zanje ne dan tallar kaina in samu gindin zama to ni narigada na samu shigar ,bbu dalilin da zai sa na takurawa kaina me kadauki ni ,nafa san irin son da yarinyar nan take min ,kawai dai ni banda lokacin wannan shirme dakace km nasan ita ta aiko ka fitowa ne kawai bazakayi kafada ba .
Fk yaja tsaki shima yace kai ,dan Allah wani irin bahagon mutun ne?
To wlh ka canza wannan budadden halin naka, to ko waya ce ka tsiya mata ,DEENi yace shima din baza'a tsiya ba ,duk abinda zai faru ya faru ciki har da fasa aurena ,fk yace kai fa kafiyye kafiya ,da maida karamar magana tazama babba ,. yace sake cewa yanzu dai kayi hakuri dan girman Allah ka Sai mata ko karamar waya ce.
DEENi yace kasan Allah ko game bazan Sai mata ba , ballanantana waya , tunda har taiya zuwa ta sameka da maganar bana kiranta fk yace kadaina cewa tasameni ni kawai Gani nayi ya dace muje DEENi ya tabe baki tamkar fk din na ganinsa Shikenan kai ka sani ni km kar ka sake damuna da maganar wata yarinya ya kashe wayarsa batare da ya tsaya jin abinda fk zai ce ba .
Wasa wasa lokacin bikin ya dinga karatowa da kwanaki ya wattani har zuwa yanzu dayayi sauran wata cif cif ayi daurin aure to Ganin kurewar lokaci yasa DEENi yasamu Ummi da maganar shifa baya son zamansa cikin estate din taje Ummi tayi kicin kicin da ranta sannan ta dago tana dubansa tace bangane abinda kake nufi ?
Sai da ya sake maimaita mata tukun Ummi tace sam ita bata yarda ba salon yaje yana dinga cin amanar Yar marainiyar Allah ga babbin gurin bid dady yasa an Gina musu shida sauran enuwansa shine kai dan iyayi zaka ce bazaka zauna ba ,to wlh kaji na rantse anan zaku zauna Sai naga yana yin zaman naku cikin yin kasa da murya yace Shikenan first lov na hakura duk abinda kika ce shi za'a yi tace da dai yafiye ma a yi mutun Sai girman tsiya da iyayi yace to kiyi hakuri .
Zeenat dake sauransu ta lumshe idanunta jin Ummi bata amince ba dan tana matukar jin tsoro zaman daga ita Sai shi ahankali cikin sanyi jiki ya mike idanunshi suka sauka akan inda zeenat ke kwance suka hada ido da sauri ta gaidashi hade da dauke idanunta ,bai sake kallonta ba bare ya amsa gaisuwar ta .
Shirye shiryen biki ya tashi gadan gadan enmata duka a tare suke shirinsu dan yanzu zeenat ta saki da shemah sun koma kmr da ganin da tayi wanda ma take haukar akansa bai san da zamanta ba wata safiya suka shirya zuwa siyayar su irinta amare mutun biyu ne abayanta mota Maryam da shemah yayinda zeenat ke gaba kai tsaye kasuwar Lagos suka nufa sukace derive yayi parking a idimota su kum suka shiga cikin market din
Derive yaja ya tsaya suna fitowa da yaya kamil suka soma cin karo tun shigowar motar dayaga hango zeenat zaune ya zubawa motar ido har sanda ta fito ahankali suka jiro suna hira Amman banda zeenat dataji gabanta ya yanke ya fadi dan tun lokacin da aka mata rana ,rabonta dashi dai dai sun kusan geftashi yakira sunnanta zeenat..... tacigaba da tafiyarta dan batason abinda zai km hada ta dashi cikin sassarfa ya biyo bayanta yasha gabanta cak taja ta tsaya suna kallon junansu,yayinda su Maryam suka cigaba da tafiyarsu suna tsaye batare da dukkansu suyi yunkurin yin magana ba kamil ya gyara tsayuwa ya tura hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa ya kafeta da idanunshi ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace lfy yaya ka tsayar dani muryasa a dashi yace lfyr ce takowa haka yanzu zeenat kin kyauta kennan ki zabi wani kibarni byn duk lokacin dana dauka Ina fama da soyayyarki ,a she kinsa bakya sona kibarni inata faman hauka akanki tace Allah yaya ba haka bane Amman kayi hakuri dan Allah, ya sake gyara tsayursa , yayinda idanunshi ke kanta har yanzu yace iya hakuri ne kawai zai wadatar da zuciyar da tayi sama shekara biyu tana mata da miki so.... yace Shikenan bbu komai Nagode Kwarai da abinda kika saka min tace ka dauka haka Allah yaso ni din ba matar ka bace yayi murmushin karfin hali sannan yace haka ne fa al'amarin ubgj Amman agaskiya DEENi ya cuceni ,tace kabar cewa ,tayi ta dago suna kallon juna fuskarta dauke da murmushi ta bude baki kennan Sai ga motar DEENI ta kuno kai cikin compound din km shi suke facin Ai take maganar ta ta tsaya sakamakon DEENi data Gani zaune a mota yana kallonsu duk kasancewar akwai dan duhun magariba hakan ba zai sa takasa gane bscin ransa ba , gabanta ya yanke ya fadi , ,shima kamil din shr yayi bai sake yin magana va kusan minti goma yayi yana kallonsu koda bata ga fuskasa sosai ba tasan a daure take ,har sanda DEENi ya fito yayi matarsa key idanunshi na kansu ,cikin tsoro da frigice zeenat tace ni zanshiga ciki ,kamil yace Shikenan Allah yabaki zaman lfy ta gefensu yazo yazo ya gifta hade da jan tsaki sannan ya wuce . a filli ta furta wayo Allahna nashi uku kamil ya sake yin murmushi dole sannan yace da'aka me,da kika shiga uku, nifa Banga abinda ya birgeki a DEENi ba,har da kika iya zabarsa , kalli fa yadda jikinki ke rawa saboda Allah tamkar kinga wani malaika tsaki taja hade da zabga masa harara dan Allah kabarni naji da damuwa Ai duk kai kaja min matsala Ina zaman zamana da yanzu Ina cikin gida
MMN SUDAIS CE💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 21-22
Wani irin kallon mamaki fk yake masa , ,gabadaya ya zamo tamkar mutun mutimi a zaune a gurin ,
Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa " wai shi DEENi wani irin bahagon mutun ne ?
Shi sam bbu ruwan shi da fadar duk magana da tazo bakinsa .
In a low voice fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?
A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita " fk ya sake dubanshi sannan yace dan rainin wayo kawai kar mai dani kmr wanda bai san komai ba mana .
,tunda har zuciyarka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta definitely kana sonta" ko yaya ne" ,.
deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" matsala dakai kennan rashin saurin fahimta fk yace idan son da kake mata ne ,na fahimta ,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba , DEENI ya sake first da huci may zafi ranshi tasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son musamu matsala dakai fa" muddin baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .
Idan km kafin son haka ya daga kafadarsa alamun Shikenan , parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci yayinda deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da runtse idanunshi ya dan jin daci maganar fk 'ta yaya ma " zai nace akan yana son yarinyar byn shi yasan aure kawai yake da bukatar yi bawata ,aba soyayya ba ...
maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution tunda yarinya ta rigada ta amince ?
Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai kagama may wuyar "ya maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu .
girgiza kai kawai fk yayi uhmm shi wannan bazai taba canzawa zai ba .
halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso " shi komai baya so matsawar ba ra'ayin sa bane" duk yayi magana ne akasan ransa,,.
Ganin ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama .
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi yaja ya tsaya byn ya tura ayi masa kiranta fk tafito sanye da doguwar rigar material puppy colour mai shegen kyau hade yane kanta da karamin mayafe baki ahankali take isowa gareshi duk step daya Sai kirjinta ya motsa tun fitowarta ya zubawa kirjinta ido kyam yana kallon yadda kirjinta ke motsawa lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin sannan ya sake budesu ahankali mutuwar tsaye a gurin har takaraso inda yake ta gaisheshi cikin sanyi jiki bai dauke idanunshi akanta ba yacigaba da da binta mayataccen kallo da sallamarta iso inda yake ta gaisheshi ya amsa yana sake bin koina na jikinta da kallo cikin sanyi tace yaya faruk Gani Yace Ai naganki ,daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki ,nan dai yasanar mata koma , tunda yasoma magana tayi shr kawai hade da sunkuyar da kanta badan tana jin dadin abinda yake kokarin fahimtar dai ba ahankali ta dago ta zuba masa idanunta Sai data tabbatar ya gama fadar abinda yakawoshi sannan tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina Gaza bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya hakura dake ba Amman zan baki lokaci yi tunani akai tace nifa bawani tunanin dazanyi akai ka dai yi hakuri ka nemi wata ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye ,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunta ahankali tafe yake yana saka da warwara da tunanin malomasarsa a gurinsa ,a fusace shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace matabakomai.
Byn kwana biyu
Da misalin karfe takwas na dare fk ya km samu shemah da zance shi fa ba zai iya wani hakura daita ba kawai tayi hakuri ta amincewa da bukatar domin shi yana matukar son ta km aurenta yake son yi ,tace dan Allah yaya kayi hakuri wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya soka dan kaima baka rasa komai da zankika ba , kadai yi hakuri kawai .
al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa yadda zanyi daita yayi can dabara tazo masa,ya tsareta da idanunshi Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa ni zaki cewa kina da wanda zaki kike so byn Banga uban da kike saurara ba ,lafazinsa yayi mugun bata mata rai dan haka a ranta abace tace to dole ne Sai na aurenka kaje Kanemi wata mana ko ana soyayya dole ? ta juya a fusace zata bar guri ,ya fizgota hannuta , gabadayanta ta fado jikinsa , idanun ta zaro a tsorace, ,take taji wani irin faduwar gaba , .
Hannuwansa dukka yasa rungumeta tsam ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya daidai kunneta ya kai bakinsa Yace maimaita abinda kikace Ina jinki cikin tsiwa tace wannan wani irin iskanci dazaka wani rungume mutun ? Ok nine ma nake miki iskanci ?
Uhmmmm fa shemah karkibari muyi haka dake zaki amince ta girma da arziki ne ko km na jawo soyayyata ta karfin tsiya ,.batare da na wahalar da kaina ba muryarta na rawa tace anki a amince da soyayyarka .
ko ana so dole ne ?
, dan Allah ni kasake ni ,ya zuba mata manyan idanunshi kawai ,yasoma yawo da hannushi a jikinta gabadaya jikinta ya dauki kirma abinda bai taba faruwa daita ba kennan tunda take arayuwar ta ,wai namiji ya rabi jikinta har takaita ga runguma ,dan takaici ma batasan sanda , kwalla ta cicciko a idanunta ba , hawaye yaga yana silalowa daga idanunta ahankali ya sauke ajiyar zuciya, ya dan sausauta rungumar da yayi mata yasa yatsansa ya dangwalo hawayen dake bin fuskarta yana kallo Yace duk wannan kukan akan nace Ina sonki ne kike zubda hawayen ki?
,tayi shr taki cewa komai dan haushi ji tayi kmr ta daura hannuta akanta ta kurma ihu , ahankali ya sake maida ita jikinsa ya rungumeta yana shinshina wuyanta daidai nan Sai ga big dady dake dawo daga masallaci , a tsorace yake binsu da kallo cike da mamaki da alajabi abinda yagani , meke shirin faruwa km yau acikin zuri'arsu ,fk yacigaba manneta da jikinsa yana rarrashi ta amincewa aurensa , dagowar nan da zai lyi karaf idanunsa suka sauka kan big dady dake tsaye duk da duhu ne hakan bai hana gareshi ba gabansa yaji yayi muguwar faduwa jikinsa ya dauki kirma duk da ya tsorata Amman yaji dadi Ganin da big dady yayi musu ,yasan hakan zai sa a aura masa shemah batare da bata lokaci ba tsabar frigice yasa yakasa rabata da jikinsa gabadaya jikinsu rawa yake shemah da batasan wainar da'ake tuyawa ba sake lafewa tayi ajikinsa saboda irin rungumar dayayi mata ba wacce zata iya kwacewa bace har big dady ya wuce su a gurin shemah batasa big dady yagansu , ahankali fk yasoma rabata da jikinsa har zuwa yanzu hawaye bai daina bin fuskarta ba hannuta yakamo yasoma tafiya ita kum tana biye dashi bbu wanda ya iya cewa dan'uwansa komai har yakawo part dinsu yaja ya tsaya ahankali Yace shemah kiyi hakuri dan Allah kibar kuka ba nufi na kuraki ba Ina matukar kaunarki bansan lokacin dana fara sonki ba Amman zan baki lokacin kiyi tunani akai ,zan dawo zuwa jibi yana gama fadar haka ya juya da kyar yake iya daga kafafunsa tsabar frigice da nauyin da suka masa zuciyarsa tamkar zata buga , dan fargaba haduwarsu da big dady shi yasan ba makuwa tunda har big dady yagansu aure kmr anyi an gama Amman kunya fa ,har ya iso part dinsu wanda kusan nan samari suke zaune wayanda basuyi aure ,
Itama tana shiga dakisu ta wuce kai tsaye tana kuka , mamanta dake zaune a parlour tace ke lafiyarki Amman ko juyo batayi ba fadawa tayi kan gado tana risgar kuka to meye yaya faruk yake nufi daya sonta alhalin ita DEENi take mutuwar so ..... Dan haka bata taba aurensa ba ,tunawa datayi ba'a musu auren dole a family dinsu sai sun amince da juna yasa taji hankalinta ya kwanta Amman gabadaya jikinta yayi bala'in sanyi haka ta wuni a daki batare data sake fita ko parlour ba ,fk bai dawo ba kmr yadda Yace mata kusan sati tsakani shiyasa tayi tunanin ko yayi wa kansa fada ne ya hakura daita dan haka ta sake abinta kwasam Sai gashi a wani daren lahadi byn tagaishi a dage ,yayi murmushi yace yazo ne akan maganar su ,a fusace tace wata magana kennan i tough mun gama da wannan zance tunda nace ban sonka , Yace haka kika ce ,tace eh ko dole soyyaya dakai ,Yace uhmm Amman dolenki ki aureni ya wuce batare da damuwa ,
DEENi yasamu yaya mahamud yayi masa bayanin shi kuma ya samu big dady da zance tsohon yaji dadi Sosai jin sun hada kansu yace Shikenan bbu damu zai tuntubi yarinyan tukun asan abinyi .
Nan dai aka saka ranar aure tare da yanka sadaki yaya mahamud ne yayi komai ko sisin Kobo bata fita daga aljihun ogo deeni ba ko mahaifin zeenat yayi murna sosai da jin DEENi ne zai aure diyarsa
Anyaka sadaki da dukiyar aure naira duba dari biyar wanda duk a aljihun yaya ma
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 23-24
Ni dan girman Allah kabarni na wuce tun kafin laifina ya Karu.
,Murmushi karfin hali kawai yayi ,tare da nuna mata hanya da hannushi alamun ta wuce din.
, kasa tafiya tayi " sakamakon idanushi da taji yana mata yawo a gangar ajikinta . Gabadaya taji tamkar ya daureta ne .
takasa kwakwaran motsi" jikinta yayi bala'in yin sanyi.
,taji ina ma zuciyarta na da yanci da bata kamu da soyayyayar deeni ba.
Da bbu shakka zata iya hakura da kamil tunda shima yana da nashi kyawun daidai gwargwado .
Yayi shr kawai yana kallonta" kaunarta ce ke tasomasa tare da nukurkusan zuciyarsa.
,ya dinga jin tamkar ya halaka kanshi lokacin daya tsinci idanun deeni akan su.
ya dinga kallonta "yana jin yadda zuciyarsa ke tafarfasa " da gske dai yana shirin yarasata kennan ,rashima na har abada.
km ta haramta ta zama matarsa wani irin zugi zuciyarsa keyi ahankali
Yakira sunanta..Zeenat kina son deeni sosai ko ? Cikin sanyi
ta dago kanunun idanunta ta kalleshi dasu "sannan tace , wannan wace irin tmby ce ? Yace amsa kawai nake bukata ,tace to bana son shi shikennan.
Karkimin karya mana Kina son shi kalli...kalli yadda yanayinki ya canza jikinki har rawa yake saboda kin ganshi .
ya tabbata kennan baki sona ,rainamin hankali kawai kika dinyi .
A fusace Zeenat tace Nifa karka zageni da laifi da bansan na aikata ba. mgnr ina sonshi ko bana sonshi ma duk bata taso ba .
kai kanka kasan bantaba amsa maka da Ina sonka ba.
ballanantana kace yaudararka nayi ka dai yi hakuri Allah ya hada kowa da rabonsa , yace ok yanzun duk tarin son da na miki yazama tarihi kennan ?
Ta zuba mishi ido kawai dan tasan duk abinda zata gaya masa ahalin yanzu ba fahinmta zai yi ba shiyasa tayi shr taki cewa komai
Ahankali Ya girgiza kanshi kawai batare da sake cewa mata komai ba ya juya yasoma tafiya.
, Tayi jim jikinta ya mata tsanyi ,bata ji dadin yadda taga reaction dinsa ba .
tasan kwata kwata bata kyautawa masa ba. Amman ba yadda taiya da zuciyarta " DEENi shine muradin ranta .
raba zuciyarta dashi tamkar barazana ce ga rayuwarta.
Duk da taji ba dadi ba hakan bai sa taji tausayinsa yashigeta har taji zata iya hakura da auren DEENi . Dan haka ko ajikinta ta wuce.
Jikinta a sanyaye yashigo part dinsu hankalinta a tashe
Tana shiga daki Ta daure fuskarta "ganin ya shigo dan a zatonta yana shigowa zai zabgamata mari.
sanye yake da t shirt din su na sojoji da wando.
Tana jinshi yacewa Ummi shi ya wuce sai da safe "Ummi tace can zaka kwana ne yau ?
yace eh "akwai abinda zai maidani tace to Allah ya tsare min kai ya km bada sa'a ,ka yawaita addu'a dan Allah yace Ina yi sai dai zan kara kulawa .
ya sake wuce zeenat zaune ko kallon inda take baiyi ba .
bayansa tabi da kallo tana jin wata irin masefaffiyar kaunarsa nabin jininta, hade da ratsa kowani part na jikinta.
, aranta tace attajirina kennan ,miskilili zaki maza .
nan ya fita yabarta da dadeden kamshinsa tare da fargaba.
sai dai, da ganin yanayinsa yana cikin tsananin fushi .
da misalin karfe tara dare tana kwance akan gado" juyi kawai take, yayinda zuciyarta ke nazari akan irin kallon da yaya deeni yayi mata, dazu sakamakon ganin da yayi mata tare da kamil .
ta ji tamkar takirashi tabashi hakuri amman tsananin tsoransa ya hanata aikata hakan , zuciyarta ce ta bata shawara kan tura masa text ba sai takirashi ba .
dan haka ahankali ta mirgina ta janyo wayar Ummi dake kan bedside .
ta soma rubuta masa text da niyar turawa masa " sai km taji zuciyata na gargadinta akan kar ta sake ta tura masa text din . Tayi tana tunanin ,ta tura ne ko ta share
Tayi haka ya yafi sau goma kafin daga karshe tayi jahadi ta tura masa .
Yaya dan Allah kayi hakuri idan na bata maka rai dazu wlh bazan sake ba ... daga zeenat
Byn ta tura sakon ne ta goge "sannan takoma ta kwanta lamo tana jin yadda kirjinta ke tsarkewa ,ahankali ta lumshe" idanunta ,xuciyarta ke beating tare da yi mata fadar abinda ta aikata .
ita kanta tasan tayi babban kuskure sosai wajen tura masa text ,dan tasha jin yadda yake yawan yi complain akan tura masa sako ko kiran wayarsa yayinda yake kan aiki ,
Sai dashi duk lokacin daya gadama zai kiraka idan km baka dauka ba yazama matsala .
dan haka tayi shr kawai tana fidda numfashi sama sama .
Tsawon lokaci tana kwance "tana tunanin abinda zai biyo baya idan yaga sakonta , addu'a take Allah yasa ba karawa kanta laifi tayi ba agurinsa .
take tsoro da fargaba suka taru suka dira mata " alokaci daya.
Idanunta a lumshe har lokacin tana saka da warwara deeni dan ra'ayi baka masa dole ballanantana ta tursashi .
can taji alamun shigowar sako a zaburi ta mike" ta rarumi wayar jikinta har rawa yake .
idanunta ne suka ci karo da reply dinsa .
hankalinta a tashe tasoma karanta text din .
Ke ... Banida lokacin karanta wannan shirmen naki na baza , aikina yana da mahimmanci a wajena banida lokacin hada aikina da zantuttukan marasa ma'ana dan haka ki kiyaye gaba ..
Tana gama karantawa ta sauke ajiyar zuciya sannan ta sulale takoma ta kwanta tare da lumshe idanunta.
Tabbas tasan ta daukarwa kanta abinda yafi karfinta .
tayi shr ,tana son tayi nazari akan kalamansa tasan dai yakaranta sakonta sarai .
tsabar rainin wayo ne da miskilanci irin nasa .
yasa ya nuna kmr bai da lokacinta .
tayi juyi tana mai tausayawa kanta na nacewa auren DEENi.
yanzu Gabadaya son aurensa ya sire mata ya fita akanta.
, tsoro aurensa take km sai yanzu maganganun Ummi ke sake shigarta .
Inda tace zeenat ,kin fahimtata ne kawai deeni dana ne dana haifa a cikina.
baki fini sonshi ba sanin halin miskilancinsa da girman kai irin nasa yasa kikaga naki amincewa da aurenku wahala kawai zakisha a hannushi .
, gara yaje waje can ya nemo matarsa.
batayi aune ba taji saukar hawaye nabin kuncinta" bata hana su zubowa ba ,domin ita kanta zata fi so ta zubar dasu ,kodan samun natsuwarta.
Km ko ba komai hakan zaisa taji sanyi da ragewa kanta radadin abinda ke nukurkusan ruhinta.
Jikinta yayi matukar yin tsanyi ahankali tasoma sambatu ..
Wayo Allahna... ni zeenat yaya zanyi da zuciyata data ta makance akan kaunarka.
Ina sonka yaya deeni har bansan yadda zan misalta tarin soyayyata gareka ba.
kaunarka ajinina da ruhina yake .
daita Allah ya hallice . bazan iya daina sonka ba muddin rai .
koda baka sona ni Ina sonka km zan iya jurar komai akanka ,raba zuciyata da soyayyarka tamkar rasa numfashina ne .
Haka tayi surutai har sanda Tajiyo motsen shigowar Ummi .
tayi shr tare da saurin juya mata baya.
tana cigaba kukanta, kasa kasa batare Ummi ta Gane halin da take ciki ba .
Zuciyarta ke mata wani irin ciwo da radadi mai zafi .
Washegari ma sukusuku ta tashi tamkar wace batada lfy ta rame sosai " idanunta a kumbure kallo daya Ummi tayi mata ,ta Gane kuka tayi .
km daman tana lura daita jiya bawani baccin kirki tayi ba .
taji wani irin tausayinta ya tsarga mata har cikin zuciyarta "dan tasan tunda ta kwallafawa ranta auren DEENi , ta hadu da babban aiki .
km sai ta hadu da abinda yafi haka.a addu'a dai zata cigaba dayi musu Allah ya kauda fitana atsakaninsu.
Ahankali Ummi takira sunanta ...ta dago da kumburarun idanunta tana kallon Ummi dasu batare da tace mata komai ba byn gaisuwar datayi mata .
,Ummi tace meke damunki ne zeenat naga duk idanunki duk sun kunbura" sai naga ma kmr kuka kikayi .
Zeenat ta danyi murmushi dole sannan tace kai Ummi bbu komai fa, idanuna kemin ciwo ,km jiya da ciwon kai na kwana .
ta fadi hakan da hankalin Ummi ya kwanta .
Ummi tayi shr kusan minti goma tana kallonta sai da tagama nazarinta tsab sannan ta numfasa tace shikennan Allah ya sawake kinsha magani ?
Zeenat ta girgiza kai kawai.
Ummi tace maza ki tashi kije daki ki dauko magani kisha.
a sanyaye ta mike jikinta babu kwari tace to ...
tare da shigewa kitchen dan bataji zata iya shan wani magani a halin datake ciki yanzu ,dan tasan ko tasha bazai taba yi mata maganin damuwarta.
kusan duk dare sai bacci ya katse mata sakamakon tunanin DEENI da hali ko in kula da yake nuna mata .
, shi sam mutun ne da babu ruwanshi da wani damuwa harakar gabansa kawai yakeyi hankalinsa kwance .
tayi shr cikin zullumi irin zaman da zatayi da DEENi,a zahirin ce tagama duk wani tunani da zatayi akansa ,amman sam bata hango wani jin dadi ko kulawa da za samu aurenta dashi ba .
Sai yanzun take gane manufar Ummi" tana guje mata wahala ne yayinda ita km ta kasa fahimtar hska . gashi yanzu lokaci ya kure mata bata da daman tace ta fasa .
Misalin karfe takwas na dare .
kwance take a parlour kan doguwar kujerar three site .
hannuta rike da wayar Ummi ta juyata idanunta kuru akan TV .zaka dauka ko kallo take .
amman a hakikanin gaskiya kallo daya zaka mata ka gane Gabadaya hankali bai gurin TV .
tana can ta lula cikin duniyar tunani tunani .
, kamshin turarensa ne ya ankarar daita ,take tayi firgigib da dawo duniyar kasa dan tasan tunda Tajiyo kamshinsa yana kusa kennan dan haka ahankali ta dan juyo tsaitin datake jiyo kamshin nasa , ahankali idanunta suka cin karo da kyakkyawan fuskarsa ko kallonta inda take baiyi ba , yakarasa shigowa parlour fuskar nan tashi a daure tamkar zaki .
,take taji zuciyarta ta tsinke tasoma rawa wata irin zazzafar kaunarshi ce ta dinga taso mata tamkar ta tarwatsa mata zuciya , lokacin data daura idanunta kansa.
kamshin turarensa ya addabi hancinta ji take kmr tajita a kusa dashi .
sallama Yayi aciki.
ta amsa tare da sunkuyar da kanta kasa har ya wuceta yasoma taka step bata dago da kanta ba, sai da tabbatar da tadaina jin motsen takunsa" sannan ta dago tana sauke ajiyar zuciya tare dafe kirjinta tace wayoooo Allah kirjina .
dan ita kadai tasan yadda ta dinga ji .
can taji sautin shigowar sako a wayar Ummi " ,sharewa tayi tunaninta ko yan network ne.
Dan haka ta maida hankalinta kan shirin da'ake gabatarwa a TV.
minti biyar tsakani taji wayar ta dauki kara ta dauki wayar tana dubawa .
Wata bakuwar number tagani" yana yawo akan screen din .
Dan haka ta manna wayar a kunneta tare yin sallama .
muryar da tafi so da tsoro ne "ta daki dodon kunneta hakan yasa jikinta ya sake daukar rawa gabanta yashiga faduwa da sauri .
,yace ke dan iskanci da rainin wayo bakiga sako na bane ?
Muryarta A sanyaye tace ban gani ba Amman kayi hakuri dan Allah tsaki yaja tare da kashe wayarsa .
Da sauri tashiga in box din tasoma duba sakon
Kisame ni a dakina yanzu " abinda tagani kennan .
,take gabanta yacigaba da faduwa , duk da tana cikin fargaba hakan bai hanata ,mutunta kanta
da son janyowa kanta martabarta ta Diya mace .
Sai da ta dauki mintina tukun ta mike cikin sanyin jiki ta nufi dakin shi .
tsaye take akan kafafunta a bakin kofar dakinsa zuciyarta na dokawa .
tsoro taji yana shigarta sai ta daura hannuta kan handle din kofar .
sai tacire hannuta da sauri .
,da kyar tasamu tattaro duk wani kuzarin dake jikinta .
,karfin hali tayi wanje murda handle din kofar da iya karfinta tashiga parlour'n da sallamarta .
shr parlour bakajin komai sai karar TV tsayawa tayi tana jirashi kusan 5 minti bata ga alamunsa ba ko jin motsensa batayi ba . dan haka ta yanke shawarar shiga Bedroom dinsa.
tana shiga dakin gabanta ya tsananta faduwa , cikin sanyin murya ta sake yin sallama .ya amsa da kyar km a ciki .
Zaune taganshi yana operating system sanye cikon wando three counter da pure whit singlet , ahankali take takowa har inda yake yayinda kanta ke sunkuye .
tsugunnawa tayi a gabansa muryata na rawa tace Gani Yaya .
GA TSARABARKU TA KANO BA YAWA KUYI MANAGE 😃😃😃
0 comments:
Post a Comment