A matukar haukace ummi tayi kan zeeent Tana jijjigata tana kuka tana kiran sunanta zeenat .....zeenat ki tashi dan girman Allah ki tashi kar ki min hk kar ki mutu kibarni ....idan wani Abu yasameki bazan taba yafewa kaina ba nice sanadin komai ni najawo miki duk wannan wahalar da maseefar please zeenat....
shima deeni a zabura ya mike tsaye yayo kanta yana girgizata da wani irin sauri yaje ya dauko ruwa yashiga tsiyaya mata Amman still ko motsi batayi ba hankalinsa yayi mugu mugun tashi fiyye da tunani me karatu. sunanta kawai yake Kira yana girgiza kumatunta hatta haidar da Anan kuka suke sosai banda junior dake zaune yana kallonsu yana sheshekar kukan dayaci.
hannuta haidar da Anan suka rike suna kiran sunanta aunci aunci ki ta chaci ki chaci aunty dady yace ki chaci deeni ya tallabota agigice ya rungumeta jikinshi yana kiran sunanta gabadaya ya rikice yarasa yadda zaiyi .
da inda zai nufa daita kawai ya cicibeta ya nufi dakinsa daita ummi da yaran na biye dashi abaya suna faman kuka Yana shiga dakin ya kwantar daita akan gadonsa.
" ummi wacce gabadaya tagama rudewa da gigicewa ta fita haiyacinta tarasa takamaimain abinda yakamata tayi .
ta saka wani irin Kara tare da cewa Dan ubanka nan yakamata kayo min daita ko hospital? Uhmmmmm wato kana son kashe min ita ne ko ?
Deeni da alamun kana bukatar ganin bayana kanason ganin karshena wallahi muddin wani Abu ya samu zeenat wlh wlh bazan yarda ba .
bazan barka ba sai nayi kararka zuwa court... azubure ummi ta sake frigita ganin yadda kwata kwata zeenat bata motsi bata numfashi sai surutai kawai take zuwa tana zagin deeni.
A matukar hassale deeni ya juyo yana kallon ummi muryarsa a kausashe yace haba ummi ya kike son nayi da rayuwata?
Ni kaina bazan so wani mummunar Abu yasameta ba first love.
ko babu komai zeenat Matata ce km yar uwata ce front &back babu ta inda zan yakiceta ajikina da zaki dinga cewa idan wani Abu yasameta bazaki yarda ba bazaki barni ba .......
ince duk kece kika jawo mata wannnan matsalar da tashin hankalin kece da kanki zaki kasheta da hannunki bani ba kece kika sakata cikin wannan damuwar da tashin hankalin bani ba da tun farko kin barni nayi aurena abayyane tasani kowa yasani da duk hk bata faru ba .
Amman gabadaya first love kin hana komai kin bata komai kin ruguza komai Amman kina neman daura min laifin da banawa ba.
wlh first love koni idan wani abu yasamu zeenat ni da kaina zan fara kai kararki court kafin ki kaini .
Dan ni aka fi cuta kisani yin *AUREN SIRRN* da yarinyar mutane batare da saninta ba sbd kawai naki farincki keda yarki kina neman kaini wuta first love bisa ga zunubin zeenat yarinya tana aikata kuskure Amman Kiri Kiri baki son laifinta baki tsawata mata bakison wani yayi Mata hukunci bisa ga kuskurenta yanzu WA gari yawaya?
Ummi ta fashe da wani irin mahaukacin kuka batasan sanda ta cire Hannuta ta daukeshi da gigitaccen Mari tana kuka tace yanzu deeni har mu kawo wannnan stage din?
Yanzu ni Kake gaggayawa mgn hk?
ina fada kana fada?
Nice nazama abar sakace hakoranka.
ni kake fadawa duk abinda yazo bakinka dan kawai soyayyar wata ya Rufe maka ido .Amman wlh bazakasan bakada hankali ba sai kabari wani Abu yasamu zeenat dina a sanadinka lokacin zakasan ko waceceni.
km lokacin zakayi dakasanni kasancewata uwa gareka ta juya fuuuuuuuuuu ta nufi dakinta da sauri har tana hadawa da gudu gudu ta dauki waya tana kiran family doctor dinsu hawaye na Bin kuncinta.
Jiki a matukar sanyaye deeni ya dauko ruwa a fridge yashiga kwara mata still shr Kake jin zeenat ko gezo batayi ba wayarsa ya zero yashiga neman layin doctor yana zariya adakin yaran suka haye gado suna jijjigata da kiran sunanta idanusa ya zuba masu Yana mamakin yadda yaran datake jin haushin akan sunki sabawa daita suka damu daita..
duk da basanin halin datake ciki suka Yi ba .
ya runtse idanunshi daidai lokacin da'akayi pik din call.
a hanzarce ya bada Umarni kawai tare da cigaba da kaikawo acikin dakin ....hankalinsa atashe.
Yayinda nablah dake tsaye a parlour junior rabe ajikinta .
sbd tsabar rudewa da frigicewa da tashin hankali ganin abinda take gani sandarewa tayi agurin tazamo tmkr mutun mutumin tabbas babu karya cikin zancen deeni .
fuskar mahaifinta take gani har lokacin yana murmushi wanda tarasa na mene yana cigaba da daura aurenta da mutumin dake ganin jegoni ne arayuwarta .
babu abinda take gani sai hoton mahaifinta yana mikawa wasu daga cikin makwatansu hannu suna gaisawa alamun angama daurin aure yana musu godiya.
Nocking din kofar parlour gidan ake da Danna bell da karfi.
koina agidan ya karade da sautin Kara deeni yA fito da sauri ya wuce nablah tsaye wiki wiki da idanu still tana kallon TV wanda ke sake rewaning din kanshi.
ya nufi kofa yana budewa yaga Ammar tsaye aiko take ya hade rai dan tunani shi ya dauka doctor ne yakaraso. muryasa a dan kausashe yace ya'akayi ne?
Amar yace daman Big dady ne yace kazo yanzu yanzu yana son ganinka gabansa ya buga yashiga dukan uku uku nazo fa?
Amar yace uhmmmmm hk yace.
OK kace masa gani nan zuwa bai tsaya bi takan amar ba ya juya yakoma ciki tare da kule kofar. Ya
Janyo hannu nablah gabansa na tsananta faduwa ya zaunar daita please nabeelah ki dawo cikin haiyacinki kisanyawa jikinki natsuwa kinsan bake kadai bace kurka sa zuciyata ta buga... shr kawai tayi takasa cewa dashi komai still imagine din abinda ke faruwa take acikin memory dinta .
yaja hannuta cike da sanyi jiki muje ki sauya kayan jikinki kin mikewa tayi sai ma alamun da tayi masa da kanta daya barta kawai.
dan hk yabarta ya Mike yaje dakinta ya dauko mata doguwar riga ya zira mata daga zaune a in datake ..
Byn kmr mitin 15 sai ga doctor yazo .
da hanzari deeni ya shigar dashi inda zeenatb take kwance tmkr matacciya.
batare da bata lokaci ba yasoma AIkinsa cikin iya da kwarewa ummi takasa tsaye takasa xaune ta fice daga dakin tana adduar Allah yadawo mata da numfashin diyarta kuka take sosai tana furta duk adduar datazo bakinta da adduar da mutun zai Yi idan yana cikin kunci da damuwa *allahumma lasa'alah illa maja'altahu sahla WA'anta taja 'alul huzna iza shita sah'alah*
Shi take ta maimaitawa da Inna lillahi wa Inna ilahi rajiun...
Shiru shr Big dady zaune zaman jiran zuwa deeni shr har awa daya ta wuce bai ganshi ba .
ya yunkura ya mike tsaye tare da sandarsa yasoma takowa ahankali yana saukowa daga balcony dinsa dan duk dramar da akayi akofar gidan deeni akan idonsa komai ya Faru kasancewar babu wani nisa tsakaninsu tundaga lokacin da zeenat ta hankado nablah harabar gidan ta fada kirjin deeni har zuwa sanda deeni ya rungumo yarinyar da bai san kowacece ba zuwa cikin gidan.
tun lokacin hankalinsa ke tashe yakasa samun natsuwa. Ahankalin dattijon yacigaba da takowa har ya sauko zuwa harabar gidansa tare da kwallawa amar Kira ...
amar yataso da sauri yana amsawa Big dady yace muje ka kaini gidan deeni .
amar yacewa big dady yaface yana zuwa.. Nidai kaini kawai hankalina yaki kwanciya da alamun akwai wata Matsalar dake faruwa agidan.
Hk suka shiga mota amar yaja sai gidan deeni amar yayi parking ya fito da sauri ya budewa big dady kofar motor .
big dady ya fito ya nufin door din gidan da kanshi yashiga dannan bell deeni ne still yazo ya bude masa yana ganina ya hau shafa keya yana masa sannu da zuwa kana yace big dady ai dakayi zamanka zanzo koda baka zo ba yakarasa fadar hk yana me bawa dattijon hanyar shigowa wanda daidai wannan lokaci numfashin zeenat yasoma dawowa tana farkawa ta saki wani ihu me karfi gaske deeni ya bar big dady zaune ya hanzarta da sauri.
" shi da ummi suka shiga rigerigen shiga dakin tana ganin ummi ta sake rushewa da wani sabon kuka ummi ta rungumeta ajikinta tana kuka zeenat na kuka shi dai deeni godiya yashiga yiwa Allah dayasa numafshin ya dawo jikinta .
yakarasa inda take rungume da ummi yakamo hannuta yana mata sannu tayi saurin zame hannuta cikin nashi tare da rutse idanunta alamun batason ganinsa.
ya mike jikinsa a matukar sanyaye yana yiwa doctor godiya suka fito daga dakin suka nufo parlour inda big dady ke zaune .
suna fita numfashin zeenat yasoma sezing da kyar take jawo shi tana fitawar .
ummi ta saketa ta rugo da gudu tana kiran deeni da doctor turussss tayi ganin big dady zaune yana rike da junior yayinda idanunshi kyam Akan nablah wace har lokacin bata cikin haiyacinta .
take ummi tawayance tare da nuna wa doctor hanyar dakin da zeenat take.
Doctor ya juya ya da wani irin mahaukacin sauri ya koma .
bayan doctor ummi tabi batare ta tsaya bi takan big dady ba.
tayi cikin dakin da sauri byn komai ya daidaita numfashinta ya dawo normal wanda zuwa lokacin kukanta ya Dan Tsaya sai numfashi datake janyowa.
da kyar ta bude bakinta kmr batason yin mgn tace ummi fitar Dani daga dakin nan zuciyata ummi zata buga idan nacigaba da zama cikinsa .
babu mutsu jiki na rawa ummi ta kamota jikinta suka fito .
kiyi hkr manana kiyi addua mamana zaki ji saukin radadin abinda ke damunki.
ta nufi hanyar up stairs daita da niyyar kaita dakinta zeenat ta girgiza mata Kai ummi karki kaini... Kifitar Dani daga gidan nan gabadaya banason zama cikinsa take ummi tayo Hanyar main parlour din gidan batare da taso ba.
Yayinda big dady still yana zaune suna zantawa da deeni ya bude bakinsa Kennan da niyar tmbyrsa abinda ke faruwa ya hango tahowarsu ummi zeenat makale agefenta suna takawo ahankali yayi shr kawai yana dubansu.
ganin hk yasa ummi kasa wucewa ta gabansa ta zaunar da zeenat akan kujera itama ta zauna hannuta rike da yatsun zeenat sai lokacin ta gaida Big dady .ita ko zeenat kasa mgn tayi ta runtse idanunta gam tana jijjiga jikinta... Big dady ya amsa gaisuwa yana dubansu daya byn daya gabadayansu har nablah fuskarshi dauke da tambayoyi irir iri.
sai daya gama nazarinsa akansu tsab sannan ya numfasa yace ya duk naganku wani iri hk kmr akwai damuwa meke faruwa daku ?
Deeni yayi Shiru yayi kasa da kanshi yana yashafa keyarsa gabansa na cigaba bugawa jira kawai yake yaji abinda ummi zatace.
ahankali yaji sautin muryar ummi tace babu komai big dady.
deeni ya dago kanshi da sauri yana duban ummi afrigece take suka hada ido ta tawatsa masa wani irin kallo tare da wata uwar harara sbd atunaninta shine yakira big dady .
big dady yace ya ina kallon tsantsar damuwa da tashin hankali afuskokinku har wannan baiwar Allah da bansa kowacece ba Amman fadeela kice min babu komai .
ummi ta daure fuskasta sosai ta sake cewa babu komai big dady .
ganin da deeni yayi kmr ummi batason asan abinda dake faruwa agidnsa ballantana asamu matsalaha Da daidaituwar lamari.
gashi shi yanzu yagaji Da boye boye gara ayita takare kowa ma yasan komai shi badamuwarsa bane.
dan haka gabansa na bugawa da karfi. muryasa a dake yace big dady akwai damuwar nan fa da tashin hnkali wanda km duk first love ce silar komai .ya sauke numfashi da ajiyar zuciya kana yacigaba
big dady wannnan yarinyar da kake gani zaune yana nablah da yatsansa *MATATA CE* ta Susan wacce ummi ce da kanta takawo min ita gidan tace na aureta batare da duniya tasan da hk ba .
Big dady yayi Jim yana kallon deeni da ummi da da alamun yana bukatar Karin bayyani daga gunta.
ummi ta tsunkuyar da kanta kasa Take wani gumi me zafi ya rufeta.zeenat ta dinga kallon ummi zuciyata na bugawa tason taji ummi takarya ta abinda deeni yace Amman taji ummi tayi shr .muryar na rawa tace karkawa ummi karya yaya ummina bazata taba min hk ba wlh, deeni ya watsmata wani kallo kana
Ya gyara zama yashiga zaiyanewa Big dady komai daki daki daya fair tun daga farko shirya lamarin har karshe .big dady dake zaune yana sauraron deeni har sanda ya dasa aya ya numfasa yana duban ummi sannan yakira sunanta fadeela kina jin abinda deeni ya fada meye gskyr lamari.....? Ummi Tayi shr tana kallon big dady... Kennan gaskiya ne abinda deeni ya fada ta fashe da kuka tana jijjiga kai alamun hk ne... Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kawai big dady yashiga furtawa yana maimaitawa yana kallon ummi jikinsa a matukar sanyaye..
Wani irin razananiyar Ihu May karfi gaske zeenat ta saka tayi zumbur ta Mike tsaye jikinta na kirrrrma ta jingina jikinta da bangon gurin tana duban ummi afrigice sannnan ta fashe da wani marayan kuka me taba zuciya da cin rai tace Wayyyyyyyyyyyyyo allahnah ummi kin kasheni na mutu na lalace wayyo ni muZeenat shikenan tawa ta kare atsorace deeni ke kallon zeenat yadda ta birkice ta fita haiyacinta ta zama tmkr wata sabuwar mahaukaciya sabon kamun hauka .
ta haukace ta Dinga kuka tana ihu tana kiran ummi kin cuceni ummi kin rabani da farincikina ummi ta dafe kirjinta azuciyarta narawa aranta tace tabbas na cuceki manana Amman bansa hk abun zai juye bisa kaina ba.
kinci amana ummi kin yaudareni kin ci amanata kin cuceni .
da mahaifiyata na Raye nasan dabazaki min hk ba yanzu ummi ke da kanki kika yiwa zeenat dinki kishiya.....
Keda kanki zakiwa zeenat dinki kishiya..kishiyar ki rasa wace zakimin sai yar aikina.... gsky baki kyauta .
Baki kyauta min ba ummi sbd bana haihuwa .
laifin danayi ban cancanci wannan hukuncinba yar aikina fa ummi .
Ummi wani cikin ne fa daita har na tsawon wata shida nan da wata uku zata sake haifar masa wasu ya'ya nashiga uku ni muzeenat wannan wace irin bakar rana ce gareni .
ta sake zabura tayi wani irin ihu tayi kan nablah ummi tayi saurin rungumeta ajikinta tana kuka ummi nayi .
kiyi hakuri diyata bawai nayi hk Dan na cutar dake bane diyata .
nayi dan nema maki farinciki acikin rayuwar aurenki ne.
bansan gadar zare nashiryawa diyata mafi soyuwa araina ba tun ba yau nake kukan nadamar abinda nayi ban km san rashe zai juye da mujiya ba kiyi hkr tabbas kuskurena ne ya jefaki cikin bakinciki dakike ciki.
Amman duk rintse duk wuya bazan taba Barin ki wulakanta a duniya ba matukar ina raye ina sonki zeenat fiyye da komai dake cikin duniyar nan adalilin sonki yasa na aikata hk..
kuka suke sosai gwanin ban tausayi. Kuka zeenat tacigaba da Yi Don yanzu wani irin haushin ummi takeji matuka acikin ranta ganintake duk abinda ya sameta ummi ce silar komai ahankali ta dinga zame jikinta daga jikin ummi tana girgiza kai tana kukan ummi kin cuceni kingama da rayuwata kin kassara zuciyar zeenat dinki tunda Arasa wace zaa min kishiya daita sai wannan ..... Diyar talakawar Mara galihu wacce sanadin babu taxo aikato ina zaune da kishiya guri daya batare da....big da ya katseta yana girgiza Kai batare ya iya furta komai ba dan gabadaya abin ya girmama tunaninsA bai Taba jin inda akayi aure irin wannan ba.
Wani irin kallon nablah kewa zeenat ME tattare da tsansar takaici
Take tana gama jin komai tazama mahaukaciya tuburan tafita daga hankalinta tafita cikin natsuwarta tasoma surutai bake kadai aka cuta ba aunty har Dani .
ni aka cuta wallahi ni aka cuta ..hankalin amatukar tashe takarasa inda deeni yake tsaye yana dubanta tashiga nunashi da yatsanta deeni ka cuceni na tsanaka bana sonka bana kaunarka deeni na tsaneka har abada bazan taba sonka ba kai ne Ashe kasaka rayuwata Cikin kangin rayuwa da bakinciki da ukuba da tsananin kunci rayuwa .
kai ne ka ruguza min farincikina ka lallaba ka dirka min ciki yanzu ga wani ciki .
Meyasa baka zo min a siffarka ta mijina ba ?
Meyasa baka Aureni ta hanyar da Allah ya halallata aure ba ?
Meyasa baka inganta rayuwata ba ?
kasa na haifi ya'yana a wulakance ankirasu da shegu alhalin halallatattu ne ankirasu da yayan zina Kasa ankirani da Mazinaciya karuwa deeni .....kasa ni kaina ina zargin kaina .
Kasa ni kaina nakasa yarda da kaina takarasa mgnr tana zubda hawayen tausayin Kanta ahankali ta juya tsaitin da ummi ke durkushe Gaban zeenat har lokacin suna kuka me taba zuciya muryarta cike da matsanancin kuka tace ummi yanzu inda yarki ce ni ta cikinki zaki yarda Amata irin wannan auren wulakancin da kaskancin kodayake ma diyar da kike ikirarin kina sonta itama kincin amanatar duk da yake mu talakawa ne ta maida idanunta cikin na zeenat sosai sannan tacigaba da mgn cike da tashin hankali.
ba kaskantattu bane mu ba Km wulakantattu bane ko aikatau da kikaga nazo Yi .
tawa kaddarar ce tazo hk bawai talauci ko rashin abincin dazamu ci bane yasa haka .
mahaifina bai da matacciyar zuciya sbd har yau yana neman na kanshi km yana rufa mana asiri tunda bai bar mu da yunwa ba ko kishin ruwa tunda ba tsirara muke yawo ba.
Da zakice yar talakawa yar aiki naji ni yar talakawa ce Amman na mishi ranar da ke baki mishi ba .
Sosai ta dinga sakin magannu batare da wata fargaba ko shakka ba hakika ummi ke da danki kun cuce rayuwata.
ummi na rikeki bisa amana tmkr mahaifiyata Amman sai gashi yazamanto da saka hannuki cikin jefa rayuwata cikin matsanamcin kangi me wuyar fita .
wlh wlh yau ko numfashina zai Kare sai nabar muku gidanku ta sake Maida shanyayyun idanuta masu cike da ruwan hawaye kan deeni sosai tana kallonsa wasu ruwan hawayen na tsiyaya, tasa hannuta ta goge hawayen kana tace ya'ya km naka ne na dade ina kwankwanto hk acikin zuciyata deeni na dade ina zargin wani alamari game da Kai.
Na Dade ina tunanin cewa kaine kake zuwanmu acikin mafarkina ashe bamafarki bane gaske ne ummi na dauke uwa nabi ki har daki nagaya miki matsalar dake damuna game da aljanu suna ku santata Amman kikace min wai babu wani aljanu nayita addua kin mata Ashe dake aka hadu ake son tsaida yancina zuwa bauta....
Meyasa ummi ?
Meyasa kikayi hk wlh ban taba tunamin hk dagareki ba ummi ..ko numfashina zai dauke koda zan rasa komai da kowa arayuwata zan tafi zanbar gidan nan yau km a yanzu km wallahi bazaka taba mallakata ba deeni sbd hanyar da biyo gurin mallakata. kabiyo ta hanyar da bata dace ba sannan km ya'ya nakane gasu nan sannan km wannan cikin ko Zan mutu bazan haifeshi ba .deeni ya zabura ya matso gareta jikinsa na rawa zai tabata tayi karka taba mugu ME cin amanar ya'yan mutane ta juya da sauri tayi hanyar dakinta..
Wani irin kuka xeenat ke Yi nafitar hankali da taba zuciya ahankali big dady da kanshi ya mike ya dagota ya runguneta ajikinshi yana shafa bayanta sun kusan miti goma ahaka sannan ya Dakota ya kura mata idonsa dake cike da ruwan hawayen tausayinta .. Girgiza Kai tafara cikin kuka tace big dady karkamin kuka kada kada zubda hawayenka akaina duk abinda ya faru Dani ,ni njawowa kaina. Da kaina da nayi hkr lokacin da Allah yabani nawa arxiki ya'ya da yanzu ban tsinci kaina cikin wannan damuwar da tashin hankalin ba. Gabadaya tausayinta yakama mutane gurin. Kuka take sosai tana nadamar abinda ta aikatawa rayuwa ta rarrafa zuwa inda ummi ke zaune tana goge hawaye.
ta daura kanta bisa cinyoyin ummi.. Ummi kiyi hkr kiyi hkr ummina ki yafemin ki min aikin gafara bisa furuncina gareki bazan taba yin fushi dake ba ummina nasan ni na cuci kaina bakece kika cuceni ba nasan kinyi hk ne sbd daurewar faruncikina a gidan yaya bazan taba butulce miki ba ummi duk duniya banida wacce tafiki ...Tana kuka take mgn ummi ina neman alfarma agurinki ki taimakamin kisa deeni ya sauwakemin aurenshi dake kaina na hutawa rayuwata da ganin bakin ciki.
ummi tashiga girgiza mata kai tana kuka.. ummi bazan iya ganin da jurar kallon yaya tare da wata ba .
zuciyata ummi zata tarwatse zan mutu.... Mutuwa zanyi ummi muryata cike da kuka takarasa mgnr...haidar da anan har junior da suke zagaye da ummi suka shiga goge mata hawayen dake tsiyaya da hannusu....
Yaran kamar wasu manya suka rungume ta, suna kuka, itako Nablah da gudu kamar zararriya ta sauko daga sama tayi hanyar fita, kota kan yaran bata bi ba balle kayan ta, cikin zafin nama Deeni yayi kanta ya manta da jama'ar dake falon, rik'o ta yayi gam a jikin sa, yace " pls Nablah karkiyi min haka, karki guje ni, kar ki hukuntani da laifin da ba nawa ba, wallahi kece rayuwata idan kika barni mutuwa zanyi, matuk'ar bakya kusa dani Nablah rayuwa ta bata da wani amfani, ke haske ce a gare ni, pls karki min haka, ya k'arasa maganar hawaye nabin fuskarsa, da k'arfi ta hankad'e shi ta kalleshi ido cikin ido ta nuna masa yatsa tace " don't, don't ever touch me again, I hate you Deeni, you are monster, you are cheater,you are liar, deceiver, I don't want to see you again in my future life.
, ka yaudare ni, na yarda dakai, na d'auka kafi kowa so na, da tausayi na, ashe kai mugu ne, I can believe it, Deeni kaine kayi man haka. Duk yaran suka taso suka bar jikin zeenat suka rungumeta a fusace ta cire su daga jikinta. Tana cigaba da mgn.
Yara gasu nan, dama sune burinka, to Allah ya cika maka, ka rik'e kayanka, Deeni yace " pls Nablah you are my life, don't live me, murmushi tayi cikin kuka tace " ur life, kanka kawai ka sani, ta juya zata fita, da sauri yace " a matsayi na mijinki ban baki izinin fita ba, juyowa tayi ta tako gaf dashi tace " miji!!! , ta nuna shi tace " wai kai kana tak'amar miji, gaya man meye miji meye aure?
"Sannan ka sanar dani hakki na d'aya dakataba sauke min, bayan biyan buk'atar kanka, kai yanzu baka ji kunyar kiran kanka mijin Nablah ba, yanzu .
Deeni shi kanshi mahaifina kaji kunyar sa, bai sanka ba, bai san daga inda ka fito ba ya d'auki 'yarsa ya baka, ya baka yarda da amana, nasan mahaifina ba dan matsayinka ya bakani.
dan nasan baima san waye kai ba, balle yasan abinda ka mallaka, Deeni daga ni har mahaifi na ka cuce mu, ka yaudare mu, amma ba komai Allah na nan, ta juya saitin zuciyar sa ya dafe, yana kuka sosai kamar k'aramin yaro ya matso inda take, yace " wallahi Nablah ina sanki fiye da komai da kowa a duniya you are my first love, I love you so much, wallahi Nablah idan kika barni zuciya ta bugawa zata yi, mutuwa zanyi Nablah, rayuwata bata da wani amfani matuk'ar bakya tare dani.
Wani irin mahaucin kuka Zeenat ta saka tabar jikin Ummi tace " Ummi kinga abinda kika jawo min ko? Ina zaman lafiya da miji na kin d'auko min bala'i tunda nake da Deeni bai taba'a furta kallar koda yana so na ba , balle yace he love me so much, Deeni bai tab'a gaya min kalaman soyayya ba, Ummi alhakin Nablah ne zai kamaki, shiyasa Allah ya jarrabi Deeni da sonta fiye dani, koma ince fiye da kowa harke tunda kema da kunnanki kinji abinda yake cewa akan ta, Ummi kinga yadda tunaninki ya cutarda mu, ta k'ara fashewa da wani mahaukacin kuka.
Shidai Big Dady kallan su kawai yake ya rasa abinyi, nablah tasoma daga kafafunta Deeni yace" pls ku taimka kuyi mata magana kusa baki karta tafi ta barni, wallahi ita ce rayuwa ta, kafin kowa yayi magana Nablah tace" wallahi ko mutuwa zakayi deeni sai na barka, kai koda gawarka kace a gaba na zan saka k'afa na tsallake ta, tasa hannu ta share hawayen dake zubo mata tace " akan me zakayi *AUREN SIRRI* dani,.
shi ban kai maccen da za'ayi Auren bainar nasi dani bane komai?
Kai ya girgiza mata yana kuka kamar wani k'aramin yaro, tace" san kai ne yasa kayi min haka, ka aure ni, ban sani ba, ka rink'a kusantata ba tare dana sani ba , harka yi min ciki, ka k'ara lallab'owa ka d'irka min wani ciki, yanzu ma in banda Allah ya toni asirinka da sai dai kayi tayi man haka, ina haihuwa ka yanke min jin dadi kanannaye komai na rayuwata ta fashe da wani sabon kuka tace " Allah ya isa Deeni, Ubangiji ya saka min, & I will never for gv u, ta jiya zata fice sosai Deeni ke kuka ya durk'usa gwiwa bibbiyu a gaban Nablah yana kuka wiwi yana rok'onta karta barshi.
Zeenat ma kukan bak'in ciki take, a gabanta mijinta yake durk'usawa agaban macen da bata kaita komai ba yake rok'onta ta so shi, zuciyar Ummi kuwa kamar zata tsage don bak'in ciki da takaici, ji take kamar ta d'ora hannu aka ta fasa ihu, ta gwammaci mutuwarta da ganin wannan rana, Deeninta ...tilon danta mai kyau,da tarin ilimi,da aji, gata, ga naira, yau shine yake rusa kuka durkushe a gaban mace yana rok'on soyayyarta, a gabanta kuma ba Zeenat d'inta ba.
Deeni na dafe da zuciyar sa, yana kuka a gaban Nablah, ganin zata fita ne, kuma babu wanda ke da niyyar yi mata magana kan ta tsaya.
ya sashi cewa " idan kika fita nabeelah ban yafe miki ba, Allah ya isa, ci gaba tayi da tafiyar ta,batare data juyo ba yaran ma suka bayanta suna kuka.
murmushi irin na manya Big Dady yayi sannan ya kira sunanta NABEELAH!, cak ta tsaya ba tare data jiyo ba, yace " zo nan, diyata a hankali ta jiyo ahankali tazo gabansa ta durk'usa, sai kuma ta fashe da kuka, da rarrafe Deeni ya rarrafo zuwa inda take yazo gabanta yace " please my heart kice kin fasa bari na, yayi maganar kamar wani zararre, Big Dady ne ya daka masa tsawa yace "deeni ka shiga hankalinka, sannan ya juya ya dauki waya yakira Ammar yace " kasanar da Family gabadaya cewar akwai meeting, nan da 1hr maza da mata har wad'anda ke gidan miji ka kira su ka sanar dasu, Big Dady ya kalli Nablah yace " jeki d'auko hijab d'inki, ba musu ta shiga d'aki ta kintsa kanta sosai sannan ta fito, Big Dady ya kalli su Ummi da Deeni yace " nan da 1hrs ku hallara,r ya kalli Nablah yace " muje, da sauri Deeni ya mik'e yace " nima zan bita, wani wulak'antaccen kallon Big Dady ya watsa mai wanda yasa shi ya shiga hankalinsa dole, Anan, Haidar, Junior gaba d'aya suka rik'e Nablah suka saki kuka mai ban tausayi, Big Dady ya kalli Ummi yace " jebi yara abin tausayi dan Allah, wallahi hakkin yaran nan kad'ai ya isheki, kodan gashi nan ma kin fara gani, Big Dady ya rik'e hannun Anan, ya kalli Ammar yace " rik'e Babanka, Ammar yayi murmushi ya d'auki Haidar, da junior big dady ya d'auki Anan, suka tafi gidan Big Dady. Har nablah.
Meeting room
A babban falon Big Dady kowa ya hallara manya da yara, maza da mata, ciki kuwa harda FK, gefe ga Deeni sai Zeenat dake ta faman kuka, kusa da Ummi, Nablah ma har lokacin kukan take, yaranta na nanik'e da ita, Big Dady yayi gyaran murya, ya kalli Fk yace " bud'e mana taro da addu'a, bayan an kammala ne Big Dady ya kalli Deeni yace " maimaita abinda ya faru, ba tare da tsoro ko wani fargaba ba Deeni yashiga zayyana duk abinda ya faru tun daga farko har k'arshe, kmr yadda ya sanawar da big dady kowa a wajen ya hau kallon Ummi yana mamaki, had'i da yin sallallami, gyaran murya Big Dady ya kuma yi sannan ya kalli Ummi yace "
Yanzu ke fisabilillahi kinyiwa yarinyar nan Nablah adalci, idan 'yarki aka yiwa haka ya zaki ji, wanne irin mataki zaki d'auki, ki duba yadda kika tauyewa yaran nan hakki akan farin cikin ki keda 'yarki, a ganinki kinyi dai-dai, ke yanzu ko tausayinsu baki ji bA.
, baki kunyar mahaliccinki, haba fadeela gaskiya baki kyauta ba, shiyasa Allah ya nuna miki baki isa komai ba, ya fifita yarinyar a zuciyar Deeni fiyye da taki 'yar, mai gatan, shiyasa Allah ya nuna miki ikonsa yasawa Deeni matsananciyar soyayyar Nablah, ta yadda bazai iya daurewa ko yi miki biyayya ba, a gabanki, akan idonki ya durk'usa a gaban ta yana kuka akan ta so shi, wannan kad'ai ya isheki izzina, da kuma darasi ga masu halin san kai irin naki, ki dubi yaran nan ya nuna su Haidar yace " idan suka girma suka ji abinda kikayi musu, da mahaifiyarsu kina ganin zasu k'aunace ki, ke ko tausayinsu baki ji, baki tausayin yarinyar nan k'arama yarinya kmr wannan dan nasan batafi 18yrs ba, kinga yadda Ubangiji ya nuna buyawarsa akanta ya hana 'yarta ki haihuwa da Deenin.
"Ni nasan bazaki tab'a yarda ayiwa 'yarki haka ba, idan ko akayi mata sai inda k'arfin ki ya k'are, gaskiya kina da san kanki, baki da adalci, wallahi ki nutsu ki koma ga Allah, ki nami yafiyar yaran nan, kinga dai yadda Allah ya saukar da aya a kanki wannan kad'ai ya isa ki gane kuskuren ki.
Kinga dai yadda ke da kanki kika had'a muku GADAR ZARE, keda 'yar taki, kika yiwa 'yarki kishiya abinda tafi tsana arayuwarta, kuma bata tashi sani ba sai da kishiyar ta zama dole k'anwar nak'i, dan ko ba'a zauna da ita ba dole a zauna da 'ya'yanta tunda ga tanan nan ma wani tsohon cikin, kinga keda kanki kinyi mata illar da harta mutu bazata manta ba, wannan kad'ai ya isa kusan komai na Allah ne, shike yin abinda yaso akan wanda yaso, a kuma inda yaso, dan haka mutane mudaina gaggawa a rayuwar mu.
Sosai Big Dady yayi musu fad'a gaba d'ayansu ya had'a dayi musu nasiha mai ratsa jiki, sannan ya sallami kowa, duk wainar nan nan da ake toyawa inna bata sani ba, dan idan ta sani ba zaman lafiya shiyasa Big Dady ya hana a fad'a mata, yace " Deeni ya tsaya,
MAMAN SUDAIS
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
Dedicated to
Hauwa A Usman
jiddarh
Kainuwa writers association
(united we stand and suceed our ambition is to entertain & motovite the mind of readers)
https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/
Page 106
Byn kowa ya watse. parloun'n ya dauki shr na tsawon wani lokaci big dady ya dinga kallon deeni yana mamakin reaction dinsa na dazu daya dinga Yi akan yarinyar.
"ahankali Big dady ya cigaba da kallonsa tmkr wani sabon Halitta agabansa.
sakamakon yadda cikin kankanin lokaci gabadaya kamaninsa suka sauya ya dawo wani irin mutun Abin tausayi.
Ahankali big dady yake kalleshi tare da nazarinsa Kana ya numfasa muryarsa a matukar raunane irin ta Manya ya kira sunan shi..... deeni ya dago rikitattun idanunshi da suka gama canza kala tsabar rudani da tashin hankalin da yake ciki .
ya zubawa big dady su yana kallonsa batare da yace uffan ba.
" sai ma hadiye abinda ya tsaya masa amakoshi yayi yana maida hankalinsa sosai gurin sauraron abinda big dady zai ce .
Big dady ya sake fuskantarshi da kyau sannan yace nasuruldeeni na fuskacin kana matsanancin son yarinyar nan nabeelah kana mata mahaukacin so fiyye da tunanin me tunani wannan kalubali ne agareka sannan km babban yakine akanka daka San yadda zaka shawo hankalin yarinyar nan cikin sauki.
sbd daganin yarinyar tana da kafiya da taurin Kai da taurin zuciya sai kayi mugu mugun aiki da km yaki sannan Zaka samu ka shawo kanta da hankalinta.
" musamma sbd abinda akayiwa yarinyar wanda kowace Mace akayiwa hk zata iya yin hauka fiyye danata .
na Lura sosai kafi son yarinyar akan zeenat duba da yadda ka dinga yi wasu abubuwa agabanmu gabadaya idanunka sun Rufe deeni akanta.
so nidai abinda zance anan bai wuce nace kayiwa Allah kayi aldalci atsakaninsu deeni.
kayi adalci atsakanin matanka kada ka taba fifita daya akan daya karka sake kabari daya tagane kafin son daya akanta .
duk wacce Kake so axuciyarka kabarwa ranka yazama sirrin zuciyarka .
daman dole ne sai kasamu wacce zakaji kafi so atsakanin matanka .
Amman karkar kuskura ka bayyanawa kowace daga cikinsu.
kabarwa zuciyarka kayi adalci kaji tsoron Allah karike matanka amana dan karkaga nabeelah ce me haihuwa uwar ya'yanka kace zaka wulakanta zeenat sannan kada kaga zeenat yar'uwarka ce ka biyewa mahaifiyarka.
ku taru ku wulakanta nabeelah..
sosai big dady ya dinga masa Nasiha me ratsa jiki da huda zuciya dasa zuciya nadamar abinda ta aikata. Sannan zance ita yarinyar nan nabeelah kabarta anan tukun kafi asan abin Yi. ya daga kanshi alamun yaji.
byn big dady yagama dashi yace idan ya fita ya turo masa zeenat. Jikinsa a matukar sanyaye ya mike tsaye da kyar yana yiwa big dady sallama hade da godiya...
Byn ya fito ya iske zeenat zaune a karamin parlour'n gidan ya zauna kusa Daita sosai yana jin wani irin matsanancin tausayinta yayinda sound din kukanta ke taba zuciyarsa. "gabadaya nadamar abinda ya aikata agabanta yakeyi.
hakika bata cancanci hk daga gareshi ba kodan duba da yadda take matukar kaunarshi fiyye da komai arayuwata . cikin sayin jiki ya kamo tafin hannuta cikin nashi yasoma murzawa ahankali ahankali kafin yace wani Abu.
Da sauri ta zame hannuta cikin nashi tare da juyar da kanta alamun bata son ganinsa .
yaja numfashi da karfi ya fetsar yana tsura mata rikitattun idanunshi yana kallonta cike da tausayawa.
sannan ya bude bakinsa da kyar ya kira sunanta complete Name dinta muzeenat, ..............
zeenat taki juyowa ta kalli inda yake ballanta yasa rai da samun amasart.
sai ma jijjiga kafar daya da take tana cizan lips dinta.
Miryarsa a raunane ya sake kiran sunanta My Zeenat am sorry.... am very sorry for what I did...nasan ban kyauta miki ba .
sannan baki cancanci hk agurina ba.
" tabbas naso na kuntatawa rayuwarki alokacin da kikayita zubar min da cikina arariya ....Amman bata wannan hanyar ba.
Ko auren sirrin dana Yi da nablah ba'a son Raina nayi ba.
Umarnin first love nabi wanda alokacin gabadaya daurewar farincikinki take nema agidana .amman kiyi please ki yafemin bisa biyyewa first love danayi gurin boye miki..
duk wannan bayanani dayake mata bata juyo ta kalleshi ba har yagaji ya Mike da niyar wucewa tare da Sanar mata da sakon Big dady.
zeenat wacce taci kuka tkmr zata bar duniya idanun nan nata suka sake kankancewa sukayi sumtuma sumtuma sukayi jawur dasu . tashiga dakin da big dady yake zaune zaman jiranta.
wasu hawayen bakin ciki da takaicin abinda mijinta yayi dazu yashiga silalo mata bisa kuncinta.
ahankalin tasamu gurin nesa kadan ta zauna tana fuskantar big dady sosai .
wani irin tausayinta gyaraye da tsantsar kaunarta ke ratsashi. hakika yasan anyi mata laifi me girma...Wanda ta cancanci atausayawa rayuwarta da komanta. an tauye mata hakinta... anci zarafinta da mutuncinta.
an hukuntata da hukunci me radadi da ciwo da wuyar mantawa.
ya ja numfashi da kyar ya fetsar idanunshi kyam akanta yana nazarinta sannan ahankali yasoma da yimata nasiha akan yarda da kaddara .....
muzeenat kiyi hakuri da yadda kika tsinci kanki. ki yarda da yadda kaddaraki tazo miki.
wannan Abu ba daga umminki bane ba daga nasuruldeeni bane ba daga ita yarinyar bane daga Allah ne .
wannan hukuncin Allah ne ,ya zarta akanki.
" kada kiyi jayayya da ikon Allah.
kada kiyi fushi da abinda mahalinciki Allah ya zarta akanki .
"sannan rabon yayan nan ya rigada ya rantse muzeenat sai Sun xo duniya.
in ma ba haifesu ta hanyar sunnan aure ba sai sun zo duniya ,tunda Allah yarigada ya Kaddara akwai rabon ya'ya atsakain nabeelah da nasuruldeeni sai an haifesu kota hanyar shegu ne, musamm ma idan kikayi duba da yadda Allah ya nuna ikonsa acikin shekara daya Allah yabashi yaya har uku sannan ga wani cikin wanda Allah Kadai yasan abinda zata haifa.. wasu zafafan hawaye masu ciwo da taba xuciyar ma,aboci tausayi suka shiga gangaro mata a fuska ..
zeenat ta dafe kanta datake jin yana mata wani irin sara da mugu mugun ciwo.
cikin wani irin matsanancin kuka tashiga girgiza kanta yayinda aranta ta dinga furta kalmar Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un ...yaushe ni muzeenat zan samu sauyin rayuwa me dadi irin na kowace mace agidan aurenta?
.. Big dady ya numfasa kana yacigaba muzeenat ki natsu ki sanyawa zuciyarki salama akan lamarin nan sbd idan kin matsa dayawa rabo zai iya kasheki, ki mutu kibarsu, su cigaba da rayuwarsu cikin kwanciyar hankali .
Dan hk ina son kiyi hakuri ki Karbi wannan kaddarar data zo miki da hannu biyu biyu.
" ki rungume kaddarki muzeenat km da alamun yarinyar zata biki yadda ya dace .
zata miki biyayya kada ki zubda girmanki a idanunta itama Sosai yayi mata nasiha me ratsa jiki da sanyaya zuciya tunda big dady yasoma mgn bata dago kanta ta dubeshi ba .
Sai kuka datake kawai tana sake nadama abinda ta shuka arayuwarta.
wanda shi yajefa rayuwarta takasance hk.take wasu wurare suka dinga budewa jikinta suna karbar kaddarar tada fada mata. wani irin tsoron Allah ne ya sake shigarta..
Kafin kace me tunin zance ummi yakarade ilahirin estate din .
"masu zaginta nayi masu side dinta nayi kowa da yadda yake fadan albarkacin bakinsa akanta .
wayanda basa side dinta kuwa suka dinga Yi daita suna zaginta.
Tare da tsananin mamakin sonkai irin nata da butulci da cin amana da yaudara da haincin irin nata.
Sosai suke mamakinta . wannan wani irin sonkai ne daita?
kwata kwata batayi adalci ba.
Daga gidan big dady kai tsaye zeenat gidan babanta wasu daga cikin yan'uwaa suka nufa daita.
yayinda nablah ke gidan big dady Dan koda big dady ya gwada Yi mata Zance takoma gidan mijinta kafin asan abinyi.
kin yarda tayi, ta koma gidan deeni...
Daren Rana banda kuka babu abinda zeenat keyi wanda daga karshe ta yanke shawarar kaiwa Allah kukanta.
,ta Mike taje tayo alwala tashiga jero nafilloli tana kuka tana neman sausauci agurin Allah, ya kawo mata sauki cikin lamarinta .
byn ta idar ta Dade zaune hannuta rike da carbi tana lazimi .
kwata kwata takasa runtsawa sakamakon tuno ummi datayi tasan duk inda ummi take tana can cikin tashin hankali da kuncin zuciya .
tasan ummi bazata taba iya runtsawa ba.
Tasan yadda ummi ke matsanacin sonta da kaunarta fiyye da komai aduniyarta .
wasu zafafan hawaye masu ciwo suka shiga silalomata.
tana nan zaune tana ambaton Sunan Allah har sanda aka Kira asalatu bata runtsa ba addua Kawai take...
Sosai ummi tashiga tashin hankalin rashin zeenat tashiga uku tarasa abinda ke mata dadi ta rame acikin kwana daya kacal .
abun Duniya duk yabi ya dameta gabadaya yanzu kunyar dangin take ji.
da gudun shiga tsakaninsu sbd duk magangun da suke fada yana dawo wa kunneta hankalinta yayi mugu mugun tashi tarasa inda zata saka ranta taji dadin arayuwarta.
bata da kowa akasar Nigeria sama da zeenat da deeni suka gareta.
idan har zasu iya gujemata zamanta bashida amfani akasar.
Ahankali ta mike tsaye jikinta kasalance ta shiga tsintiri adakinta na ainihin gidanta.
Kafin daga baya ta nufi inda ta,ajiye wayarta takira Wanda ke mata biza zuwa kasar haihuwarta.
byn tagama wayar ta dauko yar karamar jakar matafiya tasoma shirya kayanta ciki tana hawaye tana jin wani irin radadi da kewar tilon danta deeni da zeenat aranta .
Tsab tagama shirya komai..
Itama tunda rigimar nan ya faru bata samu ta runtsa ba har zuwa yau din nan .
Washegari tana idar da sallah asuba ta dauki Jakarta da niyar barin kasar gabadaya.
ahankali take saukowa daga matattakalan gidan xuwa parlour'n kasa taji motsen alamun bude kofar cak ta tsaya da tafiyar datake jikinta ya dauki kirrrrrma...abinka ga jikin girma kadan ya rage batayi kasa ba.
Km har lokacin danunta na kallon kofar shigowa.
tilon danta deeni taga Yana kokarin sanyo Kai cikin gidan. Ahankali karasa yashigowa jikinsa sanye da farar jallabiya fara kal da alamun daga masjid yake.
Take wani irin sanyin dadi ya zirayarci ilahirin jikinta da zuciyarta.ta dinga jinta wani Iri wani iri.
Amman ta kauwar da kanta da abinda take ji tacigaba da saukowa ahankali jikinta naciga da rawa wanda har yar karamar Jakarta hannuta rawa yake.
gaban deeni ya buga da matsanancin karfi ganin umminsa rike da jakar matafiya .
Wanda duk sanda kaganta da ire iren jakunkunan Kasan tafiya zatayi.
har tazo ta gifta ta kusa dashi idanunshi akanta yana kallonta da mamaki a saman fuskarsa.
ganin tana shirin bude kofar yasa da sauri ya riko jakar hannuta Jikinsa na wani irin rawa ..muryarsa cike da in... Inna... yace u'm.... ummi ina km zaki tafi hk ?
Meyasa ummi zaki mana hk ?
ummi please.......
ummi kada kiyi hk Dan girman Allah kiyi hakuri ki yafemin ya zare Jakar hannuta ya ajiye agefe daya tare da tsungunawa agabanta gwaiwa biyu biyu ya daura tafin hannusa duka bisa kafafunta please ummina kiyi min afuwa bisa ga laifin abinda na aikata miki bazan sake ba.
na tuba ummi nabi Allah da manzonsa na biki. ummi karki kujemu.idan kika gujemu rayuwarmu zata tagyara zamu shiga wani hali dagani har zeenat dinki......
ahankali ta zare kafafunta zuciyar na wani irin bugawa jikinta yayi sanyi.
Take zuciyarta tashiga shawagin barin tilon danta da diyarta zeenat .. Taku daya tayi zuwa biyu taja ta tsaya hade da juya masa baya tana jin wani irin matsanacin kunyar deeni .har zeenat ahalin yanzu kunyar hada ido
take dasu.
Batason km hada idanunta danasu.
tarasa ina MA zataje ta saka ranta taji dadi da
wa zatayi hirar ta rage zugin da zuciyar ke Yi akan abinda ya faru zeenat kadai gareta diya Mace gashi itama tagujeta ta juyawa rayuwarta baya akan abinda ya faru...
Jikinsa na rawa da rarrafe ya samu ya matso inda take.
yace kiyi hkr ummina karki tafi ki barmu bamuda kowa a nan sai ke idan kikabarmu yaya kike son rayuwarmu takasance?
Ummi taja naunauyen ajiyar zuciya da numfashi ta sauke da kyar.
Kana tayi dauriyar juyowa tana kallonsa duk da har lokacin zuciyarta cike take tab da jin kunyarsa da kunyar abinda yayi mata gaban big dady da gaban dandazon daginsa sbd common Mace.... Mace ma wace itace da kanta ta tsaya tsayin daka ta aura masa ita ,yana kukan bai sonta....
"muryarta a dake tace Ai wannaN bakomai bane idan na barka deeni.. karka manta yanzu kana da madadina wacce tafi agurinka .
har kake kokarin yimin tawaye akanta you give me double surprise deeni akan Macen da nice na tirsasaka ka aureta ba dan kana sonta ba..
ni... ni deeni ta nuna kirjinta da dan yatsanta Amman babu komai karku damu duniya ce.
sai dai kasani ayau din nan zanbar muku kasarku da danginku gabadaya na koma tawa kasar .
dama dan wa Nike zaune?
Dan kai da zeenat ne Amman ayau kun nuna min ni din bakowa bace agareku km nasan ko babu ni arayuwarku zaku cigaba da rayuwarku yadda kuke so.... Takarasa fadar hk tana kuku .
deeni ya rude ya gigice hankalinsa yayi mugu mugun tashi ya sake rungumo kafafunta please ummi karki ce hk kice komai mu kice rayuwarmu kece farincikinmu kece jigon komai agurinmu karkiyi mana hk ummi yana mgn yana kuka yana rokonta tayi hakuri tayi masa aikin gafara ko a'lamura zasu daidaita gareshi.
gabadaya jikin ummi yayi tsanyi zuciyarta tayi rauni tausanyi dan nata ya huda kirjinta.
take komai ya kwance mata ita kanta bata kaunar abinda zai nisantata dashi shi kadai gareta sai marainiyar Allah zeenat .
Tana tsananin son deeni Amman soyayyar zeenat dinta daban ce kasancewar kaunar dake tsakaninta da mahaifiyarta .
tsawon lokaci suka dauka ahaka deeni nacigaba da kuka yana bata hakuri.
da kyar yasamu ya shawo kanta hannuta na rawa ta daura bisa kanshi ta shafa sumar kanshi Kana ta zauna ya daura kanshi bisa cinyarta yana kuka yana bata hkr .
yayinda ita km ta cigaba da shafa sumar kanshi muryarta a matuKar sanyaye tace is OK son kukan ya isa hk komai ya wuce Allah yayi maka albarka Allah sanya albarka arayuwarka data iyalinka gabadaya.
bai samun damar amsa mata ba sbd kukan dayake.
shi kanshi yayi muguwar nadamar abinda yayiwa mahaifiyarsa mafi soyuwa azuciyarsa... Ka tashi ka zauna akan kujera deeni ya tsinci muryar mahaifiyarsa..
ya dago kanshi yana dubanta yana girgiza mata Kai first love barni anan .
ya sake gyara zamansa agabanta suna fuskanta juna.
ummi ta numfasa tana dubansa gabadaya duk ya rame yayi dogon wuya data tuno dalilin abinda yasakashi dawowa hk tayi saurin runtse idanunta gam tana kukan zuci da blaming din Kanta.
itace silar fadawarsa cikin Matsala yana zaman zamansa da matarsa.. Da kyar ta bude idanunta tace ina zeenat dina take yanzu tana gidanka ne?
Ya girgiza mata kanshi sannan yace dukansu basa gidana.
Gabanta ya buga yashiga dukan uku uku bakinta na rawa tace ina zeenat Dina take ?
Tana gidan babanta....... ummi tayi dif kirjinta na wani irin lugude wasu sabbin hawaye suka zubo mata tasoma magana cikin harshen indiyanci , akan zeenat ta gujeta ta daina sonta sbd kuskurenta nason ganin rayuwarta ta inganta agidan danta. kuka take sosai tana daura laifin komai akanta.
deeni na rarrashinta da goge mata hawayen idanunta first love ki daina kuka yanzu zanje na dauko miki zeenat dinki bake kadai kika tsinci kanki cikin damuwar da tashin hankalin rashinta ba.
ni kaina nayi nadamar ramuwar gyayar da nayi niyyar mata yacigaba da gogewa ummi hawayenta .
ita km sai girgiza masa Kai take muryata na rawa tace kaje deeni ka... Kawo min zeenat a duk inda take ko zuciyata da ruhina za samu salama. sai da ya sake goge mata hawayen idanunta sannan ya Mike jikinsa a sanyaye ya juya yasoma tafiya hard ya kawo bakin kofa yana daura hannushi kan handle yaji an murda kofar.
ya dan dakata .. ahankali aka bude kofar.... Zeenat yagani tsaye sanye da doguwar riga da hijab lulube har kasa .
ido cikin ido suke kallon junansu kowace da abinda zuciyasa ke sakawa akan dan uwansa.
ahankali ta raba ta gefenshi ta wuce shi batare da tace masa uffan ba .
ya meida kofar ya Rufe ya biyo bayanta ummi na arba da zeenat ta Mike zumbur jikinta na rawa bakinta na rawa gurin fadar ma..ma... na tana me ware mata hannunta duka alamun tazo gareta zeenat ta fashe da kuka takasara tare da shigewa jikin ummi.. Ummi ta rungumeta ajikinta tana kuka.
a she tunani bai zama gaskiya a she zaki kawo kanki gareni byn duk abinda na miki? Gabadaya na ji kunyarki zeenat .
naji kunya akan yadda fasaha ta dauke min na kulla miki gadar zare da hannuna akamiki kishiya batare da saninki ba. ...
ummi ki daina kuka bazan iya barinki ba ummi dake kadai nasaba arayuwa bansan dadi uwa ba sai ke ummi.
ban rayu da mahaifiya ba sake ummina Kin nuna min gata fiyye "dan" cikinki ummi duk inda zanje nayi rayuwa aikin banza ne idan bana tare da ke.. dan bazan iya jurar rashinki ba ummi. ina sonki duk duniya nan banida kmr ki hakika kin raya zumuncin dake tsakaninki da mahaifiyata.
kin duba byn mahaifiyata domin nasan ko tana Raye da wuya tamin abinda kika min kin nuna min gata kinsa ban Yi kukan maraici ba.. takarasa mgnr tana kuka ummi ta yafito deeni da hannuta yakaraso ya zauna kusa daita tayi saurin goge hawayenta kana ta kamo Tafin hannushi ka bata hkr deeni....Ka Tausayawa rayuwarta har yanzu ina jin xeenat araina tmkr fareeda.. Ita kadai ke mayemin kurbin fareeda arayuwa.
ita kadai ke dabemin kewar fareeda a duk sanda hkn yataso min .....takarasa mgnr idanunta na fidda wasu ruwan hawaye.. jikin deeni a sanyaye yace first love tun jiya nake bata hakuri kwana nayi ina kiran wayarki danata Amman akashe .fisrt love nima abin atausayamin ne .ina bukatar tausayawarku ke da zeenat....
Nasani... Nasani deeni Amman Kasan mace tafi bukatar tausayawa akan namiji.
ummi ta hade hannusu gurin daya ta damke cikin Nata sosai .
atake zuciyoyinsu ya buga sbd tuno da rana da suka mallaki junansu amatsayin ma'aurata ranar da ummi tabasu amanar junansu tare da tabbatar musu da su din yan'uwan juna ne mafi kusanci da juna .
atare suka dago suna kallon juna kowanensu zuciyarsa cike da tausayawa...
muryarsa a raunane yace am very sorry zeenat.. I Din mean to hot you .
ummi ta saka baki kiyi hkr diyata... Duk nice silar cutuwarki denni bashida laifi komai. Ki daura laifi gareni zeenst nice na miki laifi bashi ba.
zeenat tashiga girgiza kanta tasa hannuta daya tana gogewa ummi hawaye muryarta raunane tace ummina na yafe miki ...nasan duk abinda kikayi kiyi ne sbd ni... Nasan ko diyar da kika haifa acikin ki irin kulawar dazaki bata Kennan .
ummi ki manta da wani abu makamancin wannan ya taba faruwa arayuwarmu wallahi wallahi ummi na yafe komai .
shima yaya na yafe mishi duniya da lahira Amman ummi akwai wani hanzari ba gudu ba.
Dan Allah kicewa yaya ya sawake min aurensa dake kaina tunda ni baya sona baya son farincikina.
bansan wani irin kiyayya yaya yake min ba wanda ya manta kowa da komai ya manta da irin rayuwar da muka gudanar a farkon aurenmu ya tsugunawa wata Mace agabana yana rokon taso shi ummi....
Idan har nacigaba da rayuwa aure dashi wlh ban kyautawa kaina ba ...
amman dan hakuri na Hakura da komai na dauki kaddarata nima zanje gaba nacigaba da rayuwata.....
Deeni yayi sororo tare da tsura mata rikitattun idanunshi yana kallonta cike da mamaki abinda tace.
ummi tayi gyaran murya tace mamana bazan takuraki ba sbd tun farko aurnku ma ban takuraki ba ballananta yanzu Amman da zakiyi hkr ki rungumi kaddararki dana nafi kowa dake cikin duniyar jin dadi.
burina ba wuce naganku kuna rayuwa tare ba . abinda bakusani ba batun yanzu nake son ganinku cikin inuwa daya ba.
Amman sbd sanin halin deeni danayi yasa naki hadaku tun farko ko lokacin dayazo min da zance aurenki naji matukar dadi Amman ganin ba sonki yake ba alokacin kawai yana son yin auren ne dan na matsa masa yasa naki amincewa .
Amman kikace kinji kin gani zaki iya...
Ahankali ummi ta meda idanunta kan deeni bazan takurata mata ba idan kaji kana bukatar matarka Kanason cigaba da zama daita.
kasan yadda zaka Shawo kanta idan km kasan bakada bukatarta arayuwarka sakar min abata.
domin abinda wani yagaji dashi yaga yayi masa tsufa shi wani yake so da dauki ganin ya mallaka.
deeni ya runtse idanunshi da sauri sbd jin haushi da takaicin zance ummi.
Ummi na mgn fadar hk ta Mike tsaye tabar gurin ta nufi dakinta tana goge hawaye .
bathroom tashiga ta zauna kawai tarasa abinda ke mata dadi.
zeenat ma zame hannuta tayi cikin nashi yana kallonta Tabi byn ummi.
a sikwane Yabi bayanta da wani irin kallo .
tana shiga dakin ummi ta fashe da wani sabon kukan sbd har lokacin tana jin mugun kaunar mijinta.
sonshi acikin jinin jikinta yake .rabuwa dashi babban tashin hankali ne gareta Amman zata dakewa zuciyarta ko zata samawar ruhinta salama sosai take kuka tana tuna rayuwarta acikin dakin datake yanzu.
da yadda abubuwa suka dinga gudana daya byn daya suna wucewa da yadda ta rayu da matsanancin kaunarsa batare daya Sani ba.
da yadda ya dinga jiyar daita dadin aure ta dinga jin dama lokacin zai dawo mata da ta sake sabuwar rayuwar me inganci.
ashe daman zai kara aure arayuwarsa shi yasa lokacin datace yayi mata alkwarin bazai mata kishiya ba yace a'a zeenat bani ne da rayuwata ba.
ban isa Na tsarawa kaina rayuwa ba.
Aure nufi ne na Allah idan Allah ya kaddaromin sai nayi.
kedai ki tabbatar da kin tsare min hakina .
babu mamaki idan kika tsaremin hakkina dake kanki ta yuwu gaba naki kara aure .
duk da babu yadda Allah baya juya lamarinsa.
tuno wannan zance nasa ya sake haukatata ta dinga kuka tana datasani arayuwarta.......
ahankali ta mike tsaye tana safa da marwa ...motsin turo kofar dakin taji anyi tayi saurin goge hawayen dake tsiyayowa daga idanunta batare data juyo ba.
ahankali taji an meda kofar an rufe alamun an shigo dakin.
jingina bayansa yayi da jikin kofor tare da rungume dukka hannuwasa akirjinsa.
ya tsurawa bayanta idanu kawai yana kallonta yayinda ahankali ya dinga jin wani irin tausayinta yana ratsa kowani shashi na gangar jikinsa hakika bata cancanci wulakaci ko sabanin hk daga gareshi ba a kullun yana yabawa da tarin kaunarsa gareshi.
cikin wani irin sayin Jiki yakaraso gareta ya rungumeta ajikinsa ta baya yana me juyo daita suna fuskatar junansu.
atare suka sauke ajiyar zuciya .
ya tallabo fuskarta da hannuwashi yana Kare mata kallo ya bakinsa ya tsotse bakinta muryarsa a matukar raunane yace ki bini mu koma gida zeenat mukarashe rayuwar aurenmu tare.
nifa bazan koma ba domin bazan iya cigaba da rayuwa dakai ba...... Daga yanzu kasawa ranka mata daya kacal gareka..no... no.. don't do this to me zeenat . kiyi hakuri please kishirya yanzu mu wuce tare.
ta girgiza masa Kai alamun bata komawa gidansa yin duniya yayi daita Amman taki amincewa ta bisa..
hk yagaji ya Hakura yabar gadan. Kai tsaye gidan big dady ya nufa ya duba yaransa ita kam nablah bai samu damar ganinta ba sbd taki yarda sukaga juna.
Hk ya koma gida ya shirya zuwa office.
koda ya dawo daga office gidan ummi ya nufa rarrashin duniya yayiwa zeenat amman tace Sam ya barta lokacin data aureshi bai matsawa rayuwarta ta aureshi ba Dan hk yanzu bata Yin auren ya sallameta kawai ta aure wani .
kmr ya mutu hk ya dinga ji alokacin datake fada masa hk..
a matukar fasace ya fito tmkr zai tashi sama .
ko gidan Big dady bai je dubo nablah ba. Ya wuce gidansa
dan yasan haukanta ya zarta na zeenat.
sai dai gabadaya bai da salamar zuciya .
Daren ranar da kyar yasamu bacci barawo ya samu nasarar daukarsa cike da matsanancin damuwa.
washegari zeenat gabadaya akwance take ta zube tayi wata muguwar Rama sallah kadai ke tadata koda ko abinci ta manta rabon data sakawa cikinta ummi tayi ta matsa akan ta saki ranta taci abinci Amman furrrrrrr taki.
Gabadaya komai ya cukudewa deeni guri daya takowani bangare babu sauki da sausauci gida da office baida natsuwa tafiya kawai yake Amman zuciyarsa tap take da damuwa da tsantsar tashin hankali da tunani mara misaltuwa.
daga office kai tsaye gidan ummi ya nufa yashigo gidan bakinsa dauke da sallama ummi kadai ya tarar tana zaune ta amsa masa tana kallonsa.
dan ramar tasa ta yau tafi ta kullun nunawa ahankali ya zauna tare da ajiye jakar system dinshi yace first love mun yini lfy.
lfy lau son ya aiki .
yayi dan jim sannan yace alhamdullahi kusan minti goma yayi zaune baiji motsin zeenat ba wanda abinda yasani ne matsawar ummi na guri dole ka isketa kusa daita.
jikinsa a sanyaye ya fito da system dinsa cikin wata karamar bakar jaka yasoma dudubawa yana son karasa tura sakwanni .muryarsa akasalance yace first love ina zeenat?
Ya fadi hk batare da dago ba.
Ta mike tsaye tare da bashi amsa tana sama yanzu ta tashi .
OK turo min ita first love .
koda ummi tasanar mata da sakonshi bata mutsa ba taxo a parlour ta sameshi zaune kan daya daga cikin kayatattun kujerun parlour'n ummi na alfarma system dinsa akan center tablet agabanshi yana latse latse jikinsa sanye cikin wani farin yadin volya fari kal me shegen kyau hasken yadin da kyawunsa, su suka tona asirin tsadarta kashim turaren nan nasa na yau da kullun yana nan. yacika gurin batare daya dago ya dubeta ba ya nuna mata kujerar zama da hannusa cikin harshen turanci yace have a sit.
ba mutsu jikinta a matukar sanyaye ta zauna kusan minti goma bai ce daita komai ba yanata danne dannesa ta dago idanunta tana duban agogon dake manne a parlour muryarta a sarke cike da matsanacin tsoro tace nifa gsky ina son komawa daki dan ina da abin Yi.
ya dago rikitattun idanunshi ya dubeta..ya lashin lips dinsa na kasa kana yace Kibani minti biyar local in kammala muhinman aikina.
Taja numfashi hade da kawar da kanta gefe .
ahankali ta sake kallon agogon minti biyar din tacika tana shirin sake yin mgn taga ya ture system din dake gabansa ya mike ahankali ya zagayo gefen datake zaune kafafunsa babu takalmi ya janyo wata yar karamar akujerar stood dake daf daita ya zauna ya rusuno sosai kusa daita har suna jiyo numfashin junansu.
Muzeenat........ ya Kira sunanta cikin laulausar muryarsa .
ta tsuke fuskasta sosai batare data amsa masa ba .
bai wani damu da yanayin yadda tayi ba yacigaba da mgnrsa.
muzeenat meyasa kika Xabi rabuwa Dani ki auri wani?
alhali nasan kina mugu mugun sona?
da sauri ta dago idanunta ta sauke cikin nasa gabanta ya buga da karfi take ta kawar da idanunta tace daba lokacin ban san ciwon kaina ba Amman yanzu gsky bana wani sonka.
Uhmmmmm ya sauke numfashi tare da yin murmushin yake.
nasan kin fada ne kawai sbd girman laifi da kike tunanin miki Amman in da gaske kin daina sona ki dubi kwayar idanuna ki tabbatar min da ba kya Sona ......
cike da rashin tsoro wanda duk daurace kawai ta aro tasanyawa jikinta ta Kalli cikin idanunshi tace yaya deeni na daina sonka.
bana kau... Yayi saurin katseta ta hanyar daga mata hannu tare da runtse idanunshi gam zuciyarsa na wani irin harbawa da suya muryasa a raunane tamkar zaiyi kuka yace naji na yarda kin daina sona Amman ki duba wasu abubuwa kafin kiyi tunanin barina na farko Ki duba rayuwar ummi bazata taba jin dadin rabuwarmu dake.
sannan mutane zasu zagene idan nabarki wasu ma sai Sun tsnemin akanki.
kiyi hkr ki dawo mukarasa rayuwarmu tare mu ingantata tare gidana bazai Yi hasken da nake bukata ba matsawar ba kya cikinsa .
zaman gidaka din me zanyi yaya?
ni ba da "da" ba ba samun kulawa daga gareka ba.
Ince ana hakurin zaman auren ne idan har ya'ya sunshiga tsakani.
, to ni banida ko daya atare da Kai gara kawai kowa ya Hakura .
na Kara gaba ko nima zan samu farincikin dana rasa agurinka takarasa fadar hk tana meda kukan dayaso kufce mata.
Zeenat zaki haihuwa Dani Jikina nabani zaki haihu Dani...
Zan haihuwa man nima na San da hk Amman bada Kai ba.
yanzu kinfi son kije ki aure wani ki haihu dashi bani ba..
Kina son kibarni kiyi rayuwa da wani na alhalin ina Raye?
OK kai kai ka iya aurenka a boye har da haihuwa ina Raye.
OK a she fa nice bazan iya yin hk ba Ko?
tabbas bazan iya aikata hkn ba alhalin da aurenka a kaina .
Amman ai zan iya rabuwa da Kai matsawar bana sonka?
ya sake runtse idanunshi gam sbd radadin furucinta dan ya tsani jin kalmar bata sonshi daga bakinta .
sai daya furzar da iska me gyaraye da zafi zafi kishi sannan yace dake zan gama rayuwata zeenat kece uwargidana anan Duniya km ina fatan ko alahira ki zama shugaban matana a aljanna .
ina bukatar mucigaba da rayuwa tare ke kadai kika kasan halina kika San yadda kike bi Dani .
duk wata Mace da zan kasance Daita abayanki take .
ki rigada kin sha gabanta takowani bangareni ta tabe baki wannan km matsalarkace.
matsalata ni yanzu nabarka nayi nisa dakai nayi maka Nisan da bazaka taba Kamoni ba.
ya kamo tafin hannuta cikin nashi yana murzawa cike tasasawa yace muzeenat dan Allah ki taimake ni.. wlh bazan iya rabuwa dake ba sbd ina sonki............... haka zaki tafi ki aure wani ki barni?
karka soma furtamin wannan kalmar yaya naso ka furta min ita tun ba yau ba Amman sai tsintarshi nayi abakinka durkushe gaban wata kana rokonta tasoka kana furta mata wannan kalmar dana fi son ji daga gareka ,batare da kayi alakari da ina gurin ba...
kiyi hkr ki dawo dakinki mucigaba da rayuwarmu Wlh bazan iya barinki ba sbd ina sonki.
Kabar soyayyarka zeenat tace batayi.
ka kara akan wanda kakewa na..blah wlh na yafe mata Kai dan wlh yanzu banasonka tuni ka Gama fice min arai gabadaya ya marairaice mata yana mammtsa tafin hannuta taga yana neman zube mata tun kafin yakarasa kasa tayi saurin tareshi tana juya masa Kai. kibarni zeenat sbd naga durkusawa nablah danayi agabanki shi yafi tsaya miki arai kibari kema namiki ko zuciyarki zata rage radadin datake miki akaina.
Wasu hawaye masu ciwo da radadi suka shiga zubo mata .
Kanta Kawai take girgiza Masa uhmmmmm uhmmmmm bazan taba lamuncewa da hkn ba yaya.... Bazan lamunci ganinka durkushe agabana ba........ Ni ni dai kawai aurenka yarigada ya fice min rai yayi wata irin zabura ya Mike tsaye wanda hakan yasa hantar cikinta kadawa.yashiga zariya adakin gumi na tsaftsafo masa ya dumkule hannushi guri daya ya cure sannan ya naushi iska.
yajuya ahankali jikinsa na wani irin kirrma ya dauki naurarsa me kwalkwaluwa bai sake cewa daita komai ba ya fice daga gidan..
nan ta zube kasa tana rusa wani irin kuka Amman bataji zata km zama dashi matsayin mijinta... Da daddare suna zaune ita da ummi .
ummi ke tmbyarta yadda sukayi da deeni bata boye mata komai ba tasanar Mata yadda sukayi dashi ummi tace mamana kiyi hakuri ki koma dakinki Allah ummi bazan iya cigaba da zama dashi bane .
Allah ya hada kowa da rabonsa ummi agabaki agabana agaban big dady yaya ya tsugunna gaban karamar yarinya yana kuka tasoshi... Alhalin nida muka dauki sama shekaru takwas da aure bai taba mafarkin furtamin ba....
niko me zai saka nacigaba da zaman aure dashi yaje can Allah yabasu zaman lfy da matarsa nima Allah yabani nawa mijin ummi ta goge hawayen dasuka zubomata a boye....
Duk wannan gurmin da ake nablah na gidan big dady batasan komai ba . kwana biyu nablah takoma gidan deeni wanda da kyar big dady yasamu ya Shawo kanta ta amince ta koma gidan da Zumar taje tashirya ranar lahadi zasuje gidansu gurin mahaifinta har shi.
Amman tana komawa gidan tana ganinsa ta tada balli ta sake tuburewa ta haukace masa agida tana kuka tace ko sama da kasa zata hade ko duniya zata nade koda zan rasa raina baxan taba zama agidan nan ba wallah kaji na rantse sai na barmaka gidanka km na fasa bar maka daya daga cikin ya'yana domin nawa ne ni kadai.
km da ya'yana zan tafi tunda ban yayesu ba .
ta tubure masa sosai deeni ya riko hannuta. tayi wani irin ihu hade da fixge hannuta cikin nasa ta kwasa aguje ta nufi hanyar get......... Zeenat dake cikin dakinta wanda zuwan Kennan kwasar abubuwanta na bukata ta fito sbd hayaniyar da tasoma cika gidan .
Deeni Wanda ranshi Yayi mugu mugun baci a matukar harzuke ya bi bayanta abinka ga dogon mutun tattaki yayi cikin sauri zaraf ya damkota xuwa gareshi tun bata karasa zuwa bakin get ba.
tirtirjewa tasoma Yi tana ya saketa Amman yaki sakinta sai daya shigo daita cikin gidan .
xeenat wace takarasa saukowa tabisu da kallo zuciyarta na tsananta bugawa .
ranshi a bace yasoma yaryarfa mata maruka masu rai da lafiya zuciyarsa na wani irin zafi da tafarfasa ya zaunar daita ta Mike tsaye zumbur tana watsa masa wani mugun kallo ka mareni an mareki .
ko zaki rama ne?
ahankali zeenat ta Juya ta tabar gurin ta nufi dakinta .
Dan yanayin yadda tagansu .
Ya taba zuciyarta har yasa ta dinga jin zuciyarta na wani irin suya kirjinta ya dinga bugawa da sauri da sauri ahankali tasoma karanto duk wata adduar datazo bakinta domin samun sausauci dan har lokacin babu abinda ya ragu a zuciyarta a game da kishin mijinta.
Nace zaki ramane ya sake ta dauketa da wani gigitaccen Marin dayasa har "dan" dake cikinta yayi wani irin juyawa da sauri ahaukace take saki wani ihun tana dubansa da mamaki deeni kasake Marina ta fadi hk tana nuna kanta.
Suna nan tsaye zeenat ta sauko ta raba ta gefensu ta wuce abinta.
Wlh sai Allah ya saka min .
Bai sanda haushin kalmarta da ganin zeenat ta fice yasake yarfa mata wani Marin ba yana nunata da yatsansa Muryasa a matukar harzuke ya bude bakinsa ya Kira sunanta nabeelah....
wace irin halitar mutun ce ke da baki da tausayi ?
wacce irin zuciya gareki da babu imani cikinta ?
wace irin zuciya gareki da baki yafiya?
kina son ki kasheni ne ....?
sai ga kwalla yasoma saukowa daga idanunshi da sauri ya juya mata baya yasoma mgn cike da sanyi murya matsayina da mukamina da shekaruna wanda akalla da nasamu haihuwa arayuwata da wuri da yanzu kusan ina da kamarki...
Amman duk na karyar da matsayina da girmana na durkusa miki gaban mahaifiyata gaban Matata sbd kawai nasan a miki ba daidai ba arayuwarki .
Amman duk kika kunyarta dasu.
muryata a hassale tace ai duk kaine kaja ya Ciro hanky acikin aljihun gaban rigarsa ya goge hawayensa ya juyo ahankali idanunsu suka sarke cikin juna kowanesu sai da zuciyarsa ta buga da mugun karfi gaske kawai taji ya rungumeta ajikinshi nabeeah ki taimakeni a sanda na durkusa miki ban damu da yanayin da kowa yagani ba nablah idan kin cire soyayyar Allah da manxonsa da mahaifiyata kece kike bayanta Dan Allah nablah ki taimakeni zan rike ki amana zan rikeki da kyau ki bani dama nayi miki alkwarin zan zama tmkr bawanki ta fixge jikinta daga nashi ni kabarni please nifa gsky bana jin zan cigaba da rayuwata da kai wani irin duba yake mata yana jin yadda kaunarta ke sake huda masa zuciya da bawa kowani shashi na gangar jikinsa.. Shr yayi kawai yana kallonta kafin daga bisani ya daga waya yakira sule direbansa byn yazo yace Kaita gidansu .
wani duba tayi masa kana tace ka bani ya'yana Dan wlh bazan barsu ba. Ai kinsa inda suke kije ki daukesu. Ka dai je ka dauko min su
banza yayi mata yayi tmkr bai ji abinda tace ba yana aika mata da kallon bata isa ba . ganin bashi da niyar bata yaranta yasa ta Mike ta fice abunta.
Sam bata ji wani tausayinsa ko kadan acikin ranta ba........
shi kuwa tana fita yashiga sintiri acikin parlour'n tsananin damuwa tayi masa yawa yarasa yadda zaiyi duk yadda yazaci zai shawo kan nablah da zeenat . abin yaci tura sai dai baya jin zai iya Hakura dasu.
hanyar dakinsa ya nufa. Cikin sauri ya kira wani direbansa yasa takalmi da hula ya dibi kudi masu yawa ya zuba cikin aljihun ya fita...........
Mmn sudai ce
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
🌈kainuwa writers association
(united we stand and succed our ambition is to entertain &motivate the mind of readers)
https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/
page 107
Kai tsaye gidan big dady deeni ya nufa jikinsa har tsuma yake tsabar tashin hankalin daya tsinci kanshi ciki.
gabadaya komai na duniya ya rigada ya tsaya masa cak , sai km taimakon Allah yake nema da zuba ido yaga ta inda sauki zai zo masa.
"murya a marairaice yakewa big dady bayanin abinda ya faru atsakaninsa da nablah byn komawarta .
da halin dayake ciki da zeenat .
" big dady ya numfasa yana sauke ajiyar zuciya sannan yace shikenan Bari na tashi mutafi yanzu gurin mahaifin nata daman naso abari mu hadu da sauran kawun nan ka domin muhada karfi da karfi muje , sbd rashin kyautatawar da akayiwa mahaifin yarinyar.
Ita kuwa zeenat kabarni daita Nata me sauki ne Inji Cewar Big dady. wanda oready yarigada yagama mikewa tsaye suka fito tare da deeni yace su biya su dauki mahaifin fk dana zeenat da ita ummin karankata ..
Hkn ce kuwa takasance big dady da kanshi ya sanar mata data shirya maza maza daita za'a je gidansu nablah.
Ummi tace zeenat ma ta taho suje tare motor ummi daban ita da yar gaban goshinta Direbanta adekule Najansu.
yayinda deeni da big dady da yaran duka uku suna cikin mota daya , mahaifin zeenat dana fk cikin mota daya
sai motocin escort dinsa dake biye dasu agaba da baya .
Deeni zaune akan kujera me zaman bazan agaban motarsa renge Rober ya dan kara karfin AC motor sbd wani irin gumin dake tsaftsafo masa ta koina ajinkisa.
anan rungume ajikinsa. ciro wayarsa yayi agaban aljihun gaban rigarsa yashiga dieling number sule .
Kira daya Sule direbansa ya dauka yana ambaton sunan boss cike da girmamawa .
deeni yace sule kuna daidai ina yanzu?
Bangaren sule kuwa cewa yayi muna daidai underbrige din oshodi express.
OK idan kun kai daidai ladipo kasan yadda Zaka Yi kujerani agurin ganinan zuwa yanzu OK boss .
deeni ya katse kiran Tare da ajiye wayar kusa da giyar motor .
gabadaya hankalinsa yayi mugu mugun tashi yarasa yadda zai Yi da rayuwarsa da yadda zai fuskancin mahaifin nablah da zance dayen aikin da yayiwa diyarsa..
Ya juyowa ahankali yana sauke naunaiyen ajiyar zuciya tare da bawa direbansa umarnin ya taka Motar sosai ......
big dady yace dan me zai taka mota sosai kmr ya dibo dabbobi.
sannan ya maida hankalinsa kan direba yace yayi tuki ahankali ..
nablah dake zaune a byn mota taga sule direba yana rage gudun motar da yake hade da gangarawa gefen titi ya Tsaya yana jujjuya kai alamun motor ta samu Matsala, ta dan gyara zamanta kana tace lfy baba sule naga ka tsaya?
Wani abu zan dan duba a motar yabata amsa da hkn .
taja bakinta ta tsuke batare da ta sake cewa dashi komai ba.
dan ita kanta hankalinta a matukar tashe yake da wannan ranar dazatakoma gidansu dauke da wani cikin wata shida da wani abu ...
Lokacin da su deeni suka kusan kawowa ladipo oshodi ya sake kiran sule direbansa yace yashirya gashi nan karasowa .
Suna wuce ladipo oshodi deeni ya sake kira sule yace ya biyosu abaya OK boss ai naga wucewar motocinku yanzu .
nablah tayi shr tarasa gane kan inda zance sule direba ya nufa kawai ta kawar da kanta gefen titi da kawar da zance dan gabadaya burinta bai wuce taganta acikin gidansu km gaban mamanta da babanta da yan'uwanta zaune ba.. Sunkai daidai iyana paja ta gane kmr tare suke da motocin deeni ranta abace ta juya bayanta aiko taga Motar escort dinsa abayanta tsaki taja kawai tare da hada uban tagumi...
Cikin minti talatin motatocin su deeni suka shigo unguwarsu nablah yayinda Jama'ar dake zaune akan layin unguwar kowa ya maida hankalinsa akan hadaddun motacin dake kokarin shigowa cikin geto area din tasu da kokarin son yin parking a akofar gidan mlm salisu me wanki hula .......
Cikin ikon Allah suka ci sa'ar samun mlm salisu me wanki hula akofar agidansa. Wanda yake ta faman kokarin yin alwala ba dan lokacin sallah yayi ba sai dan yin alwala akoda yaushe ya zamemai jiki.. .
Ahankali su deeni da Big Dady tare da sauran jama'a da suka zo tare ke kokarin fitowa daga cikin motor daya byn har suka gama fitowa gabadaya har nablah wace ta dan yi jimmmmmm kafin ta sanyo zara zaran yatsun kafafunta zuwa waje. Kana ta fito da jikinta.
aiko junior nayin arba daita ya nufi gurin yana murmushi sauran yan'uwansa ma suka marasa baya.
" yayinda mlm Salisu wanda ya kammala da alwalarsa dayake ya dago kanshi ahankali da zumar mikewa tsaye idanunshi karaf suka sauka akan deeni dake tsaye tare da wasu mutane wayanda bai san ko su waye ba .
Gefe daya km diyarsa ce nablah tsaye jikin mota yake kallonta zagaye da wasu kyawawan yara masu mugu mugun kyau da daukar hankali sak masu tsananin kama da deeni. Idanun mlm salisu kyam akanta yana kallonta a matukar tsoroce domin idan ba gitso idanunshi ke masa ba diyarsa yake kallo tsaye km kmr ciki ne ajikinta....... Ga km yara
ahankali mlm salisu yake kallon deeni da nablah da sauran mutanen dake tsaye cirko cirko da ya'yan dake jingine jikin nablah suna manne daita Ya sake kai dubansa ga Anan...... take yaji wata irin mummunar muguwar faduwar gaba from no where .........
tayi masa ruf da dubu aka .
Hankalinsa yayi maseefa maseefar tashi .
tunani kawai yake to meye yahaddin nasuruldeeni da nablah guri daya .
Dayaga ta fito daga cikin jerin motocin da suka fito.
shi dai asaninsa da yayi deeni gurinsa yazo ya nemi auren nablah batare daya tafi daita ba .
to ina nablah taje tasamo ciki km har da ya'ya har guda uku.... Wani irin tsoro ne me cike da tsansar frigici da fargaba yayi mugu mugun shigarshi ya dinga jin Wani Abu na taso masa yana hawa kanshi.
take yashiga addua acikin zuciyarsa hade da Kane abinda yaji yana tasomasa gabadaya mahaifin nablah ya kasa motsi daga inda yake itama nablah wacce sai yanzu hankalinta ya kai ga mahafinta gabanta ya shiga faduwa at the same time zuciyarta tashiga tsinkewa da harbawa.
deeni yayi saurin karasawa inda mlm salisu yake tsaye ya mika masa hannu.
jikin mlm salisu a matukar sanyaye ya bashi hannu suka gaisa sai dai har lokacin idanunshi nakan diyarsa nablah yana kallonta zuciyarsa cike da frigici.
murya deeni a kasalance yace baba gurinka muka tare da dagina.
Mlm salisu yayi saurin kawar da tarin damuwarsa .
sannan km take zuciyarsa tashiga Yi masa wasi wasi akan batare suke da nablah da nablah.
da dan hanzarinsa ya shiga cikin gida sannan ya dawo yayi musu iso ciki.
Byn sun shiga gidan aka gaisa zuciyar kowa cike da fargaba ..
mahaifin nablah ya boye tarin fargabansa hade da nuna matukar murnarsa da zuwan deeni big dady ya numfasa yace to deeni gamu a gaban mahaifin yarinya sai kayi masa bayani komai game da abinda yakawo mu Dan waka abakin meshi tafi me...?
Sauran mutane dake zaune agurin suka amsa da tafi dadi..
Jikin deeni yayi mugu mugun sanyi ya sake sunkuyar da kanshi kasa sosai wanda daman tun sanda yashigo parlour 'n kanshi sunkuye yake kana muryarsa a sanyaye a raunane yasoma bayani tundaga kan farkon aurensa da zeenat da labarin zubar masa da ciki da zeenat take Yi masa har zuwa kan yadda akayi aurensa da nablah da yadda asiri ya tono kowa a daginsa yasani har zuwa yau din nan dayake bashi labari.
Hankalin mahaifin nablah ya tashin kwarai da gaske zuciyarsa ta dugunzuma guri daya ta yunkuro abinka ga me zuciya..
ya Mike tsaye jikinsa na tsananta rawa tare da cewa Zance banza zance wofi.
"Zance banza inji mutane banza.
Oh ! byn kungama cutar min da yar kun mata ciki ga ya'ya har uku ta haifa sannan ga wani ciki.
shine kuka kwasota kuzo min daita.
to kuzo in muku me?
AI banida wani amfani yanzu ko ina dashi amfanina ya rigada yakare.
mlm Salisu ya meda idanunshi kyam akan deeni tunda da ina da amfani agurinka ko km kasan darajata da yadda kaxo ka aureta agurina kamata yayi ka dauketa ahannuna ba wai kaje ka rike min ita agidanka ba .
kayi mata ciki agidanka ta haihu ka sake dirka mata wani cikin ba.
Sam wannan ba adalci ne bane km wallahi azim nasuru baka min adalci ba yanzu yartawa ce tazama hk kmr a gidan magajiya nasamota ?
Ranshi a bace ya dinga zazzaga masa tujara iri iri wallahi nasuru kaci amanata.
" Domin bansaka ba ban San asalinka ba na amince maka har nabaka auren diyata.
a fusace yashiga nuna deeni hannushi yana nuna masa kofar fita ni maza maza ka tashi anan kabar min gidana bana ko son ganinka acikin idanuna na daukeka mutumin arziki mutumin kirki ban tsaya tmbyr ko kai waye ba.
na dauki yarta nabaka wacce ma acikin yayan nawa itace mafi soyuwa araina shine zaka min irin wannan sakayyar?
Daman da niyyar dakazo auren nablah Kennan dan ta haifa maka ya'ya?
Amman babu komai kaje kawai Allah ya ........ Kafin yakarasa deeni yayi saurin mikewa tsaye ya katse shi ta hanyar cewa dan Allah dan annabi baba karka min Allah ya isa.......nasan matsawar kamin Allah ya isa zata bini.... Sbd nasan nablah yarkace .
Dan girman Allah ka taimakeni karka min Allah ya isa kar ka Kai karata gurin mahalicina..
A matukar fusace mahaifin nablah ya furzar da wata iska me zafi me cike da tsansar tashin hankali mara misaltuwa idanuwanshi suka rine suka jawur ya cire hular kanshi tare da goge gumin dake tsaftsafo masa sannan ahankali ya maida idanunshi kan nablah yace Kalli yadda kika maida rayuwarki......abin kwatance kanki kika cuta bani ba duk abinda yasameki ke kika jawowa kanki.. Muna zaman zaman mu lfy bamu rasa ci ba bamu rasa sha ba bamu rasa gurin kwanciya ba .
duk da talaucina Allah ya rufawa min asirin da zan dubaku .
km da talaucin nan nawa dakika raina na rufawa sauran yayyeki asiri har suka rayu suka zama abin alfahari agurina har namusu aure Amman ke kika daurawa kanki buri da son kwadayin duniya wai ke a dole sai kinyi karatu me zarfi to yanzu wa gari ya waya.
karshe ga kaddarar abinda son karatuna nan ya fada miki nan..
GA kaddararki nan kin je a miki wulakaci abanza a wofi an wulakanta rayuwarki .
an dirka miki cikin da baki san ma kowaye ubansu ba.
" kika haifi ya'yan aka kara dirka miki wani cikin... Uhmmmmm kaddaraki Kennan da kika jawa kanki.
Amman bada kowa zanyi bakiciki ko nayi Kuka ba.
dake zanyi kuka yanzu da badan Allah ya yanke miki wahala ba da yanzu ahaka zakiyi tayin ciki kina haihuwa batare da sanin kanki ba ballantana mu iyayenki da kikabar mu cikin fargaba da tashin hankali dubi yadda mahaifiyarki ta dawo kalar tausayi kusan damuwarta har ta zarta nawa kullun zanceta akanki nabeelah kowa kika kalla agidan nan bashi da kwanciyar hankali..
Sosai ya dinga zazzzaga mata itama nata tujarar har ya kusan dukanta yayi mata gabadaya ranshi yagama baci idanunshi suka rufe wata irin jawowa yayi mata da tshon ciki mahaiifin zeenat ya kwaceta ahannushi.
shi km deeni gani aika aikan da mahaifin nablah ke shirin masa yasa hankalinsa yayi kololuwar tashi da sauri sauri zuciyarsa ta dinga dokawa tana bugawa da karfi.
mlm Salisu yace ku miko Mara jin mgn na sabautata na huta me zanyi daita.... Arayuwata.
yarinya ta dinga janyowa mutane maseefa da ciwon zuciya duk cikin ya'yana nafi son wannan shegiyar yarinyar da amincewa daita dabata yardata da amanata Amman Kalli abinda tajawo min tajawo kanta tuzarci banda a Gaban shedu da Jamar arziki na daurawa yarinyar nan aure da me mutane gari zasuce .
kinje an rike min ke har kika haifi yaya uku me kike son nacewa yan'uwa na da danging da abokan arxiki Dan wani ko ka rantse masa ba yarda zaiyi ba cewa zai Yi cikin shege tayi.
deeni yayi saurin runtse idanunshi dan shi kwata kwata ya tsanani jin wannan kalmar arayuwarsa.
idan kuwa akwai abinda yafi tsana nan duniya tana byn wanna kamal... Wallahi yau sai kin gane Taurin kai bai inda yake kai mutun sai nadama da danasani gara na kasheki na huta, daga ita har cikin dake jikinta....
Deeni fa yaga da gaske mlm salisu so yake yayi masa hasarar cikinsa .
ga km tarin mugun son dayake WA nablah na sake fizgarsa take yashiga bawa mlm salisu hkr yana karawa.
zuciyarsa kadan ta rage bata buga ba
hade da yin wani irin tsalle .
cikin kirjinsa sai luguden tashin hankali da fargaban abinda mlm salisu ke shirin Yi masa yake.
zuciyarsa ta dinga tafarfasa ranshi yayi maseefar maseefar tashin ya dinga jin jikinshi na wani irin tsuma tsabar tashin hankali yayinda nablah data fixge daga hannun mahaifin zeenat .
tayi byn deeni ta kamkameshi ajikinta tana wani irin kuka me ban tausayi tana kuka tana furta dan Allah ka taimakeni wallahi babanmu nada zuciya zai iya kasheni tunda yace zai kasheni zai iya kasheni ya huta.. Nasan halinsa zai iya kasheni tana kuka tana sake kamkame deeni ajikinta wannan ririkewar datayi masa ya sake jefa zuciyarsa cikin rudani da mawuyacin damuwa shi kansa afrigice yake da ganin yanayin mahaifin nata.
wanda tunda yake zuwa gurinsa bai taba ganin wannan sifar atare dashi ba .
Ahankali tausayinta da wutar sonta ke sake shigarsa da ingizashi .yayinda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da karfi... Sbd yadda take gogar jikinsa da nata jikin...
Ahankali big dady ya mike yana duban ummi da wani irin yanayi yayinda deeni ke ta faman aikine bawa mahaifin nablah hakuri shi km yana furta sai ya kasheta.
da bata bijirewa maganarta ba .
da bata kai kanta gidanka har kaganta kaxo yin *AUREN SIRRI* daita ba... Zuciyar mahaifin nablah fa ya dugunzuma ya dinga kokarin ture deeni ya fixgo nablah ..
a zafaffe ya dinga cewa nasuru ka miko yarinyar nan idan ba hk ba wlh har kai zan hada inyaso duk abinda za'a Yi ayi..
Big dady daya mike da kyar yace mlm salisu ka dubi girman Allah kadakata ka zauna miyi mgn..
Wannan mgnr da big dady yayi ita ta dakatar dashi daga abinda yake shirin aikatawa ko babu komai girman Allah da mutumin ya hadashi dashi da km ganin Girmansa wanda akalla shekaru zai kusan daya da kwatan nashi.. Shiyasa hankalinsa ya Dan dawo jikinsa tare da kokarin son sanyawa jikinsa natsuwa daga tsumar datake ba kaukautawa..
Sannan ahankali ya nemi guri ya zauna zuciyarsa na zafi da radadi yana huci zufa na sake karyo masa ta koina ajikinsa mahaifiyar nablah na kuka nuratu na kuka hatta yaran kuka suke ganin za'a dukar musu uwa .
Cikin sanyi murya big dady yace kayi hakuri mlm salisu ka yarda da kaddara datazo maka.
ka dubi girman Allah da cikin dake jikinta da km wayan nan ya'ya dake kuka kayi hakuri ka godewa Allah da wannan Abu daya faru da ya'yan data haifa da cikin jikinta ba'a titi ne tasamoshi ba.
aure tayi .
Aure km na Sunnan ma'aiki wanda kaine da hannuka ka daura shi.. Duk abinda Allah yakaddara bawa sai ya faru ..
km duk abinda Allah ya kaddara maka ka amsheshi da hannu biyu biyu.. Shine cikar imanin mutun.
Ka sake godewa Allah da nablah ba cikin shege tayi ba wanda hakan shine abu mafi muni gareka damu gabadaya..
Da Allah bai Yi hikimarsa ta zartar da aure tsakanin nasuru da nabeelah ba dafa tabbass sai an haifi yaran nan duka atiti wanda zuciyoyinmu bazai taba lamunta wannnan bakar maseefar ba .
amman alhamdullahi tunda abin nan ya faru nake godewa Allah da ya'yan nan ya'yan sunan ne.
ba shegu bane .
idan ya'yan gaba da fateeha ne idan km cikin shege tayi me zakayi?
yaza'ayi dole dai hakurin nan zakayi har gara yanzu ma kana da hujjar Kare kanka da bakin mgn acikin jama'a.
Kai kmr ba babba ba ina hankalinka da tunaninsa suka je ai idan rai ya baci hankali ke nemoshi ka tuna akwai yarda da kaddara acikin cika cikan muslinci mai Kyau ko mara Kyau.
soaai big dady shima ya dinga bashi baki har zuciyarsa ta dunga kasa tana lafawa da yin sanyi ahankali big dady ya dinga masa nasiha zuciyarsa tayi sanyi sosai Amman duk da wannan nasihar da big dady yayi masa bai hanashi mikewa tsaye yace naji km nagode sai dai bazan taba karbarta ba takoma can inda tafaro rayuwarta tayi cikin har ta haihuwa batare da sani ba.
Ba munyi alkwari dake ba akan wata uku zakayi ki dawo gareni ba ?
Nablah ta girgiza masa kanta...mlm salisu yacigaba Kana ganin yarinyar nan sbd auren dana mata bada saninta ba yasa lokacin data rokeni akan nabata wata uku zata je gurin aikinta ta dawo nabata bisa ga kyautatawa Amman shine tayi zamanta sai data haihu ta dawo min da wani cikin dayake makira ce ita..
Km tasan abinda tana son shuka.
nabeelah shi kanshi mijin daya zagayo gurina aureki km ya dinga zagayawa yana miki ciki kina haihuwa dame zai daukeni ?
tunani ma zai inda ace bashi ne yayi miki cikin ba hk zan km daukarki da ciki na bashi .
nabeelah kin cuci kanki kin zubarwa da kanki da mutunci da kima ki bari azo gurin mahafinki aureki akai ki gidan mijinki kmr yadda akewa kowa ce budurwa me mutuncin da kimarki da daraja Amman kika cuci kanki .
sbd da baki bijirewa mgnta ba, kin zauna lokacin dana ce miki karki sake kije koina da bai ganki ya zagoye ya aureki agurina da wata manufa ba.
nablah na wani irin kuka ta rarrafo zuwa gurin mahaifinta .
Tana kuka mlm salisu yace wacce irin ya Mace ce me mutunci da daraja da kamun kai zata aikata irin abinda kika Yi domin cikar burinta ?
Tana kuka tana girgiza masa Kai alumun babu kana muryarta cike da kuka tace wlh baba bansan komai ba ...ban San komai ba akan cikin jikina da ya'yan dana haifa ni kaina wayar kaina nake nagani dashi dan Allah babana kayi hkr ka yafe min bazan sake kinji mgnrka ba duk abinda kace nayi shi zanyi bazan sake sabawa umarninka ba.. tana kuka tana rokonsa furzar da iska yayi yana girgiza Kai .
zeenat tayi shr tayi zugun azaune tana kallon ikon Allah yau ga talaka me zuciya tagani .
Ashe daman talauci bayasa mutun ya kaskanta da wulakanta yazamo Mara galihu?
A she daman talauci bayasa mutun ya
tozarta kanshi?
A she daman talauci bayasa mutun ya daydayta yazamo abin tausayi ?
A she talauci bayasa mutun yazama kasasshe har zuciyarsa ta mutu.
Tasashi jin bazai iya kwatarwa kansa yancinsa ba ?
A she talauci bayasa mutun yazama me matacciyar zuciya km Mara zuciyar kanshi.
Yau ga deeni me tarin arziki tsohon retaya soldier me tarin camfanoni da tarin dukiyar da shi kanshi bai san adadinsu ba .
tsaye GAban wani wulakantaccin talaka me wakin hula yana masa fada da maseefa har da rantsuwa..
Yau ga big dady shugaban plant nuwaun rows family estate shugaban dagin gabadaya na nesa dana kusa ya zauna a gidan talakan dako inda me gadinsa ke rayuwa yafishi daraja Amman ya zauna yana masa tujara yana rokonsa dan Girman Allah yayi hakuri ajiyar zuciya taja da karfi zuciyarta ta sake yin ladab akan rayuwar duniya sai lokacin km tasan lallai ba komai kudi ke wa mutun arayuwa ba..
Hk kazalika ba komai kudi ke sai maka ba lallai akwai talakan dayafi me arziki zuciya da tunani .. Atunaninta yadda motocinsu suka shigo unguwar da yadda arxiki ya nuna ajikinsu yaci ace ko tarin kirki mahaifinta bazai ba akan mgnr da suka zo masa daita Amman sai gashi ya dage iya karfinsa da gaskiyarsa yana surfa musu tujara..
Hk ma ummi tunanin datake Kennan Ashe tagudu bata tsira bane datace a auri yar talaka Mara gata da galihu kaskantacciya. Ashe baban nablah ba kaskantacce bane Mara galihun datake tunani mutun ne sak me zuciya ba wanda za'a iya cin galaba akanshi bane domin yadda take kallonsa a irin wannan zuciyar tashi ko shara'a zai iya Yi dasu duk kudinsu.
lallai yau tagamu dagamonta.
aranta ta dinga jin idan baban nablah me arziki ne da basan me za Yi ba. tana cikin wannan tunanin nata na wuncin gadi mahaifin nablah ya gyara tsayuwarsa sosai yace yanzu sai ki Mike ki bisu ku koma inda kuka fito tare .
da son kokarin barin gurin mahaifin zeenat yayi saurin tararsa ta hanyar shan gabansa yace Dan Allah kayiwa iyayenka ka sauraremu. Mahaifin nablah yace ku daina hadani da Allah da iyayena akan cutar da'aka min kana ganin abinda nasuru danku yayi min kana ganin irin yaudara da cin amanar da nasuru danku yayi min wasu irin iyaye za,a yiwa irin hk a wanna duniyar da muke cike su lamunta ?
.Da kyar da Allah da big dady aka samu aka shawo kanshi har yazo ya km zama .
itama ummi jikinta a sanyaye tashiga bashi hakuri tare da ce masa wlh duk wannan laifina ne sannan kuskurena ne ba laifin deeni da nablah bane .
asalima nabah batasan komai ba kmr yadda tagaya maka domin kuwa batasan deeni na kwamciyar aure daita ba sbd magani yake mata amfani dashi kafin komai ya wakana a tsakaninsu sosai ummi ta dinga vashi hkr akan Abunda daya faru.
sannan km tace yayi hkr ya yafewa nablah batada laifi komai idan ma akwai me laifi to itace babbar me laifi domin itace silar komai.
hatta zeenat ma da jikinta yagama yin sanyi da lamarin sai data saka bakinta gurin bawa mahaifin nanlah hkr Takara yarda da sanin Duniya da abinda ke cikinta ba komai bane ta dinga tunanin matsayi na big dady da deeni da sauran mutane dake zaune agurin Amman gabadaye kowa hkr yake bawa mahaifin nablah jikinta yayi mugu mugun sanyi ta bude baki tace Dan girman Allah baba kayi hkr ka yafemana gabadayanmu dukkaninmu masu laifi ne km masu kuskurene ko agurin Allah Amman kayafe mana Dan Allah.
Deeni ma ya matso sosai yace baba munayiwa Allah laifi ubangijin daya halicemu yabamu ci da sha yabamu lfy sannan km yabarmu da rayukanmu km muyi masa laifi km rokeshi yafiya ya yafemuna sosai deeni ya dinga bawa sirinkin nasa me kafiya da daurin zuciya hakuri yayinda nablah dake durkushe tana kuka .
ta rike kafafuwan mahaifinta tana fadar babana ka yafemin sau daya tak nasan nataba Saba umarninka aduk tsawon rayuwata Amman Kalli yadda rayuwata ta dawo baba?
idan ka cigaba da fushi Dani bansan yadda rayuwata zata dawo ba. ta dinga risgar kuka tana rokonsa yafiya gabadaya jikin mlm salisu ya sake yin sanyi sosai .
nuratu da mama mahsifiyar nablah suma kuka suke suna nabashi hkr muryasa a raunane ya dubi gabadaya mutane gurin yace shikenan na Hakura na yafe mata....
take hankalin kowa dake gurin ya kwanta.
take Kuma mlm Salisu ya bugawa Manyan ya'yansa waya da wasu daga cikin danginsa na nan kusa waya sannan yakira waliyan da suka daurawa nablah aure.
duk akazo aka hadu da dattawan unguwa har yayyenta da kannanta da aunty Salma .
Amman mlm salisu bai fito ya gaya masu gaskiyar lamarin ba sai yayi musu karyar cewa tun sanda aka daura auren.
deeni yazo daga baya ya dauki matarsa Amman sbd wani dalili yasa bai fitO ya sanar wa kowa ba sai yau din nan gashi nan har sun haihuwa ga MA wani cikin nan ajikinta ga danginsa nan....
To byn yan unguwa Sun fita .
sai yagawa daginsa da ya'yansa gskyr ainihin abinda ya faru nan dai aka sake neman yafiyar juna aka yafewa juna sosai .
byn komai ya natsa mahaifiyar nablah tace dan Allah abar mata nablah zuwa wani lokaci har ta haifi cikinn jikinta zuwa lokacin hankalinta zai kara kwanciya.
da kyar deeni ya yarda ya amince da barin nablah agidan Amman banda yaransa .
bai samu damar kebewa da nablah ba Suka koma gida zuciyar kowane cike da farinciki Amman banda zeenat wace duk da abinda ta dinga Yi karfin hali kawai take Tana addur samun saukin abinda ke tasomata akan mijinta..........
Sannan ta wani bangaren km zuciyar cike take da jimami da tsantsar tausayin mijinta ta koma gida.
Ko kadan xuciyarta ta kasa samun sukuni tunanin shi kawai take km tana matukar tausaya masa sbd ganin irin soyayyar da yakewa nablah acikin kwayar idanunshi..
Abun tausayi ita data taso marainiya ta rayu da tarin kaunarsa cikin zuciyarsa ita tafi cancanta yaso fiyye da komai baki kadai bazai iya furta adadin kaunarsa gareta ba hk xuciya bazata taba misalta yadda take jinsa cikin jini da jikinta na.
ita tasan da tarin soyayyarsa zata mutu Amman ba komai zata tsaya daidai matsayinta da jajircewa akan rayuwarta wasu hawaye ne masu dumi suka sauka akan kyakyawar fuskasta.
Jin motsin shigowar ummi da muryar anan yasa tai Yi saurin goge hawayen fuskasta tashige bathroom wanka tayi hade da dauro alwala gabadaya ta fito tana goge gashin kanta da gudu anan tazo ta rungumeta tana mata mgn cikin gwarancin mgnrsu ta yara aunty ina kika Shiga tun dazu?
wanka nakeyi my ummi Bari na shirya sai muje muci abincin ko .
zaunar daita tayi kafin ta fara shirinta tasoma shafa mai a lallausar fatar jikinta kafin ta shafa powder ta km gyara gashin kanta tasa ribon ta kamasa atsakiyar kanta ta feshe ilahirin jikinta da sanyaya turare me dadin kamshi kana ta dauko doguwar riga meflay har kasa anan na zaune tana kallonta.
suna hada IDo zeenat ta sakar mata murmushi ta cikin mirrorw tana me juyowa ahankali hannuta rike da kwalbar turaren tace ya'akayi ummina anan tayi murmushi siraren hakoranta wayanda suka fara fitowa suka bayyana. zeenat ta gyara mata jikinta da kanta itama tare fesheta da turare sannan ta dauke ta sabata akafa suka nufi parlour'n ummi Kai ta janyo haidar da junior zuwa dining area tasoma da hadawa yaran tea tana basu daya byn daya ummi dake tsaye tana kallonsu ta lura tunda suka dawo daga gidansu nablah yanayinta ya sake sauyawa zuciyarya tayi rauni, da alamun zeenat dinta ta soma canzawa koma tace ta canza gabadaya sai faman jan yaran take jikinta ummi takaraso ahankali xuwa inda take zaune .
ta zauna kusa daita tana dubanta sosai ita da yaran gabadaya tausayinta yakamata ta dinga addur Allah daidaita tsakaninta deeni yasa takoma dakinta tasamu nata rabon ya'ya muryar ummi a raunane tace manana yakamata ace kiyawa kanki fada Ki koma gidan mijinki kizama tsohuwar gidan sai dai akwai Abu daya da nake son ki fahinta a yanzu .
ki kiyaye sharin zuciya sannan ki rage wannan sakarcin naki ki tsaya ki kula da rayuwar mijinki fiyye da yadda kike Yi abaya .
zeenat ta hadiye abinda taji ya tsaya mata arai tasoma cin abinci batare datacewa ummi komai ba Har tagama cin abinci fada da nasiha ummi ke mata byn tagama ta mike tsaye tana shirin barin gurin ummi tace mamana bakice komai ba game da komawarki dakinki ?
Muryar a matukar sanyaye tace ummi sai nayi tunani tukun bazan koma inda baa san mutuncina da kimata ba. Sannan ta saba anan akafadarta suka Koma kan kujeru suna kallo.....
Daren ranar zuciyar deeni fessss yayi bacci sai dai cike da tunanin matansa yayinda ya dinga ganin kima da mutuncin abinda zeenat tayi masa agaban mahaifin nablah tana kulawarta gareshi duk da yasan zuciyarta cike da jin haushinsa. Yasan irin maccen datakasance agurinsa ba kmr kowace Mace bace Tana sonshi tana sadaukar da farincikinta gareshi sosai ya dinga tunaninta yana bata matsayi me girma acikin tsokar dake makale da zuciyarsa.
Washegari da kuzari ya tashi byn yayi wanka cikin shirinsa na zuwa office ya fito ya nufi gidan ummi escont dinsa na biye dashi abaya .
agidan ummi yayi breakfast Haidar da junior zagaye dashi suna zuba masa surutu tubda bai ga anan ba ya tabbatar tana gurin zeenat dan tun jiya ya lura da yadda take makale daita.
har yagama break bai ga saukowar zeenat ba Dan hk yana kammalawa bai tsaya tmbyr ummi ba ya nufi dakinta kai tsaye ahankali ya tura kofar yashiga cak ya tsaya yana Kare musu kallo gabanshi na wani irin faduwa sannan yana jin wani bakon alamarin atare dashi dan ganin Anan rungume ajikin zeenat tana faman Yi mata murmush da alamun biyewa Shirman yarinyar take .yayinda jikinta sanye da doguwar rigar bacci me shara shara wanda bai boye komai na jikinta ba take ya dinga reaction dinsa na sauyawa duk kwanakin nan amatse yake Amman tashin hankalin dayake ciki ya girmame bukatarsa.
ko kadan zeenat bata wani damu da tsayuwarsa ba agurin duk da taga shigowarsa km tun lokacin daya shigo hankalinta ke kansa kirjinta na wani irin bugawa Amman tasharesa tacigaba da biyewa Anan kawai.
ahankali yacigaba da kallonta yana takowa zuwa inda suke zuciyarsa cike da tsantsar soyayyarta gareshi .
barin yadda yazo yaganta rungume da anan hkn bakaramin faranta ranshi yayi ba.
yasan ta nuna masa tsantsar kauna da tausayi hade da sadaukarwa soyayya .
stood din dake ajiye agefenta ya janyo ya zauna idanunshi akanta yanaciga da kallonta.
gabanta na wani irin dokawa ta dago idanunta tana kallonsa anan tayi saurin fadawa jikinsa tana kiran dadyna zan sha shuwet ...ya rungumeta ajikinshi yace sweet km mamana da sanyin safiyar tace uhm yace OK let me true with your aunty tare da sanyata atsakiyarsu .
shi km yana me fuskasta zeenat da wani irin sanyayen kallo gbadaya ya kashe mata jiki da kallonsa har takasa dago idanunta muryarta asanyaye ta bude bakinta tace yaya ina kwana... wani irin kallo ya jiho mata batare da ya amsa mata ba.
ta sake maimaitawa a tunaninta bai ji bane duk da tana da yakinin yaji Amman taji sai idanunshi dataji yana mata yawo a sansar jiki.
ta dago idanunta asanyaye taga still ita din yake kallo .
idanunshi cike da mamakinta yadda yaga yanzu gabadaya ta canza biheviours dinta akanshi tana hira da kowa da sakewa da kowa acikin gidan shi kadai ta canzawa ..
batason kebewarsu tare sannan bata wani daukin son ganinsa ko nuna damuwarta dashi wanda da ba hk take masa ba.
cikin sanyin jikin nasa ya kamo tafin hannuwanta duka cikin nashi yana murzawa ahankali yana kare mata kallo
Kana muryas a kasalance ya Kira sunanta..
zeenat meyasa kike son tarwatsa zuciyar masoyinki?
Meyasa kike son tarwasa rayuwarmu....?
duk ma ba wanna ba na Lura atsakankanin wannan lokacin kin sauya Hali zeenat kin canza kwata kwata bansanki da taurin kai ba ballantana dagon fushi akan abu.... Meyasa kika kasa hakura da laifin dana miki.
kinki komawa Gidana alhalin km kince kin yafemin.....?
Narasa gane kanki da gindinki zeenat yanzu har takai ta kawo har suna kin canza min na tashi daga zuciyarki na dawo zuwa yaya.... Wanda rabon danaji hk abakinki tun kafin muyi aure dake sai km cikin wannan hatsaniyar kika dawo da kirana da wanna sunan ....... Sbd kawai Yanzun kin daina sona ko..?
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
🌈kainuwa writers association
(united we stand and succed our ambition is to entertain &motivate the mind of readers)
dedicated to
Hauwa A usman
jiddarh
Page 108
Ya tsura mata rikitattun idanunshi kawai yana kallonta tare da jiran jin abinda zatace masa yayinda km ahankali wutar sha'awarsa ke sake tasowa tana kokarin bawa kowa part na gangar jikinsa circulating . naunauyen ajiyar zuciya ya sauke ahankali .
tare da sake sanyaya muryarsa .
Yace I've been talking to you and you're not replying me , plz talk to me, now zeenat.... so that I'll ve peace of mind still shr tayi masa taki cewa dashi komai wani irin lugude da harbawa xuciyarta keyi har jikinta na shaking domin Kalmar ta daina sonshi din daya Ambata tayi matukar mugun girgiza zuciyarta da raunana ilahirin jikinta cikin wani irin salo yacigaba da murza tafukan hannuwanta cikin nashi yana sake tsareta da rikitattun idanunshi Masu saurin susuta mata gangar jiki da zuciya .
ganin yadda yanayinsa yasoma sauyawa zuwa wani babin bukatuwa gashi itama yanason tada mata tsumin nata sha'awar ,yasa tasoma kokarin zare hannuta cikin nashi tana fizgo numfashi da kyar" Amman ina da sauri yayi saurin riko yatsun hannuta guda uku ya tsura mata idanunshi. Ido cikin ido suke kallon juna.
Ahankai ta tattaro jarumta ta sanyawa jikinta muryata a matukar raunane tmkr wacce zata zubda kwalla tace yaya... Kayi hkr please ka barni bana son kusancina da kai ahalin yanzu .
kai ko kebewa tare da kai banaso ina son nisanta kaina daga gareka bana bukatar wani abu ya sake shiga tsakanina da kai....gabadaya Ina son na mantaka aduniyata Sannan km tabbas mgnrka babu karya cikinta hakika muzeenat ta daina sonka kmr yadda Kake tunani.
dan me zeenat zata zauna da mutumin da bai sonta bai kaunarta bai son farincikinta da walwalarta arayuwa sannan mgnr na canza maka suna na daina kiranka da zuciyata sau nawa Kana min gargadi da kashedi akan hk akan na daina kiranka da zuciyata ... hkn bai taba damuna ba sai kaine yanzu kazaji babu dadi aranka dan na daina ... Ka rigada ka gama fice min arai ba km zan koma gidanka nacigaba da zama da kai alhalin zuciyarka naga wata ba .... Kawai ni ka sakeni na hutawa Raina kaima ka hutawa rayuwarka mubar junanmu mucigaba zumunci dake tsakaninmu kawai ya ishemu.
" ahalin yanzu idan na tuna da wahalar dana sha a zama da kaina ina jin tamkar na mutu nabarka a doron kasa kacigaba da rayuwa da wacce tafini daraja agurinka .
duk da tarin abubuwan da Ka dinga min ina hadiyewa hk bai isheka ba yaya sai dakaga ka musgunawa zuciyata ta hanyar quntata mata.
ni dai na rokeka da girman Allah kamin afuwa ka sauwakemin aurenka ......
"muryarsa a kasalance tmkr zai Yi kuka yace ki min afuwa zeenat wlh bazan taba iya sakinki ba sbd son da Nike Miki ,Amman na yarda ki Xabi horo me tsanani wanda kike ganin yafi kowane horo wahala ki min shi na yarda Na amince in dai zaki janye mgnr saki.
ki koma gidana ....
bai gama rufe baki ba ta dakatar dashi tace wazaka yaudara ni?
Ta nuna kirjinta da Danyatsan hannuta tana sake kallon cikin kwayar idanunshi sosai wallahi ko kadan kalamanka bazasu taba tasiri acikin zuciyata ba har su sanyaya min raina .
ba .
waye zai yarda ya dangwama cikin damuwa da wahala da bakinciki rayuwa?
Kalli yadda nazama yaya .......
nice fa wannan muzeenat din da Nke ji da kaina takowane fannin kyau kwaliya diri uwa uba asali da nasaba me kyau Amman na zama abar wulakantawa agurinka bisa ga kuskurena danayi maka ..
ni wani irin hakuri ne ban baka ba Akan kuskurena gareka ?
Wani irin azabtarwa ce bakamin ba
Yaya.
hk Ka Rufe idanunka ka min abinda kagadama batare da kula da wahalar dana sha ba gurin fitar cikin kansa. shine ni yanzu Kake wani bani hakuri nakoma gidanka nacigaba da zama da kai ka Karasa kasheni ko?
.
" ni nasan ko mutuwa nayi alhalin yanzu baka da hasara yaya kana da me mayye maka gurbina koma nace wacce tafini da komai agurnka ni dai alfarma daya kawai nake son kamin wanda bai wuce ka Sak.....a zabure ya mike tsaye tare da katseta yana aiko mata da wani irin kallo yana Huci.wanda sauran kadan anan ta fadi yayi saurin tarota jikinsa kina hauka ne wai ko kuwa
kinsa abinda kike fad?
Wannan wace irin maseefa hk? Sai lallabaki nike kina botsarewa
laifi na miki na km baki hakuri .
kince na tsugunawa wata Agabanki nace inasonta wanda nasan shine Abu mafi muni gareki wanda kike tunani na Miki kema km nace zan durkusa miki kince A'a nace ina sonki kin maida abun shirme to mekeke son na miki?
na kashe kaina nabaki shine zai Tabbar miki da ina sonki ko me ..?
kinsa Allah idan MA Zaki Hakura ki koma gidana ki koma idan km bazaki hakura ki koma ba fine kiyi tazama Saki ne dai ko zaki mutu bazan taba sakinki ba sai dai ki mutu da aurena akanki .
Ince gidan nan ma shima tmkr matsayin gidana ne, kicigaba da zama acikinsa har randa kikaji zaki dawo gareni ni km wlh zanbaki mamaki fiyye da tunaninki yana gama fadar hk yasa hannu ya dauki Ana ya rungumeta akafadarsa juya fuuuuuuuuu .
yana zuwa kasa ya ajiyeta a gefen ummi tare da yiwa ummi sallama ya wuce office ..
Da rana byn zeenat tagama baccinta ta tashi tayi wanka tasa sabon dinkinta wanda laraba ta karbo mata tasha kwalliya bazaka taba tunanin akwai abinda ke damun zuciyarta ba.
ko tana tattare da damuwa ba sbd hadiye damuwarta.
tayi fess daita simple make up tayi shima abinda yasa tayi dan sbd ya rigada yazame mata jiki ne yin kwalliyar if not bazatayi ba.
ta sauko parlour 'n kasa hannuta rike da pos taciro kudi tabawa laraba kudin cefane tare da bata instroction din abinda zata tsiyo mata sbd sakwara take son ci yau nan dana laraba ta shirya ta fita cefano musu kayan sakwara da miyar agusi hade da busasshen kifi.
tana zaune Wayarta ta dameta da karar shigowar massage's tana daukar wayar tasoma cin Karo da zafaffan sakwanin mijinta wanda gabadaya sakwanin ban hkr ne da yadda yake sonta cikin harshen turanci kanta yayi mugu mugun daurewa ta sake tsurawa wayar ido tana kallon text messages dinsa tabbas sakonnin mijinta ne take gani daki daki take sake Bin text din tana karantawa sororo tayi taji tmkr amafarki take ganin dubin kalaman ban hakurinsa gareta.
tmbyr ta anan yaushe Ne deeni yasoma sonta irin hk?
Km abin mamaki ta yaya zuciyarsa ta Yi saurin saukowa domin tasan da fushi ya bar gidan wanda aduk lokacin da yayi irin wannan fushi hk yana kwana da kwanaki bai sauko ba .
wani lokacin ma sai itace zatayi ta binshi da rarrashi sannan zai Hakura .
sosai taji dadin hkn aranta sai dai km abun bai wani birgeta ba ko dadata da kasa ba.
yayinda a bayyane km tace ka hadu da wahala deeni domin wlh kaima sai kasan kimata da darajata ta diya Mace sannan ko zankoma gidanka.
ahankali ta dinga bin sakonin nashi tana gogewa daya byn daya Cikin farinciki ta wuni ranar zuciyarta fess cike da tsantsar soyayyar mijinta ita kanta tasan bazata taba iya rayuwa babu shi ba .
shine duniyarta rayuwarta.
duniyar da babu deeni cikinta, rayuwace me tattare da damuwa da kuncin rayuwa wanda daga karshe tasan zuciyarta bugawa zatayi ta mutu .
Zaune a office dinsa yake amman gabadaya zuciyarsa cike take tap da tunanin zeenat da mamakinta iya gaskiyarta fa yake hangowa acikin kwayar idanunta tabbas zeenat tazabi rabuwa dashi ta aure waninsa zeenat me sonshi da nuna masa kulawa ada ta daina sonshi zeenat wacce ki fargaba da tsoron gaya masa mgn ada Amman yanzu gabadaya babu wannan tsoron shi kuwa ko sama da kasa zata hade bazai taba sakinta ba... Jikinsa a sanyaye yasamu ya dinga cike file files din dake zube bisa makaken table din dake zagaye dashi yayinda lokaci zuwa lokaci yana dago idanunshi yana kallon agogon dake manne a jikin bangon office din wani time km ya dauki wayar ya tura mata text ahaka dai har yasamu ya kammala tarin ayyukan dake gabansa daga office kai tsaye gidansu nablah ya nufa...
A k'ofar gidan su Nablah yayi parking din hadaddiyar motarsa Dan bai Bari escort dinsa sun biyo shi ba ya fito, cikin takun nan nasa me cike da daukar hankali waige waige ya fara yi yana neman yaran dazai aika,zuwa cikin gidansu nablah Abba k'anin Nablah ya gani ya fito,Da gudu daga cikin gidan yana tsale ..
kiransa Deeni yayi, Abba yazo da sauri yana gaida deeni fuskarsa dauke da murmushi Deeni ya kalle shi yace yauwa Abba" Baba na ciki?
"Eh Abba yace, " OK yi min sallama da shi, juyawa Abba yayi, yakoma cikin gidan tare Abba da Baban Nablah suka fito,.
" har falo Baba yayiwa Deeni iso, yana ce masa " kaima ai d'an gida ne yanzu ka daina tsayawa daga waje,inda kazo murmushi Deeni yayi hade da durkusawa har k'asa ya gaida iyayen Nablah.
, fita Baba yayi da kansa ya kira masa Nablah, da sallama ta shigo d'akin ta nemi waje ta zauna nesa dashi kadan tana me had'e fuskarta tamau
, ido ya k'ura mata yana kallonta tayi masa kyau sosai tayi fresh da ita da gani hankalinta a kwance yake bata da wata damuwa.
, ganin bata da niyyar yi masa magana balle ta gaida shi yasa shi had'i rai ya kawai da kansa gefe, shima ya basar da ita, yaciro wayarsa yashiga internet kusan minti 30 suna zaune babu wanda yacewa dan'uwansa ko kala sannan ganin Da yayi bazata yi masa magana bane idan bashi yayi mata ba .
ya sashi mik'ewa a sikwane ko sake kallon inda take bayyi ba yace " idan kina da buk'atar wani abu kiyi min text bai jira mai zata ce ba yayi gaba abinsa aranshi kuwa yace ni za'a Shawa kamshi gidan kika zo yarinya da sannu zan sa ki shiga hankalinki ki gane kuranki kisan ba'a yiwa maza irinmu wannan salon iskanci sannan km ya Yankewa kanshi cikin ita da zeenat babu wace zai kara lallasa ko ya bata hakuri .
Ganin yadda Deeni ya nuna halin ko in kula a kanta ne yayi masifar d'aga mata hankali, tsoro da fargaba suka durar mata lokaci d'aya, take zuciyar ta ta bata karfa garin jan aji ajin ya tsinke yabarta da wahala karfa Deeni yazo ya daina santa har ya kai ga yayi zuciya ya sake ta.
, aiko take gabanta yayi wani irin muguwar fad'uwa da karfin gaske har dan dake cikinta ya motsa da sauri tasa hannuta ta dafe inda taji baby ya cure guri daya, kirjinta ya shiga bugawa da k'arfi, fashewa tayi da kukan da ita kanta bata san kona menene ba,
Daren rana deeni yaje gidan ummi aka kawo mishi sakwara da akayi yaci Sosai yayi nar.
suka shiga hirar duniya da siyasa da ummi zeenat na zaune ko kallon inda take bai Yi ba Amman yana dan Lura da yadda take satar kallonsa kasa kasa idan taga zasu hada ido sai tayi saurin dauke idanunta.
sai wajen shabiyu ummi tace bazaka tafi gida bane?
yace uhmmmmm nima yau anan zan kwana ummi tace Dan me to byn ka wuce kwana s gida yanzu .
yayi murmushinsa me kawata fuskarta tare da fidda aininhi kyawunsa sannan yace uhmmmmm nasan da hk first love gidana ne ke bani tsoro yanzu shiyasa kawai naga yakamata nima na tattaro na dawo nan gabadaya.
ummi naji hk tasan akwai abinda yake nufi da wannan tsarin nashi ta Mike tsam bata sake cewa dashi komai ba tace to da alkhari .
itama zeenat tana ganin ummi ta wuce ta dauki junior da haidar taje ta kwantar dasu.
ta dawo daukar Anan dake jikinsa yace naga inda ake kin uba ana son ya'ya.
Cak ta tsaya takasa daukarta ta dago idanunta tana dubansa ya kashe mata idonsa daya yana sake balance ganin yau jin wani abu aranshi yasa ta bar masa yarsa takama gabanta.
da kanshi yaje yakai mata Anan ya kwanar adakinta ita kuwa da tana jin motsin shigowarsa ta juya masa baya.
ya nufi dakinsa ya kwanta sai dai kwana yayi yana juye juye agado hannushi dafe da mara yayinda bukatarshi takai kolowa gurin bukatuwa ya matse pillow a kirjinshi gam yana cicciza lips dinsa ya dinga watsawa kanshi ruwa kiran sallahr farko ya zabura mike ya sake sakawar kanshi ruwa sannan ya nufi masjid .
Washe gari wajen k'arfe 5:00pm Deeni yaje gidan su Nablah bayan sun gaisa da 'yan gidan ne aka kira masa Nablah, ana ce mata tazo inji Deeni ta mike da sauri, tafiya take kamar zata hantsila tama manta daga ita sai daguwar rigar bacci ta shan iska a jikinta, bakinta d'auke da sallama ta shiga d'akin, guri ta samu ta zauna muryar na rawa can k'asan mak'ogwaro kanta a k'asa tace " Abban Anan ina wuni........, wani dadi ne ya ratsa Deeni tun Daga tafin kafafunsa zuwa santsar jikinsa saboda dadin sunan data kira shi dashi, cikin jan aji ya amsa mata da lafiya lau, kefa ya kike?
"Alhamdulillah ta bashi amsa, duk suka yi shiru Nablah tace" ya su Junior da Ummi da zeenat ?
" duk muna lafiya, ya fad'a yana lek'a fuskarta dan san ganin yanayin da take ciki, mik'ewa tayi tace" bari na kawo maka ruwa, kai ya d'ago da niyyar yi mata mgn amma cak maganar ta tsaya masa a mak'ogwaro, rigar dake jikin Nablah babu abinda ta boye gashi ko bra babu a jikinta koya ta motsa sai jikinta ya motsa, ai bai san sanda ya jawo ta ta fado jikinsa ba take km jijiyarsa ta mike sambal sbd ganin abincinta azahirance.
Baki ta bud'e zatayi masa magana, aiko caraf taji ya had'e bakin su guri daya kwata kwata , bai bari tayi maganar ba, sosai Deeni yake tsotsar bakinta yayinda hannunsa yake wasa da nononta, Nablah ko da yau ne rana ta farko data tab'a jin haka a zahirance tuni ta rude ta firgice ta fara k'ok'arin kwatar kanta, amma ina wane ita, sosai hankalin Deeni ya tashi mak'ura dan dama a buk'aci yake tunda abun nan ya faru baiyi sex ba shiyasa yake . rigar baccin jikinta ya zame ya jefar a gefe ya cire tashi rigar, dama daga ita sai rigar babu ko pant, bakinsa ya kafa akan nononta ya fara tsotsar su, ita Nablah wani yarrrr take ji a jikinta, gaba d'aya ya gama fita a hankalinsa ya manta a ina yake burinsa kawai aji shi a samanta, k'ok'arin kai hannunsa k'asanta ya farayi, hannunsa ta rik'e ta saka masa kuka tace" please a gida fa muke wani yana iya shigowa ya ganmu a haka please ka daga ni, amma baima san tana yi ba, hannunsa ta rik'e gam taki saki dakyar ya kwace hannunsa ya danna a k'asanta numfashinta ne ya kusan d'aukewa saboda abinda taji, shiko k'ara ficewa yayi daga hankalinsa ya ji gabanta a jike sharkaf da ruwan ni'ima.
Deeni ya fara k'ok'arin ciro sandar girma daga cikin wandonsa duk ta rude ta frigice tasoma kuka sosai tana bashi hkr dan karkamin komai wlh tsoro take bani bazan iya ba.
karasa fito da jijiyar, yayi da niyyar shigarta da sauri Nablah tasa hannu ta rik'e shi sosai tana rokonsa " dan girman Allah kar kayi man haka, ka rufa man asiri nan fa gidan mu a d'akin mahaifiya ta, haba Deeni wannan wane irin abin kunya ne kake k'ok'arin ja mana sosai take kuka tana maganar.
Ajiyar zuciya Deeni yayi, a hankali ya daga ta ya mayar da kayansa itama ya mayar mata da nata ya koma gefe ya jingina da bangon dakin yana mayar da numfashi sama-sama, a hankali yakamota ya rungumeta a jikinsa yana shafa bayanta yana mayar da nufashi, lamo tayi a jikinsa itama, a hankali ya kai hannushi zuwa kanta yana shafa sumar kanta yace beelah I love you more than anything in this world " please ki bini muje gidana ko zafi ne na raga dake ba sai nayi sex ba, please ki taimaka min .
feelings na damuna, dago da kanta tayi atsorace tana kallonsa tare da sauke naunaiyen ajiyar zuciya sannan tace" ni wannan abin kunyar badani ba,wlh agaban Mama da Baba ka d'aukeni zuwa wani guri haba aida kunya, shiru yayi baice mata komai ba,sai ma ya kara matseta a jikinsa tsam yana sauke ajiyar zuciya sai da sukayi 30mts a haka sannan ya sausauta rungumar da yayi mata ya kai bakinsa cikin kunneta ya xira harshensa ciki yana mata wani irin sotsa wanda yasa taji gabadaya tsigar jikinta Sun mike tsaye wani shaukin dadi na dibarta muryasa a raunane yace ki Bari muje gidana please please wallahi amatse nike beelah yanzu zamu dawo sosai taji yabata mugun tausayi Amman wlh bazata iya biye masa tabishi wani guri ba ita bama hk ba tsoron wannan abun dake cikin wondansa take .
Ya tsura mata rikitattun idanunshi dasuka gama canza kala tsabar jarabar dake cin ranshi yasa hannuShi yasa ya janyo nata hannu ya daura saman jijiyarsa ta zaro ido afrigice please beelah kishafa min zan dan ji dama dama.
jikinta na wani irin kirma tace uhmmmmm wlh bazan iya ba to kana da mata ba kaje wajen matarka Man ka dai zamo me kwatata adalci atsakaninmu yanzu fa lokacinta ne banawa ba.wani irin sanyin dadi yaji yana ratsashi da ratsa every part of him .. jin abinda ta fada yasa ya sake susuce mata yana sake yawo da hannuta akan jijiyarsa yana lumshe mata ido tare da zaro nononta daya yana shafawa ahankali da murza kan nipple dinta yana sake matse hannuta da jijiyarsa sosai yana fidda wani irin numfashi yayinda gabadaya ta sake tsurewa da ganin yanayinsa Dan tunda take arayuwarta bata taba ganin jijiyar babbar mutun ba sai yau.
yau din km taci sa'ar ganinta katuwa ga girma ga tsawo da kauri tmkr robar faro .
sai gurin sha daya ya bar gidan byn daya dan ragewa kanshi zafi daita sannan jiki a sanyaye ya mike yana kakkabe jikinsa da gyara zaman rigar jikinsa yayi mata sallama ya tafi .
Kai tsaye gidan ummi ya nufa kmr jiya kowa yayi bacci daga zeenat har yaran sai ummi kadai yasamu zaune tana kallon tasharta ta gado yayi mata sannu da gida hade da hayewa sama yashige dakinsa yayi wanka yayi shrin bacci sannan ya dawo parlour'n ya zauna yana kiran wa..shiiiiii Allah ummi ta juyo tana dubansa tare da Yi masa sannu tace ga abinci can fa .
ya girgiza mata kanshi first love bar abincin nan kawai da dai zan samu coffee dana sha bana jin cin komai yanzu .
Ummi ta mike taje ta hado masa coffee takawo masa har da flaks din gabadaya takara gaba .
tabarshi nan zaune yana kora coffee Yana kallo yana jin yanayinsa na sake canzawa wani irin azabbaben fillings ya ke jin yana taso masa from no where yashiga mammatse kafafunsa yana cicciza lip's dinsa the more yadda yake kora coffee din the more yadda yake sake jin feelings na sake taso masa .
karfe daya daidai ya mike da kyar ya kashe komai na parlour 'n ya hau sama da niyyar shiga dakinsa har ya daura hannushi kan handle din kofar dakinsa .
km ya fasa ya juya kawai ya nufi zuwa dakin zeenat yana murda kofar yajita a bude ajiyar zuciya ya sauke ya tura kofar yashiga dakin ahankali yashiga laluban inda makunni fitilar dakin yake.
cikin saa ya gano ya kunna take haske ya gauraye dakin kwance yaganta kan bed Anan rungume daita suna baccinsu hankali kwance idanunshi ya tsura mata sanye take da right pupul din rigar bacci ahankali jikinsa amace yasoma takowa cikin sanyi jiki yakaraso inda suke yasa hannushi ahankali ya zare Anan ajikinta yaje ya shimfida mata blanket me kaure ya shimfedata tare da lullubeta.
ya dawo ya mayye gurbin Anan tare da hade bakinsu guri daya yashiga tsotsar bakinta yana yawo da duka hannuwanshi a sansar jikinta kayan dake jikinta ya cire sannan shima yasoma kokarin cire nashi still bakinsu na hade.
nonuwanta yake murzawa son ranshi cike da wani irin salo ME cike da shauki tare da zafafan kissing ta koina na jikinta ita kuwa sai mika take tana gantsaro masa kirjinta alamun sakonninsa na shigarta aiko nan da nan deeni sake gigicewa yacigaba da sarrafa albarkatun kirjinta.
yana murza jajayen kan nipples dinta yayinda kafin kace me tuni wasa yasoma canza salo cikin bacci zeenat taji yanayinta na sauyawa ta dinga mika tana gantsarowa tana sake turawa deeni breast dinta shi km sai sake susucewa yake yana manneta da jikinsa frigigib ta farka daga bacci tasoma kokarin bude idanunta har ta ware su fess akan fuskar deeni suna hada ido ya kashe mata idonsa daya yana cigaba da tsotsar kan nipples dinta yana lumlumshe mata ido afrigice tayi kokarin mikewa zauNe yasa iyakancin karfinsa ya danneta hade da hayewa bisa ruwan cikinta yana aika mata da salonsa masu saurin kashe mata jiki.
tafara kici kicin kwatar kanta Amman ina sosai deeni ya sauke mata karfinshi gabadaya bisa kirjinta yacigaba da sarrafata kafin daga karshe ya dauke hanyarsa daya kwana biyu bai shiga ba.
yasoma aiki sex daita yana gurnani nan ita km tafara yi masa shagwaba har da kuka .
bai saurareta ba sosai yake biyawa kanshi bukata itama tun tana nokewa da kuka har ta hakura sakar masa jiki babu yadda ta iya dan yadda yake zira mata jijjiya babu sauki bazata iya hakura dashi ba har ta bijirewa bukatarsa .
ihu yake sosai akanta har dasu I miss you.....
I love you so much bby ya kamkameta ajikinsa yana mata wani irin mugu ci. atare sukayi release ita dashi bai dagata ba yacigaba da aiki akanta yana zuba mata surutai kala abinda zeenat bata saba ji ba Kennan daga gareshi Dan hk batasan sanda ta kamkameshi ajikinta tana sake bashi hadin kai ba .
deeni bai barta ba sai dayayi mata ci hudu masu rai da lfy shima ya barta ne kawai sbd yasan yanayinta ba me juriya bace agurin sex yanzu ma sai Data bashi mamaki dauriyarta batare da nuna masa gajiyarta ba domin yasan dai bata iyawa dashi iyakacinta dashi two round ne tace masa ita tagaji .
yana mikewa daga kanta ta juya masa baya tana kumbure kumbure da wani ciccin magani ita ala dole matsa mata yayi.
ya kalleta yana tabe baki tare da juyowa part din data juyar da fuskarta yana duvanta muryasa a sarke yace meyye abin juyar da kai byn kingama kwasar dadi na .
ta yamutsa fuska tace ni babu wani dadi dana ji byn takurani kayi meyasa bakazo min idona biyu sai daka bari nayi bacci ka wani sato hanya.
babu wani dai yarinyar kisha dadin kawai borin kunya kike ni nasan ni kadai zan iya dake sannan ni kadai zan jiyar dake dadin wannan abar ya nuna mata jijiyarsa dake rike a hannushi yana shafawa alamun yana bukatar Kari dan a mike take still ...Kai dai kawai ka yarda kayi satar hanya.
uhmmmmm nayi na isa ne that's why.
Ko kina da abincewa yanzu wlh kiga wani satar hanyar..ni sani duk duniya babu wanda ya isa ya gamsar dake bayana kwadayina na hango cikin kwayar idanunki shiyasa kawai naga yakamata aka she bosss ko ba hk yakarasa fadar yana dage mata girarsa daya hade da cewa ni
tashi muje muyi wanka tana jinshi tayi masa banza ba taki tashi tsaya .
ya sake maimaita mgnrsa kawai taji yana kokarin cicibarta zuwa bayi tayi saurin mikewa tsaye zumbur tayi hanyar bathroom.
tare suka Yi Wanka dashi yana manne daita ajikinsa yana wasa da nipples dinta da wasu part din jikinta yayinda ita km sai faman buge masa hannu take.
Allah yaya kabarni hk nayi wankana wlh bacci nake ji ya hade rai sosai tare da kamkameta ajikinsa wlh idan baki daina ce min yaya din nan ba wlh zan shuka miki rashi mutunci better ma ki cigaba da kirana da zuciyarki zai fi miki sauki wlh yama fi dadi abakinki yakarasa fadar hk yana hade e bakinsu waje daya ..
Washegari koda zeenat ta tashi agajiye ta tashi taji mararta tayi mata wani irin nauyi da kullewa da kyar taiya Mikewa tsaye taje tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga ta sake Bin lfyr gado yana shigowa dakin yaganta kwance tana sheka bacci yayi murmushi yace lallai ma wannan yarinyar tagama rainani dayawa.
wato har yanzu bata sauko ba ballannata tabi ta kaina.
ya girgiza kanshi kawai ya hawo gadon cikin bacci taji ana murzata da murza breast dinta da sauri ta tashi afrigice shima tashi yayi ya rungumeta tare da bata kiss takoina mgn tafara masa dan Allah ya...ai kafin takarasa taji lip's dinsa ya sauka akan nata ya cafka lips dinta da karfi tsiya yana masu tsotsan mugunta .
tana kallonsa kmr zatayi kuka sai daya gama ladabtar da bakin sannan ya zare bakinsa ya riko duka tafin hannunta cikin nasa yana murzawa ahankali yana kallon cikin kwayar idanunta muryarsa a sanyaye yakira sunanta zeenat...... Ki tattara inaki inaki ki koma gidanki wlh wlh ina insonki idan bana sonki da tuni na sakeki kmr yadda kika bukata sannam Idan bana sonki da tun farko ban shiga damuwa ba sanda umminki tace bazata bani aurenki ba sbd cutarki zanyi .
kece Mace ta farko da zuciyata takasa Hakura Daita yayin gwagwarmar neman aurenta.
nasan kinsa da hk kawai dai kishinane ya rufe miki ido har yasa kika ganewa kike ganin kmr bana sonki nablah nike so.
nablah kaddarata ce babu yadda zanyi na gogewa kaina kaddata please zeenat kiyi hkr ki koma gidana karki barni gidana bai Zai yi hasken danake so ba idan babu ke acikinsa.
ta zame hannuta duka daga cikin nasa tana bata ranta tare da cewa bafa zan koma gidanka ba ka kyaleni kawai yadda nike rayuwata din nan yafi min dadi.
karya kike zeenat ya tari numfashinta rayuwa tare dani shine koman ki km shine kwanciyar hankalinki da farincikinki wlh idan babu ni acikin duniyarki bazaki taba iya rayuwa me inganci ba.
ranta a matukar bace tace shiyasa ai nace kabarni nacigaba da rayuwata hk babu kai acikin duniyata, kagani ko wani abu zai sameni inda babu kai acikin duniyata .
muryasa a hassale yace OK har yanzu baki hakura ba Kennan gaki ga gidan nan nabarki... ki cigaba da zama acikinsa .
sakin aure ne dai bazan taba yin sa ba.... Yakarasa fadar hk yana me daga mata kafadar sannan abinda baki nasani ba ni kadai zan iya dake da jiyar dake dadin duniya ya juya har zai bude kofar dakin ya km tsaya tare da juyowa yana mata wani duban mgn yake son Yi mata.
ko me ya tuna ya km fasa ya juya ya fice.
tun daga wanna ranar zeenat ta sake nisanta kanta da deeeni duk abinda zai hadata dashi guje masa take yayinda abun ke bakanta ranshi cikin wannan lokaci zeenat tasoma zazzbin dare da amai Amman babu wanda yasani tunda abatajin komai da rana sai idan dare yayi kwana zaune take har sai goshin asuba tayi take samun daman runtsawa tayi fari sosai ta rame ta daina cin abinci sosai idan kaga tana cin Abu to Abu ne me tsami kmr lemun tsami .
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah, gashi har cikin Nablah ya isa haihuwa, kullaum Deeni sai ya zo gidan sau biyu, sosai suka shirya da Nablah komai ya wuce a zuciyarta suke shan soyayyar su, haka dai lokaci yayi ta tafiya, da safe Deeni zashi office ya biyo ganin Nablah.
Mama da kanta ta shiga tayi magana, dakyar ta iya bud'e baki tace " Mama yashigo nan, saboda tun dare Nablah ke yin mak'uda, Deeni ya shigo da sallama amma Nablah bata iya amsa sallamar sa, a gefen gadon ya zauna yana fuskantarta, aiko ciwo kamar jira yake, nakuda taho gadan-gadan, ai tuni Nablah ta firgice ta fita daga hankalinta, ta fara salati, hankalinsa a tashe ya sungume ta ya fito waje da ita, da sauri Mama ta mike tana salati, tace" haihuwa ce ko Deeni amsa yake bata yana tafiya " eh Mama, kasancewar Mama macece mai kara da kunya ce shiyasa ta kasa binsu, tayi musu addu'a dai, Deeni nayin parking ya fito da sauri ya d'auke ta yayi cikin hospital da ita, da sauri nurses suka karb'e suka shiga labour room da ita.
Wannan Haihuwar kamar waccen , dan Nablah bakaramin wuya ta sha ba .
iya wuya tasha sosai bashiri deeni yasa akazo da mahaifiyarta wasa wasa sai da nablah tayi kusan kwana uku tana labour gabadaya hankalin yan'uwanta yayi mugun tashi nuratu anty salma kuka hatta mama kasa dauriya tayi yayinda nablah ta dinga barin wasiha iri iri deeni ya rude ya fita hankalinsa shi kansa sai daya zubda mata hawayen tausaynta har an Yanke shawarar Yi mata aiki ,kmr wannce Karon Allah ya taimaka ta sumb'ilo yaranta 'yan biyu mace da namiji kyawawan gaske farare tas masu kama da Deeni suma sak, Nurse ta fito d'auke da yaran dukkan su biyun ta mik'awa Deeni dake ta faman safa da marwa a k'ofar lobour room din, tace " congratulations sir, ta fada tana mik'a masa yaran, ajiyar zuciya Deeni ya sauke ya k'arb'i yaran ya zuba musu take yaji kwalla na zubo masa, Doctor ya dafa shi ya nuna masa d'akin da aka kwantar da Nablah yace " ta haihu lafiya nan da 2hrs idan ta huta zamu sallame ku, da sauri ya nufi d'akin.
Yana shiga tana bud'e idonta a kusa da ita ya zauna ya dora mata namijin akan ta, yace " kin ga kyauta da Allah yayi mana ko? kinga iko da kudurar ubangiji ko, wannan kadai ya ishe mutum tsoran Allah, a bamu kai 2yrs da aure ba Allah ya bamu kyautar yara biyar, murmushi Nablah kawai tayi, waya d'auko ya kira Ummi ya shaida mata Nablah ta haihuwa an samu 'yan biyu, cikin farin ciki Ummi tace " kuna ina yanzu, " muna abitin Family, ok gamu nan zuwa, Zeenat dake zaune ta shaidawa Nablah ta kara haihuwar 'yan biyu, jikinta yayi mugun yin sanyi, idon Ummi ta fakaita ta goge hawayen daya zubo mata, " Deeni kuwa gidan su Nablah ya kira ya shaida musu ta sauka, nan Deeni ya rink'a kiran waya yana tura text yana shaida musu, cike da farin ciki.
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
🌈kainuwa writers association
(united we stand and succed our ambition is to entertain &motivate the mind of readers )
Dedicated to
hauwa A usman
jiddarh
Page 109
Cikin kankanin lokaci ummi ta dinga bugawa dagin na nesa dana kusa wayar akan zance haihuwar.
da sanar musu cewar me jegon tana family hospital dinsu.
Kafin kace ME tuni labarin haihuwar nablah ya karade koina a estate din.
Gabadaya koina ya dauka da zance haihuwar har su maryam da shema da sauran su lubnah sun kira zeenat suka mata barka ta amsa musu fine tmkr babu wani abinda ya faru atsakaninta da nablah. dan har ce musu tayi su sanar da jama'arta da zance haihuwar.
wanda hkn yayi maseefar basu mamaki .
aransu sukace anya kuwa wannan zeenat din da suka sani ce kowatace daban.
domin idan kuwa ita ce Lallai zeenat tayi mugu mugun tsanyi da canzawa .
gabadaya ma ta sauya ta daga zeenat din da suka sani ta dawo musu ruwan tsanyi.
Tun sanda ummi ta sanar da zeenat zance haihuwa nan jikinta yayi mugun tsanyi .
sannan takara tabbartawa kanta Dan Adam ba'a abakin komai yake ba arayuwa.
sannan km mutun bai isa ya canzawa kanshi kaddararsa ba.
Ita kam ta yarda ta amince kaddararsu ce nablah ita da mijinta.
Domin tayi imani da Allah idan ba Dan Allah yayi nablah zata shigo cikin rayuwarsu ita da mijinta ba.
da tata kaddarar xubda ciki bai shigo ba.
Dole kaddarar zuwan nablah da hahuwar da zata yiwa deeni ya janyo nata kadddarar zubda cikinta .
jikinta ya sake yin wani irin mugun sanyi take km jikinta yasoma rikicewa tasoma rawar tsanyi ta sake rungume anan dake rungume ajikinta tana jinjina girman alamarin ubangiji da kudirarsa domin duk yadda Allah yaso da lamarinsa hk zai Yi .
shekara biyar Kennan tana neman haihuwa ido rufe byn zubda cikinta sai gashi cikn shekara daya tal deeni yasamu ya'ya har biyar .
hk tunani suka dinga zuwa mata iri iri game da rayuwar duniyar suna wucewa .
duk da yadda take jin jikinta hkn bai hanata budar bakinta tacewa ummi yakama ace xuwa yanzu an isa zuwa hospital.
ba sai wasu daga cikin dagin Sun rigamu zuwa ba.
ummi wacce oready tagama mikewa daga zaune datake tace tunanin da nike Yi Kennan barin na dauko mayafina da Jakarta sai na tafi tunda ke bakya jin dadin jikinki ......
A'a ummi tare zamu har yaran ai bawani Abu ke damuna normal nike .
zeenat tasaka laraba tayiwa yaran duka wanka ita km tasoma da gyara haidar da junior .
Sannan ta shirya Anan tsab cikin wasu kayan redymedy ta shafa mata baby oil akanta ita dasu Haidar sbd har lokacin ganinsu take they are still baby's.
kawai dai jikin girma jiki garesu sakamakon cimar abincinsu da km kulawa da tattali da suke Samu me kyau .
dan ko abincn da ake basu irin na kasar turai ne.
sai kyalli yaran suke xubawa da daukar hankali barin ma yar gata Anan domin gabadaya gidan sun fi ji daita kasancewarta mace.
Ta feshesu da turare me sanyin kamshi tana tushe hancinta dan jin turaren yasoma hawa kanta.
" sannan Itama ta Mike tsaye da kyar ta zaunar dasu akan kujera three stars tace kujirani baby's dina ina zuwa .
murmushi Haidar da Anan suka mata banda miskilili uban miskileye wato junior me halin ubansa sak kana ganinsa babu tmby like father like son .
tashiga dakinta Kai tsaye bathroom tashige gabadaya tasoma yunkurin amai aiko tashiga kwara amai tmkr zata amayar da hanjin cikinta.
sai datayi me isarta sannan tayi wanka ta fito tana fidda numfashin wahala sama sama.
ta shirya kanta tanajiyo sautin muryar ummi tana ce mata tagama fa ita take Jira .
Bata wani Yi shafa ba ko fesa turare ajikinta sbd yanzu kusan duk bata bukatar shakar kamshinsu .
wanda ta fesawasu anan ajikinsu ne ma yanzu yasakata Amai.
daguwar rigar jallabiya ja wace tasha stone work tun daga samanta har kasanta da hannuwanta ta zira ME shegen kyau da daukar hankali .
tayi rolling din kanta da bakin mayafi sak idan kaganta kaga ba indiyar asali .
duk da rashin shafan da batayi ba hkn bai sa fuskarta yin fesss ba farinta bai disashe ba.
sai ma wani fari data Kara Yi na musamman ta dauki farin ledar tsamiyar birinta wanda shansa ya zamemata jiki tasaka cikin yar karamar Jakar ratayawarta.
tayi kasa.. Suka nufi hospital suna isa kai tsaye dakin da aka kwantar da nanlah suka nufa wanda daman deeni yasanar masu .
bakinsu dauke da sallama suka shiga dakin .
Zaune suka tadda oga deeni manne kusa da nablah makale daita tmkr zai shege mata jiki yana bata tea abaki ganinsu yasa ya dan gyara zamansa yana yiwa ummi sannu da zuwa yana cigaba dabata ita km ganinsu yasa ta Kai hannunta tana kokarin karbar Cup din a hannushi.
babu musu ya sakar mata ita km sunkuyar da kanta kasa sosai takasa sha yayinda yaran sukayo kanta suna murnar ganinta .
dan rabonsu daita kusan tsawon wata uku Kennan.
deeni yayi saurin taresu . aiko junior ya saka kuka yana kallon uwarsa da son zuwa gurinta Amman antareshi.
deeni yashiga rarrashinsa yana ce masa momy she's not filling fine.
bata da lfy Kalli yana nuna masa kyawawan baby's dake kwance cikin dan madaidaicin gadon jarirai momy ta haifa maka baby masu kyau kana so ?
duk cikin harshen turanci yayi masa mgnr junior yayi shr yana kallon baby's sai dai basu dauki hankalinsa ba.
shi dai gurin uwarsa yake son zuwa .
muryar nablah asanyaye tayiwa su ummi sannu da zuwa ummi da zeenat suka amsa tana mata sannu da jiki.
zeenat MA ta bude baki da kyar tace sannu nablah ya karfin jikin?
Ta fada ahankali byn ta zauna suna fuskantar juna.
jikin nablah na Dan rawa da bakinta .
da sauki ta bata amsa still muryarta cike da rudani .
Dan wani irin matsanancin kunyarta taji tayi mugun rufeta.
to Allah ya baki lfyr jiki da lafiyar shayarwa ameen tace muryarta kasa kasa.
ummi ta janyo hannun junior ta zaunar dashi kusa da uwarsa tace makale mata ME shegen bakin nacin tsiya ai idan baganinsa yayi akan bed din kusa daita ba hankalinsa bai zai taba kwanciya ba.
ballantana ya Bari ruhinsa yassmu salama.
aiko take deeni da zeenat suka sa dariya wanda itama ummin dariya takeyi gurin fadar hk.
shi dai junior jinsa kusa da uwarsa yasoma murna yana farinciki sauran yan'uwansa suka makale su km jikin zeenat .
zeenat ta mike tsaye jikinta a matukar sanyaye ta dauko baby's ta mikawa ummi daya itama ta rike dayan tana nunawa anan da hadar yayinda kadan kadan junior ke kallonsu yana kallon uwarsa.ummi tace ki karasa shan tea Man kafin yayi sanyi
nablah ta girgiza kai na koshine ummi. Amman dai takai cup din bakinta.
ganin junior bata bin cup din hannuta da kallo yasa tace masa Zaka sha tea?
ya Dan daga mata Kanshi alamun zai sha tasoma bashi da spoon din hannuta ahankali daman ita kanta tea din ya isheta ga km tarin tsarguwa da kunyar aunty zeenat datake jin yayi mata ruf da dugu. ahankali deeni ya koma ya jingina da bangon dakin tare da ciro wayarsa yana lallasawa Amman gabadaya hankalinsa da natsuwarsa sun karkata ga zeeenat wacce take zaune jugun .
sbd idan dai idanunshi ba gizo suke Yi masa ba rama yaga tayi sosai fiyye da kwanakin baya daya ganta .
Kasa kasa yacigaba da kallon wanda hkn ya takurata sosai har yasa zuciyarta dokowa da sauri .
Kusan awa daya da zuwansu sannan sule direba ya sauke aunty Salma da nuratu sai wata kanwar mahaifiyar nablah .
suna shigowa deeni yabar dakin.
sosai aka shiga gaisawa da juna tare da yiwa juna barkar samun karuwa. wuni cur ummi sukayi a hospital din hira sosai ke gudana atsakanin ummi da deeni inda jifa jifa ummi tana saka zeenat cikin Amman ita zeenat sai tabasar dasu .
tayi murmushin yake kawai .
Dan kar nablah tagane akwai wani Abu.
Amman gabadaya ma tafi meida hankalinta akan nablah tana janta da hira.
Sai yamma list sannan suka kama hanyar gida.
ummi da zeenat zaune abayan mota da haidar da junior anan km rungume ajikin deeni agaban motor kule direban ummi na tukasu ahankali dan deeni Yabar sule a hospital domin ya maida su aunty salma gida .
ahankali deeni yasa hannusa ya tsaita kan morrow motor ta yadda zai ji dadin karewa zeenat Kallo .
Kallonta yake cike da wani irin mamakin ramarta .
jikinta ne yabata yana kallonta dan hk ta dago idanunta ahankali aiko karaf idanunwansu suka sarke cikin Juna take zuciyarta ta buga da karfin gaske .
sosai ya kura mata ido .
ta kau da kanta gefe ahankali tare da lalubar Jakarta taji wayam alamun tsamiyar birinta takare .taja tsaki mara sauti ummi tajuyo tace ke km lfy ta bata fuska ummi tsamiyar birina ce takare ummi ta tabe baki km shine yazama abun tsaki ?
deeni yaki dauke idanunshi akanta kmr minti biyar tsakanani ta km juyowa taga ko ya duke idanunshi Akanta duk da jikinta yana bata still ita din yake kallo. sake tsarkewa idanunsu sukayi cikin juna wannan Karon atake zuciyoyinsu ya buga.
wani tsaki ta sake ja Amman wannan Karon aranta tayi tana me watsa masa wata uwar harara.
wani tsadadden murmushi yasakar mata wanda tasan da wuya kaga yayi irinsa idan bata kure masa ba.
cikin kwantar da Murya sosai yace first love meke damun yarinyarki naga duk tayi wani iri ? Yakarasa fadar hk yana kokarin gyara anan ajikinsa .
ummi ta juyo ahankali ta dube zeenat tace wlh son bansani ba.
kusan ko ni wannan ramar nata yasoma damuna.
Kin km tmbyeta?
nayi tmbyr duniya nan Amman tace babu komai ba km je hospital?
ummi tace bamuje kasan zeenat da kin zuwa hospital ai.
AI kamata yayi ace kuje kuga likita domin asan abinda ke damunta. shima nayi mata mgn kwanaki har nuna mata bacin raina nayi Amman abanza ni abunda ma yafi damuna yadda bata cin abinci sai kayan tsami kullun ita Kennan shan lemun tsami.
ya sake tsareta da rikitattun idanunshi yana kallonta yana cewa ai dole kam yanzu taga likita Dan bana bukatar wanna ramar nata .
idan ma wani abun ne atareshi da wuri.
ko km ni tasanar min da damuwar nayi maganinsa.
ummi tayi murmushi kawai kana tacigaba ai zeenat din da Kasani.
ta yanzu kam gabadaya ta sauya ta canza tazama me shegen zurfin ciki tsiya komai Aka tmbyeta yanzu tace babu komai .
wlh har abun Nata yasoma data zuciyata bana jin dadin ganinta hk yanzu zeenat tafi bukatar mutuwa akan rayuwata ummi takarasa mgnr kmr zata zubda kwalla..mgnr ummi ta taba zuciyar zeenat sosai magana take son Yi Amman takasa bude bakinta sbd yawun dake cike cikinsu.
lura da hkn da deeni yayi ne ya umarci kule ya tsaya ta zubda yawun abakinta .
akan hanya tace kule ya tsaya .
Tayi warning glass din motor tare da kira me sai da kayan fruit dake zaune gefen titi .
Matashiyar mata takaraso jikin motor da sauri ta tsaya tana tmbyr abinda suke so.
abinda ya daurewa deeni kai bai wuce ganin abinda tayi point ba.
Lemun tsami da agwalima wanda bai karasa nuna ba da kyau wanda dagani yasan zaiyi mugu mugun tsami tace akawo mata matar ta hado duk abinda zeenat ta lissafa mata.
ta mika mata ta karba ta zuba ajakarta shi dai deeni sai binta yake da idanu dazata biya kudi ne ma yayi saurin zaro 5k ya mikawa matar duk da yasan kudin kayan basu kai hk ba .
yace kule yaja motar.
mashiyar matar nayi masa Bayanin ai kudin bai kai hk ba .
ya daga mata yatsunsa alamun tabarshi kawai tun cikin mota zeenat tasoma Shan agwalumarta tana lumshe ido sbd dadin dataji ya ratsata.
deeni dake kallonta ta cikin mirrorw ya sakar mata wata uwar harara akayi sa'ar itama kallonshi take.
Take ta rama tana cigaba da tsotsar kwallon agwalomarta .
Muryasa a kasalsnce yace meyye hk zaki kama shan abu batare da kin wanke ba?
Salon wata sabuwar cutar takamaki .
ke nifa ban ma yarda da shan wannan agwalo ....me take da suna da lemun tsamin ba muryarta kmr zatayi kuka tace ummi kingansa ko nifa banson takura da sa ido fa.
ki gaya masa ya fita harkata da abinda nike ya dago hannu zai buge mata baki tayi saurin gocewa kinga shi ko ummi.....
Nifa banason damuwa ni ne ma damuwa zaki gane kinkirani da damuwa wlh .
ummi tayi murmushi kawai tana girgiza Kai
har suka karaso gida zance zeenat da matsalar dake damunta suke tautaunawa da ummi ...
Tana zuwa gida wanka da sallah tasoma yi sbd lokacin sallah tayi ta dawo parlour'n kasa ta zauna .
tana nan zaune ummi ta sauko taci abinci ita da yaran ta mikasu gurin deeni.
ita km takaraso gaban zeenat ta zauna tana kallonta tare da cewa bazaki ci abinci bane?
ummi banajin cin komai yanzu wlh ni kaina ina son cin abincin Amman da zarar na zauna gabadaya sai naji ya fita akaina.
ummi ta tsura mata ido sosai tana kallonta tana nazarinta sannan daga baya ta numfasa.
ummi batasan sanda tace ko dai ciki gareki zeenat?
Zeenat tayi murmushi kai kai haba ummi wani irin ciki km .
byn every month ina yin period dina kawai dai hk nike jin kaina yanzu Amman wlh banida komai .
OK yanzu meyye amfanin zamanki zeenat agida kiyi hkr ki koma gidanki shine gatanki da rufin asirinki.
duk yan'uwanki suna zaune gidajen mazajensu lfy lau ,da dadi da babu duk da nace bazan matsamiki ba Amman wlh komawarki shine kwanciyar hankalina.
zeenat taja numfashi da kyar ta fesar Kana tace ummi kiyi hkr da abinda Zance gsky bafa zankoma gidan deeni ba adduata bai wuce ya sauwakemin .
Allah ya hada kowa da rabonsa mafi alkhari . ahankali ummi ta dinga mata fada cikin zafin rai da kunar zuciya ki zauna saunanci har wannan karamar yarinyar ta dawo ta kwance miki miji gabadaya.
,ki kara rasa gane kanshi gabadaya tun yana binki yana baki har yazo ya tattaraki ya watsar .
sosai ta dinga mata fada ta inda take shiga ba tanan take fita ba daga baya ta dawo nasiha.
ta kamo hannuta cikin nata hb mamana ki tashi tsaye ki karbi mijinki.
ni nasan kina matukar son mijinki.
zeenat ta zaro ido waje tare da cewa kai ummi wanna ai zance da Kennan.
wai ina son yaya ?
wlh kina sonshi sai dai idan kin ce min bakamar da ba na yarda.
km ko ni zanji dadin hk Dan zakewarki akanshi yasa tun farko ya dinga nuna miki ko inkula Amman abinda nake so dake yanzu ki natsu ki shiga hankalinki kiyiwa kanki fada kishiga ilimin ta natsu ki koma dakinki .
Zan yiwa hjy turai mgn tasamomin me
gyara min jikinki ciki da waje .
ta yadda kema zaki zama abar alfahari agidanki.
km akwai sakon danabada akamin daga India suma duk na gyara ne .
zeenat tayi dariya sosai wanda rabonta dayin irinta tun kafin hargitsin daya faru.
tace kai ummi ina kyawun sona?
dole ne mamana akanki babu abinda bazanyi ba matsawar zaki samu farinciki uhmmmmm ummi Kennan kina son dai nakoma gidan yaya alhalin kinsa baya sona shikenan hk zan koma gidansu yacigaba da wulakantani agaban matarsa ummi ki bar zance komawar nan tawa bashi da wani amfani wlh ...
Yana da amfani mamana kema wanann Karon dole kiyi hkr ki zage ki kwato yancinki agidanki abinda baki sani ba matar Fari da mujin fari suna da wuyar rabuwa duk runtsi km ko Sun rabu wlh kowannensu zaishiga damuwa da tashin hankali mara misaltuwa koda kuwa rabuwar tasu bata arziki bace.
aganina yakamata ace ..... Cak ta dakata da mgnrta ganin saukowa deeni ......kunnenshi makale da waya yana hira da sanyi idanunshi Yakaraso inda suke ummi tace ina yaran ?
yayi mata alamun duk sunyi bacci da hannushi. ya zauna kan kujerar da zeenat ke zaune akai har cinyoyinsu na gogar juna damm gabanta ya buga shima hkn ce tafaru dashi ta Dan saci kallonsa ta kasan ido suka hada ido ya kashe mata ido daya yana cigaba da wayarsa .
ta kawar da fuskarta gefe tana Kallon ummi .
muryasa a sayaye yace nablah bazafa ki taba ganewa ba ke yarinya ce bangaren nablah kuwa cewa tayi tayaya zangane kuwa.. Allah abban anan kayayyakin sunyi yawa ne sosai shiyasa kaji nace hk hatta aunty salma ma sai datayi mgn akai .
Ina aunty salma take?
gata OK kibata wayar kawai .
jin hk yasa zeenat tasan da nablah yake waya hkn km yasa zuciyarta tayi wani irin harbawa da sauri .
da sauri tashiga kokuwa da numfashinta dake neman daukewa.
take km tasoma karanto addua acikin ranta .
nablah ta mikawa aunty salma wayar yayi mata bayanin abinda yake so ayi .
tace ai abun ne yayi yawa wlh bai Yi ba aunty. komai nayi mata ta cancanci hk daga gareni to to shikenan angode Allah kara budi .
yace ameen sannan ta mikawa nablah wayar suka Yi sallama daita tare da cewa zai kirata zuwa anjima karta Yi bacci tajirasa yakarasa fadar hkn ba ta yadda zasu ji ba .
ummi ta mike tsaye tana cewa yakama kazo ka koma gidanka hk fa.
kar fa daginka su sani gaba da kanan zance .
bangama fita cikin wance surutan ba ka sake jawo min wani... ajiyata ce agidanki first love ki bani ita kawai nakama gabana yana gama fadar hk ya waske tmkr bashine yayi mgnr ba take ummi da zeenat suka gane abinda yake nufi..
ummi taji sanyi sosai aranta domin yanzu tana jin dadin yadda deeni yake nuna kulawarsa akan zeenat da damuwa da lamarinta.
tayi murmushi sosai tace wlh deeni ka rainani dayawa to yazanyi first love abubuwa sun min yawa most especially matsalar zeenat first love Kalli ki duba yadda zeenat ta dawo kullun sake ramewa take bata rasa ci da sha ba da komai Amman takasa damuwa aranta.
Wlh ji nike tmkr xuciyata ta buga akan hk .
ummi tace hkr zakayi komai zai Wuce Inshaallahu yazama labari .
zeenat ta furzar da iska tana sauke naunauyen ajiyar zuciya aranta km tace kaji shi.
da iyayin tsiya yana yin wani abu dan ace ya damu da lamarin mutun ...
alhalin ba hk bane ackin zuciyarsa .
nan ummi tabarsu tayi Dakinta tana adduar Allah ya daidaita lamarin komai atsakaninsu.
ahankali ya janyo system dinsa yasoma operating yana tura sakonni ayanar gitso ta mike tsam itama zata bar gurin batare daya dago kanshi ba yakira sunanta tare da cewa ta hado masa coffee juyawa tayi zuwa hanyar kitchen ta hado masa coffee.
cinki daurewar fuska takaraso ta'ajiye masa batare data kalleshi ba .
ta juya abunta aiko bazato ba tsammani taji ya fezgota zuwa fadadden kirjinsa ya rungumeta tsam ajikinsa yana sakin numfashi tare da ture system din gabansa .
dagowa tai tana kallonsa ya Sakar mata wani kayataccen murmushi wanda ya bugar mata da zuciya yasa kirjinta yashiga dukan uku uku tayi saurin dakewa.
ya tsura mata ido yana kallonta sai dai ita kam juyar da fuskasta tai tare da shan kunnu sosai cikin murmushin nan nasa me hargitsa zuciyar ma'abocin kaunarsa.
yace my sweet wife wai duk meyye, zafi hk?
fushin nan yayi min yawa fa wlh yayiwa zuciyar deeni nauyi dago da idanunta tayi ta xubesu cikin nasa .
fushin me zanyi ai inda mutun yasan andamu da fushin nan yake .
yau kusan wata uku Kennan nake binki zeenat Amman kina garani kmr wani ball sai ma ki dinga shareni kina wani babbatsar dani.
kwata kwata ma na Lura yanzu baki son ganina yakarasa fadar hk yana sake narke mata ajiki yana shafo fuskarta .
wasu hawayene masu zafi suka samu nasarar Zubowa a idanunta da sauri yasaka harshensa yasoma lasar hawayen yana dauke mata su tana mugun son mijinta idan yayi mata wani abun ji take tmkr ta ciro zuciyarta tabashi .Tana son caring din mijinta Tana son mijinta yasan value dinta da mutuncinta koda zata koma gidansa.
muryarsa a matukar sanyaye yace my First Lady ....suna daya kirata dashi yayi mugun tsanyaya ranta ta lumshe ido tana jin wani tsanyi na ratsata daman deeni zai zame mata hk?
daman deeni zai Yi laushi hk? Wasu ruwan hawaye ne suka zubomata
ahankali yacigaba da mgn me km yayi zafi hk harda zaki dinga kuka daga mgn?
nifa a yanzu banason ganin kukanki ballantana bacin ranki dan Allah ki daina kukan nan yana taba zuciyata ya hade hannuwansu ya daura daidai saitin zuciyar ina sonki zeenat ni kaina bansan ina matukar kaunarki ba sai danaga kina kokarin barina ki aure wani na.
dago fuskasta tayi tana kallonsa yayinda shi km ya Saka hannuwansa duka ya tallabo fuskasta ya hade goshinsu guri daya .
tsinin hancinsa na gugan nata suna shakar numfashin juna cikin tsigar rarrashi muryarsa cikin salon Mai dadi yake mata mgn am sorry ones again my firstlady stop crying please am very sorry .
nasan kina sona nima km hk nasan kina kishina ne sbd kina sona.
km na yaba da wannan salon kishin naki.
yanzu salon kishin naki matukar birgeni yake sbd bakisa yaranki Ciki ba, da ita nablah abun iya kaina ya tsaya.
hkn yasa nakasa hakuri gurin shareki kmr yadda nayi niyyar.
you mean anything to me shr tayi ta daina kuka sai dai takasa ce masa komai sbd yadda jikinta yayi sanyi .
dan yawo yashigayi da hannushi a sansar jikinta kafin daga baya ya kamo tafin hannuta ya xira yatsunata guda biyu cikin bakinsa yana tsotsa ahankali yana sake kashe mata sansaR jiki duk da tana jin dadin abinda yake mata da jin wani irin mugun feelling dinsa .
Amman ta danne ta dake ta samkame mishi ajiki. ya mike tsaye daita ya nufi dakinta suna shiga salonsa ya sake canzawa zuwa wani salo First Lady deeni .....yakirata ina son ki jiyar dani dadi yau wanda banta ji irinsa ba.
ya fadi hk still hannushi na yawo ajikinta .
dago idanunta kai tsaye ta jefa cikin nashi ido motso daita yayi sosai suna shakar numfashin junansu .
cikin muryarsa data soma canzawa zuwa ta shauki yace ina bukatar natsuwa daga gareki yake Matata.
hk ya dinga binta yana romancing din jikinta har yasoma mantar daita zance kinsa datace tana Yi ayanzu .
wanda alokacin shi burinsa bai wuce yasamu ya biya bukatarsa da zeenat ba.
yau ma still babu laifi she real try to him dan akalla sunyi round 5 daita take kakare masa tasoma matse kafafunta alamun tagaji batare da tace masa tagaji din ba .
ya barta dan shi ahkn ma kokarinta yagani ...
Ya kwanta tare da janyota jikinsa ya rungumeta yana fidda numfashi ahankali .
cikin hk bacci ya daukeshi rungume da zeenat batare da ya kira nablah.
ganin yayi bacci yasa Zeenat zare jikinta daga jikinshi ta mike tsaye da kyar tashiga bayi tayi wanka tsarki Tare da dauro alawala taxo ta gabatar da shaf'i da wutiri sannan ta zauna tayi yan adduointa ta roki Allah ya mallaka mata zuciyaryar mijinta yacigaba da yadda yake mata yanzu kota koma gidansa kada ya canza mata sannan ta koma ta kwanta ..
yayinda ita kuwa nablah takasa runtsawa ta dinga kiransa awaya taji ba'a dauka ba.duk ranta ya dagule daga karshe ta kwanta kawai ta runtse idanunta batare da tana jin bacci ba .
zuciyarta ta dinga kissima mata abubuwa iri iri daban daban akan deeni addua ta dinga karantowa akasan zuciyarta ahankali taji wata natsuwa tazo mata .
Washegari zeenat tana tsaye gaban mirror deeni yashigo dakin sanye yake cikin farin yadi fari kal har mutun yana iya hango singileting jikinsa da kwantaccen gashin kirjinsa ta sama kadan.
tayi masa kallon tsab ta mirrorw Kana ta dauke kanta tacigaba da abinda take ya isa gareta ya rungumota ta baya yana shinshina wuyanta ya dan kai habarsa kan kafadarta yanacigaba da goga mata gashin kasumbarsa tare da cewa should I help you?
hade fuskarta tayi sosai batare datace masa komai ba.
ya juyo daita ahankali yana kai bakinsa kan lip's dinta ya tsotsa sannan yace kina wani basarwa ina miki mgn wlh ki daina wani pretending zeenat har yanzu fa kina son deeni .
son deeni acikin jininki yake.
uhm ta tabe bakinta sannan tace hk dai kake gani Amman ni babu .....yayi saurin juyo daita hade da hade bakinsu guri daya.
sai daya tsotsi bakinta sosai sannan yace kinsa wani abu salonki na yanzu yafi birgeni uhmmmmm ta bashi amsa da hk .
shima yace uhmmmmm kamshi turaren jikinsa yasoma autsineta tayi saurin fexgewa daga jikinsa tayi bayi da sauri tashiga sheka amai yakaraso da Sauri yashiga har cikin bayin ya dafa kafadarta yana Yi mata sannu ya bata ruwa ta wanke bakinta da mamaki yake kallonta ya mikar daita tsaye ya kawo dakin ya kwantar daita ya riko hannuta yana me tsura mata ido tsawon minti goma ya dauka yana me kare mata kallon tsab.
kana yace when did you start vomiting like this?
ta yamutsa fuska tana shafa gefen fuskarta taki bashi amsa sai daya sake maimaita mgnrsa tukun tace today... Yayi Shiru can km yace are you pregnant?
tayi saurin girgiza masa Kai .
ya zabura ya matso sosai yace ke wlh banyarda ciki ne dake zeenat .
ki shirya kawai muje hospital ..ta sake bata fuska kana tace yau fa duka duka kwana uku Kennan dana gama period to yaya zanyi ciki?
.
Mtssss yaja tsaki to meyyesa ki amai irin hk?
babu komai I think malaria ce ke damuna sbd zazzabin daren da nike yi .
OK yace yana gyara mata jiki tare da lullubeta yace shi ya wuce office .
Lumshe ido tayi Tabi bynsa da kallo inama zarginsu zai zama gsky?
ina ma ciki gareta?
sharrrrrrr hawaye ya balle daga idanunta nan fa ta dinga kuka tana cizan lips...
Hospital ya cika mikil da dagin deeni da abokan arziki takoina Ka kalla daginsa ne.
ahaka ma ba duka bane suka zo.
hatta dagin nablah dawowa sukayi tmkr wasu yan kauye sai binsu da kallo suke.
da safe koda deeni yazo shareshi nablah tayi ko kallon inda yake bata yi ba baya ga gaisuwar datayi Masa .
yasan fushi take dashi sbd tun kafin yaxo yake kiranta awaya daki dauka yakaraso ya zauna kusa daita sosai ya kamo tafin hannuta cikin nashi yana murzawa muryarsa kmr zai kuka yace am very sorry pure hrt nasan kina fushi dani ne sbd bankiraki ba jiya wlh manta nayi .....muryarta a dan raunane tmkr zatayi kuka itama tace ai nasani... Ya tsaya slow yana kallonta yana cigava da massaging din hannuta .
tacigaba da mgn cikin sanyi rai nasani abban anan acikin irin wannan lokacin bazaka taba tunawa Dani ba. Dole ka manta cikin duniyarka Koma cikin wani hali zankasance.
takarasa fadar hk tana runtse idanunta.
nablah ki sausautawa kanki kada ki bari kishina yayi tasiri acikin zuciyarki har ya zarta son da kike min Dan... Saurin katse shi tayi ta hanyar cewa dan me zanyi kishinka abban anan alhalin nasan bani kadai gareka ba .
gaba ma Zaka iya ganin wata kace kana so ni dai kawai naji babu dadi ne domin kaine kace najiraka Zaka kirani if not bazan damu ba ...
Ya lura tsab kishinsa take Amman dayake wayon tsiya ne daita ta waske.
OK to kiyi hkr I made a mistake nan dai komai ya wuce atsakaninsu.
kullun sai deeni yazo ganinta sau biyu arana.
da safe kafin yaje office da km byn ya tashi aiki anan yake tarewa ya bata lokaci yana riritata da shagwabata har taimaka mata yake wajen baya yara abincinsu .
inda km ya koma gida still zai kirata awaya su kwana suna sha hirar love abunsu ..
Sai da nablah tayi kwana biyu a hospital sannan ta fito sbd Karin da'aka mata gurin haihuwa. Deeni ya dinga hauka da barin kashe kudi har abinda bana amfani bane sai da ya tsiya .
har sai da mlm salisu yayi masa mgn akan kashe kudin dayake yayi yawa .
yace baba naji Amman kayi hkr karka damu ina dashi ne da ban dashi ba zan kashe ba .
zeenat ma ta sake sosai Tana walwalarta cikin mutane daman km ita ta jamaa ce ta fidda komai aranta tsakaninta da nablah komai daidaita kwata kwata bata jin haushin yarinyar azuciyarta .
sai Dai dan kishin mijinta datake wanda ba za,a rasa ba daman .
A tsakaninta da deeni kuwa babu wata jituwa Kwata kwata batason abinda zai hadasu ko kebewarsu guri daya bataso dan yanzu ne zai nemi dagula mata lisafi km baya barinta hk sai yayi yadda yasan yayi sex daita kota karfin tsiya ne.
idan tayi masa mgn tace a gidan ummi fa suke .
sai yace OK to ki koma gidanki Man idan kunyar ayi sex dake anan din kike dan wlh muddin baki koma ba .
nan zan dinga kawo miki duty ki.km dolenki ki karba
hk dai yake mata abubuwa cike da sanyi zuciya da rarrashi.. Ummi ta dage gurin kula da zeenat musamman aka kawo mata me gyaran jiki ,ciki da waje wanda matar tabbata wa ummi diyarta tana da cutar sanyi ajikinta dan hk sai Sun gama treatment dinsa sannnan zaa soma gyaran ciki da waje ta yadda me gida zai ji dadi sosai zeenat bata ki ba dan tasan dole zata koma gidan mijinta sai dai ba acikin wannan lokacin ba sai tagama sanin matsayinta tukun.
Sosai itama mahaifiyar nablah take bawa diyarta kulawa gurin gasata da ruwan dumi dayi mata amfani da sassake iri iri kmr su garin Karo da da garin baga ruwa dana magariyya da alam hk zata hadesu guri daya ta dafa su sosai ta cika babban baf tace nablah tashiga ciki ta zauna .
Nablah da kuka da ihu hk mama zata dannata ciki akai aiko kafin suna tuni nablah ta dade da hadewa tayi rass tayi fari kyau tayi fresh bobss dinta suyi wani irin cika tkmr ba haihuwa ta biyu ba.
Ranar suna yara suka ci Sunan mahafin nablah da mahaifiyarta take aunty salma tayi musu lakabi da wani suna Macen tasa mata Mimi namijin km mu'alim.
Wani katamfarin holl ya kama me suna trusted deeni ya kashe kudi kmr babu gobe tmkr akasa yake hakosu.
Hk ma danginsa sunyi rawar gani sosai zeenat ma akwati goma shabiyu ta yiwasu nablah yaran hudu hudu nablah biyu.
sosai mutane suka jinjina wannan karamcin nata amatsayin na uwar gida yayinda wasu ke mamakinta da ganin kimarta banda masu kallonta duk inda ta gillama nunata ake ga uwargidan nablah. dan sosai tayi rawar gani da bajinta ranar suna .wasu haddadun les ta saka wanda kudinsu zai kai dubu dari da hamsi ga wani make up Datasha na fitar hankali abunka ga meson kwaliya a wannan kyawun datayi har raina kanta tayi a zuwa wai dan bata jin dadin jikinta ne .
Ummi ma ba'a barta abaya itama tayi bajinta duk wanda ka gani agurin neming fuskarta cike take da farinciki da murna sbd bakaramin rabo akayi ba manya jakunkuna me dauke da hoton baby's har da amfofi acikinsu abun fa yayi sai san barka Mashaallah hk akayi taron suna lafiya kowa ta kama gabanta tare Da dinbin kyaituttuka ..
Duk wani abu da'akeyiwa me jego mahaifiyar nabla tayi mata fiyye da haka domin sosai ta tsuma diyarta da magungunan mata iri iri da km kayan fruit abinka ga basakkwata kowa km yasan yadda mutane sokoto suke gurin maganin mata abun babu sauki .
ko zama nablah tayi aguri sai gurin yajike jagab ta dinga tsiyaya Kennan .
Shiyasa Tun kafin ta dinga jin wani yanayi na bukatuwa da da namiji wasu wurare na budewa ajikinta wata irin muguwar sha'awa ke bijiro mata.
idan deeni yazo kuwa ana film ke faruwa dan taruwa suke su haukacewa junansu suyita tsotsar juna ta ruda shima ya rudata da Salonta me wuyar mantawa.
hk zata shige masa jiki ta lafe tana ya mutsashi da dagula masa lissafi ta rinka manne masa ajiki especially a chest dinsa ta zira hannuta cikin rigarsa byn ta balle masa maballin rigar ta dinga shafa kirjinsa zuwa mararsa tana murza kan nipples dinsa wanda ita har mamakin kanta take idan tana masa wani hk zasuyita ta gudar juna ya kamo ya rungumeta ajikinsa tare da ware kafafunta yayita shafa Kasaanta yana wasa da fingers dinsa cikin kasanta daga karshe km ya zarce da fingarin dinta shi km yasa ta daura hannuta kan joystic dinsa tana shafa masa da laylaya kan a wannan zuwan da deeni yake Yi gurinta ya dinga koyar daita wasanni iri iri masu tsayawa arai duk kuwa randa wani uziri ya hanashi zuwa ta dinga cika Kennan tana batsewa ko kiranta yayi da kyar take masa mgn a wannan wata uku da mama mahaifiyar nablah taso nablah tayi tace bazai yiwu ba sbd ganin tsagwaron rashin kunyar da suke tayiwa mata adaki bashiri ta nemi mlm sule maganar yakamata ace nablah takoma gidanta yace ai daman ido na xuba miki Amman wannan tsarin naki duk shirme ne tunda yarinya tayi arbain zaman ME takewa mutane takoma dakinta man dan ku mata duk abinda aka hada daku sai anga daban.
dan hk mlm salisu da kanshi yayiwa deeni mgn yazo ranar lahadi ya dauketa.
tundaga ranar jummaa akasoma shirye shiryen komawar nablah dakinta
0 comments:
Post a Comment