Yar lesbian ce 1
Zaune take A Harabar makaran tar tasu Inda yanmata Masu ji dakansu kowacce keshiga tsalatsalan Motocin da Aka yiyyi parking dinsu daga dukkan Alamu Hutu Daluban makarantar suka Samu, Haba FEENAT yakamata kawai kizo mu'ajeyiki A kd tunda muma kan Hanyane Asalima Sai munhuce
Kaduna Zamu Huce Zaria Wannan direvern Naki bawani tawowa yayiba idan banda haka ina kaduna ina Abuja Hmmm Wacce Aka kira da feenat Tayi Ajiyar Zuciya tace kausar Kawai ku wuce nagode Zai karaso nan bada jumawaba Kausar Zata kara magana ta kusa da Ita Ta jata Suka bar wajen, Haba Khady Yazaki wani jani haka bakiga har yanzu direvern ta be karaso bane ba Ok don bekarasoba mukuma Saiki shanyamu tunda tace bataso ai ba'a dole naga Kausar bata kara tanka mataba taja mortar Sukabar Harabar makarantar, feenat tana Zaune Awajen har Wajen 10:30 na Safe bini bini taja tsaki mtswwwww daga kan da Zatayi Suka ido2 da besty dinta Leemah Atare Suka Zare Ido😨 Leemah baki tafiba feenat baki tafiba Suka hada baki wajen fada A'tare kuma Suka Sakar ma junansu murmushi feenat ce tace wlh besty kinga har yanzu Haruna driver be karasoba Nakira daddy yace Yana Hanya Ina tunanin Ko Akwai abinda Ya tareshi Shikenan besty Ba wanan ba kinga Nima Yanzu brother na Ya karaso tashi mutafi Leemah tafadi tana murmushi Kai Anya karkuma yazo besameniba Aa basaiki kira daddy kice Ace ya komaba kawai Ouk muje toh Suka kama haryan inda brother din Leemah yayi Perking Suna Zuwa Leema ta buga uban tsalle wooo bro I miss you yawani yatsina fuska Shiga muje nidai ta tabe Baki dan idan da Sabo Ta saba da halin yayan Nata bude baya Tayi Tashiga tamai feenat Alama da Tashiga gaba 😕murguda baki feenat Tayi itama Ta bude baya tashige Shikam cije Baki Yayi yaja fuuuuuuuuuu yabar Wajen Sunatafe babu Mai mgn Acikinsu Saichan feenat tajawo Hand back dinta taciro waya tafara kiran Nomber daddy Ringing......2 tayi yadaga Hello Ummina Haryanzu bekarasaba ne daddy bekarasaba Amma gani Ahanya Wata frind dita zata kaini Ummina kikula dakanki Toh Allah ya tsare Amin daddy Saika kirashi kada ya karasa Ok daughter Shikenan bye Ya Kashe wayan, Juyawa tayi Suka hada Ido da Leemah Ta kashe mata Ido Suka Kwashe da dry Kerr.......... Sukaji Mortar Ta tsaya yja tsaki dalla kufitoh kubani Waje malamai yafada ba Alamun Wasa😡😡
Page......2
Bacewa nayi kusakkobane wai yafada yana kara tamke fuska😡 Leemat ce tayi karfin halin cewa dan Allah my brother kayi Hakuri bamusan Bamusan lafinmuba So Sorry tsaki yaja nikke gayama bakusan laifinkuba kushigomun mota kowacce takama waje A baya ta zauna Sannan wacchan sai wani Magana take kasa kasa Tawani Cika ma mutane kunne Kamar Sakarya ya nuna Feenat dake baya tana Zare ido Sanan ma tukunnah Uban wa kuke ma dariya ne, bro Dan Allah dai kayi hakuri Wlh badakai muke ba Girgiza Kai yayi yakoma mazaunnshi Ya Zauna Still yaki Jan motan Leemat ce ta tabo feenat Alamar ta tashi takoma gaba nuke kafada feenat tayi Alamar taki, Leemat taga idan ta biye ma Feenat haka zasuyi tazama ta tashi Ita takoma gaban Dan tsaki yaja kadan Sanann ya figi motar yatafi.......Yanzu dan nashigo motar da batawa ba shine har wani yasamu Damar Yimun wannan wulakacin wai harni yake cema Sakarya Wlh ba laifinshi bane Laifin Haruna driver ne duk Wannann mgnr Feenat keyi cikin Ranta tadan jaaa tsaki mtswwww Karar wayan shice ta dawo da kowanne daga tunanin dayakeyi dagawa yayi yasa A has free HELLO! Yazeed yazeed Feenat takara nanatawa Aranta karo guda Kuma ta yatsina fuska Hello yazeed wai ko bakajine da Ker ya bude baki inajinka Yusuf Banza Sarkin miskilanci Kanaji kana wani shamun kamshi kamar mace yanzu dai ya'akaiyine Yusuf Yazeed yafadi yana mai Son kaudar wacchen maganar, Kaifa muke jira tun dazu ko kamance dacewa Yau Zamu cin Girkin Amarya gidan Dr Khalid ne Uhum Yazeed Ya fada ban mance ba Yanzu Ina Hanyar Kawo nakusa karasawa Leemat na dauko daga Ckul, Lana nufin yanzu daga Abuja Kake kenan Ummm Yazeed yace Toh yanzu Ina Leemat din take? Keyyyttttt Yazeed ya Kashe wayan Banza parrot kawai yafada yacigaba da Kallon hanya, Kanada Aiki Wannan murtuke fuska kamar wani Zaki ta fadi Aranta tana mai kara jin Haushin Shi, Leemat ce tace yawwa bro Zamu Aje Feenat A unguwar dosa Feenat yace Aranshi Afili kuma Ya kara hada Rai bece kala ba yawwa besty Saiki mishi kwatance ko? Kwatance faaaa kikace besty Ohhh Namance kefa baki iya komai ba Leemat ta fadi A tsokanance bayan 2mnt Karan text Taji tashigo wayanta duba Tayi taga Leemat Wallahi besty kisamo Mafita yanzu Abinda Sakon ya kunsa kenan tunani tayi kadan ganin yakusa Zuwa Unguwar tasu gashi batasan wajeba Kawai number mumy tayi dealing.......Hello Sweet daughter Kun karasone dadynki yace Kuna hanya Tare da friend dinki Eh mumy but turamun Location yanzu na gidanmu Ok daughter cikin minti 2 text din mumy yashigo take ta tura ma Leemat dubawa tayi Tasaki murmushi Aranta tace Kawata kenan wato Ita bazatamai magana ba Hmmmm Ajemai wayan tayi gabanshi bayan ta kunna mai location din bro kashinan kaduba hanya Kallo daya yayi ya kauda Kai Domin ya gano Wajen lokaci kadan baya yayi parking Akomar katafrn gidan su Feenat take G.R.A. yan majilisu Unguwar dosa fitowa tayi Leemat ma tafito Sukai hugging Juna Feenat tasakar ma Leemat kiss A kunatu I will miss you besty Ahhhh Besty Kada kidamu bro zai kawoni tunda yaga gidan, bye ok bye Sukai Sallama har takai bakin kofar Tajuyo Leemat cema Wannan nagode da driven dina dayayi Bye🙋ta nago mata Hannu itama ta Naga mata Afusace yaja motar yabar Wajen, Noking tayi Wani dan dattijo yafitoh ya bude Wayne nace wayane turus yayi Lokaci daya kuna ya washe baki Ahhh nafisa ce Sannu ya Hanya murmushi tayi Sannu Baba hanya Alhmdullah Toto Kawo Kayan Ashiga dasu Aa baba kabarsu Ba nauyi Toh Allah yamiki Albar Amin tafada tana mai Shigewa ciki. Mumy mumy! Naji tana kwala kira..... Wlh kinji nafada miki Leemat duk Sanda nakara zuwa daukoki Kika kara kwaso mun wata Sai jimiki ciwo nonsense Ji yarinyar Sam batada kunya Saikace wata yar'iska kurrrrrrr Cikin Leemat yayi kara Toh Kodai Bro yagabe Feenat YAR LESBIAN CE Kai Ina idan da yagane cewa zaiyi Nafita Harkarta, badake nake mgn bane Leemat firgirgit tayi Sorry brother insha Allah bazai kara faruwa ba Murmushi yayi yace that is my One and Only Sister ajiyar Zuciya tayi tayi murmushi itama Adaidainan Ya karasa Get din gidan nasu dake Unguwar Rimi.......... atare Suka fitoh duka Ur Wlcm Aunty Feenat wasu yaran su biyu suka fada atare daga gani twins ne Thanks twins din mumy kunkara wayo daddy ne yakaro ur wlcm my Ummi Rungumeshi tayi Tnx daddy nasameku lfy lafiya qalau Ummina Mumy ce tace Aisai kumukarasa tunda ba'asan daniba Sai tsabar kirana kuma Ake murmushi tayi takara tayi hugging din mummyn tata I miss You Mumy na me too my daughter Zomushiga ciki kihuta gjy kice Abinci Atare family din Suka shiga gaba dayansu dared Sama Feenat ta Haye tayi dakinta Cike da gajiya tsaffff dakin yake ko'ina Sai kamshi yake komai nacikin Dakin kuma pink ne samular da jakar Hannun ta tayi tacire kaya Ta daukko wani dan karamin towel ta daura tayi toilet.........
Page.......3
Mamy Wlh gaba daya banji dadin Abinda Bro yazeed yayi ma Feenat ba...... kinriga kinfi kowa Sanin halin brother dinki jinshi yake kamar Wani Sarki.........Mamy cewa Zaki kamar dai bake kika haife Shi ba.....Kinci gidanku Maza dai yaje yajiki Mamy tafada tana dariya....Rufe bakin Mamy kenan Saiga Shi yashigo Sum Sum Leemat ta tashi tabar wajen. Mamy ya gida lfy qalau Son ya gajiya Alhmdullah Mamy.....Son kwata kwata banji dadin Abinda ka mawa Su Leemah ba Mamy Ayi hakuri Hakan baze kara faruwa ba....Toh Allah yamaka Albarka Amin mamy ta. Ringing....wayanshi tafara Mamy bari nashiga daga Ciki, Afitoh lafiya my Son....... Hello Yusuf! Haba yazeed Kasan bazakaje ba meyasa kasa muka gaya ma Khalid Zamozo? ni Zani Kawai gajiya nayi gashi Wanka nake So Nashiga. Kawai Kace bazaka ba mana Basai Ka Rainamun wayo ba Yusuf yafada Rai Abace Toh Yusuf duk yanda kace hakane ya Kashe phone din yawurga kan gado Yayi hanyar Toilet.
Haba khady Tunda dai kinriga da kin biyo Nan kibari ki kwana da Sassfe Saiki tafi Kausar dama kinriga da kin Shirya Hakan Shiya kika hada mana kaya waje daya Murmushi kausar tayi tace Aa Kawata Bahaka bane Shikenan Bari nashiga Nagaida Hajiya khady ta fada tana bin Harya kofa.
Gaskiya kam khadija kibari gobe Saiki kama Hanya Amman yanzu idan kikace Zaki tafi dare Zai miki Sosai katsina nisa gareta Hajiyar Kausar ke magana Cikin kulawa Toh Shikenan Hjy Allah ya Kaimu, Amin Yata Kuci Abinci ni bari nashiga daga Ciki, Afitoh lafiya Suka mata Kausar ce ta Maida Hankalinta Kan khady Khadija gsky yakamata kesauke Abinda ke kanki, Kamar Name fa ta fada tana yastina face Haba khady ke kanki kinsan Feenat tawuce da Ajinki Amma kinbi kin tsane ta why khdy why? daga mata hannu khady tayi Alamar dakata✋ Malama Abinda ki keson gaya mun kenan yasa kika Ajeni gidanku Haba khady ke haryanzu gsky ce baki So......katseta khadija tayi Yayin da ta tashi tabi Hanyar dakin Kausar. Tabe baki Kausar tayi tace Allah ya kyauta. dealing...number Feenat tayi Hello my Kausar Hy Feenat I miss u! Me too Kausar bawani Feenat idan kinyi missing dina me ya hana ki kirani Sorry Kausar kina Raina Wlh gjyn Skul ce, hakane kuma Feenat mayi waya Anjuma Toh Allah ya kaimu Amin Kausar tafada takashe wayan.
Atare yaran Suka Turo kofar dakin Aunty Kausar mumy tace Zata wajen daddy muzo muyi miki fira Mubeen Yafadi Aranta tace Haka Suka iya kaikuma kanuna Kana Son Auren Anki Maka Ai duk Wani Hali danajefa Rayuwata Iyayena ne Sanadi Kinji Mubeena ce ta katse mata tunani.....kinji Aunty feenat Ajiyar Zuciya tayi tace twins din mumy kaina ciwo yake kubari gobe Sai muyi fira mai yawa yanzu kuje kuyi bacci gobe kunada Skul,,,,,,,Mubeen ya tsuke fuska ni Awajenki Zan zauna gobe bazani Skul ba mubeena tace nima haka dafe kai Feenat tayi tace kataba su Sumaka kwari. Waye keson Yazama Soja irin yaya Nazir Nine mubeen ya daga Hannu Sama☝ waye keson tazama doctor nice mubeena itama ta daga hannu yawwa twins dina duk mai so yaje ya Kwanta gobe muyi fira mai yawa 🏃🏃🏃da gudu Suka fita Suna kiran Ladi Mai Aikinsu........ Tashi itama Feenat tayi taje tayi brush Tayi Shirin bacci
Cikin bacci taji Kamar Ana tsikarinta lokaci daya kuma Taji Abin nakara damunta Tashi tayi ta Zauna Innalillahi tafada da karfi Dan ko ba'a fada Mata ba Tasan Sha'awar tace ta tashi wayarta ta lalubo tashiga kiran Leemah Hello! beaty baki bacci ba kenan Leemah I need your help pls. temako kuma name? Leemah kinsani Wlh Yanzu nakara missing dinku keda Kausar toh Sarkin Sha'Awa yanzu Itace ta tashi kenan Eh Leemah Dan Allah kitaimaka kizo Zare Ido Leemah tayi kamar tana ganinta kinsan cewa Mamy Bazata Bari ba dare nefa yanzu mekike tunanin Zan gaya mata Shikenan Leemah tunda baki iya dubaraba keeetttt ta Kashe phone dinta turo kofar Akai my daughter baki bacci "Ummm" mumy Tashi muje dadynki keson magana dake yunkurawa tayi zata tashi takasa "Subhanallah" Feenat bakida lfy ne? Eh mumy yanzu yafara, meke damun ki? MARATA. Ko period ne? Aa mumy nayi fa,,,,,, kallonta mumy tayi Sosai tace Sha'awar ce kenan ta tashi nace miki kirinka Azumi Kina karanta qur'an Akai Akai bari na kawo miki Lemon tsami kirinka lasa tafita. Hawaye Feenat tafarayi Wai Ace yanzu Wannan Uwata ce tasan matsalata Amma Akan wani kudirinsu na Karatu An tauyemun Hakkina😢😢 dan tsaki taja mtswww wai lemon tsami.....
"Mamy" "Mamy" wannan kira Haka Leemah meye ya faru Mamy Shikenan yau na kade..... mai yafaru kuma? Mamy Uncle Adam yabamu Assignment Mamy Cewa yayi duk wanda beyi Ayau ba Allah ya'isa Mamy kuma kece maijan Hankalina Kan kada na Aikata Abunda Za Amun Allah ya'isa... Hakane daughter Amma dare yayi dakinyi bacci gobe Saikiyi, Mamy Allah ya'isa fa yace. Hakane kuma Jekiyi Toh Allah ya temaka Mamy tafada tana tafiya.....Mamy book dina na biology yana wajen feenat. Saiki bari Sai gobe kenan mamy dan Allah ketaimaka na Amso Ayau......Haba Halimatu Bakida Hankaline dare nefa Mamy pls Dan Allah bana Son Allah ya'isan Nan ne.........Saikije ki kira yayanki yakaiki Tsallen murna tayi tace nagode mamy. but Dan Allah kigaya mishi dakanki innice bazai yarda ba, jeki kice ni Nake nemanshi Toh tace takama Hanyar part dinshi Assalm. Wai kazo yanzu inji mamy, Uban me kuma kikace nayi bance komai bafa. tace Kazo Yanzu bin bayanta yayi Suka Fita. Mamy gani. "SON" Halima Halima Zaka kai gidan kawarta ido yazaro Mamy duba time fa.....Umarni nabaka fita yayi Afusace Leemat tafi bayanshi. Tayi mamakin da har Suka karasa gidan Su feenat be tanka mata ba mai gadi naganinta yabude mata tashiga feee yazeed yaja motarshi yabar wajen Assalm Alaikum. Wa'alakmssalm Mumy da tafito kitchen yanzu ta Amsa Sannu mumy, yawwa Halima Cikin dare? Murmushi Leemah tayi tace mumy inata kiran wayan Feenat bata dagawa Shine Mamy tace nazo Naga ko lfy.......Ayya batajin dadi ya mamayn taki? Tana Lfy tacema Agaida ki ina amsawa muje tana Sama feenat din tare Suka haura Sama.......Mumy tace Halima Shigar mata da lemon tsamin Nan Ni Zan Kwanta toh mumy Saida Safe yawwa daughter. kema ki Kwana dasafe driver ya kaiki Toh Mumy.
Tura dakin tayi tashiga kwance ta hango Feenat ta daka mata duka tashi Sarkin Sha'awa bude ido feenat tayi Tamayar ta lumshe leemah Ashe Zakizo eh kinsan bazan Iya barinki A'irn Halin Nan ba Hakane feenat tafada yayin da tajawo Leemah jikinta, bakinta tasaka cikin na leemah lokaci daya tafara tsotsan lips dinta ta kamo harshenta tarinka tsotsan shi kamar lollipop take leemah takamu tafara Mayar da martani ciremata yar karamar Rigar jikinta tayi Brest dinta Suka bayyana Tarinka Shafasu Tana murzawa tuni Feenat tafita hayyacinta Dan ko mayarwa bata iyawa,,,,,,, Hannu Leemah ta tura cikin pant dinta tarinka murzawa nishi Kawai Suke Ahhhhhh washhhh kusan minti 30 Sukayi Ahaka feenat ta kankame ta Alamar Tasamu tayi riles.
Page.....4
feenat ce daure da towel gawani karami A hannunta tana goge gashin kanta da Alama daga wanka tafitoh wajen makeken bed din dake tsakiyar Dakin ta nufa, Leemah Leemah tashi kishiga nafitoh. Haba Feenat kaina Sai yayi ciwo ni kibarni da Asuba Nayi Leemat tafada cikin muryar bacci Feenat bata Kara bi takanta ba ta dakko wata doguwar Riga tasaka tajawo darduma tafara gabatar da nafilfili Raka'a 4 tayi ta daga hannu Sama tana kwararo addu'oeh take! Abinda ta Aikata dazun ya bijiro mata Azuciya kuka mai tsanani tashiga Rairawa Tana, Ya Ubangiji ka gafarceni Kan Abin nan danake Aikatwa ya Allah Kasani Nauyina kan iyayena yake wajibine Su magancemun matsala ta Amma Suka banzatar Dani gashi nafada kan turbar Shedan Ina Aikata Abu mafi muni Agareka, ya Sarki mabuwayi mai Shiryar da bawaYayin da yaso ya Allah Kashiryar da Zuciya ta Nasani nidin mai girman Zunubice gareka Ubangiji ya Allah badan niba ka gafartamun Zunubaina kakuma ganar da Mahaifana,,,,, ya Allah narokeka Dan girmanka Dan Albarkacin fiyayyen Hallita Ka yaye mun yawan Sha'awar nan Ka Kara daurani kan Hanya maidaidaciya......wani Kuka ne ya kwace mata 😵😵kuka take Sosai na nadama Abinda take Aikatawa,,,, Haba Feenat wan nan wani irin Abune kin Hanani bacci da ihun kukanki Leemat tafadi Rai Abace... Dan Allah Leemah kitaso Muyi magna feenat tafada cikin dashashshiyar murya Kinga ni ba'inda Zan Sakko kibarni nayi baccina tunda ke kika Jawoni, Abinda Zaki fada din yawuce kice kinyi Nadama Kuma Sau nawa kina Alkawarin kin bar lesbian,,,,,,wannan kukan naki dashi Gara babu ki tsaya idan Nadamar gsky Zaki kikai Zuciyarki nesa,,,,,,,,bare kuma Nasan ba nadamar bace Dan Wanda besan Halinki ba Shi Za'a ba labari. Toh nima dai NADEEYA ban San Halin Feenat ba kuma masu karatuma Zasuso Suji wacece feenat.......
SHIN WACECE FEENAT NE
Alhji Ibrahim dattijo mai dadtaku Tare da matarsa Nafisa Asalin fulanin yola ne Suna Rayuwarsu cikin jindadi da ganin girman Juna Sunada yawan Arziki SHANU RAKUMA da dai wani dabban kiwo na fulani Allah ya Azurtasu da haihuwar Yara 3 Nazir Shine babba Sai Aishatu Sai Sukai Auta Umar daga nan haihuwar ta tsaya musu, kusan kansu duk daya dan ita Nafisa Akai Akai take haihuwar ta, duk da cewa Fulanine Iyayen su basuyi kasa a quiwa wajen ganin yaran nasu Sunyi Karatun Islam dana Zamani ba, Sun taso da hazaka Nazir da Aishatu Aji daya Suke Inda suka wuce Umar da Aji daya,,,,,,, bayan Su Aishatu Sun Kammala Secondary dinsune Tasamu miji tayi Aure Anan yola inda yarage Nazir da umar wanda tun tasowarsu suke Son junansu Ahaka Nazir yaki ci gaba da karatunshi cewa Sai Umar ya Zana jarabawarshi ta Secondary Sucigaba tare,,,,,,,,,Masha Allah bayan lokuta Sun Samu addimetion Suka tafi makaranta a .A. B .U . Zariya,,,,, Hutu ke kaisu garin yola Suna matukar temakon iyayensu duk dacewa babu Abinda Suka nema Suka Rasa hutun Karshe dasukai Suka koma yola Anan ne Nazir yasamu mata yayi Aure yacigama da business Alokacin Aishatu tana da yara 4 duk Maza Anso Umar yafito da mata Ahadashi da Dan uwanshi yace Shifa Ina karatu mai Zurfi yake So yayi inda yasha banban da Sauran yan uwanshi kenan,,,,,,,Alhji Ibrahim bai cika takuraba indai wajen karatune Shiyasama ya Amince da Hakan, Umar kaduna yakoma don cigaba da karatunshi wanda da ker Nafisa ta Amince da Hakan yakanje ya dubasu Akai Akai, karatu yake Sosai wanda yasamu degree har biyu Anan ne ma ya yake Shawaran yafara business gun Wani Mahaifin Abokin Shi Alhji Aminu,,,,,,,,Suna gudanar da komai cikin Amana da gsky lura da Hakan ne watarana Alhji Aminu ya kirashi...... Umar badon komai na kiraka ba Nalurada irin Amanarka da Iliminka Da nagartarka Sannan Kwanakin baya dakuje yola da Sulaiman yabani labarin irin mutumcin iyayenka,,,,,,,,Don Haka na yake Shawaran Zan baka Auren Yata "Hafsat" Sai Asan nan Umar yadago Kai yace duk Abinda Ka yanke daidaine Baba Nasan bazaka taba cutar daniba Nayi matukar farin ciki duk dai Nasan cewa daman bazanji Kunya ba. Kaje Zanje yola muyi magana da Mahafinka Kafin nan Zaka fara Zance da Hafsa dan kufahimci Juna Yace toh Baba Alhji Aminu yaje yola Mahaifan Umar Sunyi farin ciki matuka Duk dacewa Sunso dan nasu yayi Aure a yola cikin yan uwanshi, Amma basu nunaba Sabida Alhji Aminu dattijon kwaraine bayan wata biyu Umar da Hafsa An fahimci juna inda Suke gudanar da Soyayya mai tsafta abinka da masu ilimi Acikin watan kuma Aka Saka Aurensu Ranar Wata juma'a misalin Karfe 10:00 dunbin mutane Suka Sheda Auren Umar Ibrahim da Amaryarshi Hafsat Aminu, Su Aishatu dasu Nazir duksunzo kaduna Kasancewar Agidan Alhji Aminu Ake gabatar da komai Hatta Su Hajiya Nafisa da Matar Nazir data haifa yara biyu mace da na miji duka suka dungumo Anci Ansha Anyi komai cikin Mutumci. Wani katafaren gida da Umar yagina A Unguwar Dosa Nan Aka kai Hafsa Gidane kato nagani nafada komai yayi👌
Bayan Shekara daya
Hafsace Zaune da katon Cikinta Tana duba wasu takaddu Sai rintse ido take tana cije baki daga dukkan Alamu batajin dadi Abun taga Saici gaba yake tayanke Shawaran kiran Mijinta Awaya. tana Sanar dashi yatawo Dan dama banisa yake da gidaba Sabi da ita kasancewar Soyayya Suke Sosai danko Sharokan Sai Haka lol Hafsa machace yar boko Ga Kyau Kota'ina ta hadu Ga iya Zama da miji Shiyasa Suke cin karansu ba babbaka. Yana ganin Halin da take Ciki ya temaka mata Suka Shiga mota Sai Asibti Cikin mintuna da bazasu wuce5 ba Aka fito da jariri Kato farisol kyakyawa dashi. Wayyo zokaga murna wajen masoyan nan biyu dama duk Wasu masoya nasu. Ahaka Aka Sallmesu Suka wuce gida cikin farin ciki Aishatu Ita tazo ta Zauna da Hafsa har'akai Suna Ranar Suna yaro yaci Suna NAZIR Sunan yayan dadyn shi kenan. Bayan watsewar taron Suna da dare yana Zaune Suna fira Ga yaronsu sun rungume daga yau dai Hafsa kin koma "Mumy" murmushi tayi tace kai kuma "daddy" ba Ahaka Zamansu yacigaba da tafiya... yaron yanada wayo Sosai Dan haka yana Cika 3years Suka Sashi makaranta dama gaba dayansu Burinsu Kenan yana kokari kuwa matuka Bayan yacika Shekaru biyar ne Mumy ta tashi da wani Zazzabi mai tsanani Ai ba bata lokaci Suka wuce Asibiti gwajin farko ya nuna tana dauke da Ciki Wata 4 Murna Sukai Sosai dawowarsu kenan daga Asibiti Aka kirashi daddy A waya cewa Allah yama maihafinshi Rasuwa gaba daya Nima danake Typing Saida naji Ajikina Kasancewar tsowo mai Mutumci yarigamu gidan gsky😵 Tuni Suka Shirya Suka dunguma yola Harda iyayen Hafsa watoh Alhji Aminu da Hajiya Amina mahaifiya gun Mumy Kenan. Sunje inda Achan wasu Sukayi dan koke kokensu bayan Kwana bakwai Kowa yadawo Akabar Inna Nafisa Achan Haka Suke kiranta. Sundawo gida lafiya inda mumy tacigaba da Rainon Cikinta daddy yana kula da ita.
Page......5
Bayan Rasuwar Alhji Ibrahim Kamin su daddy Sutawo bayanda basuyi da Inna Nafisa kan ta biyosu ba Amma firrrr taki, Acewarta inda Kasar mijinta take itama Nan Za'a Saka ta idan tasu tazo. bayan Wata Tara da Wani yamanci Mumy Suna Zaune Suna fira da Matar Sulaiman Aminin daddy kenan, Dan Su daddy Tare Suka taso Sunayin komai da Sulaiman da Wani Abokinsu Ahmad duk dacewa Ahmad ya Rigasu Aure Dan Saida yayi Aure ya haihu ďa Namiji Sannan daddy yayi nashi Auren Saikuma Sulaiman yaya Awajen Mumy kuma Aboki Awajen daddy Shima yayi Nashi Auren. Mumy Takasance irin matan nan ne masu tattalin miji wanda Ko Zumunci basucika yiba Sabida kula da mazan su dan Haka bata zuwa ko'ina daga gidansu Sai wajen Aikinta dan Cikakkiyar barrister ce, Tana dan Zuwa YOLA wani lokacin idan daddy Zaije, ba kasafe tacika Ziyartar Maryam Matar Sulaiman ba Saidai Ita maryam din ke yawan Zuwa mata, ko Sau daya Kuma bata taba tunanin Zuwa gidan Fatima matar Ahmad ba itama Kuwa fatiman tace bazatazoba harsai mumy taje mata,,,,,kullum cikin Sa Rana take Amma ina,,,,,,,,hakan ce takasance Ayau ma tare Suke da Maryam Wacce Nazir yarada ma UMMA Tana ma mumy korafi Wlh kedai Hafsa bazaki chanza haliba kullum kina gida Kamar daddawa da Anyi magana kice daddyn Nazir na Gari Kamar dan ke kadai Akai miji, Kai Maryam kedai kullum maganar ki kenan idan ban Kula da Shiba waye Zai kula dashi beda kowa Anan garin wanda ya wuce ni da Nazir Sai wannan Cikin Nawa Uhum Toh dan Allah badole na Zamemai gata gaba da baya ba? Kizama Shi yazama ke Kawai karshen magana kenan Maryam tafada tana gyara Zamanta,,,,,,,,, Bari Nakawo miki Abinci kici Amma maganar nazama Shi yazama ni na nawa kuma Ai munzama tsoka daya mumy tafada tana bin Hanyar kitchen,,,,,,,Kayattacen Abincin da ta dafa ma daddy Aciki ta iba ma Maryam, tanaci Suna fira, Umma ce tace wai kuwa kinsan Fatima ta Haihu yau kwana hudu kenan, Kai Haba mai Aka Samu? Tahaifi diya mace, kai tubarakallah Allah ya Raya.Amin Umma tace Sannan Takara dacewa Saiki kishirya Kije Barka, Kai Maryam bakida tausayi wan nan Cikin Nawa Haihuwa ko yau ko gobe Zakice naje barka, Uhum haka kawai ma Anki Ziyara bare yanzu da Akeda Hujja mai Karfi. Kyadai ji dashi Ai Zan kirata namata barka. Allah yasa. Ni Zan tafi, haba Maryam tun Yanzu? Eh Ai nafi Mara Zumunci, ki kwantar da Hankalinki nima Zanzo. Muna jiran Ranar da babu. dahaka ta tashi Mumy taimata Rakiya.
Cikin daran Ranar Nakuda tazo ma mumy, tun tana daurewa Har takasa ta tashi daddy dake bacci cikin Rudu ya dau key din mota ya temaka mata Suka fita yasata Amota yadawo ya dau Nazir dake bacci Sai SULTANA HOSPITAL dake nan Unguwar Dosa KADUNA Mumy tasha wuya A wannan haihuwan dan saida Aka kwashi Awanni tana Abu daya daddy Zufa kawai yake yana kaiwa da komowa, daker ya'iya daukan waya ya kira Sulaiman ya Sheda mishi daga bisani ya kira Ahmad, Kusan atare Suka karaso Sulaiman da Maryam, Sai Ahmad wanda matarshi ta Haihu badaman tazo, Zuwan Su Kuma yayi daidai da fitowar wata nurses tasheda musu Anhaihu diya Mace, Atare Suka Shiga dakin Suna ma mumy Sannu yayin da daddy ya dau yarinyar, SUBHANALLAH tsarki ya tabbata ga Allah wanda da ikonshi yake Samar da Abu mai Kyau da Mara Kyau, daddy ne yafada yana nunama Ahmad (Abba) dake kusa dashi babyn, Sunyaba da kyan babyn Dan Ajin farkoce wajen Kyau. Ahakadai washe gari Aka Sallamesu Sukayi gida, Kai Alhmdullah duk dacewa Mumy bamai Son Zumunci bace mutane Sai zuwa barka Ake, Sabida kyan jariryar ke rudan wasu yarinyar tun tana jaririya da farin jininta. RANAR SUNA yan YOLA duk Sun Hallara Mutane kota'Ina kowa farin ciki yake Anci Ansha taron Suna yatshi lfy inda Yarinya taci Sunan Kakarta mahaifiyar babanta wato NAFISA Zasuna cemataa (Feenat) Haka Rayuwa tacigaba Mumy na kokari wajen faranta Ran mijinta yara kuwa Tasamu wata dattijuwa Ladi ita ke kula dasu.
Lokacin da Feenat tacika Shekaru Uku Alokacin Aka Sata makaranta nursery "iman Academy" dake Unguwar Dosa, makarntar hade take da Islamiyya, Idan Sun tashi 12am Sai suke Shiga Islamiyya 5pm driver ke daukosu lokacin Nazir yana primary6 Mamah LADI itaa ke kula da komai nasu, Feenat tana Maida Hankali yarinayace mai hazaka aduka bangare biyu, Bawanda feenah ke Kulawa Dan ita din yarinyace marason Hayaniya, Kawarta daya Halima Itama Sabida kokarinta Yasa Abotarsu tazo daya da Feenat, BAYAN WANI LOKACI Abubuwa da dama Sun faru, Feenat Sun Zana jarabawar fita daga Secondary. Ayayin da Suka kara Shakuwa da Kawarta leemah Sosai, daddy ya tura Nazir Kasar Turkey Achan yake cigaba da Karatun inda yake Karatun Soja, Alokacin Feenat ta damu kan rabuwarsu da yayanta Sabida Shakuwar dake tsakaninsu, Leemah Itama tasanar da feenat cewa brother dinta yaje karatu America yana karatu Doctor, Mumy takara Haihuwa inda ta Haifa Twins, Mace da namiji namijin yaci Sunan kakanshi daya Rasu Ibrahim Suna kiranshi (Mubeen) inda macen taci Sunan Mahaifiyar Mumy Aminatu Suna kiranta (mubeena) Anyi Shagali Sosai. Haryanzu mumy batasamu taje gidan Fatima matar Ahmad ba............Feenat basu hada iyayensu Kawanceba ita da Leemah Acewarsu Koda Zasuyi Karyar fita yawo sarinka karya dazuwa dagidajen juna tunda kowacce Agidansu Ansan irin Shakuwar da kawayen biyu Sukayi
BAYAN SHEKARU.
Wata tsaleliyar budurwace wadda Aqallah Zatai Shekaru 18 duguwace ba irin Sosai ba,farace mai matsakaitan idanu Samanshi dauke yake da dogayen gashin idanu, girarta Aciki take ta kwanta lufff, Tana da diri batada kiba Kuma ba Arame Take ba, kirjinta cike yake idan baka Zata ba Zaka Iya Cewa Wata mai yawan Shekaruce. fuskarta dauke take da dogon Hanci yayin da pink din bakinta y kasance karami, kwance take kan makeken gadon dake manne jikin ginin dakin tana danne dannen waya da Alama Chat take Ringing..... dayar wayar dake kusa da ita tafara. Hello besty daga dayan bangaren Aka amsa Hy feenat ina hanya zan zo gidanku fa, dagaske? Allah da gaske,Saikin karaso ok. Ba'afi Minti20 tsakaniba Saiga ta tashigo, turo Kofar tayi, dasauri Feenat ta Sakko Suka Rungume Juna, leemah Shine Baki gayamun Zakizoba, Sorry Kawata magana Zamuyi, Inajinki besty, Hawaye tafara Feenat yanzu Rabuwa Zamuyi, Zaro ido feenat tayi tace Akan me?muda muka Shirya yanda Rayuwarmu Zata kasance,kokinmance cewa komai namu iri dayane kinsan matsalata nasan taki,ke kikace Hatta Ranar aurenmu Rana daya zekasance, Leemah kin mance Ranar da kikacemun Mu Auri miji daya kokuma Mu Auri wa' da kani duk Dan mukasance Tare. Leemah duk kinmance yau kikemana Zancen Rabuwa. dan Allah Feenah ki kwantar da Hankalinki Ki Saurareni. INAJINKI besty Abba nane yasmamin Wata School Of Nursing A Abuja Shine yace Zai turani, Sabuwar Makarantace yanzu take tashe Akace. Hmmm Ajiyar Zuciya Feenat tayi tace Dan wan nan besty Shine kika dagamun hankli indan Wannan Zanmawa daddy magana Nima yasani Skul din Ai dani dake mai Rabamu Sai Allah.
Page....6
bayan tafiyar Leemah. fitowa tayi da niyar Samun daddy tafada mishi, mumy tasamu Zaune a parlor ga Twins gefenta bangare guda wasu takaddune birjik da Alama Akwai Abinda take nima cikinsu. tawowa tayi ta Zauna ta jingina da jikin Mumy, Mumy Sannu, yawwa my daughter Ai najiki da Halima Shine bata Shigo yau ta gaidaniba, mumy Tana cikin damuwa ne wai Acewarta yau Zamu Rabu, kinsan ma wai menene dalili?? "Aa"mumy tafada tana girgiza Kai, Mumy wai Akan Abbanta ya Sama mata Skul a Abuja,,,,,,, 😊Murmushi Mumy tayi tace Ai dole tace Za'a Rabaku tunda ganin Juna Zemuku wuya, da Sauri Feenat ta dago kanta, Mumy Zuwa nayi Nagayama daddy nima yakaini Skul din Ai, Ke dai kincika Son Rigima. daga.....koda yake aima kunfi kusa da dadyn naki mumy tafada tana daga kafada🙅 Yayin da tacigaba da dube dubenta. Feenat Maida kanta tayi kan tv dake manne jikin bango, wani American film Akeyi a Mbc Action, lokaci daya ta rintse idonta ganin Abinda turawan ke Aikatawa, mace ce Rungume jikin Wani Saurayi Sanye da wata yar riga wanda komai na jikin ta Abayyane yake, shafa jikinta yake Very Slowly, Yayin da bakinshi yake cikin nata yana tshotsa Kamar yasamu Sweet, itakuma Hannu daya tasakalo ta bayanshi tana Shafawa tanayi tana lumshe ido,,,,,,,,, take wani Abu ya Ziyarci Feenat wanda takan Dan jishi lokaci Zuwa lokaci, Kafafunta tahada ta matsesu waje daya Dan wani Abu takeji kamar yana yawo jikinta, Remote tajawo ta chanza tasha Zuwa Zee Aflam, Cikin Kasan Zuciyar ta kuwa cewa take Aure Zanyi Gaskiya tunda malan musa yagaya mana idan Kaji makamancin Haka Sha'awa ce kuma wajibine kanimi mijin Aure idan Kaji Zaka Cutu.
Sallamr dady ce ta dawo da Feenat daga tunanin da takeyi, Amsawa Sukai Yayin da mumy ta tashi tayi hugging dinshi barka da dawowa, ga bashi ba nima da Aure nayi duk lokacin da mijina yadawo Haka Zanmai maiyuwa bazanji Abun da naji dazun ba, Feenat ke fira da Zuciyar ta, Ummina yau ba magana, cikin inda inda tace Sannu da zuwa daddy, yawwa Ummina ko bakijin dadine? Jiranka take Shiyasa tayi wani kamar Mara gaskiya mumy ta fada tana ciremai takalamin kafarshi, my Kinji mai mamynki ta fada ko fira Zamuyi, daddy kaci Abinci ka huta Saina fada maka, wayaki ya Saurari Zancen Umminshi cikin Zumudi? fadamun kamin naci Abincin, Sunkuyar da Kai kasa tayi daddy dama Akwai Wata Skul Of nursing da Aka bude a Abuja Abban Su Leemah Chan Ze kaita pls daddy inason Skul din nima. Shiru nadan lokaci daga bisani daddy yace ban Amince ba, nace ban Amince ba Ita Leemah din dako iyayenta bamu Saniba Zakice komai Sai kinyi irin nata, indai nine na haifeki ban yarda ba inada burin nayimuku komai dakuke bukata Amma banda wannan, daga haka yatashi ya Haura Sama, tashi mumy tayi Zata Bishi Feenat ta Rukota mumy pls kisa baki yabarni kinfi kowa Sanin irin Shakuwata da Leemah, Mumy tun muna yara fa muke......kuka ne ya kwace mata, dafa kanta mumy tayi tace my daughter am sorry to said you kibi Umarnin mahafinki, Sabida kinfi kowa Sanin dadynki yafi kowa Son yaga kunyi karatu kunzama wani Abu, tunda kikaga bai Amince ba kiyi hakuri Kawai, daga Haka mumy ta tashi. da gudu itama feenat ta tashi ta Haura Saman daret dakinta tayi tafada kan bed tana kuka mai tsuma Zuciya, Saida taci kukanta Mai isarta tukun ta jawo phone dinta tafara dealing number Leemah, HELLO.... my besty dafatan daddy ya Amince Kinga harna Suyomana wasu kayayyakin Amfani kinsan Anko Zamu rinkayi yanda Zamu birge duk wata maijin kanta Askul din nan, Ke Kinga wani takalmi duk yanda Akai kwanan nan yafito yayi Kyau, Ke mayyar Abaya nasiyo Miki Su birjik, idan Kinga Akwai Abunda kikeso ki hanzarta gobe Kije kasuwa, Dan Wlh harna hangomu A Skul din nan, Skul dinfa ance sai Dan wane da wane Kinga yanzu Za'a kara Sanin muba yaran Kananan mutane bane. besty kinbarni inata Mgn kice wani Abu mana.
Ajiyar Zurciya feenat tayi yayinda taji Son Kawarta ta yakara dira mata A'zuciya, Cikin dashashiyar murya tace leemah daddy.......aitun kamin takarasa Leemah tace kada kice mun be Amince ba Yanayin muryanki ya nuna Hakan. Wlh Leemah yace "Aa" Itama mumy namata magana wai nabi umarnin Shi hakan Shine daidai. Innalillahi ni Yanzu Zan iya cigaba da Rayuwa batare dake bane, Ina nima Nahakura da tafiyan nan duk Skul din dazakishiga nima ita nakeso. Karki haka Leemah kamata yayi kisa Abba yazo yasamu daddy ya fahimtar tashi. Wow inasonki Feenat kin Iya hango Abu mai Kyau, Bari Anjuma Zan Samu Abba na da maganar Allah yasa idan yazo daddy ya Amince, Amin dai my Leemah Nima inasonki. Nariga na dade dasani ai kawata, besty bari nacigaba da hada mana kayanmu, kincika Zumudi. Keko Ai dole Muma Zamu Zama manyan yara, Atare Suka kwashe da dariya. Jeki karasa saimunyi waya Anjuma. ok.bye.
Tunani Kawai take Azuciyarta barkatai Shin Anya daddy ze'amince kuwa? Kodai nakira Leemah Nace tabari, Maiyuwuwa Karatuna A kaduna Shine yafi Alkairi Shiyasa daddy yaki Amincewa, Toh Amma ai karatun zaifi dadi Idan kana Tare da kawarka wacce kuke Shawara da ita tunda Ita mumy bata fiye Zama Ai fira da Itaba. Kai kada na takurama Zuciyata kan tunani bari nabari Leemah ta turo Abbanta Kawai. remote tajawo ta kunna t.v. take Abinda tagani dazun a Mbc Action ya fado mata Arai, Haka kurum taji tana Sha'awar cigaba da kallon film din, bari nagani ko basu gamaba tafada cikin Ranta tana chanza Tashar, Oh Wow basu gamaba, 😨Kai basu gama irin wannan wajenba kenan film din duk haka yake, dukufa tayi tana kallo Sosai har'inda wasu turawa Su biyu Suke fira da Harshen turanci, dukansu mata ne, dayar ke fada ma yar'uwarta irin Son da take mata, Kallmar So karara take Zayyanemata kamar irin Saurayi da budurwa din Nan, take kuma tajawo ta Suka koma Suna fuskantar juna tana cigaba da gaya mata tana Shafa fuskarta, dayar ce takara matsowa Sosai ta hade bakinsu waje daya tafara kissing dinta Sosai, Feenat lisp dinta ta kamo tafara lasa jitake kamar itace Akema hakan, turawan Nan Sun lula har takai ga Sun cirema juna kaya, Shafeshafe Kawai Suke Suna nishi, Wayyo Allah feenat tafada tana kankame jikinta, dama Ana irin haka mace da mace Toh koshine lesbian din da naji Ana fada Kai Subhanallah Ance ubangijimu Allahu yana fishi mai tsanani damasuyi irin Wannan harkan. Kashen TV tayi gaba daya tafara istigifari na kallon da tayi, bangare guda jikinta Sai Rawa yake Wani Abu takeji yana yawo A jikinta, kawai itama Sha'awan take takasance jikin namiji. turo kofar Akayi cikin Sallama, Kasa amsawa tayi Saidai yunkurin tashi da takeyi takasa, my feenah fushi kike haryanzu jifa idonki Yanda Suka kumbura Alamar kuka kikai Sosai, Mumy banjin dadi ne, Sannu daughter na kada kisa Abun Aranki Kinji, Allah yasa Hakan Shine Alkairi. Mumy jitayi Feenat bata amsaba take kuma ta lura da yanda jikin yar tata yake Bari taba jikinta tayi tace Zazzabi kike feenah, Ummm mumy. Ya Allah. Bari nakira dadynki muje Asibiti fita tayi Suka Shigo tare da daddy taba jikin yar tashi yayi yaji kamar wuta, maza Hafsa temaka mata mukaita Asibiti, Cikin kankanin lokaci Mumy tashiryata Suka nufi Asibiti dama Mubeen da mubeena LADI ke rainonsu.
Ruwa Aka Saka mata bayan bincike da doctor yayi Akanta, fitowa yayi yace daddy ya biyoshi Office. Alhji na tabbata din Kai mutum ne mai Hikima, Amma ya'Akai yarka ta Dade Abu nadamunta baka gaggauta Sama mata mafitaba, kodayake Kai namijine ba Lallai ka lura da Hakanba Amma mahaifiyarta tayi babban Sakaci. dacta meyake damun yata yimun bayani Menene matsalarta, Alhji yarka tana fama da Sha'awa me karfi wanda Ayanzu kamata yayi Asama mata Mijin Aure, ✋dakata dacta yar Tawa guda Nawa take, duka duka shekarunta 18 ne me tasani, A karatunma me tayi? dacta inaganin Akan maganar Barinta tayi karatu A Abuja dabanyi bane, Shiyasa tasaka damuwa Aranta, Amma yanzu na Amince mata taje tayi. daga Haka ya tashi Dr nakiranshi ya fahimtar dashi Amma inaaaa tuni yabar Office din, Zuwa yayi yace ma Su mumy Sutaso. Har bakin inda motarsu take dr ya biyosu daddy naganinshi yatada motar yabar wajen, Cikin mota daddy ke Sanar da mumy Abinda Dr yafada mishi........Shiru Mumy tayi nadan lokaci daga bisani tace Bana tsamanin Haka Feenat guda Nawa take, mganar jiyace tasata Zazzabi kawai. Atoh Nima Haka Nace Amma yanzu Na Amince kawai Zan Kaita makarantar, tunda Ajiya nayi Searching naga makarantar Mata Zalla ce nidama makarata da mazan nanne banaso. Aishikenan Hakan ma yafi mumy tafada. Feenat duk tanajin Abinda Suke fadi bangare daya taji dadin Amincewa da daddy yayi game da karatunta, Yayin da bangare guda kuma takejin bakin Cikin kin yarda da maganar Dr da daddy Yayi. Kamar tabude Baki tace ita tanason Auren Amma Ina bazata iyaba.
Suna isa gida ta dau wayarta ta kira Leemah tana dagawa tace besty kada kifada ma Abbab. Meyasa kikace Haka besty? Sabida daddy ya Amince, 💃💃Tsallen murna Leemah tayi tace Alhmdllh. Amma ya A'Kai ya Amince? feenat Sanar da leemah Komai tayi Abinda ya faru har kan kallon da tayi da zuwansu Asibiti da duk yanda daddy yama mumy Bayanin Abinda da Dr yace mishi bata moye Komai Acikiba, Hmmm Nifa dama Feenat nadade ina tunanin kinada Sha'awa Sosai, Sabida Na lura da Abubuwa da yawa game dake. Zan gaya Miki Wasu Abubuwa ne Amma saimun Hadu. Shikenan Saimun hadu din. Washegari daddy yaje Abuja Yayi ma Feenat komai kan karatunta zuwa kawai ya Rage mata, Sunje da Mumy kasuwa Sunyi Siyayya mai yawan gaske inda kusan Komai tare take dakko musu da Habibiyar tata Leemah. Bangaren Leemah ma Komai ya daidaita Rana daya Zasu fara zuwa Sun yanke Shawara kan cewa drivern Su feenah ne Zai kaisu domin Su tattauna game da matsalar feenah.
Page.....7
Feenah ce Sanye cikin wani material milk colour yana dauke da Ratsin Brown Ajikinshi, dinkin Riga da Siket ne yazauna tsam Ajikinta Mayafi ta daura Akai Brown colour Haka takalmi da jakarta duk Brown ne, Wani Dan Siririn Agogo ne manne A hand dinta Sai wani zobe makale da yatsanta, Kai daka ganta Kasan Akwai Hutu Atare da ita Dan fatar jikinta luwai take, bawani make-up tayima face dinta ba Amma hakan be hana kyawunta fitowaba. Mumy ce ta turo kofar tace my daughter baki gama Shiryawa bane Haruna tun tune yake jiranki A waje fa, nagama mumy kinsan nace miki Tare Zamu tafi da Leemah bata karaso bane sai yanzu, yakamata Kifitoh haka nan, "Alright" Mumy nafito. Toh daughter fadan da namiki dazun Allah yasa yashigeki Sannan kinji Abinda da dadynki ya fada miki, Allah ya bada Sa'a kikula da kanki kinji, Zuwa tayi tace thanks mumy ta yayinda kuka yakeson kwace mata, Haba feenat banace banason Yawan kukan Nan ba idan bakya Son tafiyar ne Saiki fasa, da Sauri tasaki mumy tafara Share Hawayenta,mumy Ina Twins? Suna wajen Baba Ladi jekiyi musu Sallama, Zuwa tayi tasamesu Baba Ladi namusu wasa Suna dariya, Kissing dinsu tayi A kumatu daya bayan daya taima baba ladi Sallama, kukan mubeen taji Alama Yanaso yabita tajuya ta daukeshi mubeena itama tamika Hannu, Ina Zan iya daukanku duka Baba Ladi Dan Allah daukota muje bakin gate. Suna karasawa Mumy ta Amshi mubeen daker ya yarda Feenat ta shiga mota. Suna fita ta hango motar su Leemah Haruna tsaya. Yana tsayawa Leemah tafito tashiga, Leemah tayi fes Don itama badaga baya ba wajen kyau. daret hanyar Abuja driver ya dauka.
Karyar kika Zuba ma Mamy tayarda Zamu tafi tare ko? feenat tafada tana kare mata kallo, dariya Leemah tayi tace yau Kai tsaye nafada mata tadanyi fada daga bisani kuma tayarda........ Ai gara mumy bata So maybe wani Abun ya Sameki ne but Shifa daddy Kai tsaye yake nuna bayason wani da Namiji yakulani, Kinsan Wlh Leemah Ran nan da daddy yake waya da Inna Nafisa ta yola inaji tana cemai yakamata Aimun Aure tunda Shima da ya Auri matarshi bata kai yawan Shekaruna ba, Wai Sai ce mata yayi Yana tsoron mazan yanzu ko Anyi Alkawari Za'a cigaba da karatu Sai Anshiga Su hana, cemai tayi A hada ni Aure da babban yaron Uncle dina Nazir, Amma firrrr daddy ya kauce maganar da take mai, kuma Leemah Wlh kabeer yarone mai hankali da Addine Kuma dama addini Shine babban Abu mai taka Rawar gani wajen Niman Auren miji nagari, ke bama Haka ba babban Sojane wanda Kasar Najeria take Alfahari dashi, kuma Wlh Ga Kyau idan kika ganshi Kama da dadyna yayi Sak. Gaskiya feenah daddy yayi Nisa burinshi kawai yaga Ance yau ga yarshi tazama wani Abu toh baya lura da kedin macece? daya sani gaba daya burin nashi kan yaya Nazir dinku ya daura da yafi. Idan baki manta wani hadisi da muka taba yi muna Aji Shida A islamiyya ba, "Sahihul bukari ne" "Alkam ya Ruwaito hadisin" CEWA! "Watarana sayyidina Usman yasamu Abddullah bin Mas'ud (Abu Abdrrahman) Sai yace mishi ya Abu Abdurrahman Shin na Aura maka budurwa domin ta tuna maka da yarintarka" Awata Ruwayar kuma " Shin Na Aura Maka budurwa domin ta tunatar dakai Samartakarka" kinsan me wannan Hadisi yake nufi, wannan hadisin yana Gaya mana cewa Aure Shine kwanciyar Hankali kuma Aure Shi ke Samar da natsuwa. Ke Wlh duk Matar dakiga ko mijin dakikaga Suna korafe korafe Kan Cewa basu Samun natsuwa game da iyalansu Toh ki tabbata Soyayar da Suka Kullah Kamin Suyi Aure ba Soyayyar Gaskiya bace, idanma Ansamu wanda Suka kulla Soyayar Gaskiya din Toh tabbas Basu San Yaya Ake Sarrafa taba, Soyayya ba'Ita ke Haifar da natsuwa gidan Aure ba Sarrafa Soyayyar Shine Ke Haifar da natsuwa. Misali Atambayeki me kika fi So Arayuwanki Saikice Waina, Sai Akawo miki Waina har kashi biyu, dole wacce kikaci Kikaji tafi dadi ita Zaki yaba, Sanan Kuma idan kika gama Zakiso Kiji wacece ta Sarrafa wannan wainar. Toh Haka Abun yake idan Ma'aurata Suka iya Sarrafa Soyayya Zaman takewar Aurensu Zata daure Sosai. Kuma duk mace Ko Namiji da baya Samar ma dayanshi natsuwa Shine Zakiga Aure yana tabarbarewa. Bafa natsuwa ta kwanciyar Auratayya kadai ba natsuwa Zamn auren Gaba daya nake nufi. Manzon Allah S A W yace. Idan kuka Samu NamijI mai Addini da kakkyawar dabi'a Toh ku'aurar mishi da yar'uku ANNABIN ALLAH FA Akace, wanda duk wanda yabishi yashiga Aljannah, Haka kuma duk wanda ya kaucemai Wlh Saiya Koka. feenat kinga Addi da dabi'a mai Kyau Sone manyan Abu da Suke da Muhimanci game da Aure, Allah S.W.T yana cewa da Za'a kawo mahaifiyarka San'nan Akawo mazon Allah S A W Ace kazaba Allah yace Zaka Zaba Annabi ne. Yakamata ki fahimtar da daddy yagane Aure Shine darajar diya mace, ke kojiya Saida muka kara magana da Abba yace indai inada muradin Aure tare da tsayayen Saurayi namishi magana, feenat Kinsan mazan yanzu dole Sai Kana bincike Akansu Sosai. Kingani Anbani Zabi ballatana Ke dana fuskanci Sha'Awa gareki mai karfi, ina lura dake Sometimes Idan Muna Kallo ko Wani fira yanda kikeyi, Amma mucigaba da Addu'a Allah ze kawo mana Mafita. Feenat da tunda Leemah take magana ta mayar da Hanklinta duka Kanta tace besty kedin ta dabance wlh Shiyasa banida Abokin Shawara wanda ya huce ke, Allah yabarmu tare. Haruna dake driven duk yanajinsu yaran sun burgeshi kuma yadau Alkawarin idan yadawo Saiya ma Alhji magana gameda ya Aurar da feenah. AHAKA Suka karasa Abuja Cikin Makekeyar makaranta da Akayita domin mata Zallah. Sunyi komai cikin Lokacin Kankani hostile Suka nufa Ana ganinsu Aka duba sunansu kowacce Aka bata key din dakinta domin dama Anmusu komai kamin Su karaso, key daya Suka amsa Suka dire a wani makeken daki da gado ne kato a tsakiyarshi Sai wardrobe dake gefe, dauke Dakin yake da toilet dakin dai daidai irin yanda Su feenah kesonshi. Wanka duka Sukayi Sannan Sukay Searching Unguwar domin nemo wajen Abinci dadai wasu Abubuwan.
After 2 months
Su feenah Ankara Wayewa Suna kokari Wajen karatunsu domin yanzu gabaki daya makarantar Nan Ansan da Zaman NAFISA .U. IBRAHIM (feenah) da HALIMA .A. MUHD ( leemah) kowani Malami yana Alfahiri da Su da irin kokarinsu, Sun Samu wani malami wanda Suka ware lokaci yake koyardasu bangaren Islamiyya. Wanka kuwa babu wanda Ze nunamusu bare Uwa uba Kyau da tsafta, Komai Nasu Abun birgewane, gashi basa kula kowace Mace komunji dakanta, Lokaci Zuwa lokaci Kowacce Ana Zuwa mata daga gidansu. Shakuwa mai karfi takara Shiga tsakanin kawayen Nan biyu, matsalar dasuke Samu dayace yawan Sha'awa da feenat takeyi. Akwai wani Zuwa da Su daddy Sukayi Feenat tacire kunya Ta sanar dasu Mumy Amata Aure Amma Sukace Zancen Banza tafara karatu tayaya Zata yanke, data fahimtar da mumy Abinda ke damunta Cewa tayi Tarinka Azumi da Karatun qur'an Sannan duk lokacin da taji Tarinka Shan lepton da lemon tsami. Ahaka Rayuwa taci gabanmusu, Idan Leemah tace Zata gayama Mamy domin taje ta Samu mumy sai Feenat tace bataso Kunyar Mamy takeji haka Leemah ta hakura ta Rabu da Ita. Kowacce Tana Waya da brother dinta dake Kasar waje, duk Sanda Feenat ke waya da yaya Nazir saita bashi labarin Leemah, Shimakam yaya Nazir yaji Son ganin yarinyar, itakuwa Leemat da tafara ba Yayanta labari bayama Saurarenta Yake kashe wayar. Yauma kamar kullum Sunje wani Restaurant dake cikin garin Abuja Sunacin Abinci, Wasu yanmata Suka hango Su biyu Suna nufosu Suna karasowa dayar tayimusu Sallama. Amsawa Sukayi yayin Yayin Leemah tayi musu izini Su Zauna. Zama Sukayi dayar tafara magana Ni Sunana KAUSAR HAFIZ Wannan kuma ta nuna wata dake bata Rai Kamar bataso Zuwa wajen nasuba Sunanta KHADIJA AMINU. Leemah tace "Nice" yayin da itama ta gabatar musu dakanta da feenah. Kausar ce wow Ai na lura kuna Son junanku da Alama kundade tare domin tare nafara ganinku a Skul, Room dinmu Shibe No. 12 na yaba da Hankalinku Naga Ana kuyardaku Islam Shine Nida kawta mukeson Muyi joning dinku, da Sauri Khady tace kikeso kiyi dai Murmushi kausar tayi tace O.k. nakeson Nayi, feenah tace badamuwa mun Amince Amma Tunda ke kadai kikeso pls ke kadai muke bukata. Da Sauri Khady taja tsaki tabar wajen. ba Damuwa Ngd da karbata da kukayi Zanso nazo nakara muku gdy wajenku. Pls idan Zakizo kada kikawomana waccen Banzar dan Zan'iya marinta Leemah ta fada tana kara tamke face, Sannan Room dinmu 14 no ne, Sai kinzo dahaka Leemah taja hannun Feenah Sukabar wajen.
Page......8
Zaune Suke Suna fira Suna dariya daka gansu dama Kasan cikin farin Ciki Suke. Noking din kofar da Akeyi Shi yadawo dasu daga firar tasu. Open d door leemah. pls feenah open it. ni batashi Zanyiba dan naji dadin kwanciyar nan. Noking Aka kara akaro na biyu, tashi Leemah tayi ta nufi kofar Dan tasan ko kwana Za'ayi Ana buga kofar Kawarta ba budewa Zatai ba. ganin wacce Suka hadu da ita jiyane yasa ta Murmushi tace Come in. Shigowa tayi tasamu waje ta Zauna, tashi feenah tayi lokaci daya Kuma tana mata Sannu. Yawwa Kausar ta amsa yayin da takara gabatar musu dakanta. Tace ni A Zariya Nake da Zama takara dacewa nazone ku nuna mun books din da kuke Amfadi dasu na Islamic. Idan bazaku damu ba kuma zanrinka Joining dinku muna Zuwa tare wajen Malamin. Ok Leemah tafada yayin data kwaso littafan gaba daya. Tace Mukuma muna Kaduna ne. Kausar nace "Wow" Sannan tafara duba takaddun. Oh dama wa'innan kukeyi Ashe? Su mukeyi feenah ta fada atakaice, Leemah kuma cewa tayi kinga Wanda ke bamu wuya nan ta nuna NAHAWU. Lallai ni gaba daya litattafan nan na haddacesu, atare Suka Zaro ido Sukace "Me kikace" eh na haddace su duka Kausar ta maimaita yayin da tarinka Zakalo wasu wuraren tana karanto musu. Kungani ko? Kawai yanzu Zan kara binku domin nakara tilawa. Take feenah taji Son Kausar ya Shigeta, yayin da leemah ta fada Afili, Wlh kinburgeni Kausar daga gani gidanku Sun baki tarbiyya Kuma Sun tsaya miki wajen neman Ilimin Addini. Feenah tace Gaskiya Kam. Kausar cewa tayi Hakane Amma kuma Abu daya ya gagare iyayen nawa ba. Yayin da ta tashi tana kokarin tafiya. Dan Allah ko zaki rinka zuwa muna koyan darasi Awajenki? Me Zai hana Feenah indai kunason Hakan. Leemah tace munaso. ba damuwa zan rinka Zuwa Sai Anjumanku, Toh mungode.
Feenah Gaskiya yarinyar ta burgeni Sosai, iyayenta Sun tsaya mata, Ashe Shiyasa tun farko yarinyar ta kwanta mana Arai, mukai Saurin Accepting dita as we frind. Eh gaskiya kam nima ta burgeni Amma komiye yasa take qawance da wannan Kawar tata Oho. Wlh nima bata Kwanta mun ba feenah Yarinyar kalar yan iska ce Sam bata dace da Rayuwar kausar ba. Allah ya kyauta bamusan me ya hadasu qawance ba koma yar'uwar tace Kinga be Kamata mushiga tsakaninsu ba. Hakane feenah Leemah ta fada yayin da Take kokarin dauko wayar ta dake Ringing cikin Handbag dinta. brother ke kirana Feenah. tabe Baki feenah tayi Azuciyarta tace Wanan brother din nata da ko Sunanshi ban saniba, daga gani yacika miskilanci daga yanayin yanda yake firar da Sister dinshi kamar wani yasa Shi ya kiranta, ni mema yashafi ni tunda bani yake mawaba Hasalima ban taba ganinshiba. Take ta chanza Tunani dan bataga Amfanin wanda takeyi yanzuba.
khady Wlh Sun hadu ko ta'Ina wa'inan babys din nisunma kara burgeni Sosai fiye da Ranar da nafara ganinsu A School din Nan, nayi mamakin dasuka saurin karbata A matsayin kawarsu, Amma ba Abun mamaki bane Ilimi na yajamun, ni wlh nakara Alfahari da Karatun Addini din nan nawa. Kefa daga gani khdy kinsan yaran manyan mutane ne, domin daga fatar jikinsuma ya isa kigane, Dan ma dayar naga batacika son yawan magana ba. Dan Allah Kausar dakata kin isheni Wlh, naga dai koma menene nice nasakaki A hanya, kuma kinfi kowa Sanin bana Son Ana Yaba wasu Agabana, Amma ba laifinki bane Son da nake miki Shi yajawo Hakan. Kausar taja wani Uban tsaki mtswww Toh Hanyar Arziki kika daurani kokuma Hanyar Halaka? kinfi kowa Sanin Abun da muke Aikatawa babban Zunubi ne, Atunaninki Zan tunkari Su Feenah da maganar nan ne? Abun Arziki dashi Ake tunkarar mutananin Arziki, bazan taba nuna musu Inada Hali irin Wannan ba. Yanayin tarbiyarsu ma ba irin taki bace da Alkairin nakeson friendships dasu bada mummunan Abu ba. Yakamata kigane......Haba Kausar miye na tada Hankli haka nazata da irin Harkar Kike nemansu Shiyasa nake kishi,Amma yanzu Na fahimceki, Dan Allah kada Hakan ya taba Kawancenmu. Me yajawo Hakan. kawaii khady dama kece kika fahimcini ba daidaiba. Ai yanzu Na Gane Kausar tashi Kije ki Shirya. Tashi Kausar tayi. Khady ta girgiza kanta Cikin Ranta tasha Alwashin Saita tona Asirin Abunda takeyi da Kausar A gaban qakawayen nata domin ta Hakane Zasu Rabu da Ita cikin Sauki.
AFTER TWO WEEKS
Su feenah Ankara Wayewa malmansu Kullum kara Alfahari Suke dasu Sabida kokarinsu da Hazakarsu, bangaren Addinima ba baya ba Suna matukar maida Hankali, yayin da qawarsu Kausar ke kara fahimtar dasu Abun da basu ganeba. Hakan yaqara ma qawancensu karfi Sosai yanzu duk inda Suke tare Suke Su Ukun Nan wajen cin Abinci, da dai Sauransu. Yanzu har lectures tare Suke Shiga. Hakan ba karamin kara bata Ran khady yakeba, Ayaune kuma tasha Alwashin Saita tona ma Kausar Asiri wajen su feenah. Kausar wai Ina Zakijene haka? Wajen Su Leemah Zani yau Sunce fira Zamuyi, kai Aiko baza'a barni Abaya ba, nima yau Zuwa Zanyi. Sakin baki 😨Kausar tayi tana kallon khady So take ta gano Wani Abu a idonta Amma ta kasa. Kikai Shiru ko bakison najene Kausar? Ah wace ni nicema maison Kije, domin kisauke Girman kan dake kanki, dan duk yanda kikeji da kanki Sun fiki. Yatsina fuska khady tayi tace Naji muje Ga 7up Nan kisha nazuba miki. bani nasha kadan dan naji Sanyinta yayi yawa.
........tashi ki bude kofa feenah inaganin Kausar ce. Tashi feenah tayi tanufi kofa tana budewa ta gimtse face tace yau kuma wakika jawo mana Kausar. bani waje kedai khady ce tace tana Son Zuwa yau. Tabe baki feenah tayi tashiga Suka biyo bayanta. A'uzubillah keda waye Haka kuma yau Kausar? Khady jitayi kamar ta juya tafita Amma Ina taci Alwashin yau Saitayi Abunda tasaka kanta.. .. Murmushin karfin Halin ta kakalo tace Nice nazone muyi firar tare.. kokuma kinzo gulma ba Leemat tafada Aranta. Fira Suke Sosai feenah, leemah, da kausar. Khady gajiya tayi gakuma wani takaici da takeji Aranta, yawwa Leemah ga wani American film kisaka mana ance yanada kyau pls. Wow inason American films Leemah tafada tana kokarin Sakawa. Kausar Aranta tace Anya ba wani Abun khady ke kokarin Shiryawaba, kai noo Zato Zunubi ne koda ya kasance gaskiya. Kallo Suke Sosai Leemah tace Kausar wannan tana kama dake Sosai. Shirun da tajine yasa ta waigawa, ganin idon Kausar tayi yayi jaaa gashi ta Susuce kamar me bukatar wani Abu. Subhanallh Kausar bakida lfy ne? Atare Feenah da khady Suka juyo dama khady tun dazun take Satar kallon Kausar, Kaina kedan ciwo tafada jikinta na Rawa, kallon T.v. tayi daidai inda wasu turawa biyu Mace danamiji ke Soyewarsu bako kunya, take hankalin Kausar yakara tashi nishi take Sama Sam tana cije lisp dinta. Juyawa feenah tayi ta kalli t.v. din Abunda taganine yasata Saurin rintse ido. dubanta ta dawo dashi wajen su Leemah. Khadija ce ta matso kusa da Kausar tace Sannu Kausar kamar feelings Kike, jawota Kausar tayi da karfi lokaci guda tafara tsotsar bakinta kamar ta cire mata. Zaro ido Leemah tayi tace Uzubillah dama Kausar YAR LESBIAN CE? Juyawa tayi da niyyar yima Feenah magana taga ta kankame jikinta waje daya tana fitar da numfashi Sama Sama, take tausayin Kawar tata yakamata Dan tasan Sha'awar tace ta tashi. Leemah magana takema Su Kausar subari Amma ina basuma San tanayiba. Juyawa tayi ta kashe TV din tahaye kan bed tajuya baya don idan tacigaba da kallon su Kausar zasu cutar da itane. Feenah fellow tajawo ta kankamishi Sosai domin Ita kadai tasan meke damunta. Sukam manyan Matan Akalla Sundau minti40 Suna Abu daya. Suna gamawa Khady tafita tayi Room dinsu. Kausar kuwa Anan bacci yayi gaba da ita.
Karfi 4 na dare Kausar tafarka ganin a inda take yasa ta tuno Abunda yafaru jiya, gabatane yafadi Rasss , Shikenan yaune Rabuwana dasu Leemah na karshe, Anya Zargin danakema Khady ba gaskiya bane kuwa? Komadai Menene nice nafara jawota Dan haka nice mai Laifi. Tashi tayi da Ker tashiga toilet dinsu feenah tayi wanka ta dauro Alwala. Nafila tayi Sannan tayi addu'Oeh ta Shafa. Tuno a yanayin da taga feenah jiya tayi Allah Sarki Maybe Sha'awa Take. Najamata. Kiran Sallahn Asuba ne yatashi feenah daga baccin wahalar datayi jiya tashi tayi taniyar Shiga toilet taga Kausar kan Abun Sallah kintashi feenah? "Ummm" kawai feenah tace tashiga ta dauro Alwala. Leemah tashi kishiga kiyi Alwala. Kausar din ta tafine? da Alama da Abun ta Kwana Aranta. Feenah bata bata amsaba Saima tada Sallah da tayi. Kausar ce tace kintashi Leemah? Bata kulataba tayi Hanyar toilet. Tana idar da Sallah yau ko addu'a bataiba bare Azkar tajuyo Kan Kausar. dama kedin yar Iskace Kausar Shine kika bari kika Shiga Rayuwarmu? Why kika Aikata Abun jiya Kausar? Kukane ya kwace ma Kausar Yitake Sosai wanda harfeenah tafara tayata don itadin Haka take da Karyewar Zuciya da wuri. Saida tayi mai isarta tukun ta fara basu labarin yanda Suka hadu da Khady dakuma yanda khady ta daurata Akan wannan mummunar Hanya. Takara da Cewa lefin iyayenta ne dasuka ki yimata Aure wai Saita Ga Karshen biro. Sun tausaya mata matuka Sunsha Kuma kuka. Kausar tace nasan yau Shine karshen Rabuwata daku Don Allah kuyafeni. Leemah tace bazamu Rabuba Sabida matsalarki kusan dayace data feenah, zance miki ne dai Kawai kirabu da Khady kidawo muzauna Anan tare. Dadi Kausar taji Sosai ta kalli feenah tace kema kin Amince da Hakan? Murmushi Feenah tayi tace Abinda ke Zuciyar Leemah Shine yake a Zuciya ta. Rungume junansu Sukai gaba dayansu Cikin farin ciki.
Page....9
Atare Suka jero Su Uku daga babban wani Restaurant dake nesa da School din tasu, tafiya Suke Suna fira Cikin farin ciki. Kausar yakamata da munkoma mushiga ki kwaso kayanki ko? Toh Leemah Saimu Shiga daku kutayini iban wasu, nidai ba kayan dazan Iba Kushiga ni nawuce Room dinmu, kefa feenah dama bawani kwari garekiba ballatana musa Ran Zaki iya daukan wasu kaya. duka feenah takai ma Kausar tace Naji kuje ku karata. Suna karasa Shiga cikin School din feenah tayi dakinsu yayin da Su Leemah Sukai room din su Kausar. bani key din na bude tunda bakida kwari Leemah tafada tana kwace key din hanun kausar. Suna Shiga Leemah ta ballama Khady dake kwance tana waya Harara, take gaban khady yabuga Rasss, ganin kausar tare da Leemah. Karfin Halin kauda kai khady tayi tana yatsina fuska. daret Kausar kan kayanta ta nufa tarinka hadasu waje daya leemah na tayata. Saida Suka gama tsafff Suka iba Sukai hanyar fita. Kausar kinshigo ko magana, Sannan kuma kin kwasa kaya Zaki fita bakimun bayani ba. Eh Hakane kuma khady Hankalina ya tafi Nakoma Dakin Su feenah ne, daga Haka Suka fita Suka bar dakin. Hannu ta daura Akai Wayyo🙆 ni khadija garin neman gira An Rasa ta ido. Ina neman Rabasu Ashe kara hadasu Nayi, Wlh Saina Samu Mafita, dama ni nabiyota nan Dakin gashi kuma tabar min Shi.
Bayan Wasu lokuta
Abubuwa da dama Sun faru,Ciki harda Zuwan su feenah Hutu Kaduna, wannan karon Kausar har Zaria takaisu, Shakuwa mai karfi takara Shiga tsakanin feenah, leemah nd Kausar. Yauma tare Suke gaba dayansu Suna hirar Duniya. Kausar tace yakamata mufara Shirin fita practical din nan, naji Suna cewa Zuwa nan da Sati biyu Za'a fara fita. Hakane Kam feenah ta fadi, yayin da Leemah tace Nifa dama nariga dana shirya, kallanku kawai nakeyi. Muguwa Ai kinriga kin Saba mugunta.😊Murmushi tayi tace Ai ko ina mugunta bazan ma feenah ta ba. yawwa ku tsaya wani novel Zan karanta mana Kausar ta fada tana daga musu hannu. munajinki Novel din tafara karanta musu "miswasmiti" Na AISHA ALI KARKUWA😄 Tunda Naga haka nace nima bari naje Muyi fira da khady kamun Su gama Sabi da yanzu ita kadai take Rayuwarta. Lekowa nayi da niyar Naga kosun gama, Abun da nahango Shi yakara Angizani nashiga room din na Rakube bayan kofa. Feenah pls kifada mana meke damunki mana lokaci daya jifa yanda Kika koma. hannun Kausar ta kamo tace Kausar Ban saniba nima. daidai ina kikejin ciwon? Hmmm kila Sha'awarce ko feenah leemah ta fada cikin Damuwa. Kausar tace Sha'Awa kuma saiya Sata haka? Eh haka takeyi Bare inaga wannan book din dakike karantawa ne. Yanzu miyene Mafita Leemah naga tana jin wuya? Kawai Bari na hada mata lepton da lemon tsami. hada da Sauri pls. hannu Kausar dakai Kan maran feenah tace daidai nan Zakiji kamar wani Abu na miki yawo ko? daga Kai kawai feenah tayi. Bari nashafa miki naji Ance idan kana Sha'Awa Ana Shafamaka Mara kana samun relief. feenah dai bata tanka ba, cigaba da Shafa mata Mara Kausar tayi ganin tana lumshe ido yasa ta gane cewa Lallai tana jin dadi, Cije lisp tayi. Adadai Nan Leemah tashigo da Cup A hand dinta. Zaro ido tayi ganin Abunda Kausar kema feenah, cewa tayi kimata hakan? gani nayi kin Dade kuma hakan Shine Mafita mafi Sauki. Ai gashi na kawo, feenah tashi kisha, runtse ido feenah tayi yayin data kara kankame hannun Kausar dake kan mararta tacigaba da Shafawa. Kingani ko Leemah tana jin dadin hakan Bari tadan Samun relief Saiki bata lepton din. gefe Leemah takoma tayi tagumi tana tausaya ma kawarta cikin Ranta kuma Sake Saken Wasu Abubuwa take, gefe guda kuma tana jin haushin yanda Kausar ke Shafa Marar feenah. Nishin dataji Shi yadawo da ita daga tunaninta.
0 comments:
Post a Comment