Ciki yashiga da ita ya sauketa kan makeken gadon dake tsakiyar dakin Shi. Muga kafar yazeed yafada fuska ba yabo ba fallasa! Nuna mishi tayi yana duba wa tana washhhh kayi Ahankali Honey Akwai Zafi fa. Ni banga komai Anan ba, maybe ciki yashiga idan kana tabawa Zafi wajen ke mun. Bari na kawo miki magani kishafa..Ok honey nima daman haka Zan ce maka yanzu, fita yayi be tsaya Saurarenta ba, yana fita mufeeda ta jawo handbag dinta wani kwalban turare ta ciro ta shafa ajikinta tai Sauri ta Maida tana Murmushi. Shiga yayi bakowa A parlon dan haka ya haura Sama, dakin Mamy ya wuce nan ma basanan, wucewa yayi part din Abba Achan ya samesu, mamy na chat a wayarta Inno na waya, da Alama da Leemah Suke wayan, jinayi tana cewa Ai Wlh Halimatu nice na koresu yarinyar yanayin kafurai gareta, har wani gashi ta kawo tasaka kamar diyar bokaye...dariya Leemah tayi daga bangarenta tace inno kinyi daidai,tunda naga baki So yarinyar ba nasan bata haduba . Ke Halimatu Ai cewa nayi Zan hadashi da Ubanku Shine ya Mayar da ita, yarinyar tayi Sa'ar uwarku fa,daga gani yar bararoji ce ma. dariya Leemah tayi tace Inno kibarni haka kinata sani dariya, toh Halimatu yaushe zaki dawo ne? Inno Saura 8months nadawo gaba daya, mekenan? Wata takwas inno! Aradu yayi yawa nida nakeso kidawo da wuri gidan ba dadi wannan Mai bakin Halin babu Abinda ya'iya sai tsaki da fadin Rai. Toh inno kikara hakuri zuwa nan da wata biyu Zanzo hutu. Ai gara haka Halimatu Dan Idan baki gidan kamar duhu ne. Toh inno bye. Ai kece bye din me kikace kokema kin fara Zagina ne irin na dan"uwanki? Aa Inno ta wace ni ina nufin sai Anjuma ne. toh Halimatu Kice ina gaida Nafisa,Kuma kice mata iyayenta Sunzo jiya sun gaida ni harda Nazeeru Yaron Albarka. Zan gaya mata inno kettt Leemah ta kashe wayanta Sanin idan ta biye ma kakarta bazasu kasheba. tabe baki yayi ya Zauna kusa da Mamy. Inno itama kauda kai tayi tace "Mai bakin ciki Shine Atabe Shi yakan mutu Ranshi Abace" ko kallonta beyiba yace mamy gani. Wannan yarinya Aina take? Mamy Amalali gidansu yake. Menene hadinka da ita? Yooo kema Fatima macen dayake so ya Aura Kenan inno tafada. Kallonta yayi yaja tsaki. Kama Ubanka tsaki, tsaka kawai. Mamy tace yanzu Ina yarinyar? Mamy na kaita tashiga mota ta koma. Tashi katafi toh. Ke yanzu Fatima haka yakamata kimai? Jan kunanshi yakamata kiyi domin gobe kada ya kawo wacce ta fita maguzanci. Mama Ai kinmai fada bazai kara ba. Kwaji dashi inno tafada. dakin Mamy yashiga ya dauko wani Cream da take Shafawa Akafa, sakkowa yayi daidai Sanda inno itama ta Sakko. Yazeedu kudi Zaka bani naje kasuwa, Nasan idan nace ka kaini ba Zuwa Zakai ba. Kinga inno ni ban fito da kudi ba. toh muje kabani, kibari Zan kawo miki ciki. Yazeedu dan Albarka mudaije kabani...inno pls leave me. Kaini kamun katafanci nafi ganewa. Yanzu mai Zakai da wannan na hanunka? Shafawa Zanyi yazeed yafada Rai Abace. Muje na tayaka Shafawa domin lokacin da Ubanka na karami nice ke Shafa mai. Bana bukata yazeed yafada yabar wajen, binshi tayi Abaya tana fadin Kodai Wani Abun Ka boye wanda baka Son nagani? Yana Xuwa ya tura kofar da karfi yasa key. dan iska mai bakar Zuciya, gaka fari Amma Zuciyarka baka, mai kama da Samudawa Kawai, Anyi kyan banza kuma Wlh Amadi Zai dawo komai kamun Akunashi ne,kafito kabani kudin kuma. daga Haka tayi Cikin gida tana fada. Zama yayi kusa da ita yace gashi kishafa. Pls help me Honey ban iya daga kafan! bude cream din yayi yafara Shafa mata Akafar danshi bega Wani wajen Ciwo ba. Ashhhh honey Ahankali pls,,,washhhhhh tafada da karfi Ta fado kan kirjinshi, wani Abu yazeed yaji ya Xiyarceshi bangare guda turaren dake jikinta duk ya daburta shi, Lokaci daya yaji wani feeling ya taso mai. Ahhh honey Ahankali dan Allah. Lumshe ido yayi... Hanunshi ta jawo kan kirjinta, Honey taba Kaji yanda Sonka ke kara bijiromun Cikin Xuciyata, kaga Sanadin Xuwana gidanku Har Ciwo naji, Amma Shine kake maganar Mu Rabu, gashi kakar ka Bata Amince dani ba....dan Allah kasoni muyi Aure Honey idan narasaka Bazan iya cigaba da Rayuwa adoron kasa ba, Kana Sona? ta kalli idonshi harya Kada. Lumshe ido Yazeed yayi bece komaiba, ganin haka yasa mufeeda tace bari naji ko Xuciyarka Na harbawa kamar yanda tawa takeyi! boturan Rigarshi tashiga ballewa, hannu tashigar Ciki "Oh my God " honey gabanka faduwa yake. Kenan kaima kana Sona? Wani turare ne wannan yazeed ya tambayeta cikin Rashin kuzari. honey inamaka maganar serious Kana maganar turare, Kaine kajishi Yanzu Amma ni daga gida nasaka. "Uhum" yazeed yace. Mufeeda kuwa gashin kirjinshi tafara wasa dashi, Honey inason irin wannan. Hungging dinta yayi da karfi yana shakar turaren data Saka. Menene haka kakeyi Kuma? bakinsi yasa Cikin nata,Aikuwa Nan da Nan takama tana tsotsa, yazeed duk Ya daburce daukanta yayi yadaura kan bed Atare Suke Saukar da nunfashi, mufeeda Sai Shafa Kan dan karamin Brest dinshi take, kara fita yayi cikin hayyacinshi. Ganin haka Mufeeda ta Cire rigarta (ya Allah ka Shiryar da Zuciyoyinmu, ya Allah karaba yayyanmu Maza da kaninmu maza da mazajenmu daga Sharrin matan Zamani wa'Inda Shedan yariga yamusu fitsari Akai😢👏Amin) ganin brest dinta Awaje ba karamin Kara daga mishi hankali tayiba, bakinshi yakai yana tshotsa itakuwa Sai nishi take gaba daya takosa ya Shigeta...Shiko ina ko wandon jikinshi yaki cirewa, ganin Andau Lokaci tafara tsoro wannan Wani Irin namijine like a Hariji! Nayi relies Sau biyu bayida Alamar ya Shigeni, Zame jikinta tayi dan Xuwa yanxu ta gaji.mirginowa yayi Zai kamota ta tashi da Sauri ta sauka kan bed din....mararshi ya rike Yana juyi daga bisani wani bacci mai nauyi ya daukeshi.
Wani waje ne cikin School din da'aka kayata Shi da Ado, Shuke Shuke da Sauransu! Student din Sukan je Chan Su huta, Zaune Suke Suna hira Suna dariya, Leemah ke basu Labarin firarsu da Inno, dariya kausar keyi kamar cikinta Zaiyi ciwo, yayin da feenah Saidai ta Tabe baki ta juyar dakai, Kausar ce tace Shima banda Abin yazeed me Zaiyi da babban mace,kodai ma Kishi inno takeyi tace yarinyar yar bararoji ce? Kai da wuya inno kiga ta kushe Abu Leemah ta fada. Kausar tace Ai jiya Yusuf ya tura Mun pic dinta, yace budurwan yazeed ce,but banyi downloading dinshi ba Bari na duba yanzu! Wayanta ta jawo ta kunna "Data" pic din ta bude gani kawai nayi ta kwashe da dariya har tana kokarin faduwa....mugani Leemah tace tana Amsan phone din. dariya itama ta kwashe dashi harda kwallarta, juyawa tayi ta nuna ma feenah, tana gani ta juyar da kai tana Kumshe dariyarta. Lallai Leemah dole inno ta korasu,yanda brother dinki keda Kyau da Aji ga kwarjini Amma yarasa wacce ta burgeshi sai wannan tana dariya ta karasa maganar. Kedai Bari kausar Saikace wanda Asiri ya kama, Ai Wlh inno tamun daidai gara ma data zo. Ai Leemah koda inno batazoba banajin mamy zata Iya barinshi ya Auri wannan Macen. Umm Wlh Kausar koni danake mace bata birgeniba ballatana Shi namiji, Hhh gsky koni bataimunba kalletafa kamar mata maza din nan. besty kinyi Shiru Leemah ta fada tana kallon feenah. " toh Ai Zancen be Shafeniba Leemah" Amma kyace Wani Abu ai: nace mai bayan Ra'ayinshine Hakan, Indai yarinyar Zata iya jure girman kanshi da isa menene Aciki! Wannan ba yarinya bace feenah Zata kai 34yrs fa. toh Kausar ni miye nawa koma 70yrs take? Ai yazeed brother dinki ne kema feenah yakamata Ki karbi number dinshi kibashi Shawara ya rabu da ita. Mtsww Kausar duk Abunda bazai yuhuba Shi kike misaltawa, tunda yana Sonta ku Menene naku banda ido, ba gara ma Amishi Aure ba ko ya rage fadin Rai. da Sauri Leemah tace wai talle nama audi gori..kina ganin katuwar Mace kice gara ma Amishi Aure! Wannan ai Saita lalatamun bro. Kokuma Shi ya lala....da Sauri Kausar tace ke feenah bakisan irin matan nan ba yanzu Saikiga ta daura Shi Akan hanyar bata dan daga gani idonta Abude yake... eh fa bansaniba kuda kuka Sani ai saiku hanashi aurenta tunda kune kuka Xaba mai ita daga haka feenah ta tashi,idan kun gama Zancen banxar Kwazo kusameni a daki. Cigaba Su Leemah sukai da firarsu Suna Kara kallon picture din mufeeda Suna dariya.
Kiran wayar Shi da'akeyi Shi ya tasheshi daga baccin daya daukeshi mai nauyi. bude ido yayi Ahankali ya jawo wayar yasa A kunne. Hello! Kai yazeed banason wulakanci fa tun yaushe nake Kiran wayarka kaki ka dauka? "Sorry friend" Sorry for what? Kasan dole Zanzo na tayaka Murnar dacewa da Kayi an Amince ka Auri mufeeda shine kaki dagawa. Shiru yazeed yayi bece Komaiba. Kayi Shiru dan Rainin wayo ko bakaso nayi Celebrating before daurin Aure! "Umm" yazeed yace.. wai kai me kakeyi haka? inafa Hanyar gidanku. da Sauri yazeed ya kalli gefenshi mufeeda ce kwance tana bacci hankalinta kwance. Yusuf gidanmu kuma? Eh ko bakaso nazo taya murna ne? "No nagajine" Kaman ya ka gaji kana magana Kamar wanda yayi Shaye shaye. "Oh God" Yusuf bana gidane inno nakai kasuwa tagama Siyayya, Shine yanzu wai Saina kaita gidan Aminiyarta. baka gida kake nufi yazeed? Eh mana bakaji me nace bane? O.k. bari nakarasa nagaida mamy inyaso saina jiraka! Mamy bata gida fa taje gidan Matar uncle dina. Kash naso naji yanda Akayi da budurwanka, Amma bani labari yanzu. Yusuf kaina ciwo bari Anjuma kazo mana....ciwon Kai kamar ba Dr ba. Dr baya Ciwo kenan? Bance ba Kawai dai inaganin Kamar ciwonka na kwanakine ya dawo, yanayinka ya Nuna hakan. Mtsww yazeed yaja tsaki ya kashe wayar Sanin Halin Abokinshi da tambaya har sai ya'Iya gano matsalar Shi. juyawa yayi yakara kallonta ...take Abinda yashiga tsakaninsu ya fado mishi...dama yarinyar nan yar'iska ce? Tambayar Xuciyarshi yake Dan duk Abinda ta mishi yadawo kanshi,tabbas daga baya tasaka turaren nan..innalillahi Abinda ban taba Aikatawa da farko ba Saiyanzu danake da Hankalina, dafe kanshi yayi yace ZINA! da Wacce ba muharramata ba A'uzubillah! Juyawa yayi ya daka mata duka, Afirgice ta tashi zaune, kofa ya nuna mata Alamar ta fita. dan Allah Honey kayi Hakuri Sharrin Shedan ne, tsawa ya buga mata da karfi tashi kifita nace ai kece babbar Shedaniyar, ganin ba Alamar wasa a face dinshi yasa ta hada kayanta tayi hanyar fita....yazeed Yace kuma Wlh kika Bari Wani yaganki you are very Sorry. Sadaf sadaf tafita Agidan gaba daya....yanzu ya Kara lura da makirci ta hada mishi dan gatanan Ras take tafiyarta,,,Alhmdllh ma tunda babu Abin da yashiga tsakanina da ita. istigifari ya hauyi daga bisani yatashi yayi Hanyar toilet rike da mararshi.
Page...24/25
Kwance yake daga dukkan Alamu tunani ne fal Cikin Ranshi, Alumshe idonshi yake Amma ba bacci yakeyi ba. tura dakin da Akayi ne ya maido dashi daga tunanin daya Lula.... yaya Nazir "mum" tace gobe Zaka kaimu gidan Su mai Kyau muyi weekends Achan. Shafa kan yaron yayi yace Mubeen Ina ne gidan Su mai Kyau kuma? Yaya Nazeer gidan Uncle Ahmad inda Akwai Aunty Leemah da inno da Mamy da....katseshi mubeena data Shigo yanzu tayi,eh Mubeen gidan Su bro Yazeed mai Kyau Zaka ce mishi! dariya Sosai Nazir yakeyi yace kune kuka Rada ma yazeed mai kyau ko? Mubeen ne yake cemai haka, yaya kuma Ai baya dariya Ko? da Sauri Mubeen yace Nidai yamun dariya damukaje da mum, chuno baki Mubeena tayi tace Ai Kadan yake dariyan....toh Nidai yanzu Naji Xan kaiku goben...yeeeh yaya Nazir tnx. Harzasu fita ya kirasu Twins ita Anty Leemah tana dariya kuwa? Atare Sukace tanayin dariya, tana mana wasa, kuma tana kawo mana Sweet da Chocolate. wow tanaji daku, kuna Sonta kuwa???? Yeee yaya Nazeer "We Really love her" daga Haka Suka fita da gudu....Murmushi yayi har cikin Ranshi, wani Abu ya tuna Aranshi ya ciro wayanshi yafara dialling Number Feenah. bugu Uku ta daga. Hello yaya Nazir! Hy my sister how are you? I'm fyn bro nd I miss you, miss you more sister, kullum haka kake cewa yaya Nazir, but tunda nazo u have not to visiting me. I will come sisto Sorry. Umm bayan Xama muzo Hutu; Oh Haka fa, kinga idan kukazo dakun koma Saina rinka xuwa sosai, Allah yasa d gsk, kin Raina ni ko? dariya tayi tace wace ni Sorry. ina kawayenki ne? Kausar ta fita saidai Leemah. bani ita mu gaisa....Leemah take! "Wa"? Kiyi magana kiji ni bari naje nemo Kausar Feenah ta fada tayi hanyar waje. Asanyaye tayi Sallama gabanta Sai faduwa yake....Cikin muryar kasaita ya amsa sallamar, My baby hw are u? Am fine yaya Nazir, Nidai Gsky banason yaya din nan.....dariya yanayin yanda yai maganar yaba Leemah, me kake so kenan? Kece Xaki samo kisaka Mun tunda zuwa yanzu nasan sakona ya isar miki. kikai Shiru baby Ko haryanxu bansamu waje Cikin Xuciyarki ba? da Muryan tausayi ya karasa maganar Dan Haka Leemah Saitaji yabata tausayi, yaya Nazeer ni kunya nake Ji, dariya Yayi Sosai yace I know baby, karki damu idan mukai Aure Xan Cire miki kunyar nan, Rufe ido tayi Kamar Yana ganinta tace Uhum.... magana Xakiyi baby Abu daya nakeson ji daga bakinki, yaya Nazir inasonka kamar yanda kake sona kuma Na Amince Mu kullah Soyayya wacce tafi tasu Romio da juliat fakat Idan kika gayamun haka ya wadatar dani.....Xaro ido tayi Kamar yana ganinta tace Wlh yaya Nazir ban'iya fadin haka yayi tsawo,,,,, Zaki iya baby inhar kin Amince dani, Kinsan wani irin so Nake miki Leemah, ban taba Son wata ya mace kamar yanda Sonki ke hanani bacci ba, tun Ranar dana Sakaki cikin idona ban kara samun natsuwa ba pls ki Amince mun Mu kulla Syy wadda tsantsar kaunace Aciki, I love you with all my heart Leemah. "I love you too yaya Nazir" kettt ta kashe wayan.....tashi yayi daga kwancen dayake ya daga Hannu Sama "Alhmdllh ya Allah" farin ciki ne falll yacika Xuciyarshi tashi yayi ya nufa part din Mamy da karfin guiwan Shi......
fitowarshi daga wanka kenan daure da towel Sai Dan karamin dake Hanunshi yana goge jiki.....Inno ce ta turo kofar tashi da karfi har saida yadanji tsoro, ganin Itace yasa ya daure face yaja tsaki. tsaka ma tayi tsaki Allah ya tsine mata ballantana mutum Dan Adam makaryaci inno ta fada tana kallonshi, be ko kalli inda take ba ya fara taje kanshi da kum..... gafa mutun har mutum Amma Yayi kyan banxa...kallenta yayi ya galla mata Harara, Bazan fasa cewa Amadi ka Harara ba wlh.... kasan ma me yakawoni? be tanka mata ba....kwantar da murya inno tayi kamar ba ita tagama Zaginshi ba.....yazeedu dan Albarka jiya kace Xaka kawomun kudi baka kawo Mun ba Shine nazo Amsa, kayi hakuri Idan dan narabaka da kafurar yarinyar nan ne, gani nayi ka wuce Ajinta koni tsohuwa nafi yarinyar nan lasting Ayanda naganta, kallonta Kawai yazeed yake yanda take Surutu Kamar Radio, yazeedu idan ma kana ganin Zan gaya ma Amadi Abinda kake mun ne Wlh "Aa" waye ke fishi da jikanshi Ai sai wawa. Inno yanzu kudi kikazo dai nabaki ko? Eh yazeedu yaron kirki Allah yabaka mata yarinya daidai yanda Xaka more Rayuwarka, tsaki yaja, inno batai magana ba tunda Abu tazo nema gunshi, tashiyayi ya bude wani Dan karamin Box ya ciro kudi ya mika mata, yawwa yazeedu yanzu kashirya ka kaini Dan Allah. gaskiya Inno kincika takura Wlh babu inda Zani kibarni naji da Abunda Ke damuna. dan iska ba gara Abun yayita damunka ba tunda baka da Mutumci, Kana wani mun magana da gadara Kamar ba gidan dana nazo ba, ko Kuma Angaya Maka Nima sakarkarun yan matankace? Ni koxanyi Soyayya Ayanzu Ai nafi karfin nayi da kamarka, dogon baza Kawai. Kwafa yazeed yayi yace Zaki kara neman Abu aguna, Allah ya Sawwake mun na nimi Abu Awajenka,kudin naka ma danasan bawani Albarka Xasu yimunba Sabida baakin ranka....Amadi ya kusa yadawo ya maidani garinmu...daga haka tafita ta jaaa kofar da karfi....tana fita yace gara kitafi din ko mutum ya huta....wayarshi ya ciro ya kira Yusuf yace yaxo ya Sameshi.
Atare Suka Shigo dakin, ganin Leemah A kwance yasa Kausar tace Halumcy kin gaji ne Haka....Batama San Anayi ba, ta Lula kogin tunanin Nazir dinta, ganin idonta Abude kuma batajuyo ba yasa Kausar ta kalli feenah tace, feenah Wannan qalau take kuwa? Nima shi nagani. besty Lfy kuwa? Shiru ba Amsa, atare Sukayi kanta Haleemah Suka fada da karfi...Afirgice ta tashi tana Zaro ido. Ajiyar Xuciya Sukai atare, kausar tace iskanci muna magana kinyi Shiru kin bamu tsoro. Ajiyar Xuciya itama Leemah tayi tace bacci fa nake, hada ido Sukai feenah da Kausar atare kuma Sukace bacci Ido Abude?..dafe kai tayi tace ba bacci nakeson nace ba, toh mekikeso kice feenah ta wurga mata tambaya? Ina tunani ne wai lokaci ba wuya gashi har Zamuje hutu da mun dawo Saikuma tafiya gida gaba daya...Kausar ce tai saurin cewa naki wasane, aini inajin dadin hakan Sabida da mun gama karantun Nan Sai maganar Aurena da Yusuf daga baya Saiya samamin Aiki....dariya Leemah tayi tace ikon Allah kowa da damuwarshi, Ita dai feenah bata yarda da Abinda Leemah tace ba, tabe Baki tayi tace toh bani phone dita besty kin Rungumeta Kamar kin Samu baby. Atare dukansu Sukayi dariya. Karasowar yusuf Yayi daidai da fitowar inno daga Cikin gida, tana ganinshi ta washe Baki yusufa Kaine? Shima dariya yake yace inno nine, ina Zaki haka? Kasuwa Zani yusufa, inno ko nazo nakaiki ne? Aa Fatima ta Samo driver yanzu ma Shi Zai kaini, toh Inno Adawo lfy, yawwa madallah yusufa. Inno Yazeed naciki? Tsaka yana Ciki tun jiya yake dacin Rai,Sabida yakawo kafura gidan Nan nakoreta, Yusufa yazeed ya haukacefa dan bakaga matar daya kawo jiyaba Xatai Sa'ar Fatima,Shine dan nakoreta yake bakin ciki....dariya Sosai yusuf keyi yace Inno kinyi daidai dakika koreta Haka dama nakeso, eh aishi wawan besan gata ba, Shiyasa yake cika Yana batsewa. Inno bari nashiga nasanar dashi Gata kikaimai, daga nan kace mishi uwarshi ta samomun driver, toh inno Xan fada Mishi.daga haka yayi ciki,Inno tafita. Shiga yayi ya Sameshi kwance rike da mara. Dr ya dai? dagowa yayi ya kalli yusuf ya mayar d kanshi, karasawa Yusuf yayi kusa dashi, yanxu naga inno Xataje kasuwa, tace nacemaka mamy ta sama Mata driver...karamin tsaki yazeed yaja yace ina ruwana ni: gsky Inno tana son kasuwa jiyama kace ka kaita fa! Ummm yazeed yace. Meyasa kace nazo kasan ba magana Xamuyiba, Naga Allamar tunda kasamu Su inno suka amince da maganar Mufeeda shikenan Kake Wani Kara Shan kamshi. Cemaka tayi Sun Amince? Ni bamuyi maganar da itaba, Amma Nasan dansun Amince dinne Kake mana yanga. ... Cije Lebe Yazeed Yayi yanaa runtse ido. Wai kai meke damunka ne? Kodai Ciwon kanne haryanzu? Eh Shine Yazeed yaba Yusuf Amsa a kufule. Allah yabaka hakuri Yusuf yafada yana kunshe dariyar dake cinshi. yazeed ne yajuyo yace Yusuf Ashe dama mata haka Suke? Xaro ido Yusuf Yayi yace Mai Mata Sukai maka? Shiru yazeed Yayi nadan lokaci daga bisani ya kwashe Abinda yafaru dashi game da Kausar ya fada mishi, gaba daya babu Abinda ya Rufe ma yusuf....da mamaki Yusuf ke kallon Yazeed yace Shiyasa Kake ta Wani Rike mara, ba kasamu Abinda kakesoba? Kuma ai ka rage Xafi kadan....tsaki Yazeed yaja ina gayamaka Nayi Sabon Allah jiya kanamun Shirme! Yusuf ne yace toh ai ba lefinka bane kaidin mata ne ya Afka maka, Yanzu kayita neman gafarar Allah, da Sauki ma tunda baka Shigeta ba, Sannan yakamata Xuwa yanzu kasamo Matar Aure, Sabida nafi Kowa sanin matsalarka game da ciwon mara, kaga kafin Ka gagara moruwa yadace Kayi Aure. Nifa yusuf wannan matsalar bata dameniba kamar yanda Yanzu mata duk suka fitamun Arai ba...Shiru yusuf Yayi take Kuma Murmushi ya bayyana A fuskarshi tonowa da wata mafita dayayi, fuskantar Yazeed yayi, Dr na dade ina gaya Maka kananan yara yan 16,17,18 Xuwa 24 idonsu begama budewaba Kamar Wanda Shekarunsu ya daura Akai, Amma Kayi burusss kace kai Sai yar 30yrs, toh Yanzu basaina gaya Maka Abinda yasa nake jimaka tsoro da babbar mace ba, toh tsaya kaji Na fadamaka na Mufeeda ma mai sauki ne kan wasu matan, tunda har tanada tsoron Namiji jarumi ai bata gama wayewaba, Abu daya Xan gaya maka Kanemi yarinya sa'ar kanwarka Ka aura kawai, idan Kayi shawara kanemeni yazeed, daga Haka Yusuf ya tashi yafita......tunani yazeed Yayi Lallai maganar yusuf Akwai kamshin Gaskiya, Sabida duk yanmatan dasuke bina Sun wuce 24yrs kuma gaba dayansu nemana suke da Zina, Akasin babu yarinyar data taba nemana wacce take Kasa da 24yrs Akan wani manufa ta daban, Saidai Yasha Samun Cikin yaran su biyoshi har Office suna kuka Akan cewa suna sonshine da Aure......Ajiyar Xuciya yayi to Amma.....Yaran Nan kawayen Leemah Anya Kuwa?? bafa Xan mance Ranar danaji suna Wasu irin Xanceba! da Nishi Ranar harsaida feeling ya tashinmun, Koda yake nafi Xaton Wani film din Suke kallo, Shikenan Xanbi Shawarar yusuf Nasamu karamar yarinya Wacce baxata wuce 28 ba. Ahaka yazeed yayita saka da warwarshi har bacci Yayi gaba dashi.
Page...26
Kwana biyu kadai dasu Mubeen Sukayi Agidan Mamy ba karamin Sabawa yazeed yayi dasu ba, Zama yake yayita fira dasu kamar Sa'anninshi, duk dacewa Rabin firar tasu kan Antynsu feenah Suke mishi. babu inda be Zagaya da Twins ba Cikin garin kaduna, kayan Ciye Ciye na yara kuwa harsun gaji dashi, bangaren Inno ma ba karamin Son yaran take ba, Uwa Uba mamy dakejin yaran har Cikin Zuciyarta. Yauma Zaune yaran Suke A babban parlon dake kasa, Cikin Shiri Suke da Alama gida Xasu koma domin Gobe Monday Sunada Skul. yazeed ne ya Shigo parlon Aiko Suna ganinshi Suka tashi atare Sukayi kanshi, mai kyau gida Zamu tafi, Sunan dasuka Rada ma yazeed kenan, mamy tace muje Zata Siya mana Sabon Kaya. Murmushi yazeed yayi dan yagane wayo Akai musu idan ba hakaba bazasu tafi ba. Ainima dazun naje gidanku Naga sabon kayan da Mamy ta Siya muku, yazeed ya fada yayin da yake kokarin Xama kan kujera, daurasu yayi kan Cinyarshi da Sauri mubeena ta Sauka tace mum ta hanani Xama kan Cinyar maza, Sanan mum ta hanani wasa da maxa. "Yazeed Cikin Ranshi yace, this is right mubeena and please gum it in ur mind, I'm so impressed with this" Mubeen ya katse mishi tunani, mai Kyau Nima mum tace kada na rinka taba Brest din mata, Kuma nadaina Shiga toilet tare da Mubeena, Sanan mum tace Idan nakai 10yrs Xata kaini dakina Ni kadai banda mubeena. " wow Yazeed ya fada Cikin Ranshi, Gaskiya gidansu Akwai tarbiyya Mai Kyau, is good children to learn all this at such an age to avoid learning it from the society in a negative way. Ya Rabbi Allah kabani Mata wacce Zata Koyar da yarana irin wannan tarbiyyan" Afili cemusu yayi that mumy Said there is not good ko? tare Suka hada Baki wajen fadin yes. Yazeed cewa yayi this is Amazing. "God bless the mum and may the knowledge stick with him for life, jazakumullah bi Kair for All parents they are teaching their Children this" Cikin Ranshi yace Anya Antynsu ta rike tarbiyyan gidansu kuwa? Sabida Abun da Naji Sunayi kwanaki....Mubeena ce ta katse Shi mai Kyau kaga Aunty feenah dinmu ko kullum Saitayi kuka. da Sauri Mubeen yace Ai Yanzu batayi, Kuma daddy yace Idan ta dawo daga Skul Za'amata Aure da Kabir din Uncle Nazir dinmu. Mai Kyau kasan Kabeer din? Kada kai Yazeed Yayi Alamar Aa, mubeen yace A yola Suke inda Akwai Shanu. bude baki Yazeed Yayi da niyar tambayansu, Saiga inno ta Sakko. Muniba baku tafi ba Ashe....dariya yaran Suka fara Mubeen yace ba Haka bane Sunanta, Sunanta mubeena. Toh Aini ban iyaba inno fada, kallon Yazeed tayi daya daure face..tsaka katashi ka kaisu gida yanzu Hafsa ta kara kira. tsaki yazeed yaja cikin Rashin yace bata Bari Naji Meke Saka Antynsu kuka ba tazo ta katseni, Koda yake macigaba a mota. mtswww ya kara jan Wani tsakin, Ai Bazan fasa cemaka tsaka ba, mai bakin Ciki, tashi Inno tayi tana Wani irin tafiya tace Haka yakeyi Kamar Wani Zaki....dariya Sosai Twins keyi Suna Cikin haka Nazeer ya Shigo parlon. da Sauri Twins Sukayi wajenshi da murna Yayin da inno take fadin maraba da Nazeeru dan Albarka,da Murmushi ya karaso wajenta Yana gaidata, amsawa tayi tana fadin Ai kafi wasu masu kwana da bakin Rai Su tashi da bakin Ciki. yasan da Wanda take dan haka be kulataba, kusa da Yazeed yakarasa Suka gaisa, Saidai yazeed gaba daya haushi yakeji ba'a bari Sun karasa firarsuba Anwani katse musu, tambaya yama kanshi waima miye Nawa na damuwa? Oho yaba kanshi amsa, ya tashi yabar wajen dan yasan Nazeer yazo daukansu ne....Allah ya Raka taki gona Inno ta fada da karfi...be juyowo ba bare ya tanka mata. Naziru bari Nakira Maka Fatima ku gaisa kamin katafi, toh Nazir yace. Cikin minti3 mamy ta Sakko rike da wata babban laida da Sauri Nazir ya karasa ya karbi laidan Yana gaidata. Cikin Sakin fuska mamy ta Amsa tana tambarshi mutan gidan,amsawa Yayi da Suna Lfy sunce agaidaku, Kazo daukan mun baby's ko? Sosa kai yayi yace mum ce tace Axo a daukesu, Murmushi mamy tayi tace toh Wannan na hanunka na Twins dina ne Agaida Hafsat din...tashi yayi yace Zasuji Mamy...Rungome Twins tayi daga bisani takaisu Har Wajen motar Nazir bye bye Kawai suke Mata Har motar tabar harabar gidan.
Cikin mota labarin Zamansu Agidan Mamy Kawai Sukeba Nazeer, Shi kam Wani Abun ma dariya yake bashi,wani kuma gaba daya Shirme ne. Kallonsu yayi yace bakunce yazeed baya dariya ba? Mubeena tace Ai yanzu yana mana manya ne kawai baya musu...dariya Nazir yayi yace Wake so nakira mishi Antynshi???? Atare Sukace nine-nice, dialling number din Feenah yayi tana dagawa yace Twins keson magana dake, Mubeena ya mika mawa aiko tana Amsa tafara bata labarin mai Kyau....daga bisani Mubeen ya Amsa Shima dai labarin nashi Kenan...Nazir ne yadan Matsa daidai kunanshi yace kace Abaka Aunty Leemah. Aiko haka yace Ana bashi,Nazir ya karba yasa phone din a hands-free, fira mubeen yake da Leemah Suna dariya, Ita batasan dawar garin ba, Cewa tayi Ina yaya Nazir? gashinan yana dravin, Mubeen ya bata Amsa. Kace mishi nace "i missed him" Ok Mubeen yafada Suka kashe wayan...Nazeer murna yake Kamar yatashi yataka Rawa ga Sweet Voice din babyn shi dayaji ga kulawar data Nuna Akanshi....Mubeen yace yaya Nazir tace tayi missing dinka. Ai najita Mubeen Ta kusa Zama big Aunty dinku kullun kuna tare da ita...Mubeena tace yaya Nazir dakkota Xakai ta dawo gidan mu? Eh Mubeena Idan ma bata dawoba Xan rinka kaiku gidana kullun kuna ganinta! Yeeee Suka fada Atare daidai lokacin da Nazir yayi parking a harabar gidansu....fitowa Sukai da gudu Sukai cikin gida. A parlo Suka tarar da mum tana kallon Wa'azi A Sunnah Tv. Fadawa Sukai jikinta mum I miss you Suka fadi atare....Nima Nayi kewarku Twins dina...Mubeena tafara Zancenta mum yaya Nazir yace Xai kawo mana Aunty Leemah very Soon. Mum Cikin Rantatace ai nafada ma daddyn Shi be yarda ba, Afili cewa tayi Allah yasa.
Feenah ce Zaune tana kallon Leemah, matsowa feenah tayi tarike Hanunta tace besty gaba daya kin Chanza, Idan na tambayeki Saikice bakomai, bakomai kuma Zaki Zauna kina tunani Abinda ba Halinki bane Ada. Kara hada hanuwasu leemah tayi tace besty ki yarda dani babu Abunda nake boye miki, kausar dake Saurarensu tace Haba Leemah yazakice bakomai kigafa har dan Ramewa kikai, haka Kawai Za'ai ta miki magana kiyi Shiru ne, kawai kedai bakya Son musan Sirrin dake Cikin Ranki. Haba Kausar kunsan dai babu Yanda za'ai na boye muku Wani Abu... babu wani Kausar ta katseta Wannan karan kinfara boye boye Amma Kije idan tayi tsami ma Ji. Shiru Leemah tayi kasan zuciyar ta kuma cewa take Son yaya Nazir ke damuna da Rashin jin muryarshi....Kausar ce ta katse mata tunani wajen fadin kutashi muje time din Malan ne yanzu. Feenah Cewa tayi ni banajin dadi Kuje ni bacci Zanyi, besty meke damunki Leemat ta mata tambaya? babu Ruwanki da matsalata kema tunda kin rike taki......Uhum Leemah tace Abunma dariya yabata dan Tunda Suke da feenah basu taba fada Akan Wani Abuba, Hijab ta jawo tasaka Suka fita da Kausar. tashi take kokarin yi takasa Alamar Ciwon marar da takeji yayi yawa, Cije baki tayi da Ker ta tashi tashiga toilet, bayan minti biyu tafito daret Inda kayanta yake ta nufa, dube dube Kawai take bataga Komai ba, Ahankali tace Oh God banida pad, juyawa tayi ta koma Kan kayan Leemah tana dubawa, wata takkadace ta gani ta dauka, takaddar kuwa Sai kamshi take, Rubutun tafara dubawa Ahankali tace, kamar Writhing din yaya Nazir! budewa tayi tafara karanta Abunda Ke Ciki, Xaro Ido tayi lokaci guda tasaki kara hade da murmushi, dama wannan Shine Abunda Leemah Ke boyemun dariya tasaka Ita kadai, take taji Ciwon dake jikinta ya Rabu da ita.....Alhmdullah ta fada da karfi! my besty Amaryar my best nd Only bro kai Naji dadi....jakarta ta dauko taciro paper tafara Rubutu Kamar haka """"""""I Smile because you are my Sister in-law, i Laugh because you will married my brother, don't forget am ur besty that i love you So much""""""" tana gamawa takara Sakin murmushin jin dadi ta Saka pepper din Cikin na farko ta dauki pad din ta Maida kayan Yanda Suke...tayi Hanyar toilet tana yar rawar ta.
Page...27
Zaune yake Cikin Office dinshi wanda ya kayatu da kayan Ado, Sanyi A.c. da kamshin turare Shi ke maka Wlcm Idan ka Shiga....wata Nursing ce tayi knocking, yace yes Come in, Shiga tayi rire da wasu papers A hunanta, tana Shiga ta Aje kan table din dake gabanshi, juyawa tayi Xata fita, "yace ke" juyowa tayi tace Sr,,,,,beko kalletaba yace kiramun Fadila, Ok Sr ta fada tayi waje....Mintuna kadan Wata yarinya black beauty da Bazata wuce 17yrs ba ta Shigo Cikin Office din, daret Kujera ta jawo ta Xauna tana kallonshi, baki iya gaisuwa ba yazeed ya wurga mata tambaya? durkusar da Kai tayi kasa tace Gud Morning! Be Amsa ba yace kince kina sona da Aure kuma kina wani Nokewa kamar ba mace ba. Shiru tayi ba Amsa, kikai Shiru Ina magana! Turo kofar Akayi fadila na ganin Haka ta tashi ta fita...Shima yazeed mikewa yayi yana daga ma wacce ta Shigo hand ✋get out from my Office... Haba yazeed kabari kaji Menene ya kawo ni mana,,,, kifita nace yazeed ya fada da karfi. Hawaye ta fara pls yazeed ka dakata na fada maka dalilin Xuwa na...yazeed ya tsana kuka A Rayuwarshi Dan Haka ya Xauna be kara mata mgn ba....itama karasawa tayi ta Xauna, dan Allah kayi Hakuri da Abin da yafaru A baya Wlh Sharrin Shedan ne, nayi nadama Hakan Bazata kara faruwa ba, for give me pls. Naji Mufeeda Abinda ya kawoki kenan ko? Kin fada tashi kifita, Amma.....katseta yayi tashi kifita Mufeeda Rai Abace yayi maganar😡 tashi tayi ta karasa gab dashi Cikin Muryar Shagwaba tace Naji Honey Dan Allah kabari mucigaba A yanda muke da...gaba daya yazeed Ji yayi jikinshi ya Saki, turaren da tasaka gakuma yanayin yanda tai maganar duk Sai yaji wata irin kasala gashi ya kasa ture Ta.....Saitin face dinshi takai Tata face din tace Kayi Shiru Honey! Jawota yayi kan jikinshi ta fada kan cinyarshi, Naji yazeed yace, Amma waye yace kisaka wannan turaren? Honey nifa Shine turarena da'iman, Ok Naji kiss me for a minut, Cikin wata irin murya tayi magana, Honey Ni banaso Xaka kara fishi dani...be Bari takarasa maganar ba yasaka bakinshi Cikin Nata....Itama tanajin haka takara hade bakin Nasu waje daya....kissing din juna Kawai Suke gaba daya Sunfita Hayyacinsu Sun mance A inda Suke.....knocking din da Ake Shi ya dawo da Mufeeda da Sauri ta Cire bakinta tana maida Ajiyar Xuciya,,,,,, tashi tayi ta koma kujerar dake kallon tashi, Shima gaba daya yazeed ya chanza idonshi ya koma kamar garwashi....da Ker ya iya daga murya yace "Yes" turo kofar Akai Aka Shigo, Mufeeda na ganin Yusuf ne ta tashi ta fita kamar munafuka, Shima wani irin kallo Yusuf ya watsa ma Mufeeda ya karaso ya Xauna. Shine inata Knocking ka Shareni? Sorry banjiba ne... yayi ita wannan me tazoyi nan bayan Kace kun Rabu? Yatsina face yazeed yayi yace tazo wai bani hakuri kan Abunda ya faru. Kallonshi Yusuf yayi yace Shine kayi mata kuka? Mtsww kukafa Kace! Toh idan ba kuka kayiba Menene ya jawo jan ido? Ko Anyi 1round ne Yusuf ya karasa maganar yana kashe mai ido daya...kallonshi Yazeed yayi yace Zakafi Kyau da dan jarida ba Likita ba! dariya Yusuf yayi yace Allah Ko? banxa yazeed yayi dashi domin Shi kadai yasan yanda yakeji...Yusuf ne yace ya maganar mu, kokuma har Yanzu kana kan bakarka ta yar 30yrs??? Shiru yazeed yadanyi daga bisani yace No na chanza Ra'ayi! Oh Wow da Kyau Yusuf ya fada yana mai Alamar jinjina👍 kenan Kashirya yin Aure kafin ka karasa Shekara 30 din? Yusuf ba dolena ba kafin wannan Shegiyar Mufeeda din takarasa Kasheni! Murmushi Yusuf yayi yace Kasamu wacce kakeso kenan? No ni ban Samu ba, dama Wata yarinya ce Anan kwanaki ta dameni tana Sona da Aure lokacin bana kulata, So yau nakirata muyi maganar tana wani wresting din time dina. kallonshi Yusuf yayi yace Wace yarinyace Anan Hospital din wacce ban santaba? Fadila mana yazeed yabashi Amsa atakaice:: Tunani yusuf yayi kadan Cikin Zuciyarshi " Lallai yarinyar Tanada Hankali da natsuwa Amma Ko Kadan bata dace da yazeed ba gsky" Afili yace toh kai yazeed kana Sonta ne? da Sauri yazeed yace kai nifa Kawai Xanyi Auren nan ne Sabida Na kare mutumcin kaina if Not wlh Saina karasa 30! Kuma ni gaba daya yarinyar ma Yanzu bataimunba, Ina mata magana Tana Abu Kamar wata munafuka, Nifa Nafison Mace mai kuxari wacce Xata iya kallon Cikin idona tayi magana, ba irin wa'inan matanba Kana mgn Ana Sunkuyar da kai.... fantastic Yusuf ya fada yana murmushi, yanzu Dr yazeed indai kasamu mace wacce Xata iya kallon idonka tayi mgn Xaka Aureta koma wacece? Ofcouse yazeed ya fada....da Kyau Abokina tashi muje kasaukeni a gida..tashi Sukai Suka fita atare.
fitowarsu kenan daga lecture, hostel Suka nufa....Suna Xuwa Sukai Room dinsu, Kowacce Xubewa tayi Akasa Alamar Sun gaji. Kausar tace daga gobe dai mutum Xai tafi ya huta Kafin ya dawo yaji da Exam din karshe...Leemah ce tace kedai Bari, karatu da dadi da wuya. Aidai Ankusa Feenah ta fada yayin da take kokarin jawo wayarta,,,,,ganin mai kiran yasa feenah Murmushi da gangan kuma tasaka a hands-free, Hallo big yaya! Sisto ya kike, Lfy yaya Ina mum, tafita dasu Mubeen, goben Xaku dawo kuwa??? Kallon Leemah tayi daketa lumshe ido tana Murmushi da Alama cikin jin dadi take! No bro tunda hutun Na week ne Basai munzo ba. da Sauri Nazir yace Har Leemah? toh Kai yaya Nazir Nace Ni baxanzo ba kuma kake tambayar Wata Leemah. Am..ehhhh....dama kawai na tambaya ne Nazir ya fada Cikin inda inda, Feenah Cikin Ranta tace "wai su Soyayar tasu kuma da haka tazo, Arasa wanda Za'ayima boye boye Saini" kwafa tayi Afili tace, toh yaya Nazir Naga dai Xuwan baida wani Amfani Shiyasa. Yanada Amfani mana Sisto, kawai kudanxo muganku ma muji dadi Ai yanada Kyau, Murmushi feenah tayi tace "Aa" yaya kawai...katseta yayi yace idan kin Xauna mai Zakiyi Achan kudaizo yafi daga Haka ya kashe wayar....gira feenah ta daga Sama ta tabe baki tace Ikon Allah. Kausar tace Shi yaya Nazir kullum Saiyace ina Leemah Nikuma baya tambaya ina nike kodai....da Sauri Leemah ta katseta toh aikema yusuf Ke kadai yake waya dake.eh aini Soyayya Nake dashi kuma Yana tambayarku....feenah tace Ummm Soyayya Ruwan Xuma wasu na bayya tasu wasu Kuma na Sirrintata Lallai Soyayya Ansha wuya! Cikin Rashin kuxari Leemah tace besty Suwaye? A film ne Feenah ta bata Amsa. tashi Kausar tayi tace ni bari naje Na kwaso Sauran kayana domin gobe gaba daya nakeson na Mayar dasu, kai Kausar Kodai khady tanimi Sulhu kun Shirya Xa'aje Ayi Abinda Aka Saba..tsaki Kausar taja tace kincika maida Abu baya,,,Um um Kausar kidai fadi gsky dama daxun naga kina dan ciccije lips Feenah ta fada tana kallon Kausar:::Afusace kausar ta fita tace kanku Akeji. Tana fita Leemah ta mike tace bari naduba Abu....Wajen kayanta ta nufa tana kokarin Neman takardar dan dama duk lokaci xuwa lokaci Saita duba Letter din da Nazir yayi mata! Karo taci da takardar da Sauri taciro ta juya baya.....kallonta kawai Feenah keyi tana Murmushi. budewa tayi ta ware Ido ganin paper din tazama biyu, ta farkon tafara budewa tana ganin rubutun tagane Rubutun feenah ne! Gabantane ya fadi Cikin Ranta tace" Shikenan ta gani" karantawa tayi ta juya tana kallon Feenah wacce ta daure face Kamar batama San da Mutum a dakin ba. Tashi tayi takarasa kusa da ita, my Feenah am Sorry Namiki Laifi..katseta feenah tayi mekikaimun? Ehm...dama naga...toh Dan kinga Shine yaxama kinmun laifi, kece kikaima Kanki lefi tunda har kika iya barin Abu Na damunki Cikin Xuciya, koma menene dalilinki na boyemun I don't know! Kuka Leemah ta fashe dashi ta Rungume feenah, namiki Laifi besty wannan Shine Abu nafarko da nataba boye miki, kuma Shima inada dalilin yin Hakan. Haba Leemah Wani irin daliline Xai hana Ki fadamun Abu mai muhimanci irin wannan? feenah Idan Baki mance irin Rashin kunyar damuka Sha yiba,Zakiyi fargabar Ranar da Yaya Nazeer Zeji labari, kada Kiyi tunanin Abun ya tsaya Acikin gida ne kadai, Kinsan fa duk Abinda mutun ke aikatawa na boye dole wataran Sai Abin ya fita waje, kokin mance hausawa nacewa ba'a Cewa gaskiyar Mutum ta kare saidai Ace karyar Mutum ta kare.feenah bangare guda ga tsananin Kunya danakeji gaba daya Sirrin Jikin junanmu muriga da mun Sani Sannan Nazo na aure yaya Nazir da wani idon Xan kalleshi. (Hi Leemah help me Ask her😊 ni Kaina kun dade kuna bani kunya🙈🙊) Ajiyar Zuciya feenah tayi yayin da hawaye ke Sauka kan face dinta, Lallai yau nakara nadamar Abinda na Aikata Abaya! Leemat ai bake bace dajin kunyata nice ya kamata Naji taki, Amma Kuma Leemah yazamuyi da kaddara tunda tariga fata? Kawai inaganin kucigaba da Soyayarku har Allah ya nuna mana aurenku, Sabida ai Allah yariga yasani munyi laifi Abaya kuma Yanzu munyi nadama Mun tuba, Allahu gafururrahim ne kuma Shi ke rufama bawa Asiri Aduk Halin da yatsinci Kanshi, Leemah tun farko ba'a gane kedin kinayi ba, bekamata kixauna kina daga hankali ba tunda kedin kin tabbatar Yanzu kowani kikaga yana aikata irin laifunmu Zaki mishi Nasiha, duk kicire wannan Aranki maganar jin Kunya babu tunda wannan sirri ne tsakaninmu Kawai. Hakane Leemat ta fada Allah ya tabbatar mana da alkairi Ya kara Rufa mana Asiri duniya da lahira. Amn Feenah ta fada Suka Rungume Juna Cikin farin Ciki.
WASHE GARI
yau ta kama Ranar Hutu gaba daya daluban Cikin Shiri Suke na tafiya gida....ba'abar Su Feenah Abaya ba dankuwa driver Suke jira ya karaso,Yayin da Kausar ita nata har yazo ta tafi, besty Saiki Sauka Agidanmu ko? No Feenah gida Zaku Ajeni...Oh Na mance yanxufa ni Sirika ce, duka Leemah takaima Feenah Suna dariya daidai Sanda driver yayi parking gabansu, karasawa sukai gaba dayansu baya Suka Shige Haruna yajasu Suka bar Wajen. Nazir ne yashiga Cikin gidan yana Kiran "mum" Amsawa tayi tace gani a kitchen fa, karasawa Nazir Yayi yasameta tagama girke girke kwashewa take tana kaiwa Kan dinning table...mum duk Wannan Abinci Haka da yawa bayan Feenah ita kadaice, waye ya fada Maka ita kadaice, dad dinku yau Zai dawo, Sosa kai yayi yace ai namance ne, Ai dole kamance! Sai Wani rawar kafa kake Kamar Yau Zaka fara ganin Feenah din. bahaka bane mum Kinsan nadade banganta ba, Uhum Kaji dashi mum ta fada,Oya tayani Shirya Abincin Nan. Zaune Suke Yusuf Na fadin wlh Yazeed jina Nake Kamar naje Zaria Ayau! dan Allah katashi katafi mana, duk Ka Wani ishe Mutane kan yarinya karama. bakasan menene Soyayya ba namaka Uxuri kaikam yazeed. Eh Naji angaya Maka Koda naci Xan Auri Karamar yarinya da Soyayya ne? Kawai dan ina tausaya ma kaina nane. Hakane fa yusuf yafada Yana dariya, ina tausaya Maka Ranar da Xaka Zama wawa awajen yarinya karama. Allah ya kayuta Yazeed ya fada da karfi......inno ce tafito tana tsaka Lfy Ko Halimatu ta karaso ne?? Kallonta Yayi ya wurga mata Harara, bansan kanayi ba Sainaga idonka Akasa, badai Yau Amadi na hanya ba wlh Zaka maimaita duk Abin da kake mun, tsaki yazeed yaja yace Saime toh inno?? Sai Ubanka ya maidani, tsaka yau ina Cikin farin Ciki ka batamun Rai Allah Saiya Sakamun. Yusuf dake ta faman dariya yace inno nima Wlh yau farin Ciki Nake Sosai...da Sauri Inno tace Ai shi yazeedu ko Ranar idi ce tazo A bakin Rai yake Aini Alhmdullah Zuwa gobe Narabu da kunnama mai Zafin harbi. Tashi yazeed yayi yace idan kagama biye Mata Kasameni. Wayyo Sunanka Suri yau tsaka, dariya Sosai Yusuf yayi yace Inno tamu. Uhum yusufa yushe Zakayi Aure? Inno Sai yarinyar tagama Karatu. dafatan dai ba katuwa bace irin kafurar yarinyar nan? Inno Wannan yarinyace kawar Halimatu ce kunama gaisawa da ita, Laaaa Kafso kake so dama? yarinya Mai hankali....dariya Yusuf yayi yace inno ba kafso ba kausar take....Oho Aini ban Iya Sunan yan boko din nan ba. toh inno bari na tafi, duk Abinda Yazeed ke Miki ki fada ma Abba dan yace mun wai Aure yakeso Shiyasa yake Miki haka! Bude baki inno tayi tana Salati yusufa Ashe Shiyasa Ranar da yakawo Kafura Naganta tafito daga wajenshi tana Sanda????? mamaki Yusuf yayi Cikin Ranshi yace Chafff Inno ta ganshi, Afili Cewa yayi Inno Ai aure yakeso Sosai, Kinsan feenah Kawar Halimatu kuwa? Kai dan Nan nikuwa nasanta itama tana Miskilanci irin na tsaka.yawwa Inno kawo kunnanki kiji! Mika kunne tayi Yusuf ya fada mata mgn. Tashi Naga tayi tana Rawa Tana haka Za'ayi yusufa... Karfe 5 daidai na yamma driver ya Sauke Su Feenah A mamakenken gidansu Wanda Leemah baccinta take batasan Anzoba, daka mata duka feenah tayi tace tashi Sarkin bacci! Adan tsorace ta tashi, haba Feenah bayan Nace Agida Xan Sauka kikasa y kawo ni nan. Ai naga Nan din ba daji bane. Nidai kirashi ya kaini, Sakko da kanki. Atare Suka sakko Leemah na Kiran Haruna....daidai Kuma Sanda mortar Nazeer tayi parking A harabar gidan, tare Suka fito da dad Suka nufo Wajen Su feenah. da Sauri feenat ta karasa ta Rungume dad, dady ur wlcm. Tnx Ummina. Karasowa Leemah tayi itama tana mishi Sannu, Amsawa yayi Cikin Sakin fuska,,,,Nazir Kuwa gaba daya idonshi nakan Leemah, dad ne yace mukarasa Ciki, Wai tafiya zatai dad feenah ta fada tana kallon Leemah, Aa halimatu muje kici Abinci kihuta sai Nazir ya kaiki Anjuma, toh Leemah tace tabi bayansu jiki A Sanyaye, Shiko Nazir murmushi kawaii yake najin dadi.
page....28
gaba dayansu Sun Hallara Kan dining table din Suna Shirin Cin Abinci. daddy ne yace Hafsat ina yaran Nan ne? Inaga ko basu gama huta gajiya bane mum ta fada tana kokarin Serving din Nazir dake wajen... ya kamata Akirasu ko? daddy ya fada yana kallon mum. Kallonshi tayi tace da Nabari ne Saci nasu daga baya. Nazeer ne yace Ai gara kawai Aci gaba daya mum! Banza tayi dashi, ganin Haka yasa dad yace ma Mubeena ta tashi ta kirasu, tashi tayi ta tafi da gudu Zuwa Sama. ba'afi Minti5 tsakaniba Suka Sakko Atare....daddy Yana ganinsu yace duk gajiya dince Haka yarana, Murmushi Leemah tayi ta Sunkuyar da kai qasa, yayinda Feenah tace dad Akwai gajiya Wlh. Ai kun kusa gaba daya daurewa Zakuyi dad yafada. tashi feenah tayi tafara Zuba Nasu Abincin, Sunaci Suna fira banda Leemah da duk take jinta A Takure musamma data dago taga Nazir take fuskanta, Haka dai kawai ta daure tana ci gashi duk Sanda Zata dago Saisun hada ido Atare Kuma Suke Sakar ma juna Murmushi... mum ce ta dago tace Nazir Anjuma Zan Aikeka gidan "Umma" ka kaimata Sako. Shirun data jine yasa ta kalleshi, gaba daya Hankalinshi baya jikinshi magana Suke da Leemah da ido ga wani kallo dasuka tsare junansu dashi! Mumy ce ta Saki Spoon din hanunta ta dan bigi Kafadar dad tana nuna mishi Su Leemah, daga gira dad Yayi Sama yana murmushi lokaci daya Kuma yayi gyran murya Ehmmm...gaba daya Suka juyo Suka kalleshi ganin Su Ake kallo yasa Leemah taji Kamar ta nitse Awajen, durkusar da kai tayi Kasa. Nazir kuwa Inda inda yafara yace Mum maga kikai? dad ne yai Saurin cewa ba magana tayiba nine nakusa kwarewa, Hafsat tashi muje kiban Ruwa, tashi mum tayi Sukabar wajen ita da dad. feenah kuwa da dama tunda Suka Zauna ta lura da yanda Suketa mgn da ido da Hanci😄itama tashi tayi tace Alhmdllh nakoshi....tashi Leemah tayi da Sauri besty jirani Nima na koshi, da Sauri Nazir yace baki koshi ba Common Xauna ki karasa,marairace Fuska tayi kamar Xatai kuka Allah yaya Nazir na...Kafin ta karasa yace Naji kin koshi Xauna muyi mgn, Xama tayi. Yace feenah dawo kema tare Zamuyi mgnr, dawowa tayi ta Xauna Nazir ya kalli Twins yace kuje Baba ladi ta Shiryaku Xankaiku gidan Su mai Kyau! Ai da Sauri Suka tashi Sukai Cikin gida. Juyowa yayi yana kallon feenah Sisto Nariga Nasan Kinsan ina matukar Son besty dinki ko? Umm ni bansaniba feenah ta fada tana yatsina face...Kara juyowa yayi yana kallonta Haba my Sis Nasan kinsan komai kuma bakya karya kigaya mun gsky. Eh Nasani Yaya Nazeer kawai Haushin boyemun dakayi Nake ta karashe mgnr harda Dan Hawayenta....haba Sis Menene Abun kuka kuma, Nifa daman Nabari ne kidawo Nagaya miki kamar Surprise Haka, kinsan bana boye miki Abu itama Leemah ban so tasaniba Nakasa daure ma Zuciya tane yasa Nagaya mata. Turo baki tayi tace Naji Amma dafatan Son tsakani da Allah kake mata? dariya tabashi yace irin Son danake miki Shi nake mata, Aa yaya Nazir nafison Nata yafi Nawa...Shiru yayi yace toh kitayani addu'a tasoni fiye da komai, toh yaya Nazir Zanyi. Leemah ce tace karfa mum tafito! bayan Sun gane komai feenah ta fada tana dariya..Atare Suka Zaro ido fada musu kikai Leemah ta tambayeta? No kune kuka tona kanku kallon juna Kamar wani Xai dauke dayanku din nan. Nazir yace Ai Hakan ma yayi kinga Sai Amana Aure da wuri! Leemah ce ta marairaice fuska Aa nifa Sai feenah tasamu miji Zamuyi Aure Rana daya...dariya Nazir yayi yace wato Ku Haryanzu yara ne, banda Abunku Ai gara daya taga auren daya Sabida idan Rana dayane daya bazatakai daya gidan Aurenta ba. Waye ya fada maka yaya Nazir? Aikoda Rana daya mukai Aure Sai Nakai Leemah gidanta kafin na wuce Nawa. Nazir ne yace kinmanta Kabeer Xaki Aura kuma yola Za'a kaiki,ba Lallai Na yarda baby taje yola Aranar Aurenmu ba...da Sauri feenah ta tashi tana cewa Ai bazaka Rabamu ba dan yanxu kasamu mun Amsheka, daga Haka tabarsu Zaune A wajen. Juyawa yayi yana kallon Leemah baby kawarki Akwai Rigima, Uhum bata Rigima Kaidinne Kake Sakata Rigima, Umm Na lura bakwason Laifin junanku Toh ya Soyayya ta yanzu Aranki??? Shiru tadanyi daga bisani tace tasamu waje babba Acikin Zuciyata, kallonta Nazir yayi kamar ba ita tayi mgnr ba ta wani fuske, Cikin Xuciyarshi yace Lallai Leemah irin macen danake muradin Aure ce, Afili cewa yayi Alhmdllh my baby Yanzu kinga kamin Ki koma Skul Sai Asaka mana Rana...Xaro ido tayi tace da wuri Haka? Eh mana bakiji Hausawa nacewa Abari ya wuce Shi ke kawo Rabon wani ba? Hakane but yaya Naz..but what? Nazir ya katseta da Sauri. Kabari lokacin daxa'a Saka Ranan feenah da kabeer Sai Asaka tare da namu. Kin kawo Shawara mai kyau baby Shiyasa nake kara Sonki,duk da kin barni Cikin tunaniki, kullum dake nake Kwana kuma dake nake tashi. Nima Haka yaya Nazir. Kin tabbata? Kallonshi tayi Suka hada ido ta kashe mai Ido daya tace Ummm, Ajiyar Zuciya Nazeer yayi Dan wani irin farin ciki yakeji wanda baya misaltuwa. "I love you So much my baby" Nazir ya fada yana Mata Murmushi. "love you more my baby" Leemah ta bashi Amsa kasa kasa. Xancire miki kunyar Nan Soon duk da Naga Alamar nama fara kokari Wajen cireta....dariya Leemah tayi ta tashi tace kada Su mum Su Sakko, tashi Shima yayi ya rakata Har kofar Room din Feenah yace kishirya Anjuma Nakaiki gida. Ok tace tashige Ciki.
Inno ce tsaye Kan yazeed Tana fadin Haba tsaka ka kiramun ita Naji ko tana inane. Inno nace miki wayata Bazata iya Zama A kunanki ba dan Allah kitafi ki bani waje yazeed ya fada yana nuna mata Hanyar Sama.... tsaka! tsaka! tsaka! Sau nawa nakira ka? Oho yazeed yace ke kikasan tsaka. Kwafa Inno tayi tace yaro yarone ina tausaya maka Ranar da Zaka Shigo hannuna, Xakayi nadamar yimun wannan Abun Dan Ubanka,yanzu namaka Uzuri dan nagane dalilin dayasa kakemun wannan Abun...Amma muje Zuwa ni inno jikar Saluhu da balaraba Nakusa Na dana maka tarkon da bazaka iya tsallakeshiba. Kallonta yazeed yayi yace iyaka kice idan Abba ya dawo Xaki fada mishi, Toh Sai me? Haka kace ko? Eh Haka nace mtsww kizo kitafi koma ma huta. Fatima kayimawa tsaki bani ba...muxuba ni dakai. Tashi yayi yana toshe kunanshi...daidai nan Abba yayi Sallama Cikin parlon. Suman tsaye Yazeed yayi dan yasan yau Inno Sharri Xataimishi ba kadan ba. da karfi Inno tace Ayirirerere yau Ga dana Ya dawo huta Roro. ...da fara'a Abba ya karaso kusa da ita ya gaidata amsawa tayi Cikin walwala da Sakin fuska, Abba ya kalli yazeed my Son lfy kuwa? Sannu da dawowa Abba! Yawwa Son duk kuna lfy ko? Alhmdllh Abba. Ya katsaya Haka kamar wani police? da Sauri Inno tace Nakirashi ne ya kiramun Halimatu A waya Shine yake kokarin kiranta Saikuma ka Shigo. da mamaki yazeed yake kallonta Suka hada Ido ta watsa mishi Harara, Shi kuwa cikin Ranshi yace Tabbas wannan tsohuwar Akwai Abinda ta Shirya Mun. Abba ne ya katseshi toh kakirata mana, toh Abba. Kiran Leemah yayi ta dauka ya mika ma Inno! Allo Halimatu. daga bangaren Leemah tace Na'am Inno ta. Kina inane munata jiranki Shiru Har Abbanku ya dawo. Inno Naje gidan Uncle Umar ne, yanxu gani Ahanya tare da feenah da Twins. Har Naji dadi Halimatu chanake kokin fasa Xuwa ne. Aa Inno Gani nan,me kika dafa mana? Saidai kinxo Yar nan.Toh Inno gani nan. Anshi tsaka kashe ban iyaba....Amsa yayi da Sauri yabar parlon danshi tsoro yake kada tamai Sharri wajen Abba. Mamy ce ta Sakko daga Sama Cikin Adonta, barka da dawowa Abban Leemah,yawwa barka Maman Leemah.tashi inno tayi tace bari nabarku Ku gaisa, Kuma Amadi gobe Xaka maidani inda ka daukoni, bata jira amsarshiba ta bar wajen. Yazeed na fita yaci karo da Yusuf dake Shigowa Yanzu...Aa Dr Ashe kana ciki? Ina ciki Yusuf Zomu karasa Akwai matsala fa. Karasawa bangaren yazeed Sukayi, Yusuf yace Matsalar Menene Aboki? Yusuf mamaki nake Abba ya dawo inno batace mishi komai ba, kasan Halin Inno da Rashin hakuri gani Nake Anya ba Wani Abun ta Shirya ba? Gyara Zama Yusuf Yayi yace banajin Akwai Abunda ta Shirya, Inaga kawai dan tasan Za'a Maka fada Shine tadan kauda Zancen. Shiru yazeed yayi daga bisani ya girgixa kai, Anya Kuwa yusuf? nasan Halin Inno Sarai wlh Amma mubar mgnr ni bawani tsoroma nakeji ba taje tayita fada. dariya Yusuf yayi wanda shi kadai yasan Ma'anarta yace Aikuwa Abar mgnr kawai. yawwa yazeed haryau baka samo Wacce kakesoba? bansamo ba Yusuf ni banga wacce tamunba! Kallonshi Yusuf yayi yace duk Matan dake fadin garin kaduna babu wacce tamaka? Eh Yazeed yace Atakaice danshi gabanshi ma dan faduwa yake.. Ok Yusuf ya fada Amma Kana nan kan idan kasamu yarinyar data kalle Cikin idonka tayi magana Xaka Aureta ko? daga Kafada yazeed yayi yace yes.
Atare Suka Sakko daga motar gaba daya Suka Shiga gidan. Da gudu Twins Suka karasa Ciki Suna kiran mai Kyau! Suma Shiga Su leemah Sukai ba kowa a parlon dan Haka Sukai Xamansu Anan. Nazir yace bari Naje Wajen Yazeed da Sauri Twins Sukace Suma Zasuje, fita Sukai Atare Sukai part din yazeed. Feenah tace ina mamy da Inno Suke ne? Leemah tace kya tambayeni nida mukazo tare, Kinsan Abba yadawo maybe mamy Taje mishi wlcm Sunyi missing juna kinsan, itakuma inno Inaga Wani Abun takeyi duka feenah takaima Leemah ke bakida Kunya ko? Toh Menene Ai gsky na fada, yawwa Feenah dazun baby kecemun Wai Asakamana Rana kamin nakoma Nace Nooo Saikin tashi Naki Auren. Toh waye kuma baby!? dan Rufe ido leemah tayi tace yaya Nazir mana. Tabe baki Feenat tayi tace Umm. Saiki bashi phone number dinki Kada mukoma Skul kina tunani. dariya Leemah tayi tace baki lura ba Amota ya amsa? Ina Xanlura fa kunshige gaban mota kuna Xancen love, Amma harda kukan munafurci ni feenah ina tsoro waye waye mtsww magulmata daga Ke har Shi. Inno ce ta Sakko daga Sama tana A'uzubillah wake tsaki irin na tsaka? Tashi Leemah tayi takarasa gunta tana dariya. Inno ta ya gida? Lfy Halimatu ta Shine kika fara Xuwa gidan Su Naziru baki Xomunba. Sorry Inno ba gashi yanzu Munzo tare da feenah ba. Kallon feenah Inno tayi tace Nafisatu yan makaranta... ina yini Inno? Lfy Nafisatu ya karatu? Yasu Hafsat?ya garin kuma? Ya Ummaru? Kallonta feenah tayi ta kauda kai don idan Akwai Abinda tafi tsana Shine yawan tambayoyi irin ya kaza ya kaza. daga gira Inno tayi Sama Ahhh Wlh kwarai Halinku daya da tsaka....kallonta feenah tayi tace waike kowa Saikin bata mishi Suna ne? bude baki inno tayi tace Laaa aisaiki fadamun bakyason Ina tsokanar yazeedu bawai ki rinka mun Kwana kwana ba. tsaki feenah tadanja Kadan. Inno tabe baki tayi tace Ummm gaskiyar Yusufa. Kallonta leemah tayi tace inno mai yusuf din yace miki? Zomuje daga Chan na fada miki Inno taja Hannun Leemah Suka bar Wajen. Kinsan me Yusuf ya fada mun kuwa? Aa inno fadamun! Kasa kasa tayi da murya, yace mun yazeedu da Nafeesatu Sun dade Suna Son junansu, Amma Sabida gaba dayansu Sarakan miskilanci ne yasa Suka Ki tsayawa Su Sanar da junansu, Amma yazeedu ya fada ma Yusuf yana Son Nafeesatu, kuma yazeedu Aure yakeso Sosai Sabida RANAR dana kori Kafurar yarinyar nan naje amsar kudi gunshi ya rufe kofa da Sauri ya Hanani Shiga, daga baya da idona Naga yarinyar ta fito daga bangarenshi tana Sanda, Toh ke Halimatu Kawar taki bata taba gaya miki tanason yazeedu ba? Leemah datunda Inno tafara maganar ta daskare Awajen tace, inno bata gayamun ba, Kuma inaga yusuf Wasa yake miki Feenah bazata boyemun komaiba,inno ke bakiga basa Shiriba ma da bro? Ke da alla Sakarya Yusuf yace irin tasu Soyayyar Kenan kedai Kada kifada Mata kibari muga gudun Ruwansu. Ajiyar Zuciya Leemah tayi tace Toh Inno.Amma kasan Xuciyarta Sam bata gasgata maganar ba. fitowa Sukai parlon Leemah jikinta duk yayi Sanyi So take Abunda Inno tafada yazama Gaskiya da tafi Kowa farin Cikin hakan kuwa. Su mubeen ne Suka Shigo tare da Nazir Wajen inno Suka nufa Suna dariya. Yusuf Naga ya Aje Wata mage kofar yazeed ya nufo Cikin gidan Shima. Kiran feenah Akai Awaya tace laaaa Leemah Kausar ce, bari Naje Waje na'amsa karfa kibiyoni. Toh Leemah tace Hakan ba Karamin dadi yama yusuf ba. Tana fita yace inno inaga wajen yazeed Zataje bakiji tana kada Leemah ta betaba. Ai ita Sakaryar Halimatu din nan bata yardaba inno tafada. Kallon leemah yusuf yayi yace barta inno yanxu zata yarda ai. Fitan Feenah yayi daidai da lokacin da Yazeed ya fito daga daki da Sanda A Hannu,dama ganin magen da yayi yasa yakoma ya dauko Sada dan yakoreta dan idan tana wajen bazai iya wucewaba tsoronta yake. Sandar yasaka yana dan ture magen itakuwa taki tashi. Feenah ce ta hango Abunda yake tace Kausar dan kashe kadan, bro din Feenah Kema mage mugunta Bari naje namishi ta tassss.
*Gud nyt lovers💕💕 Ina typing Ina gyangyadi duk because inasonku kamar yanda kuke Sona yasa na daure nai muku wannan*
Page....29/30
Karasawa tayi Cikin tafiyarta wacce kamar bata Son taka kasa. daidai gaban yazeed taja ta tsaya Kai Malan! dagowa yazeed yayi daga durkusan da yake ya Zuba ma kaykyawar fuskar feenah ido take gabanshi ya fadi Rasss. Itama feenah Ido ta Saka Cikin Nashi yayin da itama gabanta ke faduwa wani irin kwarjini taga yamata,jitake kamar ta juya ta koma Amma takasa motsin Arziki, daurewa tayi ta k'ara Saka idonta Cikin Nashi still takasa mgn, durkusar da kai kasa tayi tafara motse da dankaramin bakinta, Kai Anamaka Kallon mai tausayi Ashe Kai mugu ne! Yusuf ne ya karaso wajen yace Ahh feenah yazeed fa mai tausayi ne tsoronta yake Ji kawai, Amma idan kin isa ki kalli Cikin idonshi kifada mai bashida tausayi mana. kallon Yusuf Feenah tayi ta yatsina fuska tace, Kan mai Xan kasa?? Toh idan Zaki iya Kiyimana. d'aga kanta tayi tasaka idonta Cikin Na yazeed yayin data daga Dan yatsanta tana nunashi kai yazeed Sam bakada..... ai da Sauri Yusuf yabar wajen yana fadin Wlh itace matarshi. Feenah itakam mgn take mai bako iftawa bare inda inda,,,,,Kai dama duk wannan fadin Ran naka barinshi kayi domin Sam baya maka kyau, yanzu kazo kana ma mage mugunta katuna itama Hallitace kamar ka! kuma Sai Allah ya muku hisabi kan muguntar dakai mata, kana ganin kaidin kamar kafi kowa ne Toh kasan wa'inda Zaka rinka mawa mugunta,kada Abun ya kasance Har kan bayin Allah. daga Haka feenah ta bar wajen....da Sauri Su inno dasu Leemah dake lekensu Suka koma Ciki ganin ta tawo, Ashe Yusuf daya koma yace musu Suzo Suga su feenah na Soyayya, bayan Sunma Nazir bayani kuma Sunci Shima kada yamusu magana Shine Suka Leko Suna kallonsu Amma Sam basajin Abinda Suke cewa, Leemah har picture ta daukesu Dan ba karamin kyau Sukayi Ayanda Suka tsaya ba.....yazeed a inda tabarshi ya daskare pic din bakinta kawai yake kallo lokacin da take motsashi da irin yanda take nunashi da Hannu Sam babu tsoro ko fargaba Atare da ita lokacin da take maganar.....Yusuf ne ya karaso yadan bangaji kafadar yazeed firgitgit yayi yadawo Cikin Hankalinshi, Janshi Yusuf yayi Zasubar wajen Saiga feenah ta fito da Ruwa A wani Cup na plastic ta Aje gaban magen ko kallonsu bataiba ta kara komawa Ciki. daki Yusuf yaja Yazeed Kan bed Suka Zauna, yusuf Ya kalleshi ya daga mai gira yaaa tayi ko? Ajiyar Zuciya yazeed yayi ya yatsina face wace? Yusuf ne ya kalleshi yace wace kake tambayana, yarinyar nan mana. Aini koda Nace maka nasaka gasa tsakanina dakai bance maka harda yarinyar nan Ackiba, wannan yarinyar Abinda yafi hakama Zata iya, Dan dama batada kunya yazeed ya fada yana kara kauda kai. gyara Xama Yusuf yayi yace Wlh Malan baka isaba Ai Kaine Kace Mun koma wacece, Kuma Ai Wannan tacika kowani Sharadi dakace kafison mace ta kasance tana dasu. Yusuf Sharuddana Uku ne dan tayi daya Ai batai Sauran biyunba. Karya kake duka tacika yazeed. Na1. kace wacce kakeson ka Aura ta kasance mai tausayi! Agabanka yanzu ta dibo Ruwa taba mage, Kuma kana gani magen tasha Ruwan Sosai Sannan tabar wajen Kenan dama k'ishi take ji yasa tazo kofarka. Na2. Kace ta Kasance mai kuzari tahaka Xata iya kula da gidanka da kai kanka da kuma yaranka! So Ayanda feenah tamaka mgn tana Nuna maka yatsa bakinta na furta Abinda takeso ya'isa kaa gane cewa ita din Mai kuzari ce. Sai Abu na3. Kace wacce Xata iya kallon Cikin idonka tayi magana, Naga feenah tunda tafara magana bata kifta ido ba, gashi ta Sumar dakai Atsaye Sabida Xakin muryarta. Toh me kuma kakeso ka fadamun yazeed??? Numfashi yazeed ya Saukar Ahankali yace Abinda nakeso yanzu ka kyaleni Yusuf tunda kai kacika naci kabari Zanyi Shawara. "Alright" Yusuf yafada yace kasan gobe Xani Zaria ko Zaka Rakani? Allah ya kyauta na raka ka wajen Mace yazeed ya fada yayi Hanyar Cikin gida. Tashi Yusuf yayi yabi bayanshi Suka Shiga parlon Atare. Yanzu hatta Mamy da Abba Suna parlon fira kawai Suke Suna dariya. Inno Naganin yazeed Sun Shigo tafara waka....."Namiji kuchaki Ahadashi da kuchaka Kamarshi, Na miji miskilalle Ahadashi da Miskila Kamarshi" gaba daya parlon Suka Saka dariya Abba yace Inno keda waye haka? Kallon gefen idon yazeed tayi tace Amadi wakar mu muna yara na tuna kawai...tabe baki feenah tayi Aranta tace tshohuwar Nan bazata Rasa Aljanu ba bakinta Sam baya Shiru. Shima yazeed Cikin Xuciyarshi Cewa yayi ai gara dai goben tazo kitafi muhuta. Inno kamar tasan mai suke fada cikin Zuciyarsu tace Wanda ya Zageni Cikin Ranshi Allah ya hadashi da daidai Shi. dariya Suka kara kwashewa dashi. yayinda yusuf yatashi yace nidai Zan tafi Saida Safenku. Inno tace yusufa Agaida gida, Abba da mamy ma Sukamai Saida Safe. tashi Nazir Shima yayi ya Kalli Twins kutashi mutafi, tashi Sukai gaba dayansu harda feenah...Abba ne yace Nafisatu Kibari ki Kwana Anan mana.durkusar da kai tayi kasa tace toh Abba. Saida Safe Nazir yamusu, Yana kashe ma Leemah ido Sukafita da Twins dake ta rigima su Abarsu. Cemusu yayi gobe zasuzo tare da Mum, tukun Suka yarda. bayan Sunci Abinci Su Mamy Suka nufa Sama,inno ma tashi tayi tace bari naje nahada kayana tun yau. dariya Leemah tayi tace toh inno Saida Safe. Yarage parlon Saura Leemah da feenah besty tashi Muma muje mu Kwanta, tashi feenah tayi suka Haura Sama Atare. Cikin dare yazeed kasa bacci yayi daya rufe Ido pink lips din feenah yake gani Yayin da take motsa Small Mouth dinta, ga manyan idanunta lokacin da take magana wani irin Haske dasuke Kamar mai Shirin yin kuka, kara Mirginawa yayi tunowa da Yanda Kumatunta Suke lotsawa Ga Cool Voice dinta dake fita Ahankali wai Nan Ahakama bude murya tayi. Murmushi ya Saki tunowa da yanda take Nunashi da yatsa tana k'aradashi irin Alamar honing din nan. OMG yafada da karfi Cikin Ranshi kuma yace "Tabbas irin matar danakeson Aure kenan, duk Sharuddana ta Cika Su, Sannan gata da Kyau da ilimi" Noooo yafadi da karfi yayinda ya dunkule hanunshi ya buga Cikin dayan, Ni bazan Auri yarinyar Nan ba Sabida Abu daya, Abunda Naji Sunayi lastym, har Sai Nasan menene Sukayi Aranar. Sannan ma Ai Twins Sun fadamun Cewa tana da yawa kuka, ni banason mace lyk dat, don bansaniba ko Aljanu gareta, gata daji dakai, bama Hakaba Ai Sunce Aure Za'a Mata da yaron Uncle dinsu.tsaki yaja yacigaba da mirgine mirginanshi, da ker dai bacci barawo yayi gaba dashi Aranar. bangaren feenah itama kasa bacci tayi tana tunanin Anya mutum ne kuwa wannan brother din na Leemah? Shi Sam baya ganin darajar kowa, wannan Shi dama Sojane Sai ace Sun Saba da bakar Xuciya but ko yaya Nazir da yake Soja Ai baya irin haka. Kai Wannan matar dazata aureshi tashiga uku, Ni misali ko dauramun irin mazan nan Akai A kafa inajin da gudu Xan kwance Wlh. Tsaki taja tunowa da muguntar dayayi ma magen nan, take takara jin tsanar yazeed Acikin Ranta. bude Ido Leemah tayi jin karar wayarta dama ita Tuni bacci yayi gaba da'ita. ganin feenah batai bacciba Sai juyi take yasata waro ido besty baki bacciba kinaji Aka kirani har 5miscall baki peeking ba kuma yaya Nazir ne fa! gani tayi bata kalletaba yasa ta d'aka mata duka ina mgn kinyi Shiru feenah. Arazane Feenah ta tashi Xaune tace banfa jiba. daga gira Leemah tayi tasaki Murmushi lokaci daya tace da kyau,tunowa datayi lokacin da take irin haka A Skul. Menene feenah ta wurga ma leemah tambaya? Aa ba komai ki Kwanta kiyi bacci nace. Ok feenah tafada yayin da taja blanket ta rufa. Murmushi Leemah takara Saki yayin data d'aga wayarta dake famaan Ruri.....
da Sassafe Inno yau tariga kowa tashi,daret kuma kitchen tashiga Acewarta bari ta hada musu karin kumallo Yanda dasun taso Sukaci Abba ya maidata katsina. Aiko waina tayi da miyar taushe wanda yaji tantankwashe.feenah ce tafara Sakkowa jin kamshi kamshi tanufa kitchen inno ta gani ta gama hada wainar tashirya tsaff. Inno ina Kwana, Saida Aka dan kwashi lokaci tace Lfy a takaice wai itama miskilanci tafara irin na yazeed da feenah😂 tabe Baki Feenah tayi tace toh dame Xa'aci wainar? Kular data Zuba wainar inno ta dauka takai kan table saida tadawo tace, da Ruwan Lipton...tsayawa feenah tayi tana kallon Inno ganin Yanda take bata Amsa, daga bisani ta daura Ruwan Zafi a huta tana Shirin yin kunun gyada. Kasa daurewa inno tayi tace Nafisatu Ki kira hafsat tazo da iyalinta dan naga tanason waina kinga Saisu karya Anan ko? daga mata kai feenah tayi kawai.Inno takara Cewa Zaki kirata ne koni na kira ta? Kirata feenah tace A takaice, Inno ta karkada Kai Alamar mema yasa take kula wannan yar? daidai Sanda Feenah tagama hada kunun gyadar inno takara juyowa Nafisatu Mutan gidan har yanzu basu tashi ba? "Eh" feenah tace tafita da place din hanunta, kwafa Inno tayi tace Zakuyi nadama. Karfe 8 daidai duk yan gidan Suka tashi Kowa nashirin wanka. Inno taba Leemat waya takira mata Mum mahaifiyar Feenah wai suzo su Karya tayi waina.Amsan phone din Leemah tayi Sanin fitina irin ta Inno. Aikuwa ba'afi Minti 30 ba Su mum Suka karaso gabaki dayansu Har dad, Nan Akayita Murna aka wuce danyin breakfast. Fitowar Yazeed daga Wanka Kenan Yana Shirin Shafa mai yasa Kaya,tura kofarshi Akai Ahankali Aka Shiga, Innalillahi ya fadi da karfi ganin Mufeeda ce! Murmushi tayi takarasa shiga Ciki tace yadai? Kofa ya nuna mata yace tashi kifita kamin na karyaki Acikin gidan nan.Murmushi ta kara yi tace duk Abinda kace daidaine Zanfita Amma kasani Ayau Saina dandana Yanda yazeed yake! Ido yafiddo waje yace bakida hankali ne?kitashi kifita nace, kona Zaneki Cikin gidan nan kuma Naga Uban da Zai tsaya miki. dariya Mufeeda tayi Sosai tace babu wanda Zai tsaya mun kuwa Sabida Kana takama da kyau da dukiya, Amma Kasani yau Saika biyamun bukatata Zanbar gidan nan,kokuma wlh yanzu Nafita Nashiga gidanku nace Raping dina Kayi Kuma Kake guduna kaki ka aureni, kuma kasan tsaff Zasu yarda domin ran Nan kakar ka taga Sanda Nafita Inaga tarufamaka Asirine kawai. dafe kai yazeed yayi ya Zauna kan bed yana kara dayasanin Sanin mufeeda Cikin Rayuwarshi....karasowa tayi gaff dashi Honey Kayi hakuri Sonka nake da yawa Sha'awarka ta Hanani Sukuni ka daure muji dadin Juna wata kila kaima kasaba da irin haka. Runtse Ido yayi wani irin takaici yakeji Aranshi, tashi Yayi Xaidau jallabiyarshi yasa, mufeeda takara Xaunar dashi pls honey ka kulani mana...hannu takai kan kirjinshi tana Shafa gashin tana honey wanann yana burgeni, Yazeed duk jikinshi yayi Sanyi yafara fita hayyacinshi domin shidin mai Saurin Sha'awa ne. Ganin haka Mufeeda tafara zarcewa! gaba daya tafara wasa da Sasan jikinshi, Shima gaba daya yafita hayyacinshi bakinta ya kamo yasaka nashi yana kissing dinta sosai tana mayar mai da martani. dad ne yace munata cin dadi banga dana ba. da Sauri Inno tace Halan yana chan yana cika yana batsewa,dad yace yakamata Akirashi Shima yazo yayi breakfast. Mum tace Mubeen jeka kira mai kyau kace yazo. da Sauri inno tace ai tunda Nafisatu na kusa Kawai taje takirashi, kallonta Feenah tayi ta galla mata harara, dad yace Ummina kirashi mana tashi tayi tanajin Haushin inno ta nufi part din yazeed. Su yazeed an Lula gaba daya bema san awaci duniya yake ba. Knocking take iya karfinta ba'a budeba. Mufeeda da tunda aka fara taji, murmushi tayi domi burinta yacika, dama So take Wani yagansu tasan dole za'ace ya aureta ta hakane Xata cika burinta na mallakarshi. tura kofar Feenah tayi da karfi dantana ganin kamar wulakanci yayi mata.....Ido ta fiddo waje yayin da take maimaita innalillah. Mufeeda Aranta tace yawwa kanwarshi ce Afili kashe mata Ido Mufeeda tayi tana cigaba da Shafa Jikin yazeed duk dacewa da kaya Ajikinta Shikuma towel ne kawai amma ya rufe.....Saman kirjinshine kawai Abude. fita feenah tayi jiki ba kwari har wani duhu take gani tace yace yana Zuwa daga haka tayi sama Abinta. Shikuwa gogan bema San me akeba kokarin cire ma Mufeeda kaya yake tayi Sauri ta Tashi daga jikinshi, domin dama ita har ga Allah tana tsoronshi irin yanda yake juya mace baya ko gajiya. jakarta ta dauka da gyalenta tace honey Anzo Ana knocking inaganin nemanka Ake, kaje kada Akara zuwa ni natafi, Karka damu zanfita lfy. daga haka tayi Hanyar waje. tashi yayi rike da mara yashiga toilet.
0 comments:
Post a Comment