*♣ABBAKAR♣*
*Rubutawa*
*Fatima Aminu Ya'u*
*(F.A.Ya'u)*
*Godiya*
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da yabani ikon rubuta wannan labari, Fatan Allah ya nunan ranar dazan kawo qarshensa.
Kazalika ina godewa iyayena fatan Allah yasaka musu da alkairinsa.
*jinjina*
Jinjinata gareku take masoyan novels dina bazan gaji da jinjina mukuba masu bada lokacinsu su karanta littattafaina.
*'Dan bayani*
Wannan labarin qirqirarrene na qirqire shine dan fa'dakarwa, nisha'dantarwa, duk wanda yaji wani abu dedai da nasa ayi haquri akasi aka samu.
Kuskuren dake ciki amin afuwa ajizanci ne na 'dan adam.
*Sadaukarwa*
In dedication to my life.
*1-5*
*Dasunan Allah me rahma mejin qai.*
Juyi kawai yake baccin yak'i zuwa, tun bayan hutun dasukai na semester ending bacci yai masa k'aura koya kwanta baya iyawa saidai yaita juyi farin ciki tuni ya da'de da masa k'aura komai yake yak'e kawai yakeyi......Yau take jajiberin komawarsu makaranta duda ba al'adarsa bace shiga sch ranar da aka koma anman segashi tun watan da ya wuce yake tsimayin ranar dawowa..
Ji yake gabaki daya daren ya masa nisa gani yake kamar garin bazai wayeba ganin da yai baccin da gaske bazaizo ba yasa shi mik'ewa dan dauro alwala.
Asubar fari ya farka daga gajeren baccin da besan sanda ya 'daukeshi ba duda kuwa yadda wani bacci me dadi ke 'dibansa ayanzun haka ya daure yai wanka yafice masallaci.
Shida dai-dai ya gama shiryawa ko abinci bai tsaya ci ba ji yake kamar yai tsuntsu yaje makarantar, Da 'dan saurinsa ya sakko daga samansa yai sashin Hajiyarsu yana 'daura agogonsa.
Kamar yadda ya zata tana zaune tana wutiri kamar yadda al'adarta take ya'dan zauna kamar minti talatin bata shafa ba yana duban agogo yaga shida da rabi ya mik'e yai wajen falon yana kiran maryam dasauri ta fito daga magirka rik'e da cokali....Yaya ina kwana lafiya lau agogo sarkin aiki har'antashi kenan eh yaya to yayi kyau kicew Hajiya nazo tana addu'a nafita to yaya abincinfa a'a kibarshi innaje office nasha ruwan zafi to yaya seka dawo.
Harya kai bakin k'ofar dazata sadashi da babban falon gidan Hajiya tace Allah ya dawo dakai lafiya dasauri ya dawo ya zube har 'kas ina kwana Hajiya lafiya lau ta fada tana murmushi ni zan futa to Allah yakaika lafiya ya dawo da kai lafiya Amin Hajiyarmu ya mi'ke yabar falon.
Bakwai da rabi a B.U.K ta masa office dunsa ya wuce ya 'dan shisshirya takardun dazai bu'kata yasha tea sannan ya fito zuwa
class.
Ahankula yake tafiya burinsa koda sau dayane ya doro idanunsa akanta dan abinda yada'de yana muradi kenan.
Kamar daga sama yaji ance good morning sir har cikin ransa yaji wani abu yar yasokeshi tabbas ita ce dan muryarta ta da'de da zama daram a kwanyarsa duk inda ya jita cikin mata 'dari sai ya ganeta.
Be juyo ba ko nuna alamar ya kula ya amsa da morning yai gaba kamar ko yaushe bata damuba Aisha tace kuyi sauri mu tafi aji kunsan halin mutumin nan inyashiga minyi rashin tayau inyaso se yai attendance.......gaskiya ni fitsari nakeji kamar ya zubo sai dai inna rasa dan bazan iya zama dashi ba inji Ummulkhairi se kindawo inji Aisha.
Muje in raka ki inji Fatima a'a Fatina ki tafi karkiyi missing banso mu biyu mu rasa inkinanan kamar inanan ne a'a wallahi se naje kina da matsala muje.
Ina captain yake ya fada yana tsaye jikin madogarar malamai bezoba yayi kyau wani yazo ya gogen allo ya fada yana mik'o duster din .
Yayin da 'dalibi guda ke goge allo shikuma yana duba takaddun da yazo dasu saidai ahak'ik'anin gaskiya bawai takaddun yake dubawa ba afakaice 'daliban dake zaune yake kallo kaf ya dubesu sedai idanunsa sun kasa hango masa ita wato bata zo ba kenan kome.
No to muryar wa yaji hakan kenan na nufin santa yafara zautar dashi ta yadda inyaji muryar wata zai zata ita ce .....wani tunani ne yazo masa yai bakin k'ofa inda makararun 'dalibai ke tsai tsaiye duda sunsan bazai barsu su shigoba.
Kaf yabisu da kallo bata cikinsu yadan fito kadan suna zaune ita da k'awarta sai wata dabai saba ganinsu tareba sai namijin da indai zaigansu zaigansu dashi shima yana zaune kome suke tattaunawa yafada aransa oho.
Sannunku wato kune shafaffu da mai ko dabazaku iya tsaiwa ba sukai zuru zuru da ido suka kuma kasa mik'ewa yayi kyau yace .
Kuna tsayen zaku iya shigowa wannan yazama last time dazaku zomin aji a makare. Mungode malan ku godewa kanku ya shige ajin sukuma suka bi bayansa.
Bayan ya rubuta Topic din dazasuyi yau yajuyo kamar yadda na fada muku a first semester wata'kil in zama mutumin da zan daukeku wannan course din wata'kil a canza to ba'acanzaba kunsan dokoki na dan haka bana bu'katar sanar daku wanda suka mance su tambayi sauran 'Yan aji.
Yadan matsa bakin k'ofar kai yanzu bakaji kunya ba kana namiji kana cikin mata azaune ragwanci ba na maza bane yai shiru any way wato ku baza iya mik'ewar ba ko a'a malan munyi zaton bazaka barmu mushigo bane inji Fatima yayi kyau to yajuya Sorry sir yaji muryarta ta daki zuciyarsa yadan murmusa burinsa daman tai magana be juyo ba yace sorry for ur self pls sir amana afuwa ta kuma fade yadan juyo fuakar nan murtuk zaku iya shigowa but this should be ur last time coming to my class late. Ya shige ciki.
Yana rubutu suka shigo juyowar dazaiyi Ummulkhairi na 'kok'arin zama me idonsa zai gani ciki gareta dan da'kyarma ta zauna anya kuwa ba gaskiya idansa ya fada masa.
I have to get my self prove ke da kika zauna yanzu dawo gaba, Ummi da suka shigo tare ta mi'ke no bakebafa I mean Ummulkhairi bemasan ya fadi sunan ba gabaki daya ajin suka juya suna kallon Ummulkhairi watoyama san sunanta kenan wannan dan girman kan malamin.
Itakuwa mutuwar zaune tai jin yakira sunanta wato bama afuska kawai yasantaba harda by name wai bakiji ni bane Fatima ta tab'ota ki koma karya koreki.
Ta mik'e daK'yar tayo gaba innalillahi wa'inna inna ilaihirraji'un dagaske cikin gareta mesan samu nane yafa'da cikin ransa wato matar aure yake ma masifar so san da baijin zai iya rayuwa without ita a rayuwarsa.
Tazo inda ya nuna mata ta zauna da sauri ya juya ya ya goge hawayen da yatawo masa dan besan sauran 'daliban su gani.
Wayarsa ya'dauka kamar yana waya ya hau salati to ganinan ya maida aljihu captain dinkuwa yazo ya mi'ke 'dalibin dake zaune dasu ummu ne ungo wannan out line yana ciki gameso zai iya photostat dinsu inada wani abune me mayin manci pls am sorry yafice bai jira amsarsu ba........
*Zancigaba insha Allah*
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*5-10*
*Dedication to my life*
Yana barin sch gate 'din hawayen da ya boye suka kwace seda yai nisa ka'dan da makarantar sannan yai packing kuka kuwa me 'karfi ya kwace masa yai kuka sosai har saida dankansa ya fara rarrashin kansa da zuciyarsa ya'dan jima a gun kafin ya goge hawayensa yabar wajen.
Acan sch kuwa bayan fitarsa 'dalubai sukayo kan Ummu suna tambayarta waike taya akai wannan 'dan rainin hankalin yasan sunanki ta ta'be baki taya zan sani "bakuga mutuwar zaune nayi ba dajin sunana abakinsa" "Ai wallahi naso ni yakira" inji Aisha "kunifa nasan da sansa zan mutu maryam ta fada suka saka dariya gabaki daya"
Maryam wai me damun yayanki ne? Hajiya ta tambaya "wallahi bansani ba naga dai kamar yana cikin damuwa " bari inje 'dakinnasa inji ta mi'ke tai section d'insa, yana zaune kan doguwar kujera kansa sama sai filo dake ri'ke a 'kirjinsa hawaye na bin fuskarsa "subhanallahi mezan gani inji Hajiya"
Me ke damunka ni mamarka ce ka'dan meke damunka I a sure u i will clear them all cikin zuciyarsa yace "Naso zaki iya mum sedai wannan ya wuce tunaninki naso zaki iya sharen hawayena saidai bazaki iyaba bakuma naso in saka ki cikin damuwa" Allah hajiya ba komai ta kalleshi cikin fushi yanzu kanunan ban isa dakaiba tinda bazaka iya fadan damuwarka ba ta juya zata fice.
Yai saurin kamo hannunta wallahi ba haka bane kawai na tuna da Baba Alhaji ne shiyasa nashiga damuwa bakuma nasan kema insaku come kin damuwa shi yasa naga gwanda inzauna a'daki ta juyo ta goge masa hawayensa bata iya cewa komi ba tabar 'dakin dan batasan yaga hawayenta.
Ahankula yace ki yafemin Hajiya na miki 'karya na kuma tuno miki da Alhaji ki yafemin.
Ummu pls kiyi sauri karki makara katafi kawai i can drop my self kinga ni kiyi sauri bakya ganin cikin ne dake tai dariya na rasa me yasa kullun kake ganin kamar wannan cikin zaisa nazama lazy to da ke din mece pls be quick kin isheni da surutu au surutu nake ma to na fasa shiga motar taka haba abar sona pls ki tawo mutafi ta bude ta shiga tana turo baki ya rufe motar gami da jan motar yabar gun.
Allah ummu ban ta'ba ganin couples da suka dace da junaba kamar keda yayanki Allah ko sosaima tai dariya kawai.kinga kuma ni ban taba ganin dacewarmu dashi ba shi yasa ai kullin kike sansa kamar ranki baki da dama Aisha ni nace miki ina sansa any way mubar maganar.
Pls Fatina wai mene damu ne ummu ta tambaya. ina zaton 3304 muke au kina zato ne ma u are not serious wallahi anman ai nafiki tunda ke tambaya ma kike tai sukai dariya baki daya kinga mutafi aji koma mene magani acan suka wuce ajin.
Duk yadda Abbakar yaso mantawa da ummulkairi abin yaci tura kullin kamar 'kara masa santa ake innalillahi wa'inna ilaihirraji'un waime kesan samu nane Allah ka yaye min ka kuma yafemin ya fa'da.
Wayarsa ya 'dauka ya kira khairiyya wata frnd 'dinsa ta facebook be ta6a ganin yarinyar ba anman ya rasa me yasa ya yadda da ita sosai.
Wayar tata akashe take hakan yasa ya kunna Data 'dinsa ko Allah zaisa tana online aikuwa kafin ya shiga inbox 'dinsa message 'dunta ya shigo sallama ce kamar kullin wani ma ya shigo yayana yakake kwana biyu banjika ba na kira number dinka akashe yai murmushi.
Lafiya 'kalau 'Kanwata na'dan shiga matsala ne anman Alhamdulillah everything is normal ya tura mata wasu 'yan seconni sa'konta yashigo ayya Allah ya sau'ka'ka komai amin 'kanwata.
Wai yaushe zamu hadu ne? Ya tambaya ta turo hoton emoji alamar she is thinking matsalarki kenan kullin na miki maganar ha'duwa sekiyi tamin wala wala tai dariya let's give time some time yai dariya kullun haka kike cewa yayana mu hadu anjima yanzu malami ya shigo ajinmu ok .
Yau sati biyu kenan rabon Abbakar da sch tun randa yaga ummul kairi da ciki yaji a tsani makarantar ji yake kamarma yabar aikin sedai tuno yadda yasamu aikin yashi dolensa ya yanke shawarar komawa kodan kar ya cutarda students dinsa.
Yau yashirya zuwa hakan yasa yagama komi section din Hajiyarsu yaje sukai sallama ya wuce.
Yana tu'ki yana addu'a Allah yasa yau bata gaba wata'kil inbata gaban inbaya ganinta sosai yafijin kwarin gwiwar yin lecture din.
Aikuwa yana 'dora kafarsa acikin ajin idanunsa ita suka fara gani tana dariya ita da Fatima 'kawarta da alamun tanajin dadin firar dasike tai masa kyau sosai a ido innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un abinda kawai ya fara fa'de kenan jiyai kamar 'kafafunsa bazasu 'daukeshi ba juyawa yau dan barin ajin........
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*10-15*
*In dedication to my life*
Haba Abbakar be strong mana wani 6ari na zuciyarsa ya fa'da masa ya juya kawai ya shiga ajin duda yadda 'kirjinsa ke bugun uku- uku.
"Good morning class ya fa'da" morning sir suka fa'da suma "am sorry for my absence banji da'di bane kwana biyu hope u all read the manual i gave?" Yes gabaki 'daya ajin suka fa'da yayi kyau "I just have to guide u kunmin aikin" suka saka dariya gabaki 'daya.
Daurewa kawai yake ji yake like 'kafafunsa bazasu iya supporting 'dinsa ba dole in nemo ma kaina mafita ya fa'da.
Kamar yadda na fa'da muku banji da'di ba kwanakin baya sabida haka bazan iya tsaiwa na 2 hours anan ba inaganin zan koma baya zanyi anfani da microphone 'dinnan danku fi jina.
Captain ne ya mi'ke sir bari in samo maka kujera no kabarshi ga empty sit can Anman sir se minfi ganewa in muna ganinka inji Aisha eyye but i might ended the two hours standing before this ur lazy lout captain find the sit for me, i just don't me kuka gani kuka zabeshi as ur captain but sir He is a hard worker fa inji wani student, oh I see shiyasa He can't stand for 30m ya gwammaci zama cikin mata pls let me go back before u just called me lazy teacher gabaki daya student 'din suka sa dariya.
Bayan ya gama lecturing student 'din ya fice at list ya'danji sanyi cikin ransa, yana fita wasu cikin 'yan iskan ajin ya mi'ke ai mu daman tuni muka gane dan Haka kai captain ka shirya zamu sayo ma zani da hijabi ka koma 'daurawa, babawo ya mi'ke ai se aha'do dana malan inda yai dedai da shigowar Abbakar dan 'daukan takardun daya mance oh abie ya fa'da se asayon me kyau, yabar ajin be jirayi amsarsu ba. Gabaki daya ajin suka sa musu dariya ganin yadda suka tsure.
Yau kimanin sati hu'du kenan Abbakar bega Ummu a class 'dinsa ba ada zatonsa da tunaninsa inbaya ganinta santa da kullin ke ruruwa a zuciyarsa zai ragu sedai rashin ganinta na 'yan kwanakinnan ya dameshi tunaninsa kullin me yasa bata zuwa.
Kota mutu ne ya fa'da no she won't die in ta mutu am dying too but she belong to some one zuciyarsa ta fada masa Ya'ilahi save me out of this.
Ashe sani ne beba 'dan ganinta da yake ba 'karamin 'debe masa kewa yake ba gashi khairiyya Facebook friend 'dunsa bata online sati biyu kenan ko wayarta ya kira bata shiga gabaki 'daya duniyar tai masa zafi ya rasa wazai fa'dama damuwarsa yaji da'di.
Hello wai kana ina ne gani a gidanku Hajiya tace yanzu ka fita mahfuz ne ya kirashi, No ban fitaba in garden ok ganinan yana zaune yaji anyi sama da littafin da yake dubawa na lecture da zaiyi gobe mtss yai tsaki wai kai mahfuz yaushe zaka girma ne bakamin sallama to al'uztaz Assalamu alaikum ya amsa ga guri.
Kasan Allah banyi zaton ganinka yanzu ba mahfuz ya'dan 6ata rai eyye wato ban isa inzo gunka ba kenan No ba haka bane kawai ina tuna rabuwarmu ta baya ne mtsss matsala ta dakai ru'kon tsiya inji mahfuz pls forget that's was bygone .
Pls Abbakar kafa'dan gaskiya me ke damunka jibi duk ka rame ka kuma yin ba'ki, me kuwa zai da men banda abunka mahfuz kasan munsha strike kullin ina gida yanzu ankoma kullun kana tafe ga hayaniyar student dole in 'dan rame kafin jikina yasaba.
No Abbakar kark layance min mana look at how u are turning to skeleton bawai fa ramewa kawai ka'danyi ba kamar yadda kake fa'de yasa dariya kaifa 'dan iskane mahfuz wato ni ne skeleton 'dinma no bance kai bane nadai ce kana komawa am ok nothing is wrong inji Abbakar.
Any way what's the urgent call for eyye lallai mutumin wato ma tambaya kake to sarkin mita calm down ba haka nake nufiba kawai dai nasan me zakace maganar kwanaki ce kai wallahi kafi matsala that's was bygone pls learn to forget mana ok ya wuce.
Yanzu dai bazaka fadan meke daminka ba ko mahfuz ya tambaya oh my Goodness aikaima kasan mahfuz duk duniya babu wanda yasanni ciki da bai kamarka inda akwai matsalar kasan before hajiya taji kaine zakaji bazan 6oye maba.
Ni wallahi matsala ce babba ta taso min inji mahfuz subhanallahi matsala inji Abbakar eh wallahi mahfuz ya fa'da.
Am in love mahfuz ya fa'da cikin muryar tausayi dariya 😂Abbakar yasa kai malan karka bada maza mana being in love isn't problem malan inji Abbakar mtsss mahfuz yaja tsaki kai ana kaika kana tirjewa matsalar shi ne wadda nake so 'din to wace kuwa wannan mesa'ar.
Bafa kowa bace face Ummulkhairi wannan cousin 'din tawa what Abbakar ya fa'di yana zare ido alamar firgici.
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'U*
*15-20*
*In dedication to my life*
Wai khairiyya dai dakai ta bani labarinta ehfa ita wadda tai sanadin fa'danmu kwanaki ta You must be joking abbakar ya fa'da wallahi Ba wasa nake ba I mean my words.
Anman kaima ka cika tarar aradu da ka how do u think zata so ka Abbakar nasani nima ba lallai tasoni ba nasani zan iya zama mutun na farko da duk duniya ta tsana sedai ba lefi na bane kullin innai 'ko'karin mantawa da ita se abin yaci tura kai nifa kamar 'karan santa ake, Abbakar yai 'dan murmushi irin na tausayawa natausaya ma anman kasan mene alhakinta ke 'dawainiya dakai Yanzu abinda zaka ce kenan nagode no ai gaskiya ce nasan kuma kasani sedai kasallama.
To yanzu kai sa'ace kasan inda take yanzu se kaje kace kanasanta me zai hana shi yasa ma nazo dan ka temakan in nemota dan in convincing 'dinta ta yadda ta aureni hhhhh lallai mutumina ka kamu da yawa inji Abbakar kasan Allah inkana dariyar nan mugun haushinka nakeji inbazaka temakanba ne ka fa'dan.
Kafin Abbakar yace wani abu wayarshi tayi qara da sauri Mahfuz ya le'ka to sarkin gulma kalli da kyau sukai dariya tare sallama ya Amsa gami da fa'din lafiya lau 'kanwata ya gida ya kike sun 'dan ta6a fira kafin suyi sallama.
Daman nafa'da u are in love fa'dan ne bazakayi wato baka yadda dani ba shiyasa bakasan fa'dan sirrinka oh my goodnes kanada matsala wallahi .
Wayarsa ya 'dauka ya kira khairiya bata wani yi ringing da yawa ba ta dauka hello qanwata na'am Yayana lafiya dai yanzu mun gama waya ka kuma kira wannan abokin nawa ne da nake baki labari yakesan magana dake wai yana fa'din muna datin junanmu ne tai dariya baka fa'da masa kaine ma'daurin aurena ba gashi ki fa'da masa dakanki.
Sun gaisa da mahfuz kafin tace abokin yayana be fa'da ma inada miji bane yai dariya taya zai fa'dan to gashi ku gaisa kafin yace wani abu yaji muryar namiji ya amsa suka gaisa ai kullin inajin labarinka gun Khairi se yau Allah yai zamu gaisa mahfuz yace bama Abbakar 'din bane abokinsa ne oh to bashi mu gaisa sun gaisa ya kashe wayar batare da baima khairiyyan ba.
Hope u are now convince yai dariya sosai ma, kaga daga yanzu nagane wallahi u don't trust ne inji Abbakar harfa rantsewa kake eh wallahi inma ka yadda dani not like I trusted u, for me u don't have to prove what u said is gaskiya ko qarya, what I need na yadda shine kawai kace 'din in yadda.
Am sorry nima ai bance dole se ka kirata ba impact ma bani nace ka kirata ba mtss kaji dashi yamiqe yai cikin gida.
Gabaki daya abun duniya ya ishi Abbakar dan ya rasa wazai fa'dama abinda ke damunsa gashi 'dan ganin ummun da yake ma ya dena kwata kwata.
Yau yana zaune gabaki 'daya duniyar ta masa zafi yarasa me zaiyi kamar daga sama idea tazo masa ya miqe yana murmuahi nasan me zanyi.
Wayarsa ya duba kaf babu number 'din da yake nema can ya tuna a littafin da ya rubuta ya'dauko ya kira ringing 'daya ya 'daga.
Daga 'daya bangaren aka yi sallama ya amsa yawwa ina magana da mas'ud ne eh aka bada amsa to ka fasanar da class members 'dinka ranar litinin zanyi C.A 'dina kana magana da Abbakar muhammad Abbakar ok sir nagane zan sanar dasu ya kashe wayar.
Shi ka'dai yasan dalilin yin hakan ada be ma da niyar yin test 'din a 'yan kwanakinnan.
Wallahi Aisha narasa yazanyi kinsan monday mutumin nan zaiyi test gashi Ummu bata da lafiya nasan kuma in nayi mata zai iya ganowa tunda yasan sunanta kumafa haka ne.
Mas'ud yace kawai kuzo muje office 'dinsa inyaso se mu masa bayani in anyi sa'a in taji sauqi in yaso Allah se ya mata
Ni wallahi tsoronsa nake inji fatima daurewa zakiyi muje yazanyi haka zani ai.
Sunyi sa'a kuwa yananan bayan sunyi nocking yace su shigo suka kuwa shiga da sallamarsu, sun gaisheshi kafin captain yace daman sir game da test 'din dakace zakayi ne ok wata matsala ta farune ya fa'da yana duba takaddunsa a'a daman daya daga cikin student dince lafiya shine mukazo mu fa'da ma ko in taji sai'ki za'a mata make up.
Wace kenan Ummulkhairi muhammad Dalhat saida gabansa ya'dan kafin yace meke damunta eh daman an mata CS ne tazo haihuwa a'dan ratsane ya 'dago what cs ya fa'da ayanayin dashi kansa besan sanda ya shiga ba eh ok Allah ya bata lafiya suka amsa da amin.
Ungonan ya miqo paper rubutan sunanta da registration number 'dinta ok sir gashi na rubuta to intaji sau'ki sai tazo ta sameni ta tawo da shaida 'din tabbas bata da lafiya ok to sir mungode suka fuce.
Hankalinsa gabaki 'daya ya tashi tausayinta duk ya kamashi ashe Aiki akai mata yadda ya damu wani 6arin na zuciyarsa ke fa'da masa matar wani ce fa kake damuwa akanta subhanallahi ya fa'da yai saurin miqewa ya shige toilet.
*Zancigaba insha Allah*
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*20-25*
*Wattpad Fadimafayau*
Miqewa yai ya shiga toilet ya dauro alwala yazo ya alwala gabaki daya yarasa abunyi hakan yasa shi tada sallah ko Allah zaisa yadanji sanyi cikin ransa.
Saida yai azahar sannan yabar office din bayan ya gama nemawa Ummu sauqi da datan Allah ya raya abinda ta haifa.
Yunwa yakeji sosai hakan yasashi wucewa gida duda a yan kwanakinnan be cika san zama cikin jama'a ba.
Da maryam qanwarsa yaci karo a farfajiyar gidan tana baima Habu me tuqi saqon ta qara fada da murmushin fuakarta yah sannu da zuwa shima ya amsa yana dariya yawwa gami da shaqar numfashi hmmm qanwar me ake dafa mana ne wani abin dadi ne kamar kinsan yunwa nakeji aikuwa dai sha kuruminka yanzu cikinka zai cika yabi bayanta batare da yace komaiba.
Pls qanwar ki fadan me kike dafa mana ne kaidai kawai kabari azubu ta shige madafa yabi ta kitchen din zai leqa tukunyar pls yaya to sanmin kar qamshi ya qosar dani ta dan debo miyar a ludayi ta bashi yana kaiwa baki yasaki wata qara gami da cillar da ludayin.
Tai saurin matsowa daf dashi yah lafiya ya dago ya galla mata hara anman ke muguwa ce wallahi kinsan da zafi zaki bani tasa dariya kai yaya anman kai ragone wallahi ni nadauka wani abune ashema dan zafinnan ne zaka wani saka ihoo au dariya ma kike to anma fasa cin abincin naki danma inai miki kara ina cewa kin iya girki to ki sani ba abinda kika iya fuuu ya fice daga madafar ta ci gaba da dariyarta.
Saida ya watsa ruwa yaji dagaske yunwa yakeji gashi qamshin abincin ya cika masa hanci ya sauko daga sama yai sa'a bata falon sai hajiya.
Kai tsaye dinning area ya wuce ya debo a plate yai sama hajiya tace ina zuwa inazuwa hajiya bari inkai daki kar wannan mara kunyar ta ganni hajiya tasa dariya kwaji dashi.
Saida yakai matattakala ta biyar yajiyota tana dariya ahab ashedai na iya abincin tunda har yasamu matsayin akaishi daki aboye mtss ya saki tsaki anma fasa ci yazo ya dire eh ya qara afki au haka kika ce to sema naci.
Yq haukan kujera ya fara zubawa ai yarinya da dakudinki kika siya to bazanci ba eh anman ni na dafa abinda bama dadi ci karka mutu ne fa yana fade yana yamitsa fuska ya turawa abaki kamar anai masa dole eh shiyasa naga anata saka loma.
Hajiya innaje masallaci bazan dawo da wuriba zan biya ta gidansu mahfuz karkiga nayi dare ok inka dawo nayi bacci katashi maryam ta shiga daki katabbatar dik sun rufe dakunansu ok hajiya.
Yau ya yanke shawarar samun mahfuz ya fada masa komai ko yaji sanyi aransa dan zatonsa rashin fadawa kowa da barin komi cikin ransa yasa abin ke damunsa sosai.
Yaje gidansu mahfuz sun dan gaggaisa da mutan gidan dan gidan yawane mahfuz baya dakinsa hakan yasa ya zauna a farfajiyar gidan suna fira da mamar mahfuz din ya tura ummi ta kira masa shi danshi bashi da al'adar zuwa gidan yai ta shige shige tun yana yaroma balle yanzu duda ba inda aka masa katanga da shiga.
Maman maufuz tace kudai zanga lokacin da zakuyi hankali yasan kwanan zancen dan haka yai shuru ace kuduk qannenku sunyi aure ku godai godai daku kunkasa sai yawo kuke waiku samari bakusan kun tasanma zana tuzurai ba ta sosa qeya aishi hajiya sure lokacine eh haka kullin kuke cewa mahfuz yafito riqe da yaro ya miqawa hajiya kai kana da matsala ace kai bazaka taba zama dan gida ba Tashi muje sukai bangaren mazan gidan.
Sun dan taba fira kafin mahfuz yace nasan da magana shi dan haka kawai bazan ganka da daddareba kaidai bari inji Abbakar ina cikin matsala.
Mahfuz ya zaro ido matsala eh wallahi am in love mahfuz yasa dariya kaji wai matsala love isn't a problem malan wace me sa'a ce haka student dina ce and she is married with baby mafa what mahfuz ya fada.
Taya haka ta kasance zakayi kuskuren kamuwa dasan matar aure nima bansani bafa sedaga baya subhanallahi da matsala babbama inji Abbakar kullin wallahi kamar qaran santa ake a zuciyata narasa meke min dadi.
Inada mafita Abbakar yace mafita kamarya kace she is ur student eh and kasan students can do anything to pass there exam kayi anfani da wannan daman ta zama secret wife inka what me kake nufi nasan ka gane ka nuna mata if bata yadda dakaiba she is failing ur course kawai yaja tsaki wannan ai ba mafita bace shirmene.
Cemaka nai inasanta bawai ina sha'awarta ba and i wanted us to be together for the rest of our life not for wani lokaci kayadda dani once ka sameta zakaji abinda ke daminka aranka aqalla rabi ya ragu ko kuma ta qaruba yaja tsaki koda banyi shashanci ba sai yanzu da girma ya kamani ya fice daga dakin afusace.
Zaune yake yana marking test din daya yi aka kwankwasa kofar yace yes shigo ta shigo da sallamarta ummu ce ya fada dan ko cikin mata dari yaji muryarta sai ya ganeta .
Ita dince kuwa tai masa kyau sosai kana ganinta kasan me danyen jego ce nan da nan shaidan yafara qawata masa ita maganar mahfuz ta fara dawo masa .
Bangaren zuciyarsa ya fara fada nasa yes maganar mahfuz is the only solution to ur proble this is the best chance tazo dan test ne kayi anfani dahakan wani barin na fadin no karkayi .
This is the best chance and the right time ya fada ya miqe yai inda take atsaye itakuwa sai baza ido take yayin da zuciyarsa ke bugawa anya kuwa dedai ne hakan ya fada but this is the only solution u have if not ka mutu da ciwon santa ganin yazo dab da ita yasata faduwar gabanta yq qara qaruwa..........
Zan cigaba insha Allahu.
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*25-30*
*Wattpad Fadimafayau*
Jiyai kamar an tsikareshi yai saurin cewa muje wajeko tai saurin budewa dan gabaki daya jikinta rawa yake Time in sallah yayi so u come back letter tace ok sir shi kuma yai C.mosque.
Acan masallaci yai sallarsa ya roqi Allah gafara na yunqurin saba masa dayai ya kuma gode masa da yasa bai saba masanba.
Tabbas yanasan Ummu so bana wasaba saidai yasan tai masa nisa ya rasa me yasa duk yadda yaso ya cireta aransa yake kasa wa yarasa wane irin so yake mata.
Wayarsa ce tai qara hakan ya dawo dashi daga dogon tunanin da ya fada ya kai duba kan screen din wayar Qanwata yagani yai murmushi khairiyya ce frnd dinsa ta facebook ya kai hannu zaidauka kiran ya tsinke yabi bayan kiran.
Da sallamarta ta Amsa shima ya amsa mata qorafunta ya biyo baya yanzu yah na ka kyauta kenan kanaji ina kiranka kaqi dauka to sarkin qorafi nazo dauka ta katse ayimin afuwa tai dariya bakamin komi ba.
Yanzu abunda kike kina kyautawa kenan duk kin barni da tunaninki ta zaro ido kamar tana gabansa me menayi kyace me kika yi mana saiki kashe wayarki innemi in rasa yau wajen sati uku fa kenan ko a online bana ganinki tai dan murmushi amin afuwa haka kullin kike cewa wallahi ba ina sane na kasheba wayarce ta sami matsala aishikenan ya wuce suka dan taba fira kafin suyi sallama.
Ya kashe yana murmushi yasani yanasan Ummu wanda be taba yina wata mace shiba sedai yasani ya yi trusting din khairiyya fiye da kowacce mace yasani aduniya in aka dauke ummansa sai maryam qanwarsa babu wata mace da yake sakewa yayi fira da wasa da dariya kamar khairiyya duda kuwa betaba ganinta ba.
Asannu a hankali tunaninsa ya fara sauyawa kanasan ummu anman ka yadda da khairiyya har kana iya sakewa da ita why not ka mata tayin soyayya inyaso kayi aure ko ka rabu da san ummu ya aminta da zuciyarsa but dole se yaga khairiyya before yai gabatar mata da abunda ke ransa yasan duk duniya babu abinda ta gijini kamar ya nemi su hadu anman yanzu dole ta yadda if not zai yanke alaqarsu.
Ummu ke zaune tana kallo ya shigo da baby a hannunsa ungoshi kuka yake ta karba tana dariya Allah yaya kana shagwabashi infa ka tafi ya dinga kuka kenan sai zainab ta daukeshi tai masa rawa kasan ni ba iyawa naiba ace kaita jijjiga yaro sai kace wata yar tsana.
Yai dariya to banda abinki inban jijjigashi ba wa kikeso injijjga kinsan kuwa yadda nakesansa tai dariya ai basai ka fada ba kowa yasan baba nasan dansa to ni nawa san da nakema nawa dan yafi na kowanne baba harke mamarsa suka saka dariya gabaki daya.
Mutumina ya kaji shawarar tawa kuwa tayu ko yai tsaki wace shawara kuma au har kamance eh tunamin kan yarinyar da kake so mana yaja tsaki shawara ko cuta Allah mahfuz baka sona inda kana sona bazaka bani shawarar indauki qafata da kaina inkai jahannama.
Kagani tunda kaga zaka iya jurewa aishikenan ni kaban shawara wallahi bana iya bacci kullun da tunanin cousin dinnan tawa dashi nake tashi kai ko ni daya na zauna ita kawai nake hangowa haquri zakai matarma dabu san inda takeba balle kawai kaita addu'a Allah ya yaye maka.
Hawaye suka biyo kuncinsa Abbakar kafadamin taya zan iya haqurin wallahi ni asan khairar bansan wani abu waishi haquriba kafadan yazanyi inba haka ba wallahi santa zai iya hallakani a kwanannan.
Uhum mahfuz kenan kadunga saka dangana a'al'amranka wallahi nasan abinda kakeji aranka bekai nawaba kawai nafika haqurine kadena sama ranka komai kakeso zaka samu in kuma mutuwa taifa.
Kadinga sama ranka ta mutune bakuma zata dawoba zakaji sassauci to Habu nagode zan gwada insha Allah yawwa nawan be a Man dan Allah.
Wayarsa yadauka ya kira Khairiyya sun gaisa kamar koyaushe be bari ta fara surutunnanta ba yace magana nakesan muyi me mahinmanci to yah na inajinka.
Wallahi ina cikin matsala inasan kiban shawara kamar yadda kika saba sai dai ba ta onkine ko through phone calk ba a'a inasan ganinki face to face tace what eh sai ta kashe wayar.
Saqo ya tura mata khairiyya nagaji da kullin sedai mudinga magana a waya ko through chat if baki yadda mun hadubu wallahi wannan shine qarshen alaqarmu bazan kuma kiranki ba and kuma bazan kuma daga kiranki ba and in facebook u will be out of my frnd list and I will soon block u in WhatsApp.
Har safe ba reply be kuma yi abinda yace ba.
Yashirya zashi aiki saqo ya shigo wayarsa yana dubawa nata ne ayi haquri abin be kai ga haka ba kasa kuma kwatancen gidansu ne but kazo ran Friday ko lahadi sauran ranaku inada sch yai murmushi yau talata Allah ya kaimu juma'ar.
Bayan ya dawo yaje gidansu mahfuz sunsha fira mahfuz din duk yai baqi saidai ba kamar randa yazo gunsaba ya dan ciko.
Kasan me ya kawoni zuwa nai infada na zaka rakani gidansu khairiyyar nan frnd dita ta Facebook ok yaushe gobe Allah ya kaimu yace amin.
Baisan me yasa yaketa rawar kafar zuwa ganinin khairiyyanba ji yake kamar zashi ganin ummu ne rasa kayanma da zaisa yai qarshe ya nemo milk shadda dinsa mai dunkin coffee sai yasa hularsa ita kalar dunki da ratsi ratsin milk takalminsa coffee yai kyau sosai kai kace wani sabon ango ne.
Kamar sun hada baki shigar da mahfuz yai kenan dan yawancin kayansu iri dayane tun suna yara komai tare suke halinsu ne kawai ya ban banta.
Hajiya na ganinsu ta baro girginsu ah kace yau in sadaka nayi suruka suka hau sosa qeya bata tambayi ko ta wayeba ta musu fatan alkairi suka fice.
A qofar gidan suja faka motar suka fito Abbakar ya kirata tace gatanan.
Tai kyau sosai dan kaya ma na qasan kwaba tasa ko mace yar uwarta ce ta ganta saita yaba balle kuma namiji.
Alamar bude qofar gidan da suka ji yasasu gabaki daya maida hankalunsu kan qofar kowa da tunanin yadda zai ganta.
Gabaki daya sukai mutuwar tsaye daga su har ita da gudu ta koma cikin gidan tana kuka mahfuz na fadin Abbakar khairi ce yayin da Abbakar yarasa abinyi bakowa shi kuma idansa ya gane masa face kuma ummu dalibarsa ya riqe mahfuz wace khairin causing dintawa mana kasan me kake fade khairiyyace fa da nace ka rakoni gunta mahfuz ya zube agun sumamme inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un kawai Abbakar yake fade.....
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'U*
*30-35*
*Wattpad Fadimafayau*
Ganin bashi da amsar tambayarasa yasa shi katse musu shirun nasu da fadin bari muje asibiti amaka dressing in ciwon da kaji naga kamar ma yana buqatar dunki ok kawai mahfuz yake dan yasan yanzu magana kadan zata iya sa shi fashe wa da kuka.
Adedai gurin Parker motoci na emergency na asibitin nasarawa Abbakar ya ajiye motar dan dare yayi yasan OPD yanzu ba doctor muje ko yace da mahfuz ya fito yana dingishi sukai ciki.
Kamar yadda Abbakar yaje har gida ya tawo da Mahfuz haka ya rakashi suka rabu kowa da abinda ke damunsa a rai.
Bacci ya qi zuwarwa idanun mahfuz gabaki daya tunaninsa yaushe ne yayansa yai aure shi be saniba.
Zumbur ya miqe yai area din da dakin yayyansu yake ahankula ya tura qofar kamar yadda ya zata baya dakin dakin baccinsa ya shiga anman ga mamakinsa kwance yake kan gadon yana baccinsa cikin kwanciyar hankali to me hakan ke nufi.
Gabaki daya kansa ya kulle rasa me zaiyi yai abinda be saba ba ya mike ya dauro alwala ya hau nafilfilu.
Shima dai Abbakar kusan abu guda ne da mahfuz din ya kasa bacci saidai abu guda ke daminsa wato tausayin kansa yasani ayanzu san ummu ya gama kassarashi yasani santa bazai barshi ba duniyar yaji gabaki daya ta masa zafi kamar ya kashe kansa ya huta.
Hawayene kawai kebin idansa ya rasa shi kuwa wannan wace irin gaddara ce ta afka masa shi yasani yana kuma fade So be masa adalci ba ya mike yai toilet dan dauro alwala.
Washe gari da safe kamar yadda yake al'adar gidansu mahfuz an hadu a babban falo ana breakfast wasu na kan dinning tsoffi na kasa dansu sunfi san ci a qas juya cokali kawai mahfuz yake gami da baza idanu so yake kawai yaga ta ina yah nasir zai billo.
Baikai ga dire tunaninsa ba yaji muryar nasir din na fadin kai hajiya se kace wani yaro beji farkon maganar ba dan haka be fahinci abinda suke maganar akaiba.
Kamar yadda yake al'adar gidan koda da kwana mutun ya girmeka zaka gaidashi hakan yasa Mahfuz fadin Yah nasir ina kwana ya amsa lafiya qalau qanina yahau zubama kansa abincin.
Kusa da mahfuz din ya zauna yanaci yana nazarinsa saida yakai lomar qarshe kafin yace wai qanina meke damunka ne naga duk ka rame gashi ka rigani fitowa anman har na cinye na barka bakomi yaya kawai banajin dadi ne.
Ayya anman ai daurewa zakai kaci abincin seka sha maganin cuta da yunwa ai sai abin yai yawa to yaya zanci yawwa ko kaifa ya miqe zai bar wajen.
Yai saurin dawowa subhanallahi ciwon mene haka a qafarka mahfuz ya kalleshi da mamaki kamar bashine jiya ya ji masa shi ba.
Ina tambayarka ciwon me ne haka ta yaya ka jishi ya hqu sosa qeya gqnin yadda mutanen falon suka zuba masa na mujiya kowa nasan jin yadda akai faduwa nai jiya munje unguwa da Aminin sunan da mutanen gidan ke fadawa Abbakar Ayya to Allah ya kiyaye ya fuce.
Sama sama Abbakar yaci Abincin karinsa sauran ya faki Hajiyarsu yaje ya kaiwa kaji yana yo kwana daga gurin kajin nasu yaji dariyar maryam Allah ya kamaka wato kaji kake kawowa to abakun hajiya tai saurin juyawa zatai cikin gida.
Yabita da sauri yana roqonta haba yar qanwata ki tsaya kiji mana tai masa banza ganin tai falon hajiyar yasashi kai kwanon kitchen ya bita da sauri.
Haba qanwis bafa ma haka dake karaf kunnen hajiya zonan autana me yayi fadamin ta kalleshi duk yai wani kalar tausayi vashi bane nace ya temaka yaje yamin test yace ba inda zashi ya saukar da ajiyar zuciya dan yasan indai hajiya taji yaqi cin abinci ya gama yawo.
Hajiya tasa dariya kyaleshi kije kiyi abinki da kanki zaki ci fiye dashi kinji autana anman hajiya kedai kawai ki yadda dani zakici zan miki addu'a to hajiya ai shi kenan yawwa ko kefa Hajiya ni na tafi yace mata ok seka dawo Allah bada sa'a amin ya fice.
Yakai bakin gate a cikin motarsa yana shirin fita maryam ta fito da gudunta yaja ya tsaya ta tsaya bakin tagar me zaman banxa to sarkin rigima lafiya zaki tsaidani eh kace haka mana I save u today dole kabani tukwici ko in fada mata ai daman nasan da biyu ya ciro kudi ya miqa mata ta karba tana dariya shima ya kada kai yana dariya.
Inba dan dole ba da ba'abinda zai hanashi dena zuwa buk koyarwa tun da ya fara tuqin abinda ke faman kai kawo a ransa kenan har ya isa yai parking yai qofar office insa.
Kamar ance kalli gefe ya hango ummu riqe da babyn ta a hannu Fatima na gefenta suna ta dariyarsu cikin nishadi wani qululun takaici yazo masa wuya lallaima yarinyar nan ta rainashi wato shi ta gama raina masa hankali ita tana cikin farinciki da aurenta tana chat dashi tasa ya shaqu da ita rasa abinda ma zaiyi yai.
Jiyar Fatima na fadin lah Aminiyar yafazo dan bari ya dan jima da shiga kar yaga daga zuwansa min takura masa haka ne kuma.
Da sallama suka shiga office din ita da fatima suka gaisheshi a ciki ya amsa kafin yace lafiya me ya kawoku Daman make up din dakace zakamin kullin in nazo bakanan oh shine daga zuwana zakuzo ku takuran basu ce komi ba any way zan baki assignment kiyi submitting jibi but ki baima captain inku sai ya kawon ta amshi question in tana godiya suka fice.
Binsu yai da ido zuciyarsa na ayyana masa abu buwa da dama masu kyau da akasunsu yaja tsaki gami da diban kasan zuwa inda zaima wadanda yace suzo yau lecture.
Koda yaje ma ajin be iya tabuka komi ba ya rasa wannan wace irin masifa ce ya kawo lecture insa asabar dan duk sanin yan ajinsu ummu basa karatu week end akalla bazai ganta ba anman se ace yana shigowa ita zai fara gani.
Abu daya zakai zuciyarsa ke fada masa nigeria sa fadi take kawai ka nemi aiki a wani state in ka koma can wataqil ka huta da wannan takaicin jiyai yayi na'am da shararar ya miqe dan dauko paper a dara barin dan fara rubuta takardar neman aikin in ya tashi yakai amasa printing dan bezo da system inshi va bama yasan se yaje gida ya sauya ra'ayi......
Zan cigaba insha Allah
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*wattpad Fadimafayau*
*35-40*
Ko me ya tuna oho ya hau yayyaga paper din ya miqe yabar office din.
Abinda bai saba ba wato yawo cikin sch din shi yaji yana sha'awa tafe yake cikin nishadi ransa fes yakejinsa .
Daga nesa ya hango yarinyar da kema ummu raino haka kawai yaji yanasan ganin babyn ummun ya dan matso dab da inda yarinyar keta faman jijjiga yaron yace ki miqama mamanshi shi mana tana test ne ta fada ayya kawoshi to.
Tai saurin kuma ruqun qumeshi tace kar inbama kowa to ai ba guduwa zan dashi ba ta miqa masa shi sabida kwarjinin da yai mata bawai dan taso ba cikin ranta kuwa tsoron kar uwar dakin ta tazo tazo taga ta bawa wani ne.
Masha Allah ya fada a fili yayin da a ransa yake fatan inama ace yaronsa ne yaron kuwa ya bangale da dariya dimple insa me kyau ya bayyana yasunansa ya fada sunansa Mahfuz ya kuma mai maitawa mahfuh tace eh anman abbasa ke kiransa dashi ummansa tace sunan danta Abbakar wani abu ya ziyarci zuciyarsa yai saurin kawar da tunanin da fadin Allah ya raya shi tace amin ya miqa mata shi yabar gurin zuciyarsa cike da tunanin sunan yaron.
Abin duniya duk ya ishi mahfuz hakan yasashi shi yanke shawar zuwa yasamu yayansa nasir.
Yana zaune yana rubutu a system insa Mahfuz yashigo da sallamar Nasir ya amsa batare da ya dago kai ya kalleshi yaci gaba da abinda yake Yah gurinka nazo ok yace ya rufe system in ya maida hankalinsa gareshi.
Inajinka maganar me zamuyi akan matarka ne What ya fada mata ta kuma kai kamin auran yadda yawani hade gira yasa mahfuz shiga taitayinsa ina tambayarka kaikamin auran yai saurin cewa ba.....bame ba .
Daman kan ummu ne ta gidan baba yasir anganta ne ya fada a'a kwanaki ne daman mukaje gun wata nida Amin naga ashe tayi aure ta aureka.
Bai nuna wata razanaba ko tsoro yahau fada ni ta aura kuma sanin kanka ne banida aure bakuma ni da niyarsa ayan kwanakinnan se dai in har alhakinta ne yafara haukata ka kake zaton kowa ka gani ita ce yarinyar da ba'asan inda take ba ake zaton tabi uwatta shine zaka zo kana tunanun na aureta.
Wallahi yah ita nagani kuma wallahi yah kai nagani a matsayin mijinta ai ko na haukace naganka zan ganeka saukar marin da yaji yasashi saurin miqewa a firgice fitar min adaki da alamin ka haukace din da gaske sha_sha kawai.
Washe gari da sassafe yai dakin yayan nasa ya ganshi yana bacci yai sauri ya fice daga gidan sai gidan ummun.
Bugun da yake faman musu na hauka yasa gabaki daya suyo bakin gate in da abinda basu saba ji bane.
Daba dabaya ya fara ja ganin yayansa Nasir sanye da rigar bacci yana mittsika ido alamin baccin be isheba.
Shima mittsika idon ya fara kodai dagaske na haukace ne ya fadawa kansa no wallahi da hankali.
Malan lafiya mutumin ya fada nazo tafiya da qanwata ne abarsona what kanada hankali kuwa mata ta cefa ganin bazai bashi hanya ba yasa tankadashi ciki ya hau jan ummu tana tirjewa.
Mutumin ya dauko waya ya kira police sukai gaba da mahfux din yana faman kuru ruwar sai yadauki masoyiyarsa
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*Wattpad Fadimafayau*
*40-45*
Haka mahfuz yana ji yana gani police sukai gaba dashi yana faman ihuu tuni yan kallo suka cika gurin duda kasantuwar lokacin sassafe ne.
Saida mahfuz ya kwan ya yini a police station kafin asamu labari a gida dan hankalinsu gabaki daya ya gama tashi anata tunanin ko lafiya Nasir da hajiya ne suka fara zuwa aikuwa yana ganin nasir ya hau fada da zage zage mugu azzalumi wallahi saika saketa ya shaqe nasir dagyar aka fitar daga nasir din daga dakin.
Shine wallahi hajiya shine haka kawai yake fade.
Hajiya ta riqe mahfuz cikin kuka tana fadin shine mene yaci gaba da fade ta jijjagashi sosai kafin ya koma hayyacinsa ka nutsu kafadan me ya faru.
Hajiya tah nasir ne yai aure ta miqe a razane haba dannan ni na haifeku gabaki daya yaushe kuma nasir in yai aure ka fada min wallahi hajiya shine kuma Ummun baba yasir ya aura dan naganshi yasa aka daureni ka tabbatar da abinda kake fade eh umma.
Ta koma tazauna haba biri yai kama da mutun shi yasa yaronnan yake cewa haukacewa kayi muje ina zuwa ta fice tabar dan dakin da suke ganawar.
Tana zuwa ta share Nasir da mari ya dafe gurin cikin qwalla ya kalleta menayi hajiya bansaniba ashe kai shasha ne da har zakayi aure bamu sani ka rasa wa zaka aura se yarinyar nan wadda uwatta bata ganin kowa da qima.
Ya dafe qirji cikin kuka yake magana hajiya ke kin yadda ina da aure in inadashi ai da tuni na dena kwana agida aje gidan da yace yaganni inyaso se agani inni inne tadan yi jim kafin ta koma dakin.
Mahfuz ta tambaya kwatancen gidan ya mata.
Eh kam yarinyar kamarsu daya da Ummu sedaifa yarinya tace ita ina batasan wani nasir ko mahfux ba har gidan iyayanta ta nuna mijinta ma ko kama basu hada Nasir ba police ma sun tabbatar ba nasir ne ya kawo mahfuz ba wanda yakawo mahfuz daban.
Aikoda su hajiya suka dawo da labarin komi Mahfuz ya miqe yahau dukan Nasir wallahi saina kasheka wallahi shine.
Ala dole su hajia suka yadda tabbas Mahfux ya haukace hakan yada sukayi bail insa suka kaishi asibitin kula da kwa kwalwa.
Duk wani bincike anyi anman ba'agano komi ba wato kwakwalwarsa normal take.
Saidai yadda inyaga Nasir yake tuburan dole hajiya naji na kallo ta yadda ya haukace tasa hannu dan kaishi gidan kula damasu tabin kwakwalwa.
Duk halun da ake ciki Abbakar baya da labari sai yau hankalinsa ya tashi danshi be yadda Mahfuz dinsa ya haukace ba.
Kai tsaye asibutun ya wuce aikuwa mahfuz din naganinsa yahau kuka tausayinsa ya cika Abbakar yadda kwana biyu kawai yaga mahfuz din duk yai baqi ya rame kamar bashi ba.
Ya hau rarrashinsa dan Allah amin kaje kacewa hajiya wallahi da hankalina Allah van haukace ba kai nasan zaka yadda.
Yadda yake maganar yaqarama Abbakar kwarin gwiwa tabbas Amininsa da hankakinsa wata maqirqisa kawai aka shirya masa.
Naji nayadda da hankali anman garin yaya me yafaru har aka kawoka nan ya bashi kabarin komi tabvas raina musu hankakin da yarinyar nan take ya isheshi yau zai maganin komi dan yanasan abokinsa yanaji yana gani baza'a mayar masa da Amini mahaukaci ba.
Ya kwantarma da Mahfuz hankali kafin yq fito daga gidan masu rangwamen hankalin.
Kai tsaye gidan Su mahfuz ya wuce baibi ta ko inaba yai bangaren hajiya abinda yake ba sabonsa ba shiga cikin falon gidan kai tsaye.
Yai sa'a tana falo suka gaisa kafin ya mata jaje ya dora da fadin yanzu hajiya kina kallo za'a maida mahfuz mara hankali vazakiyi magana ba.
Tai dan murmushi Habu kenan ai ba maidashi akaiba ya haukace din ne wallahi hajiya be haukace ba da hankalinsa haba dannan taya zakace be haukace ba mutumin da yake iqirarin kashe dan uwansa agabana fa.
Yana ihuuu yana shine ajalunsa yace yai aure alhalin qarya yake masa yace yaganshi alhalin bamashi bane bakajin wannan duk ba alamomin hauka bane.
Wallahi hajiya shi yagani tare muka ganshi taja tsaki daman ai abokin barawo barawo ina yabonka ashe kaima ka fara shan qwayar da yake sha nasan itace ta fara tamvayarsa inzaka tashi katafi to inkuma ansn zaka kwana sekayi tayi tamiqe tai sama dan wallahi kaima ban yadda dakaiba kar inje a afkamin.
Ya miqe yabar gidan takaici fal cikinsa.
Gidan da sukaje da mahfuz yai inda sukaga Nasir da ummun.
Yaro ya aika amasa sallama da me gidan yaron ya fito wai baya nan can saigata tafito.
Wake nemansa yai saurin dagowa daga daddanna wayar da yake dan ko a ina yaji muryarta sai ta gane nine ta fada.
Tace oh baya nan sedai inzaka jira ok va matsala yace ta koma ciki.
Ya kusa minti goma sha biyar mutumin ya parkee motarsa qofar gidan ga mamakin Abbakar ba Nasir vane anman yadan daurewa mamakinsa barka sannu ko yawwa kai kake nema na eh nine ok muje daga ciki ko suka shige.
Bayan ya shiga ya fito riqe da yaronnan da kodaga bacci Abbakar ya tashi saiya ganeshi dan tabbatar da abinda ke masa yawo arai na shakku yasashi miqa hannu kawoshi.
Ya amsheshi dadinsa da yaron kwai fara'a ya sunansa nahfuz yace ataqaice Allah sarki Allah ya rayashi amin yace ya miqo hannu ya amshe abinsa.
Nikam Kamar nasanka wataqil kwanaki dai munzo da abokina mahfuz oh naganeku kune yan iskannan masu shigarwa matan aure gidako yadan cige lebe dan yaji zafin kiransu da yan iska dayayi yaidai basar ehto koma me kakiramu ni ba hayaniya nazo ba nazone dan inasan yin magana dakai da matarka.
Ya miqe a fusace what dan mene inbazaka iyayi dani kadaiba to mata tata haramin alaik no maganece ta fahinta nakeso muyi kan abokina da kuka haukatar.
Kaga nafiskanci haka daikinyi pls tashi kabar min gida tun kan kadaga hankalin matata pls give me a chance wai baka ji me nace maka bane ko sai na hadaka da police na sassauta maka ne dan kawai na fiskanci kafi abokinka kamala.
Abbakar ya miqe yabar falon but kasani zan dawo kuma time in da zan dawo dole in magana da matar taka hakan kuma shi zai kawo qarshen matsalar nan na fada ma to muza nidakai dan halak ka fasa inji mijin nata.
Tunda yahau titi tunanin muhawarsu da mutumin yake yasan babu ta yadda zai iya magana da matarnan indai mutumin nan nanan but za'a iya kamashi inyaje ya shigar musu gida suka masa ihuuu gabaki daya tunaninsa a cunkushe yake ya rasa mafita.
Sauri kawai yake ya tafi sch ko breakfast din kirki beba ya bar gida.
Ko a office ma jira yai kawai takwas tayi ya wuce inda zaiyi lecture dinsa ta morning bayan ya gama yace wadda aka kawon complain bata da lafiya tazo yau for her make up ya fice be jira amsar student dinsa ba.
Aikuwa kamar tare suke yana shiga ta shigo riqe da babyn ta yadan kalleta ya kalli babyn zaki iya zama tace taja tazauna yai saurin murda makullin office din gami da zareshi ya zura a aljihu jikinta ya dau rawa ta mike ta daka mata tsawa koma ki zauna kika ce tak kome ya faru dake ke kika jawo yado gabanta dab da ita tana kallonsa yana kalkonta yazauna har yana iya jiyo faduwar gabanta suka hada ido ya daka mata harara tai saurin kawai da kai..........
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*Wattpad Fadimafayau*
*45-50*
Cikin kuka take magana pls let me go I beg ur pardon dan Allah, mtss yaja tsaki au daman ke kinsan Allah ne da har zaki hada wani dashi munafuka kawai taisaurin dagowa hawayen da ya cika mata ido ya gangaro.
Inkinga kinbar office dinnan to Wallahi kin fadan ke wace taisaurin kallonsa yes kinmaji na rantse sir bangane ba all i know am ur student kawai nop ba wannan nake san sani ba ki fadan mene alaqarki da mahfuz, Ni dakuma Nasir ni bani da wata alaqa dakai balle su ok kin shirya ma kwana ananko.
Ya shige toilet ya dauro alwala gami da fitowa ya tada sallah bayan ya idarne yaci abinci ya miqo mata sauran inkinyi niya kyaci ya sa hannu ya amshe babyn hannunta ya koma inda sallayarsa ke shimfide ya kwanta gami da dora babyn kan cikinsa ya lumshe idonsa hankali ba qaramin tashi yaiba ganin la'asar na shirinyi dagaske bazai barta ta tafiba.
Wata irin yunwa takeji abinka da me jego but batasan cin abincinsa dan bata yadda dashi ba yadda ta fuskanci yau din kamar a buge yake dan dazu da ya daka mata tsawa ta kalleshi taga idanunsa sun wani sauya launi batasan duk bacin rai bane kawai.
Dole in samu mafita naji zan fada ma alaqata dasu inkamin alqawarin barina in tafi ok inajinki ya fada batare da ya bude ido ba balle nuna concern innaji bayaninki ya gamsar dani mai zai hana inbarki ki tafi.
Mahfuz cousin dinane what ya fada gami da saurin bude ido ta gyada kai alamar da gaske take eh causin dina ne so Nasir fa ya fada.
Tai shiru oh baki shirya tafiya ba kenan ta kada kai cikin hawaye mijina ne ya miqe a tsorace sauran qiris babyn ya fadi ya tallafeshi mijinki ya fada eh ta fada oh i see.
Shiyasa kuka hada kai kedashi zaku haukatan aboki ko dan kawai san zuciyarku dan zalunci pls kabarni in tafi na amsa naka duk tambayoyinka dan Allah.
Naji zaki tafi but baki gama amsan tambayoyina ba baki fadan alaqarmu ba sir ni bamu da wata alaqa da kai banma sanka va sai a Bayero.
Karfa ki rainan hankali nasan me nake am 30 so kinga na fice kizo ki rainan hankali inkasa gano wa taya zakice baki sanniba bacin kinsan frnd dina if i can recall ke kika fara turon frnd requires sai yanxu na gane hakan duk yana cikin shirinku ne keda Nasir.
Sir kayadda dani bansanka ba eh naji baki sanni ba anman taya za'ai da aurenki ki dinga chat da wani harki dinga baima mijinki ku gaisa da wanin inbaya shirinku.
Sir in zaka tuna time in four years back muna chat but inka tuna bama na nigeria muna waya da kai inka tuna na fada ma i never being to Nigeria even though my Father's relative gaba daya suna nigeria na turo ma frnd requires ne dan kawai inasan yan nigeria naga kai dan nigeria ne.
Yai dan tsai yana tunani yes yatuna ok yanxu zamuje ki fadama iyayen mahfuz abokina da hankalinsa kafin inbarki ki tafi ta zaro ido what eh.
Hawaye ya gangaro mata haba sir ba haka mukai dakai ba pls let me go kazamto me cika alqawari any way zaki iya tafiya yabude mata office din gami da bata baby ta wuce.
Harta fita ta dawo sir make up test in tawa yaja tsaki pls sir tace kafin yace wani abu jeki i will think about it dan Allah sir ta kuma fade yaja tsaki gami da fadin oppps kije during exam ki amsa all question in yaso se kisa C.A a biyun zan gane thank you sir ta fada tai saurin ficewa.
Wayarsa ya dauko ya danna recording din da yai nasu yana kuma sauraro at list yasamu evidence against ita da nasir dole yai wani abu he yas to expose them dan kare martabar abokinsa.
Miqewar dazaiyi wayar ta fadi jiyai har cikin ransa faduwar wayar yaisaurin daukowa yai yai ta kunnu taqi oh my goodness ya fada yana dan dukan goshinsa memory din ya ciro yasa ada wayar sedai ba recording shedar yana kan wayar ya Allah ya fada gami da komawa ya zauna wani hawayen baqin ciki ya gangaro masa ya rafka uban tagumi yana tunanin abinyi.........
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*wattpad Fadimafayau*
*50-55*
Koda ummu ta fita daga office din kai tsaye ficewa tai daga sch din saida ta hau dan sahu sannan ta dauko wayarta tafara dialling din number din Aisha yafi sau hudu bata dauka va kawai sai ta kira Fatima ita ma same thing happen kawai sai ta zura wayarta a jaka.
Saida taje gida sannan kiran Aisha ya shigi lafiya dai irin wannan kira haka bata bata amsa ba ta kuma tambayarta kina ina ne ke muke jira fa.
Tun dazufa nake nemanku ban gankuba shine na tafi gida nakirama in ce muku na tafi gida se mun hadu gobe tsaki Aisha taja Fatima tai sautin karbar wayar cikin fada take magana anman wallahi ummu bakida muntuci inba rashin mutunci ba kinsan bazamu tafi ba sai mun jiraki kawai saikiyi tafiyarki ayi hakuri naga tun wajen fitowa ta banganku ba kofa office din ban shiga ba kutt bakishiga ba kika ce muna kallonki fa kika shiga munfi awa biyu baki fitoba.
Ganin yadda Fatima ke fada yasa Aisha karbar wayar haba ummu taya zaki mana hk tsaya ma naji fatima tana cewa wai kince ko office din baki shiga ba No bata fahince ni bane kinsan ta da fushi inta hau bata tsayawa cin ribar zance zata hau fada.
Cewa nayi ina shiga na fito fa baku dai kula bane ni kuma banyi zaton kuna nanba natafi masallaci nemanku da banganku ba na tafi gida anya ummu idanuna fa nakan office din kinsan dai karatu mukazo ko bataji komi kan maganar Aishan ba dan tasan ta da tsantseni da fadar gaskiya gama kowaye .
Ki yadda dani abinda yakaini kawai nayi banmayi make up dinba cewa yayi in answering all question 2 for test in yaso 3 for exam ok yayi kyau yanxu kina ina ina gida ki yadda ina gida bakomi ki shafan kan Abbakar zaiji insa Allah sukayi sallama.
Ta goge hawayen da ya zubo mata wani dacin rai na taso mata tarasa me ke mata dadi ji take inama batazo duniya ba ko inama ta mutu kafin a haifeta.
Gidansu mahfuz
Hajiya wai bakya ganin haqqin ummulkhairi ke dawainiya da dangin nan namu musanman nahfuz taja tsaki me muka mata da haqainta zai dawai niyada mu eyye mara mutunci.
Gani naifa yah mahfuz ya haukace gashi an kasa gano me ke damunsa Hajiya tai shiru kin tunan wani abu nasan tabbas da sahannun uwar yarinyar nan a abinda ya same shi sai yanzu na fuskanta aljanu suka turo masa suka masa farraqu da dan uwansa maza kiramin doctor yusif.
Yawwa Doctor so nake mahfuz ya dawo gida mu gwada ruqiyya tunda naga na asibitin ba sauqi kinsan nayi tunanin haka aqwada ruqiyya hakan za'ayi.
Kiramin musa ummi ta miqe saigata ta dawo da musa yana biye da ita ya russina ya gaida hajiya gami da cewa gani.
Yawwa musa so nake kaje kadauko min mahfuz a asibiti yadan fada da razana hajiya mahfuz eh shi so nake ya dawo gida mu masa na gida tunda na asibitin yaqi.
Hajiya ya warkene ya fada cikin rawar murya inda ya warke ai dabazance ma zamu masa maganin gargajiya ba ko.
Jikinsa ta hai kyatma anman hajiya taya zan iya tawo dashi cikin sauqi ina tuqi to me kake nufi yai zuru zuru da ido ummi yasa dariya wallahi hajiya da gaskiyarsa taya zai dauko mahaukaci a mota shi daya wanda yake cewa zai kashe mutane kawai ya shaqeshi.
Hajiya ta cilla mata daquwa ungonan dan uwan naki ne mahaukaci to hajiya aiba qarya akaiba ok to naji ku tafi tare sai ki riqe masa shi ta zaro ido hajiya ni eh ke inkuma bazaki ba to kinsan ba ke daya na haifa ba tasan indai hajiya ta fadi haka to taki qololuwar jin haushi.
Ta miqe muje ta hau sama ta dauko gyalenta hajiya mun tafi Allah ya kiyaye tace amin.
Tunda suka fara tafiya ba wanda yacewa kowa ci kanka kowa zulluminsa taya iya tafiya da mahaukaci cikin mota.
Koda suka isa sunje office din doctor usif sunyi cike cike kafina abasu mahfuz, yadda ummi ta ganshi ya daga mata hankali dan mahaukaci sak tagani ya tara uwar suma da gemu wanda dauda har tafara sawa ya koma jaja.
Koda ummi taje dab dashi amai ne kawai batai ba sabida wani tsamin dauda da yake tace yah mahfux ka gane ni ya kalleta ba ummi bace tadanyi ajiyar zuciya aqallah ya ganeta.
Lafiya me ya kawoki nazo mutafi ne nine nace miki inasan mu tafi yadda yake magana cikin fushi da fada ya tsorata ta a'a to ba inda zani pls yah kinga alamar wasa a idona.
Ni nariga na yanke shawar qare rayuwata anan dan haka zaki iya tafiya yah kayi haquri kazo mu tafi kowa na kewarka qarya kike kowa yafisan Nasir gashinan sabida shi kowa ya mance dani kowa ya tsaneni kowa ya gujeni.
Cikin sauri tace yah kayi haquri inkasa wa ranka kowa ya tsaneka ka cire hajiya tanasanka kullin burunta kasamu sauqi pls kazo mu tafi kodan hajiya.
Miqewa yai yabi bayansu ummi ta fara yadda da batun hajiya anwa mahfuz da Nasir farraqu tunda gashi har yasama ransa anfi san nasir duda yana cikin hauka.
Suna tafe tana kaf kaf dashi cikin mota dan tsoronta karya shaqo me tuqi ko ya bude ya fice yana fiskantar ta sosai kasantuwarsa bayan yai degree dinsa a fanni qere qere yaje yayi wani sabon degree din a psychology baisan sanda dariya ta kufce masa ba aikuwa gabaki dayansu ummi da musa hankalinsu ya qara tashi fuskantar haka ne yasa shi yin shiru.
Agida ma kowa kaf kaf yadingayi dashi har suka isa sashen hajiya sai asannan ummi ta saki sanyayyar ajiyar zuciya aqallah sunzo lafiya.
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*Wattpad Fadimafayau*
*55-60*
Baibi ta kan kowa ba ya shige
bangarensu toilet ya shige ruwa me dumi ya hada yai wanka ya wanje jikinsa yakai sau goma still bedana jin wani iri ba haqura yai ya daura towel ya hau shaving din gemun ya rarrage sumar kansa sannan ya sake wanka aqalla yadanji dadi.
Ya fito yana saka kaya ne hajiya ta shigo riqe da kofi ummi na biye da ita da flask gabaki daya sunyi mamaki mahfuz ya koma mutun sak hajiya tazauna gefen gadon ummi ta zauna gefen kujera.
Saida ya kammala sakayan yazo ya gaida hajiya aqallah ta danji dadin ganinsa yanzu va kamar dazu ba ga tea kasha ko zakaji dadin cikinka ga danwake kuma sekaci yunwa yakeji hakan yasa be musa ba ya amsa yasha.
Yanasan dan wake sosai hakan yasa ya karba da zumudi yahauci saidai taunar farko yaji ba dadi dan gabaki daya bakinsa ba dadi dagyar ya hadi a hankula ya furta Allah ya isa Nasir hankalin hajiya ya tashi tadai daure.
Ganin ya ijiye yaqi ci ne ta kalleshi kadaure ka ci hajiya wallahi ba test daurewa zakayi kaci se ahankula komi zai koma normal.
Ummi kije ki samo toka ki gasa masa nama da ita zai temakawa test din bakinsa to hajiya.
Da yamma agun cin abinci kowa ya hallara har mahfuz inka dauke Nasir mahfuz yakai lomar abinci baki kenan nasir yazo yaja kujera ya zauna kamar koyaushe kujerarsa kusata da ta mahfuz ya sha kansa qanina yajikin naka ya tankade hannunsa cema akayi banda lafiya ne ya miqe fuuu yabar gurin.
Koda Abbakar yabar office din gida ya wuce dan gabaki daya ransa ya baci yama rasa abinyi.
Da Amira qanwarsa ya ci karo zata fita tace lah yah sannu da zuwa ya amsa yawwa ina zuwa haka da yamma yah zani gidansu khairiyya ne zamu dan tattauna yai dariya zadai asha gulma tai dariya wallahi yah ba haka ne kyaji dashi se an dawo yai ciki be jira amsarta ba.
Gabaki daya mutan gidan na falo har masu aiki shima anan ya zauna bayan ya gaida hajiya yasa baki cikin firar da suke hakan ya rage masa kashi arba'in na bacin ran dake damunsa.
Kiran sallahr magariba ce ta tashi kowa dan kawo farilla ya kai kayansa samansa kafin ya daura alwala ya fice.
Daga masallaci gidansu mahfuz ya wuce baisan an dawo da mahfux dinba ganinsa ba qaramin dadi ya masa ba sun tattauna kafin suyi sallama har ya fita ya dawo.
Ban fada ma ba wani abin takaici nan ya zayyana masa komi cikin takaici Abbakar ke bashi labarin mahfuz ya goge hawayen da yazo masa ba komai Aminin Allah ya kawon mafita amin Abbakar yace.
Kasan me inji mahfuz sai kafada Abbakar ya fadi ni wallahi bawai gidan mahaukata da aka kaini ne matsalata va babbar matsalata itace San ummu da kullun ke qaruwa cikin raina ko nayi yunqurin cireta araina abu kamar.
Yana daya daga abinda yasa nake jin haushin yah nasir da ya aureta ni wallahi yanxu ji nake da rashin ummu gwanda abanni in dawwama gidan mahaukatan.
Abbakar ya dafa shi se haquri taka qaddarar ce a haka uhun ba qaddarata bace nasani haqqine ke bibiyata tunda Allah ba azzalumin sarki bane yana sakawa wanda aka zalunta kadena sa haka aranka ka ci gaba da qoqarin mancewa da ita ni zan wuce kar hajiya taga na jima.
Yana barin inda mahfuz din yake ya share hawayensa wanda tun dazu suke san fitowa yana jarumtar riqesu shi kadai yasan azabar da yake ji na san dalibar nan tasa dauriya kawai yafi amin nasa.
Ashan gida ma bayan yaci abinci yaje gurin motsa jikinsa jiyai duk jikinsa ba kwari dakinsa ya shige ya rasa abinyi wayarsa ya dauko ya hau kunnawa ko Allah zaisa ta kama amman ina tace batasan zance ba tsaki yaja yahau gado ko Allah zaisa yadan samu bacci.
Baccinma gabaki daya yaqi zuwa daya rufe idanunsa ummu yake gani tana masa murmushinta da yake qara mata kyau agunsa yarasa wace irin zuciya gareshi me nacin tsiya da take jawo masa masifa kala kala ace dik yan matan dake sansa takasa kallonsu sai matar wani.
Ganin da gaske idanunsa basu shirya yin bacci ba yasa ya miqe yashige toilet dinsa ya dauro alwala ya hau nafil filun.
Yau lahadi ba inda Abbakar zaije hakan yasa ya fito babban falo dan yin fira ko zai samu ya raje kewar da ke damunsa.
Hira suke sosai inka ganshi bazaka taba cewa yana cikin damuwa ba danshi din akwaishi da jarumtar boye damuwa duk girmanta shi yasa ko hajiyarsa take cewa yana da zurfin ciki.
Yau litinin yanada kula da masu jarrabawa qarfe biyu hakan yasa tun asuba da yasamu bacci ya debeshi yai me isarsa dan ya dade be yi me dadin sa sai goma ya farka yai wanka sannan ya sauka danyin breakfast dinsa.
Bakowa a falon sai kwanukan abinci dake kan dining da alamu nashi ne kawai saida yaci sannan yaje dan gaida hajiyarsu.
Tana kishin kide tana tasbihi suka gaisa kafin yace hajiya mu zamu fita tadan gyara zama to Allah ya kiyaye ya tsare ya amsa da amin cikin jin dadi.
Gidansu mahfuz ya wuce sun dan taba fira da hajiyar sakamakon mahfuz din na wanka a hankula ya fara sako mata da maganar ummu aikuwa nan danan ta hau wato mun samu ya mance da maganar shine zaka zo ka tayar mana da ita to ahir dinka.
Sin sin ya miqe yai dakin mahfuz din dan jiransa.
Wai mahfuz in tambayeka mana inajinka in har ka yadda ummulkhairi ba matar nasir bace me yasa sukayi qaryar aure mahfuz yai shiru na dan lokaci kafin yace waya fada maka ban yadda ba ni wallahi na yadda matarsa ce.
Kasan kawai meke ban mamaki seka fada inji Abbakar kawai ina mamakin me yasa yah nasir yakesan dole sai ya haukatani ta hanyar nunan bashi nake gani innaje gidan matar tasa.
Abbakar yai dariya ba dole ya haukata ka va fansa suke dauka shida matarsa mahfuz yai danshiru na wani lokaci yes u are right wallahi se yanxu na gano dalili wato ya zabi mace kan dan uwansa.
To wallahi tunda haka ya zabarma kansa ni nasan nafishi santa to zan nuna masa hauka sedai kowa ya rasa dan wallahi kashe shi zan yau bako gobe ba ya miqe ya zari wuqar dake kan kayan marmarin dake bed side drawer yai waje yana huci............
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*Wattpad Fadimafayau*
*60-65*
*This is specially for you @Aeshakabir I know you will like it*
Da sauri Abbakar ya riqoshi yajawo shi zuwa ciki haba mahfuz kasan nasan da hankalinka pls act serious ma katsaya ka saurareni ya amshe wuqar.
Ni ban yadda ummu matarsa bace mahfuz ya zaro ido what bafa ka yadda ba kace eh ban yadda ba to sabida me sabida kawai ban yadda ba ayanzu banda hujja anman ina ji ajikina ba matarsa bace kawai suna maka haka be dan ka fita daga rayuwarta.
Ka yadda dani karka yi abinda zakayi danasani a hankula komai zai koma dedai haka yaita tausarsa har ya samu ya sauko.
Fatima ce riqe da paper din test dinsu tana faman mita wallahi dedai nayi mutumin nan zai kansilemin dan Allah Aisha kalli nan ba haka ake ba ta kalla to ba gwanda keba nida ba'amin recording bafa to ba inkin kai masa zai miki ba.
Pls ku rakani nai photocopy din paper dinnan suna tafe fatima na mita yayin da Aisha itama keyin tata kan rashin mata recording duda yake lefin tane na rashin saka reg. Number dinta.
Ita dai Amina ba abinda take fadi se maganar absent da aka saka mata a last exam yayin da ummu tai shiru ita kadai tasan abinda ke damunta gabaki daya ta dena jin dadin sch din kawai tana daurewa ne.
Kinsan Allah maidama mutumin nan zanyi jibi fa ko makamin nan beba yaushe zaki kaimasa ya shigar miki Fatiman ta tambayi Aisha ko yau ne sai muje inasan zuwa can chemistry lab ma ok se muje gabaki daya.
Sunyi rashin sa'ar samun me photocopy hakan yasa suka kira sauran frnd dinsu kan suzo su tafi daga nan zasu viya suyi ahanya.
Sun hadu a CIT inda student dinnan suke graduating se murna suke se anan ummu tadan ji sukuni aranta dan ita din mutunce me san taga mutane sun kanmala karatu musan man data ga yara qanana se taji dama ita ce.
Tuni qawayenta sunyi gaba ta tsaya sakato tana kallom masu bikin sunata selfie yau batazo da me rainonta ba bata da lafiya koda zasu shiga exam sai wata yar level 4 ta roqa ta riqe mata Abbakar shine ya matso alamar ya tashi tai saurin sakkoshi ta matsa gefe dan bashi abinci.
Da yake yafara shan kamu shi take bashi sha yake sosai alamun yunwa yakeji yadda yakesha da kuma tunanin da zuciyarta ta tafi yasa batasan sa'adda hawayen da suka cika mata idanu ya zuboba.
Jitai an dafata ta baya tai saurin jiyowa Hafsa ce kinsan tun dazu muke nemanki ina su fatima inji maryam assha kukan me kike haba ummu ki dinga ragema ranki damuwa pls inji maryam ke wallahi kina da matsala nasan duk bazai wuce kan exam din yauva kawai ki shateta exam luck ce kawai inji hafsa to Allah ya bamu sa'a su suna waje jen fais muje nace su jirani.
Suna tafe hafsat na selfie da dan surutanta intayi wani tauawo ummu tayi musu su biyu wani ta jawo maryam, yayin da maryam ke faman tambayar ummu wace amsa ta samo a questions din yau wasu ummun ta bata amsa wasu kuma tai shiru.
Sun yi photocopy din inda fatima da amina suka wuce toilet na CIT mosque basu jima ba suka dawo.
A bus stop suka hadu da halima da sauran frnds dinsu sun hau mota tare yan hanya sun sauka ahanya yayin da su suka sauka a old side din sch din tasu dan can ne gun da zasu.
Sinyi rashin sa'ar samun duk wanda sukaje nema hakan yasa kawai ko wannen su ya wuce gida kan zasu hadu ran alhamis.
A gida ummu ta rasa me ke mata dadi dan tun randa Abbakar ya titsiyeta batajin dadi ita ba abin ta fadawa Nasir ba tsoronta daya kar yaje ya ballo mata ruwa abinci ma ba koyaushe take ci ba ko tahajin yunwa data fara ci zataji ya fita aranta.
Ran alhamis da sassafe ummu ta shirya tai sch dan sunyi zasu hadu dasu hafsa 10 na safe.
Basu wani makara ba sukazo duda kuwa ta dade da zuwa Fatima ce last din zuwa suka dunguma sai math department sunyi rashin sa'ar samun wanda sukaje gunsa bayan sun tambayi maqocinsa ko zaizo ya basu tabbacin zuwansa suka koma qasa dan jiransa.
Zaune suke sina hira sama sama yayin da karatin paper din dazasuyi yau yafi qarfi maman humaira ce ta dauko wata paper suna dan tattaunawa akai dagowar da Aisha zatai taganshi yazo suka miqe dan bin bayansa.
Faduwar da Hafsa tai ne yasa har isarsu bakin office din basu bar dariya ba ganin office din abude yasa su shiga taitayinsu suka jira na ciki ya fito kan su shiga.
Bayan sun gaisa cikin hade rai ya ce lafiya me ya kawoku paper dinta Aisha ta nuna wadda ya rubuta not recorded ya amsa da Id dinta ya shigar yayin da fatima tace complain gareta ya karba yana dubawa.
Ya dago a fusace haka na koya muku tai tsuru tsuru ya miqo mata paper dinta yayin damaman humaira tamiaqa tata itama fadan yasa hafsat na gefe tana dariya qasa qasa.
Ganin da taske ficewa zaiyi yasa Fatima yin qarfin halin qara miqa masa nanto sir bakamaka ba ya karba ya soke sir but ka makawa wasu dedai yai tsaki itama ya maka mata
Sir wai zaka bada attendance inji wa ni nai attendance ne a class dinku gabaki daya sukai tsuru tsuru pls ku fita sauri nake.
Aisha ce ta miqa nasa sir nima baka makan nanba kuma nan nayi dedai ya amsa tsaki yaja kowa ma ban maka masa ba nankuma mene sir gashi nan miqo mata takardarta yai pls kumuje nan sawa kikai wallahi sir bafa sawa nayi ba zakace nasa Dallah muje yaje suka fice gabaki daya rai abace.
Sunfi minti goma suna mita yayin da ita dai ummu bakin naganarma babu jitake kamar tai kuka dan ita bama tayi test dinba gashi exam din se a hankali shi yasa takejin su mitar dadi ma suke.
Se wajen sha biyu maryam tazo suka bata labarin yadda sukai da malamin tai ta dariya kafin su juya akalar firar zuwa karatu.
[11/22/2017, 9:17 PM] Fadimafayau: *Abbakar*
*Na*
*F.A.Ya'u*
*Wattpad Fadimafayau*
*65-70*
Sai qarfe Daya da wani abun suka bar old side zuwa new side inda zasuyi exam dinsu ta yau suna tafe a mota suna fira yayin da kadan kadan suke taba muraja'ar abinda suka karanta.
Gidansu Abbakar Hajiya ce ta shigo dakin dan nata da sallama ya dago daga kan computer din gami da dan matsar da ita ya amsa sallamar bata zauna ba tace leqowa nai inga ko lafiya tunda kazo gaisheni banji motsinka ba bakuma kazo kace min ka fita ya yadan sosa qeya gami dayin murmushi yanzu nake shirin fita ina da jire dalibai wajen qarshe biyu da rabi inata faman duba wani assignments ne dana baima yara tai dariya yayi kyau ai gwara ka hanzarta yanzu shabiyu ta kusa ya miqe ahto bari in wanka ta fice shi kuma ya shiga toilet.
Saida ya shirya sannan ya sakko Abinci kadan yaci dan baya san cin abinci da yawa inzai fita yana kuma san zuwa gidansu mahfuz yasan indai time in cin abincine sai haniyar mahfuz tasa yaci abinci ko baya so.
Hajiya ni zan wuce harka shirya eh to Allah ya yemaka amin hajiyata ta fada yana yin gaba.
Haryakai bakin falon ya dawo waiko hajiya ina wannan mara kunyar take tai dariya maza taji kana ce mata mara kunya ta tafi exam af fa hakane tacemin jiya sunada paper yai waje.
Yana shirin barin main falo din wanda dagashi sai farfajiya suka shigo Kadija ce qanwarsa wadda take aure a Zariya sai yaranta guda uku nan danan fara'arsa ta qaru a'a manyan baqi yaran sukayo kansa suna ihuuu uncle uncle ya daga su dai dai kafin su rungumo juna shida sister din nasa suna yaushe gamo ciki ya bisu dauke da qaramin data ke goyo ina hajiya ma na ganinsu murnarta ta qaru.
Yaran sukayi kanta da gudu qaramin ma yasa ihu saida ya saukeshi shima ya fada kanta ohni hashina yarannan so kuke ku qarasani Abbakar yai saurin cewa ku daga mun uwani karku karya min ita a'a kaga malan ka qyalen yan jikokina su mori kakarsu suka juyo suna masa gwalo suka saka daria gabakibdaya.
Keda me gidanne yake tambayar qanwar tasa a'a mu kadaine sai zamu tafi zaizo sai su gaisa da hajiya ok yayi kyau yadan kalli agogo opps zanyi latti inna dawo dai koma mene ne ma tattauna ya miqa mata hannu sukayi musabaha kamar yadda al'adarsu take sun riga sun saba to sai nadawo to yah sai kadawo da labari naga alamu ko tai dariya kaidai bari kawai sai kadawo nagama duk kayi baqi dama can baqin nake kinga sai nadawo ya fice aiko Malan qarami ya taso da gudu yabi bayansa yana kuka uncle uncle mamanshi tai saurin daukoshi ta dawo dashi ciki.
Ko gidansu Mahfuz din baijeba ya wuce sch dan yaga ya makara.
Wayarsa ce ta fara qara time in da suke raba booklet ga student ya migama malama zainab dan basu ina zuwa sunan ummi mabiyar autarsu ya gani kan wayar towo ya fada yasan yanzu ai yakamata tana exam room yai saurin dagawa cikin kuka take magana yah ina cikin matsala subhanallahi mene badai malpractice aka kamaki dashi ba ko tai saurin goge hawayen kamar tana kusa dashi kaji kuma yaya Abinda banyi da ba zanyi yanzu.
Sai yanzu yadanji normal to mene wallahi yaya ina cikin matsala kana ina ne ni ina chemical engineering ok ganinan bata jira cewarsa ba ta kashe ya tsaya kawai yana kallon wayar kome wannan yar rikicin ta jawo musu kuma oho dan ko autansu baya abinda take kai tama zama tafi autan tabara hajiya kuma tai ta goya mata baya kodan shi autan baya qasar ne oho.
Minti biyar sai gata kamar wadda tai gudu tai futu futu da ita kallo daya yamata daga ajin da yake yaja tsaki sannan ya kuma yima malamar da suke kula da daliban magana pls ina zuwa.
Waike lafiya kika dokan kira haka tasa kuka yah na mance ID dina kuma sun hanani shiga towo ni me kike so na miki yanzu ta kamo hannunsa so nake kaje ja roqesu nasa Bala yaje ya karbo min to se ki bari yakawo ai.
Dan Allah yah kaji qaina kasan in aka fara fitowa bazasu barni inyi ba yai shigewarsa ajin ni nace ki dinga sakaci gobe kya rage lalaci da mantuwa aikuwa ganin ya shige ajin ta fashe da kuka.
Wajen minti biyar saiga malan Mansur yazo ya shiga ajin suka gaisa kafin su fito tare tasan mansur lecturer dinsu ne saidai yah nata bai taba ce mata yana da aboki a faculty dinsu ba balle department din datake kullun sai dai ya dinga cewa ta dage tai karatu danshi ba abinda zai iya mata.
Ya dagota yawwa gashinan abokina zaije ya rakaki anman wallahi inkina irin haka karma ki yi tunanin kinsanni tai tsalle tama mance a inda suke ta fada kansa that's why i love u mansur yace muje kina kuma makara tai saurin saukar da ido qasa wai taji kunya tabi bayansa suka wuce.
Duk abinda suke ummu na kallonsu ta tagar ajin da suje wani abu yazo ya tsaya mata arai ita kadai tasan mene kawai ta cigaba da rubutunta.
Ta gama rubutunta tas tana kuma dubawa na kusa da ita ya mata mgn juyowar da zatai tace me kace a idon Abbakar aikuwa yayo waje submit yace sorry tace bazaki bayar ba kena no ba hk bane ko ki bayar ko ki cike form dinnan ya miqo mata malpractice form tai saurin bashi tana singing out hawaye na bin idanunta ita kadai tasan hawayen me take dan bawai na anqwace bata gama bane.
Tunda ta fito take kuka har Aisha ta fito dagyar suka sa tai shiru ita da halima azahiri kenan anman a badini tai shiru ne kawai bawai dan taji nasihohinsu ba dan sanin bata da wata mafita inma kukan ta cigaba dayi shirun ma shine mafi alkairin kawai.
Sunfito suna masallaci danyi la'asar su tafi gida Hafsa ta dube ta idonnan yai fayau dashi tana riqe fa Abbakar Allah ummu mutumin can sanki yake wa kenan malan Abbakar mana taja tsaki maryam tace mene haka hafsa da aurenta fa yanzu in mijinta yaji yace mene haka nefa na mance ai wallahi kinyi sa'ar miji me sanki gashi me kyau halima tai dariya a'a Hafsa kimana shiru karkisa yanzu muga ta miqe ta hau jibgarki kinsan kishi gabaki daya sukai dariya inka dauke ummu da kana kallonta kasan yaqe take.
A old side Hafsat tace ita zata ta amso wata takadda Aisha tace tunda muka fito nakira mam nace mata munfito nidai na tafi to sai gobe suka hau dan sahu ita da ummu da fatima da halima halima ce ta fara sauka a danja su kuma aka wuce dasu.
Halima na sauka ummu ta dubu Aisha inasan magana daku ina cikin matsala wallahi but me yasa tun dazu baki fada mana ba to yanzu munajinki no inaso mu samu guri ne anman yanzu ki ba sai gobe.
Gobe kuna kun mance an gama exam ah hakane tacema dan sahu pls tsaya anan ya tsaya daidai legal college of islamic studies ku fito what kinafa ji nace miki na ce mam na tawo pls ina buqatar shawararku ne da gaggawa.
Aisha tadan tsaya jim tana tunani me adai daita sahun yace zaku saukanne ko mu wuce fatima ta fito tana juyar da fuska wai ita kar wani fa tasani yaganta ta sauka a qofar sch din akai gulmarta gida ummu ta miqa masa kudi Aisha bata da zabi ta fito.
Sun nuna ID dunsu na BUK sun kuma yi sa'a anbarsu sun shiga cikin kujeran da aka tanada dan zaman students na bakin bishiya suka zauna.
Ai kuwa suna zama ummu ta fashe da kuka dagyar tai shiru saida Fatima ta miqe kinga inbazaki fada mana ba ni zan tafi ta rugo hannunta alamar ta dawo ta zauna.
Ta komo ta zauna ina cikin wani hali mene ya faru munce ki dena wannan damuwar kinqi.
Yah nasir ne matsalata me ya miki inji Aisha fatima ta dafe qirji badai cewa yai kibar masa gida ba in wannan ne ai me sauqi ne to mene suka fada cikin tsoro.
Wai cewa yai yana sona mtssss suka ja tsaki atare to saime ke ba abin farin cikinki bane mutumin da duda yasan komi game dake ya dauki kasadar riqeki duda yasan hakan zai iya rabashi da iyayansa yadauki nauyinki ya rufa miki asiri kika zo cikin Abbakar nanma bece komi ba ya dauki ragamar komi to mene ba damuwa.
Cikin kuka tace ni banasansa indai so na aure ne what ummu kinsan me kika ce kuwa eh nasani to wa kike so in bakya sansa Abbakar suka mike gabaki daya arazane suka maimaita Abbakar eh shi wai wane Abbakar din lecturer dinmi ba thermodynamic badai wanda ya koroki yauba eh shi ni shi nakeso nayi nayi na cire abun araina nakasa.
Tabdi kin dauko dala ba ganmo inji fatima Aisha tace haba ummu karki zama butulu mana ta ture hannunta da ta dafata ni shi kadai nake so shi kadai nake gani shi kadai ne burina shi kadai nake gani dashi na shirya rayuwata gabaki daya pls ya isa haka fatima ta fada cikin fushi bansan shirme wallahi........
Zanciga insha Allah
Wanna littafin
ReplyDeleteWannan littafin nawa ne pls inaso a cireshi sashi Anan batare da izinina ba satar fasaha ne
ReplyDelete