Ɗakin anty fannah na bita inda ta haɗa min turaruka masu kyau sosai, daga nan sai tace min wai zan rakata shopping, kasancewar bana fita yasa ni yin murna sannan na sanar da mummy abinda mummy tace shine
"ki dawo da wuri saboda ɗora abinci" naji daɗin yadda bata hanani fita ba ko tace sai na tambayi ɗan renin hankalin can
Kuɗina na wajen ta na karɓa kasancewar kuɗin aiki na a wajen ta yake na fito sai ɓangaren anty fannah inda na tarar da ita ta gama shiryawa muka kama hanya
Shoprite muka nufa don yin siyayyar mu, wurin man shafa wa muka je sannan sai wurin turaruka, sutura, nai mamakin irin kuɗin da anty fannah take kashe wa kamar bata san ciwon su ba
Rasa me zan siya na yi, sai dana ga alamar muna neman hanyar fita sannan nace wa anty fannah
"ni fa ban siya komai ba kuma ga kuɗina na zo da su" kallo na tayi sannan tai murmushi
"ai duk wannan siyayyar taki ce, jiya isma'il ya bani kuɗi kuma ba abinda zanyi da su don haka sai nace bari kawai in kashe miki su"
Riƙe baki nayi ina kallon ikon Allah ni na rasa bakin gode mata ma, can dai sai na ɗan buɗe baki sannan nace mata "na gode"
Yi tayi kamar bata ji ba, muka je counter ta biya sannan aka loda mana kayan mu a boot ɗin motar muka kama hanya
Na ɗauka gida zamu wuce sai kawai ganin mu nayi a saloon, muka shiga, ba kowa don haka muna zuwa aka hau yi mana gyaran kai, inda hair dreeser ɗin ta buɗe kaina wanda ya kusan sati uku da wata shegiyar kalba da nayi wa kaina
Sai da ta tsefe min sannan tai min steaming ɗin sa tunda bana retouching kan nan nawa ya sha gyara dama gani da gashi, don ma bana kula da shi,
tuni ya sauko har baya na, su ma kansu mutanen shagon sai yaba gashin nawa suke anty fannah ce ta kalle ni sannan tace
"kin ga waɗan nan ma sun yaba balle sabit" haɗe gira ta nayi
"ni wallahi anty fannah indai don sabit kike min wannan gyaran gwanda ma ki daina don ni ba san shi nake yi kuma babu abinda zai haɗa ni da shi"
"ko kaɗan ba don shi nake yi, asmau buri na ki zama mace yadda ko sabit ya sauwaƙe miki zaki zama me class yadda samun namijin da zai soki bazai yi wuya ba, kinga maza ba abinda suke so kamar mace me gyara, gyara shine mace
Amma dube ki dubi fuskar ki tukunyar kitchen ɗin ma tafi fuskar ki samun kulawa, haba asmau in ba kya son sabit mu bar zancen shi a gefe akwai wani ƙanina wallahi irinku yake so, ke dai kawai abinda nake so da ke shi, duk abinda na siyo miki kiyi amfani da su har ki goge wannan baƙin naki me dusashewa ya koma baƙi me kyau a lkcn zan sa sabit ya sake ki sannan in haɗa ki da ƙanin nawa wallahi zaki sha gata"
Ta ƙare zancen ta da murmushi daɗi ne ya cika ni ganin zan samu wanda zai soni, amma ni da sabit haihata haihata, har aka gama mana gyaran kai da kuma pedicure da manicure tana bani duk wasu tips na gyara mace inda ni kuma nake recording a ƙwaƙwalwata
Sai gab da magariba sannan muka koma gida, don haka kawai sai na ɗora wa gidan jollof na spag ɗuk da de na san sabit baya son
A zuciyata nace in bazai ci ba matar sa ta dafa masa wani ai tana koyon girki (a ƙaryar ta) anty fannah ce ta tana ni muka gama sannan ta sani yin wanka na shafa sabon man data siyo min tare da turare na kwanta
Dama haka ƴan gayu suke ko ba miji a kusa da kai sai ka baɗe jikin ka da turare ka nemi lfyr katifa ka kwanta hmmm nima in shaa Allah sai na zama ƴar gayu sai na kwatar wa kaina ƴanci daga wajen sabit sannan sai na auri mijin da zai ji dani murmushi nayi dana tuno da ƙanin anty fannah
********************
Cikin hukuncin Allah nima na fara canza wa, wannan baƙin nawa wanda yake tsokane idon mutane ya fara kyau inda na koma chocolate colour sannan ƙamshi ya fara ratsa ni amma duk da haka sai anty fannah tace be mata ba don haka sai muka fara shirin zuwa maiduguri wai zata ganin gida inda ni kuma zan mata rakiya
Da ƙyar aka shawo kan mummy ta yadda muje muyi kwana uku, inda anty fannah tace
"taga tafiyar dawowa ba sai lkcn da muke so ba"
Ban sani ba ashe ta samu sabit sai tayi masa zancen tafiyar tamu buɗar bakin sa sai yace
"in ta tafi wa zai dinga mana girki
Wai yarinyar sam bata san aikin ta bane, bata san biyan ta ake ba zata wani tsiri tafiya to ban yadda ba in kuwa ta sake ta biki wallahi sai na zare a albashinta" ya faɗa a fusace
"sabit matar ka ce faa kana nufin ba ka hanata bane saboda matar ka ce a a ka hanata ne saboda abincin da take maka anya kasan haqqin aure kuwa"
Wani banzan kallo ya bita da shi sannan tace
"itace ta ke gaya miki ni mijinta ne, bata gaya miki sharaɗin auren namu bane, wai yarinyar nan me take nufi ne, ni me zanyi da ita Allah ya sauwake min zama da baƙar mace ai ni sai fara kamar yadda nake farin nan"
Babu yadda anty fannah batai ba akan ya gaya mata yadda asmaun take a wajen sa amma duk kalmar da zata fito daga bakin sa game da asmaun ta ashsha ce da kuma yi wa kansa Allah ya tsare shi da baƙar mace
"shike nan tunda ka rainata saboda baƙa ce ka bata takarda ta inya so sai ta samu wani ta aura wanda zai so ta"
Nuna mata yayi ko a jikin sa sannan ya ƙara gaba, tsayawa tayi tana ƙare masa kallo lalle ma sabit ɗin nan ashe haka yake,
Shi ya ɗauka kyan mace a fuska ne kawai be san duk kyan mace in dai bata haɗa abubuwan da ake so na zama cikakkiyar mace hoto ce kawai kuma na wani ɗan lkc ne da an ɗan zauna an zama jiki shike nan sai kyan ya gushe kuma sai a koma zaman gaskiya zaman da ba kwaskwarima ba ƙyalƙyal banza
Amma shi sam kamar be fahimta ba shike nan mu zuba ido ni da kai sabit zamu ga wa zai zo nan gaba yana ƴar murya, lallai ma sabit ɗin nan ta kuma maimaitawa tana yin gaba abinta
Shiri muka soma yi na tafiya, ni dai murnata ɗaya zan huta sannan zanje in haɗu da wanda zai soni kamar yadda nake so, sannan in samu kulawa
Cikin ikon Allah muka kama hanyar maid. ni da anty fannah tafiyar da ta canza min rayuwa, wacce ta fidda ni ƙuncin nan sannan ta saka ni cikin wani hali da babu abinda zance sai godiyar Allah
Muna sauka muka wuce gidan su anty fannah, babban gida ne nayi mamakin irin girman gidan su, sassane daban daban, family house ne wanda yake cike da iyalai daban daban
Mahaifin anty fannah shine babba a gidan kuma shine me abin hannun gida duk da dai kowa yana da nashi amma nashi ya fi na kowa
Ɓangaren su ƙato inda mahaifiyar anty fannah ce kawai mata a wajen bbn su, tunda muka sauka nake zare ido inga ko zanga ƙanin natan da take cewa zata haɗa ni, wayaga azarɓaɓi
Sauka ta musammam akai min, kasancewar yaren su na kanuri suke yi yasa sam ban ma gane me suke nufi ba amma kuma kamar da ni suke don naga alamar sukan ɗan saci kallo na sannan su ci gaba
Kunya ce ta kamani, ko anty fannah tana wa mmn bayanin nice wacce za ta haɗa da ƙanin ta Allah ya sa na faɗa a raina cike da kunya
Sai da suka gama tsab sannan anty fannah ta ja ni zuwa ɗakinta muka ci abinci inda take gaya min cewar zamu koma gidan ƙanwar mmn ta da zama acan za ai mata gyara jiki ne in ina so sai in faɗa sai ai min
Ganin cewar jikina a haka is ok ya sani cewar bana so nafi son gani na a haka, sam bata tanka ba ko ta musa min sai da muka gama komai sannan muka shirya inda muka kama hanyar gidan kanwar mmn tata
Mun isa gidan ana kiran sallah la'asar gida ne de irin namu na mutan kano, tsarkar gida ne babba sosai sai ɗakuna da suka zagaye gidan sai banɗaki sannan wani tafkeken kitchen
Kusan rabin tsakar gidan cike yake da shirgi, da tukwane waɗanda duk aka ajiye su, sai uban itatuwa a buhu buhu sai kace ƴar me magani
Gidan banda ƙamshin turare babu abinda yake yi kamar ma'aikatr sarrafa turaruka, mata ne sun kai kusan 20 kowacce da abinda take yi, daga masu haɗa turare sai masu sassaƙa icce ko dai wani abu.
Suna ganin shigowar mu su hau yaren su, wanda sam bana ganewa amma daga dukkan alamu murnar ganin anty fannah suke, kayan mu suka karɓa, sannan suka shigar mana da shi wani ɗakin inda muma muka shiga bayan mun gama gaisawa
Wata mata ce zaune a kan tafkeken carpet ɗin daya malale ɗakin tana ta magana a waya wanda sam ban san me take cewa ba, amma fuskar ta taf da fara'ar ganin mu sannan sai ta dinga ma na nuni da hannu na alamar mu zauna
Wuri muka samu muka zauna sai da ta gama tsab sannan ta juyo gare mu, inda anty fannah ta ɗan kƙara durƙusawa tare da gaishe ta da yaren su ni ma durƙusawar nayi amma sai nayi gum
Anty fannah ce take mata bayanin gaishe ta nake, da hannu ta saka ta yafito ni inda ni kuma na tashi na ƙarasa kusa da ita
Yaran su ta dinga yi tare da ƙare min kallo ido na kai kan anty fannah sai take cewa
"tace kina da kyau" kunya ce ta kamani na sunkuyar da kaina
Wani ɗan mai ta ɗakko kusa da ita a wata ƙatuwar roba ta kwaɓa min a fuskar ta ba abinda man yake sai ƙamshi
A hankali ta fara shafa min shi sai daya game fuskar tawa gabaɗayan ta sannan ta soma murza min kamar nayi kuka don zafi amma sai na dake
Sai da ta gaji don kanta sannan ta dena ta juya tayi wa anty fannah yaren su wanda anty fannah tabi matar da murmushi nuna jin daɗin ta
Wai magunguna ta ɗauko sannan ta kira wata mata inda ta dinga ɗiba tana yi wa matar bayanin yadda za ai amfani da su ni dai ko kalma ɗaya bana fahinta,
Sai da ta gama sannan anty fannah tace min
"tashi ki bita ita zata miki gyaran jikin" tsayawa nayi na saki baki sai da ta ƙara maimaita min sannan na tashi na bayan mayar
Wani ɗaki naga mun shiga wanda ada ban ganshi ba domin yana ƙarshen gidan, muna shiga ɗakin kamar kitchen haka yake saboda tsabar tarkacen sannan tukwane sai wasu robobi manya manya ga kuma wani abu da akayi shi kamar da icce me ko me gashi nan dai kala kala
Wani ƙaton baho ta ɗauko ta zuba wani ruwa ta gama haɗe haɗen ta sannan tai min nuni da in yi wanka da ruwa, bokiti na ɗauka na zundumin ruwan sannan na kama hanyar toilet don in watsa, ko da na shiga banɗakin sai ga matar ta biyo ni
Tsayawa nayi ina kallon matar nan kar dai tace min itace zata min wanka, tsare ta nayi da ido don in san me take shirin yi
Wani riga ta ɗauko min ƴar ƙarama kamar shimi amma half vest, da wandon sa tace min in saka, ganin na ƙi karɓa ya sa ta fara min faɗa
Karɓa nayi sannan na juya mata baya, kayan sababbi ne na saka sai da na gama sannan ta juyo,
Wani botiki ta ɗauko, ta lakuci wani sabulu sannan ta fara gurza min, zafi ne kawai yake ziyartata
Ko ina na jikina wanda yake waje haka ta dinga bin jikin nawa tana dirza tana ƙara sheƙa min ruwan tare da ƙara saɓar sabulun tana ƙara wanke ni
Sai da ruwan ya ƙare ta kuma fita ta kuma ƙarowa, ko da ta dawo, sai ta ɗibo ruwa tace min in ɗauraye jikina
Ruwan na zuba na ɗauraye jiki na sannan ta kuma zaunar da ni akan wata kujera inda ƙasan kujerar
Turiri yake fita yana ratsa ni ta ƙasan sannan jikina kuma tana ta saɓar min shi kai ranar na gurzu sai kace za a canza min fata
Sai da aka gama tsab sannan na cire rigar jikina da wandon na ɗauro zani na fito, inda tazo ta sakani a cikin wani abu shi ba kwando gashi nan dai
Turare ne yake ta tashi a cikin sa gabaɗay jikina na ciki in banda kaina da ke waje, gaskiya ranar na sha gashi
Shi kanshi kai na ba a barshi a baya ba, haka ya sha gyara sai wani ni'imantaccen ƙamshi yake fiddawa
Kwanan na 7 sati ɗaya kenan ana min wannan gyaran wanda nasan dana gama zan haɗu da ƙanin anty fannah nasan yana ganina zai ruɗe yace saini
Ga kuma na sha wanda shi wannan da anty fannah muke sha, lkcn da aka gama aka bani izinin kallon mudubi na ɗauka ba ni bace 🤣
Ɗau haka na yi da baƙin nawa amma ba kamar na da ba, ƙwal haka na koma kai sai kayi zaton daga inji na fito ga wani ƙamshi daya ke tashi a jiki na kamar wacce tayi wanka da ruwan turare sannan ga santsi da laushin duk na haɗa
Ni kaina daɗin taɓa fatar jikina nake yi balle kuma wani ya taɓa, ita kanta anty fannah sai yaba min take da irin wannan haɗuwar dana ɗauka
"kin ganki kuwa asmau ai wallahi yanzu idan sabit ya ganki sai ya ruɗe ya dena kula wannan ja ja amalen tasa"
Zunɓurar baki nayi sannan nace
"ni fa ba don shi nayi wannan gyaran ba fatana Allah ya haɗa ni da mijin da zai so ni kamar ba gobe ba wannan ɗan renin hankalin ba"
Dariya tayi sannan tace
"hmmmm shima sabit ɗin bari ya afka tarkon nan zaki ga love 😍 har sai kince ya ishe ki" ni sam maganar wani sabit ma bana so balle inyi tunanin zai so ni
Me ya haɗa ni da shi ai na riga na gama da babin sa, haka muka ci gaba da hira na so ace ta kuma sako zancen ƙanin natan sai naji bata sako ba Allah dai ya sa ba ta manta bane
Satin mu biyu a maid. muka kama hanyar abj, cike da samun nasara daban daban barin ma ni ƙara kilewa da nayi da kuma gogewa,
Lfy lau muka sauka agida inda na wuce part ɗin mummy directly don inyi reporting na dawo, nai mamakin yadda ta saki baki tana kallo na kamar bata taɓa ganina ba
"mummy lfy ko sai kace yau kika fara ganina"
"asmau wannan canji haka sai kace inji kika shiga a maidugurin, kinga yadda kika koma kuwa lallai maa shaa Allah wannan gyara yayi sai dai kawai ace wa sabit ya kawo kuɗi"
Ɓata rai na nayi sannan nace
"mummy sabit ɗin daya ce in matar sa ta iya girki sakina zai yi nima ai a hakan take, ina gama haɗa kuɗin da nake so ko matar sa ta iya girki ko bata iya ba dolen sa ya ƙyale ni in tafi"
"shi yace miki idan matar sa ta iya girkin zai sake kin" shiru nayi don be faɗa min haka ba amma alamu ne suka nuna min
"asmau har yanzu sabit be san irin baiwar da Allah yai miki ba amma daya gano hakan wallahi bazai iya rabuwa da ke ba, ni ma kaina bazan so hakan ba kuma bazan bari ba"
Tsayawa nayi ina kallon ikon Allah naga alamar matar nan ma son kanta ma yayi yawa don haka nasan duk yadda zan fadalta rashin son zama na da sabit baza ta gane ba
Bana son shi kamar yadda shima yake ikirarin rashin sona da baya yi, miƙewa nayi sannan nace
"mummy ni na gudu kitchen gwanda inje in ɗaura abincin gidan don kowa yasan na dawo" murmushi kawai tayi sannan ta gyaɗa kanta inda ni kuma na fice
👩🏽🍳 *menu of d day*👩🏽🍳
*curry rice served egg sauce and banana cocktail*
*curry rice*
```ingredients```
-shinkafa
-curry
-gishiri
*method*
1) ki zuba ruwa a tukunya idan ya tafasa sai ki auno shinkafar ki ki wanke ki zuba ki barta tayi tafasa ɗaya sannan ki sauke ki tace ruwan ki wanke ta
2) ki ƙara zuba ruwa amma ba dayawa ba yadda zata ƙarasa dafa miki shinkafar, idan ruwan ya tafasa sai ki zuba curry da gishiri ki barshi kamar minti ɗaya haka sai ki zuba shinkafar ki ki rage mata wuta a barta ta ƙarasa idan ta dahu sai a sauke
*egg sauce*
```ingrdients```
-egg
-attaruhu
-albasa
-maggi
-sardine
*method*
1) ki jajjaga attaruhu da albasa sannan ki a jiye su
2) ki samu sauce pan ki zuba mai da albasa kaɗan idan man yai zafi sai ki zuba jajjagenki sai ki bari ya tafasa
3) kasancewar ba ruwa don haka bazai ɗau lkcn ba, ki zuba maggi, da sardine (bayan ki dagargaza shi) sai ki juya
3) ki fasa ƙwai a bowl daban sai ki kaɗa, idan miyar ta ɗan ƙara soyuwa sai ki zuba kwan sai a barshi kar a juya amma a rage masa wuta
4) idan ƙwan ya dahu sai a ɗan juya kaɗan don kar ƙwan ya dagargaje sai a saike
*banana cocktail*
```ingredients```
-banana
-sugar syrup
-milk
-flavour
*method*
1) ki tasafa ruwa kaɗan da sugar idan sugar ta narke sai ki sauke ki juye don ya huce
2) ki zuba madara a cocktail bowl sai ki zuba syrup da flavour ɗin ki sai ki saka a fridge don yayi sanyi, idan an tashi za ci sai a yanyanka ayaba ƙanana a zuba sai aci a take
👩🏽🍳 *BON APPETIT*👩🏽🍳
*ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
*Aisha ibrahim maina (mmn mummy) ga page ɗinki nan takanas na ta tashi na hana kaina bacci nayi typing ɗin shi saboda ke, don haka ashaa karatu lfy, ga girki nan a ƙasa da fatan za a ƙawata bbn mummy da shi*
*my asmy i lobe u cikin kwanon shaaa*😘 🤣🤣🤣🤣
*Amrath amrath & asmau ta hikima grp asmaun sabit na miƙo miki 😘, my asmy ba ke ba ɗayar Allah yasa ta gane kanta*
P⃗a⃗g⃗e⃗ 13🌹
Ɗakin anty fannah na bita inda ta haɗa min turaruka masu kyau sosai, daga nan sai tace min wai zan rakata shopping, kasancewar bana fita yasa ni yin murna sannan na sanar da mummy abinda mummy tace shine
"ki dawo da wuri saboda ɗora abinci" naji daɗin yadda bata hanani fita ba ko tace sai na tambayi ɗan renin hankalin can
Kuɗina na wajen ta na karɓa kasancewar kuɗin aiki na a wajen ta yake na fito sai ɓangaren anty fannah inda na tarar da ita ta gama shiryawa muka kama hanya
Shoprite muka nufa don yin siyayyar mu, wurin man shafa wa muka je sannan sai wurin turaruka, sutura, nai mamakin irin kuɗin da anty fannah take kashe wa kamar bata san ciwon su ba
Rasa me zan siya na yi, sai dana ga alamar muna neman hanyar fita sannan nace wa anty fannah
"ni fa ban siya komai ba kuma ga kuɗina na zo da su" kallo na tayi sannan tai murmushi
"ai duk wannan siyayyar taki ce, jiya isma'il ya bani kuɗi kuma ba abinda zanyi da su don haka sai nace bari kawai in kashe miki su"
Riƙe baki nayi ina kallon ikon Allah ni na rasa bakin gode mata ma, can dai sai na ɗan buɗe baki sannan nace mata "na gode"
Yi tayi kamar bata ji ba, muka je counter ta biya sannan aka loda mana kayan mu a boot ɗin motar muka kama hanya
Na ɗauka gida zamu wuce sai kawai ganin mu nayi a saloon, muka shiga, ba kowa don haka muna zuwa aka hau yi mana gyaran kai, inda hair dreeser ɗin ta buɗe kaina wanda ya kusan sati uku da wata shegiyar kalba da nayi wa kaina
Sai da ta tsefe min sannan tai min steaming ɗin sa tunda bana retouching kan nan nawa ya sha gyara dama gani da gashi, don ma bana kula da shi,
tuni ya sauko har baya na, su ma kansu mutanen shagon sai yaba gashin nawa suke anty fannah ce ta kalle ni sannan tace
"kin ga waɗan nan ma sun yaba balle sabit" haɗe gira ta nayi
"ni wallahi anty fannah indai don sabit kike min wannan gyaran gwanda ma ki daina don ni ba san shi nake yi kuma babu abinda zai haɗa ni da shi"
"ko kaɗan ba don shi nake yi, asmau buri na ki zama mace yadda ko sabit ya sauwaƙe miki zaki zama me class yadda samun namijin da zai soki bazai yi wuya ba, kinga maza ba abinda suke so kamar mace me gyara, gyara shine mace
Amma dube ki dubi fuskar ki tukunyar kitchen ɗin ma tafi fuskar ki samun kulawa, haba asmau in ba kya son sabit mu bar zancen shi a gefe akwai wani ƙanina wallahi irinku yake so, ke dai kawai abinda nake so da ke shi, duk abinda na siyo miki kiyi amfani da su har ki goge wannan baƙin naki me dusashewa ya koma baƙi me kyau a lkcn zan sa sabit ya sake ki sannan in haɗa ki da ƙanin nawa wallahi zaki sha gata"
Ta ƙare zancen ta da murmushi daɗi ne ya cika ni ganin zan samu wanda zai soni, amma ni da sabit haihata haihata, har aka gama mana gyaran kai da kuma pedicure da manicure tana bani duk wasu tips na gyara mace inda ni kuma nake recording a ƙwaƙwalwata
Sai gab da magariba sannan muka koma gida, don haka kawai sai na ɗora wa gidan jollof na spag ɗuk da de na san sabit baya son
A zuciyata nace in bazai ci ba matar sa ta dafa masa wani ai tana koyon girki (a ƙaryar ta) anty fannah ce ta tana ni muka gama sannan ta sani yin wanka na shafa sabon man data siyo min tare da turare na kwanta
Dama haka ƴan gayu suke ko ba miji a kusa da kai sai ka baɗe jikin ka da turare ka nemi lfyr katifa ka kwanta hmmm nima in shaa Allah sai na zama ƴar gayu sai na kwatar wa kaina ƴanci daga wajen sabit sannan sai na auri mijin da zai ji dani murmushi nayi dana tuno da ƙanin anty fannah
********************
Cikin hukuncin Allah nima na fara canza wa, wannan baƙin nawa wanda yake tsokane idon mutane ya fara kyau inda na koma chocolate colour sannan ƙamshi ya fara ratsa ni amma duk da haka sai anty fannah tace be mata ba don haka sai muka fara shirin zuwa maiduguri wai zata ganin gida inda ni kuma zan mata rakiya
Da ƙyar aka shawo kan mummy ta yadda muje muyi kwana uku, inda anty fannah tace
"taga tafiyar dawowa ba sai lkcn da muke so ba"
Ban sani ba ashe ta samu sabit sai tayi masa zancen tafiyar tamu buɗar bakin sa sai yace
"in ta tafi wa zai dinga mana girki
Wai yarinyar sam bata san aikin ta bane, bata san biyan ta ake ba zata wani tsiri tafiya to ban yadda ba in kuwa ta sake ta biki wallahi sai na zare a albashinta" ya faɗa a fusace
"sabit matar ka ce faa kana nufin ba ka hanata bane saboda matar ka ce a a ka hanata ne saboda abincin da take maka anya kasan haqqin aure kuwa"
Wani banzan kallo ya bita da shi sannan tace
"itace ta ke gaya miki ni mijinta ne, bata gaya miki sharaɗin auren namu bane, wai yarinyar nan me take nufi ne, ni me zanyi da ita Allah ya sauwake min zama da baƙar mace ai ni sai fara kamar yadda nake farin nan"
Babu yadda anty fannah batai ba akan ya gaya mata yadda asmaun take a wajen sa amma duk kalmar da zata fito daga bakin sa game da asmaun ta ashsha ce da kuma yi wa kansa Allah ya tsare shi da baƙar mace
"shike nan tunda ka rainata saboda baƙa ce ka bata takarda ta inya so sai ta samu wani ta aura wanda zai so ta"
Nuna mata yayi ko a jikin sa sannan ya ƙara gaba, tsayawa tayi tana ƙare masa kallo lalle ma sabit ɗin nan ashe haka yake,
Shi ya ɗauka kyan mace a fuska ne kawai be san duk kyan mace in dai bata haɗa abubuwan da ake so na zama cikakkiyar mace hoto ce kawai kuma na wani ɗan lkc ne da an ɗan zauna an zama jiki shike nan sai kyan ya gushe kuma sai a koma zaman gaskiya zaman da ba kwaskwarima ba ƙyalƙyal banza
Amma shi sam kamar be fahimta ba shike nan mu zuba ido ni da kai sabit zamu ga wa zai zo nan gaba yana ƴar murya, lallai ma sabit ɗin nan ta kuma maimaitawa tana yin gaba abinta
Shiri muka soma yi na tafiya, ni dai murnata ɗaya zan huta sannan zanje in haɗu da wanda zai soni kamar yadda nake so, sannan in samu kulawa
Cikin ikon Allah muka kama hanyar maid. ni da anty fannah tafiyar da ta canza min rayuwa, wacce ta fidda ni ƙuncin nan sannan ta saka ni cikin wani hali da babu abinda zance sai godiyar Allah
Muna sauka muka wuce gidan su anty fannah, babban gida ne nayi mamakin irin girman gidan su, sassane daban daban, family house ne wanda yake cike da iyalai daban daban
Mahaifin anty fannah shine babba a gidan kuma shine me abin hannun gida duk da dai kowa yana da nashi amma nashi ya fi na kowa
Ɓangaren su ƙato inda mahaifiyar anty fannah ce kawai mata a wajen bbn su, tunda muka sauka nake zare ido inga ko zanga ƙanin natan da take cewa zata haɗa ni, wayaga azarɓaɓi
Sauka ta musammam akai min, kasancewar yaren su na kanuri suke yi yasa sam ban ma gane me suke nufi ba amma kuma kamar da ni suke don naga alamar sukan ɗan saci kallo na sannan su ci gaba
Kunya ce ta kamani, ko anty fannah tana wa mmn bayanin nice wacce za ta haɗa da ƙanin ta Allah ya sa na faɗa a raina cike da kunya
Sai da suka gama tsab sannan anty fannah ta ja ni zuwa ɗakinta muka ci abinci inda take gaya min cewar zamu koma gidan ƙanwar mmn ta da zama acan za ai mata gyara jiki ne in ina so sai in faɗa sai ai min
Ganin cewar jikina a haka is ok ya sani cewar bana so nafi son gani na a haka, sam bata tanka ba ko ta musa min sai da muka gama komai sannan muka shirya inda muka kama hanyar gidan kanwar mmn tata
Mun isa gidan ana kiran sallah la'asar gida ne de irin namu na mutan kano, tsarkar gida ne babba sosai sai ɗakuna da suka zagaye gidan sai banɗaki sannan wani tafkeken kitchen
Kusan rabin tsakar gidan cike yake da shirgi, da tukwane waɗanda duk aka ajiye su, sai uban itatuwa a buhu buhu sai kace ƴar me magani
Gidan banda ƙamshin turare babu abinda yake yi kamar ma'aikatr sarrafa turaruka, mata ne sun kai kusan 20 kowacce da abinda take yi, daga masu haɗa turare sai masu sassaƙa icce ko dai wani abu.
Suna ganin shigowar mu su hau yaren su, wanda sam bana ganewa amma daga dukkan alamu murnar ganin anty fannah suke, kayan mu suka karɓa, sannan suka shigar mana da shi wani ɗakin inda muma muka shiga bayan mun gama gaisawa
Wata mata ce zaune a kan tafkeken carpet ɗin daya malale ɗakin tana ta magana a waya wanda sam ban san me take cewa ba, amma fuskar ta taf da fara'ar ganin mu sannan sai ta dinga ma na nuni da hannu na alamar mu zauna
Wuri muka samu muka zauna sai da ta gama tsab sannan ta juyo gare mu, inda anty fannah ta ɗan kƙara durƙusawa tare da gaishe ta da yaren su ni ma durƙusawar nayi amma sai nayi gum
Anty fannah ce take mata bayanin gaishe ta nake, da hannu ta saka ta yafito ni inda ni kuma na tashi na ƙarasa kusa da ita
Yaran su ta dinga yi tare da ƙare min kallo ido na kai kan anty fannah sai take cewa
"tace kina da kyau" kunya ce ta kamani na sunkuyar da kaina
Wani ɗan mai ta ɗakko kusa da ita a wata ƙatuwar roba ta kwaɓa min a fuskar ta ba abinda man yake sai ƙamshi
A hankali ta fara shafa min shi sai daya game fuskar tawa gabaɗayan ta sannan ta soma murza min kamar nayi kuka don zafi amma sai na dake
Sai da ta gaji don kanta sannan ta dena ta juya tayi wa anty fannah yaren su wanda anty fannah tabi matar da murmushi nuna jin daɗin ta
Wai magunguna ta ɗauko sannan ta kira wata mata inda ta dinga ɗiba tana yi wa matar bayanin yadda za ai amfani da su ni dai ko kalma ɗaya bana fahinta,
Sai da ta gama sannan anty fannah tace min
"tashi ki bita ita zata miki gyaran jikin" tsayawa nayi na saki baki sai da ta ƙara maimaita min sannan na tashi na bayan mayar
Wani ɗaki naga mun shiga wanda ada ban ganshi ba domin yana ƙarshen gidan, muna shiga ɗakin kamar kitchen haka yake saboda tsabar tarkacen sannan tukwane sai wasu robobi manya manya ga kuma wani abu da akayi shi kamar da icce me ko me gashi nan dai kala kala
Wani ƙaton baho ta ɗauko ta zuba wani ruwa ta gama haɗe haɗen ta sannan tai min nuni da in yi wanka da ruwa, bokiti na ɗauka na zundumin ruwan sannan na kama hanyar toilet don in watsa, ko da na shiga banɗakin sai ga matar ta biyo ni
Tsayawa nayi ina kallon matar nan kar dai tace min itace zata min wanka, tsare ta nayi da ido don in san me take shirin yi
Wani riga ta ɗauko min ƴar ƙarama kamar shimi amma half vest, da wandon sa tace min in saka, ganin na ƙi karɓa ya sa ta fara min faɗa
Karɓa nayi sannan na juya mata baya, kayan sababbi ne na saka sai da na gama sannan ta juyo,
Wani botiki ta ɗauko, ta lakuci wani sabulu sannan ta fara gurza min, zafi ne kawai yake ziyartata
Ko ina na jikina wanda yake waje haka ta dinga bin jikin nawa tana dirza tana ƙara sheƙa min ruwan tare da ƙara saɓar sabulun tana ƙara wanke ni
Sai da ruwan ya ƙare ta kuma fita ta kuma ƙarowa, ko da ta dawo, sai ta ɗibo ruwa tace min in ɗauraye jikina
Ruwan na zuba na ɗauraye jiki na sannan ta kuma zaunar da ni akan wata kujera inda ƙasan kujerar
Turiri yake fita yana ratsa ni ta ƙasan sannan jikina kuma tana ta saɓar min shi kai ranar na gurzu sai kace za a canza min fata
Sai da aka gama tsab sannan na cire rigar jikina da wandon na ɗauro zani na fito, inda tazo ta sakani a cikin wani abu shi ba kwando gashi nan dai
Turare ne yake ta tashi a cikin sa gabaɗay jikina na ciki in banda kaina da ke waje, gaskiya ranar na sha gashi
Shi kanshi kai na ba a barshi a baya ba, haka ya sha gyara sai wani ni'imantaccen ƙamshi yake fiddawa
Kwanan na 7 sati ɗaya kenan ana min wannan gyaran wanda nasan dana gama zan haɗu da ƙanin anty fannah nasan yana ganina zai ruɗe yace saini
Ga kuma na sha wanda shi wannan da anty fannah muke sha, lkcn da aka gama aka bani izinin kallon mudubi na ɗauka ba ni bace 🤣
Ɗau haka na yi da baƙin nawa amma ba kamar na da ba, ƙwal haka na koma kai sai kayi zaton daga inji na fito ga wani ƙamshi daya ke tashi a jiki na kamar wacce tayi wanka da ruwan turare sannan ga santsi da laushin duk na haɗa
Ni kaina daɗin taɓa fatar jikina nake yi balle kuma wani ya taɓa, ita kanta anty fannah sai yaba min take da irin wannan haɗuwar dana ɗauka
"kin ganki kuwa asmau ai wallahi yanzu idan sabit ya ganki sai ya ruɗe ya dena kula wannan ja ja amalen tasa"
Zunɓurar baki nayi sannan nace
"ni fa ba don shi nayi wannan gyaran ba fatana Allah ya haɗa ni da mijin da zai so ni kamar ba gobe ba wannan ɗan renin hankalin ba"
Dariya tayi sannan tace
"hmmmm shima sabit ɗin bari ya afka tarkon nan zaki ga love 😍 har sai kince ya ishe ki" ni sam maganar wani sabit ma bana so balle inyi tunanin zai so ni
Me ya haɗa ni da shi ai na riga na gama da babin sa, haka muka ci gaba da hira na so ace ta kuma sako zancen ƙanin natan sai naji bata sako ba Allah dai ya sa ba ta manta bane
Satin mu biyu a maid. muka kama hanyar abj, cike da samun nasara daban daban barin ma ni ƙara kilewa da nayi da kuma gogewa,
Lfy lau muka sauka agida inda na wuce part ɗin mummy directly don inyi reporting na dawo, nai mamakin yadda ta saki baki tana kallo na kamar bata taɓa ganina ba
"mummy lfy ko sai kace yau kika fara ganina"
"asmau wannan canji haka sai kace inji kika shiga a maidugurin, kinga yadda kika koma kuwa lallai maa shaa Allah wannan gyara yayi sai dai kawai ace wa sabit ya kawo kuɗi"
Ɓata rai na nayi sannan nace
"mummy sabit ɗin daya ce in matar sa ta iya girki sakina zai yi nima ai a hakan take, ina gama haɗa kuɗin da nake so ko matar sa ta iya girki ko bata iya ba dolen sa ya ƙyale ni in tafi"
"shi yace miki idan matar sa ta iya girkin zai sake kin" shiru nayi don be faɗa min haka ba amma alamu ne suka nuna min
"asmau har yanzu sabit be san irin baiwar da Allah yai miki ba amma daya gano hakan wallahi bazai iya rabuwa da ke ba, ni ma kaina bazan so hakan ba kuma bazan bari ba"
Tsayawa nayi ina kallon ikon Allah naga alamar matar nan ma son kanta ma yayi yawa don haka nasan duk yadda zan fadalta rashin son zama na da sabit baza ta gane ba
Bana son shi kamar yadda shima yake ikirarin rashin sona da baya yi, miƙewa nayi sannan nace
"mummy ni na gudu kitchen gwanda inje in ɗaura abincin gidan don kowa yasan na dawo" murmushi kawai tayi sannan ta gyaɗa kanta inda ni kuma na fice
👩🏽🍳 *menu of d day*👩🏽🍳
*curry rice served egg sauce and banana cocktail*
*curry rice*
```ingredients```
-shinkafa
-curry
-gishiri
*method*
1) ki zuba ruwa a tukunya idan ya tafasa sai ki auno shinkafar ki ki wanke ki zuba ki barta tayi tafasa ɗaya sannan ki sauke ki tace ruwan ki wanke ta
2) ki ƙara zuba ruwa amma ba dayawa ba yadda zata ƙarasa dafa miki shinkafar, idan ruwan ya tafasa sai ki zuba curry da gishiri ki barshi kamar minti ɗaya haka sai ki zuba shinkafar ki ki rage mata wuta a barta ta ƙarasa idan ta dahu sai a sauke
*egg sauce*
```ingrdients```
-egg
-attaruhu
-albasa
-maggi
-sardine
*method*
1) ki jajjaga attaruhu da albasa sannan ki a jiye su
2) ki samu sauce pan ki zuba mai da albasa kaɗan idan man yai zafi sai ki zuba jajjagenki sai ki bari ya tafasa
3) kasancewar ba ruwa don haka bazai ɗau lkcn ba, ki zuba maggi, da sardine (bayan ki dagargaza shi) sai ki juya
3) ki fasa ƙwai a bowl daban sai ki kaɗa, idan miyar ta ɗan ƙara soyuwa sai ki zuba kwan sai a barshi kar a juya amma a rage masa wuta
4) idan ƙwan ya dahu sai a ɗan juya kaɗan don kar ƙwan ya dagargaje sai a saike
*banana cocktail*
```ingredients```
-banana
-sugar syrup
-milk
-flavour
*method*
1) ki tasafa ruwa kaɗan da sugar idan sugar ta narke sai ki sauke ki juye don ya huce
2) ki zuba madara a cocktail bowl sai ki zuba syrup da flavour ɗin ki sai ki saka a fridge don yayi sanyi, idan an tashi za ci sai a yanyanka ayaba ƙanana a zuba sai aci a take
👩🏽🍳 *BON APPETIT*👩🏽🍳
*ASMA'UN SABIT*
[10:33PM, 5/2/2018] +234 806 399 9164: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
P⃗a⃗g⃗e⃗ 14🌹
Gyara jikina ya kankama ko dana koma gida ban dena ba sai ma abinda ya ƙaru yanzu na zama ƴar gayu don anty fannah har tsokana ta take yi wai na kile na haɗu saura haɗuwar mu da sabit
Na kan ɓata rai a ni yanzu na fi ƙarfin sabit sai wanda zai so ni mu gwada soyayya tare wacce zata kasance a tsaftace ba mix ba irin ta sabita ba
Duk wannan abun da nake bamu taɓa haduwa da shi ba tunda ba ɓangaren sa nake zuwa ba tunda badia tayi ɓari Allah ya yaye min wannan bautar
Sai dai ita badiar wacce ganina da ita na farko bayan na waye sai da ta tsorata da ganina inda ta dake sannan ta fara kushe ni har da cemin
"inde ma don sabit kike yi to ki sa ranki a inuwa don bazaki taɓa birgeshi ba sabit sai ni kaɗai" sam ban raga mata ba nima clna ce mata
"ai ni mijin da zan aura sabo zai kasance dal a leda ba saura ba" maganar ya ƙona mata rai kuma ƙiri ƙiri ta nuna hakan
Tana shirin mai da martani ne sai anty fannah don haka sai ta haɗe rai tare da barin wurin tunda basa shiri dama ko da anty fannah ta tambaye ni me ya haɗa mu sai nace mata ba komai
Don bana son ta ga ko na zaƙu in haɗu da ƙanin ta na fi son ta fara yi min maganar sa da kanta bana son nuna gazawa ta bayan na zama me class 😎
Rannan da safe na tashi mai na ya ƙare don haka sai naje part ɗin anty fannah na faɗa mata in zata fita zan bata kudi ta siyo min, sai ma tace min inzo bayan azahar sai muje siyayyar tare don itama zatayi
Da murnata na koma na je na ɗauka girki kafin wannan na gama na bayar aka kai kowanne part nashi sannan na ɗauki na mummy don in kai mata
Da sallama na shiga falon na ajiye mata, tunda na ɗau gyara na zama kamar wata sabuwar aba a wajen mummy kullum na shiga sai tayi ta bina da kallo kamar bata taɓa gani na ba
Yau ma haka na kai mata har nayi hanyar waje zan fita sai ta kira ni, dawowa nayi na tsaya sai kuma ta rasa abinda zata faɗa min can dai sai tace
"kije kice wa badia ina son ganin ta" rai nane ya ɓaci ba abinda na tsana daya wuce wai inje part ɗin sabit
Jikina a saɓule haka na fice na kama hanyar, na zo dai dai hanyar da zan shiga part ɗin sabit ne naga anty fannah
"muje ko don na gama shirya wa" ta faɗa min
"gani nan zuwa mummy ce ta aike ni wurin anty badia" na faɗa murmushi naga ta saki sannam tace min
"maza kije ki dawo kuma ki dinga tafiya da nutsuwa kamar yadda na koya miki" ban kula taba hmmm kaji ta tafiyar da tace min sai a gaban mijina zanyi shi shine take son inyi shi zan shiga part ɗin wannan mara *M* ɗin
Ƙara sauri nayi ko dana ga na kusa zuwa ƙofar falon sai na saka gudu don inje in dawo da wuri,
Kiciɓis muka ci da wani dai dai corridor ɗin da zai sada ni da ƙofar falon, ruƙo ni yayi wanda da badan ruƙon ba da tuni nayi ƙasa
Ko da nayi gaining balance ɗina maimakon ya sake ki sai ya ƙara riƙe ni tare da shaƙar ƙamshin da nake yi
Can sai ya sassauta min riƙon inda ya kwantar da ni akan hannun sa muka haɗa ido *WAT* sabit ne
"kina gudu ina zaki je, dubi jikin ki lenge lenge kamar bakya cin abinci da badan na riƙe ki ba da tuni kinyi ƙasa kuma irin masu jikinku basa wahalar karye wa"
Ya faɗa fuskar sa taf da fara'a har wani kashe min ido yake na salon yaudara, hankaɗe shi nayi wanda yai taga taga zai faɗi sai kuma ya tsaya ƙyam duk da haka ina jikin nasan
"kar ki kayar da muna preety" ya faɗa
Haushi ya kuma kama ni, na kuma haɗe raina sai ya sake ni
"ki dinga tafiya a hankali don kar kiyi wa kanki illa" ya faɗa wanda ni ko ta kanshi ban bi ba na shige ciki
*******************
Sabit tsayawa yayi yana tunanin wacece wannan gaskiya tayi matsalar ta ɗaya baƙa ce kai da fara ce wannan da anyi haɗuwa
Kasa daurewa yayi sai daya bi bayan ta don yaga ko meye dangantakar su da badiar
Ima shiga falon ma dinga ƙwala mata kira, sai mula sannan sai gata ta sauko
"bashi na ci miki da kike min wannan kiran"
"mummy ce tace kije" na bata ansa
"me zata min" ta tambaya
"wannan kuma imkinje kyaji" na amsa mata tare da juya domin in fice cin karo muka ƙarayi da shi amma wannan karon sam jikin mu be haɗe ba
"asmau" naji badia ta ƙwala min kira, juyo wa nayi ba tare da na tanka mata ba
"me zaki dafa da daddare"
"tuwon semo miyar egusi" na bata ansa
"bana son tuwo jollof nake so kuma ki kawo da wuri, *SD* me kake son yin dinner da shi" ta tambaye shi
Be amsa ta ba saboda gabaɗayan hankalin sa baya tattare da shi sai da ta ƙara mai maitawa har da ƙwala masa kira sannan ya amsa inda kunya ta saka shi shigewa kitchen wanda ni kuma na fice na bar musu falon ina jiyo badia tana tambayar sa wai tunanin me yake a zuciyata nace can ta matse muku
Ina fitowa na ɗanyi nisa daga part ɗin nasu najiyo ana kirana ban tanka ba don nasan sabit ne ƙarasowa yayi ya sha gabana
"kina ji ina ta kiranki" shan kunu nayi nai masa banza
"naji kince tuwo zaki da daddare ni bazanci tuwo ba kiyi min parpesun naman kai da meat pie" kallon sama da ƙasa nai masa sannan nace
"ai na riga na gama rufe girkin da zanyi yau, in zaka ci abincin da matar ka zata ci wato jollof too in kuwa baza ka ci ba sai ka sata ta girka maka ai ta koyi girki a wajena"
"ban gane kin rufe karɓar girki ba, ni mijinki nace miki ga abinda zan ci shine zaki wani ce kin rufe karɓar girkin to ni zaki yi wa biyayya ko wa"
"ni ban san da wani batun aure ba aiki nake yi ake biyana, kamar yadda ka ɗauki auren ka yada shi a kwandon shara haka ni ma na ɗauke shi na saka shi a masai kaga yanzu ba wannan batun ake ba don haka ka ajiye wani batun mijin aiki ne na yau na rufe karbar order in kana son parpesu gobe da safe ka kira kitchen ka faɗa" ina gama faɗa masa na raɓa ta gefen shi na wuce
Lallai le ma yarinyar nan ni zata ce wa haka, ni da nake a matsayin mijin ta nace ga abinda zan ci shine bazata girka ba sai wasu Ƙarti zata girkawa abinci wallahi da sake ya za ayi wai matata ni baza ta min abinda nake so, wallahi hakurina ya zo ƙarshe dole ne a matsayin ta na matata ta kasance tana ƙarƙashina sannan tana bauta min ne ni kaɗai
Yana masifa ya kama hanyar part ɗin mummy dole ne duk abinda za a yi ayi a yau amma ban yadda ba ace matata ban da iko da ita
Har ya shiga ɓangaren mummy yana masifa, tana zaune ta ga shigowar shi ko sallama babu duk a tunanin ta ma ko faɗa sukai da badia ta ɓata masa ransa
"lfy auta na ganka haka wa ya taɓa min kai," ran shi a ɓace ya zauna kusa da ita sannan yace
"gaskiya mummy na gaji da wannan abun da ake min wai ace matata ta zama baiwa a gidan nan, kowa zai iya juya ta yadda yake so amma banda ni mijinta gaskiya bazata saɓu ba na gaji lkc yayi da matata zat dawo ƙarƙashin iko na" sam mummy bata fahimci sai tace masa
"auta wake juya maka badiar taka" mummy ta tambaya, ɓata rai yayi sam baya son ambatan sunan asmau don gani yake yi kamar ajinsa zai zuba amma ganin mummy sam bata ɗauko maganar tashin ba ya sa shi ambatan ta
"ba badia nake nufi" ya faɗa ƙasa ƙasa, dariya ne ya so ƙwace wa mummy amma sai ta dake lallai tarkon data ɗana ya kama ɗan natan ke nan
Amma sai ta nuna sam bata gane me yake nufi ba
"auta a gidan nan kana da wata mata ne bayan badia, only ɗin taka" ɓata rai taga yayi sannan ya ƙara sunkuyar da kansa tare da yin ƙasa ƙasa da muryar sa kamar wanda yake jin kunyar furta kalmar sannan yace
"ɗayar matar tawa mana, mummy kar ki ce kin manta ta mana" shiru mummyn ta sake yi kamar me tunani dariya ce take son suɓuce mata amma kuma tafi son sai ya faɗi sunan ta da kanshi
"in banda abin auta ai da ka faɗa min in ka kuma ganin wata kana son ƙarawa, ai dama na san nan gaba dole ka nemi ƙari tunda baka samu mace ba har yanzu"
"mummy wai asmaun ce kika manta" ya faɗa a fusace dariya ce ta suɓuce wa mummy
"dama ina son jin sunan ta daga bakin ka yanzu me ya haɗa ku da asmaun kazo kuma kana complain"
"mummy yarinyar nan ko kaɗan bata san matsayin miji ba" nan ya labarta mata abinda ya haɗa su da asmaun sannan ya ɗaura da cewar
"gaskiya hakuri kawai nake yi ni matata bata da lkcn da zata kula ni kullum sai dai ta dinga girkawa wasu abinci amma ni sam bata da lkc na gaskiya baza ta saɓu ba nagaji" yai ta mita
Mummyn sakin baki tayi tana kallon ikon Allah sannan a ranta tana godewa Allah daya dawo da hankalin sabit kan asmau, don kuwa ko ba komai asmau sai tafi badia iya kula da sabit sosai
Bata da wani buri daya wuce ace ta samu me kular mata da ɗan autan ta sabit, badia ba me son aiki bace don haka gaba kaɗan sabit zai rasa macen da zata kula da shi
Amma asmau daga ganin ta zata juri wahala kuma zata iya ɗawainiya da wahalar sabit kuma ta asmau sabit zai samu zuria sosai tunda tasan shi da son ƴaƴa
Amma badia ba lallai bane ta haifawa sabit ƴaƴa dayawa, juyowa tayi ta kalle shi sannan tace
"auta yanzu me kake so"
"ni dai kawai so nake yi dum lkcn da na kira ta tai min wani aiki bana son ta kuma cewa wai zatai aiki wani ko kuma tana wani ya sata aiki nafi son ina bata umarni kawai ta ɗauka"
Gyaɗa kai mummy tayi sannan ta jinjina maganar sa
"in shaa Allah zan mata faɗa akan ta dinga bin umarnin ka a matsayin ka na mijin ta" daga nan ta shiga lallaɓa shi tare da kwantar masa da hankalin sa akan babu wanda ya isa ya raba shi da *ASMA'UN SABIT* ɗin sa
Kanshi me ya fasu kamar an masa kyauta sai da ta kwantar masa da hankalin sa sannan yai mata sallama ya kama hanyar sa mummy bin bayan sa tayi da kallo, lallai sabit daga gani ka fara dawowa hanya madaidaiciya ka fara gane cewa ```ba kowacce ƙwarya me kyau ce take da daɗin shan fura ba```
********************
Ko da muka dawo kasuwa sai mummy ta kira ni akan tana son ganina sam ban kawo komai ba don haka na shirya na tafi pary ɗin nata
Ina shiga na zauna sannan ta fara min faɗa akan halin ko in kula da nake nunawa mijina ```wai sabit```😏
Faɗa ta dinga min wai in dinga kula da buƙatin sa, menene da menene ni jin maganar tata ma nake yi kamar soki burutsu tunda dai ba ɗauka zanyi ba ai ni da sabit sai dai daga nesa amma nai masa nisa sai dai wata ba ni ma'un ba
Ta gama saki burutsun ta tsap ban tanka mata ba, sai da ta gama sannan ta sallame ni yadda na tashi na kakkaɗe rigata haka zancen nata ya zube daga kunnuwa na sukai ƙasa banji ba balle ince zan aiki da su
Komawa nayi hidimar gabana na tattara lamarin sa na watsa a kwandon shara, tsakanina da shi ya kira kitchen ya faɗi abinda yake so in faɗa masa
Wani sabon salo daya ɗauko shine kullum in an gaya masa menu na gidan sai ya canza kuma abu me wahala yake ɗauko wa sam bana jin komai haka zan dafa masa
Sai kuma ya canza salo wai innai girki in dinga kai masa nan ma nace bansan zance ba sai da mummy tai min magana sannan na fara kaiwa part ɗin nasaa
Amma bana tashi kawai sai inna ga matar sa na nan ta yadda ba yadda za ai yai min magana ko ya kawo min wani renin sense
Amma duk da haka ban tsira ba, idan na kai masa yai ta sani aiki kenan yi kaza gyara kaza, zuba min abinci kwashe kaza
Haka dai amma ban taɓa tunanin sakar masa fuska ba don dana shiga ɓangaren nasa idan na cukune fuskar nan tawa har na fito be isa ya ga sakin fuskar tawa ba balle yace ze kawo min wani wargi
Har yanzu be isa in kula shi be kai matsayin da zan tanka masa ba, duk da dai idan na shiga ɓangaren nasun yai ta surutu kenan ko kuma yai ta tambayar
Da me dame nayi abincin wai saboda badia ta koya, in na daddage na tsuke wannan fuskar tawa sai dai yayi tambayar sa ya gama amma ƙala bazan ce masa ba
Sai dai in ya gaji ko badia tai masa magana sannan zai dena amma gobe bazai daddara sai ya sake, sam wannan abun da yake yi be sani tanka masa balle inji ina sha'awar mu'amala da shi ni asmau sai namiji wanda ya san darajar mace ba muna maza ba
[4/26, 11:44 PM] Oum Haidar: *******************
Na ci gaba da kula da tattalin kaina ina yi wa ƙanin anty fannah tanadi,
Watan azimi ne ya kama don haka anty fannah in ta zo kitchen tun safe bata barin shi sai mun gama abincin iftar, in itace da girki muna gama wa sai ta tafi in kuwa ba ita baca sai mu sha ruwan mu tare
A lkcn na gano ashe macece me ibada sosai karatun qur'anin nan da azkar baya wuce ta safe da yamma, ganin haka ya sa nima na fara mata maganar akan ta koya min in ƙara sani sosai akan addini na tunda de Allah be sa na je islamiyya ba sosai ba
Karatu sosai muka fara da anty fannah ba ɓangaren da bama taɓowa, wasu karatun inji kunya wasu kuma ba komai, kamar karatun ɓangardn tsarki 🙈
Ba a karatun ilimin addini ba har da na ilimin aure, wallahi wani lkcn idan tana wani maganar sai inji kamar in nutse a ƙasa saboda tsabar kunya amma ita ko a jikin ta kamar ba itace take faɗa ba, lallai sai a lkcn nasan cewar ni babbar jahila ce wacce ba abinda ta iya sai girki
Lallai girki ba shine kaɗai abinda zai jawo hankalin miji zuwa ga matar sa ba har yaji bazai iya rayuwa sai da ita akwai dabaru dayawa ko in kissa
Kamar su kissar iya magana ```wata bata da wani salo na iya yi miji magana yadda take yi wa ƙawarta haka take yi wa aikinta shi ma miji haka, ba wani ɗan laƙwasa harshe ko yango ko kararraiya```
Sai kissar iya zance
```wasu matan sam basu iya tauna magana kafin su faɗe ta ba haka suke suyi ta zuba kamar ƴaƴan kanya marasa daɗi``` inji mmn farency 😜
Sai kissar iya kwalliya,kissar tafiya, yanga, rangwaɗa, shagwaɓa da kuma last but not d list wacce muke ganin kamar tafi kowacce itace iya kwanciyar aure, ```ƴammata ku gafarce, amma maganar gaskiya ce, duk macen da ta iya waɗannan kissosin sai dai wani ba mijinta ba```
da kuma sauran su duk waɗannan abubuwan idan muka riƙe su gam sannan muka haɗa da roƙon Allah day in day out in shaa Allah sai dai muji anayi rigimar aure a maƙota ba dai gidajen mu _Allah ka bamu dacewa da ƙarshe me kyau_
Ilimi sosai take koya min kuma nake naɗewa ina ɗauka ina haddace wa burina kawai Allah ya kaimu lkcn da zan kashe wannan auren nawa na bautaswa inyi auren soyayya 😍
👩🏽🍳 *menu of d day*👩🏽🍳
*tuwon semovita miyar egusi and kunun tsamiya*
*tuwon semo*
```ingredients```
-semo
-flour
-butter
*ki zuba ruwa a tukunya sai ki rufe, idan ya tafasa sai ki zuba wani ruwan daban a bowl sai a dinga zuba semo ɗin ana juyawa har yayi kauri
2) daga nan sai a ɗauki talge a talga tafasash shen ruwan, idan an talga sai a saya murfin sannan a rage masa wuta talgen ya dahu a hankali
3) idan talgen ya dahu sai ki haɗa flour da semo, kamar flour ya fi semon yawa sai a tuƙa bayan yayi ta sai a saka butter a ƙara tuƙawa sannan a rufe a rage wuta ya turara idan ya turaru sai a kwashe a leda
*miyar egusi*
```ingredients```
-kayan miya
-man ja
-egusi
-egg
-alayyahu
-maggi
-nama
-crayfish
-kifi
Method
1) ki saka naman ki a tukunya ki zuba maggi, albasa da tafarnuwa sannan ki rufe, idan tafasa sai ki zuba kayan miyar ki ki barshi ya dahu
2) a wata tukunyar daban kuma sai ki zuba man jan da zakiyi miyar da shi idan yayi zafi, sai ki wanke kifinki ki zuba a mai ki soya sannan idan ya soyu sa a tsane
3) daga gefe kuma sai ki kwaɓa egusi ɗin ki da ruwa sai ki zuba a man jan sannan sai ki rage masa wuta yai ta dahuwa a hankali, idan ruwan ya ɗan tsotse sai ki fasa kwan ki ki kaɗa shi sannan sai ki zuba shi akan egusin ki bar shi ya ɗan dahu sannan ki juya idan kina son egusin ki ya dundunƙule kar ki juya shi sosai
4) sai ki juye egusin a miyar sannan ki zuba crayfish, ki ƙara maggi da albasa sannan ki rufe, in ruwan yai kaɗan sai ki ƙara ruwan
5) idan miyar ta yi dai dai sai ki zuba alayyahun ki wanda kika yanka kika wanke sai ki zuba kifin ki ki rage wutar sannan ki rufe
Minti ɗaya sai ki sauke
*kunun tsamiya*
*ingredients*
- ƙulun kunu
-tsamiya
-lemun tsami
-sugar
```method```
1) ki zuba ruwa sannan ki saka tsamiyar ki, idan ruwan ya tafasa sai ki tace sannan ki ƙara mayar da ruwan don ya ƙara tafasa
2) ki zuba ƙullin kunun sannan idan yayi kauri sai ki ɗan ƙara masa ruwa daga nan sai ki zuba a cikin ruwan zafi ki rage, idan yayi kauri sai a sauke
3) sai ki kuma ɗiban ƙullin ki sakar masa ruwa sannan ki ɗauraye kunun sannan ki ɗan matsa lemun tsami sannan ki juye a flask
👩🏽🍳 *BON APPETIT*👩🏽🍳
*ASMA'UN SABIT*
[10:52PM, 5/2/2018] +234 806 399 9164: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
P⃗a⃗g⃗e⃗ 15🌹
Yin karatu a wajen malama ta anty fannah ya sani ƙara wayewa da yanayin zamantakewa ta ɗan adam, kasancewar garden ɗin gidan a bayan part ɗin su ga sanyi ga iska ya sa kusan kullum a can muke karatu
Idan nagama aiki sai in je part ɗin su sai mu koma garden ɗin mu zauna muyi ta karatun mu ko tai ta min fatawowi da dai sauran su
Har akai sallah lfy muna karatun mu kuma na ɗau alwashin ko bayan sallah zan ci gaba da biɗar ilimina don ilimi shine hasken rayuwa, in babu shi mutum zai kasance kamar a duhu yake Allah dai yasa mu wanye ƙalau kuma ya bamu ilimi me amfani da mu da ƴaƴan mu amin summa amin
Rannan muna garden ɗin sai ga isma'il ya zo
"ina ta neman ki a ciki ashe kina nan" ya ƙaraso yana faɗawa anty fannah, gaishe shi nayi sannan nayi niyyar tashi don in bar su su shana
Hana ni yayi tace shima aiki ne ya kawo shi in zauna muyi karatun mu, komawa nayi na zauna muka ci gaba, kasancewar doguwar riga ce ƙirar dubai a jikina me belt wacce ta saka belt ɗin na ɗaure jikina da shi sai ɗan kwalinta da nayi rolling kaina da shi
Ya sa sam ban sake ba ni da na saba yawo a cikin hijab kamar bukka 🤣, karatun mu muka ci gaba amma sam a nutse nake
Sallamar gogan na badia na ji a bayana inda duk muna amsa ni kuma na haɗe raina don bana son wannan shishshige min daya ke yi
Ƙarasowa yayi ya zauna dai dai kusa da ni har jikin mu yana ɗan gogar juna wanda hakan ne ya sa ni kuma na ɗan kuma matsawa ko ya sake amma bada ni ba, basarwa yayi kamar be san me yi ba sannan yace
"ku ashe anan kuka yini kuna shan iska me daɗi shine sam ba a san a gayyaci mutum ba ko" ya ƙarashe zancen sa da sigar tambaya yana kallo na
Iskar data kwaso shi ma ban shaƙa ba balle in tanka masa littafi na na ɗauko na rufe fuska ta da shi kamar ina karatu
Anty fannah ce ta tanka masa
"yo ai ba a damu da ba, balle a san a ina muke yini" na san martani ta mai da masa murmushi yayi sannan yace
"ai matsalar taku ce ba kwa fara'a ga shegiyar shariya ko an muku magana kun san da ku ake amma sai ku share mutum kuyi kamar baku jiba"
"wannan shine cikar mace me aji" inji anty fannah
Su ka ci gaba da maidawa juna martani wannan ya faɗa wannan ya mayar dana ga abin nasu ba na ƙare bane sai kawai na miƙe na sannan nace
"anty fannah naga alamar kin samu abokin hira bari ni in wuce maci gaba da karatun nan gaba" ina gama faɗar haka nai gaba abina
Nayi nisa naji yana ƙwala min kira ban tanka masa ba haka zalika ban tsaya ba, sai kuwa gashi ya sha gaba na
"baki ji ina kiran ki bane wai asmau me yasa kike da taurin kai ne"
"ai ban ɗauka da ni kake ba, na ɗauka badia kake son kira ka manta kace asmau" murmushi yayi wanda yai masa kyau kamar kar ya dena
"ashe kice abin naki kishi ne, to in banda abinki ai badia alba sa ar ki bace, yarinya kyakkyawa son kowa ƙin wanda ya rasa fara me kyan ɗaukar hankali"
Haushi ne da takaici suka cika ni tsayawa kulashin da nayi gashi nan ya ɗige da yaɓa min magana
Raɓa wa nayi ta gefen sa na wuce
"sai kace gurin ta ni kuma ka ƙyale ni Allah zai kawi min wanda zai soni ba don abinda nake da shi ba"
Wannan kalmar tai mutuƙar ɓata masa wanda har ya sa shi shan gaba na tare da damkar hannun da ƙarfi wanda hakan ya sani wani radaɗi a hannun daga dukkan alamu matse mun hannun yayi
"saboda baki da hankali da auren nawa a kanki kike maganar samun wani, to wallahi karki ga ina ɗaga miki ƙafa ina nan a sabit ɗin da kika sanni in kika sake na kuma jin wannan kalmar daga bakin ki sai ki yaba wa aya zaƙin ta"
Wulli yayi da ni inda na faɗi ƙasa har da gurje gwiwar ƙafa ta, kuka na saki dama me hali yana fasa halin sa ne na faɗa, kuma wallahi abinda kake nema a wajen nawa baza ka samu ba sai dai wata
Kuma neman rabuwa da kai ban ma fara ba sai lkcn da na tara iya kuɗin da nake so zaka san cewar shayi ruwan na faɗa a raina tare da miƙewa ina karkaɗe kayan jikina mugu kawai
********************
Tun daga lkcn na shiga wasn ɓuya da shi don duk abinda na san zai haɗa ni da sabit bana ma tunkarar sa shima a nashi ɓangaren naga alamun haka
Don yawan kiran da ya ke min da yanzu ya daina sam kamar ma be fara ba,
rannan da rana na gama lunch na kaiwa mummy na tarar da ita tana ta mita, zama nayi sannan nace
"mummy lfy kuwa"
"ina fa lfy ni da wannan har iskar kishiyar taki wai tayi tafiya amma sai da ta sauka sannan mijinta ya sani, shi ma da yake be san ciwon kansa ba ko a jikin sa" dariya ce ta so kubce min amma sai na dake
Kaɗan ya gani be gama ganin komai ba ba dai zalinci ya riƙe ba ai ba abinda ya soma gani ma,
"mummy garin ƙaƙa akai haka" na tambaye ta da alamar damuwa a fuska ta
"ai da yake kin san ta riga ta shanye shi tas baya ganin laifin ta, kome tayi sai yace ai duk abinda take yi tana sane, be san mace ba a sakar mata, kai wannan yaron wai sai yaushe ze farka ne ya fahinci abinda nake nuna masa" ta faɗa tana dafe kanta alamar abun yana damun ta
" ke ma hadda ke sam baki san amfanin mace ga mijinta ba, kin saki mijinki wata sai juya miki shi take sam kin kasa jawo hankalin sa zuwa gare ki, gashi dai kinje kin sha gyara amma sam bashi da amfani tunda duk da gyaran naki kin kasa jawo hankalin mijinki gare ki, kullum sai dai a ganki a ɓangaren wannan yaro (isma'il) kina bibiyar fannah amma ke mijinki ko a jikin ki
Haka kika ga fannah ta nayi wa nata mijin, wallahi har da laifin" faɗa ta shiga min tare da ƙarawa wai duk laifi na ne na kasa shishshigewa sabit balle har in samu fada a wajen sa ya jani jikin sa har ya banbance tsakanina da badia
Kallon baiwar Allah nan kawai na tsaya yi lallai so sone amma son kai ya fi, wato ma lefi nane, ni bata san ko a ƙafa a ɗaura min wannan koɗaɗɗan ɗan natan ba sai na yanke na gudu balle har a kai ga faranta masa ko shishshige masa Allah ya kyauta min Allah ya tsare ni
Sai da ta gama faɗan ta sannan ta sallemi tare da ja min kunne akan in fara jawo hankalin sabit zuwa gare ni,
Binta kawai nayi da to amma kuma nace hmmm wayaga wallahi badai ni asmaun ba sai dai wata ai ni da sabit hayhata hayhata
Na koma ɗakina ina tunanin abinda mummy take son nayi wa sabit wato da yake abin son kai ne, ni da nake mace nice za a ce inja hankalin sa me makon amatsayin sa na namiji ace ya fara ɗaukar action ni kuma a matsayina na mace a bani damar duba wa ko zan iya manage da shi amma sam abin ba haka yake ba nice ma zan cusa kaina lallai mummyn nan har yanzu baki san wace asmau ba
Da yamma ina cikin yin dinner na kusa kammalawa ma sai naji call na intercom ɗin kitchen ɗin yana ringing kasancewar ba kowa ya sani zuwa ɗauka,
"hello" naji ance ko bacci nake yi nasan muryar ɗan renin hankalin nan amma sai na nuna ban sani ba
"hello waye" na amsa
"mijinki ne" na ji ya bada da amsa, murmushin mugunta nayi sannan na mai da masa martani bayan na maƙe muryata na shake ta sannan na gyara ta
"kana nan ƙalau ya gidan da komai da komai wallahi ina kewar ka sosai" ina jin ɗan murmushin daya saki sannan yace min
"da gaske"
"zan maka ƙarya ne kasan ni kasan zuciyata kasan banda wani sai ka, lkc kawai muke jira ya kasance mu kasance waje ɗaya har abada"
Daɗine ya lulluɓe shi kamar me, ni kuwa da yake nasan abinda nake shukawa ya sani ƙara sakin baki sai faɗa masa kalaman soyayya nake yi shi kuma yana biye min sai can dana ga ya shiga sosai sai nace masa
"ya maidugurin kuwa, Allah dai ya san ƴam matan can basa kalle min kai dan sunga bana kusa da kai" shiru yayi na ɗan wani lkc yai jim
"ABDUL baka jina ne" na kuma maimaitawa
"uban waye abdul" na ji ya faɗa, sai da na ɗauke phone ɗin daga kunne na na ƙyalƙyala dariya ta sannan na mai da ta na kuma cewa
"ba abdul ɗina bane na maiduguri ba, don Allah waye ya kira ni sannan yace min matar sa" wani ƙasurgumin zagi da luluƙo ya antayo min ni da abdul ɗin ya sani cire phone ɗin daga kunne na na kuma ƙyaƙyacewa da dariya
"Abinda kike yi Kenan dama da auren ki to yau Allah ya tona miki asiri kuma wallahi zaki san baki da wayo" sai da ya gama bala'in sa sannan ya kashe wayar
Dariya na ci gaba da yi gobe ma ka kuma kirana, ni abin ma dariga ya bani wai mijin ki ne, ko ta ina ya zama mijin nawan mijin suna dai girki na na cigaba da yi ina yi ina maimaita conversation ɗin mu ina dariya ni kaɗai lallai yau na kunna sabit
********************
Takaicine ya ishi sabit har ya rasa yadda zai yi, tun yana kwance ya tashi ya zauna ya kuma kwanciya amma duk da haka ya rasa mafita, ya ze yi da wannan ƴar iskar yarinyar
Wai da auren shi akanta amma take kula wani ƙato, har da cewa lkc kawai take jira su kasance tare, kenan da take nufin kashe auren da gaske take
Gaskiya da sake ya za ayi ma in bar ta ta tafi, lallai ma dole ne in samu mafita, mummy ce kawai ta faɗo masa a rai, lallai mummy ce kawai zata iya kawo ƙarshen wannan lamarin
Miƙewa yayi ya nufi ɓangaren mummy sam be nuna mata komai ba kawai sai yace mata
"mummy kinga badia bata nan part ɗin nawa ba mace don haka me zai hana ki saka waccen yarinyar ta koma tunda akwai spare ɗaki a ƙasa sai ta zauna anan"
Daɗi ne sosai ya kama mummy har tana jin daɗi ita a tunanin ta asmau ce ta ɗau shawarar ta ta fara aikin da ta saka ta
"to shike nan auta ai dama tun farko kai kaso hakan kana da mata har biyu amma ki ɗige a guda gudar ma mara quality" ɓata ransa yayi shi sam har yanzu be ga aibin badia ba da mummy kullum take cikin kushe ta
Ko ma dai menene yanzu ba lkcn maganar badia a bane yanzu ta ƴar iskar yarinyar can ake yi
Mummy shawara ta ci gaba da bashi akan yadda zai kula da asmau da kuma yadda asmaun zatai masa rana da kuma yadda zata kula shi fiye da badiar
Jinta kawai yake yi amma yanzu ba lkcn wannan bane yanzu burin sa kawai yaga asmau a part ɗinsa ya koya mata hankali
******************
Sai da na gama dinner tsab sannan na zuba aka raba aka kai wa kowa nashi sannan na ɗauki na mummy domin kai mata
Ina shiga part ɗin ta tana zaune tana kallo nai sallama na jiye mata na tashi zan fita kenan sai ta kira ni
"asmau idan kin gama abinda kike yi ki tattara kayanki a yau ki koma part ɗin mijin ki da zama zaman naki a BQ ya ƙare, su ma ragowar ƴan uwan nakin na gaya musu daga yau koya ya dinga girkin sa kin dena mijin ki yace ki koma"
Tsayawa nayi na saki baki kamar wata wawiya ina kallon ta me wannan yake nufi kenan in koma ɓangaren sabit wulaƙanci ke nan sunfari sunfari zan dinga kwasa gaskiya da sake bazan iya ba
"mummy amma me yasa zan koma kin............" bata bari na ƙarasa ba ta hau yi min faɗa kamar zata ari baki, wai dama ni shegen taurin kai gare ni,
Wata macen ce mijinta ya gayyace ta ta koma ɓangaren ta a matsayin matar sa kamar yadda kowacce mace take da matsayi amma ta ƙi kina nufin kin ta zama kenan a matsayin cook ai dama wataran dolr ne ya nemi ki koma ki karɓi girki
Faɗa ta dinga min daga nan kuma ta hau faɗa min wai yadda mallaki zuciyar sabit cikin ruwan sanyi, sannan da yadda zan dinga masa biyayya tare da yin duk abinda ya sani
Duk wani faɗan ta ya ƙare ne akan yadda zan farantawa ɗan ta sabit sam bata damu da halin da zan shiga ba ƙiri ƙiri na nuna mata bana ƙaunar komawa amma hakana sam be gamsar da ita ba itadai in koma in farantawa ɗanta
Miƙewa nayi jikina a sanyaye na kama hanyar fita, sai naji mummy tana kiran me aikin ta wai ta raka ni ta taya ni haɗa kayana sannan ta raka ni ɗakina
"ai ba a bar amarya ta tare ita kaɗai ba ba ɗan rakiya"
Wannan kalmar ta amarya tafi komai ƙona min rai lallai ma waya ga amarya
Tas matar nan tasa na haɗe kayana na kwashe su ta taimaka min kwasar su sai part ɗin sabit abin haushi ma yana zaune a falon yana kallo
Wani takaici ne ya ziyarce ni danaga mun shigo ya wani taso har da karɓar jakar hannuna na tare da yi mana welcome, ita kuma babar har wani washe baki take tana cewa
"ga amarya nan na kawo maka ita Allah ya bada zaman lfy ya kawo ƙazantar ɗaki" nuna mana ɗakin yayi
"ga ɗakin ta can sai ta shiga da kayan natan" tare muka shi da babar ni ko ƙala bance masa sai da taga na shiga na ajiye kayan nawa sannan tai min sai da safe ta fice
Kayana na fara gyarawa inda duk na jera su a kwabar da nagani a ɗakin sannan sai kayan kwalliyata waɗanda na jera su a kan dreesing mirrow
Sai dana ga na gama gyaran sannan na shiga toilet nai wanka na ɗauro alwala, sallah na gabatar ta ishsha sannan na kwanta
Ina cikin addua naji an buɗe ƙofar ɗakin, gabana ne ya yanke ya faɗi, ko da dai fitilar ɗakin a kashe take amma ai nasan sabit ne
Da sauri na miƙe na nemi wani zani da ke kusa da don in ɗaura, ban kai ga ɗauka ba naga hasken pitilar ɗakin ta kauraye ɗakin ya ɗau haske
Ga wata ƴar mitsitsiyar rigar bacci da ke jiki na, saurin lalubar zanin nayi sannan ɓata rai tare da ce masa
"me ya kawo ka"
"zuwa nayi in karɓi haƙƙin ta ko ta ƙarfi ko ta tsiya na ga alamar innai sanya sai a kai wa wani abanza a wofi" gaba na ne ya yanke ya faɗi amma sai na dake don kar yaga ma tsorata ya rena min wayo
Matsowa ya fara yi kusa dani gabana yana ƙara faɗuwa
"abinda kike burin kaiwa abdul ne nake son ruguza wa, tunda yanzu halak ɗina ne me zai hana in mori kayana tun kafin a kai wa wani banza, gwanda in karɓi kayana da hujja" fara matsawa nayi baya kashe fitilar yayi sai ɗakin ya ɗau duhu wanda hakan yasa na kasa gane a ina yake,
Haƙuri na fara bashi na don Allah ya ƙyale ni wallahi wasa nake masa, jinshi nayi kusa da ni wannan ya ƙara firgita ni
Ganin bashi da niyyar ƙyale ni yasa ni ma na fara kokawa da shi wallahi bazan bari yayi abinda yaga dama dani ba ai nia ina da ƙarfi
********************
Wayyo Allah sabit ya cuce ya raba ni da budurcina ba lallami ba daɗin baki ba komai sai azaba da nuna ƙarfi in short zan iya cewa raping ɗina ma yayi
Kuma abun takaici yana gamawa yayi wulli da ni sannan ya fice bayan rashin mutuncin da ɗiban albarka daya min, ina kwance nai rigingine ina ta kuka ba abinda nake ji sai tsabar raɗaɗi
Wayyo ni asmau wannan wace irin rayuwa ce mijina ya same ni budurwa sannan yai min wannan aika aikar amma sam a lamarin sa ba tausayawa wayyo sai yaushe wai zan samu me sona ne na gaskiya gashi abinda nake ta tattalin sa ina alfahari da shi yanzu babu kuma a wulaƙance ya ba wani daraja ko nuna mutunci ko wani abu gaskiya sabit ya gama cutata har abada
👩🏽🍳 *menu of d day* 👩🏽🍳
*fatan doya, meat balls and mixed fruit juice*
*fatan doya*
```ingredients```
-doya
-wake
-attaruhu
-albasa
-kifi
-salt
-sugar
-mai
*method*
1) ki zuba mai a tukunya da albasa idan yayi zafi sai ki zuba jajjagen ki na attaruhu da albasa
2) idan ya sayu sai ki zuba ruwa da maggi da salt daga nan sai ki bar shi ya tafasa idan ya tafasa sai ki wanke waken ki ki zuba sannan ki rufe ki barshi ya dahu
3) ki fere doyar ki sannan, sai kin tabbatar da waken ya dahu sannan sai ki zuba doyar ki zuba sugar ki ƙara albasa sannan ki dagargaza soyayyan kifi a ciki ki rufe har dahu idan ya ɗauko dahuwa a rage masa wuta
*Meat balls*
```ingredients```
-nama
-kwai
-garin bushashen burodi
-maggi
-albasa
-attaruhu
-mai
*method*
1) ki dafa naman ki da albasa maggi, tafarnuwa idan ya dahu sai ki sauke sannan sai ki daka
2) bayan ya daku sai ki fasa masa kwai ɗaya sannan sai ki zuba daddakekken attaruhu da albasa da maggi in yana buƙata ki zuba garin burodi ki ɗaure shi sannan sai ki fara dunƙule wa kamar ƙwallo
3) ki fasa ƙwai a bowl daban sannan ki kaɗa shi, ki ɗora mai a wuta idan yayi zafi sai a ɗauko ƙwallon naman nan a saka shi a cikin garin burodi a jujjuya sannan a tsoma shi a kwai daga nan sai kasko a soya idan yayi brown sai a sauke
*fruit salad*
```ingredients```
Seasonal fruits
*method*
1) a samu duk fruit ɗin da kike son amfani da shi amma wanda yake bozo ki wanke ki fere sannan a yanka shi sannan a markaɗa sai a tace a zuba sugar a saka a ƙanƙara a sha
👩🏽🍳 *BON APPETIT*👩🏽🍳
*ASMA'UN SABIT*
[10:54PM, 5/2/2018] +234 806 399 9164: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻
P⃗a⃗g⃗e⃗ 17🌹
Sai dana gama wanka na tsab na fito ɗakina na ɗauki jakata na fara haɗa kayana ina hawaye yau dole ne in barwa sabit gidan nan
Ban dan ko nawa ne kuɗi na a wajen mummy ba amma dole yau zan bar gidan nan ko da kuwa tace baza ta bani kuɗina ba na tafi inje gidan abincin hjy munnira ina mata aiki inna samu kuɗin in koma garin mu amma gaskiya wulaƙanci yayi yawa sosai na faɗa ina hawaye
Ƙarar buɗe ƙofar ɗakin nawa naji ko ban kalli ƙofar ba nasan cewar sabit ne don kuwa ƙamshi turaren sa kawai nake ji sam ban kalli inda yake ba na ci gaba da abinda nakeyi
"ke meye wannan kike yin haka nan"
"tafiya zan yi ai ko aure ma sai da ra'ayi ake zama to na bincika har ƙasan zuciyata banni da ra'ayin zama da kai bana ƙaunar ban taɓa son ka ba kamar yadda kake ikirarin hakan to meye dalilin da zai sa mu ci gaba da zama bayan bama ƙaunar juna"
Ina magana hawaye na zuba daga ido na sakin baki yayi yana kallona daga dukkan alamu be ɗauka zan masa haka ba
"da izinin wa zaki fita ko ita fannar da zakije wajen ta barin ki zama zatayi"
"ban ma tafi ba kenan in dai a waken anty fannah zan zauna, garin mu zan tafi aure tsakanina da kai babu shi ka bani takarda ta an gama show ɗin daga yanzu"
"daɗin abindai sakin a hannuna yake kuma bazan sake ki ba har sai lkcn da na ga dama, wai ke asmau me kike so ne meye bana baki saboda tsabar rashin godiyar Allah da rashin gode masa shine zaki tafi ko ki tafin mu gani in hakan ne zai sani ƙara miki matsayin"
Ficewa yayi daga ɗakin ni kuma naci gaba da haɗa kayana, sai da na gama haɗa komai na sannan na ɗauko jaka ta na fito
Ko kaɗan banji wani abu ba wai zqn bar gidan duk da dai bam san wace irin rayuwa zanyi a azoren ba amma ni a ganina gwanda in tafi da wannan cin zarafin da sabit yake min
A garƙame na tarar da ƙofar fita daga falon, an rufe da mukulli daga waje jijjiga ƙofar nq fara yi tare da dukan ta ko ta buɗe duk da dai nasan a banza nake amma kuma ance baka fidda rai da tsammani
Sai da na gaji da dukan ƙofar sannan na sulale ƙasa na zauna ina kuka na, alamar buɗe ƙofar naji nasan sabit ne zai shigo muciya na shiga kitchen na ɗauko da niyyar yana buɗewa in muƙa masa sannan in tsere
Anty fannah ce ta shigo ganina da muciya a hannu ya sata ɓata rai tare da ƙwacewa ta yar sannan ta ja hannuna zuwa ɗakin na
"me ye haka sai kace wata matar ƙauye, kamar wacce bata da ilimi ina karatun da nake koya miki kar dai kice ba ɗauka kike ba kawai zuba ta nake yi kamar ƴaƴan kanya"
Bayan ta sabit ne ya shigo, faɗa ta shiga min wai sabit ya kai mata ƙarata akan ina mishi rashin kunya, sakin baki nayi ina kallon mutumin nan wanda yake ta danne danne sa a wayar sa kamar baya wurin
"Wallahi anty ba haka bane ƙar........" ban ƙarasa ba naji ta toshe min baki
"kar ma ki ƙaryata mijinki da ido na na gani kin ɗauko muciya zaki doke masa kai, in banda shima sabit ɗin me haƙurine wane namijin ne zai yadda da irin wannan cin kashin"
Fashe mata nayi da kuka ina rants rantse na wanda sam kamar ma bata yadda ba don bata nuna alamar yadda ba
Sabit da ke gefe wanda tunda aka fara bece komai ba sai yanzu
"anty ni fa bana kawo ki bane don kiyi mata faɗa ba kawai so nake yi ki ja mata kunne akan abinda take yi be dace ba"
"yi haƙuri sabit zan mata faɗa tashi ka tafiyar ka uzurinka" miƙewa yayi tare da zira hannu a aljihu sa sannan ya fice, bin bayan shi nayi da harara
"au ko a gaban nawa bazaki bari yi masa rashin kunyar ba, haba asmau wallahi duk abinda kike yi Allah dai yana kallon ki" ƙara fashe mata nayi da kuka nan na hau labarta mata duk zaman da muke yi da shi bata katse ni ba sannan sam bata nuna alamar tausayawa ba ko wani abu
Sai da nagama tsab sannan tace min in share hawaye na, tas na goge fuskata ta, na nutsa sannan ta kalle ni tace min
"Asma'u shawara ɗaya zan baki ko ki ƙi ko ki sa amma ɗaya ce ba ƙari, duk wannan abun da kika ga sabit yana yi har yanzu be san meye so bane kawai dai yana bin sahun ƙyal ƙyal banza ne
In kina son sanin ainihin waye sabit me sabit yake so kamata yayi ki zauna ki karance shi ki karanci aban da yake so kafin ki fara judging ɗin sa
Har ga Allah ina sonki da sabit kuma duk wani abunda nasan zai ƙara ku
kusanta da shi shi nake miki amma na lura sam ke ba haka kike so ba kin fison tafiya ko" ta tambaya da alamar tambaya
Gyaɗa mata kai nayi alamar ni na fison tafiyar
"to shike nan duk yadda kike so hakan za ai miki yanzu abinda da so da ke shine ki kwantar da hankali sosai akan sabit duk abinda yake so kiyi masa sai a lkcn da ya saba da ke da duk wani abu naki sai ki tsiri rama abinda yai miki tas ki rama kar ki yadda kice zaki raga masa daga lkcn idan yaga abin ya mishi yawa sai kiga ya sake ki salin alin ko ya kika ce"
Tsayawa nayi ina tunani shin anya kuwa wannan mafita ce ko kuma wani sabon salon ƙara jawo sabit gare ni ne, ganin ban amsa ba ya sa ta miƙewa
"to bari in tafi tunda na baki shawara amma naga kamar bata miki ba"
Hannun ta na kamo sannan nace mata
"ba haka bane kawai dai ni bana son abinda zai sake haɗa ni ne da shi"
"to shike nan duk abinda yai miki ya tashi a banza kenan, ai in baki koyi rama abinda ɗa namiji yai miki ba daga farko to ko kin ƙara auren ma ƙila abinda zaki tarar kenan amma kin ga inkin saba ba abinda zai zame miki sabo"
Shiru nayi ina tunani to wai ramuwar dole ce na faɗa a zuciyata ni fa sam abinda ya danganci sabit nr bana so
"kinga in shawara ta bata yi ba na yi gaba sai kine mi me baki shawara nan gaba" ganin cewar in ta tafi shikenan a ina zan samu wanda zai haɗa ni da wanda yake son irin na
Don haka dai na riƙe mata hannu tare da cewa
"na haƙura amma wallahi saboda ke" shafamin gefen fuska ta tayi sannan tace
"yauwa ƴar albarka" zama tayi ta dinga bani saƙwanni ta yadda zan kama sabit jinta kawai nake yi amma abu guda banjin zan iya amma kasancewar bana son tace na ƙi jin maganar ta yasa kawai sai gyaɗa mata kai nake yi kamar ina ji ta gama zancen ta sannan tai min sallama ta fice nice har da rakata bakin ƙofa sannan mukai sallama
********************
Tun daga lckn na koma bana yi wa sabit musu duk abinda yake so ina mishi amma fa babu batun sakin jiki kadaran de kadahan
Rannan da safe yana zaune akan dining table yana break fast sai ga call, yadda naga naga ya ɓata fuskar sa sai na ɗauka ko wani wanda yake damun sa ne amma ga mamaki na sai naji yace
"only ya dubai" ban san me tace masa nadai ji ya amsa mata da
"only ki yi zamanki ku gama siyayyar ku a nitse ni sam ba a takure nake ba am taking really good care of myself don haka kar ki damu"
Shiru yayi inda ta ci gaba da mai masa da martani
"only ba komai ko wata ɗaya zaku ƙara is ok by mee, ni yanzu am really busy at d office inna fita tun safe karfe 06 : 00am bana dawowa sai 12 :00 na dare don haka am really busy gwanda kawai ki nutsu kiyi shopping ɗinki"
Wayaga zuƙi ta malle ina kitchen ina iya jiyo sa yana ta zankaɗawa matar sa gidoga 🤣 wai office tun safe sai yamma mutumin da sai kusan 09 :00am yake fita kuma duk inda 06 :00 tayi na yamma ya dawo amma shine yake shararowa matar sa wannan sharhi kai gaskiya wasu mazan ma sai a slow da lamarin su
Ina jin sa ya gama lallashin ta akan kar ta dawo ko ta gama shopping ɗin ta zauna ta huta, har da wani cewa ko kin gama ki zauna ki huta a can, wato ga banza ka samu ko to wallahi sai na san yadda na samu number badiar na saka ta ta dawo don in samu in huta
Sai da suka gama wayar sannan ya ajiye wayar ya ƙarasa cin abincin sa, ya na gama wa ya kirani inzo in kwashe kayan
Sama ya hau inda ni kuma na fara kwashe kayan, har na zo wuce ta ta kusa tv set ɗin falon sai na hango wayar tasan tana chargy da sauri na na je na ajiye kayan sannan na zo na ɗauka na rubutawa badiar text
```only nayi missing ɗinki dana ce miki ki zauna wallahi am joking pls ki yi sauri ki dawo as soon as possible i miss u a lot```
Nai mata sending ina shirin deleting naji foot steps ɗin sa don haka sai kawai na kashe wayar na mayar na ajiye rigima ba uban wanda ta kashe barin ma rigimata da sabit mun saba
Yana saukowa ya ɗauki wayar ya fice, farin ciki ne ya rufe nk Allah dai yasa message ɗin ya shiga
Be daɗe da fita ba sai gashi ya dawo a fusace daga ganin sa nai kitchen a gujr na ɗauko muciya, gadan gadan ya nufo ni fuskar nan tasa a murtike kamar an masa mutuwa
"wallahi idan ka ƙaraso kusa da ni sai na muƙa maka ita" tsayawa yayi ya kallo muciyar da ke hannun sannan sai ya ja burki
"uban wa yace ki taɓa min wayata balle har ki min text"
"meye text" na tamyaba cike da renin sense
"baki ma san meye text ba, da kika ɗauka kikai wa badia text wai ina missing ɗin ta ta dawo zaki ce baki san text ba"
"ni tunda nake ban taɓa riƙe waya ba tayaya za a yi in san yadda ake yin text" na kuma bashi amsa
"to ni da waye a gidan da har akai wa badia text amma baki gani ba bayan anan na ajiye wayar na hau sama kuma lkcn da na hau sama akai mata text ɗin"
"oho ni dai ban sani ba don ba taɓa riƙe wayar nayi ba balle in iya wani abu wai shi text" duk wannan maganar da muke yi muciyata na ɗage daya matso kusa da ni in muƙa masa
Kallo na ya tsaya yana yi tabbas da badan muciyar nan ba da tuni ya fara muguntar tasa, amma babu halin hakan tunda yanzu am armed 🤺
Ƙwafa yayi sannan yace
"zaki gane kuren ki" a zuciyara nace oho dai nasan ta inda zaka rama kuma am already immune to it, na riga na saba yanzu bana jin komai wani lkcn ma sai nishaɗi 🙈
Juyawa yayi ya fice inda na bi bayan sa da gwalo sam ban san zai waigo ba sai gashi mun yi ido huɗu da shi ina masa, shan kunu nayi na ƙara ɗaga muciyata ƙwafa ya kuma yi
"wallahi sai kin rena kanki" ya faɗa yana ficewa, ina jin shi yana waya da badia inda yake cewa
"yanzu only kin riga kin yi booking ba za ku iya canceling flight ɗin ba ki ƙara hutawa" ban san me tace masa ba na dai ji yana ce mata ok safe jorney
Ranar wuni nai ina murna badia zata dawo in huta da jarabar wannan jarababben nata ta dawo can suje su ƙarata ni ma in samu in sakata in wala
Ina gama abinda nake yi na shiga part ɗin anty fannah na bata lbr ina ta dariya ita ma dariyar ta taya ni sai da muka gama sannan tace
" bari in baki wani haɗi ki shaa, idan kika shaa badia tana dawo wa idan ya kwana a ɗakin zai manta da ke saboda salanta mace yake"
Da murnata na ce mata tooo nice har da taya ta haɗa shi da zuma a ke sha sai tsimi wanda ta haɗa tace nata ne shi sam ban sha shi ba haka kurum ina neman hanyar gujewa sabit me zai kaini shan wani tsimi *ƙila ma na mmn fareeda ne sunan shi maƙale mata*
Da yamma kuma ta haɗa min wani shayi mara daɗi wai in shanye na tambaya ta ko na menene haɗe rai tayi tace min
"kin taɓa jin ance shayi yana maganin mata barin ma baƙi kawai ki sha" ɗaga takashin kofin nayi nayi ɗaɗɗake shi sam ba daɗi
Sai farfesu da ta haɗa mana muka sha shima sam ba wani daɗi gare shi ba, anty fannah a wannan lkcn ta iya girki amma wani lkcn in tai maka girki sai dai kawai aci da haƙuri barin ma ace pepper soup ne sam baya daɗi wani spice take sakawa me gari gari wai haka ake yi a garin su ni sam baya min daɗi
Tare mukai dinner da ita anan part ɗin nata kasancewar shima isma'il ɗin ana part ɗin ta yake
Sai yamma lis sannan na tafi da guzurin abinci na, ina shiga toilet na faɗa nai wanka na ɗauro alwalar sallah magariba
Yau gogan be dawo da wuri don har akai magariba sam banji ɗuriyar saba, sai can kusan tara sannan naji shigowar sa
Ban bi ta kansa ba don komai na buƙata na tanadar masa, bashi ga shigo ɗakin nawa ba sai ƙarfe 10 :30 na dare gashi ya hanani bacci indai br shigo ba haka na zauna ina ta gyangyaɗi
Ranar munyi wani abu wai shi till dawn 🤣 daɗin abun i was enjoying myself all along 💃🏼💃🏼💃🏼
A ɗakin ya ƙarasa baccin sa bayan ya tasa ƙeya ta toilet munyi wanka tare, Allah sabit ɗin nan yana son ɓata min tarbiyya ta
Wajen ƙarfe shida ya fita ɗauko badia kamar sallah haka nake jin kaina, ko da ya fita sai daya karta min warning ɗin kar badia ta sake ta dawo ban gama girki ba sannan yace min
"idan kika sake naji wani abu daga gare ki zaki ga yadda zan miki" yana ficewa nai tsalle tare da cewa
*FREEEEDOM* 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
********************
Yana tafe a mota yana tunani abinda asmau tai masa sam be ji daɗi ba, wannan ƴar iskar yarinyar sam ban gama mission ɗina akan ta ba ta ruguza min budget ɗina yanzu in badia ta dawo tayaya za ayi in samu sake wa da ita
Ga wani shegen abu a tattare da ita da sam mutum baya gajiya da ita, wani abun da ke birgeshi da ita shine duk da taurin kanta amma yakan juyata son ranshi
Kamar kissing sam badia bata son kissing sai tace wai ƙazantar hakan take gani, ita kuwa wannan sarkin taurin kan yaga har ta fara responding sannan wanka tare
Wannan no go area ne a wajen badia wankan ma a ɗakin shi sam bata yi balle yayi joining ɗin ta sai ta tafi ɗakin ta ta saka key a toilet sannan take wanka
Amma asmau tuni ta saba da wanka da shi duk da dai kullum kamar bata so amma shi hakan sam be dame shi ba
Sai kuma bacci tare wannan ma haram ne ga badia yana son yaga yana kwance matar shi a jikin sa amma sam badia bata so wai bata son ya farka ya ganta ba makeup
Amma ita wannan sam makeup ɗin be dame ta ba ita dai tayi wanka ta saka turaren ta me shegen tayar masa da hankali
Gaskiya tsakanin su akwai banbanci sosai amma matsalar asmau ɗaya ce baƙa ce shi sam har yanzu bashi da taste akan baƙar mace balle har ace zata haifa masa baƙaƙen ƴaƴa subhanalli ai da anyi yaƙi da shi ina shi ina baƙaƙen ƴaƴa
Ai dole ne ma ya ɗau mataki akan asmau don kar ta haihu shi sai yanzu ma ya kawo maganar cikin ashe zata iya samun ciki gaskiya dole ne ya ɗau precaution akan asmau haka kurum kar ta haɗa shi da baƙaƙen ƴaƴa ta cuce shi ya rasa yadda zai yi da su
Da wannan tunanin ya ƙarasa airport ɗin inda ya tarar jirgin nasu haɗ ya sauka, sam ba kamar da ba yadda idan badia ta dawo yake rawar ƙafa yanzu kawai sai yaji wani iri amma sai ya dake yai mata welcome kamar yadda yake mata adaa sannan suka kama hanyar gida 🚕
[10:55PM, 5/2/2018] +234 806 399 9164: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻
P⃗a⃗g⃗e⃗ 18🌹
Kafin ma su ƙaraso na gama komai na gyara gidan tsab, banji tsayuwar motar su ba kasancewar parking lot ɗin yana can wajen gidan
Sallamar su kawai naji inda na tafi da gudu naje na rungume badia tare da cewa
"anty badia sannu da zuwa wallahi nayi bala'in murnar dawo warki" abin mamaki ya bata inda take ta ƙoƙari yakice ni daga jikin ta
Bayan ta ɓanɓareni sai ta kai duban ta ga sabit
" *SD* yarinyar nan lfyr ta ƙalau kuwa" be kai ga amsa mata ba na ƙara ruƙunƙume ta
"wallahi anty badia ba komai kawai dai nai murnar dawowar kine" ina kallon sabit yana ta doka min harara sai na share shi
"yanzu tunda kin dawo sai ki karɓi duty ɗin kula da mijinki in huta da........." ban kai da ƙarasawa ba naji sabit ya toshe min baki tare da hankaɗa ni cikin falon
"wuce ki ba mutane wuri da shegen surutun ki faɗi ba a tambaye ki ba"
" *SD* wane duty ne kuma asmaun take magana na kula da kai"
Ɓata rai yayi sannan yace
"wa yake bani abinci in ba ita ba, ya yake kula da gidan duk ai itace take yi, muje only na san kin gaji ne da wannan tafiyar da kika"
Jan hannunta yayi suka shige ni kuma na tsaya ina kallon wannan wawiyar tunda kika ji nace duty ai sai ki harbo jirgin
Sai da suka jima sosai a sama sannan suka sauko kowanne su yai wanka ya canza kaya a zuciyata nace tabbas me wuri ya zo me tabarma dole ya naɗe
Yanayin fuskar sabit sam be nuna wani alamar farin ciki ba ko wani abu,
ba kadaran kadahan dai kamar ba wani abun da ya shiga tsakanin su ko me yasa sam ba haka yake yi ba in ya kwana a ɗakina da fara'ar sa da nishaɗin sa yake fitowa
Ko ma dai menene su suka sani sunfi kusa can ta matse musu ni dai na samu freedom
Ranar da wuri na gama dinner naje na jera musu bayan sun gama na kwashi, wanka naje nayi na samu na kwanta, nai juyi sosai akan gadon kamar ranar na fara kwanciya akan gado
Wani lafiyayyan bacci ne yayi awan gaba da ni, ina cikin mafarkina me daɗi kawai naji an ɗaka min duka
"bana ce miki kar ki kwanta banzo ba, maza wuce kije kiyi brush ki sake wanka kizo ina jiranki"
" Kai mafarki nake yi koo" na faɗa, ranƙwashi naji a tsakiyar kaina
"wannan ma a mafarkin kika ji shi"
Kallon shi nayi sannan nace
"wallahi ko ka fitar min daga ɗaki ko in maka ihi ai yanzu matar ka ta dawo"
"Allah ya baki sa ar ihun baza ta jiba don na ɗura mata maganin bacci, wai zaki tashi ki gyara jikin ki ko musu zaki zauna kina min"
Banni da bakin magana haka na miƙe na shige toilet ina cikin wankan ne ma sai gashi tare muka yi kamar yadda yake so sannan ya nannaɗo ni a towel na fito kamar yadda nake gani a littafi
ƙwiiiii wasa nake yi da ƙafa ta na tako ko ta kaina ma be biba, a ɗakin ya kwana, nai mamakin da ko a jikin sa haka ya kwantar da ni a jikin sa har yayi bacci
Ko cikin baccin idan nai birgima na koma ƙarshen gadon sai ya jawo ni jikin sa mun cigaba da baccin mu,
Da asubar fari ya bar ɗakin a zuciyata nace an dai ji kunya
********************
Tun daga lkcn ya tsiri min shigar dare amma ba kullum ba kwana bibbiyu zaku ga ya shigo ya kwana in kwana biyu kuma ya zagayo ko ƙeyar sa bana gani
A yanzu ma fara sabawa da sabit sosai, amma duk wannan abun da ake yi badia bata da masaniya
Rannan tafiya ta kama shi, ƙiri ƙiri na dinga nuna masa ina murnar tafiyar sa, ranar da zai tafi da daddare ya shigo ɗakina
Muna kwance sai yace min
"naga alamar murnan tafiyar nan tawa kike ji ko, bakya ganin zakiyi kewa ta"
"ko kaɗan" na amsa masa, mintsini kawai naji wanda ya saka ni zabura
"ni ma ba zan yi missing ɗinki ba da daddare ne kawai zanyi kewar ki amma zan kira badia musha hirar mu"
Ban tanka ba don nasan halin muguntar sa sai ya ƙara min wani salon muguntar tasan
Kashegari da safe sai gashi da sabuwar wayar sa ya kawo min sqm badia bata ji daɗi ba wai meye na sai min waya
Ina jin shi yana ta lallaɓe ta akan wai ko idan suna son abinci kafin in dawo sai in haɗa musu,
Yana zaune a falo kafin lkcn tafiyar sa yayi, ita kuma gimbiyar tana kan cinyar sa sai wani shagwaɓa take zuba masa wai zatai kewar sa, shi kuma sai wani biye mata yake yi sai kace gaske
Ada idan badia tai masa wannan shagwaɓar tata jin sa yake yi kamar ba yashi a duniyar nan, amma yanzi sai ganinta yake yi wani banbarakwai ba kyan gani akan cinyar sa, kyan cinyar sa asmau amma ita matsalar ta shegen taurin kai ne da ita
Ni kunya ce ma ta sake su ta kama ni, lallai ma namiji sai a gaishe shi jiya yana ɗakina anan ya kwana amma da safe yana wajen ɗayar har da wani zaiyi missing ɗin ta
Wallahi na dawo daga rakiyar sabit tabbas me fuska biyu ne, ɗakina na shige sam ban ma san lkcn daya tafi ba
Yana tafiya naje part ɗin anty fannah na nuna mata ita ta nunnuna min yadda ake operating ɗin ta ranar wuni nayi acan sai da daddare dana ci na ƙoshi sannan na tafi inda na tarar da bala'in badia wai na barta da yunwa kallo bata ishe ni ɗakina kawai ma wuce inda tabi ni da zagi
Da daddare da wuri na kwanta ban daɗe da kwanciya ba sai naji wayar na ringing, ɗaukar ta nayi number sabit kawai nagani
Sai da ta kusa tsinkewa sannan na ɗaga
"hello" nace masa
"baki iya sallama ba sai hello" sallamar nayi masa sannan ya amsa
"me kike yi"
"ba komai na dai kwanta ne bacci zanyi" na bashi amsa
"ke baki san mijinki yayi tafiya ba ki kira shi ki tambayi ya ya sauka ba ko"
"yi haƙuri ya ka sauka, yau wuni nayi ina koyon wayar nan shiyasa shap na manta da kai"
"meeeyeee kika manta dani saboda wata ƴar iskar waya lallai ma ke ɗin nan wai fannah bata koya miki yadda ake kula da miji bane"
Masifar sa daya saba ya hauyi shiru nai masa ya gaji dayi ya kashe wayar sa
Nima ajiye tawa nayi sannan na kuma kwanciya, can sai ya kuma kira, ohhhhh yanzu kuma menene ina ɗauka naji yace
"ke baki san mijinki ya yi fushi ya ajiye wayar sa ba ki kira shi ki bashi haƙuri ba" shiru nayi don sam ban san me zance ba
"asmau" naji ya ambaci sunana da harufa masu sanyi har cikin zuciyata sai da naji su
"na'am ai ban san fushin kayi ba kayi haƙuri"
"sai dana roƙa, to punishment ɗinki shine ki bani labari kawai" shiru nayi to ni labarin me ma zan bawa sabit ni sam bamu saba hira ba balle in ce ga lbrn da zan bashi
"baki jini bane"
"naji ai na rasa ko name zan baka ne"
"bani lbrin akai na" toofaaa ba gwanda yace in bashi lbr a kan garin da ban taɓa zuwa ba nayo sharhin daya zo min akaina amma labari akan kan sa me na sani
Shirun daya ji yayi yawa ne ya sa shicewar
"to gaya min abu goma da bakya son nake yi" ban wani ɓata lkc ba na fara lissafo su
"na ɗaya kana da wulaƙanci, na biyu ga mugunta,........ Haka na dinga lissafo masa halayen sa da bana soo har ya dakatar ni sannan yace
"naji yanzu ki gaya min me kike so a dangane da ni" to faaa anzo wajen
Hmmmmmmmmmmmmmmm kawai na dinga yi ashe ya ƙulu, masifar tasa dai ya hauyi, nidai nawa jine sai da yayi ya gama sannan ya kashe wayar nima sai na kashe wayar gabaɗaya na kwanta, tunda lkcn be kuma kirana ba har ya dawo gida
********************
Rannan da sassafe ya shirya inda Allah ya taimake sa na san da fitar sa da wuri don haka sai na haɗa masa breakfast da wuri
Ina kitchen ina wanke wanke badia ta kira ni wai sabit ya manta da agogon sa in kai masa agogon part ɗin mummy don kuwa a lkcn be ci ace ya tafi ba
Karɓa nayi sannan na kama hanyar part ɗin a daidai ƙofar shiga naji kamar ana magana ana ambatan sunana sai na tsaya don inji meye ake ta ambaton sunana
"kai kuwa sabit ai na ɗauka son yarinyar nan kake yi, to me zai hana ka bari ta haihu ɗin" inji mummy
"gaskiya mummy bana son haihuwa da asmau haka kurum ta haifa min baƙaƙen ƴaƴa inyi da su, ni dai kawai ina zaki san dabarar da zaki dinga yi mata har ta dinga shan ƙwayar kullum to gaskiya zan so hakan"
Duk da dai mummy taga rashin dacewar hakan amma kuma bata iya yiwa ƴaƴan ta musu, sam bata so ba amma kuma sabit be san a a ba
"to shi kenan amma baka tunanin ya kamata ka bari ko ɗaya ne ta gwada kafin a hanata"
"mummy akwai probability na asmau zata haifi baƙin ɗa kuma abinda bana soo kenan inda ace dukkan chances ɗin na fararen ƴaƴa me da zan fi kowa murna amma baƙin ƴaƴa inyi yaya da su"
Duk yadda mummy ta so hana abin amma sam sabit ya ƙi yadda ba yadda ta iya haka ta karɓa tare da yiasa alƙawari kullum asmau zata dinga shaaa
Sulale wa nayi na zauna a ƙasa gabaɗaya duk wani service nawa ya ɗauke, shin wai baƙi lefi ne da mijina baya son kalar nan
Na ɗauka Allah ne ya hallicce mu kuma yake son ganin mu a haka, kallon skin ɗina yayi wanda yake a chocolate colour, wanda a kowane lkc yake glowing
Kusan sai dai in ban fita amma sai an ta yaba kyau na amma wannan kyaun nawa sam baya burgr mijina, shi kawai baƙin nawa yake gani
Sam be damu da abinda yake cikin zuciyata ba, jin takun sa ya sani miƙewa a tare muka buɗe ƙofar falon
Sam ban nuna masa wani abu ba inda na miƙa masa agogon nasan sannan na shige don gaida mummy
Tana zaune da sachet ɗin maganin a hannun ta tana kallo, tana ganina sai ta ɗan firgita amma kuma sai ta ɗake
Zama nayi sam sai na nuna mata ma ni ban san me ake ciki ba, gaisawa mukayi sannan na miƙe zan fita
"asmauk naji ta kira ni, komawa nayi na zauna sannan nace
"na'am mummy kina son wani abun ne"
"sam ko ɗaya maganine dai na samo miki, naga ƴar uwar ki har yanzu bata haihu ba shiyasa nace bari na samo miki magani ke sai ki dinga sha ko a dace"
Murmushi ne sosai a fuskar ta da badan naji komai ba da abinda zai sa ince ƙarya ne, tashi nayi na shiga kitchen na ɗebo ruwa na kawo
Guda ɗaya ta bani na haɗiya da in haihu da sabit ɗan ya hanani barin sa gwanda ban haihu da shi in yaso in lkcn tafiya ta yayi babu abinda zai hanani tafiya
Hawaye ne taf ido na wanda a hankali suka dinga gangarowa duk wannan abunda nake wa sabit be sa shi ya fara so na ba to sai yaushe, shin wai baƙi laifi ne
Ya Allah ka dube ni ka saka min cutar wa nan da nake fuskanta ba tare da wani hakkin na ba, ganin ina kuka ya sa mummy tambayar menene
"ba komai mummy kawai da ina farin ciki ne yadda kike nuna min soo" sanyi jikin ta yayi ta jawo ni ta rungume ni sannan tace
"wani lkcn ni kaina nakan yi judging abinda nake yi amma i cant help it, wataran idan kika haihu zaki fahimci halin da nake shiga in terms of deciding wat mah kids want"
Sam ban fahimci abinda take nufi ba amma na san cewar ita uwa wacce bata saba kwaɓar ƴaƴanta ba balle ta nuna musu sun yi ba dai dai ba, wannan shine weekness ɗin ta
Her weekness is her boys kuma ban taɓa jin haushin ta ba saboda kowa a duniyar nan yana weekness ɗina sa
Amma wannan karon gaskiya ta kaini bango sam na daina ganin mutumci ta at least in ɗan ta ya tashi yin abu wanda tasan be dace ba ai sai ta kwaɓe su ko amma sam ba haka take ba
Tashi nayi na kama hanyar part ɗin mu ina shiga ɗakina kawai nayi, na kwanta kuka ne ya ƙwace min lallai maraici be yi ba
Inda ace iyayena suna nan a raye da ko hakan zata same ni zai kasance ya zo min da sauki, amma yanzu bani da wanda zan tunkara
Don ko idan na faɗa wa anty fannah hana ni shan maganin zata yi tace sai na yadda na yi cikin ni kuma kamar yadda baya son haihuwa da ni, nima haka na tsani haɗa jini na da shi, wani wahalallen bacci ne yayi gaba da ni
Sai la'asar na tashi gabaɗaya bana jin daɗim jikina da kyar ma nayi dinner, ko da na gama ma sam banci ba shayi na haɗa na sha sannan na kwanta sai bacci
Ina cikin bacci naji mutum yana tashina tare da balbale ni faɗan nayi bacci ban jira shi ba
Kaina ciwo kawai ya ɗauka sakamakom tashin nan da yayi min, toilet na shiga nayi wanka kamar yadda na saba in yazo nayi bacci nayi brush sannan na fito
Yana matsowa kusa da ni da ƙamshin turaren nan nasa ya doki hanci na sai naji amai yana taso min, danne zuciyata mayi amma a gaskiya na ina cutuwa
Yana shirin ɗaga ni wani yunƙuri da nayi sai amai ya fito gabaɗaya na wanke masa fuska da shi, sai da na amaye duk abinda ke cikina sannan na iya maida numfashi
A gaskiya turaren nan ya cutar da ni dani dayawa, ido na a rufe banyi aune sai jin saukar mari nayi, na kuma jin wani a ɗayan gefe
Dafe fuskar tawa nayi na buɗe idon nawa, nan naci karo da fuskar sa wanke tas da amai na, duk da zafin marin nan da nake ji amma hakan be hanani murmusa wa Allah ya kara ya faɗa a raina
Ɗaga ni yayi ya shige toilet inda ya watsa ruwa yana fitowa ran shi a ɓace yace
"ki kwashe bedshit ɗin nan ki wanke min su tas idan na dawo da asuba na tarar da su ba a wanke ba a bushe ba zaki gane kuren ki"
Ficewa yayi daga ɗakin ni kuma na miƙe tare da kwashe kayan shinfiɗar na nufi toilet don wanke su, to me ya saka ni aman nan, ni ko kaɗan banci wani abun a zo a gani ba balle ince ko shi ya ɓata min ciki
Ina wankin ina tunani na, ko da na gama sai na fita waje na shanya su sannan na samu na tsarkake jikina ni ko ya gama ma oho masa, ban damu ba zani na na shinfiɗa sannan na kwanta
Asuba ta gari 😴😴😴😴😴😴🤤🤤🤤
0 comments:
Post a Comment