Da asubar fari ya zo lallai mutumin ya iya doka sammako tashi na yayi sannan ya karta min warning kar ya sake ya dawo daga masallaci ban gyara ɗakin ba
Wanka na fara yi sannan na ɗauko shayata na gyara ɗakin, sannan nayi sallah asuba, na idar ina lazimi ne ya shigo ɗakin nawa lkcn garin ya fara wayewa
Ƙamshin turaren sa ya fara dukan hanci ma wanda hakan ya sa zuciyata ƙara tashi, da gudu na ruga toilet na fara amai, har banɗakin ya biyo ni
"wane irin iskanci ne yake saki wannan aman"
"wallahi ban sani ba ni bama abinda na ci" na faɗa a marairaice
Matsowa yayi kusa da ni ya damƙi gashi kaina sannan ya ɗago min fuskata wani azaba naji ya ziyarci kaina fuskar nan tasa a tamke sam ba fara'a
"yaushe rabon ki da menstruation" ya tambaye
Shiru nayi don wallahi ni na manta ba calculating nake yi ba, indai yazo min shikenan in bai zo ba matsalarsa, ƙara jamin gashin nawan yayi wanda hakan ya sani sakin wani ƙara
"wallahi ban sani ba bana lissafi"
Sakin kan nawa yayi sannan yace
"ki yi brush ki fito ina jiran ki" brush nayi sannan na fito daga toilet yana kwance akan gadon, alamar inzo in kwanta kusa da shi yayi min sannan yace min
"kika sake kika ƙara min amai wallahi sai na zane ki"
"wallahi warin turaren ka ne bana jin daɗin sa shi yake sani aman"
"Wannan matsalar kice don baki isa in dena saka turare ba saboda ke"
Ƙarasawa nai kusa da shi na kwanta ina mai ɗauke numfashi na, Allah dai cikin ikon sa dai banyi aman ba amma kuma na wahala
Bayan ya fita ne naje toilet na kwarara shi kamar ba gobe kai wannan amai sai kace me, kodai ciki gare ni 😱 ni mau naga ta kaina. Ciki a wannan marrar gaskiya dole ne in faɗawa anty fannah don ta san abinyi
********************
Sabit yana fita daga ɗakin asmau ɓangaren mummy ya nufa, fuskar nan tasa kamar an aiko masa da labari mafi muni
Tana zaune tana lazimi ya shiga ɗakin, sai da ta idar sannan ta juyo ganin yanayin fuskar sa tasan ba lfy
"auta lfy me ya faru"
"mummy ina jin fa yarinyar nan ciki gareta kuma wallahi bana so"
"wake nan kake nufi kardai asmau"
"to in banda abin mummy cikin wa zan ƙi inba nata ba gaskiya i cant stand being a father to her black kids" ya faɗa bayan ya firzar da wata iska daga bakin sa
"sabit baka ganin ya kamata kayi murna da farin ciki ganin cewar an daɗe ana neman haihuwar amma sam badia bata haihun ba ɓarin ma da take yi kwana biyu shiru"
"mummy badia zata haihu tunda ta taɓa amma ni gaskiya banason baƙaƙen yara, itama a matsayinta na matata ina manage ne da ita sannan kuma ace nazo na haɗu da ƴaƴa baƙaƙe gaskiya bazan iya ba bana sooo"
Tsayawa mummy tayi sam tama rasa abinda yake mata daɗi, wai sai yaushe sabit zai hankali ne ya fahimci halin matansa sam ita bata ga alamar badia tana son haihuwa ba, asmaun kuma da zata iya haifa masa ko nawa ne batare da ta gaji ba shi wai baya son kalar ta, hmmmm wannan abun yanzu gaskiya ya fara isar ta
"To yanzu me kake son ayi"
"mummy ai ba akan ta aka fara cikin da ba a so ba kawai sai a zubar da shi sannan sai in ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki akan ta"
"kana nufin zaka zubar wa da asmau cikin da ke jikin ta, haba sabit me yarinyar nan tai maka haka dat u soo much hate her"
"mummy sam baki fahince ni ba bana son baƙin ƴaƴa, farare nake so kamar ni, ki duba cikin gidan nam kowanne ɗan sa fari ne haka kurum akai na sai a fara haifar baƙaƙe kawai ƴaƴa na su zama bare a cikin dangi gaskiya banyi wa ƴaƴana wannan planning ɗin ba ina son su saje a cikin dangi"
"to gaskiya ba da ni ba, duk yadda kaga zaka iya kayi tayi amma ni na riga na dawo daga rakiyar ka kullum am trying my possible best inga na nuna maka amfanin da darajar yarinyar nan amma kullum sai ƙara botsarewa kake yi to wallahi kaje kayi duk abinda zakayi amma banda ni aciki"
Tana gama faɗar hakan ta miƙe tayi ficewar ta tare da barin sa a falon, sam be tsammaci hakan daga wajen mummyn nasa ba ita me goya masa baya akan komai da yayi amma wai yau itace ta zaɓi wata akan sa,
Lallai dole ko menene sai ya zubar da wannan cikin na asmau don bazai yadda ya haifi baƙaƙen ƴaƴa ba, wayar shi ya ɗauko sannan ya kira wani abokin sa likita ne, sun jima basu haɗu ba
Abokin nasan ya kasance me shegen neman matan tsiya wannan ɗabiar tasan ce ya sa suka ɓata da sabit ɗin har suka raba hanya, yasan tabbas indai yana neman mata to bazai hana sanin yadda ake zubar da ciki ba
Ringing ɗaya abokin ya ɗauka tare da cewa
"manya ashe za a neme mu"basar wa sabit ɗin sannan ya fara gaishe shi
Bayan doguwar gaisuwa da tambayar juna iyali sai sabit yace masa
"aboki na har yanzu ana halin ne ko an daina"
"wallahi sabit tunda matata ta haifi ƴa mace na sallama, sai dai ɗan abinda ba' a rasa ba amma bana ɗaukar yara sai waɗanda suka jiƙu a abin kaga ban farka ba balle a farke min tawa" ya ƙarashe zancen nasa cikin shaƙiyanci
"ashe dai ba a dena ba" inji sabit
"yo me za a fasa mutuwa ko hisabi muna dai fatan denawa kafin mu tsufa, don kar a tsufa kuma ana bin ƴaƴan ciki"
"Allah ya shirya ka wato kai abin ma wasa ka maida shi ko to Allah ya baka sa a kar ka shiryu ɗin" inji sabi
"kai fa ɗan iska ne ya ina neman shiryuwa amma kana min wani fatan, wai ma meye na nemana nasan dai ba halin da nake ciki kake son jiba"
Shiru sabit ɗin yayi don shi sam be ma san ta inda zai fara ba, can dai da ta matse shi sai yace
"wallahi abortion nake son ayi wa wata ban sani ba ko kana yi"
"ɗan iska kace kaima kayi joining grp ɗin namu ya akai haka ta faru bakwa using protection ne"
"wane grp ɗin naku Allah ya kikaye ni, kai in kasan inda za ai min kawai ka faɗa min bana son long story" ya faɗa a fusace don yanzu haƙurin sa ya fara ƙarewa
"sorry bro abin bai kai nan ba kawai ka shigo asibitin mu ana yi ni ma da kaina zan mata kar
ka samu damuwa"
"kai ka isa wallahi baza ka taɓa min matata ba, in kuna da macen da zatai aikin ka haɗa ni da ita in kuwa babu in nemi wani"
"haba bros kawai ka taho, amma me yasa kake son zubar wa da matar ka ciki"
"ai ba exams nake ɗauka ba balle ka tambaye ni kowane question sannan in amsa wannan personal matter ɗina ne, ko kana so in dinga bayyana sirrin gidana gare ka" inji sabit
"sorry bros kawai kuzo in shaa Allah kafin nan na tanadar da komai ready har dr. ɗin"
"ok see u, zan shigo da daddare"
Sallama sukai sannan sabit ya koma part ɗin sa, yai wanka ya fice ko abinci ma be tsaya ci don yarinyar haushin ta yake ji sosai wai tayi ciki to garin ƙaƙa hakan ta faru lallai yayi sanya dayawa
Jiya jiyan nan yakai wa mummy pills akan ta dinga bata amma wai a yau wai a tashi da ciki, kai wallahi da sake bazan iya ganin baƙaƙe a matsayin ƴaƴana ba
********************
Sai gab da la'asar sannan ya dawo, ina kitchen ya same ni ina wanke wanke
"idan anyi sallah la'asar zamu je a sibiti a duba ki wannan aman naki ban gane shi ba"
To kawai nace na cigaba da aiki na, sai da na gama sannan, nai wanka na ɗauro alwala na gabatar da sallah la'asr
Sannan na je falo na shi yana zaune
"na gama" na faɗa
"muje waje ki jirani gani nan zuwa"
Wajen na fita be wani daɗe ba sai gashi, motar muka shiga muka kama hanyar asibitin hankali na a kwance nasan dai me za a ce ciki gare ni shine dai be san ina da shi ba
Muna ƙarasawa asibitin ya kira wani abokin sa a waya sai kuwa gashi kamar daman mu yake yi, gefe sabit ɗin ya ja shi suka fara ƙus ƙus ban san me suke cewaba daga ƙarshe dai naji abokin yana cewa
"haba bros ai nai mata bayani baka da matsala"
Sai da suka gama gulmar su sannan suka ƙaraso, shi yayi mana jagora har wani ɗaki in da muka tarar da wata likita tana zaune akan wata kujera
File aka buɗe mana sannan ta fara mana ƴan tambayoyi ina bada amsa iya sani na,
Sai da ta gama rubuce rubucen ta sannan tace min in kwanta a kan ɗan gadon da ke ɗakin, kwanciya nayi sannan ta ɗaga min rigar da ke jiki na
Wani abu ta matsa min akan cikin nawa wanda yake a shafe kamar ba komai a cikin sa sannan ta kunna ƴaɗ computer da ke kusa da gadon ta ɗauko wani abu tana goga shi a kan cikin nawa tana kallon cikin computer
Sai da ta gama sannan ta bani tissue wai in goge, in sauko, hakan kuwa nai, ƴan rubuce rubucen ta ta kuma yi a file ɗin nata sannan tace
"positive ya nuna cikine amma kama son ayi proceding da allurar"
"abinda ya kawo mu kenan"
"ok bari in rubuta mata sai kuje ku siya sai nurse tai mata ai bazai bada wani matsala ba 6weeks kawai yake"
"ok mun gode" sam ban fahimci me take nufi ba na ɗauka tana nufin cikin bazai bani matsala ba don haka sai muka karɓi
Allura ce guda ɗaya muka siya sannan muka je nurses room akai min, allurar shegiyar zafi gare ta ga sagar da ƙafa, ko da muka fito sai muka kuma haɗuwa da wannan abokin nasa inda ya ce mana ba wani matsala in muna son zama mu zauna in kuma zamu tafi in matsala ta faru sai mu dawo
Sabit shine ya matsa mu tafi kawai don akwai abinda zai yi a office ɗin sa, sallamar mu aka yi muka kama hanyar gida
A ƙofar gida ya ajiye ni, ina shiga ɓangaren anty fannah na nufa tana ganina sai tace min
"naje wajen ku aka ba a san inda kike ba wannan ƴar iskar kishiyar" murmushi nayi yadda anty fannah ta tsani badia ni ban tsane ta ba
"ni albishir ma na zo miki da shi amma kuma kin fara kawo zancen badia" barin abinda take yi tayi sannan ta ƙaraso wajena
"ciki gare ki don ashine kaɗai albishir ɗin da za ki min inji daɗi" murmushi nayi sannan na shafa ciki nace
"wata ɗaya" ina faɗa mata ina murna, rungume ni tayi tana murna nima ina yi, sai da muka gama murnar mu sannan tace min
"asibiti kuka je aka tabbatar" gyaɗa mata kai nayi sannan nace mata
"har allura ma akai min me shegen zafi"
"allura kuma ta mecece" ta tambaya fuskar ta da alamar mamaki
"oho ni ban sani ba, don da muka shiga office ɗin su suke ta abun su banda ni"
"ƙila ko na ƙarawa babyn ƙarfi ne" inji ta muka ci gaba da hirar mu, har anty fannah tana bani shawarar kar in sake in bari badia ta san da cikin sai dai kawai ta ganshi
Hira tai hira muna ta yi can sai naji mara ta ta fara mintsini na, na share, abu wasa wasa tun ina basarwa har na kasa na faɗawa anty fannah ga abinda nake ji faa
"ikon Allah tace ba yanzu kuka je asibiti ba akace muku lfy har da baku magani ba"
Gyaɗa kaina nayi bayan na cije leɓan ƙasa saboda azaba, wani murɗawa da cikin nawa yayi sai kawai naji wani na fita daga jikina kamar fitsari
"anty fannah fitsari nake yi" nace mata
"fitsarin lfy tashi mu gani"
Ina miƙewa ta leƙa inda na zauna wani irin ƙara ta saki sannan ta kama hannun
"asmau zo muje a sibiti kar cikin nan ya zube" jikina ne ya fara rawa ina miƙewa jinin ya cigaba da zuba yana bin ƙafa ta
Har mun kama hanyar fita sai taga ina zubar da jini don haka dole ta raka ni toilet ɗin ta na gyara jikina sannan muka kama hanyar jikina sai rawa yake yi kardai ɓari nayi
Asibitin da suke zuwa ta kaini inda nan da nan aka shigar da ni labour room, ciki ya riga ya gama lalace wa, dƙn haka suka taimaka ya ƙarasa fita sannan suka dinga min tambayoyi akan yadda abin ya faru
Tsab nai musu bayani abinda ya faru anan nurse ɗin ta gane allurar abortion akai min, kuma cikin ya fita sam ba wani matsa, magani kawai aka bani sannan ta ce mu fita tunda dai komai is normal
Anty fannah ce ta bita office inda tai mata bayanin abinda ya faru da ni da kuma asarar cikin ya zube gabaɗaya bashi
Da kuka anty fannah ta fito daga office
"asmau dama sabit allurar zubar da cikin nan ya sa akai miki" ta faɗa tana kuka
Dakewa nayi don bana son taga weakness ɗina
"anty kaɗɗara tace kuma shima babyn Allah dama yayi ba me taka ƙasa bane, don haka babu komai Allah yana kallo kuma zai saka min" kuka ne yaci ƙarfi lallai yau na tabbatar da tsanar da sabit yake min ba kaɗan bace
Sai da muka gama kukan mu sannan muka kama hanyar gida bayan mun sai magani
********************
Sam sabit ya manta ma da wata sai asmau balle har ya tuna da cewar zata ɓari at any moment, hidimar sa kawai yake yi
A yunwace ya ƙarasa gidan yai mamakin da ya shiga ya kan dinning table ɗin ba komai, badia ya kira sannan ya tambayeta me ya faru yau abai girki bane ko mee
"wallahi ban sani ba ni tunda ta fita da yamma ban kuma ganin ta ba" gabansa ne ya faɗi kai dai ace ta san abinda yai mata kuma ta gudu kai ina zata gudu ai har yanzu batta da wannan wayon ƙila tana ɓangaren fannah
Miƙewa yayi ya kama hanyar burin shi yaga asmau acan in bai ganta ba yanzu tayaya za ayi ya fara rayuwa ba ita, ƴar iskar yarinyar duk da dai ba kalar sa bace amma kuma Allah ya bata wani baiwa da duk wanda ya fara sanin ta bazai iya rabuwa da ita
Gudu gudu sauri sauri a haka ya ƙarasa part ɗin fannah, itama a kulle yake bata nan, hankalin sane ya tashi, isma'il ya kira bayan ya ɗauka ne yake tambayar sa fannah
Inda isma'il yake cewa ta cemin suna asibiti ita da matar ka, wani ajiyar zuciya yayi wanda shi kansa bai san zai iya ba Allah ya taimake shi
[8:21PM, 5/1/2018] +234 806 779 9926: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻
P⃗a⃗g⃗e⃗ 20 🌹
Basu suka dawo ba sai kusan 08 :00pm sannan muka dawo, directly part ɗin anty fannah muka wuce sallah kawai nayi sannan na kwanta sai bacci ya kwashe ni
Sabit yana ɓangaren sa amma ya kasa zaune ya kasa tsaye tunanin sa kar asmau ta faɗawa fannah yai mata allura gaban shi sai faɗuwa yake yi
Sai kusan 09 :00 sannan ya miƙe, badia da ke kusa da shi ta tambaye shi
"sabit ina zaka a daren nan"
"zanje in duba yarinyar nan ne dare yayi a maimakon ta zo ta kwanta" inji sabit
"to meye na damuwa da ita in ta gaji ai dole ne ta samu wurin kwanciya ko, amma ka wani tada hankalin ka sai kace wata matar ka"
Wani kallon banza ya bita da shi sannan ya fice, ɓangaren fannah ya dosa, yana shiga ya tarar da fannahr tana kallo
Sallama sukai shida badia suka shiga, kallo ɗaya fannah tai musu ta kau da kanta gabaɗaya ta dawo daga rakiyar sabit ɗin balle wannan ƴar iskar matar tasa
"fannah don Allah ina asmau take naga har yanzu bata dawo ta kwanta ba" bata kalli inda suke ba ɗakin da asmaun take kawai ta nuna masa da hannu
"amma ta riga tayi bacci don haka zaku iya tafiya da safe in ta tashi ta koma" tsayawa yayi yana kallon fannah kai gaskiya da sake bazai taɓa iya barin asmau ta kwana a wani wajen ba sai da ɗakin ta
"bari inje in taso ta" ya faɗa yana yin hanyar ɗakin, miƙewa ta bi ta sha gaban sa
"baka isa ka tashe ta ba ai matar ka ce indai har ka matsu ta koma ɗakin natan sai dai ka ɗauke ta in kuwa ba haka ba sai da safen"
Nannaɗe hannun rigar sa yayi yana shirin shiga ɗakin, sai badia ta tare shi
" *SD* kar kace min kana son shiga ka ɗauki yarinyar nan da kanka, ka barta mana da safen ta dawo da kanta"
Kallon ta be yi ba ya shige, masifa ta fara yi tana cewa wallahi indai har ka sake ka ɗauke ta wallahi zaka sani don ni kuwa ban yadda in yi sharing miji da wata ƴar aiki ba
Kinkimar asmau yayi yai mata ɗaukar jarirai sannan ya kama hanyar fita da badia a bayan sa tana ta balbala masa bala'i inda shi kuma ko ta kanta be bi ba
Anty fannah ta murmusa dama abinda take som sani kenan da sabit shin anya yana son asmau kuwa ko a a amma ita a ganinta yana son asmaun amma kuma me yasa yake mata haka
Kuma duk wani shawarar da yakamata ya bawa asmaun amma duk da haka sabit ɗin ya kasa sallamawa wannan abun da ɗaure kai yake
Sabit har cikin ɗakin ta ya kai ta badia na biye da shi,
"to tunda ka kawo ta sai ka ajiye ta muje ko" ta faɗa masa kamar wani ɗan yaro, abin nan yai masa ciwo yadda take nuna halin ko in kula da asmaun duk kuwa da yadda asmaun take kular mata da gida
Wani banxan kallo ya bita da shi wanda ya sata jan bakin ta tai shiru, yana son rungume asmau kafin ya fita amma kuma badia ta ƙi barin ɗakin
Haka ya haƙura ya fice bayan ya gyara mata kwanciyar ta sannan ya tafi ɗakin sa badia ce ta shigo tana wani rangwaɗa tsab ya fahinci me take so amma sai ya basar daga baya ma data ishe shi sai ya kore ta ya rufe ɗakin sa
Tinanin asmau ne kawai ya faɗo masa arai yana jin yarinyar sosai a ransa amma gaskiya bazai taɓa barin ta ta haifa masa ƴaƴa ba
Sai da ya tabbatar da badia tayi bacci sannan ya kama hanyar ɗakin asmaun tana ta baccin ta kamar yadda ya kwantar da ita
Kusa da ita ya kwanta sannan ya janyo ta jikin sa ya dinga shafa mata bayanta har bacci shima ya kwashe shi
********************
Na riga shi farkawa ganin yadda yake kwance yana ta sharar baccin sa ya sani zame jikina a hankali na shiga banɗaki tare da ɗauro alwala
Ina fitowa na tarar ashe har ya fice, sallah nayi sannan na kuma kwanciya don kuwa ji nake yi kamar bacci be ishe ni ba
Bacci ne ya kwashe ni, cikin baccin nawa naji muryar badia tana min magana
"sai yaushe zaki tashi ki haɗa mana breakfast gashi lkcn office zai ƙule" miƙe wa nayi sannan ta kalle
"matsayin mu ɗaya a wajen sabit kamar yadda kike tunƙahon mijinki yake haka yake tinƙaho da ni a matsayin matar sa don haka kowacce tata ta fish she ta daga yau na daina bauta wa ko wa kowane ɗan iskan yayi aikin sa an gama wannan wasan"
Sakin baki tayi tana kallo na lallai ma yarinyar nam,
Sabit ta ƙwala wa kira wai yazo ya yi magana
Shigowa yayi shima kamar gaske bayan ya haɗe girar sama data ƙasa
"me yake faruwa ne a ana anga ana ta ƙwala min kira"
" *SD* yarinyar nan taƙi tashi tai mana breakfast nai mata magana tana gayamin maganar banza"
Juyowa yayi ya kalle ni wacce ni kuma idon yake ƙyam akan sa inga irin matakin da zai ɗauka
"ke sai yaushe zaki ki haɗa mana breakfast ne"
"bani da lfy ko kana don ingaya maka abinda yake damuna ne" shiru yayi sannan sai ya juya ga badia sannan yace mata
" Muje mu ƙyale ta tunda tace bata jin daɗi inta warke ta koma duty" ya faɗa yana tura ta don su fita
" a a ku dawo in faɗa muku abinda ke damuna mana ya kuka fita ai kamata yayi kiji ki san me ya same ni" na bita da wannan ina ganin ta juyo shi kuma ya hankaɗa ta tare da riƙe mata hannu yana janta
Ai na dawo daga rakiyar sabit zai sqn ya zubar min da ciki wallahi sai ya gwammaci kiɗa da karatu, wallahi sai ya san asmau ya taɓa bari dai in fita mu haɗu da anty fannah nasan zata bani shawara
Guduwar ma dana ce zan yi na fasa wallahi sai na zauna a gidan nan na haifawa sabit baƙaƙen ƴaƴa sannan hankali zai kwanta in ban haifa masa baƙaƙe ba ban rama wulaƙancin da yai min ba
Wallahi sai ya gane bashi da wayo da asmau yake to nima yanzu lkcn da juya kaina yayi na daina ɗaukar order daga wajen wani nima daga yanzu na zama ogar kaina
********************
Sai da na tabbatar sun fita sannan na tafi ɓangaren anty fannah, tana zaune ta zuba uban tagumi kamar an aiko mata da mala'ikan mutuwa, na shiga da fara'a ta
Tana kallona tace
"lallai yaro be san ciwon kansa ba wai har kin wats tsake kin koma duty"
"wane duty ba abinda nai musu ai yanzu ciwon ido zan zame musu a gidan nan kuma wallahi sabit abinda baya so shine baƙaƙen ƴaƴa ko wallahi anty fannah sai na haifa masa sai na cika wa sabit gida da baƙaƙen ƴaƴan daya baya so" tsayawa tayi tana kallo na
"asmau da niyyata in saka daddy ya ƙwatar miki ƴancin ki, yasa sabit ya sallame ki ke ma kije ki ne mi wanda yake sonki kk aura"
"haba anty fannah ai da kin cuce ni, sabit shi nake son ya kasan uban baƙaƙen ƴaƴana, ko yana so ko baya so wallahi sai na nuna masa shi ƙaramin ƙwaro ne a wajena, abinda ba abinda ban sani ba nashi, wallahi anty fannah cikin sakan ƙalilan zan iga juya sabit, kawai dai yana da taurin kai da tsatstsauran ra'ayi, amma wallahi na ɗau ɗamarar sai na nuna masa banbanci aya da tsakuwa, sai na nuna masa cewar wasu matan ma suna suka tara, wani ƙyalƙyal banza na mace ba lallai ta zama me quality ba"
Tsayawa kawai tayi tana kallona na bata mamaki sosai, yama za a yi in tafi in ƙyale sabit a haka ai ya ci galaba ta wannan yaƙi ne ya soma wallahi sai naga ƙarshen yaƙin nan sai na haifa wa sabit ƴaƴa baƙaƙe mu ga yadda zeyi kuma wallahi ni da sabit ya raina sai na zame masa ciwon ido
"anty fannah kayan gyara nake so" har yanzu bata daina mamaki na ba don haka sai ta jawo ni ta zaunar dani tare da cewa
"asmau ko dai ɓarin nam ne ya juyar miki da ƙwaƙwalwa, naga duk kin rikice kin zama wata ba asmaun da na sani ba"
"wallahi anty fannah nice hankali kawai nayi, kuma nasan ciwon kaina wanda yayi sanadiyyar rasa baby na innace na barshi haka ai banyi ba wallahi sai na ƙun sa masa abinda har abada bazai taɓa mantawa ba amma sai da taimakon ki sai na haifa masa baƙaƙen ƴaƴa iya son raina, goma ma zan haifa masa ko sha biyar"
Tabbas asmau ta zauce inji fannah, zaman dirshen nayi a gaban ta ina ta lissafo mata irin plan ɗin dana ɗauka zan aiwatar akan sabit da matar sa wallahi sai sun san shayi ruwa ne
Tun tana basarwa har tazo ta fara bani tips na mallakar miji a hannun na ada in tana faɗa min yana shiga ne ta kunnen hagu yana fita ta kunnen dama
Amma yanzu tsab nake haddace wa ai yanzu za a fara wasan ada ba komai akayi ba, amma yanzu wasan zai fara
Sai yamma na kama hanyar part ɗin mu abinci na naje na dafa lafiyayye na zuba a cooler na ajiye, na shiga ɗaki na ɗau wanka na sai da na turare jikina da turare na daƙƙo wata fitted gown da mukai da anty fannah na saka
Falo na fito ashe ita uwar gidan ta dawo ma abanji dawowar ta ba, cooler dana ajiye akan dinning table ta buɗe ɗan wake ta ci karo da shi da mai da yaji sai kunun tsamiya
Wani shegen kallo ta bini da shi
"bana cin wannan ki sake ɗaura min wani"
"ai ba naki bane nawa ne, ai na dena yi wa kowa girki duk wanda ya ji yunwa ya shiga kitchen muga in zai iya"
Hannu ta ɗaga zata kwaɗa min mari a dai dai lkcn sabit ya shigo
"ke badia me ya haɗa ku zaki mare ta"
" *SD* wannan yarinyar wai me take taƙama da shi ne, gaskiya na fara gajiya da zama da ita ya kamata a sallame ta"
Juyowa yayi zai min faɗan da yasa wani ƙayataccen murmushi na sakar masa tare da kaɗa masa ido cikin kissa
Tuni ya maida wuƙar tasan sannan yai gyaran murya
"me tayi miki ne da zaki dake ta, bana son hayaniya"
"ni dai kawai na gaji da ganinta" in da inda ya fara ya rasa kalma ɗaya ma da zai ce sai wani kame kame yake
Dining na nufa n zauna na fara cin abinci na ina jinta tama jarabar wai ban kai wannan matsayin ba tana ƙara yi wa sabit maganar ya kore ni ko ita ta barmana gidan
Lallaɓa ta yayi ya hau sama inda ni kuma na zauna ina ta cin abincina, nai mamakin da ya gama kintsawa ya sauko ya ci ɗanwaken
Ita kuma badia tana nan kan bakan ta bazata ci ɗan wake ba sai dai in dafa mata wani abun, iskar da ta ɗauko ta ma ban kalla ba balle ita sabit ɗin ma nai mamaki dana ga sam be ce komai ba
[8:22PM, 5/1/2018] +234 806 779 9926: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻
P⃗a⃗g⃗e⃗ 21🌹
Tun daga lkcn na zame musu ciwon ido sai haƙuri sai abinda na ga dama nake yi a falon sam sabit sai yayi wani sanyi ashe abun nashi ma iskanci ne
Tuni na ajiye girkin sai abinda naga dama nake dafawa wank lkcn badia taci wani lkcn kuma tace ita bata so kuma wallahi ruwa bana bata balle in ɗaura mata wani abu
Tuni na ƙwatar wa ƴanci sam yanzu sabit baya min abun da yake min ada kamar ma shakka ta yake yi ko ince tsoron badia tasan akwai abinda yake shiga tsakanin mu yake oho mishi
Lallaɓawa kuwa sai dai in be shigo ɗakina ba yai ta lallaɓa ni yana min wani daɗin bakin wai in kwantar da hankalina zai sanar da badia cewar ya mai da ni matar sa official
Hmmm kawai nake bin sa da shi besan ni da nawa ƙudurin a raina ba, abu kaɗan idan tayi sai in fara "ke kin san meke faruwa a gidan nan in ƙafa ta ɗauke kuwa, kina can kin saki baki kina bacci kamar mushe" 🤣🤣🤣🤣🤣
A lkcn zaku ga rawar ƙafar sabit nan da nan sai ya janye ta yai ɗaki da ita sam bazai bari mu ƙarasa faɗan ba, da gayya nake tsokanar faɗa, ko shi ma gogan yana zaune yana kallo sai inzo in canja channel ɗin kuma in ajiye remote ɗin inyi gaba sam bazai taɓa ce min ko mai
Duk wata hanyar dana san zan bi in takalo sabit faɗa muyi don in tona masa asirin shiga ɗakina da yake yi nayi amma sam ba nasara
Daga ƙarshe na tattarar na watsar na ci gaba target ɗina na neman ciki ido rufe abu kamar me ba ciki ba alamar sa, har wurin anty fannah naje ta bani maganin da take sha amma shiru, lallai ma kodai sabit yana yin wani abu ne a nashi ɓangaren sam ban sani ba amma ciki de ina nan ko ba daɗe ko ba jima sai nayi shi
********************
Wani project ne aka tura sabit lagos zai je yayi na shekara uku, sam ban so ba saboda ba lallai bane ya tafi da mu ba tunda ina lagos ina abuja ai ba wani nisa bane kuma ba lallai ne mummy ta barshi ya tafi da mu ba amma gaskiya ni ina son bin sa don haka ko daya dawo ɗakina da daddare ranar na kai shi makka da madina a ƙafa da haɗine na karɓo na musammam a wajen anty fannah na sha
Muna kwance yana min wasa da gashi na sai nace masa
"sabit kai da wa zaku koma lagos ɗin"
"kina son zuwa ne, kinga yarinyar nan ƴaɗ ƙaramar ki da ke amma baki son rabuwa da mijinki ko, shike nan zan wa mummy magana sai mu koma tare kin ga sai muci karen mu babu babbaka tunda badia baza ta ba"
"cewa zaka yi ka daina bin dare de kana lalube" mintsini ya mannara min au lalube ma nake yi
Wasa mukai da sabit sosai kafin mu kwanta bacci,
Ko da lkcn tafiyar yayi badia taji da ni za a wai don in dinga yi masa girki sai hankalinta ya tashi, itama sai taje
Sam sabit be so badia tace zata ba amma babu yadda ya iya har wani nuna jin daɗin sa yayi wai zamuje tare hmmm ni dai kallo shine nawa
Shirye shiryen komawar mu lagos ya kankama inda sabit ne ya karɓo wa badia transfer na wajen aiki, sannan muka kama hanyae birnin yanki
Mun sauka lagos lfy gidan flat ne me 4bedroom a apapa kowccen mu ta ɗau ɗaya inda sabit ya ɗau master bedroom ɗin
Zaman mu lfy sam bana shiga sabgar su haka suna basa shiga tawa girki ne inna yi in badia na da ra'ayi taci in bata da ra'ayi kuma sai ta siyo nata ba wanda yake shigar sabgae wani tsakani na da ita
Rannan da daddare sai sabit yace badia ta shirya su fita, ina kallom su aka ci kwalliya har tana cewa
" *SD* dinner zaka kaini restuarant" sam be tanka mata ba suka fice, ni kaɗai ma ci dinner ta ranar kuma sam abin ma be dame ni ba saboda ni akwai zaman da nake yi kuma wallahi ko baɗe ko ba jima sai na cimma buri na
Kusan awan su guda a waje sai gasu sun dawo, fuskar sabit kamar wacce aka aiko wa da mala'ikan mutuwa tai jajawur kamar bashi ba
Inda ita kuma badia ita ma tata fuskar sharkaf da hawaye
"wallahi bazata saɓu ba lallai ma badiar nan wallahi bazan yadda ba"
"don Allah sabit kayi haƙuri wallahi bada son raina banr naga jikina ne yake attracting ɗinka zuwa gare ni kuma idan haihu nayi loosing shape ba lallai ne ka so ni ba shiya sa na cire mahaifar" 😱😱😱
Wai kunne na ne yajiye min ko kuma mafarki nake yi
"wannan ma maganar banza ce kice min wai kin cire mahaifar ki akan wani banzan excuse naki, ni da naƙe expecting ƴaƴa na daga gare ki amma shime kika cire mahaifar ki"
Faɗa ya shiga yi sosai ni dai dana ga abin nasu ba na ƙare bane sai na ahige ɗakina amma gaskiya badia tayi kuskuren cire mahaifa
Wallahi akan wani ƙato bazan cire mahaifata ba, har kusan 11 :30 na dard suna bala'i akan cire mahaifar
Ni dai bacci na nayi na ƙyale su, ko da na tashi da safe ma atmosphere ɗin gidan ba daɗi tunda dai masu gidan suna faɗa
Haka dai akai ta zama ba daɗi don ɗan zuwa ɗakina ma sam ya daina ni ma ta shafe ni, duk ya bi ya tsangwami kansa
Allah ya ƙara shine kawai abinda yake fita daga bakina, da ka barmin cikina da tuni na haife shi amma gashi yanzu inda ya kai kansa Allah ya ƙara ai yanzu bashi da wani mafita sai dai ta haihuwa da ni
********************
Sabit yana zaune duk abin duniya ya ishe shi, yanzu ya zaiyi shi fara neman matar ma da zai aura ta haifa masa fararen ƴaƴa shine aiki
Yawancin matan yanzu ba farara bane farin kanti ne, kuma baya son kawo fara kamar badia ya ƙara ƙarawa kansa aiki, inda ace zai samu fara kamar asmau wallahi da ba abinda zai dame shi amma yanzu ga shi nan ya zama shi ba ga tsunstu ba baga tarko ba
Har yanzu bashi da ra'ayin haihuwa da asmau kai sam ma bazai taɓa yadda ya haihu da itaba, shiyasa ya bata turaren da take amfani da shi
Daga china ya taho da shi muddin mutun zai juri saka shi to har abada bazai taɓa bari asmau ta haihu da shi ba, turare ne kamar kowanne amma ƙamshin same illa ne, ƙamshin sa yana lalata ƙwan haihuwa
Buɗewar ƙofa yaji yasan ba me shigo masa ɗaki sai badia don haka sai ya haɗe rai sannan yace
"me ya kawo ki" ko kallon inda take be yi ba
" *SD* na zo ne muyi magana, wallahi ban cire mahaifa ta ba har sai da san zamu samu solution"
Jin kalmar solution ɗinne ya sashi juyowa tare da tsare ta da idon sa
Ganin ya kalle ta ya sa ta ƙaraso qa har da riƙe masa hannun sa
" *SD* me zai hana mu samo surrogate mother, wacce zata haife mana ƴaƴan mu da ƙwai na da sperm ɗin ka kaga shike nan, ni ban yi loosing shape ɗina ba, kuma ga ƴaƴan mu"
Zame hannun sa yayi daga nata
"kina nufin mu nemi wata arniya ta renar mana ɗa a cikin ta sannan ta haifa mana shi sam baza ayi haka da ni ba"
"ba arniya ba, ga asmau ai an ɗaura muku aure ba sai muyi amfani da ita ba, ba hankali gareta ba sam ba ganewa zatai ba"
Shiru yayi yana tunani tabbas wannan shine hanyar sa kawai ta samun fararen yaran da yake so wato kenan ƙaddarar sa ce sai asmau ta haifa masa ƴaƴan sa kenan ko
"to kije kiyi mata maganaa inta yadda shi kenan in kuma bata yadda ba wallahi sai na ƙara auren wacce zata haifa min ƴaƴa"
"zama ta yadda" ta faɗa da murnar ta tana miƙewa
Ina kwance a ɗaki ima ta shiɗin kwanciya sai badia ta shigo nai mamakin ganin ta amma kuma sai na dake tunda take bata taɓa shigo min ɗaki ba nasan akwai abinda ya kawo ta
stool na bata ta zauna, sannan sai tace min
"asmaj kamar yadda kika sani na cire mahaifa ta saboda wallahi ni bana son haihuwa, amma kuma sabit yana so don haka sai muka yanke hukunci sabit zamu dasa miki cikin a jikin ki in ya so sai ki haife mana shi"
"ban gane ba " nace mata
"za a saka miki ƙwai na da sperm ɗin sabit a cikin ki sai ki haife mana"
"kina gani sabit zai yadda da hakan" na tambaye ta
"ƙwarai kuwa da sabit muka tattauna shi yace ma in miki maganar" takaicine yazo min har maƙogwaro na wani abu ya tokare min wato sabit jini nane baya so ko wai sai yaushe zan samu ƴanci ne sai yaushe zan samu cikar buri na
Kallon ta nayi cike da tsana sannan nace mata
"kije ki gaya masa ciki na bazai ɗauki renon sa ba don haka yaje ya samu wacce zai biya kuyi abunku amma wallahi ni asmau bazan yadda ayi wannan abun da ni ba"
Kuka na fashe da shi na takaici lallai sabit ashe abin nashi har ya kai haka wallahi bazan renar masa ɗa ba
Kukan da taga ina yi ne ya sata miƙewa sannan ta fice, kwanciya nayi akan gado na fashe da kuka
Wannan wulaƙancin da me yayi kama, wai me nayi wa sabit ne haka daya tsani sooooo much shin baƙi laifi ne ko kuma haɗa mun da Allah yayi sam be ɗau wannan a matsayin ƙaddara ba
Wallahi baza ta saɓu ba yacce matar sa ta cire mahaifar ta ya kasance baza ta ƙara haihuwa ba dole ne ya haƙura nima gashi tunda nai ɓarin nan ban kuma samun ciki ba ko menene dalilin oho
Takaicin sabit ranar hanani bacci yayi kwana nai ina kuka dana gaji da kukan sai na miƙe na ɗauro alwala ina kuka ina faɗawa Allah matsololina duk da yasan a halin da nake ciki amma kuma ina sake gaya masa ya kawo min ɗauki
Anan kan sallayar bacci ya kwashe ni da asuba na farka sakayau haka naji ni, da wuri na haɗa breakfast ɗina sannan na zauna ina cin abinci na kasa ci nayi
Maganar badia ce ta faɗo min a raina, wai in zama wacce zan reni cikin su, lallai ma sun rena ni
Amma kuma wani ɓangare na zuciyata na son yi, ko ba komai zan dai ɗauki cikin da ba a son in ɗauka
Miƙewa nayi kawai na yi na kama hanyar ɗakin sabit hankalina Akwance, suna zaune shida badia sun yi jugum jugum abin duniya ya ishe su
"na yadda zan ɗau cikin ku amma ina da sharaɗi" kallo suka juyo wa sukai gare ni
"meye sharaɗin naki" suka haɗa baki
Kallo na bisu da shi sannan nace
"sai an biya ni ladan ɗaukar cikin"
"faɗi ko nawa kike so ni zan biya" inji sabit, tsayawa nayi na ƙare masa kallo sannan nace
"250k kuma cash nake soo"
Badia ce ta miƙe ta fita daga ɗakin bata daɗe ba sai gata da kuɗi
"gashi nan 300k ne na ƙara miki 50k" karɓa nayi ina murmushi sannan nace
"kun biya sai a saka lkcn dashen" murna sosai ya kama su badia har da rungume sabit
Fita nayi daga ɗakin naje na adana kuɗina akwai ranar da zakuyi amfani, nace a raina
Fara shirye shiryen dashen cikin muke yi abin mamaki shine na nemi turare na ko sama ko ƙasa
Babu neman da banyi ba amma babu har sabit na faɗawa sai yace min zai sai min sabo
Gaskiya nai missing wannan turaren zan so ace be ɓata ba haka nai ta neman har na haƙura
Ranar laraba muka shirya muka je asibitin akai mana test da komai da komai, komai ya kasance normal kawai lkcn dashe aka saka sati biyu
*****************
Ranar da kawo za ai dashen da kuɗi na na fita 200k a tattare da ni, sai da muka gama komai na shiga ɗakin dashen sannan nace wa dr. ɗin wacce ta kasance macece kuma bayarabiya
"nawa aka biya ki kuɗin dashen nan" kallo na tayi kamar batai magana ba, kuɗin da ke jikina na fito mata dashi kallon su kawai tayi sai ta washe baki tare da cewa
"30k"
Ɗari biyu na ɗauko gabaɗaya sannan na bata na ce mata
"kiyi aikin ki da kyau" kallo na tayi sannan tai murmushi tare da soke kuɗin sannan aka fara dashen fatana dai Allah ya bada sa a
Lafiya aka gama sai da nayi awa ɗaya bayan dashen sannan tace min in miƙe, kuma aka kafa min sharaɗin kar in kwanta da kowane namiji sai an tabbatar da cikin
Badia ce me cewa ai dr. kar ki damu bata da miji, tunda muka koma gida sabit yake nan nan da ni,
Komai na tashi zanyi sai a hana ni, har Allah ya kai mu 2 weeks inda muka koma asibitin aka tabbatar da cikina
Murna kamar me a wajen sabit da badia, kallon su kawai nake yi dafe cikin nawa nayi sannan nace Allah ya kawo min kai duniya lfy
[7:24PM, 5/3/2018] +234 806 779 9926: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻
P⃗a⃗g⃗e⃗ 23
Bayan kwana biyu sai ga mummy nai murnar ganin ta sosai har da saƙo na daga anty fannah Allah sarki anty fannah nayi kewar ki sosai
Mummy tai ta faɗa wai badia mahaifar ta bata da ƙwari kuma gashi ta kuma samun ciki amma ta ƙi zama ta kula da kanta
ba wanda ya tanka sai dai lallashi da suke ta bata wai zasu kula da cikin, ni dai ina gefe ina kallon ikon Allah wannan rayuwa wato akwai abin mamaki sosai
Kwanan mummy biyar sannan ta kama hanyar gida, kamar nayi kuka ranar da ta tafi, don kuwa yanzu zan koma rayuwa ni kaɗai
A hankali cikin ya ci gaba da girma har lkcn da zai zo duniya yayi
Rannan da yamma sai ga mmn badia tazo gidan ita da wata mata, ɗakin badia suka sauka sam ban sam me ya kawo su ba amma kuma bini bini a bini da ido
ranar wata talata da safe na tashi da nakuda, tun ina yi ni kaɗai har dai dana ga abin bana ƙare bane na fita, ina fita naci karo da wannan matar zata shigo ɗakina
"kar dai naƙuda kike yi ƴannan" gyaɗa mata kai nayi don bazan iya magana ba sabida ciwon da ke damuna
Sabit ta kira shima ya fito jiki si ɓari yake yi yaji ina labour, asibiti muka je, inda aka shigar da ni labour room Awa uku cur na ɗauka sannan Allah ya sauke ni lfy, ajiyar zuciya na saki dana ji Allah ya raba ni da wannan cikin lfy
Ɗagowa nayi na kalli yaron......... Fari tas da shi kana ganin shi kaga sabit
Miƙo min shi nurse ɗin tayi na karɓi kayana na tsaya ina kallon sa, godiya nai wa Allah daya sani ina da rabon ganin jini na
Sai da nurse ɗin gama gyara ni sannan ta karɓi babyn don gyara shi, shima, ko da aka gama shirya shi zata fita da shi na kira ta na karɓi abuna
Ƙare masa kallo nayi kamar sabit yayi kaki ya yar addua nayi masa sosai, na so ace yaron kamata ya ɗauko
Ko kuma ace baƙi ne amma ba komai duk abinda Allah yaso haka zan karɓa, kuma ina fatan ya zama me jin ƙan iyaye
Ɗa na yana hannuna na fito daga labour room, da sauri suka ƙaraso tare da karɓar sa mmn badia ce ta fara karɓar sa
"namiji ne ko mace" ta tambaye ni kalmar tai bala'in ƙona min rai ba Allah ya raya ba komai amma wai ita burin ta namiji ne ko mace
sabit ne ya karɓi shi shima daga gani maganar tai masa ciwo, karɓar sa kawai yayi ya wuce ɗakin da aka bamu na hutu
Addua ya dinga masa, ina amsa wa da amin, duk wannan abun da muke ita uwar ɗan bata sani ba don sammako tayi ta tafi kwatano wai ta tafi siyo kayan da zata saka da suna
Sai da ya gama masa addua sannan mmn badia ta kuma karɓar sa ta buɗe masa diaper inda ta gano namiji ne
Nan da nan murna kamar me, har wani ƙara ruƙunƙume shi take yi, mijinta ta kira ta shaida masa badia ta haihu,
Shima yai mata murna sannan yace a bawa badiar, nan ta hau ƙarya wai badiar bacci take yi
Mummy sabit ya kira yace mata badia ta haihu ita ma mummyn tai murna sannan tace a bawa badiar tai mata barka shima duk ɗaya yace tana bacci
Haka suka dinga kiraye kirayen waya suna shaidawa badia ta haihu, ni dai kallo ne nawa
Zuwa can baby ya fara mutsu mutsun yunwa, dabino sabit ya tauna ya lasa masa a bakin sa sannan aka bishi da zam zam
Wajen azahar aka sallame daga asibitin muka kama hanyar gida, wai don renin hankali babu wanda yake ta kaina ni dana haihun sai ta baby,
Ɗakina na shige na samu na watsa ruwan zafi a jikin sannan na fito kitchen na ɗaura indomie na ci na ƙoshi sannan na wuce ɗaki na na kwanta
Wajen ƙarfe 06:00 na yamma sai ga mummy, ina kitchen ina dafa shayi
Sai ga mummy, da sauri naje na tare ta
"mummy ashe kina tafe" tsayawa tayi tana kallona
"ya naga kamar ma kece me jegon duk kin wani ɗashe"
Ta faɗa tana kai hannun ta kan fuska ta, murmushi na saki sannan naja hannun ta zuwa ɗakin badia
"zo muje kiga jikan naki"
Bina tayi, da sallama na shiga, suna zaune a bakin gado shi kuma babyn yana cikin gadon sa na jarirai yana ta baccin sa
A razane suke da suka ga mummy, sai suka fara kame kame
"hjy fatima yaushe kika ƙaraso, muje falo mu zauna yaron yana bacci" inji mmn badia
"ni da nazo ganin baby sai ace min yana bacci, ina ita mejegon"
Tsuru tsuru sukai, nidai tunda naga na haɗa su sai nai ficewa ta na barsu
Ɗakin nawa naji an turo ƙofar, ashe mummy ce ta shigo, sai da ta ƙaraso da sannan na bata wurin zama
"har yanzu sabit ɗin basu dawo bane ko dai wani abun ne ya samu badiar"
Ni dai ban tanka mata ba saboda sam ban san ma ina ta dosa ba,
"ni wallahi duk a gajiye nake, nace musu su shirya gobee mu koma abuja ai suna acen dama dalilin zuwa na kenan"
Ni dam ban tanka mata ba don kuwa a gaskiya na fara kewar ɗana, don haka sai nai mata shiru,
Mara ta naji ta fara murɗa min, mitsss sai yanzu na tuna sam ban ma sha magani ba, miƙewa nayi don in ɗauko magani sai naji mummy tana cewa
"asmau lfy naga kina tafiya kamar kece kika haihun, gashi kuma duk kin ɓata zanin jikin ki"
Juyawa nayi don inga inda na ɓata ban ɗago ba sai ganin mata nayi kusa da ni
"asmau ke kika haihu ko badia"
Tsare ta nayi da idona wanda a yanzu suka ciko da hawaye, ɗago min fuskar tawa tayi
"asmau ke kika haihu, ba badia ba" gyaɗa kaina nayi hawaye yana zuba a ido na
"haba biri yayi kama da mutum" inji mummy takaici ne ya kamata sai ta kama hanyar fita
Ban san me tace musu ba sai gata da babyn,
"ungo shi bashi nono ya sha ki gama in gyara ki, wallahi idan sabit ya dawo yau sai yaga ɓacin raina wanna wane irin zalinci ne"
Karɓar babyn nawa nayi na rungume shi sannan na zauna na fara bashi nono kamar dama yunwa yake ji haka ya karɓa ya fara tsotsa
Muryar badia muka ji a bakin ƙofa tana masifa
"ban gane ɗan ta bane yaushe ya zama ɗanta don kawai ta rene shi a cikin ta sai ace ɗan ta wallahi bazai sha nonon ta ba, na riga na gama booking nurse ɗin da zata dinga kular min da yaro" ta faɗa tana shigowa a fusace da zummar karɓar mummy
Mummy ce tace
"wallahi kika sake kika katse masa wallahi tallahi sai na saɓa miki"
"mummy ya za ayi jini na ya sha nonon ta"
"ya akai ya zama jininki"
Nan badia ta kwashe komai ta faɗa wa mummy, bata gama ba mummy ta fashe da kuka, adai dai lkcn sabit ya shigo
Ingiza badia yayi ya kora daga ɗakin, mummy kuwa kuka ta dingayi,ba irin lallashin da sabit be mata ba amma taƙi shiru
Shima sai ya fashe mata da kuka
"anya sabit kana tuna ranar da Allah zai kama ka kuwa akan haqqin yarinyar nan, tunda Allah ya haɗa ku kake zalintar ta, anya kana da tausayi kuwa"
"mummy don Allah kiyi haƙuri wallahi sai da ta amince muka biya ta sannan akai mata dashen"
"wannan yarinyar me ta sani, da har zaku ce wani kun biya ta yanzu ɗan na wane na wacce tai dakon cikin ne ko na ƴar lelen taka ne"
"mummy ƙwan badia ne"
"mummy ba nawa bane" na bata amsa
"amma ni alfarma ɗaya nake so a barni in kula da shi in dinga bashi nono in yaso idan na yaye shi sai badia ta karɓi abinta"
Kallona mummy tayi sannan tace
"asmau ke yarinya ce har yanzu baki san ciwon kanki ba nan gaba zaki zo kiyi dana sani"
"mummy duk yadda Allah ya tsara bawa rayuwarsa haka zai yi ta" na bata amsa
Nai ta mata daɗin baki akan maganar don bana son a jata da tsaho, ta yi mugun jinjina min sannan daga ƙarshe ta saka aka kira badiar sannan ta kuma kafa sharaɗin ni zan kula da babyn
Sam badia bata damu ba, shima sabit ɗin sai ya nuna ya fi son hakan,
Mummy itace ta dinga kula dani, ko da lkcn suna yayi a can wani hotel sukai sunan su, daga ni har mummy ba wanda ya je
Amma ita da sabit da babyn sun sha hotuna kamar ba gobe, wallahi duk wannan abin da ake yi ko kaɗan a jikina be taɓa damuna ba sdon nasan akwai ranar ƙin dillance
yaro ya ci sunan bbm badia amma anace masa annur mummy tai faɗa sosai wai ai sunan daddy ya kamata a saka amma sam ba ai mara kara ba
Kaji mummy wani ɗigimi
********************
*BAYAN SHEKARA ƊAYA*
kamannin annur da sabit ya gama fitowa, sosai ga wayau kuma Sam baya yadda da badia, shegiyar ƙyuya gare shi kamar
Daga ni sai ni, ko sabit in dai ba fita yaga zai yi da shi ba sam baya yadda ya ɗauke shi
Sam badia bata damu ba, ita dai kawai burin ta taga an masa wanka an masa kwalliya tai ta ɗaukar shi a hoto ta na ɗora shi a dp, facebook da instag.
Shima haka sabit ɗin yake sai dai in ban masa wanka ya ɗau gyara ba, nan zaku ga da sabit ɗin da badiar duk suna rige rigen ɗaukar a pic
Sam wai nuna so ko jan yaron a jiki badia bata san wannan ba, ko tashi yayi da safe ya tafi ɗakin ta sai dak kawai kaji tana ƙwala min kiran in zo in dauke shi in masa wanka
Sam bata yadda ta ɗauke shi sai an masa wanka, wai ko yayi pupu ko fitsari sai dai kaji tana kirana inzo in cire masa
Wani rashin *M* ɗin ma sai in yayi pupu a ƙasa kamar ta dake shi haka take, akwai randa mukai faɗa da ita akan shi,
Ya shiga ɗakin ta ba diaper a jikin sa, sai yai mata pupu a kan gado, kawai zagin shi naji tana yi
Da gudu na tafi ɗakin ta ɗaga hannu zata dake shi, da sauri naje na tare masa,
"haba anty yaro ne"
Harara ta bini da shi sannan tace
"ni ƙazanta ta yara ce bana so, zo ki kwashe kashin nan kije kiyi masa wanka"
Tabbas ba ta san ciwon sa bane don wallahi da ta san ciwon sa da uwa tana cikin cin abincin ta ɗan ta zai yi pupu ta saki abinci ta wanke masa sannan ta zo ta ƙarasa
Ita dai bangaren kayan sawa, kayan wasa, anan fa to kusan Rabin albashinta yaron take kashe mawa,
Sai dai jawo shi ajiki ne dai batayi
Ana haka wani zazzabi ya kama shi aiko sai ya kasance ni kaɗai yake yarda in dauke shi, hatta da sabit baya yarda da shi
Anan ne wani sabon rashin mutunci ya tasowa badia inda tace ita Sam atafau ayaye yaro abata ɗanta, saboda gaskiya ita bata yadda ba tana uwar yaro amma sam be shaƙu da ita ba
A zuciyata nace me kike masa da zai sa shakuwa da ke, don kayan wasan da kike sai masa sani yayi shi yaro
Tuburewa nayi nace sam be isa yaye ba sai ya ƙara watanni, abi kamar wasa har sabit ya saka baki shima sai ya goyi bayan badia wai shima baya jin daɗin yadda annur ɗin yake masa
Ban musa ba ganin bana son sa'insa akan shi ya sa na miƙa mata shi nasan ko kukan sa na dare ya sata dole ta dawo min da shi
Ai kuwa tana karɓar sa daya tsanyare da wani kukan ko a jikinta ni kuwa wannan kukan jin sa nayi kamar ana yankan sa har cikin zuciyata naji
Ɗakina na shike ina jin sa yana cewa ```maaa``` da yake haka yake cemin don bakin sa ba wani buɗewa yayi ba
Aiko ko awa daya batayi da daukan shi ba naji ana ƙwallamin kira a ruɗe na fito inda naga yaro shame shame ahannun sabit kamar marar rai
Ruwa ne a hannun badia tana shirin sheƙa masa na karɓa a hankali na yayyafa masa yana farfaɗowa ya fara ```maaa``` ```maaa```
"na'am baby na" na amsa masa ɗagowa yayi ya kalle ni, duk da dai jikin sa ba ƙwari amma a hakan ya ɗago ya taho wajena da saurin sa ya rungume ni
Sosai na matse ɗana a jikina sai ajiyar zuciya yake saki, wanda hakan ya sa zuciyata ta karye naji hawaye ya cika min ido na
Bani ba hatta sabit sai da jikinshi yayi sanyi ni ko hawaye suke sulalo min ganin yadda yaron cikin ɗan lokaci kadan ya fita hayyacin shi amma da ganina yawani lafe ajikina harda ƙara rungumeni
Bacci ne ya kwashe shi a kafaɗa ta ina ɗan jijjigashi ko da yai baccin sai na sauke musu shi
"zo ki ɗauke shi" inji sabit
"ya ci gaba da zama a wajen ki har sai ya saba da badiar sai ya koma, ke kuma dia ya kamata ki dinga samun time kina spending da shi mana don ya saba da ke kooo" ya faɗa da sigar lallashi
"ok shike nan zan duba"
Wuce wa nai da shi ɗakina muka kwanta, kallon shi nayi sannan nace
"annur ɗana ina alfahari da kai, kuma wallahi da kai sai na nuna wa duniya cewa ni asmau ƴar halak ce"
********************
Tun daga lkcn badia take shigowa ɗakina wai don annur ya fara sabawa da ita, amma ko ta shigo tana manne da wayar ta tana chatting shi kuma daya ganta to ahike nan ya liƙe min kenan har sai ta fita
Sam wannan method ɗin be yi ba haka naji tana faɗawa sabit, sai suka tsiri fita da shi yawo, kunsan yaro da son yawo, wannan ne ma sa ya ke ɗan yadda ta ɗauke shi in dai har ya ganta da mayafi ko hijab amma da ta zauna shikenan sai ya fara ```maaam``` yana kuka
*******************
[8:14PM, 5/3/2018] +234 806 779 9926: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻
P⃗a⃗g⃗e⃗ 23🌹
Da azimi ne muka shirya muka kama hanyar abuja don muyi sallah acan a lkcn annur yana da wata 18 yayi wayo sosai
Kuma kullum kamar sa da sabit ƙara tatsowa take yi, ita kanta badiar tana koka wa duk da dai wani lkcn takance ya ɗauko farin ta
Nakan yi dariya kawai in basar, tun da muka dawo naji canjin ruwa sai na gara laulayi, ada ban ɗauka da gasken ciki gare ni ba sai da muka dawo abuja
Jakar ubacan zamu ga yadda za ayi da sabit da wannan cikin wallahi bazan taɓa yadda ya kuma zubar min ba
Tsab muka koma muka ɗinke da anty fannah har tana min maganar wai na liƙe wa annur bayan uwar sa ƙiri ƙiri take nuna wa bata son mu'amalar mu da ɗanta
Nakan yi murmushi nace ai ba dan ita nake yi saboda yaron make yi, satin mu ɗaya da dawo ta ƙwace annur daga hannuna wai ya isa yaye
A lkcn gaskiya nima na so yaye shi saboda ga ciki abun yana min yawa, gidan su takai shi, batare da sanin sabit ba
Ko da ya dawo daga yawon sa ya tarar an kai masa ɗa gidan su ranar sai da sukai ɗan ƙaramin yaƙi da shi
Ina jin su
"wallahi baza ka hanani kai ɗana gidan mu ba, don ba kai kadai kake da iko da shi ma nima uwar sa ina da shi"
" ta ina kike uwar sa abinda sam baki san komai nashi ba, ki bar wacce take ɗawainiya da shi tai magana mana" inji sabit
Ai kuwa badia sai kuka wai sabit yai mata gorin ba daga jikin ta annur ya fito ba, kuka ta dinga yi wiwi wai Allah ya haɗa ta da mijin da bai san ƙaddara ba
Ƙofata na ja na ƙara rufe wa can ta matse muku ina jin shi yana lallashin ta a zuciya nace an dai faɗi ba nauyi
Ranar da daddare ya shigo ɗakina da ƴaɗ fara'ar sa, ina zaune ina ta shan mangwaro na ko ƙarasa nuna ma be yi har wani ɗan tsami tsami yake yi amma ni a hakan nake son sa
"na lallaɓa wannan rigimammiyar ta kwanta sauran ke"
Ya faɗa yana ƙarasowa kusa da ni
"shan mangwaro cikin dare" ya tambaya, murmushi nayi sannan nace
"ai annur ya kusa ƙani ko ƙanwa" wato ko gabaɗaya tuni wani fara'a da annushuwar da ke tattare da shi kau
"ban gane ba me kike nufi" ya faɗa, ban ɗauka zai ɗau abinda zafi ba sai nace masa
"ciki gare ni kusan 2mnths"
" *WAT* * ya faɗa da manyan harufa,
"ina turaren da na baki kina sakawa kuwa"
"wane turare"
"turaren mana dana baki"
Sai yanzu na tuno ya kuma bani turare bayan na haihu, da farko turare ya ɓata lkcn da nake da cikin annur amma ina haihuwa sai ga turare ya dawo
Ko kaɗan ban kawo komai ba, zaman mummy a gidan ta nai min biƙi ya sani bata da ta tashi tafiya, sabida gaskiya turaren ba dai ƙamshi ba
Da ƙyar ma ta karɓa sai dana matsa mata,
"me turaren yayi"
"tambayar ki nake yi kina amfani da shi ko bakyayi" to kuma zancen sa ya fara bani tsoro
Muye kuma na zancen turare daga samun ciki,
"na bawa mummy" a zabure ya miƙe
"wace mummyn" kallon shi kawai nayi yanzu kuma wallahi na fara tsorata, a fusace ya fice
Ko ma dai menene a cikin turaren wannan shina abinda ake cewa ramin mungunta
Mummy tana bacci sabit ya dinga buga musu ƙofa, da ƙyar ta tashi ta buɗe masa
"lfy auta" ta tambaye shi
"mummy ina turaren da asmau ta baki a lagos"
"amma auta maganar turare shine baza a yi shi ba sai yanzu cikin dare"
"mummy don Allah kice bakiyi anfani da shi ba" tsayawa tayi tana kallon sa
"wani abun ka saka a turaren ka bata ni kuma bata sani ba ta bani" rasa bakin magana yayi kawai sai ya shige cikin ɗakin ta
Turaren yananan kan mirrow ɗin ta ɗauke wa kawai yayi yai ficewar sa, bin sa tayi da kallo sabit zan ga ranar da zaka dawo hanya madaidaiciya
Ɗakina ya dawo a lkcn na gama shan mangwaro na har nayi shirin kwanciya don sam ban ɗauka zai dawo ba
"ke kuma na dawo gare ki, wannan cikin ban san da shi ba kuma bana son shi yanzu, nawa annur ɗin yake don haɗama har kin kuma samun wani cikin to ban yadda ba, nine me gidan kuma idan lkcn da ya kamata ki kuma haihuwa yayi zan faɗa miki, a kuma ɗaukar ƙwan badia a kuma dasa miki"
Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tunkaro ni, lallai ma sabit ɗin nan wato ya mayar da ni baby making machine ɗin sa ko
To wallahi baza ta saɓu ba, ya ɗauka zan masa lakwa lakwa kamar yadda nake masa ada sai ya ga ma buɗe masa wuta nima
Ai ma koya a wajen badia naga alamar sabit zuma ne sai anci da wuta ake zaman lfy da shi,
Faɗa daya ga inayi masa nr ya sashi saukowa
"asmau ba wai bana son ki haihu bane, amma kinga kamar yadda annur yake haka nakr son ƴaƴana su kasance bana son ƴaƴana kiga wasu farare wasi baƙaƙe"
"wannan kuma kai ta shafa wallahi bazan kuma zubar da ciki na ba ka zubar min dana farko wallahi baka isa ka kuma zubar min ba"
Hayayyaƙo min ya kuma yi, daga ganin sa shi ba mutum ne daya iya lallashin mace ba, ko nice dai baya son lallashi oho, yana hawa nima na hau, ko da ya ga yayi lallami yayi faɗan amma duk da haka na ƙi yadda
Sai ya ɗauko wannan shegen turaren
"gashi nam kya ci gaba da shafawa" ya ajiye ya fice
"kuma wallahi kije kiyi nazari na faɗa miki annur be isa ai masa ƙani ba, inma ya isa da ƙwan badia nake son cikin nan"
Inda ya ajiye turare nan na barshi ban ɗauka ba ƙiri ƙiri sabit yake nuna min baya son haihuwa da ni kuma wallahi bazan bari ya samu abinda yake so ba
Kashegari da sassafe na kama hanyar part ɗin mummy don in kai mata ƙarar sa don wallahi abun nashi ya fara isata
Tana zaune tana lazimi na shiga, sai dana jira ta idar muka gaisa sannan na faɗa mata,
"je ki kwaso kayanki daga ɓangaren naku ki dawo nan inga in zai zuwa nan ya ce zai taɓa miki cikin"
Ba haka na so ba naso ace ta kira shi tai mishi nasiha ko faɗa amma dai ko ba komai an samu ci gaba a sha'anin natan
Daga nan ɓangaren anty fannah na wuce itama na fɗa yadda mukai da shi da kuma shawarar da mummy ta yanke
"hakan shine dai dai, sabit yace baya son cikin don haka Allah ne kaɗai yaan abinda zai yi don ganin ya salwantar da cikin, ki koma can kema hankalin ki zai fi kwanciya, ko kin fi son zama kusa da mijinki ne"
"hmmmm wayaga miji indeed"
Mun daɗe muna hiɗa da ita daga ƙarshe ma itace ta ma ta raka ni na haɗe kayana muka kama hanyar part ɗin mummy duk wannan abun da ake sabit ɗin be ma san anayi ba
Ɗaki guda mummy ta bani, amma sam ban ji daɗin yanayin fuskar ta dana gani ba, ran ta a ɓace sai na ɗauka ko don dawowa ta ne part ɗin nata har na fara tunanin gwanda in sabit ya tattara ya tafi in koma wurin mu
Sai kusan 12 :00 na rana sannan sabit ya shigo da sallamar sa ina ɗakin da aka bani ina kwance ina jin shi yana ƙwala wa mummy kira
"kinga yarinyar nan ta tattara kayanta ta gudu ko naje wurin fannah bata nan, yanzu ina zan ganta"
"ni nace ta dawo wajena don wallahi baka isa da shegen ra'ayin nan naka ba ka kuma ɓarar min da jika ba, kai ba a haihuwa aka haife ka, saboda tsabar ka raina wa asmaun wayo ma zaka ce wani ta zubar wallahi tallahi wani abu ya sake ya samu cikin nan sai dai ka nemi wata uwar ba ni ba ni, na fara gajiya da halin ka da kuma shegen iyayin ka"
"mummy ƙara ta ta kawo ni fa ba cewa nayi baza ta ƙara haihuwa ba ce mata nayi ra bari a kuma yi mata wani dashen kamar na farko, in yaso wannan sai t riƙe, kinga an mata a dalci kenan"
" ba za a kuma dasa mata ƙwan ko wacce ƴar iskar ba, wallahi don ma ka samu asmaun tana da sauƙin kai ne wallahi da ƴata ce da sai ka gane kuren ka duk da haka wallahi sai na ƙwatar mata ƴancin ta daga gare ka, me kake gudu ba kar matar ka ka gano ka ba sallamamme wai matar sa yake tsoro wallahi kaji kunya ka faɗi ƙasa ba nauyi tiƙ haka ka faɗi"
Shiru yayi sam be ɗauka mummyn zata masa haka ba don haka sai ya kwantar da hankalin sa
"haba mummy na ɗan autan ki ne faa, wallahi da an zubar tana watstsakewa za ai mata sabon dashen wannan karon sai ta riƙe" lallai ma sabit ɗin nan ya wuce duk inda mummy take tunani
"jinin asmau me yayi da baza a haihun da ita ba"
"mummy asmau in ta tashi baƙi zata haifa"
"to shikenan zan yadda a zubar mata da cikin in ka yadda da sharaɗi na ƙwaya ɗaya"
Gyara zama yayi ya san halim mummyn sa ai da ya karyar mata da kai zata amince da shi da bishi da yadda so
"idan an zubar da cikin zan je a saka sperm ɗin bature ko balarabe kaga sai ta haifa maka farare tas yadda kake sooo"
Zimbir ya miƙe
"mummy ban gane ba, ya za ayi a sakawa matata sperm ɗin wani kuma ace ɗana ne, wallahi ban yadda ai ba abinda ya haɗa ni da shi" masifa yai tayi ina ɗaki ina cin dariya ni kaɗai
"to menene ba de kai kace baza ka yadda ka haihu da ita directly ba ai dashe dashe ne, in har zata yadda a dasa mata ƙwan wata ta ƙyanƙyashe ai kaima baza ka damu ai mata dashen da sperm ɗin wani ba kooo"
Takaice ne ya ishi sabit yai ta faɗa wai asmaun ce ta jawo shi wallahi ba yanzu yaso ayi wa annur ƙani ba, shi meye da meye
"yo in anyi wa annur ɗin ƙani kai ne zakai renon ko menene"
"wallahi mummy in yarinyar nan bata yadda anyi abinda nake sƙ ba wallahi zan tsame hannuna daga lamarinta, kuma wallahi ta sake ta haifa min baƙaƙen ƴaƴa bani ba su"
"kar ka samu damuwa kana fita lamarin ta sai in saka daddyn ku ya saka ka ka sallame ta ai ba dole bane ita ma taje ta samu wanda zai yi alfahari da baƙaƙen ƴaƴan natan ba kai me man ta kyauta ba"
"mummy kuma me ya kawƙ zancen saki anan"
"kai ka isa ka zauna da yarinya kana muzguna nata ina kallon ka ai an wuce wajen sabit ya ga alamar in ba farkar da kai nayi abin naka sai ya fi haka"
Ya gama bambamin sa yai waje, yana fita mummy ta shigo
"kinji yadda mukai da mijin nakin ko, ai kema asmau da naki don kawai yana ganin kina masa sanya ne shi yasa"
Shiru nayi lallai wannan cikin ya ja mi ƙima a wajen mummy, shawarwa ri ta dinga bani akan yadda zan ƙwatar wa kaina ƴanci in bar zaman da nake yi a wajen sabit
Naji daɗin su sosai saɓanin anty fannah ita tana da sanyi bata taɓa cewa yi mai kaza ba ko tace idan yayi kaza in rama amma mummy ƙiri ƙiri ta dinga zayyano min yadda za ƙwatar wa kaina ƴanci kuma kar in sake ko da was in yadda in kuma bashi wani haɗin har sai ya gane kuren sa
Tunda yayi fishi ya fice be kuma shigowa, nima naji daɗin hakan dom kuwa sam bana son abinda zai haɗa ni da shi
Da yamma sai ga shi da annur, wai yaje gidan su badia ya tarar da yaron yana kuka, mummy ya kawo wa shi wai ta riƙe
"kai dai wallahi kaji kunya zanga randa zaka tattara kan iyalen ka ku zauna waje ɗaya lfy ba tare da matsala ba"
"mummy ni ba komai nake ba kawai ki kular min da shi, ina wannan me hijirar take ne" ya faɗa
"oho maka kafin a tambayi me hijira sai an fara tambayar me shirin zubar da cikin matars mara kunya" ta bashi ansa kasancewar ya san dashi take yasa shi be amsa ba sai ya taho directly ɗakin da nake
Lallashi na ya dinga yi akan in yadda a zubar da cikin wallahi ana zubar wa zai sa badia ta bada ƙwan natan in yaso idan na haihu sai in riƙe
Kallon shi kawai ina ƙarawa
"asmau bana son kizo ki haifa baƙi in dinga nuna masa bambamci tsakanin abinda kika haifa da annur shi yasa don a aguje wa hakan ya sani son ɗaukar mataki da gayya"
Shiru nai masa ya gama soki burutsun sa yai waje daya ga banni da niyyar tanka masa
Da daddare sai gashi da fura da nono na kanti me shegen sanyi, har ɗakin da nake ya shigo ya kawo min kamar gaske
Ina kwance yace min in tashi inci insha, kallon inda yake banyi ba
"asmau ki tashi ki sha furar nan don ke na siyo ta"
"bana sha" na bashi amsa, tabbas furar ta shiga raina amma sam bana son bashi fuskar da zai kawo min rainin hankali
Faɗa ya hau ni da shi wai yaje ya siyo kuma na baɗa masa ƙasa a ido, yadda naga hankalin sa ya tashi ya nace lallai sai na sha ya na sakawa furar alamar tambaya
"sabit ko dai maganin zubar ciki ka saka a cikin furar da ka dage sai na sha"
Masifa ya fara ya na rashin mutumcin sa, miƙewa nayi nima na fara balbala masa masifa,
"wallahi duk abinka sai na haife abinda ke ciki na"
"to wallahi ki haife zaki ga rashin mutunci tsirarrarsa"
Faɗa mukai da shi sosai da sosai faɗan da bamu taɓa yi ba don tun da yake min abu ban taɓa tankawa ba sai yanzu
Wai da yake bashi da kunya bayan mun gama faɗan kuma sai yazo wai yana cewa ni fa ayau anan zan kwana, fita nayi naje na faɗawa mummy inda ta zo da kanta ta kore shi
Babu irin magiyar da baiyi wa mummy ba akan ta bar shi amma ta ƙeƙashe ƙasa ta hankaɗa ƙeyar sa yayi waje muka kulle
Kashegari ya tasa ƙeyar matar sa suka koma ko sallama basuyi mana ba nima sai ya tafi sannan hankali na ya kwanta
[7:15PM, 5/4/2018] +234 806 779 9926: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
*HIKIMA WRITERS ASSO.*
P⃗a⃗g⃗e⃗ 24 🌹
Renon ciki na nake yi hankali na a kwance ga ɗana a kusa dani, sam su sabit basu tafi da shi ba nima na so hakan
Duk wani siyayya mummy tayi haihuwar kawai muke jira, amma saɓanin saɓanin cikin annur wannan cikin girma gare shi sosai da sosai
Har anty fannah tana cewa ko dai ƴan biyu ne, ko da muka je scanning twins ɗin ne kuwa
Muna dawo wa anty fannah ta faɗawa mummy, bashiri mummy ta kwashi anty suka tafi kasuwa aka sake sabuwar siyayya
Cikina yana da wata 8mths sabit suka dawo shida badia, sam duk wannan abunda ake yi badia bata san da cikin ba
Tun da suka zo bamu haɗu da sabit ba, dana ji alamar zai shigo sai in gudu ɗaki duk wannan abun Allah bai taɓa haɗa mu da shi ba
Kwanan su uku da dawo wa ya badia ta zo da kanta lkcn ina ɗaki ina bacci ta ɗauke annur, ita kanta badiar bata san da cikin ba
Ko da na tashi, sai ban ganshi ba, sai na tambayi mummy yana ina sai mummy tace min ai badia ce ta ɗauke shi
Ba badiar ba hatta mummyn ta bani haushi yadda har ta bar badia ɗaukar sa bayan tasan ƙyuya gare shi
"mummy bari inje in ɗauko shi kin san halin annur idan ya tashi be ganni ba"
"to shike nan ni sai da na hanata sai tace wai sabit ne yace ta ɗauke shi"
Ficewa nayi daga part ɗin na doshi part ɗin sabit da tsohon ciki na, a hankali nake tafiya don kuwa cikin yai girma dayawa fiye dana annur
Tun kafin in ƙarasa ciki nake jin kukan yaron nan yana kira na, sai na ƙara ɗaga ƙafa, da sallamat na shiga tana zaune akan kujera tana kallo shi kuma yana zaune a ƙasa a kusa da ƙafar ta yana kuka
Sallamata ce ta sata juyowa, ai kuwa ta ci karo da ƙaton cikina, wani ashar ta daddage ta ɗura sannan ta ƙaraso inda na ke kamar wacce zata dake ni
"uban waye ya miki cikin nan"
Kallon ta na tsaya ina yi yadda take huci kamar zaki, sai nishi take yi kamar wacce take shirin yin dambe
"tambayar ki nayi uban waye yayi miki cikin nan" ban kula ta ba saboda tsayawa ma kula ta ɓata lkc ne ai ta san zaman aure nake yi
Wuce ta nayi na ƙarasa kusa da annur zan ɗauko shi, ji nayi ta jawo ni sai saukar mari naji a fuskar ta, kammm bata ajiye ba nima na kai mata bama ɗaya nayi mata biyu
Sannan nace mata
"kina san ki san wanda yai ciki tooo mijina ne, kafin wannan ma na taɓa ɓari, kafin in haifi annur banza kawai wacce bata san inda yake mata ciwo ba"
Ban ankara ba kawai sai jin matar nan ta hau ni da kokawa tana ihu tana kuruwar
"ƙarya kike yi me sabit zai yi da ke" faɗa sosai mukai da ita
Kasancewar cikin da ke jikina yai min nauyi ya sata samun galaba akai na hai ta kaini ƙasa ta shaƙe ni tare da cewa
"wallahi duk macen da tace zata haihu da sabit sai na kashe ki na kashe abinda ke cikin naki inga abinda za ai min tunda ba wani gata gare ki"
Duka ni kuma na dinga mata inda tana ta ƙoƙarin haye min ruwan ciki Allah ya jeho anty fannah, da saurin ta ta zo ta hankaɗe badiar daga kaina
Tafiya tayi taje ta daki bango wanda har sai da kanta yai ciwo amma sam bata daddara ba kafin anty fannah ta ɗago ni tuni ta yo kaina
Wannan karon da ƙarfi anty fannah ta hankaɗa ta sai kuwa ta faɗa kan annur inajin yaro na ya ƙwalla wata irin ƙara, hankali na ne ya tashi na miƙe da ƙyar na yi wajen sa amma anty fannah ta hanani ta janye ni muka bar part ɗin
Hankalina sam ba a jikina yake ba naso in san me ya samu yaro na amma anty fannah ta hanani
Part ɗin mummy muka nufa anty fannah tana bata lbrin yadda ta ganmu ni kuma ina ce mata annur fa yaji ciwo
"ai dole sabit ya san wannan rashin hankalim da matar sa tayi" inji mummy
"Baki ciwo ba ko" girgiza kaina nayi,
"amma mummy annur kamar ya ji ciwo faaa"
"ina ruwanki da wani annur duk kin bi kin ɗaga hankalin ki akan yaro bayan uwar sa ba sanki take ba"
Kuka na saka musu ni kaɗai na san abinda yake damuna akan irin abinda sabit yake min gaskiya na kai matuƙar ƙarshe a haƙuri
Ganin ina kuka yasa mummy tace min in daina sanna in shiga ɗaki na in kwanta in huta tunda ba abinda ya same ni ita kuma badiar bari sabit ɗin ya dawo za ta ja masa kunne ya faɗawa matar sa ta fita hanya ta
Anty fannah ce ta taimaka min duk da bana jin komai har ɗakin nawa, ban daina de kuka ba, abin ya min ciwo, anty fannah ce ta zauna kusa da ni tana bani haƙuri
"wallahi anty fannah haƙuri na ya ƙare na zo ƙarshe wallahi sai na nuna wa duniya wacece mahaifiyar annur"
"ban gane ba"
Nan da nan na hau mata bayanin yadda aka samu annur, sai da naga tas sannan ta hau ni da faɗa wai nayi wauta ai duk inda muka je bani da gaskiya, tunda ga yadda aka haife shi har kuɗi na karɓa
Kuka na dinga mata ni dai a gaskiya ɗana nake so a hannuna, kukan da nake mata ne ya sa jikin ta yin sanyi, kuka wiwi haka na dinga mata
"yanzu asmau ya kike son in miki"
"ni wallahi in ba barin gidan nan nayi ba wallahi zan iya mutuwa don na gaji da matsalar gidan nan" kuka na dinga mata
Kasancewar tana sanyi ya sa ita ma ta saki kuka, muka haɗa kai muka dinga kukan,
"don Allah anty fannah ki taimaka min"
Kuka ne ya kuma ƙwace mata, mu kai me isar mu muka lallashi sannan ta hau ni da nasiha, ita dama anty fannah haka take sam bata da zafi bata taɓa ce min rama ba
"asmau wannan matsalar ke kika jefa kanki a ciki don haka ki cire annur a ranki ki mai da hankalin ki akan wannan Allah ya raba lfy"
"anty annur ɗana ne don me zaki ce in ƙyale shi"
"ba wai nace ki ƙyale shi har abada ba, amma 4 now ki ƙyale shi"
"wallahi anty na gaji da zaman gidan nan, don Allah ko wani gurin ne ki kai ni in huta in samu in sauka lfy kafin in haihu"
"in banda abin asmau ina kika taɓa jin gidan miji yai zafi, komai aka yi miki haƙuri zakiyi, kuma in shaa Allah wataran zai zama tarihi, dukkan me haƙuri wataran dole ya ga amfanin hakurin"
Kuka na dinga yi tana bani haƙuri tare da cewa ita ba inda zani kawai in zauna in shaa Allah akwai ranar ƙin dillanci, amma don Allah sai yaushe ne zan ga wannan lkcn Lallashi na ta dinga yi tun ina kuka har na zo na haƙura amma wallahi daga yanzu bazan kuma ɗaukar cin kashin shi ba
Sai da ta tabbatar na haƙura na kwanta sannan ta tafi, kuka na kuma fashewa shike nan ni ke nan a haka zan ƙare banni da wanda zai kare min ya Allah ka kawo min ɗauki, bacci ne ya kwashe ni
********************
Sabit yana wajen abokan sa yaji call ɗin badia tana kuka wai ya zo yaga asmau da fannah sun haɗa su ita da annur sun musu duka
A guje ya garzayo ya zo ya tarar da su cikin jini, shi ma kanshi annur ɗin ya kuje a goshin sa
Ita kuma ta ciwo a ƙafar ta yana ta jini, tana ganin shi ta fashe masa da kuka
"sabit kaga abinda asmau tai min, wai don kawai na ganta da ciki na tambayeta na waye shi ne tace nata ne wai zuwa tayi ta kashe mu ni da annur tunda yanzu ta kusa haihuwa bata son ƴaƴan ta su samu ɗan uba"
Sam sabit be fahimci abinda badia take cewa ba shidai kawai kallon annur yake wanda yake kwance a yashe goshi na ta jini
Ɗaukar shi yayi ya shiga da shi toilet ya wanke masa sannan ya fito da shi ya gyara masa ciwon ya saka masa plaster sannan ya ajiye shi
Itama badiar first aid box ɗin ya ɗauko ya gyara mata ciwon nata wanda daga gani wuƙa ce ta yanke da ita
Takaici ne ya hana sabit magana, yana gama gyara su ya shirya su sai da ya tabbatar sun kimtsu sannan ya fito daga part ɗin nasan directly part ɗin mummy ya taho a fusace
Ina kwance kawai naji an janyo ni daga kan gadon na faɗo ƙasa sannan ya shaƙe min wuya tare da miƙar da ni sama sannan sauke min yatsun sa guda biyar a kan fuska ta
Tuni na watstsake na ware ina kallon sa
"sabida baki da mutunci har ki shiga part ɗina ki yi mata ta illa sannan ki cutar min da ɗa........
Be gama ba sai ga mummy ta shigo
"wallahi ko ka sake ta ko in ɓata maka rai"
Wancakar da ni yayi ya fice in da mummy ta ɗago ni sannan tace min
" kiyi haƙuri komai me wucewa ne"
Wucewa wallahi an gama da ni haƙuri na ya ƙare anzo wani abu wai shi d end
Miƙewa nayi na wuce part ɗin anty fannah ina mata kukan ta bani aron kuɗi zan tafi ni na gaji da wannan bala'i
Ta so ta lallashe ni amma da ta ga yadda na rufe ido na sai tace min,
"to yanzu in kika tafi ina zaki"
"wallahi ko ina ne ni dai in tafi kuma wallahi bazan bar musu ɗana ba wallahi da abina zan tafi kuma wallahi ko ki taimaka min ko kuma in tafi ko banni da ko ƙwandala"
Jawo ni tayi sannan ta zaunar da ni kusa da ita,
"kwantar da hankalin ki akwai gidan da zan kaiki ki zauna wallahi sai sabit ya gane kuren sa sannan zan dawo da ke"
Wani sanyi naji ya ratsa min zuciya, sannan nace mata
"to yaushe zamu"
"haba so kike a gano ni na fita da ke, ai ke kaɗai zaki fita da annur akan zaki kaishi asibiti nima idan na fita sai ku haɗu, gidan yayana ne shi da matar sa sai kiyi zaman ki a can har sai yadda hali yayi"
Daɗi naji kamar me na kama hanyar part ɗin mummy na fara haɗa kayana
Duk wannan abun da ake yi mummy bata sani ba, sai dana gama haɗa kayan tas sannan na ɗauko su na kawo su part ɗin anty fannah
Itace ta sato min annur sannan muka kama hanyar barin gidan, ƴar tafiya mukai kaɗan sannan muka iso gidan da zamu,
Amaryace ashe na ɗauka ma babba ce kasancewar dare ne yasa san anty fannah bata daɗe ba ta kama hanyar gida
Ɗaki guda aka bani wanka nai wa ɗana sai alkcn naga cieon goshin nasa
"Allah ya saka maka annur"
Sallah kawai nayi na kwanta sai bacci
*******************
Sai sha ɗaya na dare sannan sabit ya dawo gida yana can yana ta fafutukar yadda zai wa asmau rashin mutunci so yake yi tana haihuwa ya kwashe abinda ta haifa ya kai gidan marayu wallahi bazai zauna da baƙaƙen ƴaƴa ba
Yana shigo wa gidan directly ɗakin annur ya shiga yai mamakin daya ga baya nan don haka sai ya ɗauka ko yana tare da badiar ne
Sai da yayi wanka ya gama komai sannan ya shiga ganin shi kafin ya kwanta, badia tana ta sharar baccin ta amma sam be ga annur a kusa da ita ba
"badia badia ina annur yake"
Cikin magagin bacci tace
"yana ɗakin sa da wuri yai bacci na kwantar dashi"
"ban gane ba yanzu daga ɗakin yake sam baya nan"
Miƙewa tayi itama tare da yin hanyar waje domin taje ɗakin annur ɗin amma wayam kamar sabit ɗin ya faɗa
Nan da nan hankalin su ya fara tashi, kafin me wannan tuni gidan ya ɗauka asmau ta ɗauke annur ta gudu
Mummy sabit hankalin su ya fi tashi, fara neman su akai abin takaici ma shine sam ba a san lkcn da ta tafi da su ba
Sabit kamar yai hauka, kasa zama yayi inda ya shuri motar sa ya fice neman annur don ita asmaun sam baya ta tata duk inda taje ai dole wataran ta neme shi ko don abinda take ɗauke da shi
nema aka dinga yi har tsakar dare sannan mummy ta kira sabit ya dawo gida
Da kuka ya dawo mata
"wallahi mummy sai yarinyar nan ta gane bata da wayo, wallahi sai na haɗa ta ƴan sanda ta sace min ɗa na ta gudu"
Kamar zararre haka ya dinga magana lallai sabit ya shiga tashin hankali, ko da mummy ta nemi ya kwanta ƙin kwanciya yayi a haka ya kwana yana ta trying number ta
Da asussuba ya miƙe ya nufi part ɗin sa yana zuwa ya tarar badia itama ta shirya
"wallahi sabit sai mun shiga kotu da yarinyar nan sai ta gaya min menene dalilin ta na sace min ɗa"
Tanka ta be yi ba saboda yanzu haushin ta yake ji duk ita ce ta jawo sam bata san ciwon yaron ba wai har kana gidan amma a sace yaro sam bata sani ba
Kaya kawai ya canza yana ji tana waya tana faɗa wa mmn ta asmau ta sace annur, takaici ne ya ishe shi yadda yake ta jinta tana ta zage zagen sai kace bamagujiya
Yana canza kaya ya fito zai fita
"sabit ina zaka na ga ka shirya wallahi ko asmau ta dawo min da ɗana sai munyi sharia da ita akan sace min ɗa da tayi sai kotu ta raba su wallahi sai na saka an mana katangar ƙarfe tsakanin mu da ita, duk babu muna fiki sai kai ko kunya baka ji ƴar cikin ka kake kwanciya da ita saboda ka zama sallamamme wallahi kaji kunya"
Har ya fice sai ya dawo, wani kyakkyawan mari ya kwaɗa mata sannan ya juya yai ficewar sa, yana jinta tana zagin sa ta uwa ta uba amma sam ba ta ita yake shi dai kawai burin sa ya ga ɗan sa
Ɓangaren mummy ya shiga ya saka mata kuka, lallashin sa ta farayi sannan ta sanar da shi ai ta aika a gano musu ko asmau taje garin su
Kuka ya dinga mata wiwi
" mummy wallahi asmau ta cuceni ta raba ni da farin ciki na annur shine komai nawa shine farin cikina ya zanyi idan banganshi ba don Allah mummy ki taimaka min, don Allah mumy ki cece ni ki dawo min da ɗana"
Tausayi ɗan nata ya bata, gaskiya asmau bata kyauta ba duk da dai duk abinda sabit yayi mata ai bai kamata tayi masa haka ba
Sallamar hjy munnira suka ji, da sauri mummy ta tashi ta tare ta sabit wanda yake zaune yai shaɓe shaɓe da hawaye ya rarrafa yaje wajen su
"don Allah ina ɗana yake" ya tambaya
Mummy ce ta daka masa harara gabaɗaya sabit ya susuce
"wallahi hjy har garin su aka je bata je, babu wanda kuka san ta sani a garin nan, wallahi tunda kika kirani jiya wallahi hankalina yake a tashe na rasa kwanciyar hankali yarinyar nan a dalilina aka san ta kuma ace ta ɗauki ɗan masu gida ta gudu da shi wallahi tun jiya jiki na yake ɓari"
"wallahi hjy na san bata wajen ki, asmau ce tayi wauta sosai" inji mummy
kuka sosai sabit ya saki kamar wani ƙaramin yari, kunya ce ta rufe mummy kamar ta nutse ƙasa sam be ji kunyar hjy munnira ba, kun san tsakanin ɗa da uwa tun tana masa faɗa akan kukan
Har ya karyar mata da zuciya, ita ma sai ga hawaye, hjy munnira sai ta saki baki tana bawa uwa da ɗa haƙuri
Suna cikin wannan halin ne sai ga ƴen uwan badia nan sun shigo
0 comments:
Post a Comment