Sallama nayi musu amma babu wacce ta amsamin, na maimaita sallamar har sau ukku amma dukansu babu wacce ko kallona tayi bare nayi tunanin zasu amsa min, murmushi nayi tare da cewa aikin banza kare da gudun layya.
Wuri na samu na zauna, ina zama gaba d'ayansu suka tashi suka bar wurin aka barni zaune ni d'aya kamar mayya, banji wani damuwa ba haka banji bak'in ciki ba domin dai nasan gaba d'ayansu nafi su ta ko ina da ko ina, tunda kuwa nafi su ai babu dalilin ni na biye musu muyi gaba, bawai dan ban iya ba na iya kuma idan na fara nawa bashi da kyau....
Ban tashi a wurin ba na haska wayata na fara kwafar lambar Alhaji daga saman takarda zuwa cikin wayata da nayo mishi vidio, nafi minti biyar ina rubutawa karantawa ne dai bana iyawa amma ina kwafar abu, idan kuwa zan kwafa da guda guda nake d'aukarshi, kuma zansa a bud'emin whatsApp amma ya zamar min na "yan gaisuwa saidai duk wanda zanyi magana dashi inyi masa voice note, na ajiye number shi a wayata, abinda na saka mishi shine lamba 1
Mik'ewa tsaye nayi tare da cewa bak'in ciki da fushi ba naki bane Sultana tunda kina da aikinyi, d'aga muryata nayi tare da cewa waye yake san k'amshi mu bashi turare ? Tou tabbas maik'o saidai a barwa balangu ansha gaban mai tsiri......
Kujerata na d'auko na zauna k'ofar d'akina tunda na lura suna neman su haramta min zaman tsakar gidan ne kuma aradu basu isa ba, watsa kunnuwa na nayi ina jiyo firarsu k'asa k'asa bana iya cewa naji abinda akace duka ba amma da yake Saude bata iya maganar sirri ba, bama itama ba duk matan gidan ga haka suke, ji nayi tana cewa ai wallahi ki had'ani dashi in nemi taimako....
Daga inda nake zaune nace hattara dai matar aure, idan dai an ciza a busa, ki kiyayi duniya da rayuwar mutanen cikinta, ita duniya da kika ganta juyi d'an magwaro takeyi yayin daya fad'i k'asa zai kwaso k'asa da tsakuwa, idan kika wanke zak'in zai fita idan kuma kika sha baki wanke ba zaki ci da k'asa duniya tafi karfin kowa, wanda yafiki iskanci yazo yayi ya koma ki kama kanki kuma kiyi k'ok'ari ki koma gaban Allah kina mai kamanta gaskiya, amma na horeki da ki kiyaye darajar aurenki tun kafin duniya ta juya miki baya....
Cikin hayagaga Nana tace ai ba tsoronki akeyi ba a gabanki ma za'ayi maganar dan kutumar ubanki idan kin isa ki hana wani abu in gani, tirr na fad'a tare da cewa kutumar ubana tafi k'arfin kaff zuri'arku wallahi, saboda ko da yake raba kutumar wa mata badai irinku masu tsamin daud'a ba...
Kaina Nana tayo da gudun bala'i kafin ta iso na d'auki kujerata na rik'e nace wallahi kika kuskura kika iso nan saina raba miki kai gida biyu, tsoro ya hanata ta iso taja tayi tsaye, tsoki nayi tare da cewa k'aryar rashin kunya sakarkarin banza daku, insha Allah ko gani nayi zaku shiga wuta saina watsa muku fetir, ina fadin haka na shige d'akina na kyale jahilai, dan gaskiya na lura wallahi jahilci ne kawai yake cizar musu kwalwa, inma banda b'atar basira matar aure za'a kai wurin wani namiji ta nemi taimako.....
*** *** ***
Sati na d'aya kenan bana shiga safgar kowa a gidan da nake haya, ni dama fil'azal magana bai dameni ba, shigowa na ma gidan nan ne naga har na iya surutu idan dai har magana da sune zaisa su raina ni har kowa yake k'ok'orin magana kad'an ya dakeni tou na fita sabgarsu danni ina da wata irin zuciya da idan har na gama da abu tou fa tabbas na shafe labarinsa a babin rayuwata, niko nace hada Dikko Sultana ?
Cikin kud'in da Alhaji ya bani na shiga kasuwa na kwankwaso tsadajjiyar sutura, na siyi kaya na kece raina, gyale takalmi jaka turaruka mayuka na shafawa irin ya wayayyun mata, agogo sark"a da "yan kunne "yan hannu zobuna saida na tabbatar nima na zama gogaggiyar mace ta sahun farko a fanni sutura.
Sannan naje nakai dinki wurin telan da nasan shima yasan hannunshi, kuma da naje kai d'inkin na fad'a mishi cewa irin d'inki karuwai nake so yayi min, nace yamin d'inkin dako tuk'i namiji yakeyi idan na wuce saiya dakaya saiya manta da kan sitiyari yake ya tsaya ya kalleni, mukayi tsada dashi na biyashi kud'inshi tare da sharadin idan fa ya lalatamin kayana wallahi saiya biyani, yace kuma yaji ya yadda.
Na gyara d'akina sosai nasa kayan kallo na sake katifa mai kyau na saka ledar tsakar d'aki na saka fanka amma ta k'asa, na kuma k'ara biyan kud'in haya daga lokacin da suka k'are daga lokacin zan siyi gida haka shine tsarina na gaba... Saina sayi gidan zama sannan zan sayi mota kuma duk zakuji ta inda kud'in zasu rik'a fitowa babu b'ata lokaci....
Hankalina kwance banda wata damuwa, banda rashin ci haka kuma babu rashin sha, cikin "yan kwanaki k'alilan na fara sauyawa, k'oshi babu abinda ya bari dan duk daren duniya sai naci nama abinda nake so ci nake ci kuma duk abinda naga dama shi nakeyi babu mai kwab'a kuma babu mai kyahra, jikina kuwa yasha mayuka gani bana jin wahalar wanka dan ko agwagwa bata kaini san ruwa ba, ya jama'a ku tayani hasko kyau ya had'u da gayu, ku tayani ganin gayu ya had'u da wanka, ku tuno wanka ya had'u da k'amshi...... Wuta Sultana lokacina ya fara...... Kalu bale gareku k"azaman mata.....
Kwance nake saman katuwar katifata da tasha shinfid'a da tsaftataccen zani, { bedsheet } iskan fanka sai kad'ani yake ta ko ina, ga wani ni'imtaccen k'amshi dake tashi daga d'akin har jikina, yanzu tunani na bai wuce in addabi Bello ba abokin Babana.....
Dan yanda ya haramta wa Babana wali a cikin garin shi, inda aka haifeshi ya girma a ciki yayi iyali, amma ya gudu ya bar "yan uwa da "ya "ya da matanshi tou shima katsina zata haramta yayi wali a cikinta, idan kuma yayi iskanci saiya d'aure kayanshi yabar birinin katsinar gaba d'aya....
Hannu na, na saka k'ark'ashin katifa na jawo wata "yar k'aramar kwalba dana anso hannu wani d'an daba, ya fad'amin sunan abun amma wallahi kafin inzo gida har na manta, abun fesawa gareshi kamar na turare, kud'i na bashi ya siyomin nace mishi abinda idan na fesawa mutum kawai zai kama bacci babu b'ata lokaci shine ya kawomin shi....
Tashi nayi na rufo d'akina dan ina so in gwada inga ko abun yanayi, saman katifa na kwanta sannan na fesa shi a fuskata..... Luuu wani bak'i na gani ya gittamin daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba saida 11:30am tayi.....
Salati nayi tare da godewa Allah dana farka na ganni a duniya, d'auko kwalbar nayi tare da sunbatar ta, tabbas kece abokiyar tafiyata, amfani biyu zakimin daga Bello sai Dikko daga nan aikinki ya k'are zan yadaki shikenan.....
Wanka naje nayo tare da d'auro alwalla nazo nayi sallah asuba da ban samu nayi ba, ina gamawa na hau shiri domin yau ba abinda zai dawo dani gida sai nayi ido ido da Bello kuma saina tabbatar da k'udurina akanshi.....
Mai da powder na shafa sai kwalli dana shafawa idona, ban shafa jan baki ba saboda bakina baya buk'atar shafe shafe sai kuma lura da nayi da irin manyan mata mawuyaci kuga sun daddab'awa fuskarsu irin abinda muka shafawa, irinsu jagira aishadow duk basa shafawa shi yasa idan suka shiga wuri suke fita daban, bana buk'atar bilicin koda na kasance ni b'aka ce shima ku lura da kyau bilicin na maciyata ne, d'iyan masu kud'i basa shafe shafe mayuka gaskiya....
Doguwar rigar shadda getzner na saka bak'a, kuma tayi matuk'ar martabani domin dai ta zauna min a jikina ciff na d'aura d'an kwalina coge, na kawo gyale na ida kafe wankan dashi komai dai dana san zai martabo min mutunci na saida na saka a jikina, sannan na yayyafa ruwan turare nayi gaba...
Tun kafin in fito k'amshin turarena yakai tsakar gida, a lokacin dana fito ina rufe k'ofar d'akina kuma gaba d'aya hankalin duk wanda ke gidan saida ya dawo kaina, ina rufe d'aki na saka makulli na a jaka na wuce abuna banma kowa magana ba... Da kallo suka bini domin dai sun gane kura ba sa'ar kare bace ba.....
Tunda na fito gida har nakai bakin titi na zama abin kallo ga jama'a , ban damu dasu ba domin dai duniyar yanzu gaba na bata ba baya ba.....
Napep na tare na fad'a mishi inda zai kaini na shiga muka tafi, cikin "yan mintoci kad'an muka isa, na sauka na bashi hak'k'inshi, majalissar ciki take kamar zata fashe saboda yawan dandazon mazan dake cikinta, ina fitowa napep duk wanda ke wurin idonshi ya dawo kaina...
Banji fargaba ba haka kuma ban daburce ba, banji bazan iya tafiya ba dan ana kallona duk wani bargaba da kunya ko tsoro duk basa tare dani a wannan lokaci, tafiya na farayi zuwa wurinsu na k'addara ma kawai ba maza bane mata ne....
Tsofaffin banza tun daga yanayin kallon da sukemin zaku gane duk sun fad'o rami, kallon tarko suka faramin kamar mage ta ritsa bera. Sallama nayi musu yayin dana isa wurin, kusan gaba d'ayansu saida suka amsa kamar ana biyawa dalibai karatu....
Nima kujera naja na zauna sannan na gaishe su, duka suka amsa cikin sakin fuska, inda Bello yake zaune na kalla tare da cewa Baba wurinka nazo , tou yace amma ban ganiki ba, sadda kaina k'asa nayi sannan na d'an murmusa cikin sigar bariki nace d'iyarka ce ta wurin Aliyu Binna...... Na k'arasa maganar tare da d'ago kaina na kalleshi da kyawawan idanuwa na da suka sha da ado da kwalli nakai karshen maganar tare da d'an sassauta kallo na, sannan na bud'e idanuwan dukansu,
Yashe baki yayi yana dariya kamar yaga wawan zama, sannan yace ahaf tou tou Uwar masu gida ce ? Murmushi nayi tare da cewa Eh, kinyi aure ne ? Ya tambaye ni ? Da kaina na bashi amsa cewa A , a, tou kina ina ne haka ? Ba tare dajin kunyar kowa ba nace ina bariki ne ? Dariya yayi sosai tare da cewa "yar gari kenan yarinya ta gane makoma.....
Nima dariyar duniyanci nayi harsai da kyawawan hak'orana suka bayyana idan dai nayi irin wannan dariya ni kaina nasan tana k'ara min kyau sosai sannan na kalleshi nayi murmushi sai kuma na kama kaina, kallon maita ya bini dashi kamar ya cinyeni a bakin titi sannan yace ina kike zama haka ne ? Ina nan tsohuwar anguwarmu daka sani dai....
Tou taso mana ya fad'a tare da mik'ewa, a raina nace wato tunda na zama karuwa bari a bini a lalace ! Zakaci ubanka domin nima kaina tsoron kaina nakeyi, duk a zuciya ta nayi magana....
'Daukar kujerata nayi muka matsa gaba, zama nayi na d'ora k'afa d'aya saman d'aya sannan nace ya ake ciki Baba ? Am tou aike zan tambaya kinga tunda ga gida ai ba'a kai k'aruwa waje ba....
'Dan gajeren murmushi nayi sannan nace gaskiya kam, amma yanzu kana da mota kuwa ? Eh akwai mota hannuna mana, wace iri ce ? Na tambayeshi yana k'ok'arin fad'amin nace dakata ma barshi kawai kasan ko ka fad'a bazan rik'e ba zan manta ne ,
Duk'owa yayi kusa dani waini zai tambaya yanda muka k'are da Dikko kwanaki, dariya nayi sannan nace ai Dikko ba abinda yayi min kuna tafiya yasa aka dawo dani gida, tsoki Bello yayi tare da cewa kaji sakaran banza wannan tunjumemiyar mace ya bari baisha ruwa ba ?
Murmushin mugunta nayi tare da d'aga girarena nace kila bayajin k'ishirwar ne, tou waike kawai sai kika fara bariki abunki ? Nace sosai ma, tou ya akayi kika zab'i wannan harkar bayan baki san yanda abubuwan suke ba ? Duk zan baka bayani idan kana da wurin saukeni mu tafi kaji komai....
Tou ina zuwa, ya fad'a tare da tafiya wurin abokansu, sallama yayi musu tare da cewa zai dawo da daddare duk zasuji bayani, wani ne daga can yace kayi min register idan ka gama ina layi nima.... D'iyar abokinku maimakon kuyi k'ok'arin d'orani hanya A , a, saidai kuyi k'ok'arin k'ara dilmiyar dani....
A mota ya d'aukeni muka tafi, ko a hanya sai wani kyarma yake yana k'ok'arin kai hannunsa cikin rigata, kallonshi nayi tare da cewa saurin me kakeyi haka ne wai ? Ban bari ya bani amsa ba naci gaba da cewa ko da kayi tunanin yau zaka sameni ? Yace a , a nace tou kasa ma ranka natsuwa har muje inda zamu baje kolin iskancin namu muci karenmu babu babbaka babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani...
Kyah kyah kyah ya kyalkyale da dariya tare da cewa gaskiya ne Uwar masu gida, kunji ihu kura ta samu nama, wannan dariya itace yayi shi ya samu Sultanar banza zaije ya gurji banza a tunaninshi, baisan ni nafi shi iya iskanci ba domin dai ni naci uwarshi nasha ruwan kanwa maganin kwarnahin ciki....
Har muka iso ban sake magana ba, horn yayi mai gadi ya yaye mana get muka shige ciki, parking yayi sannan yace muje, kai jama'a kuji rashin kunya don Allah dan kwatawalci d'iyar abokinka, uhum cije lebona na k'asa nayi sannan nace masa rubutamin number wayarka don Allah a takarda, yo baki da waya ne ? Ya tambayeni cikin gatsali, murmushi nayi sannan nace aini ko a cikin kwarin k'arama ce har yanzu da sauranmu kafin mu gama nuna Baba....
Hahaha a haka ma baki nuna ba ? Nace yo dana nuna ka ganni a napep baki da dama yace tare da fara rubutamin number wayarshi, mik'omin yayi bayan ya gama, yana k'ok'arin fita nace ka sallameni kafin mu shiga mana.....
Dubu biyar ya mik'omin , ansa nayi tare da jujjuya kud'in nace ashe gara da bamu shiga ba, yo Baba banda abunka wannan ai ko kud'in fira baka biya ba, zaro ido yayi tare da cewa dubu biyar ? Ke kin raina dubu biyar ? Murmushi nayi tare da cewa tou turaren dana shafa idan akace maka kayi tukwuici ai kasan nafi k'arfin ka bani 5k , koni ai nayi kyautar dubu biyar wallahi, ka bani kud'i masu yawa idan kana bani kaji malam....
Daga gaban motarshi ya jawo wani wuri kud'i na gani kamar in zabgaga ihu saboda yawansu , saida na gani sannan ya maida ya rufe kin gansu nan kud'in da zamuyi caca ne na had'a gobe na k'ara miki ki anshi 5k in mana...
Babu gardama na ansa muka fita daga motar dukanmu muka shiga ciki, saida ya rurrufe ko ina mu kuma mukayi ma junanmu masauki saman gado..
K'ik'iy k'ik'iy ya cire riga ya cire wando, jakata na bud'e na d'auko kwalbata sannan nayo wurinshi cikin karairaya, yana k'ok'arin rungumata nayi ma shege feshin maganin sauro, babu b'ata lokaci ya tafi bacci rik'eshi nayi har yakai k'asa sannan na cire mishi gajeren wandonshi na dauki d'an iska hoto, nayi mishi kuma vidio ko ina saida na d'auka, bayan na gama na janye shi daga saman hanya, saida na lalube aljihunan shi kaf sannan na zauna gefen gado na shigar da numbershi cikin wayata, bayan na gama na ajiyeshi da lamba 2.
Makulin motar na d'auka da jakata na bud'e d'akin na fita, cikin mota na koma saida na kwashe kud'in nan kaff sannan na rufe na maida makullin kusa dashi na ajiye, fitowa nayi na tunkari hanyar fita daga gidan, dubu biyar d'in daya bani itace naba mai gadin gidan kyauta, yana ta godiya na wuce abuna ban tsaya saurarenshi ba na fice daga gidan abuna..........
20/08/2019
*JAMILA MUSA...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 14
Saida ma na fita daga gidan nakejin wani irin bak'in ciki ya tokaremin zuciyata, wallahi dana iya mota saina taho da motar Bello, zanje gida na jira zuwan shi domin dai nasan nabar baya da k'ura babu yanda za'ayi ya barni na ci kud'in nan , murmushi nayi sannan nayi magana a bayyane cewa Allah ya kawo ka lafiya Baban kwali Baban tusa.....
Ban tsaya wasa ba haka kuma banyi gigin biyawa gidan kowa ba na yanki santa na fara neman gidan da nake kwana....
Tafiya mai zurfi nayi kafin na fito bakin titi, Allah kuma ya taimakeni ina fitowa na samu abin hawa ban wani b'ata lokaci ba, ko ciniki ban tsaya yi ba na afka nace muje.
Inda zamuje ya tambayeni, ni kuma na fad'a masa yaja muka tafi, raina fes zuciyata dunk'ule da farin ciki na isa gida, ko mai napep 1k na bashi yayi ta zabgaga min godiya tare da jawo addu'o'in samun nasara a rayuwata...
Godiya nayi masa sannan na shiga gida da sallama kamar yanda na saba bawai dan zasu amsa min ba, a , a, inayi ne dan fita hak'k'in musulinci, kai tsaye k'ofar d'akina na tsaya na ciro mukulli na bud'e na shige abuna....
Saida na fara adana kud'ina a ma'adana mai sirri sannan na fara neman abinda zanba baba uban ba'u, { ciki } saida na d'ora girkin abinda zanci sannan na fita nayo alwallah dan ganawa da mahalicci na...
Bayan na fito daga bayi ne naji su Saude suna fira kuma ga dukkan alamu zance Dikko ne sukeyi, da wutsiyar ido na kalli wurin, wata bak'ar cikakkiyar buduwarce na gani tsaye, amma ban tab'a ganinta ba sai yau, kallo d'aya zakayi mata ka tabbatar tanaji da hutu domin ta huta d'in, duk inda ta fito yarinyar can d'iyar wani attajiri ne...
Fasa alwallar nayi na tashi na koma d'aki na kashe d'an gass d'ina na d'auko asawaki dan inaso inji inda labarin nasu zai tsaya, dawowa nayi na zauna ban kalli inda kowa yake ba kuma banyi ma kowa magana ba na tusa buta a gaba naci gaba da gogo asuwaki a bakina....
A ` i ce ke cewa kai amma gaskiya Hafsat baki da hankali ai da ki nemi d'an mai kud'i da asiri gara ki tafi tsirara kawai ki huta, kina ganin ubanshi banza ne ? Wannan Dikkon da kike gani tun yana ciki an gama dafashi da asiri yanda Babanshi yasha wahala kafin ya samu namiji kina ganin daya sameshi da wahala zai barshi ne yai ta yawo figifigi a duniya ba tare da an bashi dafa'i ba ? Kai wallahi kimayi hak'uri ,
Cikin muryar sakataccin "ya "ya tace no ai da ina kiranshi wani lokaci yana d'aukar wayata amma yanzu ya daina d'auka kwata kwata, da sauri na d'aga kaina na kallesu sai kuma na basar kamar ina kallon wani wuri, wato ita tana ma da number Dikko, tunani na farayi yanda wayarta zata zo hannuna na, ba ansar wayarta zaimin wahala ba yanda zan gano sunan Dikko shine wahala a wurina....
Kawai gaba d'aya tunanina ma har ya tashi daga d'aukar number, kawai harma na hango gani nan na d'auko tsiraicin Dikko na balbad'a a social media, tabbas Dikko saina had'a shagalin partyn wulak'anta mishi rayuwa.... Tunani na ya dawo ne a lokacin da naji Saudatu na cewa aiko ki dage yarinya dan nan da shekara d'aya Dikko baya rik'uwa, tunda shi dama bai dogara da kud'in gidansu ba gaskiya Dikko yana da sa'ar rayuwa idan kika auri shi kin more rayuwa domin dai cikakken namiji ne...
Banyi musu magana ba dai naci gaba da goge hak'ora na, wayau sukayi ma Hafsat suka amshi kud'i masu yawa a hannunta da sunan za'ayiwa Dikko asiri, ci gaba da tattaunawa sukayi amma hankalina baya wurin firarsu ya tafi wurin karatun halayyar Hafsat, tab'e bakina nayi a bayyane nace itama dai "yar mad'igon ce { Lesbian }
Kallona tayi nima na watsa mata mayatattun idanuwana masu sa mutum ya rikice na k'ura mata su sosai domin ina so ta yabani idan har ta shigo hannu na nice zan koya mata barikin da zata kawo min Dikko k'asan k'afaafuwana nima in rama wulak'anci da yayi min dan nayi alk'awari nima sai Dikko ya lashi k'afata kamar yanda yasa na lashi tashi...
Shegiya ta kuwa daskare ta kasa barin kallona, kyakkyawan murmushi nayi mata tare da cewa sannu ko ? Na k'arasa maganar tare da d'an wasa da idanuwana... Murmushi tamin tare da cewa ya kike ? Ban bata amsa ba naci gaba da alwallata...
Ina gamawa ban sake bi ta kansu ba nayi d'aki inajin tana ta magana amma na basar da ita, nadai juya ta ganni maza ma sun gani sun rikice ina ga mata mayun mata kuma ?
Ina shiga na kunna gas ina na kabbara sallah. Bansan yanda suka k'are ba, amma nasan tabbas saita dawo saboda taga ina da irin k'addarar da suke nema...
Bayan na gama sallah na zuba abinda zan dafa a tukunya sannan na zuba ruwa na tafi wanka, lokacin da nayi wanka na dawo har ya dahu, dan haka kashe gas ina nayi sannan na shafa mai da powder, d'aurin gaba nayi sannan na zuba abinci na naci gaba daci....
Bayan na gama duk abinda nake na kunna kallo, sannan na saka kayan bacci na koma saman katifa na kame kamar d'iyar wani shege... Kai gaskiya inajin dad'in wannan rayuwa tawa, saida na kwanta sannan na bud'e data ta, lamba d'aya na gano bayan na ganoshi na tura mishi vidion dana d'auko , tare dayin voice note na tura mishi. Ina turawa na sauka online na kashe wayata gaba d'aya, na kashe kallo na rufe d'akina nayi kwanciyata.......
Tashin hankali shine kalmar da Alhaji ya fad'a a lokacin da yaga vidion dana tura mishi, wata irin gagarumar zufa ta yayyafo mishi a lokacin da ya saurari voice note ina, tashi yayi tsaye cikin tsananin tashin hankali ya rasa gane a wace rayuwar yake rayuwar mutuwa ce ko ta duniya ?
A gefe kuma wayarshi ce take ta kwarara ihu, lambar mai gida Dikko ce keta tsalle babu k'ak'k'autawa amma Alhaji yau kam bata Dikko yake ba, saida kiran ya tsinke sannan Alhaji ya sake kunna maganar Sultana yana sauraro, ga abinda take cewa....
_Ina mai farin cikin sanar dakai wannan mummunan labari, d'abi'a na ne yin albishir da farin ciki yayin fad'ar abu mai munin gaske, kuma nakanyi farin ciki yayin fad'ar abun farin ciki, wannan vidion dai dani dakai ne a ciki kuma kaga irin bad'alancin da muke aikatawa a ciki, nidai banajin komai idan wani ya gani domin ni iyayena tuni sun sallama ma duniya ni, saboda haka ni duniya itace uwata kuma itace ubana, idan na yad'a wannan vidio banajin komai tunda biye nake da mutanen cikinta ina basu, nayi tunanin maidashi faifayin filet na sidi dan in siyar na samu kud'i , sannan kuma in watsashi a yanar giza gizo dan inyi suna, kai kuma kana da dama d'aya tak data rage maka, idan har ka bani naira miliyan d'aya nayi maka alk'awari zan goge shi sai in hak'ura basai nayi suna a duniya ba...... Idan kuma baka dasu in turawa "ya "yanka ko suna da kud'in fansar ka ! Sultana, Sultana ce yarinyar mai dogon zamani, idan kuma kace zakayi gigin sako hukuma a ciki na riga dana turama k'awata nace da taji an kamani firr zakaji su sun watsu a duniya kamar saukar tsuntsaye. Ka huta lafiya habibinah muah_ 💋
Goge zufa Alhaji yayi tare da cewa Allah ka tsinewa yarinyar nan albarka, shegiya tsinanniya ubanta da uwarta basuyi addu'ar kwanciyar aure ba yayin da zasu kwanta Allah ya basu cikin d'ebabbar albarkar yarinyar nan, a daidai wannan lokacin kiran Dikko ya sake shigowa.
Jiki a sanyaye Alhaji ya kalli wayar tare da cewa mai gida kayi hak'uri wannan abun kunya ina za'a dashi na watsu cikin duniya ina zina, abun bak'in ciki da d'iyar da nayi d'iya da ita, garin ciye ciye na har naje na ciwo ma kaina bala'e, kila sai ta k'arar da arzik'ina, kuma tace idan na fad'awa hukuma taba k'awarta vidion zata yad'ashi wannan shine ciwo ya riga ajali zuwa...
Kuka Alhaji yayi tayi tare mitar ya shiga 3 ya bani ya lalace, wannan labarin abun kunyar waye ma zai fad'a mawa bare kuma yasa ran zai samu wata sahihiyar shawara, kai ya bani ya bani ya bani........😰🙆🏻♂😭, a daren nan Alhaji baiyi bacci ba kuma baibi kiran Dikko ba, wayar Sultana kuma ya kirata yafi so adadin yawan dutsinan da ake jifar shedan dasu amma maganar dai d'aya ce cewa a kashe.......
Da safe , tunda nayi sallar asuba na koma bacci, can cikin bacci naji ana dukan k'ofar d'akina, addu'ar tashi daga bacci d'auke a bakina bayan na gama nace waye ? Na tambaya cikin muryar bacci tare dakai idona saman agogon dake lik'e a saman bangon d'akina k'arfe 10:36am, cikin muryar murna Nana tace "yan sanda aka d'auko miki Sultana....
Murmushi nayi tare da jawo wayata na kunna sannan nace ma Nana da Allah kije kice waye ya d'aukomin "yan sanda ? Cikin farin ciki ta koma zaure sannan ta tambayi d'an sanda waye yake k'arata ?
Fad'a mata yayi tayo cikin gida da har yanzu tanajin dad'in k'arata da akayi, a bakin k'ofar d'aki ta tsaya sannan tace wai abokin Babanki Bello, jinjina kaina nayi tare da cewa tou ina fitowa....
Data na bud'e na nemo lamba 2, hotunan dana d'auke shi jiya na tura mishi tare da yin voice note na antaya ma banza, ina gamawa na kashe wayata, saida nayi wanka naci gayuna na watsa turare na d'auku iyakar yanda hankali baya tunani duk wanda ya ganni saina burgeshi, fitowa nayi banma kowa magana ba na tunkari zaure, dan zuwa wurin hukuma a yanayin talauci yana jawo ma mutum raini....
A k'ofar gida na samu d'an sandan nan ya gama shak'e b'acin rai daga gani yana jira muje can yaci uwata, a yangance na fito cikin aji na kalleshi tare da cewa "yar labai barka da aiki......
'Dan sakin fuska yayi tare da cewa yawwa, gaishe shi nayi tare da ce masa nice Sultana, kallona yayi sama da k'asa sannan yace tou hajiya muna gayyatarki zuwa ofishinmu ai anyi miki bayanin mai k'ararki ko ? murmushi nayi tare da cewa babu damuwa muje amma Allah yasa ba'a cikin motar "yan sanda zaka d'aukeni ba, murmushi yayi tare da cewa ai hajiya napep zamu shiga, ajiyar zuciya nayi cikin sigar jan hankali sannan nace tou ai har naji natsuwa.
Napep muka hau muka nufi c p s , kuma nice na biya kud'in 1k ne na bayar kuma daya anso canji nace ya rik'e yasha ruwa, tunda muka fita a napep gaba d'aya wurin saida hankalin kowa ya dawo kaina, na farko dai ga wanka ga gayu ga k'amshi uwa uba kyau Allah yayi min kyawun da mutum baya gajiya da kallona, ga gashina na tik'ashi nayi mishi wani irin parking irin na wayayyin mata, baka isa ka rainani ba ko waye kai domin sitirar dana saka ita kad'ai ta isa ka gane ni ba sa'ar wasan yaro bace ba.....
Ofishin d c o muka nufa, a ciki na samu Bello zaune tare dashi da wasu abokan Babana, sallama nayi sannan na gaishesu dukansu cikin kyakkyawan yanayi, bayan mun gaisa nima na samu wuri na kame kamar yanda naga kowa yayi.....
Kallona d c o yayi bayan ya gama karanta wata takarda dake gabanshi sannan yace Maryam miya had'aki da Bello ne ? Murmushi nayi tare da gyara zamana nace ranka ya dad'e ai Baba Bello abokin kasuwanci ne, halak'a ta mutunci ne a tsakani na dashi bayan wannan babu komai....
D C O yace tou jiya ina kika had'u da Bello ne ? Ranka ya dad'e majalissar su naje gaishe su, bayan mun gaisa kuma ya tambayeni nayi aure nace masa A , a, yace yanzu ina nake zama ? Nace masa ina zama a tsohuwar anguwarmu daya sani, ya tambayeni ko ina kasuwanci ne ? Nace masa Eh yace me nake siyarwa ranka ya dade nace masa karuwanci nakeyi, tsakanin mai saye da mai siyarwa ai babu fushi anan muka daidai suka d'aukeni muka tafi wani gida, nuna yawan duka abokan Babana nayi sannan naci gaba da cewa ranka ya dad'e dukansu nan babu wanda baiyi ba kuma duk saida suka k'ara zagayawa "yar labai, kuma gasu nan ka tambayesu idan nayi musu k'arya. Kuma cikon kud'in ma har yanzu basu bani ba..
Kowansu zaro ido yayi tare da dafa k'irji cikin yanayin mamaki yace ke mune mukayi iskanci dake ? 'Daure fuskata nayi kamar gaske nace aini banajin kunya tunda dai banji tsoron Allah ba nayi zina wallahi banajin kunya gaban kowa in fad'a nayi, kunyi mana ko k'arya zan muku ne ? Lokacin da bakuyi ba nace kunyi ?
Gaba d'aya wurin hayaniya ta tashi har bakajin bakin wani, d c o ya dakatar dasu tare da cewa suyi mishi shiru, bayan kowa yayi shiru ya kalleni sannan yace ke Sultana Bello yana tuhumarki kud'in shi da kika d'auka. Cikin natsuwa nace wasu iri kud'i kuma ranka ya dad'e ?
Bayani d c o yaimin kamar yanda na sani, jinjina kai nayi tare da cewa idan sun gama k'arata nima zanyi k'ararsu saboda b'atamin suna da sukayi, ranka ya dad'e a gaban idon waye na d'auka kud'in ne ? Nifa bana sata amma ina neman maza gaskiya, duk abinda nakeyi bana jin kunyar asan inayi domin dai duk sana'a sunanta sana'a, idan ma na d'auka aka tambayeni idan nasan na sata kawai zan dawo musu da kayansu in basu hak'uri tunda karuwanci da nakeyi ai ban b'oye ba na fad'a tunda ba abun kunya bane....
Tambayar Bello D C O yayi ko yana da wata sheda ne ? Baida ita tunda an tambayi mai gadi yace shidai bai ganni cikin mota ba, duk iyakar binciken da akayi dan asamu wata sheda babu ita, dan haka aka rubuta takarda cewa an janye k'ara, bayan an gama rubutu aka bani na saka hannu da larabci nayi sigining ina, an mik'e za'a tafi nace ma d c o naga fa sunamin wani kallon hadarin kaji sufa fita ido na, d c o yace ai duk an rubuta, nace to ranka ya dad'e cikon kud'ina kuma sai yaushe zasu bani ?
Hak'uri d c o ya bani tare da nunamin tunda anyi masa sata inyi hak'uri inma barshi da ramuwar biyan kud'in mutane, babu kunya ba komai nace kenan ni yanzu ranka ya dad'e sunci banza ? Duk wanda ke cikin office in saida ya kalloni, nace ranka ya dad'e kafa duba lamarin nan gaskiya ni ba'amin adalci ba, shiru wurin yayi wutar kowa ta d'auke, murmushi nayi tunda basu da amsa nace nawa ake yankar sammaci ? Sammaci ma ake cewa abin ko miye ?
A kotu ake yankar sammaci d c o ya bani amsa tare da fad'amin abinda ake kiran nasu da turanci, oho dai da yake kan baya ganewa kasa maimaitawa nayi saidai kawai nace nawa ne ? Kud'in aka fad'amin na bud'e jakata na bada sannan nacewa d c o ga wanda nake k'ara nan Bello ina tuhumarshi akan b'atar mahaifina daya tafi babu wanda yasan ina yaje..........
21/08/2019
*JAMILA MUSA...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 15
*_Had'inkai group ina tare daku aminan albarka, Allah yabar so da kauna ubangiji ya k'ara yadda da aminci, HALIMATU SADIYYA {{ Leema }} HABIBA IDRIS {{ Hubbie }} HAUWA'U USMAN {{ Smasher }} MAIMUNA O . G {{ Aunty Munari.... }} muna tare_*
*_Mrs Abdul-aziz ina godiya sosai da dogon sharhi kuma ngode sosai page 14 na baki shi kyauta...._*
Lahaula walakuwata illah billah, kiji tsoron Allah ke uwar masu gida a ina na b'atar da mahaifinki ? Sharri zaki min ? Kiji tsoron Allah in babu nan akwai ranar hisabi duk wanda yaci zalin wani daidai da kwayar zarra ubangiji bazai barshi ba, ki daina ganin kin samu dama ta tak'in lokaci yasa ki manta da rayuwar gaba, karki biyewa zuciya ki kafa abinda zaisa kiyi nadama wata rana.....
Gaba d'aya jikina yayi sanyi tsoron Allah ya kamani nasan k'azafi da sharri ba abu ne mai kyau ba, kuma addini na bai koyar dani haka ba, amma d'an kamewa na sakeyi sannan nace ni rayuwar dad'i baza ta tab'a zama takaitacciya a wurina ba, jin dad'i na d'aura insha Allah daga nan har zuwa ranar da numfashi na zai k'are, ina Babana yake wai ina ka kaishi ne............?
Cikin nadama Bello yace na rantse da ubangiji daya bani aron lumfashi ya bani aron lafiya nake ganinki nake kuma saurarenki ya bani hankali da tunani idan nasan inda mahaifinki yake Allah ya tsinemin albarka. Wallahi Uwar masu gida bansan inda ya tafi ba na rantse miki da girman Allah. Tausayi ya bani yana rantsuwar yana wani kwantar dakai kamar an ritse macen da tayi cikin shege ta haihu kuma ta kashe d'an....
Kallon D C O nayi tare da cewa "yar labai shikenan tunda yayi rantsuwa baiyi ba kawai na janye, zan iya tafiya ? Na tambayi D C O, cewa yayi na zauna zamuyi magana, zama nayi su kuma su Bello aka sallamesu suka tafi ni kuma naci kud'in banza Ehe....
Ta wutsiyar idona na kalli d c o bayan fitarsu Bello domin ina son na gano tashi manufar a kaina, murmushi nayi bayan na gama fahimtar shi, a bayyane nace lamba 3 tazo kenan, ajiyar zuciya ya sauke tare da tattaro duka hankalin shi wurina yace ranki ya dad'e ya hak'uri da jama' a ? Kallonshi nayi ba tare da nayi magana ba domin wallahi tsarin bakinshi kwata kwata bai burgeni ba. Amma ba komai zan hak'ura nayi maleji dashi haka nan saboda idan na taro watan aug zai gina min gada nabi na wuce ba tare dana sha k'ashin ruwa ba....
Wayan cewa nayi tare da gyara zama na nace Allah dai yasa aiki zaka d'aukeni mai girma d c o, murmushi yayi tare da komawa ya kwanta saman kujerarshi irin masu juyawa d'in nan, sannan yace wai gida zan saukeki idan ba matsala, d'an yamutsa baki nayi tare da cewa na gode amma ni ba gida zanje ba...
Ina zakije haka da rana ? 'Daure fuska nayi dan ya fara cika min ciki nace wurin aiki zanje, wane irin aiki ? Tsoki nayi tare da cewa kai komai sai anyi maka b'aro b'aro kake ganewa ko ? Tou abokin lalata zanje nema.....
Murmushi yayi tare da cewa ke bakya gajiya ? Cikin wuta wuta nace ka tab'a ganin inda mutum yake rayuwa babu abinci ? Yace a , a, nace tou ni da kud'i da karuwanci sune abokan rayuwata, domin sai nayi nake samu sannan naci nasha na kuma d'aura har in fito na burge abokan harka , idan kuma kaima d'an hannu ne karka wani cuci kanka kawai kayi magana idan kajira sai an maka tayaki tou fa lallai zaka kwana da yunwa, amma kayi hak'uri da tambayar da zan maka tsakanin ka da Allah nawa ne albashin ka...... ?
Kallona yayi tare da cewa hajiya maryam kenan , miya shafi albashi da harkar bariki ne ? Bai shafa ba amma ni ina duba nasabar namiji da cancantar shi kafin wata sahihiyar mu'amula ta shiga tsakani na dashi, dan duk wanda ya jawo maganar aure a rayuwarshi tabbas ya tara abun hidima, bata yuwuwa na biye maka ka k'ok'ar dani ba tare da ka sake bani kud'in da zan sabon fenti ba, dan kai kanka da ban d'aukar maka ido ba duk yanda nake barikin baza ka taya ba,
Kallon agogon dake d'aure a tsintsinyar hannu na nayi tare da cewa zama wuri d'aya tsautsayi inji kifi, malam d c o zan wuce ka rubutamin number ka a jikin takarda idan ayyuka sukamin sauk'i akwai dawowa......
Babu musu kuma ba tunanin komai ya d'auki biro da takarda ya gwagwad'amin number wayarshi, ansa nayi tare da mik'ewa tsaye sannan nace sai ka jini, baki bari mu tafi in ajiye ki ? Ya tambayeni, juyawa nayi na fara tafiya tare da cewa ban hawa mota sai napep a daidai lokacin dana fice daga ofishin....
Ina fitowa wuri na samu na tsaya, wayata na fiddo nayi saving in no d c o da lamba 3 , sannan na kira wayar Alhaji, babu b'ata lokaci ya d'auka tare da cewa ranki ya dad'e tun jiya inata kiran ki wayarki a kashe ko yau da safe ma na kira a rufe.... Ban bashi amsa ba nace kawomin kud'in yanzu nan ina nan c p s ina jiranka kuma karka b'atamin lokaci, ina fad'a na kashe wayata......
Lambar Bello na kira amma bai d'auka ba, daga kira d'aya nima ban sake kira ba, domin dai nasan idan yaga abunda na tura mishi shi da kanshi zai nemeni, k'ok'arin maida wayata nake cikin jikka naji ana cewa shegiya k'awata kece kika koma wata hajiya haka ? Da sauri na d'ago kaina domin jin muryar Amisty da nayi...
Cikin farin ciki muka rungume juna, bayan gaisuwa sai kuma muka shiga firar duniya, yayin da nake tambayarta wane ci baya ta samu na bariki naga har yanzu bata fara hawa mota ba, ajiyar zuciya Amisty ta sauke tare da cewa kinsan mazan babu kud'i hannunsu kullum tsuwwa da kukan babu......
'Daure fuska nayi tare da cewa waye ya fad'a miki ana hawan jirgin sama bashi ne ? Ai filin jirgi ma baka shigarshi dole sai kana da tikitin tafiya, haka nan kike basu suna hayewa basu baki kud'in mai, tou ina uwar d'akin taki ne ko bata nan bata fad'a miki illar maza ba ? Haba Amisty idan baki ridowa da yawa wallahi bariki kasheki zatayi, niko kin ganni nan ni zanyi gwanjo bariki kafin ta wurgar dani gefen titi, kinsan bariki bata da tabbas d'auka da ajiyewa gareta, ni zan kashe bariki bazan yadda ta kashe ni ba, zanyi amfani da talata ta kafin laraba ta, ta riskeni, wannan uwar d'aki taki k'atuwar jahila ce batayi karatun komai ba haka nan ta tara yawan dalibai, har yanzu kuna da dama ki nemi canji makaranta ki dawo makaranta ta zan baki ilimi akan namiji, kud'i kike so ko suna ......?
Horn Alhaji yayi da mota wanda tun d'azu yakeyi amma magana ta hana na saurareshi, juyawa nayi tare da nuna mishi da hannu ina zuwa, ni kuma naci gaba da magana da Amisty, wata matace ta fito daga ciki tayo wurinmu kuma ga dukkan alama tare suke da Amisty, gaisawa muka yi yayin da Amisty ta fara tambayarta ya aka k'are, basu bani labari ba suna ta maganar ne cikin munafinci, ni na fahimta suna magana ne kamar tayi ciki..
Datsar maganar nayi da cewa keko ya akayi kikayi cikin shege ? Gaki a fuska kamar wayayya taya akayi haka ta faru ? Ita kuma a tunaninta Amisty ta fad'amin dan haka tace kin gane ni bawai cikin bane matsala a, a mijina yau watanshi bakwai baya nan kuma ga ciki wata hud'u, kuma nayi a zubar da cikin shi wanda yayi cikin yace wallahi bazai yadda ba saboda bai tab'a haihu ba, idan wannan abu ya fito ai kinsan akwai matsala.....
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un na fad'a tare da cewa ke matar aure kike zina ? Hasbinallahu wa ni'imal wakim, amma kinyi k'atuwar asara, kallon Amisty nayi tare da cewa zance zaune ba na tsaye bane idan kuna neman taimako ku sameni gida, ina nan tsohuwar anguwarmu idan kika shigo ki tambayi gidan da nake haya za'a kawoki, ina fad'in haka nayi wurin motar alhaji ina zuwa na kama na bud'e na shige nace muje...
Har muka isa gida banyi ma Alhaji magana ba domin ni yau naga macen da tafini kafirci kina k'ark'ashin bautar aure amma kina aikata sab'o, wannan wai wane irin zamani ne muke ciki lallai ya kamata nasan ita kuma wane rud'un duniyar ne yaja mata neman mazan waje ga nata mijin da yake hak'k'inta amma ta tsallake shi ta tafi wurin na wasu , gaba d'aya jikina yayi sanyi kuma na dawo daga rakiyar duniya....
Ansar jakar da Alhaji ya zubomin kud'i nayi tare da direwa daga motar, zaiyi min magana nace mishi muyi waya kawai nayi gaba abu na, lokacin dana shiga gida bana ko ganin gabana saboda bak'in ciki da kishin aure, d'akina na bud'e na shiga, saida na adana kud'ina sannan naje nayo alwalla nayi sallah azahar, yinin ranar haka na yini sukuku kamar wata mara lafiya, koda nayi sallah isha'i kwanciyata nayi , duk yau banda ruwan shayi babu abinda ke cikin cikina, haka na kwanta da tunani iri iri, ko bacci nayi na farka abun yakan fad'omin a rai har gari ya waye da tunanin matar nan a zuciyata..
Da safe bayan nayi kalaci na gyara d'akina naje nayi wanka na shirya cikin doguwar riga ta atamfa da tasha d'inki buba, hula mai raga { net } na saka kaina na fice tsakar gidan....
Kujera na sa a k'ofar d'akina na zauna tunda fitowa wajen ya zamar min dole, kallon inda Karima take nayi sannan na maida kallo na wurin Saude dake zaune saman turmi, babu ko breziya jikinta kuma babu kaya sai siket ondie da taja saman kirjinta, amma komai na halittar ta babu abinda ya b'oye duk a bayyane yake.....
'Dauke idona nayi gefe na kallo inda Nana take kwance A ` i tana durk'ushe ta duk'a samanta sosai suna k'ushin k'ushin, jinjina kaina nayi sannan na sake kai idona wurin Saude nace ke Saude wai da Allah in tambaye ki ?
Murmushi tayi tare da cewa tambayarni kanki tsaye, b'ata rai nayi sosai sannan nace nan gidan ubanki ne wai da zaki zo ki rik'a zama mana tsirara dan baki da kunya ?
Gaba d'ayansu dariya sukayi ,sannan Saude tace tou ke mai tambayar gidan ubanki ne ? Ni nan ba gidan ubana bane amma ya zama na ubana tunda na biya kud'in haya, d'aki d'aya na kama amma ina da hurumin da zan sauke ubana a ciki, ke ko fa ? Nana ta anshi maganar da cewa yanda kike tak'amar kin kama haya muma kamawa mukayi kuma muma muna da hurumin da zamu kawo mutanen da muke so su zauna tare damu, kedai kawai kice kina so ayi dake.
'Dan gajeran murmushi nayi tare da cewa duk wanda yaci naman arne tabbas zai iya cin mushen alade , banda abinki miya had'a makaho da ganin wawan zama ? Ni bana iya cin naman jaki amma idan na samu doki zanci duk da an yanka shi nasan wata rana zanyi hazaka, ko banyi gudu ba tabbas nasan zanyi tafiya, magana ce na fad'a miki a jimlace idan kina da ilimi sai ki warwareta banzanye da ku masu wahalallen bariki.....
Gaba d'aya wutar kowa d'aukewa tayi sukayi shiru babu wanda tace komai, murmushi nayi tare da cewa ba'a bariki dole saida ado kuje ku ibi ruwa kuyi wanka kusa toka ku wanke baki ko ya rage k'annin koko, daga haka ban sake ma kowa magana ba kuma suma babu wanda ya sake cewa komai,
Bayan Alhaji ya bani kud'i ya dad'e k'ofar gidanmu ya kasa tafiya, hankalinshi a tashe saboda yaso yayi magana dani na goge vidion nan kuma yaji ina na dosa ? Amma samsam ban saurare shi ba, kuma yasan lallai saina sake tambayarshi wasu kud'in tunda akwai vidio a hannuna ban goge ba,
Rasa yanda zaiyi yayi zuciyarsa ta yanke mishi kawai ya fad'a wa Dikko komai yasan babu mai iya magani na saishi amma fa a nashi haukar , d'aga waya yayi ya kira Dikko kuma har zuwa wannan lokacin yana k'ofar gidanmu bai tafi ba.
Bayan Dikko ya d'auki waya Alhaji ya gaishe shi cikin girmamawa kamar yanda ya saba, Dikko ya amsa shima cikin mutuntawa, dan a haife Alhaji ya haifi Dikko amma igiyar naira tasa yana k'ark'ashin Dikko kuma k'asan k'asa ma, dan ubangidan Alhaji na ainahi shima yaron Dikko ne na biyu, tou abinda yasa Alhaji yake kiran Dikko kai tsaye saboda yanajin dad'in yadda yake kularmishi da dokunan shi, shi yasa shi Dikko da kanshi ma ya anshi number Alhaji ko wata matsala ta taso ga dokunan shi, dan dama ubangidan nashi na farko kafin yasan Dikko wurin kula da dokuna ajiye shi Alhajin....
Alhaji yace mai gida kayi hak'uri don girman Allah wallahi jiya daka kirani ina cikin yanayin da bazan iya magana ba, cikin jimami Dikko yace meya faru haka ? Wato ranka ya dad'e ina cikin tashin hankalin dana zab'i mutuwa ma da rayuwa, salati Dikko yayi tare dayin murmushi domin shi yaji mugunta, sannan yace Alhaji duk dad'in duniyar wato tai maka d'aci ko ? Alhaji yace Eh wallahi ranka ya dad'e, Dikko yace tou Allah ya kyauta...
Da sauri Alhaji ya fara bayani wa Dikko dan yasan daga Allah ya kyauta kawai zai kashe wayarshi ne yasan baya doguwar waya, ranka ya dad'e wato wallahi wata yarinya ce muka d'an keb'e da ita, tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya dad'e tana d'auka cikin waya ban sani ba, tou ta rik'e vidion sai wahalar dani takeyi tana ansar kud'ad'ena, yauma na bata kud'i kuma a police station nakai mata kud'in inaji wani ne ya d'aure mata gindi take iskanci a garin nan....
Murmushin mugunta Dikko yayi tare dayin kamar bai gane ba, yace wane irin vidio ne ? Gyara zama Alhaji yayi tare da goge zufa yace wato ranka ya dad'e harka daice irin wadda muka saba, Dikko yace wadda ka saba dai , wato ka samo daidai dakai ko ? Tou turomin vidion in gani ya fad'i maganar cikin sigar zaulaya, Alhaji yace ranka ya dad'e vidion fa irin na kafirawan nan ne masu d'aukar tsiraicinsu suna yayad'awa a duniya.......
Dikko yace tou banda abunka kace taje ta yad'a ba hada ita a vidion ba ? Alhaji yace ranka ya dad'e ina za'ayi wannan abun kunya tsiraicina a yanar giza gizo cewa tayi fa har "ya "yana zata tura su gani, Dikko ya gaggab'e da dariyar mugunta tare da kashe wayarshi, irin wannan abun Dikko kadai yake ma dariya a duniya, duk abin burgewa ko na nishad'i Dikko baya mishi dariya kuma baya murmushi idan kaga murmushin shi ko dariya yaji ko yaga k'eta, amma kai kana iya ganin abinda zai baka tausayi kayi kuka wallahi Dikko sai yayi mishi dariya saboda tsabagen shi cikakken mugune....
Cikin sanyin jiki Alhaji yaja motarshi ya tafi, Dikko kuwa saida yasha dariyarshi ya gaji sannan ya sake kiran Alhaji, bayan ya d'auka yace tou waikai kawai sai tayi maka vidio ? Alhaji yace Eh ranka ya dad'e Dikko ya sake shek'ewa da dariya sannan yace kai amma wallahi yarinyar nan tantiriya ce ta fad'a a duniya,
Dikko yace tou yanzu me kake so nayi maka ne ? Alhaji yace ranka ya dad'e so nake kayi min maganinta, dariya Dikko yayi sannan yace nima so kake ta d'aukeni ? Cikin biyayya Alhaji yace haba ranka ya dad'e kada Allah ya had'aka shegiyar yarinyar nan.....
Dikko yace aini ko ta had'u dani bata da yadda zatayi dani, nidai bana neman mata kuma bana sabgarsu bana shiga huruminsu gudun raini, kayi hak'uri insha Allah zanzo katsina jibi idan Allah ya kaimu zata goge vidion dan wahala, ranka ya dad'e ai tace ta turawa k'awarta ne, Dikko yace k'arya take kadai jira zuwana .....
Godiya Alhaji yayi sannan sukayi sallama da Dikko,
Murmushi nayi a daidai wannan lokacin sannan nace duk mai niyar yin magani na nice zanyi maganin d'an banza, zomon bana shike maganin karen bana, maganin d'an iska kuma karen maguzawa, dani dakai dashi mu zuba duk wanda ya fasa yaci k'aniyarshi.......
Sallamar Hafsa ce da wasu zugar tantiran mata, a ciki kuwa harda Amisty, kila sunzo ne suci min uwa tunda nace uwar d'akinsu k'atuwar jahila ce, oho koma dai miye su shigo ina jiran isowarsu wurina inji su kuma da wace suka zo................???
22/08/2019
Taku a kullum mai san farin cikinku wato .
*MEELAT MUSA*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 16
*_Bandai ji komai ba , 71 , 29 babu damuwa zamu rama muma..._*
_____```^^=°°--- Basarwa nayi tare da d'auke fuska ta daga dubansu, mutum dai bai isa yazo har gidana ya dakeni ba, kallon banza ko maganar banza mutum yamin wadda batamin ba wallahi ina da Lamba3 d c o zaici k'aniyar mata....
A daidai lokacin da suka iso gabana maganar zuci ya k'are, Amisty ce tace wurinki fa muka zo kina yi kamar baki ganmu ba, saida na gama kallesu tsaf sannan nace sannunku da zuwa tare da mik'ewa zan shiga d'aki dan d'auko musu tabarma...
Gaba d'ayansu rufa min baya sukayi suma suna k'ok'arin shigamin d'aki, ja nayi na tsaya tare da tambayarsu ina zasu je ? Amisty tace ciki zamu shiga ? Murmushi nayi tare da cewa kuyi hak'uri ku jirani ni bana kai mata cikin d'akina...
Hafsa zatayi magana Amisty ta dakatar da ita, kallonsu nayi tare da cewa barta ta fad'i cikinta, Amisty tace barta kawai d'auko mana kedai, munafikin murmushi nayi tare da juyawa na shige cikin ɗaki, domin ita Amisty tasan wace ce ni, tabarma na d'auko nazo na shimfiɗawa banza nace su zauna...
Dukansu zama sukayi lokaci ɗaya, su A ` i da Saude Nana da Karima duk suka taso suka dawo ƙofar ɗakina, nima zama nayi tare da cewa meke tafe daku ne ? Na ƙarasa maganar tare da kauda kaina gefe ɗaya....
Amisty tace Sultana ke kikace mu sameki gida ! Kallonta nayi tare da cewa sai akayi ya ya ? Amisty tace ai shine muka zo ! Kallon tantiran mata nayi sannan na maida hankalina wurin Amisty nace da Allah daga yau idan zaki zo wurina kidai min kwashe kwashe , da sauri Amisty ta kalleni sannan tace haba Sultana mi yasa haka kuma ?
Kai tsaye nace kinsan bana san munafirci kuma ban tare da munafikai, waccan bak'ar yarinyar da kika gani na nuna Hafsa budurwar Dikko sannan naci gaba da cewa gaskiya aminci take da mak'iya na saidai ta zab'a ni take so ko su A ` i , murmushi Hafsa tayi tare da kallona sosai ni kuma na d'an gyara zama yanda zan d'aukar mata hankali sosai, saboda ina so na rabata tarayya dasu A ` i idan ina tare da Hafsa suma suna tare da ita riƙa zugamin ita zasuyi har su hanani na cimma buruni tunda na lura ita Hafsa doluwa ce kuɗinne kawai ba wayau sai tsabar neman matan bala'e. Kwazzaba tasa har bata iya tantance kifi bata gane kwad'o,
Cikin ruɗewa Hafsa ta fara magana irin ta "ya "yan masu kuɗi, kin gane Sultana nifa ba abokaina bane kawai gaisawa mukeyi sai kuma wata huɗɗa tamu data haɗamu amma ba komai tsakaninmu gaskiya,
Ɗaure rai nayi tare da cewa nifa ba abinda ya haɗaku nake so na sani ba cewa nayi kawai ki faɗa ni zakiyi abokiya dani kibar su A ` i ko kuwa su A ` i kika zaɓa, Hafsa tace haba aike tawa ce kuma ina tare dake, murmushi nayi tare da cewa magana ta ƙare mata tacewa mijinta shege...
A ` i zatayi magana nace dakata malama ta bakin gulbi, ki taka sannu da lafiya kafin insa a ɓatarmin dake cikin garin nan, nuna yawan su Amisty nayi tare da cewa nan da kika gansu duk dalibai na ne, zan fara basu karatu daga jibi idan Allah ya kaimu, na kafa ƙungiya ta mai take *kwarata* duk wacce kika gani anan mabuƙaciya ce, zan haɗa ne zanba mace namiji idan an sallami mace zata fiddani, zan haɗa mata da mata amma a tafiyata ban tafiya da taron banza, sabbin ɗalibai ku na ɗaukeku kyauta basai kunyi register ba, amma daga ba yanzu ba duk wacce zata shigo cikinmu saita ajiye dubu talatin kuɗin register haƙƙina neman maza da mata masu abun hannunsu....
Miƙa hannuna nayi tare da cewa duk wanda yake tare dani ya ɗora hannunsa a saman nawa, kowa ɗora hannunshi yayi harsu Nana matan aure ba'a barsu a baya ba, ku ɗauki alƙawari babu cin amana , gaba ɗaya suka amsa munyi alƙawari bazamu ci amana ba, nace kuyi alƙawari zaku zama ɗalibai masu biyayya, munyi alƙawari zamu zama ɗalibai masu biyya nace idan kun samu ina nan ko bana nan zaku ajiyemin nawa kason, shima suka maimaita, sannan nayi addu'a tare da neman Allah yasa albarka a cikin wannan ƙungiya tamu mai albarka wanda nayi ma laƙabi da *KWARATA* saboda dukanmu lalatacci ne ,
Bayan an gama nace tou kowa ya tashi ya tafi nima zan fita inda fuskar jama'a take na samu gida na siya idan kuɗina yakai, idan basu kai ba kuma zamu kama shago, wannan shago zai zama nan ne kowa zataci gayu da safe taje ta zauna, yayin da zamu kafa ƙaton allonmu ya kalli al'umma, za'a rubuta a gaban shagon ko gidan tambarin *KWARATA* idan ma baka iya ba kazo za'a koya maka.
Zamu rubuta a jikin takarda mukai kuma a buga mana su da yawa, ni zanbi manya ofisoshi da kasuwa da kuma kamfaninika da inda "yan siyasa ke zama saina zabo mana manyan alhazawa sai mu raba musu, duk wanda ya gani ya karanta dama ga number wayata nan a jiki, ku kuma kuna shago kunsha wanka kunayi kuna ƙara powder da jagira ina binku ina muku wanka da turare, da mutum yace zaizo zance ya iso akawai kaya a ƙasa, yana shigowa ya ganku wayyo shikenan labari zai canja salo, ni kuma ina da wata dabara ɗaya amma bazan faɗa muku ba saboda karuwa bata da amana,
Nana tace tou mu da muke da aure fa ? Kallon ta nayi ƙasa da sama sannan nace duk iskanci da kukeyi keda A ` i sai yanzu kika tuna Allah ? Tsoki nayi tare da cewa tunda na lura kema kinasan duniyar sai in ɗaukeki aiki ki riƙa sharewa kina gogewa, ke kuma Karima idan mijinki ya barki zan zuba miki kayan mata da maza na gyaran harka duk wata zan baki dubu biyar ko anyi ciniki ko ba'ayi ba, amma idan mijinki ya barki fa.
Tun kafin in rufe bakina Karima tace koma bai barni sai naje wallahi, dubu biyar fa ? Ina nan kullum zaune gida naira hamsin ma wahala take min , kuma Sultana ki rubuta a jikin takarda duk wanda zaizo ya taho da kaza kinga idan anci an rage ai muma zamu maida miyanmu.....
Kallon Karima nayi sannan nace kazar Lbura'uba, an faɗa miki *kwartancin* wahala zamuyi ? Kudai kuyi ta addu'a a samu bakin titi, addu'a sukayi tayi Allah ya taimaka ya bada sa'a, daga ƙarshe dai kowa ya kama gabanshi, nima na kulle ɗakina na fantsa ma cikin gari...
Ina bakin titi tsaye naji wayata tana ta kururuwa dan haka dole na dakata, fiddota nayi na duba dan ganin mai kirana, Lamba 2 wato Bello kenan, ɗauka nayi tare dayin sallama, bayan ya ansa na gaishe shi, bai ansa gaisuwar ba yace ke Uwar masu gida hotuna na gani ?
Amma ai ka gane ko waye a jikin hotunan ko ? Eh nine , tou kuɗi zaka bani naira budu ɗari biyar nan da gobe idan Allah ya kaimu idan kuma kace babu sai ina watsa su duniya kowa ya kalla kyauta.... Ɗanka da matarka da abokanka duk suna kwance a saman gado zasusha kallo abunsu...
Sirikinka da surukarka zasusha kallon siriki tsirara... Tou nabarka lafiya, ina faɗin haka na katse kiranshi, ina duba yanayin samun mutum kafin na yanka mishi haraji, Bello baida ko sisi kuma baida wata sana'a data wuce caca, kuma caca ba kullum akeyinta ba, gashi kuma na sace kuɗaɗanshi kaff da na gani a mota ba damuwa na bane nidai kuɗi kawai, ina gama waya da Bello na kira lamba3 wato d c o, mai girma ɗan sanda yarinyar jiya ce, Maryam Sultana Aliyu Binna, ya garin ? Haka nayi masa bayani bayan ya ɗauki wayata....
Hajiya ya kike ? Lafiya qalau kana ta ina haka ne ? Yace naje ganin gida ne baby, cikin salon cuta na kwantar da murya ƙasa ƙasa nace kuma "yar laɓai maimakon ka kirani inyi rakiya ? Murmushi yayi sannan yace wallahi nima tafiyar bazata ce wife ina ce bata lafiya, tou lallai wannan kuwa da sa'a take wace ce ita, dan bansan abinda wife in take nufi ba, dana dangantata da mace saboda naji yayi magana da sunan jinsin mace ne, yace wife itace ba lafiya,
D c o yace matata nace, danshi yanda yake kallon wayewa ta ya ɗauka wata shegiyar baturiya ce, danaji yace mata nace ai shine nace wannan tana da sa'a, da kaji kuma nace wace ce ita ina tambayarka amarya ne ko uwar gida ?
D c o yace ai mata ta ɗaya ce, nace tou yayi kyau yaushe zaka dawo ne ? Zan dawo amma sai ta samu sauƙi, to Allah ya sawaƙe ya bata lafiya, d c o ya amsa da amin mukayi sallama.....
Lallai duk yanda akayi wannan matar tashi tasan damarta ne, idan ta riƙe d c o sosai taya zamu samu wani abu a wurinshi ne to ? Wato ita munafika nufinta ita ɗaya zataci ? Taci gidansu bari dai d c o in ya dawo bata ƙara ganinshi dan ubanta ba rashin lafiya ba ko mutuwa tayi sai anyi jana'izarta baije ba....
Napep na hau na nufi gidan Alhaji marenin wayau na, tsoho ya tsufa amma zuciyar bata mutu ba, buɗe na samu gidan dan haka na banka kaina tsaye na shiga, babu dawakuna ko guda ɗaya duk an fitar dasu an share gidan ƙwal gwanin burgewa, sai cire yana akeyi ana wani kakkaɓe kakkaɓe get in gida sai wanke shi akeyi ana goge duk inda yayi ƙura....
Cikin masu sharar na tamabaya lafiya ko Alhaji ya tashi ne ? Yace lafiya qalau bai tashi ba ubangidan shi ne zai dawo gobe, tsoki nayi tare da cewa shine ake ta wani share share ? Yace Eh , Dikko ko ? Na tambayi yaron yace Eh ai ance ma ya iso yana Abuja ko zasuyi me ne ne ? Amma dai naji ance jirgin safe zaibi yaje kano akwai abinda zasuyi sannan zai shigo katsina....
Jinjina kai nayi sannan nace tou shi ina Alhajin ne ? Ai sun tafi kano taroshi, daga nan har kano suka tafi su taho dashi saboda tsabar basu da aikinyi ? Yaron yace ai ba rashin aikinyi bane ba hajiya duk abinda kika ga sunayi dan sun san zasu samu, Alhaji fa baya saida fari baya saida baƙi kiwon dokuna yake amma kiji irin dukiyar dake gareshi, sun san suna samu da D ---K ɗin ne shi yasa suke laƙafe dashi, da yana nan da baya nan kuɗi suke samu kamar tashin hankali...
Tou zan tafi kawai mayi waya dashi, jakata na buɗe nayi ma yaron alheri godiya yayi tayi tare da cewa Allah ya kareki ya ƙara arziƙi hajiya ubangiji yasa kifi haka Allah ya ƙara lilka darajarki ngode sosai. Ban saurareshi ba nayi waje abu na,
Gida na koma saida nayi sallah isha'e sannan na fara nazari akan Alhaji abinda zance masa kawai ya bani mota da gida sai in fita daga harkarshi, dan ni duk inda zanji ƙamshi ko labarin sunan D ---K na tsani wurin tsakani da Allah bana san Dikko na tsani rayuwarshi wallahi, amma idan har Allah yayi min cikakken arziƙi saina wulaƙanta ma Dikko rayuwa,
Wani irin baƙin ciki naji yana tasomin hawaye ya cikamin ido na abinda ya faru tsaƙanina da Dikko ya dawomin sabo fil a zuciyata, zuciya ta tace min ƙaryane baza a fita daga harkar Dikko ba sai na halakashi, kamar mai aljannu lokaci guda na burkuce nayi nayi na saita kaina amma na kasa wuƙa na ɗauko tare da kwarara wani irin ihu nace wallahi saina kashe ka........ Na ƙarasa maganar cikin kururuwa.
Duk wanda ke gidan nan babu wanda baiji ihuna ba, da gudu Nana da Karima sukayo ɗakina amma banda su A ` i saboda yau da wuri suka tafi gida. Lokacin da su Nana suka shigo duk na yanyanki wasu wurare na jikina da wuƙa, abin ya tada musu hankali dakel suka riƙeni suna tambayata waye Sultana kallon Nana nayi cikin kuka nace wallahi saina kashe shi gobe zai shigo katsina bana ko ƙaunar jin irin sunanshi a rayuwata....
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abinda Dikko ya faɗa a daidai wannan lokacin tare da janye ruwan dake gabanshi, hankalin kowa yayo kanshi tare da tambayar lafiya ranka ya daɗe ? Dafa ƙirjishi yayi tare da cewa gabana ke faɗuwa babu gaira babu dalili.
Duk kusa dashi suka matsa suna mishi sannu, kallon babban yaronshi yayi sannan yace maza kiramin gida, ɗaukar waya yayi ya kiro dadyn dikko, babu ɓata lokaci dady ya ɗauka D --- K babu ko gaisuwa yace Dady lafiyanka qalau kuwa ? Murmushi Dady yayi tare da cewa mi kuwa zai sameni ? Bayan ina nan zaune cikin iyalina muna farin ciki saboda zuwanka ! Dikko yace Dady karka ɓoyemin dan Allah miye ? Dady yace tsaya ma kaji, saida ya haɗa Dikko da kowa yayi magana sannan yace kaji ko ?
Ajiyar zuciya Dikko yayi kamar wanda yasha kuka ya ƙoshi sannan yace kawai haka nan naji gabana yana faɗuwa, Dady yace saboda zaka ga ganni ne, kayi ta addu'a Allaah ya tsare kuma kayi bacci da wuri, jinjina kai Dikko yayi tare dayi ma Dady sallama suka ajiye waya....
Dakel su Nana suka lallasheni nayi shiru, Karima tace inyi ta addu'a don Allah sharrin shaiɗan ne, nace tou amma har yanzu ban daina baƙin ciki ba, saida suka tabbar hankalina ya kwanta sannan suka tafi bayan sunsha fama na faɗa musu ko waye naƙi faɗa musu...
Suna fita na rufe ɗakina nayi addu'a na kwanta bacci,
Da safe kuwa misalin 12:45pm na fara gwagwaɗawa Alhaji kira, bawan Allah banda zufa babu abinda yake haɗawa, idanuwanshi sunyi jajir saboda tsabar tashin hankali duk wanda ke wurin saida Alhaji ya bashi tausayi duk da babu wanda yasan abinda yake damunshi, amma banda Dikko dakeyin kyakkyawan murmushin dake fito masa da tsananin kyawunshi, da yasan yanda yakeyin kyau idan yanayin murmushi daya dawwama yanayin fara'a, duk da ko baiyi murmushi ba yana da kyau sosai gaskiya, taunar rainin hankali yake ma cingom in bakinshi sannan yace wai har yanzu ta hanaka ka huta ne ?
Kamar Alhaji yana jira yace Eh ranka yadaɗe, Dikko yace bani ita, Alhaji yace ai kiran ya tsinki, ɗaure fuska Dikko yayi sannan yace kirawo min ita...............
23/08/2019
*JAMILA MUSA* 🤙🏻
Ina mana barka da juma'a,
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 17
_Don Allah kuyi haƙuri mu dukanmu mubi labarin nan a hankali, wannan labari na faɗa muku yanda yake, an rage wasu abubuwa ne wasu kuma an gyara su, labarin yana da yawa sosai ba'ayi komai ba yanzun muka fara wasan , kuyi haƙuri muje a hankali, ni jamila musa nake cewa asha karatu lafiya...._
Gajiya nayi da kira ba'a ɗauka ba dan haka na haƙura banyi yunƙurin sake kira ba, ina ƙoƙarin ajiye wayata kira ya shigo a cikin wayata mamaki ya kamani sosai ganin kiran Alhaji, taya zai kirani bayan ni na kirashi da kaina bai ɗauka ba ?
Haka nan naji tsikar jikina ta tashi zuciyata namin wasi wasi lallai akwai wata ƙullallah da ake son ɗaura min, duk yanda akayi wani baƙon lamari zai faru tou amma bansan ko miye ba, kashedi zuciyata tamin tare da hanani ɗaukar wayar, sau biyu aka kira ban ɗauka ba dan haka suka haƙura basu sake kira ba...
Kallon Alhaji Dikko yayi sannan yace yarinyar nan zata kai shekaru nawa ? Saida Alhaji ya kwantar da kai cikin biyayya sannan yace baza ta wuce sha shidda zuwa sha bakwai ba, D --- K yace tou wallahi wannan yarinya tasan abinda takeyi kila shekarunta ya wuce yanda kake tunaninta tana abunta da lissafi, amma baka taɓa kiranta a waya ba ko ... ?
Alhaji yace Eh gaskiya chat kaɗai mukeyi da ita, sai ranar da ta turomin vidion nan shine na kirata, amma daga ranar ban sake kiranta ba saidai ta kirani, Dikko yace tou jikinta ya bata ba kaine kake kiranta ba shi yasa bata ɗauka waya ba, amma nasan zata kiraka zuwa anjima zatayi tunanin wayar ta koma hannunka, ajiye wayar yayi a gefenshi suka ci gaba da abinda sukeyi..
Ina ajiye wayar kiran Bello yana shigowa, ɗauka nayi bayan mun gaisa yace min Uwar masu gida nifa har yanzu ban samu kuɗin da kike magana ba, jinjina kaina nayi tare da murmushi nace kanajin wasa bazan iya tura hotunan ka ba a yanar giza gizo ko ? Tou wai babu zan baki ne ? Cikin faɗa yace tou banda su ko satowa zanyi in baki saboda inajin tsoronki to ki turawa uwar yanar giza gizo dan kutumar ubanki ko an faɗa miki tsoronki nakeji ko inajin tsoron a ganni tsirara, idan baki sani ba har gasar fitowa tsirara nayi daga ƙofar gida na har bakin masallacin juma'a naje ranar juma'a babu kaya a jikina na dawo, ni zaki ɗauka hoto kimin hauka ? Tou bake ba ubanki ma nafi ƙarfinshi ki riƙe kiyi ta kallo mtsw ya kashe wayatshi....
Murmushi nayi tare dabin wayar da kallo, har zan haƙura wata zuciyar tace wallahi ƙarya yakeyi bai wani fita tsirara ba idan kika fahimci maganar shi ta farko a sadudance yayi miki magana, karki sauƙaƙa mishi number wayar matarshi zaki fita ki samo ki tura mata zata bashi labari, idan kin tura mata ni na sani sai ya kiraki, idan ya kiraki sai kice kin turawa ɗanshi ma, shi kuma ɗan ba hoton za'a tura mishi ba voice note za'ayi mishi da wasu maganganu masu zafi zuciya zata tunzurashi yayi ma baban magana, tashi dai ki fita duk ki samo numbobinsu ki dawo sannan musan abunyi...
Bello kuma shida abokinshi suka kashe sannan yace na faɗa mata, abokin yace tou yanzu zata shafa maka lafiya kaga kun rabu lafiya zata gaji da ajiyar hotunan ta gogesu, Bello yace ni tsoro na ɗaya tace ta turawa wata ƙawarta hotunan fa, karka damu sun gaji su goge dan ubansu, dariya sukayi tare da ƙara kashe wa cikin duniyanci....
Ina fitowa daga wanka nace ba'asan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, zakayi dana sanin hanani kuɗin nan, kila kuma rabona ne yake da yawa kuɗin zasu sake yawa.
Har na gama shiri da abinda nake saƙawa nake warwarewa, Nana na kwaɗawa kira ta kwararo da gudunta tazo, kallonta nayi sannan nace Nana aiki yamin yawa zan fita neman wurin zama sannan kuma zanje wurin wani Alhaji dake tamin rainin hankali, ai kinsan majalissar babana ko ? Nana tace Eh na sani, nace ai kinma san Bello abokinshi ko ? Nana tace sosai ma, tou lambar wayar matarshi da babban ɗanshi zaki kawo number wayoyinsu zan baki dubu ɗaya...
Yashe baki Nana tayi sannan tace godiya nake Sultana, wani sauran biredi da naman da naci jiya na rage na miƙa mata ansa tayi taita kwarara godiya harta fita, tana fita nima na tattara nawa ya nawa na fita nabar gidan...
A ƙofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, wasu irin zuƙa zuƙa motoci tun daga ƙofar gida har cikin get in gidan, kuma yauma get ɗin a buɗe yake daga inda nake tsaye ina hango komai na gidan !
Matashin jiya daya faɗa min cewa Alhaji yayi tafiya shine yazo wurina da sauri ya gaisheni cikin girmamawa ansawa nayi cikin sakin fuska sannan nace gidan naku lafiya naga taron motoci ?
Lafiya qalau ubangidan nasu ne ya dawo ko gida ma baije ba ya fara da ganin dokuna, jiya da aka fidda dawakunan doki ɗaya ya kare a ƙafa shine ya fara da ganinshi kafin ya wuce.
D --- K ne ya fito daga cikin palon yana magana daga ganin yanayin maganar shi faɗa yakeyi, saida ya fito tsakar gidan sannan ya riƙe ƙugunshi da duka hannuwan shi biyu yaci gaba da magana amma bana iya jiyo abinda suke cewa saboda tazarar dake tsakaninmu.
Zubinsu da yawansu ya bani tsoro gasu ƙosasshi, inda Dikko yake tsaye na kalla, gaskiya Dikko ɗan gayu ne wankakken namiji yasha wanka ya ƙoshi tsaftatacce dashi ya cika ya fito cikakken namiji har wani gemun rainin hankali ya ajiye kamu ɗaya gaskiya duk da bana ƙaunar shi jarumin namiji ne duk inda mace take san namiji Dikko yakai tsakani da Allah zan faɗi gaskiya, domin Allah Dikko yana da kyau mai burgewa da ɗaukar hankali , sauke hannunshi ɗaya yayi daga riƙon da yayi mishi ya saka a aljihu ya ciro ibadar tashi, ya ciro cingom in daga cikin takardar shi ya jefa a bakinshi sannan suka fara taho wurin motocinsu...
Murmushi nayi kaɗan yayin da wani sashe na zuciyata yake cewa kira sunanshi idan ya juyo ki caccakawa uwarshi zagi komai zai faru ya faru idan ma ta tafasa ta ƙone, yayin da wani sashe na kwalwata yake bani shawara cewa duk abinda zakiyi kisa nazari da lissafi kiyi ma takonki linzami mai kyau duk daren daɗewa Dikko sai kinci ubanshi.
Zuciyata tace kiyi masa magana dan ya tunaki kuma yasan kina nan kuma ki faɗa masa cewa zaki ci ubanshi idan babu yau akwai wata rana....
Sallama nayi da matashin daya faɗa min Dikko ne yazo sannan na wuce ciki, a lokacin dana isa wurinsu tuni D --- K ya zauna cikin mota ana ƙoƙarin rufe masa mota na riƙe murfin motar ,
Kowa kallo wurin hannun daya riƙe murfin mota yayi dan ganewa idonsa ɗan rainin hankali daya isa yayi wannan iskancin, kwantar da kaina nayi saman murfin motar cikin tausasashshiyar murya nace Dikko, kallo na yayi tare da cewa na'am ya tsareni da idanuwa, shiru na wani lokaci ya ratsa wurin bai daina kallona ba kuma nima ban daina kallonshi ba haka kuma babu wanda yayi mana magana...
Nice na fara cire idona daga kanshi dan idan har ina kallonshi tou lallai babu abinda zai hana in burma mishi wuƙa, kaina yana kallon ƙasa nace ka kuwa gane ni ? Na ƙarasa maganar tare da ɗago fuskata amma ban sake kallon idonshi ba...
Cikin ɓacin rai yace Al ' Ameen mtsww muje ya faɗi maganar tare da jan murmufin motar da ƙarfi ya rufe, zuciya bata da ƙashi ganin Dikko zai maidani sakara yasa na dunkule hannuna na kaiwa gilashin motar duka saida ya tarwatse , jini kuwa yace gashi nan zuwa...
Duk da haka Dikko baiyi niyar tsayawa ba saida nace kai ƙaramin ɗan iska yau itace rana ta ƙarshe a gareka kamar yanda na dasa lissafin kwanaki mutuwarka , idan har kayi nasarar guduwa ina nan tafe gareka sai ka ɗanɗani azaba kwatankwacin irin wacce ka ganamin baka da aiki sai cin cingom kamar wata karuwa sakaran banza daƙiƙi ɗan gidan matsiy......
Wanda aka kira da Al " Ameen shine ya ɗaga hannunshi da niyar kwarara min mari Dikko ya riƙe hannunshi tare dayin murmushin mugunta yace waye yace maka irinsu ake duka ? Tsaya daga gefe kaga maganin ta, Allah ɗaya nake tsoro amma yau dasai nayi mata allurar natsuwa, amma ka barta nayau zan mata kaɗai idan na sake ganinta tou nasan abinda take buƙata, Al ' Ameen yace mai gida ka sakeni in koya mata hankali, murmushin mugunta Dikko yayi tare da cewa bari in bata abinda ta roƙa...
Sakin hannun Al ' Ameen yayi sannan ya matso kusa dani, ɗan kauda kanshi yayi gefe kamar yana nazari fuska a ɗaure ya juyo ya kalleni ni juyowar da yayi gaba ɗaya wurin kowa ya juya baya, hannuwana ya haɗa duka biyun ya maidasu ta baya ya riƙe, hannu ɗayan kuma ya riƙe fuskata, ƙasa ƙasa yayi magana cewa.
Naga dai kina san cingom in nan kinsan kwanaki da muka haɗu ban "yan maki shi ba, kuma sai kiyi ta abu babu kawaici a gaban jama'a sai kiyi ta wani zalamar Dikko kuma ko an baki ni nayi miki yawa ba inda zaki je dani dan ruwa ba sa'ar kwando bane, kina da daraja ɗaya a wurina kuma albarkacinta kike ci amma wallahi dasai na nuna miki ni tantirin ɗan iska ne, darajar tasa kawai bazan wulaƙanta ki ba, amma idan kina neman rainin hankali da tsantsagwaron rashin mutunci daga kaina an rufe littafi.
Tattaunawa yayi cingom in cikin salon jan hankali saida ya busa cingom in yanda ake cewa kwai, sannan ya kalleni da wani iri salo sai kuma yayi murmushi da gefen bakinshi, hannun daya riƙe min fuska ya ciro cingom in sannan ya tura minshi cikin bakina, tuf tuff na fara tofar da cingom in , murmushi yayi tare da rufemin baki yace ai ƙarya kikeyi sai kinci....
Iya ƙoƙari nayi na tofar yaƙi fita ga kuma ya riƙe min hannuwa duka, daidai saitin maƙoshi na yayi min wani duka wanda yasa dole saida na haɗi cingom in, dariya yayi sannan ya sakeni tare da turani baya yace sai mun sake haɗewa an mata....
Tangal tangal na tafi kamar zan faɗi su kuma suka shige motocinsu suka tafi aka barni a filin tsakar wurin daga ni sai Alhaji, dakel na iya haɗiye yawun bakina saboda azaba da raɗaɗin da maƙoshina yakemin saboda nushin da yayi min.
Kallon hannu na nayi da jini yake ta ɗiga sannan na kalli Alhaji nace kaini asibiti, cikin damuwa yace muje, dani dashi muka nufi wurin motarshi muka shiga gaba ɗayanmu muka nufi asibiti,
Muna zuwa babu wani daɗewa akamin diresin , bayan an bincike hannun kaf ko akwai wani gilashin a ciki, magunguna aka bani sai kuma allurai da akayi min duk Alhaji ne ya biya kuɗin bayan an gama komai ya ɗaukeni muka tafi gida !
A ƙofar gida yayi parking duk muna cikin mota daga ni harshi, shiru mukayi na wani lokaci sannan Alhaji yace hajiya dan girman Allah ki goge wannan vidio dan darajar manzan Allah S. A. W, ki taimaki rayuwata ki goge don Allah, badan halina ba,
Ajiyar zuciya nayi sannan nace tou nima ka taimakeni dan darajar manzan Allah S. A. W dani dakai duk mu taimaki juna daga yau nayi maka alƙawari zan goge vidio sannan kuma zan fita rayuwarka babu dawowa...
Tattaro hankalinshi yayi wurina sannan yace faɗamin me kike so idan har ina da hali zan miki ! Ba tare dana kalleshi ba nace mota kawai zaka bani daga ita na rantse maka da Allah na fita sha'anin ka vidiwo kuma zan goge...
Goge zufa Alhaji yayi sannan yace wace iri kike so ne ? Ni bansan mota ba amma dai mai kyau nake so, kallon motarshi yayi sannan yace kina san wannan ? Ba tare da ɓata lokaci ba nace Eh tamin kuma ina santa,
Alhaji yace tou na baki ita, kina da wurin ajiyarta ne ? Yanzu ma zan ajiye miki ita insa azo a tafi dani amma ki goge hotunan nan dan Allah, karka damu zan goge wallahi, a , a nidai ki goge a gabana don Allah, tunda nace zan goge ai zan goge, Alhaji yace tou bayan wannan sai me ?
Abu na gaba ina so ka faɗamin waye Dikko ? Miye asalinshi waye babanshi a garin nan ? Wane irin matsayi gareshi kuma wane dalili ne yasa yake ɗagawa ta rayuwa ina san ka faɗamin asalin Dikko da kuma tarihin rayuwarshi.....
Gyara zama Alhaji yayi sannan yace fara bani mazaunin motarki na ajiye ki goge vidio sannan sai muyi magana kinga lokacin ina cikin natsuwa, ba damuwa na faɗa tare da buɗe mota na fita na shiga cikin gida !:',
Kuyi haƙuri don Allah yau ina can gidan uwar ɗakina nima inacin shagali da miyar mutunci, wurin uwar ɗakina wato *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* ina alfahari dake uwar ɗaki ɗaya tamkar da dubu banda kamarki kuma kina da matsayi na musamma a zuciyar *MEELAT MUSA*.....
24/08/2019
*JAMILA MUSA CE...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 18
*_KOMAI DADIN DUNIYA KIYAMA TA FISHI , daga alƙalamin Ummerherny Nerserllerh idan kika bari aka barki baya bazan baki labarin wannan ƙayataccen labari ba wanda ya fito daga alƙalamin haziƙar marubuciyar zamani, Allah ya taimaka surukuta yasa a kammala lafiya amin..._*
Ina shiga gidan ko sallama banyi ba yaro ya shigo da saurinshi wai ance Sultana tazo Alhaji yana kiranta , Nana ta fara miya sameki naga hannunki a ɗaure ... ? Duk hankalin su A ` i ya tashi sunga uwar ɗakin kwarata hannu da ɗamara, murmushi nayi tare da cewa yawwa A ` i da Allah inda zan ajiye mota nake so nayi maganar dan kauda tambayar abinda yaji min ciwo, Hafsa tace ina motar take ne ?
Ba tare dana kalleta ba nace tana waje, dan haushin Dikko ya fara shafar Hafsa saboda soyayyar da take mishi bana san Dikko haka kuma bana soyayya wa duk wanda yake ƙaunar Dikko, Hafsa tace sai in ajiye miki a gidanmu, ban bata amsa ba nabi yaron muka koma waje...
Motoci biyu na gani a ƙofar gida , wurin motar Alhaji na tsaya daidai saitinshi sannan nace gani, wani wuri ya buɗe ya tattaro wasu takaddu ya bani ansa nayi naɗan basar ina kallo a zahirance karatunsu nakeyi amma wallahi a baɗinance bansan ko na miye ba...
Fitowa yayi daga cikin motar ya bani makullin tare da cewa ga motar nan zanje mai gida yake kirana dana gama zan dawo insha Allah amma ki rufamin asiri Sultana ki goge vidion nan don Allah, wallahi karkaji komai Alhaji zan goge amma kaɗan bani na kati plz, yace ina zuwa bara in gama tattara tarkacena a motar nan...
Komai nashi ya kwashe a mota ya zuba cikin motar dana gani, bayan ya gama ya ciro wayarshi yace kalli ki gani, kallon wayar nayi yace kinga na goge nawa ko ? Nace Eh nima zan goge insha Allah, godiya yayi sannan ya bani kuɗi amma basu da yawa yace idan ya dawo anjima insha Allah zai bani tukuicin goge vidio, godiya nayi masa sannan mukayi sallama ya shiga mota tare da cewa karfa kiyi wasa da takardun motar nan ki adana su kinji ko ? Sai yanzu na gane abinda takardun suke nufi godiya nayi masa suka wuce ni kuma na koma gida...
Ina shiga gida Hafsa na ba makullin nace kije ki ajiyemin zan ɗauko ta ƙarshen satin nan insha Allah, ansar mukulin tayi taci gaba da maganar ta, kallonta nayi sannan nace saurara kiji, kije ki ajiyemin mota ki dawo, tashi tayi ita dasu Saude suka tafi ni kuma na shiga ɗakina, ban daɗe da shiga ba Nana ta shigo tare da bani number matar Bello amma bata samo na ɗanshi ba , ansa nayi da nayi niyar bata 500 sai wata zuciyar tace kawai in bata 1k in ka nema ma ka samu ai arziƙi ne...
Jakata na buɗe na bata 1k nayi godiya, itama godiya tamin ta fice a ɗakin, tana fita na kulle ƙofa na kwanta saman katifa na fashe da kuka mara sauti , duk duniya babu wanda ya taɓa wulaƙanta ni kamar Dikko nice zai bawa cingom in bakinshi da yawun bakinshi na haɗe a cikin cikina , duk duniya babu abinda yakai miyau saurin sadar da shaƙuwa, shi yasa masu wayau ko bariki suke basa yadda suna haɗa bakunansu da na wasu, waccan ranar bai haɗa bakinmu ba amma shine yau ya ciro abu daga cikin bakinshi ya bani, yana da wata manufa ta daban shine dalilin da yasa yace ma Al ' Ameen bara suga magani na, wato wannan dalilin ne yasa kowa ya juya mana baya ko ? Saida na goge hawaye na sannan nace ƙarya kakeyi yawun bakin ka bazai taɓa zama hukunci a gareni ba...
Nayi kuka har na gode Allah daga baya kuma bacci ya kwasheni wanda bansa lokacin daya zo ba kuma baiyi shawara dani ba,
Washe gari koda na tashi nayi sallah bacci na koma bayan na gama kwashewa Dikko karama , misalin 09:30am Alhaji yasa aka kirani a waya, bayan na ɗauka nayi sallama dakel Alhaji ya amsamin sallamar cikin nishi yace Sultana ina federal medical center { F M C } saida ya sake yin nishi cikin yanayin wahaltuwa sannan yace ina nan Accident & Emargency kizo yanzu don Allah inasan zanyi magana dake....
Har a zuciyata banji daɗi ba cikin muryar tausayi nace kayi haɗari ne ? Hawaye ya gangaro masa daga cikin idonshi yace kizo dai dan bana tunanin zan ƙara awa ɗaya a cikin duniyar nan....
Subahanalla da Allah ka daina wannan maganar gani nan zuwa insha Allah, cikin rawar jiki na kashe wayata, da sauri na sauko daga saman katifa na zuba ruwa, a gaggauce naje nayo wanka tare da wanko bakina, mai fauda da kwalli kaɗai na shafa, baƙar riga ta jallabiya na saka na yana gyalen a saman kaina na zagoyo dashi har gashin kaina saida ya fito ta ƙasan gyalen jallabiyata, gilashi mai saukin duhu na saka sannan na wanke jikina da turaruka masu sanyi ƙamshi, masha Allah na faɗa a lokacin da naga kaina a cikin madubi, nayi kyau sosai na fito kamar baƙuwar balarabiya a nigeria,
Wayata na ɗauka da jakata, na fito ina tsaye ina kulle ɗaki Hafsa ta shigo, ita ɗaya ce babu abokan nata su Saude, su Nana ma duk basa tsakar gida, ɗan gangarowa tayi da wani irin salon tafiya, ta wutsiyar idona na kalleta sannan na ɗaure fuskata na kallota dukanta a daidai lokacin dana gama rufe ɗakina...
Wow uwar ɗakin karuwai kinyi kyau fa kamar dai ba'a mutu ba, share maganar nayi tare da cewa da mota kika zo ne ? Eh ta faɗa tare da bina da kallon cin wanka , gaba nayi tare da cewa muje ki saukeni f m c biyoni tayi muka fito a tare, a ƙofar gida muka haɗu dasu A ` i hada Amisty da Saudatu....
Amisty tace wurinki zamuje munji shiru har yanzu, kuma mun rubuto takarda an tsara jaddawalin yanda zai ƙawatar ya kuma tafi da hankalin maza gaki kuma zafi fita, buɗe gaban mota nayi na kame sannan nace ku shigo muje kuma, baya suka shiga, Hafsa kuma ta zauna mazaunin tuƙi taja muka tafi....
Saida muka fara tafiya sannan nace karanto min ina saurarenki, Amisty fa tasan komai tasan bana ganewa bana rubutawa kuma bana iya karantawa amma sai tace kidai duba ki gani Sultana, basar da ita nayi tare da miƙa hannuna ta baya na anso takarda ko buɗewa banyi ba na ajiye shegiya ban sake bi ta kanta ba kuma ban sake magana ba har muka isa asibitin...
Wani irin tuƙin ganganci Hafsa tayi tare da sakin sitiyarin saboda taga D --- K , a tare muka iso dasu sai leƙawa take tana kiranshi, wato abinda na fahimta idanma ka nunawa mutum ka damu dashi sai yayi ta ɗagawa, kallon Hafsa nayi tare da cewa ke kuwa baki da aji a haka kike tunanin zan riƙa haɗaki da zafafan mata babu class, raina ya ɓaci sannan nace uban waye Dikko da kike ta hauka kina kiranshi mutane suna kallonki kamar wata zararriya....
A daidai lokacin da muka fito mu dukanmu daga mota shima Dikko ya fito kuma yaji zagin da nayi masa , bai kallemu ba yayi gaba ana take masa baya nima gaba na shiga su Hafsa suka rufomin baya, murmushi Dikko yayi a daidai lokacin da muka tsaya bakin ƙofar ɗakin kowa da muƙarrabenshi a bayanshi, kallona Dikko yayi tare dayin murmushi sannan yace zaki ci ne an mata yayi tambayar tare da ɗaga gira ? Ya ƙarasa maganar tare dayimin wani irin kallo mai tattare da mugunta, yaci gaba da cin cingom inshi cikin salon jan hankali gemunshi yana motsawa a hankali cikin salon ɗaukar hankali , murmushi nayi saboda gaskiya yanayin da yayi ya burgeni, ƙarshen harshenshi ya kawo cingom in yayi wasa dashi a daidai lokacin da aka buɗe mana ƙofa duk muka shiga, daga waje bai sake kallona ba kuma bai sake murmushi ba babu magana har muka isa gaban gadon Alhaji...
Duk matan da muke tare ihu muka farayi saboda tsoron yanayi da Alhaji yake ciki yayin da wasu suka nufi hanyar fita, dani da A ` i aka bari yayin da A ` i ta duƙushe tana kuka ni kuma na cire gilashi na wurgar a gefe na rufe idanuwa na naci gaba da dire dire ina kuka saboda na kasa gaba na kasa baya....
Shi kuma Alhaji burinshi inje wurinshi in taimaki rayuwarshi na goge vidio sai kirana yake cikin dasasshiyar murya da yayi magana sai jini ya kwararo , Dikko yace ya daina magana amma yaƙi saurarenshi Sultana kawai yake kira,
Kusa dashi Dikko ya ɗuka sannan ya tambayashi me zan mishi ne ? Hawaye na zuba a idon Alhaji yace ma Dikko ya rufa mishi asiri ya kawoni wurinshi magana zamuyi ta sirri, Dikko yace faɗamin na faɗa mata kaga ta firgita wani abu zai samunta, cikin wahaltacciyarar murya Alhaji yace kayi min wannan arziƙin na sauran mintunan da suka ragemin a duniya lokacina yana tafiya zan iya mutuwa ko wane lokaci, yanda yayi maganar ne yasa Dikko ya kallo inda nake tsaye ina ta direre kamar anyi ma lafiyayyan diko allurar hauka.
Ɗauke idonshi yayi daga kaina sannan ya kalli zugar daya zo da ita, Al ` Ameen ya faɗa cikin wani irin yanayi kamar bashi ne yayi maganar ba, gaba ɗaya waje suka fita harda A ` i aka fita, inda gilashina yake Dikko yaje ya ɗauko sannan yazo kusa dani, ta gaban rigata ya jawo ya sagala gilashin sannan yace buɗe idonki, jikina yana kyarma na buɗe na kalli Dikko, dakel ya haɗe yawun bakinshi sannan ya tofar da cingom in bakinshi gaba ɗaya yanayin Dikko ya canza ɗaure fuska yayi sosai sannan yace miye tsakaninki da mara lafiyar nan ? Miye dalilinki na zuwa ganinshi ? Me kikaje yi gidanshi ? Kema "yar iska kike so ki zama ko ?
Cikin gatsali nace Ey "yar iska zan zama ina ruwanka da iskanci na ne ? Jinjina kai yayi tare da cewa Allah ya sawaƙe wuce muje yana kiranki, tirjewa nayi tare da juya zan fita da gudu ya riƙoni yace ai ƙarya kike sai kinje, har gaban Alhaji ya jani ya kaini sannan ya zaunar dani saman kujera ya tsaya ta bayana yace gata nan me tayi maka ne ? Ko kaima taci kuɗinka kamar yanda taci na Umar ?
Ɗaga kaina nayi na kallo Dikko ɓacin rai kwance a cikin idonshi zare min idanuwa yayi tare da cewa bari kallona kar fashe miki kwayar ido wallahi, jiki a sanyaye na sauko kaina daga kallon da nake ma Dikko naci gaba da kallon Alhaji ina kuka, dafo kujerar yayi ya duƙo kusa dani sosai saitin kunne na yace na rantse da girman Allah idan na gano akwai wani abu tsakaninki dashi saina kashe ki, ya faɗi maganar tare da shaƙemin wuya sosai na fara ƙoƙarin ƙwalƙwale hannunshi na kasa, tun ina iyawa har nasa wani abu na fara halbe halbe har na faɗo daga saman kujera Dikko bai saki wuyana ba naci gaba da halbe halbe, yanda nake halhalbe ya jawo hankalin mutane suka yo kanmu amma an kasa cire hannun Dikko daga wuyana,
Hayani tayi yawa sosai wanda yasa su Al ` Ameen suka shigo ciki da gudu amma wallahi duk yawan mazan nan suka kasa ɓanɓareni daga hannun Dikko harsai dana suma, riƙe Al ` Ameen yake da hannun Dikko yana cewa don girman Allah mai gida ka ƙyale yarinyar nan karta mutu, zaro jajayen idanuwan shi yayi kamar yaci mutuwa yace fita idona Al ` Amenn ya faɗi maganar yana fitar da wani irin lumfashi kamar ranshi zai fita, Al ` Ameen kuwa ƙin sakin hannun Dikko yayi saboda tunda yaga Dikko a wannan yanayin yasan komai zai iya faruwa....
Yace mai gida karta mutu, Dikko yace ta mutu idan ta mutu kaine ka kashe ta ko kaine zakayi azumi ? Ya ƙarasa maganar tare da kwalalo idanuwanshi waje , sannan yace duk abinda ya faru da ita nine ya ƙarasa maganar tare da nuna kanshi, haƙuri akayi taba dikko dakel aka samu ya sakeni ,
Bakin gadon Alhaji ya koma ya ɗauki wayarshi iyakar bincike Dikko yayi bai samu komai ba, kuma number na dama Alhaji baiyi saving ba, jerin kira ya dawo yaci gaba da binke, saida ya gama sannan ya ajiye wayar , kallo gadon da nake kwance yayi har an sakamin ƙarin ruwa da taimakon Al ' Ameen dayayi tsaye yace a bani taimakon gaggawa,
Kusa da Al ' Ameen yaje tare da cewa bani makullin mota, cikin girmamawa ya ɗauko ya bashi baiyi mishi musu ba saboda yasan Dikko baya san gardama idan yace ayi kawai ayi mishi idan yace a bari barin kawai za'ayi sai a zauna lafiya,
Cingom ya ciro daga aljihu ya ɓanɓare ya saka bakinshi yaci gaba daci, Al ' Ameen kuwa bin Dikko yayi da kallo harya fita daga ɗakin yana mamakin hali irin na Dikko zuciyarshi tayi yawa idan ya burkuce wani lokaci kamar bashi ne yakeyi wasu abubuwan ba...
Ta jikin window ya leƙa Dikko, har ya shiga motar yaja ya tafi cikin tuƙinshi na ganganci wanda baya kaucewa kuma baya ɗagawa kowa ƙafa idan ya tafi sai yakai inda zaije hankalinshi yake kwanciya, Allah ya tsare hanya Al ' Ameen ya faɗa tare da dawowa wurin gado na ya tsaya, su Hafsa da Saude da A ` i da Amisty sunyi jigum kowa yana jiran farfaɗowa ta yaji abinda ya haɗani da D --- K......
Dikko kuwa tuƙi yake amma yana tunanin maganar Alhaji ranka ya daɗe wato wallahi wata yarinya ce muka ɗan keɓe da ita , tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya daɗe tana ɗauka cikin waya ban sani ba....
Dukan sitiyari Dikko yayi tare da cewa tabbas yacemin yarinyar nan shekarunta bazai wuce 16 zuwa 17 ba daidai saitin zuciyarshi ya daka tare da cewa kece .... ?
Akan titi duk ƙurewar wuri Dikko ya juya kan sitiyarin mota ya koma baya ba abinda ya dameshi da halin da wani zai shiga kanshi kawai yakeji amma baya sauraren talakawansu, da gudu ya ibi shararra ya komo asibiti, a lokacin su Al ' Ameen sun fito zasu tafi ganin Dikko ya dawo yasa Al ' Ameen ya dawo cikin ɗakin da gudu yasa aka ɓoyeni, danshi Alhaji tuni Allah ya anshi rayuwarshi har an tafi da gawarshi, duk zunubin da Alhaji ya cacumar ma kanshi an samu wani marar rabo a lahira ya dira gidanshi yayi mishi caccakar wulaƙanci aka kawoshi asibiti dan ceton rayuwarshi Allah yasa ikar ibar da yayo kenan, Allah ya jiƙanshi yasa mu cika da imani ubangiji ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo...
Ana ɓoyeni su Al ` Ameen suka fito, a waje suka haɗu da Dikko yana ƙoƙarin shiga suka faɗa mishi mutuwar Alhaji ni kuma an canja min asibiti, Allahu Akbar Dikko ya faɗa tare da cewa ubangiji ya ƙarɓi baƙuncinka Muntari Allah ya kyautata tamu bayan taku, da Amin kowa ya ansa sannan suka tafi a tattare baki ɗayansu...
25/08/2019
Taku a kullum
*MEELAT MUSA...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 19
Har yanzu kalar idon Dikko bai koma fari ba, idon nan jajir kamar yaci bala'e, amma a hankali yake washewa zuwa kalarshi ta ainahi, fuskar nan a murtuke ya jingina bayan shi da kujerar mota kana kallonshi kasan yana tattare da tsantsar damuwa.
Ɗan gajeren tsoki yayi tare da gyara zamanshi, hannunshi yakai ya shafe gefen fuskar shi, tunanin safiyar haɗuwarshi da Sultana ya fara dawo mishi sabo fitikil kamar yanzu ne abun yake faruwa, da sauri ya rumtse idanuwan shi tare da haɗe leɓunan sa wuri ɗaya ya danne su da haƙoranshi ta ciki, buɗe ƙofafin hancin shi yayi saboda lumfashin da yake shaƙa yayi mishi kaɗan ya buɗe ƙoƙofin hancin ne dan iskan ya yalwace shi.
Har suka isa gidan rasuwa Dikko bai sake ma kowa magana ba, tunda dama shi ba ma'abokin surutu bane, mota nayi parking ya fita cikin damuwa danshi dama kullum haka yanayin shi yake , farin ciki da ɓakin ciki duk yanayin iri ɗaya ne a wurin shi, babu wanda ya isa yasan lokacin farin cikinshi kuma babu wanda ya isa yasan lokacin da yake damuwa.
Tunda ya fito aka fara gyara mishi wurin da zai zauna dan zamanin ga mutane basa abu domin Allah basa darata girma shekaru da mutumci amma suna ba naira matsayi na musamma, Dikko yana da rashin mutunci amma alherinshi yasa mutane basa ganin rashin mutuncin nashi dan Allah yayi masa kyauta idan dai kukayi ido ido dashi tou tabbas zai baki kuma baya da kwauro idan zai bayar mai yawa yake baka, tou kyautar itace ta danne rashin mutuncin shi ga idanuwan al'ummar gari...
Sabuwar tabarma aka amso daga cikin gidan aka shimfida mishi, takalman shi ya cire ya taka tabarmar da safa, saida ya zauna sannan kowa ya zauna kuɗi suka fara nuna ikonsu domin masu neman asan dasu sukayi ta zubewa suna bada gaisuwa, saida ya jinjina kai dan shi kaɗai yasan tsutsar baƙin cikin dake lasar masa zuciya...
Wanda suka bawa duniya gaba ne suka fara bawa Dikko labarin yadda abun ya faru amma a zahirance yana jinsu amma a baɗinance hankali shi yana wurin Sultana so yake kawai a dawo jana'iza yaje ya ganota wallahi sai ta faɗa mishi miye tsakaninta da Muntari, inma banda take daƙiƙiya dan ta tona mishi asiri shine zai haɗa kirji da ita taje ita kuma ta haɗa da yaronshi...
Wayarshi ya ciro yayi "yan rubuce rubuce bayan ya gama ya tura, wayar shi ya maida aljihun gaban riga a zuciyarshi kuwa yana tunani Sultana ta gama barbaɗashi a duniya kowa kallon ɗan iska yake mishi,
Mikewa tsaye sukayi gaba ɗaya dan an fito da mankara, sai yanzu wasu keyin alwalla shidai yana da ita takalmin shi ya saka suka fita sarari dan sallatar gawar Alhaji Muntari , Allahu Akbar ubangiji kayi mana kyakkyawan ƙarshe hanyar dai ɗaya ce duk wanda yazo sai ya koma Allah kasa mu cika da imani idan ajalinmu yazo ameen....
A asibiti kuwa ina kwance cikin tsaka mai wuya, ina tafiya ne tsakanin rayuwa da mutuwa, duk wanda ya ganni saiya tausayamin ga hannu na naɗe da bandej wanda na fasa shi a jikin gilashin motar Dikko, su A ` i kuwa suna bani kulawa ta musamman tare da tattalina kamar mun fita ciki ɗaya !
Tsaye suke zagaye jikin gado na hankalin kowa tashe, jami'an tsaro ne suka shigo gaba ɗaya suka fatattaki su A ` i , kujerar da ake tura marasa lafiya aka ɗauko aka ɗorani a samanta suka tun kari hanyar fita dani daga cikin ɗakin, wani irin ihu Saude tayi tare da cewa ina zakuje da ita ne ?
Basu saurari kowa ba suka fito dani, cikin mota aka sakani mazaunin baya sannan aka rataye ƙarin ruwan a jikin kujera yaci gaba da shiga cikin jikina,
A wurin suka bar kujerar duk suka shiga mota sukaja muka bar asibitin, kuka su Hafsa sukayi tayi tare da tambayar kansu wane irin laifi nayi wanda har hukuma bata ragamin ba ina kwance a gadon asibiti, sunsha kuka har sun godewa Allah daga ƙarshe suka haƙura suka tafi gida...
Daga maƙabarta Dikko basu dawo gidan rasuwa ba gida suka wuce kai tsaye, tun a get na biyu ya sauka tare da cewa zai shiga yayi bacci , Al ' Ameen yace ranka ya daɗe bara muje get in ƙarshe sannan mu sauke ka amma daga nan ai zakasha tafiya, ba tare daya kalli Al ' Ameen ba yace nan zan sauka ya ƙarasa maganar tare da kallon Al ' Ameen , tuba nake ranka ya daɗe Al ' Ameen ya faɗa tare da jan motar yayi gaba...
Saida ya daina hango ɓurɓushin motar sannan ya fiddo wayarshi yayi "yan lashe lashenshi sannan ya kara a kunnenshi , bayan wani lokaci yace kuna ina ne ? Magana na cikin wayar yayi sannan Dikko yace ku shigo ta get in baya, yana faɗin haka ya kashe wayarshi tare da kiran wata wayar kuma.
Ta baya ya dawo ya bi wata hanya daban , tafiya mai nisan gaske yayi wurin tsitt bakajin ƙarar komai sai motsin tafiyarshi tunda tsakuwowi ne baje a wurin irin wannan fararen wanda idan ana rana har kashe ido suke, idan ya taka sai kaji tsus tsuss ƙarar tafiyar shi ,
Wata hanya ya bullo sai gashi jikin wani makeken get, masu gadi yayi ma magana suka buɗe motarmu ta shigo cikin gidan, gaba yayi motarmu tanabin bayanshi saida mukayo nisa da get in sannan ya tsaya, shima matuƙin motar tsayawa yayi tare da fitowa Dikko bai mishi magana ba ya shiga mazaunin dirver yaja motar yayi gaba.
A bakin ƙofar falonshi yayi parking sannan ya fito yaje ya buɗe ɗakin, dawowa yayi ya buɗe baya inda nake kwance rai hannun Allah, ciro robor ƙarin ruwan yayi ya fara riƙewa sannan ya ɗaukeni ya shiga ciki, a falo ya kwantar dani saman kujera 3sieter saida ya gyara ruwan suka ci gaba da shiga sannan ya fita tare da rufe ɗakin ta waje...
Motar ya ɗauke daga bakin ƙofar falon sannan ya ajiyeta a inda suke ajiye motoci, motar ta gidansu ce kuma jami'an suma na gidansu ne yayi amfani dasu...
Dawowa yayi tare da rufe ɗakin sannan ya wuce ciki, wanka yayi ya cire manyan kaya zuwa ƙanana, falo ya dawo ya zauna yana jiran lokacin da zan buɗe idona ya haɗa partyn shagalin wulaƙantani,
Zama yayi saman kujera wacce take kallona, ba abinda yake tashin shi a wurin saidai yaje yayi sallah ya dawo, idan yazo ya zauna kuwa lokaci zuwa lokaci yakan kalli agogon hannushi sannan ya kalli inda nake kwance, waya kuwa idan an kishi saida ya duba kawai ya latse,
Ruwa ma daya ƙare shine ya cire min, bai daɗe da zama ba aka fara dukan ƙofar ɗakin, ɗan latse baki yayi tare da cewa waye ? Dikko buɗe nice, muryar yayarshi yaji miƙewa yayi yaje ya buɗe ƙofar suka shigo cikin falon tare,
Salati nayi a daidai wannan lokacin jin muryar Dikko da sunanshi da aka kira, wani irin abu naji ya daki zuciyata, na ƙara lafewa bamma yi gigin tashi ba haka kuma ban kuskura na buɗe idona ba, amma jikina ya mutu murus , zama yayi a saman kujerar da yake itama kusa dashi ta zauna saman hannun kujera sannan tace ina ka samo larabawan daji ? Ta faɗi maganar tare dayin dariya...
Banza yayi baice mata komai ba, dariya ta sakeyi tare da jan gemunshi sannan tace dan ubanka bakaji ina maka magana, tayi maganar cikin sigar zaulaya, tsoki yayi tare da cewa ni bana san irin abinda kikemin yayi maganar cikin haɗe rai kamar dai yanda ya saba, kaiji ɗan iska ni zaka ɗaure ma fuska ko mutuwa zakayi na faɗa maka bazan daina janka ba, duk wannan haɗe haɗen fuskar gabana aka haife saida ma nayi aure dan ubanka kazo duniya wane girma zakayi gabana, ko inda take bai kalla ba, kuma baiyi murmushi ba bare tasa ran zaiyi dariya, sansar wauta dai tayi ta nunawa da sakarci amma Dikko tunda yace mata baya san abinda take mishi bai sake magana ba saida ta ƙari rashin wayanta sannan ta taho inda nake kwance...
Ko kallonta baiyi ba dan hankalinshi ma yana kan wayarshi amma yana kallonmu da zuciyarshi, tsaye tayi gabana idona da jikina suka ɗauki kyarma da sauri na buɗe ido na kalleta a tsorace sai kuma na kallo inda Dikko yake zaune amma yanzu bayacim cingom maido kallona nayi wurinta kawai sai na fashe da kuka....
Sai yanzu ya ɗago kanshi cikin tsawa yace ki rufemin baki, da sauri na haɗe kukan tare da rufe idona dan wallahi a halin yanzu tsoron Dikko nakeji dan na fara tunanin kila mahaukaci ne amma har yanzu jikina bai daina kyarma ba.
Juyawa yayar tashi tayi tai mishi magana da yaren arna { turanci } bansan abinda sukace ba, ɗan ɓata fuska yayi sannan ya ajiye wayarshi shima yayi mata magana cikin irin harshen da tayi masa, Allah ya bata lafiya ta faɗa tare da cewa zan koma wurin momy da Allah kayi ƙoƙari ka shigo, da kanshi ya amsa mata, saida ta ƙara kallona sannan ta kalli Dikko ta sakeyin magana da yaren ɗazu, kyakkyawan murmushi yayi sannan yace ngode ya faɗi maganar tare da ɗauko cingom ya fara ci, abinda na fahimta cin cingom in kila yana da ƙa'ida domin yafi amfani dashi a wasu lokutta wanda shi kaɗai yasan su...
Fita tayi daga ɗakin tare dajan ƙofar garam, har yanzu idanuwa na a rufe suke jikina kuma bai daina kyarma ba, tashi yayi yaje ya kulle ɗakin sannan ya dawo ya zauna, cikin kujera ya tura hannunshi ya zauro wata irin zureriyar wuƙa sai kyalli takeyi saboda sabinta,
Ke zo nan , kamar ina jira na tashi dan nasan babu wata ke a ɗakin sai ni, da sauri na isa gabanshi na durƙusa cikin tsoro na sauke kaina ƙasa, cikin natsatstsiyar murya yace kalli , ɗago kaina nayi na kalleshi amma ba ido cikin ido ba, cikin murya maisa natsuwa yace mi yasa bakijin magana ? Shiru nayi naci gaba da lissafin "yan yatsu na, bana san ina magana ina maimaitawa, raina yana sauri ɓacin ne , banda haƙuri zuciyata a kusa take ina tambayarki kawai ki bani amsa...
Mi ya haɗaki da Muntari kikayi mishi vidio ? Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji kardai Alhaji ya nunawa Dikko vidion nan, Dikko kuwa ɗoro tsinin wuƙarshi yayi daidai saitin maƙoshina, wanda ya shaƙeni a gaban mutane lallai zai iya kasheni tunda babu mai ganinmu sai Allah, ina san ganin idonshi domin ta nan ne kaɗai zan iya gano idan Alhaji ya bashi labarin vidio,
Ɗan kartar min wuya yayi da wuƙar tare da cewa ke nake sauraro, cak na ɗauke numfashina tare da kallon kwayar idonshi sannan nace waye Muntari ? Na tambayeshi ne dan san gano ko gaskiya ne ? Da ƙafarshi ya takamin baki sannan ya halbi daidai saitin hancina har saida jini ya fita.
Ƙasa ƙasa yayo da wuƙar daidai saitin ƙirjina inda daya burma min ita tawa ta ƙare, cikin kuka na riƙe wuƙar tare da cewa to yanzu kuma laifin me nayi maka ? Na ƙarasa maganar hawaye na kwarara daga cikin idona, shima hawaye ne kwance a cikin kwayar idonshi cikin damuwa yace saki wuƙar kinji, sakin wuƙar nayi sannan yace zaki iya kasheni ? Cikin rashin fahimta nace kamar ya zan iya kisa bayan nasan ba abune mai kyau ba ?
Dikko yace tou mi yasa kika zaɓi zunubi mafi muni a rayuwarki ? Kin kuwa san illolin dake tattare da zina ? Kinsan bala'en ta kinsan matsalolin da take haifarwa ? Kina ƙaramar yarinyarki ki tunkari mazan bariki, kinsan bala'e kuwa irin na mazan bariki ? Kinsan haɗarinsu ? Mazan bariki basa taɓa jin tausayin macen bariki kuma basa tattalata basu san darajarta ba haka kuma bazasu taɓa raga mata daidai da ɗigon kwayar zarraba bariki ta fito kuma shi za'ayi da ita tunda sunsan idan sun lalataki gobe ma wata zasu nema, kinga kuwa da wannan bala'e da kika bashi gaba kawai gara ki sokawa Dikko wuƙa ki huta ya ƙarasa maganar tare da miƙomin wuƙar....
Kallonshi nayi amma banyi magana ba, murmushi yayi tare da ciro cingom in bakin shi yace na ƙoshi ko zaki ci ne ? Banza nayi kamar banji ba , ɗaga kafaɗun shi yayi tare da cewa kin huta 🤷🏻♂, ya faɗi maganar tare da maida cingom inshi cikin bakinshi yabi ni da kallon rainin hankali,
Shiru na wasu mintoci sannan yace kinsan abinda yasa nazo dake gidan nan ? Keda ke gidanki idan kinyi magana tou na tankawa Dikko, ci gaba yayi da cewa anan kaɗai zanyi magana dake cikin natsuwa, ki daina hayemin kuma ki rage rashin kunya sannan ki taka a hankali duniya taƙaitacciya ce ga kowa amma babu kamar mace,
Ki taka sannu An mata ki faɗamin duk abinda kike so a duniyar nan ko miye zan miki kuma zan baki idan dai zaisa ki kwantar da hankali ki natsu, kuma ba yau kaɗai ba zan ci gaba da kyautata miki daga nan har ranar da numfashina zai bar gangar jikina zanci gaba da kyautata miki dan kiyi farin ciki , ke yarinya ce baki san komai na rayuwa ba, amma zan sake faɗa Allah ya baki sa'ar rayuwa da har kika shigo rayuwata sheɗan kuma ya samu galaba a kaina, tunda ni zina ba aikina bane ban taɓa ba tunda nake wallahi sai a kanki.
Kinsha dani kuma kin gama dani har badan duniya, kina da matsayi na musamman da bazai taɓa goguwa a zuciyata ba kuma kin shiga cikin babban tarihin da bazai taɓa gogewa ba a rayuwata har abadan duniya , duk wacce ta shigo kece farko, ni haɗuwata dake na barshi matsayin ƙaddara kuma bansan abinda ubangiji yake nufi da ita ba.
Daga ni harke babu wanda yasan abinda anjima zatayi bare gobe, amma ina riƙonki da Allah kiyi haƙuri kuma ki yafemin akan duk wani abu daya faru tsakanina dake, taɓe bakina nayi tare dayi magana ƙasa ƙasa amma baiji abinda nace ba, Eye ? Ya tambayani tare da yatsina fuska yace banji me kike faɗa ba ,
Kai tsaye na kalleshi tare da cewa bazan yafe maka ba har abadan duniya, jinjina kai yayi tare da cewa to ba komai Allah yasa rashin yafiyar shine alkairi a rayuwata, kina buƙatar wani abu ne daga gareni ? Ni bana san komai saboda baka da abinda zaka bani ni bakayi kuɗin da zaka taimakeni dashi ba har yanzu, bai sake magana ba, ya ɗauki wayarshi ya kira mutumin daya kawoni yace yazo ya mai dani gida...
Ci gaba nayi da zage zagena ƙasa ƙasa yanda bazai iya juyoni ba, anan nayi ganganci ɗaya kunsan masu iya magana sunce idan mutum matsiyaci ne ko an sakashi a tandun man shanu aka tsamo shi haka nan zai fito jikinshi ƙamas.
Babu wani ɓata lokaci mutumin ya iso, Dikko yana jin tsayuwar mota yaje ya buɗe ɗakin ki ya dawo ya zauna, da sallama mutumin ya shigo tare da kallona yace muje, tashi nayi tare da ƙara kallon Dikko har yanzu bakinshi yana motsawa cikin salo mai burgewa da ɗaukar hankali yana cin cingom inshi cikin kwanciyar hankali , gaskiya nidai yanamin kyau idan yana cin cingom, amma fa bana ƙaunarshi, bai kallemu ba kuma baiyi mana magana ba hankalin shi yana saman wayarshi,
Nayi tunanin DK zaiyi ta haɗani da Allah ko kuma idan yaga zan tafi zai kirani amma ko ɗaya ba abinda ya faru, haka nan naji babu daɗi haƙura kawai nayi na shiga mota muka tafi, 11:30pm a cikin ɗakina tayi min, daga Nana sai Karima kawai a gidan sunata jajantamin.
Kuma sune suka faɗamin mutuwar Alhaji, nayi kuka sosai musamman ma a lokacin dana ga vidion dana ɗauka muna ai kata saɓon Allah wani irin imani da tsoron Allah ya tsargamin zuciya tare da ganin kamar mutuwa zanyi yanzu yanzu,
Na daɗe ina kukan mutuwar Alhaji a cikin kwanaki ukku daga nan kuma na ɓarar da lamarin zance mutuwarshi muka fuskanci rayuwar bariki.....
Bani canzawa, kuma yanzu aka fara....
Muje zuwa....
26/08/2019
*JAMILA MUSA...* 🤙🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 20
*_Shafin ga gaba ɗayanshi kyauta ne ga group mai albarka da mutanen cikinshi masu mutunci MEELAT MUSA FANS kuna fa sakani nishaɗi idan kuna sharfi nakanyi dariya sosai domin kuma ilimi ne na musamma ngode sosai Allah ya ƙara haƙuri da juriya, wata ma dai wai cewa tayi Oga Dikko ! Star Dikko ubangidan KWARATA , nafa gode Allah ya baku wayoyi masu riƙon caji da caja mai saurin cika hand set amin... Ni Meelat ko ince JAMILA MUSA nake cewa asha karatu lafiya...._*
*_Ina miƙa saƙon ta'aziyya ga "yar uwa kuma abokiyar aiki haziƙar marubuciya Fadeela Lamiɗo ina tayaki jimamin rashin ɗan uwanki Allah ya jiƙanshi ubangiji ya amfani zuri'ar daya bari , Allah ya baku haƙurin rashin sa annabi yasan da zuwanshi, mu kuma Allah ya kyautata namu zuwan bayan nasu ubangiji yasa mu cika da imani idan ajalinmu yazo..... Am3n ya Allah..._*
Duniya sabuwa inji masu iya magana yayin da wani yake kuka a lokacin wani yake farin ciki, kukan mutuwa da jimimmamin rayuwa yana gidan Alhaji Muntari yayin da a gidan da muke haya yau muke shagalewa muna raƙashewa muna cin duniyar mu da tsinke...
Zaune muke a saman tabarma yayin da ni nasha riga da zani na atamfa nayi ɗaurin ɗan kwali na irin na sabbin karuwai, na nemi bakin kwalli na daddaɓawa bakina, ga kitso na matan bariki da aka yanyaramin ɗinki rigata ya kameni sosai duk rabin halittun jikina sunyo waje, kallo ɗaya zakamin kasan ni tantiriyar karuwa ce wacce ta anshi lasisin iskanci bada jimawa ba, yanayi na ya fita a cikinsu kana gani na zaka gane nice uwar gidan *kwarata...*
Miƙe ƙafafuwa na nayi a saman tabarma nayi zama irin na matan da basu da kamun kai, a gefen damata Amisty ce zaune da jaddawalin sabuwar bariki mai fara aiki a cikin satin nan..
Nana , Karima , Hafsa , Amisty , A ` i da Saude duk suna wurin daga gabana suna ta bani wani irin matsayi na musamman sai kace nayi musu asiri zakayi mamakin yanda suke darajani, yaran nawa dai su shidda ne duk dani mun zama bakwai mune sabbin *kwarata* a cikin wannan zamani kuma nice shugaba kuma zanzo da salon da tarihina bazai gogu ba a cikin tarihin birnin garin katsina...
Juyawa nayi gefen hagguna zuga ce ta "yan daba dana ɗauko su haya zan riƙa basu albashi duk ƙarshen wata, dalilina kuwa na ɗaukarsu duk yana cikin labarin, sunsha kitso irin na ɗiyan kafirawa kallo ɗaya dai zakayi musu ka tabbatar sunsha iskanci sun ƙoshi...
Saida na gama kallesu tsaff sannan na fara nazari da tunani , na farko dai zamanin ga ya canja rayuwa bata tafiya dole saida ilimi, waye zan samu mai amana da zai riƙa karantawa rubutuwa da fassarawa idan anmin turaci, babu shi zuciyata ta bani amsa tare da cewa karki sake ki yadda da matan bariki dan basu da amana...
Kallon Amisty nayi tare da cewa karanto min ina saurarenki, miƙomin takardar tayi , murmushi nayi bance komai ba na ansa, biro na ɗauka na juya bayan takardar nayi rubutu da labarci kamar yanda nayi a police station miƙa mata nayi bayan na gama rubutawa sannan nace haɗa dukansu ki karanto ina saurarenki...
Zazzare ido ta farayi ta ƙurawa jaddawalin ido, alifun kanshi idan zaki kasheta bata iya karantawa ba, ganin ta kasa nace tou ki kiyayi kanki da duniya duk baiwar ki wani yafi ki, kece kika rubuta kuma kece zaki yaɗa ba kowa ba, karki damu basai naji abinda ke ciki ba, kije kawai....
Ku tashi muje na faɗi maganar tare da miƙewa tsaye, ɗaki na koma na ɗauko gyale na sannan na fito, gaba nayi zugar daba ta da tasha suka biyoni baya harsu Nana ba'a bari ba, ina gaba suna bayana "yan daba kuma suna gaba cikin siga mai kalar bada tsoro,
Gidan da zan siya a cikin anguwarmu mukaje dubawa, ƙaton gida ne sosai akwai ɗakuna birjik ɗaki yakai goma sha ukku, sai bayi guda biyu sai baranda inda ake dafa abinci, amma gidan gidan ƙasa ne irin tsufin ginin da can can, akwai yalwataccen filin tsakar gida...
Nidai gidan yamin sauƙi gaskiya ko dan ina matse na siya ? Miliyan biyu aka masa kuɗi babu gudu babu ja baya gaskiya yayi arha dan da a bakin titi yake bazan iya siya ba , daren jiya na bada miliyan ɗaya da rabi, nace zan cika sauran yau idan Allah ya kaimu....
Shine muka zo gani da kowa , gaskiya sun nunamin farin ciki sosai kuma basu nunamin hassada ba, bayan mun gama dubawa muka fito, tunda muka fito yanayin yadda naga anguwar tayi shiru ya taabbatar min Dikko ya shigo...
Shine kuwa ɗan iskan , ya fito daga gidan dokunan shi na anguwarmu da yake daga get in gidan zaka iya hango komai na cikin anguwar idan aka shigo santar kuma gidan dokunan Dikko yake kallonka,
A tsiyace ya fito kamar yadda ya saba, duk tawagata suka koma da gudu baya suka kauce daga saman hanya yayin da ni kuma na shigo hanya hankali kwance Amisty ta taho da gudu zata jawoni wani mutum ya riƙeta dan a ganinshi biyu babu za'ayi tunda dai ni na tafi sunamin addu'a Allah ya jiƙana, ihu Amisty ta farayi tare da cewa Sultana don Allah karki biye wa zuciya ki dawo ko ki gudu bana so ki mutu yanzu wayyo Allahna, kowa duƙar da kanshi yayi yayin dana tsaya cas kuma Dikko ya sheƙo da gudun tashin hankali, wallahi da bani bace ko wacece sai Dikko yabi ta kanta ya wuce babu abinda ya dameshi...
Gab dani ya taka wani irin wawan birki ya fito cikin tsananin ɓacin rai ko mota bai tsaya rufewa ba , hannushi ya ɗaga da niyar marina kuma ko meye ya hanashi ya mareni Oho, ganin ya juya zai koma mota nace Allah ya auna maka arziƙi yau dasai nasa anyi maka fiɗa irin wacce akewa raguna, daka takani ko ka bigeni dasai naga ko waye ubanka a garin nan...
Uhum yace tare dayin gajeran murmushi da gefen bakinshi sannan yace ake yarinya ce a tunaninki kama nayi miki da ɗan wa a garin nan ? Dake da babanki da kowa naki da kike taƙama dashi talakawan mahaifina ne , ni kuma abinda na ɗauki talaka takalmi na ne zan takashi yayin da nake sha'awa in kuma cire na jefar a duk lokacin dana gaji da ganinshi, ke abinda na ɗaukeki baki da banbanci da dabbar layya a wurina ina kiwonki ne kafin ranar da zan yanka ki , abinda yasa kuma banbi takanki na wuce ba idan na kamaki zaki basu labari...
Murmushi nayi tare da cewa duk takalmi takalmi sunanshi amma ko a cikin takalmin wani baka sakashi yayi maka daidai, talakawa suna taku amma kai da mahaifinka bata tasu kuke ba, duk wadda yace kayi takanshi ne baka zo ba, ba'a saka ka kayi ba'a saka ka daina zakin roba dana sanin mafarauta mugu ɗan gidan mugaye kana mugunta amma kana daɗa suna azzalim baƙin cikin talakawa, kafin ka gama ciwo na ni na gama naka ka saurareni ina dawowa ƙarshen shekaru biyu masu zuwa nan gaba nice maganin tsagerancinka....
Ina faɗin haka ban saurari abinda zaice ba nayi gaba na shige cikin gidanmu da muke haya , tafiya nayi irinta in ka isa wannan ma ka sayeshi....
Murmushin mugunta yayi mai nuni da na gama dake yarinya zaki nemi Dikko ruwa a jallo, juyawa yayi ya koma mota ya fita daga cikin anguwar...
Ban daɗe da shigowa gida ba su Nana suka shigo harda ƙawar Amisty wacce muka haɗu da ita police station tayi cikin shege da aurenta, ɗaki suka sameni ina waya da Bello dan tunin duniya na turawa matarshi hotuna anyi tashin hankali na idon duniya kuma shima hankalinshi ya tashi ya yadda zan iya turawa media hotunan, ya yadda zai bayar da kuɗin anjima bayan sallah isha'i.
Sannu nayi ma kowa bayan na gama waya nace ku zauna mana, wuri kowa ya samu ya zauna, kallon ƙawar Amisty nayi mai cikin shege sannan nace sannu hajiya, murmushi tayi tare da kallon ƙasa cikin yanayin jin kunya,
Ɗan kauda kaina nayi gefe tare da cewa ya akayi da cikin ne ? Ba tare data kalleni ba tace... Wallahi har yanzu bai yadda ba, murmushi nayi tare da cewa bariki da ciki ko goyo wahalalliyar bariki kenan , bariki da tsarin iyali magani ko allura halaka ne saboda baki gwada mahaifarki ba kika tabbatar kina aihuwa ko bakyayi , kallon su Amisty nayi sannan nace tashin farko dai kowa ta nemi gishirinta ta saka a jaka yayin da buƙatar namiji ta gama kammaluwa akanki ki zuba gishiri a bakinki sai ki kora da ruwa,
Nana ta tambayeni maganin me ? Kallonta nayi ido cikin ido sannan nace maganin hana ɗaukar ciki, waye ya faɗa miki haka ne ? Murmushi nayi tare da cewa wani feƙaƙƙen dan bariki mai bariki cikin gidan iyayenshi , tunda kuwa har yasan gishiri yana hana ƙaramin ciki zama a cikin mahaifa ai kinsan ya gogu a harkar bariki.
Dariya kowa yayi tare da cewa wannan dai ai mugunta ce gishiri ai saida yasa maka cuta , ba tare dana kallesu ba nace shigar wata cutar itace take kore wata, Allah dai yasa mu fita bariki lafiya , kowa ya amsa da amin...
Fira dai mukaci gaba dayi daga baya A ` i tace bara suje ita da Saude su anso mukullen shagon da muka kama haya tasan zuwa yanzu sun kammala fenti , sai sun dawo nayi musu suka fita daga ɗakin yayin da Nana da Karima suka fita suma, aka barni dani da Amisty sai Hafsa da ƙawar Amisty matar aure...
Kallona Hafsa tayi tare da cewa uwar ɗakinmu idan babu damuwa nikam ina so na tambayeki. Hankalina yana kan wayata ina ganin rubutun da d c o ya turomin nace ina saurarenki yayin dana kanga wayana daidai saitin bakina nace ni aiki nakeyi ko ka kirani a waya, ko kuma kayomin voice note idan na kunna saina saurara , ina faɗa na tura , yayin da Hafsa tace wai miye tsakaninki da DK ?
Ajiye waya nayi a gefe na sannan na tattara duk hankalina da natsuwa ta wurin Hafsa nace idan na faɗa miki abinda DK yayi min ke kanki sai kinci ubanshi da yake taƙama dashi yana ma mutane iskanci saboda shi , yau ya taɓo ubana yace talakan babanshi ne , nima kuma na taɓo babanshi a cikin magana na, nuna Amisty nayi tare da cewa duk wanda nace ya faɗamin waye uban Dikko a garin nan ba'a bani amsa idan zaki faɗamin Dikko ko waye ubanshi zan faɗa miki abinda ke tsakani na da Dikko....
Hafsa tace Gwamnan garin nan shine uban Dikko, shiru nayi banyi magana ba Hafsa taci gaba da cewa dole sai kunyi haƙuri sannan kuma kunyi ma Dikko uzuri soyayyar da ake nuna masa a gidansu da yadda ake tsoron mishi faɗa yasa yake ganin duk abinda yayi daidai ne a rayuwarshi , wallahi ba'a dakawa Dikko tsawa ba'a masa kallon banza domin mahaifinshi gani yakeyi kamar duk idan akayi masa zai mutu ne , ya ɗauki soyayyar duniya ya ɗora akan Dikko yana mishi soyayyar da duk duniya babu wanda yake ma irinta a rayuwarshi , fitar da Dikko yake yi da duk wannan iskanci da wulaƙancin da yakeyi ubanshi baisan yana fitowa ba , yasan dai ya baro ɗanshi gida...
Cikin jin haushi na kalli Hafsa tare da cewa nikam bazanyi haƙuri ba kuma bazanyi masa uziri ba , can gidansu ya zama dole suyi masa duk abinda kika lissafo amma badai ni ba , wallahi ko Dikko zai mutu saina tozarta shi , saina wulaƙanta mishi rayuwa a garin nan , ki jira zaki ga yanda zanci uban da ya haifi Dikko saina maida shi abun tausayi da kwatance uban nashi kuma duk daren daɗewa saiya gama gwamna ya sauka tunda gidan gwamnati ba gidan ubanshi bane ba...
Shiru Hafsa tayi bata sake magana ba , bayan wani lokaci tacewa Amisty ku tashi mu tafi , gaba ɗayansu suka fita tare da cemin sai Allah ya kaimu , ban basu amsa ba na ɗauki wayata naci gaba da abinda ya dameni.
Hafsa kuwa kamar ubanta na zaga , tana shiga mota ta fashe da kuka tare da kiran wayar Dikko har ta gaji ta haƙura bai ɗauka wayar ba , daga baya ta yanke shawarar tura masa text duk zagin da nayiwa Dikko komai dana faɗa saida Hafsat ta rubuta ta ƙara da nata dan sharrin ya tafi daidai , bayan ta gama ta tura mishi. Sannan taja motar ta suka bar ƙofar gidanmu...
Su Hafsa basu daɗe da tafiya ba su A ` i suka dawo kuma sun tabbatar min cewa shago yayi yanda ake so an tsara shi gwanin burgewa , naji daɗi sosai suma sunyi farin ciki idan Allah ya kaimu gobe lafiya zamu fara fita aiki , saida akayi sallah magrib sannan suka tafi gidajensu.
Bayan sallah isha'i kamar yanda Bello yayi alƙawari ya kawo min kuɗi , a gurguje ya bani ya tafi dan yacemin suna da wasa jiranshi akeyi , a daren nakai cikon kuɗi kamar yanda nayi alƙawari zan bayar a gaban shedu aka rubuta takarda aka bani ....
Umar ne durƙushe a gaban Dikko cewa mai gida kaga dan Allah tunda kazo gashi har zaka koma gobe don Allah kafin ka tafi ka taimaka ka siya gidan wallahi matar tana buƙatar taimako,
Umar yana magana amma hankalin Dikko yana kan saƙon Hafsa , a fili yayi dariya tare da cewa rigima kenan Allah ya baki sa'a akan duk wani kudirin ki akaina An mata , murmushi yayi sannan yace Umar ni babu abinda zanyi da gida , amma nawa ne kuɗin sai in bashi ayi mata aikin...
Ba'a mugun sarki sai mugun bafade , kuma wani abu za'a bashi a cikin kuɗin gidan idan an siyar dashi, dan haka ya gyara zama tare da cewa mai gida dan Allah tunda dai yafi so ka siya ka siya ɗin kawai , kila gidan ne ya gaji dashi tunda da taimakon yake so da zaice ka taimaka mishi.
Dikko yace tou tunda yanzu yayi maganar siyar da gida ai kowa yasan taimako yake nema insha Allah kafin in tafi zan baka ka bashi , Umar yace mai gida abinda yasa nace ka siya gidan kusa da gidajen daka siya ne kaga idan ka siya sai shima a rushe maka a haɗe wuri ɗaya,
Baiyi magana ba sai ƙara kallon text in Hafsa yake yi yana mamakin ɗabi'u irin na An mata da ba gobe zai tafi ba dasai ya ƙara zuwa ya jawota faɗa kuma yanzu dare yayi dasai ya firgito mata hankali , lallai zai haƙura ya riƙa waya da Hafsa dole kodan dan ya riƙa jin halin da Sultana take ciki.
Umar yace mai gida kayi shiru baka ce komai ba , kallonshi Dikko yayi tare da ajiye wayar shi gefenshi yace wato so kake in ƙara baƙin jini ko ? Cikin rashin fahimta Umar yace wurin wa zakayi baƙin jinin ne ? Ajiyar zuciya Dikko yayi tare da kwantar da bayanshi jikin kujera lumshe idanuwanshi yayi cikin shauƙi sannan yace wai An mata ne tace zataji min mutunci bayan shekaru biyu masu zuwa,
Ya ƙarasa maganar yana murmushi , Umar yace haba ranka ya daɗe ina ma zata ganka ? Kafin shekaru biyun masu zuwa kayi mata tazarrar da baza ta sake ganinka ba har abadan duniya , kai babbar ƙaddara ce da kayi nisa da tazara ga duk wani ɗan ƙaramin sakarai , ka siya gidan kawai ka manta da sha'aninta me zata iya maka ne ? Buɗe idonshi yayi tare da cewa baza ta iya min komai ba kuma badan inajin tsoron tayimin ba kawai dai tana bani tausayi ne...
Umar yace bata da kunya ta raina hankalin mutane ka daina tausayinta shegiyar kanta ce , Dikko yace ba itace shegiya ba nine shegen barni dai da Dikko take wasan , zan bada kuɗin gidan na siya , wani irin farin ciki Umar yayi tare dayi ma Dikko godiya saida ya koɗashi sosai sannan ya fita,
Fitar Umar Dikko ya ɗauki waya ya turawa Hafsa saƙo cewa shifa baima gane yarinyar da take magana ba , tayi masa bayani na yadda ya sani ta tuno masa asibiti da dai duk wani abu daya shiga tsakanina dashi Dikko yace sam bai ganoni ba amma idan tana da hotona ta tura mishi ,
Hafsa tace bata da hotona amma zamu haɗu da safe insha Allah zata ɗauko masa ni ya kwantar da hankalinshi , Dikko yace ai dama hankalinshi a kwance yake amma ya zama lallai zai koyamin hankali ,
Tunda gari ya waye muka sha gayunmu kamar yanda muka tsara , motoci biyu aka ajiye a ƙofar gidanmu ɗaya ta Hafsa ɗayar kuma tawa ce sai kenap ɗaya wacce "yan dabana zasu riƙa amfani da ita kuma ni na siyi ,
Dukanmu a ƙofar gida muka fito , muna ƙoƙarin shiga mota mai gidanmu da muke haya yazo bayan mun gaisa yace ya siyar da gidan nan saboda haka duk abinda muke so zuwa jibi mu kwashe kayanmu,
Cikin ɓacin rai nace wai miya sa kuke abu babu adalci a rayuwarku ? Kai kuma nawa ya baka ya siyi gidan dan nasan za'ayi haka tunda har yaga gidan dana shiga nasan wallahi saiya siya , sakaran banza matsiyaci dashi tou idan ka ganshi ka faɗa mishi nayi gidan zama idan yanajin shi wani mai kuɗine yazo ya sayi anguwar nan duka...
Ina faɗin haka nace ku shige muje , gaba ɗayanmu kowa ya shiga mota , Hafsa ta tuƙa nata , tawa kuma driver na samu saboda har yanzu ban iya mota ba , zugar daba ina kuwa suka shiga napep muka tafi, ashe duk abinda na faɗa Hafsa vidio tamin ta turawa Dikko dan ya gani da idonshi ya kuma ji ina faɗa da bakina , ni kuma bansan anyi ba tasan idan ya gani da idonshi dai zaici mutunci na yadda ya kamata bansan abinda ke cekin zuciyar Hafsa akaina ba...
28/08/2019
*JAMILA MUSA* 🤙🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 21
Cikin farin ciki muka isa bakin shagonmu wanda yasha fenti kuma aka gwagwaɗa masa tambarin *kwarata* , tsayuwarmu da fitowarmu shine ya jawo hankalin al'umma masu wuce da wanda suke zaune saboda munzo da sabuwar shiga mai matuƙar bada al'ajabi a karon farko da ta zama abin kallo ga jama'an gari...
Takardun da aka gurzo wanda yake ɗauke da tallar karuwancin mu nasa "yan daba suka raba titi biyu duk motar da zata wuce aka ci gaba da basu babu sauƙi babu sauƙaƙawa !
Bakin shago mu mata muka koma muka jera layi amma babu wacce ta zauna tsaye muke , Nana da Karima suna daga gefe suna kallon ikon Allah ,
Waya Hafsat ta fiddo ta fara latse latse daga baya kuma sai naga ta koma gefe guda tana waya , ta ɗauki tsawon lokaci bata gama wayar ba haka nan kawai naji na tsargu da wayar , bayan ta gama sai ta goge number data kira...
Ƙurawa Hafsa ido nayi harsai data kama kanta , tabbas akwai cuta a tare da rayuwar Hafsa akwai abinda take shiryawa ko kuma take so ta aikata idan kuwa na ganota da wani laifi na cin amana babu abinda zai hana na tona mata asiri,
Yana gama waya da Hafsa ya buɗe saƙon da tace ta turo mishi , ɗan soɓaro baki yayi irin na sakatattun "ya "ya sannan ya cire vidio ya ɓoyeshi a gellery vault bayan ya gama gani...
Saman kujera ya zauna ya saka takalmi har yanzu bakinshi a soɓare yake , saida ya gama sannan ya kalli Al ' Ameen yace mu fara zuwa ta wurin An manta sannan mu wuce don Allah ,
Al ' Ameen yace mai gida da Allah ka fita hanyar yarinyar nan , murmushin Dikko yayi sannan yace wallahi sai anje idan baza kuje ba sai ku jirani ina dawowa , yana faɗin haka yayi gaba , Al ' Ameen biyo bayanshi yayi ƙaramin yaron daya girma kawai zai riƙa juya su dandai suna ƙasansu...
Da sauri ya wuce Dikko ya buɗe mota , ɗan ɓata rai Dikko yayi sannan ya shiga ya zauna tare da kwantar da bayanshi saman lallausan kujeran motar , wayarshi ya ciro yayi mata kyakkyawan riƙo da duka hannayen shi biyu , sannan ya ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya yake faɗawa Hafsat yana zuwa yanzu babu daɗe wa zaizo mata bankwana !
Wata irin kururuwa Hafsa tayi ta farin ciki sannan ta koma motarta da gudu , ƙara barbaɗa powder tayi tare da ƙara shafa turare sosai , sannan ta gyara ɗaurin kallabinta ta fito...
Kallon mamaki nake ta bin Hafsa dashi anya yarinyar nan bazan zameta daga harkata ba ? Tafiyar nan kuwa zata tafi kodai in fita inyi harkata ni ɗaya ? Ina wannan tunanin zuƙa zuƙan motocin Dikko sukayi parking a ƙofar shagon mu...
Cikin rawar kai Hafsa ta tashi tayi wurin motar Dikko , ƙafarshi ya ɗora saman murfin motar , kafin Hafsa ta isa wurin ya zura hannunshi aljihu ya ciro cingom , a daidai lokacin da Hafsat ta isa wurin motar , ko inda take bai kalla ba ya cire cingom inshi a cikin takaddar shi ,
Tahowa ya farayi zuwa wurina tare da ɗora cingom in saman "yan yatsunshi na hannun haggu ya daki tafin hannunshi na haggu da hannun shi na dama , buɗe bakishi yayi cingom in yayi tsalle ya shige ,
Ɗan tsuke bakinshi yayi kamar zaiyi kiss sannan ya lumshe idanuwanshi tare da nuna yanayin kamar abin harin sumbatar nashi yana kusa dashi , muah ya saki kiss a daidai lokacin daya tsaya gabana yaja kujerar rober ya zauna , sai yanzu ya fara tauna cingom ɗin cikin izza da nuna shi wani isashshe ne , ɗago ƙafarshi yayi ya biyo da ita ta saitin fuskata kamar zai takamin fuska naɗan ja baya , murmushi yayi tare da ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya :•
Robar ruwa Al ' Ameen ya miƙowa Dikko bayan ya zauna , ɓalle murfin robar ruwan yayi yakai bakinshi yana kallona , shan ruwan yayi sannan ya cika bakinshi dashi ya miƙawa Al ' Ameen robar ruwan , murmushi yayi da gefen bakinshi sannan ya fara bultso ruwan daga bakinshi suna watsowa saman fuskata...
Ƙoƙarin tashi na farayi dan banda lokacin Dikko a yanzu sai bayan shekarun dana iba , ina ƙoƙarin tashi ya maidar dani ya zaunar da ƙafarshi nayi na tashi na kasa saida ya gama watsa min ruwan sannan na buɗe idona daya cika da hawaye na kalleshi ,
Murmushi yayi sannan yayi magana cikin sigar lallashi haba ke ko an mata komai saurin kuka ke baki san wasa ba ? Karfa ki ɗauki abin da zafi albarka na saka miki , kin zageni tass amma zagin yamin daɗi bayan shekaru biyu idan muka fara farautar juna a ranar zaki gane Dikko ba zakin roba bane , zakin gaske ne farin ciki mafarauta , maganar dana faɗa mishi jiya, cewa zakin roba dana sanin mafarauta, ci gaba yayi dacewa dani dake duk wanda ya fasa , ya jinjina kainshi tare da nunani da hannu ,
Tura kujerar da nake zaune yayi da ƙarfi da bango bai tareni ba babu abinda zai hanani faɗuwa , Al ' Ameen ya kira da sauri yazo tare da miƙo mishi wata "yar ƙaramar jaka tashi yayi ya duƙo kusa dani sosai lumfashin shi yana sauka saman jikina , saman jikina ya ɗora tare da cewa ga cingom nan zai isheki amfani daga nan har zuwa lokacin da zamu fara wasa , ɗan taɓe baki yayi tare da kallon wani wuri daban sannan ya juyo ya kalleni da magana zaiyi kawai sai fasa...
Miƙewa yayi ya juya ba tare daya sake cewa komai ba , bayanshi Hafsa tabi saida ya shiga mota ya zauna sannan yasa Al ' Ameen yayi rabon kuɗi wa duk wanda muke tare dashi har "yan dabana saida Dikko yasa aka basu kuɗi amma nidai bai bani ba kuma ban damu ba saboda dama ni basu nake jira ba !
Al ' Ameen yana gama rabon kuɗi ya koma mota , har yanzu Dikko ni yake kallo gilashin saitin shi Al ' Ameen ya ɗage zuwa sama sakamakon da yake ƙasa , bai daina kallona ba har Al ' Ameen yaja motar suka tafi ,
Goge fuska ta nayi da hannu na , sannan na buɗe jakar da Dikko ya ajiye a gabana , irin cimgom in da yake amfani dashi ne sai farar takarda da akayi rubutu a samanta , suke nan a cikin "yar jakar , ban buƙatar dubawa sabona nasan gani kawai zanyi bazan iya karantawa ba, kuma babu wanda zan ba ya karanta min saƙon Dikko daga nan har lokacin da zan iya karantawa da rubutawa....
Tunda Dikko yayi min wannan wulaƙancin ban sake magana ba har aka gama raba takardunmu muka koma gida ban sake magana da kowa ba , kuma tunda nayi wanka na shiga ɗaki ban sake fitowa ba saida gari ya waye '
Bayan na gama duk abinda nakeyi na fito tsakar gida na zauna saboda ba yau zamu fara fita ba sai an fara kira a waya lokacin zamu tabbatar da cewa tallarmu ta samu karɓuwa a wurin jama'an gari,
Nana na gani riƙe da kwalar rigar mijinta tana zazzaga jikinta irin abin nan da yara keyi idan suna faɗa , zama nayi ba tare dana kalli inda suke ba amma hankali na da kunnuwa na suna wurin su , wallahi sai ka sakeni kalmar da naji ta fito daga bakin Nana kenan kuma har yanzu bata saki rigar mijin ba.
Audu yace ba ƙin sakinki zanyi ba amma sai kin faɗamin abinda nayi miki wanda yasa kike so na sakeki ! Nana tace lallai bama ka da kunya da har kake tambayar abinda kayi , tou na gaji da zaman cida kaina zaman wahala zaman kunci kullin muna can barbaɗe kayanmu a saman kai bama ƙerau bama sabuwar anguwa zama gidan haya , tou wannan aure dai a sahalewa juna uban kowa ya huta...
Daga inda nake zaune nace Audu wai duk meya haɗaku ne wai ? Ku kullum faɗa ke Nana kamar kece kaɗai matar aure a gidan nan ? Duk wadda kika gani da mijinta haƙuri takeyi ko suna wani saɓani basa fitowa tsakar gida ke kullum dake da mijinki kamar abokan faɗa ? Gaskiya ki daina wannan rayuwar kece ƙasan Audu dole sai kin kiyaye idan har kina san ganin daidai a rayuwarki.
Sakar mishi riga kizo kiji wata magana, babu musu ta sake rigar mijinta ta taho wurina, shi kuma Audu fita yayi ba tare daya sake cewa komai ba,
A ƙofar gida kuwa A ` i ce ta tare Audu bayan gaisuwa tace mishi naji shiru ya kamata kayi wani abu don Allah , zama Audu yayi a saman dakali sannan yace ki ƙara haƙuri , murmushi A ` i tayi tare da cewa ba komai Allah ya tsare ya dafa maka akan duk lamuranka , da amin ya amsa sannan ya wuce ita kuma ta shigo cikin gidanmu...
A ƙofar ɗakina A ` i ta samemu ina bawa Nana shawara , amma tana zuwa gaba ɗaya ta jagula komai ta ida firgita Nana har na kasa gano gabanta bare bayanta,
Ajiyar zuciya nayi tare da bin A ` i da kallo ban sake magana ba ina dai jinta tana ta ɗora Nana a hanyar banza ita kuma tana ta karɓewa dan a ganinta shawarar A ` i itace mafita a gareta ,
Ƙawar Amisty da tayi ciki suka shigo da sallama ita da wata mata , inda nake zaune suka nufo gaisawa sukayi dasu Nana sannan sukace wurinki muka zo , miƙewa nayi tare da cewa ku shigo na faɗi maganar tare dayin gaba suka biyo bayana !
Wurin zama na basu sannan nima na zauna muka gaisa , bayan gaisuwa ƙawar Amisty tace Sultana kin ganeni kuwa ? Murmushi nayi ban bata amsa ba , taci gaba da cewa idan da hali nima zan shiga ƙungiyarki , ga ƙawata itama zata shiga, kallo nabi su dashi bayan wani lokaci nace ita ƙawar taki tana da aure ne ?
Dukanmu matan aure ne , Ni suna na Fadeela inji ƙawar Amisty mai cikin shege , sai kuma ta nuna ƙawar da suka zo tare tace ita kuma sunan ta Zalifa , saida na ƙara kallesu tsaf sannan nace miye dalilinku na shiga wannan ƙungiya ... ?
Wacce aka kira da Zalifa tace wato ina da wata damuwa ce ta musamman wacce bazan iya biyanta ba ko cika burina ba dole saina shiga wannan ƙungiya mai albarka , ina so na samu goyon baya da taimakon tantiran dake cikin wannan ƙungiya ,
Murmushi nayi sannan nace wannan wace irin damuwa ce ? Gyara zama Zalifa tayi tare da cewa wato ina da wata maƙociya wacce na ɗauki amana da yadda na bata , bana ɓoye mata sirrina ko kaɗan .
Wata rana ta shigo gidana sai taji muna hayaniya da mijina , bayan mun gama mijina ya fita sai take tambayana abinda ya haɗamu , ban ɓoye mata ba kamar yadda na saba na kwashe komai na faɗa mata ,
Na ƙara da cewa bansan abinda nayi masa ba duk abinda bai taka kara ya ƙarya ba sai yayi ta faɗa akanshi wani lokaci ma hada duka , sai tacemin yadda Allah ya halittani da kyakkyawar siga mai burgewa na kashe aurena zan samu wanda yafi mijina ,
Nuna mata nayi cewa bana iya kashe aure na amma zan haƙura gaskiya na zauna dashi a haka tunda ina sansa wata rana zai gaji ya daina , sai tacemin ai sai anbar zomo yake zama guza , mazan yanzu da asiri ake ladaftar dasu in bada kuɗi taje ta nemo min asiri inyi maganin mijina.
Banji wani komai ba na bata kuɗi masu yawa dan tacemin itama mijinta da yake mata biyayya malamin yayi mata maganinshi , kuma naga yadda mijinta yake mata biyayya sosai kuma yanajin shakkunta dan haka na bata kuɗin nima a samomin asirin in riƙa dawwara mijina...
Haka kuwa akayi tayi ta kawo magani ina barbaɗawa mijina a abinci ina zuba mishi a ruwan wanka da abin sha laya ƙarƙashin filo wasu layun a ƙarƙashin gadonshi , tunda safe kafin ya fita na kunna hayaƙi , shirka dai iri iri da ƙazanta nayi ta barbaɗawa mijina yana lashe wa ,
Haka tayi tamin wayau tana karɓemin kuɗaɗe , murmushi tayi tare da cewa kinsan me ya faru ? Nace mata A , a, tace kwasam sai ta tayar da fitina wa mijinta da yake aurenta , kuma yanayi mata wani irin azababben so yana ƙaunarta fiye da duk yanda zan faɗa muku , amma saida ta kunno masifa ya saketa , har wannan lokaci bata daina kawomin asiri ba ,
A daren ranar data kawomin magani na zubawa mijina a abinci yana gama ci babu laifin zaune babu na tsaye ya gwagwaɗamin saki 3 ita kuma ta aure min miji gani nan na fito bani ga tsintsu bani ga tarko kinji hukuncin da tayi min....
Murmushi nayi kaɗan sannan nace kin aihu da mijin ne ? Tacemin a , a , nace ita ubanta yana raye ne ? Tace min Eh nace ya yanayin samunshi yake ? Tace babu laifi gaskiya yana da rufin asiri , da kyau nace tare da cewa mijinki kina san ki koma gidanshi ko kuwa ya kike so ? Zalifa tace gaskiya bazan koma ba so nake kawai ku riƙe mishi wuya ku jawo shi a cikin ƙungiyarku ku ƙare duk wani tattalin arziƙinshi babu asiri Sultana ki fitar min ita daga gidan...
Jinjina kai nayi tare da cewa ni bana asiri amma sharrina da kaidina yafi asiri bala'e a rayuwar ɗan adam , waya na bata tare da cewa sakamin lambar mijinki ki ajiye min ita da lamba 4 , ansa tayi ta sakamin tayi saving kamar yanda nace , bayan ta dawomin da wayana nace babanta a wane anguwa yake ne ? Zalifa tacemin gaskiya bai cika zama ba , nace to karki damu zai zauna dan dole ki samo numbershi ni kuma nayi miki alƙawari su dukansu zamuyi musu aiki ...
Zalifa tacemin ina da motar hawa idan zakuyi amfani da ita , nace tou yayi kyau mun gode , jakarta ta buɗe ta fiddo kuɗi har naira dubu ɗari ukku tace gashi taba ƙungiya tata gudumawar , godiya nayi tare da ƙwalawa A ` i kira nace ta kawo musu form su cika , Zalifa tace karki damu zan cika anjima idan muka dawo akwai inda zanje yanzu , nace tou babu damuwa sai kun dawo...
Miƙewa sukayi zasu tafi nabi bayansu dan rakiya amma ban wuce ƙofar ɗakina ba , anan na tsaya nayi musu addu'ar sauka lafiya , bayan sun fita na koma ɗaki naci gaba da "yan hididdumu na , na tattara kaya saboda zamu tashi daga gidan yau zuwa sabon gidan da na siya , kuma duk nace matan gidan subini mu koma gidana da na siya , sauran ɗakunan da suka rage zan nemo "yan gidanmu na tattara su wuri ɗaya hadashi gogon wato Babana dan nafi so nayi karuwanci a gaban idonshi ya gane cewa ba'ayiwa iskanci haye....
29/08/2019
*JAMILA MUSA ...* 🤙🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 22
Saida na tattara duk wani abu da nasan ina buƙata na adana shi a ma'adar da nasan bazai wulaƙantu ba , ko wace macen da zamu koma da ita gidan nice nasa aka kwashe kayan kowa aka kai gidan da zamu koma da zama...
Kafin azahar har mun gama saboda babu mai gado a cikinsu duk dai katifa ne kuma babu macen dake da ledar tsakar ɗaki saini !
Saida na tabbatar an ajiye komai a mazaunin daya kamata , sannan na shiga wanka , kafin in fito an share gidan ƙwal gwanin burgewa , Hafsa tazo sai kashe sulfie sukeyi ita da sauran jama'ar tamu ,
Ina fitowa daga wanka tace uwar room maza ki shirya kizo ayi dake kar a baki labari , Amisty ce tace babu wani uwar room uwarmu ce gaskiya a wani cire room kawai mu kirata da mother , shewa sukayi dukansu lokaci ɗaya suna cewa uwa...
"Yar gajeriyar dariya nayi cikin sigar barikanci na wuce ɗakina banyi musu magana ba , hotuna sukaci gaba dayi har na gama shiryawa nima na fito !
Ina fitowa suka ɗauki sowa domin sun san mother tasu ba daga baya ba wurin iya ɗaukar wanka , banje koya ba kuma babu wanda ya ɗorani nice na koya dakai na kuma ni na ɗaura kaina , banda uwar ɗaki nice uwar ɗakin kaina kuma nice uwar ɗakin wasu ,
Amisty ce ta bani kujerar roba na zauna, da "yan daba da duk wata kwartuwa mun hallara wurin, bayani na farayi musu kamar yadda muka saba a duk lokacin da muka zauna...
Hafsa kuwa ciro wayarta tayi ta faramin vidio kamar yadda naga ta koya kwanakin nan, saboda haka sai nayi shiru yayin da su Amisty suka ci gaba da goga bayani tare da ƙara ƙwarara wa kowa guiwar shi a cikin harkar bariki !
Komai ɓaro ɓaro sukeyi suna sakin maganganu yadda harshen kowa yake iya furtawa, Hafsa kuwa abinda yasa banyi mata magana ba na lura da halayyarta tana da saurin hasala sannan kuma tana da ɗauka da ajiyewa , na ukku kuma abinda na lura da ɗabi'ar ta zatayi tonan asiri haka kuma zatayi cin amana zata tona asirin wanda suke tare idan suka rabu ...
Ni kuma banda haƙuri idan abu ya ɓatamin rai saina bigi mutum nake samun natsuwa , tou zan ƙyale Hafsa amma nasan irin zaman da zanyi da ita , sannan nikam dai sirri na ƙarya takeyi taji shi kuma anƙi a rabun da ita dan idan har na rabu da Hafsa zata yankamin ƙunya biyu dani da "yan team inta zamu zama abokan hamayya , kuma babu abinda zai hana asirce asirice saboda su sun ta allaƙa da malam tsibbu amma maganinta ɗaya shine zan sace wayarta ta ɓace kwata kwata babu layi babu wayar bare kuma tabi tsohon tarihin jerin kira ta samu wasu lambobi, idan taƙamarta sabko tabbas ni a wurin na kwana ,
Har aka gama zaman ban sake cewa umm umm ba, bayan an gama duk suka zagayeni akayi ta hotuna , duk wanda yaga hotunanmu yasan ni iskanci na ya fita daban a cikin nasu, yadda suka bani shugabar iskanci tabbas iskanci ya fito a tattare dani...
Bayan an gama hotuna muka fito ƙofar gida , saman motar Hafsa nayi tsalle na haye , Hafsa tace bari in ƙara ɗaukarki hoto murmushi nayi tare da cewa ngode , ɗaukana tayi nanma kowa ya ƙara yayyaɓeni sai an mana maza da mata duka Hafsa taci gaba da bamu filasha !
Saida ta gaji da ɗauka sannan mukayi sallama da ita , ta wuce gidansu mu kuma muka koma namu gida , dukanmu a ɗakina muka sauka , har dare suna nan domin Amisty zata kwana wurina ne kuma ma dai ta dawo wurina da zama kwata kwata...
Bansan abinda yasa ba kuma ban tambayeta dalili ba , sai dare sosai su A ` i suka tafi gida , Nana da Karima kowa ya shige ɗakinshi muka rage daga ni sai Amisty, addu'a nayi na kwanta bacci ,
A ɓangaren Hafsa kuwa dan ta wulaƙanta ni ta tozarni a idon Dikko idan ina da sauran mutunci ko ƙima ta kakkaɓe a wurin shi , duk hotunan data ɗauka gaba ɗaya ta tura mishi su , da vidio maganar dana fara da kalaman batsar dasu Amisty sukayi , da kirana da uwar gidan kwarata da akeyi duk saida ta bawa Dikko labari bayan ta gama tura hotunan da vidio ',
Idan ran Dikko yayi dubu saida ya ɓaci amma bai nunawa Hafsa ba ranshi yayi mishi babu daɗi ba dan baiyi tunanin irin wannan hotunan zata riƙa kawo mishi ba , kawai dai ya ɗauka hotunan Sultana zata turo sai kuma idan tana zaginshi sune kaɗai zata faɗa , amma wannan vidio ya girmi ganin idanuwanshi maganganun sun girmi jin kunnuwanshi ,
Tabbas zai takawa Hafsa burki da irin wannan vidio kuma zai tsawatar da ita zai gwalashe abun idan ba haka ba irin wannan vidion na An mata zasuyi ta yawo a social media shi kuma idan har haka ya faru baiji daɗi ba,
Tunani dai barkatai a zuciyarshi , amma ranshi da zuciyarshi yafi bashi cewa kayi mata magana gaskiya shekaru biyu idan suka tafi a haka kaga zakayi takon saƙa da karuwa mutuncinka martabarka da ƙimarka zai zube a wurin al'umma ga siyasa bata raina abun magana, sai ka tsaya takara zaka gane abun ya zama shirme, shawarar da zuciyarshi ta yanke shine ya fita daga harkar taron yara don asali nasaba da mutunci gidansu ba iri ɗaya ne dana gidansu Sultana ba.
Burun duniya akan shi ɗaya tal mahaifinshi ya dogara yayi tsayuwar arfa wurin ganin ya zama mutumin kirki ya fito cikakkan mutum ya kashe kuɗaɗe da yawa wurin ganin ya tsaida ni a saman ƙafafuwana , mutane suna cewa duk "ya "yan da aka ɗauki soyayyar duniya aka ɗora musu gurɓatacci ne , mafiya yawansu basu da tarbiyya , ni kam ba lalatacce bane domin idan nayi duba da yadda nazo...
Tsoki yayi tare da kiran Hafsa yayi mata tatas yace daga ita harma Sultana duk zaici mutunci su bayasan maganar Sultana haka kuma itama bayasan ta sake shiga sabgarshi ko kiranshi ta sakeyi ko text wallahi sai yasa an kulle mishi ita , yafa ci uban Hafsa sosai ya ƙara da cewa itama Sultanar ta sake ambatar sunanshi wallahi zaici ubanta ne, saida ya tata iskanci mai isarshi ya kashe wayarshi,
Al ' Ameen yace mai gida lafiyarka kake ta faɗa , idanuwa jajir Dikko yace Al ' Ameen idan aka ce maka na taɓa zina tsakaninka da Allah zaka yadda ? Al ' Ameen yace mema yasa kake faɗar wannan maganar don Allah ka daina abinda ma bazai taɓa yuwuwa bane ba...
Idon Dikko cike da hawaye yace kasan yarinyar dana shaƙe a asibiti ? Al' Ameen yace Eh nasanta mai gida , Dikko yace kaga ai yarinya ce sosai ko ? Al ' Ameen yace Eh , Dikko yace wallahi da nayi auren wuri ina iya haifar yarinyar nan , amma tsautsayi da ƙaddara yasa na saki wani irin ƙatoton layin da inaji kamar in cakawa kaina wuƙa in mutu kawai in huta,
Murmushi Al ' Ameen yayi tare da cewa haba mai gida ina kai ina haifo mai shekarun yarinyar nan , da kayi aure kam da wuri baka tsaya karatu ba kuma gashi har yanzu duniyar nemanta akeyi duk wanda kuɗi yayi ma yawa so kawai yake a kirashi ranka ya daɗe , duk dai haka gaskiya baka haifi yarinyar nan ba , tsoki Dikko yayi tare da ɗaukar wayoyinshi ya shige ciki , gefen gado ya zauna tare da zagba tagumi ya fara tuno wa kanshi ko shiɗin waye.....
*_WAYE DIKKO...?_*
Dikko Umar Kurabau shine cikaken suna na...
Mu cikakkin asalin "yan cikin garin katsina ne , bamuyi rayuwa a ƙauyen kurabau ba haka mahaifina da kakana basu rayuwa a wannan ƙauye ba , amma kakan dadyna shine yayi rayuwa a cikin wannan ƙauye dake ƙarƙashin kauyen rimi local government...
Mutane ne masu cikakken arziƙi da wayewa kuma sarautar kauyen a gidansu kakana take wacce suka gada suma tun iyaye da kakanni , ko a wancan lokacin mutanen kurabawa tuni su wayayyu ne kuma tuni suka waye da ilimin zamani !
Kakan dady na duk da yake bakauye baya da kidadanci haka kuma bashi da jahilci , wayyen tsoho ne da yasan rayuwa , kuma tsohone mai cikakken ilimin addini,
Abinda ya kawo kakana cikin birni shine neman ilimin zamani , kuma shima mahaifinshi shine mutumin daya fiddoshi dan neman ilimi bayan ya tabbatar daya haddace al'kur ani mai girma a saman kanshi kuma yasan littafai na musulinci .
Karatun boko bai wani bashi wahala ba saboda yana da ilimin addini sosai , saida kakana ya gama karatun sikandire sukul { Secondry school } ya koma kauyen kurabau,
Mahaifinshi yace tunda ya ɗagawa ƙauyen na wasu shekaru ya haƙura kawai ya koma cikin garin da zama , dan a samu ci gaban rayuwa !
Mahaifinshi da kanshi yazo ya nema mishi wurin zama sannan ya bashi kuɗaɗe ya kama kasuwanci ya nemi abinda zai dogara da kanshi, dan a wancan lokacin idan mutum yayi secondry sch anan yake tsaya dan duk wanda yazo wannan matakin gani ake an ƙure.
Allah kuwa ya saka ma nemanshi albarka dan kano yake zuwa sarin atamfofi da shaddoji da yadika ,kafin shekar ya zagayo abubuwa sun fara canzawa domin Allah yasa ma neman albarka kuma Allahn ya yaddar mishi ! Dan ubangiji dayace maka zama zaka zama....
Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin ƙanƙanin lokaci sunan Dikko Muhammad wato kakana ya fara zagawa a cikim garin katsina dan zuwa wannan lokaci ya baza yara suna neman mishi kuɗi dan kasuwar tafi ƙarfin mutum yanzu, kuma mutum ne shi mai kauta ,
Shi kuwa Muhammad baban Dikko wato kakan babana ganin dukiya ta fara yawa hankalinshi ya fara tashi gashi har yanzu Dikko baiyi auren farko ba , kuma zuwa wannan lokaci ya rage zuwa gida dan sai yayi wata shidda ko fiye da haka baije gida ba , idan yaje malam yayi mishi magana yana daɗewa baizo ganin gida ba sai yace abubuwa sunyi yawa yanzu ma dakel ya samu yazo,
Ganin haka yasa malam ya yanke shawara aura wa Dikko mata kuma "yar nan cikin ƙauyensu dan malam yace idan "yar gida ce yake aure dole za'a riƙa ganinshi ko baizo dansu ba zaizo dan matarshi,
Haka kuwa akayi malam ya aurowa Dikko mata bada saninsa ba yasa aka kawo mishi amarya har katsina, saida aka kawo amarya akayi masa bayani malam ya auro masa ita , bai wani ji komai ba yace Allah ya basu zaman lafiya,
Zaman lafiya sukeyi da matarshi Binta saboda matace mai haƙuri da kuma kauda kai da duk wani abu na rayuwa , saboda itama sai tayi wata nawa bata ga Dikko ba dan shi ba auren yake saurare ba duniyar kawai yake nema ita kuma Binta bata wani damu ba tunda ci da sha har sutura bata rasa ba , idan Dikko yazo mata as miji zasuyi rayuwar aure idan baizo ba babu abinda ya dameta...
Haka dai rayuwarsu taci gaba da tafiya , kuɗin Dikko kuma har an fara zarginsu a cikin gari cewa tsafi yake yi , dan shima kanshi zuwa yanzu baisan iyakar abinda ya mallaka ba , koda Binta ta samu ciki gida Dikko ya maida ita ta aihu , tunda ya kaita bai sake komawa ba har ta aihu ta gama wanka baije ba, abinda ta aifa ma bai gani ba babanshi yayi duk abinda akeyi ma duk macen data aihu komai anma Binta da ɗanta da yaci suna Ummar wato mahaifina...
Har Umar ya iya tafiya Dikko bai dawo ba kuma bai aiko ba yana can yana neman duniyarshi danshi matan ma basu ne gabanshi ba kuɗi kawai, baisan komai ba kuma baya gane komai sai naira , abun ƙauye aka fara tira iyayen Binta su kashe auren su mayar da Baban Dikko ɗansu tunda dai ɗanshi ya zama ɗan iska, Binta kuwa ta kifa kanta ƙasa tace ita duk duniya babu wanda ya isa ya kashe mata aure,
Ganin za'a kashe mata aure dole yasa ta saɓe abunta ta dawo wurin mijinta , koda Dikko ya dawo gida ya sameta yaji daɗin dawowanta yace tayi haƙuri abubuwa ne sunka sha mishi kai da yawa da yawa shi yasa baizo ba , tace ba komai da yake itama bata da matsala.
Can ƙauye kuwa da aka tabbatar da Binta ta koma wurin Dikko iyayenta sunsha zagi da tirr da Allah wadai da halin ɗiyarsu, basu da yadda zasuyi tunda suma basu san Binta zata koma wurin Dikko ba dan batayi shawara dasu ba ta tafi.
Tun lokacin da Binta ta dawo wani abu bai shiga tsakaninta da Dikko ba , ita kanta wahalar gani yake mata dan yanzu kasuwancin nashi ya fara ketarawa , kuma babu damar taje ta faɗa gida dan tun abun baya damunta yanzu harya fara damunta.
Yau kam ta hana idonta bacci ko Dikko zai kai safiya bai dawo ba zata jirashi kuma yau za'ayita ta ƙare , koda Dikko ya dawo gida daɗin bakin yayi ma Binta kuma ta haƙura amma kam a daren nan sunɗan caskaɗe dan tunda ta dawo wannan shine haɗuwarsu na farko,
Tou haka kwanciyar auren ta koma duk lokacin da Dikko ya kwanta da binta wani rantsetstsen rabo zai fita , adadin yawan "ya "yansu adadin yanda Dikko ya kwanta da ita , yanzu tayi yara bakwai ,
Kuma rabonshi da gida tunda ya maida Binta aihuwar Babana bai sake zuwa ba har Binta tayi "ya "ya bakwai , saida itace kaɗai take zuwa, mahaifin Dikko kuwa yayi danasanin kai Dikko birni ,
Haka rayuwar taci gaba da tafiya saida malam ya rasu Dikko yaje ƙaunye ta'aziyya, mahaifiyarshi kuma tayi kuka da tir da rayuwar birni, da yake shegen wayau ne dashi lallashinta yayi saida ya kwantar mata da hankalinta sannan yace tunda bata da komai a ƙauye zai tafi da ita birni !
Haka kuwa akayi bayan addu'an bakwai suka tattaro suka dawo tare da kakar babana, zaman kakarsu dady ta gano Dikko bata mace yake ba , ta jinjina wa Binta da wannan haƙuri, ita dai batace komai ba tana dai kallon ikon Allah..
Ummar wato Dadyna, yana gama secondry sch Dikko ya korashi ƙasar waje karatu dan bayasan ganin yara kusa dashi, tafiyar Ummar babu daɗewa kaka Dikko ya tsirawa kanshi aure rana guda aka kawo mishi mata biyu shi mai kuɗi, idan an haɗa da binta sun zama 3 kenan.
Nan fa haihuwar gasa ta tashi mata sunga kuɗi duk shekara sai an direwa Dikko "ya "ya amma banda Binta dan ita tana mamakin ma yaushe Dikko yake kwanciya dasu sakamakon ita ? Ko kuwa dandai su shine ya auro su da kanshi Oho,
Tunda Dady ya tafi karatu Kaka Dikko ya hanashi dawowa , da yaga mai zai matsa mishi saiya dawo ya tusheshi da kasuwa can yace ya nemi kuɗi ya manta da rayuwar nigeria shima haka babanshi yayi mishi.
Duk da Ummar yana ɗan farko saida Binta tayi magana a maido mata ɗanta karya halaka cikin duniya , Dikko yace bazai maido ba, shi ya akayi bai ɓace ba da babanshi ya kawoshi birni, dole Binta ta haƙura ta dainawa Dikko maganar Ummar , itama kakar Dady tayi harta gaji Dikko bai dawo da Ummar ba,
Kwanci tashi asarar mai rai , abubuwa da dama sun faru a ciki kuwa hada rasuwar Kakar Dady , Dady kuma yayi shekaru kusan 15 yana ƙasashen yahudawa, tun yana marmarin gida shima harya goge ya janye zance gida a rayuwarshi.
Shi kuwa Dikko yanzu hankalinshi ya tashi saboda mata sun tara tulin ɗiya sai meeting ɗin kasheshi sukeyi su kwashi dukiya , wannan dalili yasa ya cire Binta a gidan ya sake mata mazauni ita kaɗai daga ita sai "ya "yanta dan ya lura itace kaɗai take masa san tsakani da Allah.
Tou wannan dalili ne yasashi ya ɓanɓako dady daga ƙasar waje shi kuma zuwa wannan lokaci baya san dawowa nigeria dan shima ya riga ya kafa kanshi a can yayi kuɗi wanda saida suka tadawa Dikko hankali duk neman duniyarshi, yace Ummar da nasan zakayi kuɗi duniya da na zauna na mori rayuwata ban ba kaina wahala wurin tara abun duniya ba,
Dikko dai bai ɓoyewa Ummar komai ba ya sanar dashi cewa mata zaku kasheshi su gaji duk dukiyar daya sha wahala wurin tarawa , dan haka abinda Dikko yayi shine , duk abinda ya mallaka tsakanin gidaje filaye motoci filazozoji Dikko ya kasasu 10 ya bawa Ummar kashi 9 sannan yayi rabon gado da kashi ɗayan daya rage,
Duk wacce ta samu kuɗin nan ruɗewa tayi dan wannan kuɗi da Dikko ya bada gado wa duk "ya "yanshi iyakar almubazzarancin mace rayuwar duniya dai ba ƙiyama ba ya isheka, ganin kuɗaɗe a hannunsu kuma sun tabbata babu saura yasa kowa ta tsige aurenta ta kama gabanta...
Aure Dikko ya nemowa Dady ɗiyar wani aminishi suma attajirai ne na gaske , babu wani ɓata lokaci suka anshi tayin Dikko bikin bai wani ibi lokuta ba aka daura mishi aure da matarshi Maryam , mai irin sunan Sultana...
Dady bai daɗe da aure ba , Kaka Dikko da Kaka Binta sukayi gobara gaba ɗaya gidan babu wanda ya fita , duk wanda suke uwa ɗaya da dadynmu wuta ta cinyesu sun mutu har lahira, Dady yayi kuka na tashin hankali duk mai imani saida ya tausawa Dady,
Rayuwar dai haka taci gaba da tafiya , kakana na wurin uwa shine ya cusawa dady ra'ayin siyasa kuma Allah yasa ya shiga siyasar da sa'a domin ya riƙe manya manyan muƙamai dan siyasa tayi dashi kuma tana cikin yi dashi daga baya kuma ya tsaya takarar gwamna kuma Allah ya bashi yaci ,
Matan dadyna 2 a yanzu suka rage masa dan shima ya ɗan ɗana aure aure dan samun namiji amma Allah bai bashi ba , harya haƙura ya fidda rai Allah yasa ya sameni daga tsakiya dan mata sune samana kuma suke ƙasa na a cikinsu na rayu dasu nake gogayya banda aboki sai mata shi yasa ni ban ɗauki mace komai ba dan duk wani feleƙe da iyayi na mata babu abinda za'a layancemin , zancen cin cingom da duk wasu ɗabi'u na mata duk a wurin "yan uwana na koya, amma bana ɗabi'u irin na "yan daudu kuma bana magana irin na mata...
Ina da ilimin addini domin nima sittin ce cikin kaina nasan hadissai sosai duk ƙaunar da ake nunamin da sangarta baisa na zama sakarai ba nasan abinda nake , tunda nake dadyna da mom ina basu taɓa dukana ba babu mai dakamin tsawa kuma babu wanda yakemin kallon banza tunda nake ban taɓajin kalmar zagi akaina ba saida Allah yasa an mata ta shigo rayuwata, itace mutum ta farko data fara zagina a rayuwa.
Nima haka tunda nake ban taɓa neman mata ba kuma bana sabgar su akan ta ne na nuna mazantaka na, ni ba sakaran namiji bane ƙaddara ce kawai kuma bansan abinda hakan yake nufi ba ,
Gashi ta shigomin rayuwa banda isashshen lokacin da zanyi maganinta dan nima babana ya ƙusani cikin siyasa, ya fiddo ne akan wata kujera ta abokinshi daya rasu kuma inaji a jikina nine dan ban taɓa nema na rasa ba tun ina ƙarami duk abinda naso a rayuwata bai taɓa wuceni ba , dan bana san siyasa a rayuwata amma dole sai nayi ta.
Mu fitaccin mutane ne muna da cikken asali bama da wani tambari na ɓatanci haka kuma bamu da sata bamu da maita , mu ba ɓoyayyin mutane bane sananni ne kuma fittaci tun zamanin iyaye da kakanni, haka nima sananne ne kowa ya sanni kasancewar ɗa ɗaya tal namiji a wurin mahaifina , shi yasa ban ɓoyu ba domin dady ya ɗaukeni kamar abokinshi baya ɓoyemin komai duk wani samunshi a tafin hannuna yake , ragamar komai a hannuna yake , dan zaka tara matashi kamarni wanda akeji dasu ko sukeji da kuɗi wallahi ka tara matashi talatin maiji da kuɗi da motoci basu Dikko ɗaya duk yawansu wallahi.
Daga yau wallahi nayi rantsuwa idan har Sultana ta sake shigowa rayuwata saina keta mata mutunci wanda yafi wanda nayi mata a baya.....
Taff wannan shine ƙudirin Dikko , ita kuma bara muji nata .
Hafsa kuwa tunda Dikko ya zageta fess take kuka,
Ni kuma bacci ɗaya nayi na farka ina tunanin yadda zan hudowa lamarin Hafsa.......
30/08/2019
*MEELAT MUSA* 🤙🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 23
Har gari ya waye ban sake komawa bacci ba , da safe bayan na gama duk abinda nakeyi na fara kiran lamba 4 , lamba 3 wato d c o kuma na haɗashi da Amisty bana iya wata mu'amula dashi saboda gaskiya baida tsabtataccen baki danni Allah yayi min ƙyanƙyami idan na raina maka tsaftar baki tou na raina maka kuma bazan yadda inyi wata mu'amula dakai ba gaskiya.
Lamba 2 wato Bello shi yana nan kuma muna tare har yanzu babu wani abu daya shiga tsakani na dashi saidai ina fereshi yadda ya kamata ina kwalkwalar kuɗinshi babu dare babu rana, daya bani haƙuri ma cewa nayi saiya nemo min Babana sannan zan ƙyaleshi !
Lamba 1 Alhaji ne kuma ya rigamu gidan gaskiya , na goge komai nashi a wayana daga number har vidio babu abinda na bari,
Lamba 4 shine mijin Zalifa kuma yanzu shine abun hari na, ɗan wasa na, domin shine zan jijjiga zanyi wasan kura dashi kuma saina lashe kaf tattalin arziƙishi saina cinye komai zan maidashi matsiyacin ƙarfi da yaji, idan kuma yana da rabo akaina tou in sameshi mai tsafta idan dai ɗan gayu ne kamar Dikko zan riƙe mishi wuya ya zama abokin tafiyana...
Kiranshi nayi amma har ya tsinke bai ɗauka ba , haka tsarina yake kira ɗaya nakeyi idan ba'a ɗauka ba bana sake kira , idan kuma ya biyo kiran ina maraba dashi ,
Daga tsakar gida naji Amisty ta luƙaƙa wata irin ashariya irin na shararrin "yan tasha , saida gabana ya faɗi , ban gama saita kaina ba naji taci gaba da cewa na rantse da girman Allah wannan karon bazan bar Sultana tayi haƙuri ba , saita wulaƙanta shi ko waye ubanshi ...
Da sauri na miƙe na fito tsakar gida jikina sai kyarma yakeyi saboda ni hayani da zage zage ɗimautani sukeyi , ina fitowa na kalli Amisty nace wai mene ne ? Kusa dani Amisty ta matso tace ke wai mu Hafsa zata tonawa asiri , kallon inda Hafsa take tsaye nayi sannan nace wai miye ?
Wayar Hafsa, Amisty ta miƙo min tare da cewa shiga kiga cht insu da Dikko , bayan ta tura mishi saƙo ta whatsapp ya kirata tsakanin minti 10 bayan tura saƙo, kiji zagin da yayi miki Mother ƙarshen hukuncin da yayi yasa an rushe shagonmu kuma yace idan dai yana lumfashi kika fito karuwanci yace sai yayi miki wulaƙancin da ko ance ki faɗi kalmar iskancinci da bakinki sai kince kin tuba ,
Yace zai baki azaba mai azaba ɗaya daga cikin irin azabobin daya tanadar miki shekaru biyu masu zuwa , kuma idan kinyi taurin kai yace zai tafi dake ya ɓatar dake inda babu wanda zai sake jin labarinki daƙiƙiyar banza dake....
Zuciyata ta kawo maƙoshi amma ban nuna ɓacin rai ba nace ma Amisty wai duk inji shi Dikkon yace haka ? Amisty tace imana kinsan dai bana miki ƙarya idan baki yadda dani ba ki samo wani ya karanta miki duk duniya Sultana babu wanda nake ma soyayya irin wacce nake miki , nabar uwa da uba na zaɓe ke , rayuwata da komai nawa sadaukarwa ne a gareki idan ba duk abinda na faɗa miki Dikko ya rubuto ya turo ba Allah ya tsine min albarka !
Murmushi nayi sannan na kalli Hafsa nace to ke Hafsa mi ya kawo har kukayi magana na da Dikko ? Latse banzan bakinta tayi sannan tace niba magana nayi mishi ba shine yayi min maganarki , Amisty tace ke jira kiji zan ubanki ƙarya zan miki ko me kike nufi ne ? Kallona Amisty tayi sannan tace vidionmu ta tura mishi da hotuna kuma itace ta faɗawa Dikko muna da shago inba haka ba ya akayi yasan wurin harya zo ?
Hafsa tace tou naje na faɗa Amisty kiyi magani na , ai tun kafin ta gama rufe bakinta Amisty ta rufe ta da duka tana cewa amanar ƙungiya zaki ci dan ubanki , an yadda dake zaki ci mana amana , ko an faɗa miki muma bamu iya karatun da rubutawa ba ? Tana magana tana dukan Hafsa , kokowa har ƙofar gida saboda cikin gida mata sun kasa ansar Hafsa dama su "yan gayu basu iya faɗa ba sai sakata suka iya...
A ƙofar gida dakel masu aikin rusa tsohon gidanmu suka raba faɗa , kuma sukayi sasanci cewa da Allah mu daina faɗa ayi haƙuri , candai ake basu haƙuri niko wuri na samu na zauna wai nice daƙiƙiya , kamar ni abokin hamayya zai faɗa cewa ni daƙiƙiya ce , wallahi wannan kalmar tafi komai muni a rayuwata , itace kalmar da aka taɓa faɗamin ta ɓatamin rai kuma tamin ciwo ta kartar min zuciya har sai da naji masassara ta saukomin , wai ni Dikko yace ma daƙiƙiya , gumi naji yana bimin kumatu ina kai hannuna na shafo kunci na naji lema , ganin ruwa a hannuna ya tabbatarmin da kuka nakeyi....
Bayan an raba su Amisty shine suka zo kusa dani suka zauna hada Hafsa dan kunsan su "yan duniya basu fushi duk yadda aka cakusa dole sai an koma an jone , kowa tambayata yakeyi abinda yasa nake kuka amma banyi magana da kowa ba , Hafsa ce ta fara bani haƙuri akan abinda tamin murmushi nayi amma ban mata magana ba ,
Muna na zaune ƙofar gida a saman dandamali har su Nana mun jera layi babu mai mayafi a cikinmu mundai fito karuwan na zahiri da zahiri, saboda wancan hannu duk Dikko ya cinyesu babu gida ko ɗaya filin wurin ne kawai saboda duka wurin ya sayeshi harya tsallako gefen gidanmu yaci gaba da siyewa.
Muna nan zaune muna jiran tsammani Umar yazo , yaron Dikko wanda ya yakaini gidan Alhaji , yana fitowa daga mota ni ya fara gani , shegiyaaaaa , ashe da kina nan ina kuɗi na da kika cinye "yar damfara ?
Murmushi nayi da gefen bakina sannan nace zaki ya shiga gaban ɓauna , idan dai wanda ya mutu zai dawo tou ka kwantar da hankalin ka kuɗinka zai dawo aljihunka babu ɓata lokaci ,
Aiko kuɗina baza su ciwo wurinki ba sai kin bani abuna , dariya nayi tare da cewa wallahi basu ansuwa wurinka bakai ba kayan banza ko Dikko naci gabanshi naci uwarshi naci ubanshi a iskanci ai shine dai kake taƙama dashi ko ?
Kusa dani Umar yazo yana ƙoƙari wanka min mari na riƙe hannunshi tare dayin wani irin lafiyayen fito , babu ɓata lokaci "yan dabana suka bayyana , kallonsu nayi tare da cewa ku shiga dashi ciki ku bashi ruwa yasha , ɗaukarshi sukayi sama sukai cikin gida dashi , saida suka bashi kashin bala'e sukai mishi lullusar fitar hayyaci , saida suka tabbatar jikinshi yayi tsami sannan suka tillo banza ƙofar gida...
A lokacin ni kuma ina saman mota ta nayi kwanciyata , yayin da Amisty ke gefe na tana shan sigari A ` i da Saude kuma suna zaune kan dakali suna lido, Nana da Karima kuma nace su koma cikin gida saboda su matan aure ne ,
Dakel Umar ya miƙe ya shiga motarshi yaja ko masu aikin da yazo dubawa bai duba ba ya tafi , bai zame ko ina ba sai wurin "yan sanda , muna ƙofar gida zaune muka ga motar "yan sanda , wai anzo kamani ,
Bayan mun gama magana dasu nace su jirani ina zuwa , cikin gida na koma na shirya cikin shiga ta alfarma, wata riga na ɗauka na saka a leda bayan nasa anyi mata kitar wulaƙanci ga kuma jikina da yasha sahun akaifun Hafsa nasa ta yayyakushe ni dan na shirya ƙullawa Umar sharri na gaske.
Dani da Hafsa da Amisty da A ` i da Saude muka tafi domin ni sune sheduna , mu biyu a gaba ukku a baya , cikin mota ta muka tafi saboda itace motar kece raini Hafsa ta tuƙa har muka isa police station, Umar na zaune a waje jini sai bin jikinshi yakeyi tuni ya kira Dikko ya faɗa mishi, Dikko yace da an kamoni a rufeni duk abinda yake zai shigo katsina gobe idan Allah ya kaimu , dan hankalinshi ya tashi da yaga dukan da nasa akayi wa Umar.
Office ɗin d c o aka kai case inmu , ga gaske ni kuma gani nazo da kwarata masu biyawa mutum buƙatarshi , dan suma sunyo shiga mai ɗaukar hankali duk namiji mai lafiya ya gansu sai yaji hankalinshi ya tashi ,
Kujera Amisty ta jawo min na zauna sannan suka koma bayana suka tsaya , shigo da Umar akayi a daidai lokacin da ni kuma na fara gaishe da mai girma d c o , kafin ya ansa gaisuwar tawa Umar ya miƙa mishi waya Dikko ya sake kira domin ya faɗawa Dikko munzo station in ,
Faɗa Dikko yakeyi tare da cewa bai ce a jira aji abinda ya haɗamu ba kawai rufeni yace ayi , D C O yace ranka ya daɗe ai sai anyi binceke Dikko yace ba abinda za'a bincika umarni yaba d c o a rufeni kawai , d c o zai sake magana Dikko ya daka masa tsawa dole d c o ya dauke wuta , jikina fa yayi sanyi amma ta maza nayi tare da miƙewa na anshi wayar daga hannun d c o nace Dikko faɗa a cikin waya bashine ke nuna jarumta ba , kuma rufeni na kwana a ofishin "yan sanda bashi ne zai nunamin kai cikakken jarumi bane ba ,
Kaine kaɗai maganin fitsarata idan ka isa kazo kayi magani na basai kasa an kulleni ba , kuma kake cewa kar ayi bincike kasan abinda shi yaron naka yayi min ne ? Cikin ɗaga murya nace tou mutunci na fa zai buɗe kaga yadda ya yayyage min jiki ? Kuma da aka mishi magana cewa yayi kai ka tsaya mishi ya hau duk macen da yaji tayi mishi, kuma D C O ya faɗa maka idan bai yayyageni ba , da sauri Dikko ya rufe idanuwanshi tare da matse gwangwanin maltinar da aka kawo mishi baisha ba , azabar matsa yasa gwangwanin ya fashe maltinar ta watse...
Har a zuciyarshi ya yadda da abinda na faɗa mishi dan yasan Umar manemin mata ne na ƙarshe yayin da Umar ke cewa wallahi mai gida ƙarya takeyi kawai naje duba masu aiki tasa "yan daba sukai ta dukana ! Cikin wata irin hayagaga Dikko yace rufemin baki ɗan iska mutumin banza idan na sake jin maganar ka saina ci mutunci ka wallahi ,
Tausasa murya yayi tare da cewa ba d c o wayar , miƙa mishi nayi Dikko yace da gaske ya yayyakushe ta ? D C O yace Eh ranka ya daɗe , to dole zaice Eh tunda ga sahun akaifa a jikina ya fito sosai, nidai bansan yadda suka ƙare ba D C O yace muje kawai ,
Muna shiga mota na sauke ajiyar zuciya , kai Dikko ɗan bala'e ne na ƙarshe baida mutunci gaskiya Allah ya rufamin asiri yau da sauro da zarnin fitsari ya hanani bacci , kallon Amisty nayi sannan nace kinji ɗan bala'e da saboda ni zaizo lallai dana yabawa aya zaƙinta , dariya nayi tare da cewa aidai mun daki banza....
Bayan wata ɗaya...
A halin yanzu suna na ya fara zagawa a cikin gari, domin dai harkar iskanci ta buɗe mana sosai muna ganin maza daga shiyyoyi da dama , a cikin gidana nan maza ke zuwa su zaɓi macen da suke so a tafi hotel acan ake raƙashewa, yanzu bamu da shago domin Dikko ya saye wurin kuma yasa an rushe shi , tou ina gidana anan nake baje kolin iskanci na dani da yarana...
Cikin wannan wata bakin gwargwado kowa ya samu ci gaba na rayuwa Nana namiji yake zuwa wurinta ta kora mishi sharfi akan kayan mata da maza , itama a hankali idonta ya fara buɗewa ta iya gogayya da maza , dan daga ita har Karima yanzu bata mazansu suke ba,
A fanni na kuwa ni har yanzu ban samu tsaftataccen namiji kamar Dikko ba , amma idan aka zo tafiya da mace ni nakeyin ciniki namiji ya bani kuɗi kuma itama macen idan ta dawo zata bani kasafi na , tunda kafin a tafi nasan ko nawa za'a baki , na zama kawaliya kenan..
Idan namiji yazo ya duba a cikin matanmu bai samu wacce tayi masa ba ya faɗamin irin mace da yake so ni zan nemo mishi ita walau budurwa walau zawara har matar aure ma ,
Mijin Zalifa munyi waya dashi amma har yanzu bamu samu haɗuwa ba , yadai bada an kawo min kuɗi masu yawan gaske ta dalilin waya da mukeyi ta ɓatsa dashi , na siyar da motar da Alhaji ya bani nayi ciko na siyi mota ta gani ta faɗa , kuma ni nake tuƙa abuna domin yanzu na iya mota , jikina yaɗan ƙara ginuwa ya kuma goge hutu ya zauna dan dole dan idan baka san gidan da nake rayuwa ba zakace daga G. R. A na fito, na ƙara waye kuma idanuwana sunyi fashewar da duk mutum yayi mamakinshi,
Shirye muke cikin shiga mai nuni da mutanen gari ga naku , ma'ana maza ga matan bariki, biki akeyi a gidan ƙanin Babana yana aurar da ɗiyarshi, dan haka nace kowa ya shirya muje , mota ukku mukayi hada Zalifa, mota ta , ta Hafsa sai ta Zalifa sai napep ɗaya ta "yan daba...
Tunda mukayi parking idanuwan jama'a ya dawo kanmu, fitowa nayi tare dayin magana ƙasa ƙasa nace gafa "yar gado nayi gado amma kuma har na zarce...
Ina gaba tawagar karuwai suna bin bayana , duk wanda ya ganni sai ya kauda kai tare yin gulma ta , a cikin gidan biki kuwa hankalin jama'a ya tashi ganin iskanci dana taro bamai riƙuwa bane , ƙanin Babana yana tsakar gida shima da mutane ana ta mishi Allah sa alkairi dan ba'a daɗe da ɗaura auren ba , mazauni su Amisty suka nemomin na zauna na ɗauki ƙafa ɗaya saman ɗaya na ɗora...
Kallona yayi tare da cewa Sultana haka kika zama karuwa ? Saboda shi irin mutanen nan ne masu sakin magana babu tsafta , murmushi nayi tare da gyara zaman ɗaurin kallabi na sannan nace Eh wallahi ai shine nazo na nuna muku tunda nasan duk wani ɗan uwa da abokin arziƙi yazo shine nazo wanda basu gani ba suma su gani....
Dariya Amisty tayi tare da buɗe jakarta ta jawo shigarinta ta banka mata wuta , saida taja ta bada hayaƙi sannan tace wannan gaskiya ne Mother , ƙanin Babana yace nan zaki zo ki kawo mana iskanci ? Tou ki tashi ki koma inda kika fito tunda ke kin lalace karki zo nan ki gurɓata mana tarbiyyar "ya "ya kije can ki ƙari iskancin ke ɗaya....
Kallon Baba nayi tare da cewa gaskiya ne dan naga idan guguwa ta taso wuri ɗaya takeyin borinta amma tsawar hadari tana gaurayi kaf faɗin sararin samani , ruwan sama ko na sarari yake jeƙewa bai taɓa baa na cikin ɗaki kashi duk wanda kaga yasha kashin ruwa cikin ɗaki tabbas kwanon ɗakinsa ya huje , idan yayi dibara saiya doɗe wannan haryar da zai bawa ruwa damar shigo mishi ɗaki. Gyara zamana nayi tare da ci gaba da cewa duk na kirki baya san na banza amma ni mutanen kirki sune abokan rayuwa.....
Miƙewa nayi tare da cewa ka bada tarbiyya a gida zamanin Sultana yana warware tuggun kowa , duk wanda ya kalleni a taron nan yace tir da halina ya saurari zuwan zamani na akan "ya "yanshi, har na fara tafiya na tsaya tare da juyowa nace yawwa idan kaga ɗan uwan naka Babana , ka faɗa masa cewa ina matuƙar kewarsa a kusa dani...
Sallama nayi da duk wanda ya kamata tare da buɗe bakin jakata nayi alkairi , banga "yan gidanmu ba ko ɗaya amma nace idan sunzo ace musu ina nan tsohuwar anguwarmu , gidan karuwai kawai zasu tambaya za'a kawosu har ɗakin magaji Sultana , na ƙarasa maganar tare dayin murmushi sannan nayi gaba masu sauran imani suka bini da addu'ar shiriya yayin da wasu ke cewa ubana yajamin...
Muna fitowa daga gidan kowa ya shiga mota muka ibi sararin hanya.....
31/08/2019
*JAMILA MUSA...* 🤙🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 24
Muna fita gidan biki Baba ƙarami ya ɗauki wayarshi ya fara kiran Babana abin alfahari na , mai nunamin soyayya ta zahiri da gaskiya , wayayyan mahaifi mai tafiya da rayuwarshi daidai da zamani...
Bayan Babana ya ɗauka suka gaisa , bayan gaisuwa Babana yayi masa ya taro tare da addu'ar Allah ya bada zaman lafiya wa ma'auranta , Baba ƙarami yace ameen ,
Bayan Babana ya gama addu'a Baba ƙarami yayi gyaran murya tare da cewa wato Aliyu ɗiyarka dai ta zama cikakkiyar karuwa , ka shige ka ɓoye kabarma dangi baƙin ciki su gani...
Rabbi annee massaniyadh dhurru wa anta arhamur rahmeena , Abdullahi Uwar masu gida baza ta taɓa zama karuwa ba ban haifi karuwa ba akanta amma karuwai suna zuwa kuma zasu tabbata akan duk wanda yake dangana min ɗiya da siffar karuwanci , ban gudu ba kuma ban ɓuya ba tunda har kuna nema na ku sameni ku bugo kuma in ɗauka muyi magana , na ƙauracewa zaman ne saboda duk duniya babu hawaye mafi ɓakin ciki inga suna gudana tsakanin idanuwa zuwa saman kumatu irin na Uwar masu gida,
Duk kuwa ranar da naga kukanta tou tabbas shekarar mutuwa tane ya tsaya , ɗiya ɗaya tak a cikin taron yuyuyun "yan uwa , saita tallafeni sai ta tallafe ka sai ta taimakeni sai ta taimake ka sai ta taimakesu sai tayi ma kowa taimako kuma ko bana raye wallahi ka riƙe wannan maganar karka sake ka manta ta uwar masu gida cikakkiyar mai arziƙi ce ,
Idan ina da rabo inci idan banda rabo dangi su amfana ko ƙasa ta rufemin ido nasan nabar baya mai amfani , burin duk uba yabar baya jaruma ba lusara ba , idan kalmar karuwan ta sake fitowa bakinka akan Uwar masu gida na rantse da girman Allah gaba ɗaya zuri'ar ka sai sun zama karuwai.....
Zufa ta ketowa Baba ƙarami tare da cewa Allah ya baka haƙuri Aliyu ban faɗi wannan maganar dan in ɓata maka zuciya ba , jarumin uba kenan murmushin "yan duniya yayi Babana tare da cewa nima ban faɗa maka dan zuciyarka ta ɓaci ba ina tunatar da kai dai ko waye Aliyu Binna dan naga tafiyana yasa ka manta me binna ɗin take nufi, haƙuri dai Baba ƙarami yaci gaba da bawa Babana saida ya tabbatar daya sauka sannan sukayi sallama...
Wata irin ƙuna mai kartar zuciya Babana yaji wacce tasashi zaman dole , saida yasha kuka harya godewa Allah sannan yace ki yafemin Uwar masu gida ƙaddara tayi makauniyar waiwaya , an cuceni anci amanata banso ƙaddarar rayuwarki tazo miki a haka ba , amma na rantse da Allah daga Dikko har yaronshi Alhaji sun shiga uwatar bala'e duk wadda yaci yaciwo ma kanshi masifa ,
Abinda Bello ya guda kenan shi yasa shi baiba , amma yakaiki inda akayi nayiwa Dikko uzuri kuma na yafe mishi saboda nayi imani da yasan waye ubanki ko a santa ya ganki tsirara baya kallonki bare har yayi sha'awarki , duk abinda kike ciki na sani kuma ina da labarinshi , daga Dikko da Alhaji babu namijin da zai sake keta miki mutunci har abadan duniya , idan tsafin ne ba'a fini iyawa ba , cikakken ɗan caca manemin matan aure za'a nunawa iya sihiri ? Gaki nan zakiyi yawonki tare da rayuwarki cikin "yan ci kamar yadda ko wace ɗiya mai gata zata yi amma wallahi babu namijin da zai sake kwanciya dake sai mijinki na sunna in Allah yadda...
Murmushi kasan dai Dikko yafi ƙarfinka duk wani ɗan ƙaramin tsafinka baya tasiri akanshi, kaine kaɗai halakakke ɓatacce wadda baka dogara da Allah ba ka dogara da tsafe tsafe, duk wanda ya riƙe Allah kuma ya dogara dashi Allah zai isar mishi duniya da lahira....
Dariya nayi adaidai wannan lokaci na daki sitiyarin mota ta domin fira mukeyi tunda muka taho , kallon Amisty nayi tare da cewa yaufa nasan na daki zuciyar maƙiya , mutumin dana burge a wurin bansan iyaka ba , tou dole ince mana ,
Kinga Sultana ga mota Sultana ga wayewa ga iskanci uwa uba karuwancin nan yamin kyau domin yasa na zama wata babbar hajiya da mutane ke ganin girmana , kuma nayi musu hauka da kuɗi zaki ga ikon Allah makwaɗaita sai sun biyoni saboda wannan zamani mai badawa shi ake mannemawa,
Haka dai rayuwarmu taci gaba da tafiya ! Kullum iskanci na da lalacewa na gaba yakeyi amma har zuwa wannan lokaci ban samu wani cikakken namiji kwatankwacin Dikko ba , mijin Zalifa kuma har yanzu baizo ba da nayi masa magana bai zo ba saidai ya toshe ni da kuɗi tun abun baya damuna har ya fara tsaremin rai...
Tsaye da kyau zaune da kyau babu inda Allah ya rageni amma mazan bariki idan sunzo basu tayani saidai idan nayi kawalci in samu kuɗi abunfa ya fara damuna na rasa inda zan saka raina dan ba irin wannan sana'ar na zaɓa ba gaskiya nafi so a nemeni ayi kuma a bani kuɗi ,
Amisty ta lura da halin da nake ciki ta tambaye ni abinda ke damuna , ban wani ɓoye mata ba na sanar da ita , dariya Amisty tayi tare da cewa wallahi hannu aka saka miki ,
Cikin rashin fahimta nace ina aka saka min hannun ? Na tambayeta ina kallon jiki na ! Dariya Amisty tayi sosai sannan tace haba uwar ɗakina bafa a jiki ake saka hannu ba , abinda ake nufi da sa hannu magauta zasu je wurin malaman tsubbu su biya kuɗi suce a toshe musu samunki a rufe duk wani ci gaba naki....
Tsoki nayi tare da cewa aisai suje suyi ta fama can su Allah ya azamawa , Amisty tace tou ai sai anyi maganin matsalar sannan zamu barsu suyi ta fama , kallon Amisty nayi tare da cewa wallahi kun cika canfe² babu wani jarabta na rayuwa sai asiri , an saka miki hannu , tou idan sun gaji da sa hannun zasu goge da kansu ,
Daga ƙofar ɗaki Nana tayi magana cewa Mother zamu ɗan shiga maƙota , daga inda nake zaune nace me akeyi maƙotan ne ? Nana tace Mother baƙi ne suka bayyana a cikin daren jiya anguwar nan , kinga matar wayayya ? Daga tsakar gida Saude tace matar kodai mijin ? Zamu shiga muga halinsu idan munga da lasa zamu yankawa mijin kati zai dawo gidan nan uwar ɗakinmu...
Murmushi nayi irin namu na "yan duniya sannan nace tou ku dawo lafiya , saboda ni dama Allah baimin shige² ba ina nan inda Allah ya ajiyeni duk wadda nake tare dashi shine yake zuwa ya sameni dan gaskiya bana san raini shi yasa na tsare mutunci na a gidana...
Gyaran murya Nana tayi tare da cewa ko zakije ne ? Cike da izza nace ku dawo lafiya , Amisty tace nima kam zanje , murmushi nayi amma ban sake magana ba , gaba ɗaya suka ɗinguma suka tafi gidan amma ni banbisu ba....
Gaba ɗayansu a palon matar suka sauka , kowa ta kama kujera ta haye kamar baƙon namiji a harkar mata , bayan gaisuwa kowa ta faɗawa matar sunanta tare da cewa sune maƙotan gidanta , itama sunanta ta faɗa musu Asma'u sannan ta kora da cewa bata taɓa aihuwa ba ,
Gyara zama Amisty tayi tare da cewa shekararku nawa da aure ne ? Asma'u tace gaskiya munkai shekara 8 , tou kina da abiyar zama ne ? Amisty ta tambayeta , Asma'u tace Eh mu biyu ne ? A ` i ta anshe da cewa tou kun taɓa neman maganin aihuwa ko itama abiyar zaman taki bata taɓa aihuwa bane ba ?
Asma'u tace kai tana haihu sosai ma , Amisty tace tou matsalar daga wurinki take idan mun fahimta , Asma'u tace gaskiya , daga haka dai suka tsaya domin sun shiryo barikinsu wa Asma'u zance yau iyakarshi haka....
Miƙewa sukayi gaba ɗayansu cewa zasu tafi , Asma'u tace haba tun yanzu ? Murmushin "yan duniya A ` i tayi tare da lumshe idanuwa ita mayyar mata tace ai zamu sake shigowa , rakiya tayo musu har bakin get tayi godiya sosai ,
Tunda suka fito faɗa ya kaure tsakaninsu , yayin da A ` i ke cewa ta kama matar Saude kuma ta kama mijin , Amisty tace A ` i dani zaki haɗa hanya ? Bayan ni na fara isar da saƙo na zakice kin kamata ? Nana tace kai matar fa tana da mazauna sosai gaskiya , rikici dai sukeyi sosai , dan haka Amisty ta taka musu birki da cewa duk abinda zasuyi suyi shi a waje kar su bari naji wannan labarin domin sun san babu abinda na tsana irin harkar mace da mace....
Tun a waje sukayi ma Hafsa waya suka sanar da ita sun samu lafiyayyar mace kuma daga gani zatayi shan mai domin yarinyar da zafinta , Hafsa tace gani nan zuwa , Amisty tace karki zo yanzu kina zuwa uwar ɗakinmu zata gano wani abu kinsanta da saurin fahimta , duk satin nan karki zo ki bari sai cikin sati na gaba , Hafsa tace wallahi bazan iya ba sai nazo na ganta ,
Amisty tace saurara kiji yarinya , ba'a garaje ya kike abu kamar baƙuwar harka don Allah ? Ki natsu ki kwantar da hankali wallahi babu mai yarinyar nan sai mu , ki dai bari mu ɗorata hanya ita da kanta zata riƙa kawo kanta , dakal Amisty ta lallashi Hafsa ta haƙura,
Tsakar gida suka sameni kowa tayi dabur ² murmushi nayi tare dabin Amisty da kallo sannan na kalli idon A ` i na kalli na Nana saboda sune "yan lesbian a cikinsu , da kinga sunayin kame² mace suka gani , sai kuma Hafsa itama manemiyar mata ce , jinjina kaina nayi sannan na tsare Amisty da kallo idanuwanta sunyi wani irin ja kamar taci tsidagu,
Ƙafafuwan Amisty na kalla sannan na ɗago idona zuwa daidai saitin cibiyarta sannan na dauke kaina , ɗaki ta wuce Nana ma ɗakinta ta shiga yayin da A ` i ta samu wuri ta zauna , kallon inda A ` i take zaune nayi sannan nace sannun ku *kwarata* daga zuwa maƙota har hankalinmu ya tashi ko ? Duk yadda akayi matar gidan ta burgeku , Allah ya tsallaketa daga kaidinku....
Ɗaki na shiga Amisty na samu kwance saman katifa tayi ruf da ciki , tsoki nayi tare da halbinta da ƙafa nace tashi ki fitarmin daga ɗaki ni gaskiya bana san irin wannan ɗabi'ar ,
Allah ya baki haƙuri uwar ɗakina , tana faɗin haka ta miƙe tabar ɗakin ta nufi ɗakin Nana , da yake itama Nana naga yanzu taɗan waye tana wanka tana shafa turare , har akayi sallah magrib Nana da Amisty da A ` i suna ɗakin bansan abinda sukeyi ba gaskiya....
Kuma ban damu da sanin halin da suke ciki ba danni Allah baimin sa ido da bin diddiƙin abinda wane yakeyi ba , sai bayan isha'i Amisty ta shigo da ɗaurin gaba da alama wanka tayo ,
Ko inda take ban kalla ba , itama bata kalleni ba kuma batamin magana ba taci gaba da shiri saida ta gama abinda takeyi tsaf sannan tace min dame² za'a siyo ne ?
Can zaki kwana ne ? Na tambayeta , tace ba'a can zan kwana ba wurin 1:00 zan dawo , indomie da madara kawai zaki ƙaro mana , kallona tayi sannan tace ke babu abinda kike so ne ? Ba abinda nake so na bata amsa tare da cewa Allah ya bada sa'a a dawo lafiya , da amin ta amsa sannan ta fice daga ɗakin...
Kwanciya nayi bayan Amisty ta fita dan banda inda zanje , Nana ta shigo ɗakin da sallama ta ɗauki magunguna ta fita saboda mu yanzu garin "yan gidanmu ya waye ,
Ganin Nana ta ɗauki magunguna na tashi na feshe jikina da turaruka masu ƙamshi na ɗaukar hankali , doguwar riga ta shadda na saka nayi ɗaurin ɗan kwali irin namu na karuwai dan banda daurin ɗan kwalin daya wuce ture kaga tsiya...
Tunda na fito daga ɗaki su Karima suka rufamin baya dan ko gyale tuni na daina sakawa , cikin isa da nuna ni wata shegiya , cike da izza nayi gaba sai baƙin rai nake na tun kari ƙofar gida su Nana duk suna biye dani , tsayuwa nayi a ƙofar gida nabi motocin dake ajiye a ƙofar gidan da kallo kamar anayin wani taro.
Murmushi nayi yayin da aka ajiyemin kujerar roba na zauna , ƙafa ɗaya saman ɗaya na ɗora sannan mazan bariki suka fara kawo gaisuwa kamar yadda suka saba a duk lokacin da wani zai ɗauki wata domin nice uwar ɗakinsu , suna bani girmana basu rainani ba shi yasa duk wani *kwarto* yake ganin girma na...
Duk namijin da yake zuwa wurin matan waje babu samari manyan mutane ne masuji da kansu wani ma wallahi yayi ɗiya da wacce zai kwanta da ita , ko me yasa suke baro matansu na gida suzo na bariki ? Gaskiya ina san insan wannan dalili ...
Bayan na gama samun kuɗina na miƙe na koma ciki ,ɗakina na shige nabar musu filin tsakar gidan dansu ji daɗin harkokinsu , mace ɗaya tana iya kwanciya da namiji biyar saboda tsabar haɗama ,
*** ***
Safiyar yau gidan Asma'u su Amisty suka sauka , acan suke baje kolinsu ranar da suka fara zuwa banje ba kuma yauma da zasu koma banbi su ba , gaba ɗayansu suka tafi ni kuma na fita ƙofar gida nayi zamana a saman dakali...
Wayata na ciro na fara kiran mijin Zalifa , bayan ya ɗauka yace ina gida idan na fito zan kiraki , jinjina kai nayi tare da cewa ka fito lafiya ranka ya daɗe ina faɗin haka na kashe wayata....
A gidan Asma'u kuwa ga yadda lamarinsu ya kasance a yau ,
02/08/2019
*JAMILA MUSA...* 🧚🏻♀
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 25
Tunda suka shiga sukayi ta kwarara sallama shiru babu wadda ya amsa , Hafsa itace ta basu ƙwarin guiwa cewa kawai su shiga palo , gaba ɗayansu sunkayi na'am da wannan shawara dan haka suka ɗinguma suka shiga cikin palon tare dayin sallama...
Daga cikin bedroom Asma'u ta amsa sallamar tare da cewa ku zauna ina zuwa , murmushi Amisty tayi tare da cewa ko munzo da wuri ne mai gidan bai fita ba ? Daga cikin ɗaki Asma'u tace ya fita amma yana dawowa babu jimawa wanka dai na fito ina ƙoƙarin saka kayana !
Wani irin ajiyar zuciya Hafsa ta sauke tare da cewa zanyi fitsari ta faɗi maganar cikin sigar kwartanci ma'ana tayi maganar a sakantace tare da kasalanci yanayin maganar dai sune kaɗai suka san fassarata ,
Akwai toilet a nan waje inji Asma'u tare da ƙoƙarin fitowa daga bedroom in dan nunawa Hafsa inda toilet in yake , towel ne ɗaure a jikinta ko guiwa bai kawo ba saboda tana da wani irin kugu ne shi yasa towel in ya haye saman ɗuwawunta shi ya hana towel in saukowa sosai '
Idanuwa Amisty ta zaro sosai kamar zasu faɗo ƙasa tare da jan wani irin gauron numfashi sannan tace babu toilet a bedroom inki ne ? Ta faɗi maganar kamar numfashinta zai ɗauke , murmushi Asma'u tayi tare da cewa akwai bara dai ta shiga na wajen !
A ƙofar palo sukaci karo da mijin Asma'u , tunda ya ganta ya haɗe girar sama da ƙasa tare da cewa wannan wane irin sakarci ne ? Ke wawiyar inace zaki fito haka ..... ?
Cikin biyayya Asma'u tace ai ba kowa gidan ne duk mata ne , matan banza matan wofi da Allah wuce kije ki saka hijabi malama , yayi maganar cikin kausassar murya tare da ƙara ɓata rai kamar zai daki Asma'u ,
Simi simi Asma'u ta wuce ta koma ciki , saida ta shige sannan yabi bayanta , a palo ya samu su Amisty zaune riɗi² , duk gaishe shi sukayi amma babu wacce ya kalla bare su saka ran zai ansa gaisuwar wata daga cikinsu ya wuce ciki abunshi....
A bedroom kuwa faɗa ya rufe Asma'u dashi tare da cewa ina kika samo wa'anan karuwan ? Kai ƙasa ² tace maƙontanmu ne , zama yayi a gefen gado tare da ci gaba da cewa gaskiya ni bana so suna zuwa gidan nan kima taka musu burki kar na sake ganin kowa na faɗa miki ,
Cikin yanayin damuwa Asma'u tace haba Baban Abdul babu daɗi na ce su daina zuwa , cikin ɗaga murya yace tou wallahi idan baki musu magana ba ni da kaina zan musu magana zance kar na sake ganin ƙafar ko wace a gidan nan , daga shiga bayi kilbibi zai fara yaɗuwa , miƙewa yayi tare da cewa tunda tsoronsu kikeji ni bara inje in faɗa musu...
Da sauri su Amisty suka miƙe kafin mijin Asma'u ya fito tuni sun fice daga gidan , koda ya fito palo bai samesu ba , dan haka ya koma yana cewa sun rufawa kansu asiri da suka gudu , ita kuwa Asma'u bataji daɗi ba saisu Amisty su gani kamar itace tasa mijinta ya tozarta su kuma tabbas nasan sunji kana faɗa irin haka babu daɗi...
Cikin ƙara faɗaɗa faɗanshi yace ai dama bana so suji daɗin kuma idan na sake ganinsu gidan nan saina ci mutuncinsu , Asma'u tace tou shikenan ka haɗa hadani kaci mutunci gaba ɗaya , tou zanci hada naki ki barsu suci gaba da zuwa gidan nan kiga yadda zamu ƙare dani dake...
A ƙofar gida su Amisty suka tsaya tare da saka takalminsu ko wanne yana maida nunfashi saboda gudun da sukayi daga cikin gida zuwa ƙofar gida , ajiyar zuciya A ` i ta sauke sannan tace kai wannan ɗan masifa ne zamu sha fama dashi domin zai ɓata mana lokaci gaskiya ,
Nana tace babu wani ɓata mana lokacinmu da zaiyi kawai mu haɗashi da Mother kunsan Allah ya bata ilimin saka namiji lungu , Hafsa tace idan muka haɗasu me kuke tunanin zai faru ? Kunfa san halin Sultana tana iya faɗa masa cewa ya hanamu shiga gidanshi mu maneman mata ne tunda ita bata wannan harka kuma sanin kanku ne baza ta rufawa mai irin halin asiri ba "" ,
Amisty tace tabbas zata aika wallahi , A ` i tace kuzo kuji mafita , haɗuwa sukayi wuri ɗaya sukayi magana ƙasa² dariya sukayi bayan sun gama tare da tafawa sannan suka nufo gida. !
A ƙofar gida suka sameni zaune ko inda suke ban kalla ba , zama sukayi yayin da Amisty ta ciro sigarinta daga cikin jaka ta kunna mata wuta saida taja ta sannan tace uwar ɗakina barka da hutawa ,
Bance yawwa ba kawai nace mata faɗi damuwarki , gyara zama tayi tare da cewa wallahi wani alhajin wuta ne muka samu , ga ƙira ga sarho { kwarjini } uwa uba hatimin nasara mota saidai ya shiga wannan ya fita a waccan , ga gida daya gina mai tafiya daidai da zamanin ƙarshe , jiya mata biyu yaba mota kuma nice sheda saboda na gani kuma na hau dan taya murna , matashi ne wayyan namiji ga aji kamar abokin gabarki { Dikko }
Dariya nayi tare da kallon Amisty sannan nace kiyi magana kawai ki daina shiga buhu , kashe tabar hannunta tayi sannan tace nidai shawara zaki bani ina so ko ta halin ya nima in ɓata dare ko yini dashi , a gidanshi yake kai matan bariki idan matarshi bata nan , ki taimakamin ki faɗamin taya zan nemeshi... ?
Kallon Amisty nayi sannan nace ke kin tabbata manemin mata ne ? Amisty tace ko ban tabbata ba dai inaso yayi akaina , karfa ki manta kece kikace mu nema ga mai nema kuma idan ya nema mu bashi , kuma kece kika ce idan mun gani munji muna da buƙata kar mu cuci kanmu muyi ƙoƙari mu bashi tun muna bashi yana tofarwa har mu samu ya fara haɗiyewa , nidai gaskiya ina so ya kwanta dani koda so ɗaya ne .
Kallon Amisty nayi sannan nace a gidanshi kike so kuyi alaƙa dashi ? Amisty tacemin Eh , murmushi nayi tare da cewa kawo kunnenki a baki , matsowa tayi tare da miƙomin kunne na fara mata raɗa , har ga Allah ban kawo komai a raina ba kuma ban taɓajin sha'awar kowa ba a cikinsu , inawa Amisty raɗa ta kwanto a jikina sosai tare da lumshe idanuwanta , ashe ita daɗin maganar takeji ,
Ta bayana ta tura hannuwanta duka biyun cikin rigata ta fara shafawa a hankali tana wani ƙara mannewa a jikina tana nunfashi a hankali ² , ban gama maganar ba nayi tsoki tare da tureta daga jikina nace wannan wane irin ɗanyen iskanci ne kuma ?
Dariya Hafsa tayi yayin data lushe idanuwanta sannan tace haba mother daga an riƙeki sai ki tayar da hankali ? Ba komai bane ba natsu kawai kici gaba da faɗa mata tunda kin fara kuma mu bakya so muji !
Ban kalli Hafsa ba nace bazan faɗa ba "yan iska masu guntuwar sha'awa ku ko kunyar Allah bakwaiji da kunga mace duk sai ku wani fitittike karuwai marasa aji , idan kunajin bala'e da tsabar maganin iskanci ku nemi maza sai kusan kunyi iskanci da hujja , mace me zata miki ? Inda kike buƙatar kije kafin ki sauka wurin kinsha wahala ,
Murmushi Amisty tayi tare da kishingiɗawa ta bini da kallon mai tatttare da tsabagen sha'awa sannan ta sauke ajiyar zuciya , miƙewa nayi Amisty ta jawoni ta zaunar dani , ta sake tsareni da wani irin mayataccen kallo , tsikar jikina naji ta tashi , lahira tazo min kusa kusa da sauri nace A'uzubillahi minashshaɗainir rajim ,
Gaba ɗayansu suka sheƙe da dariya , ɗaure fuska nayi tare da sake miƙewa , ƙara riƙo hannuna Amisty tayi juyowa nayi tare da cewa karki sakemin irin wannan abun daga yau bana so , makirin murmushi tayi sannan ta sakemin hannuna na tafi cikin gida ,
Suna ganin na shige A ` i tace Allah ya ɗoramu akan ni'imarki yarinya zamuyi wasan kura dake kowa saiya yagal galaki san ranshi wai ita a dole mai tsoron Allah , tuni na daɗe da haɗiyewa akan yarinyar can amma ta balɓaɗa min rashin mutunci tun kafin in furta , duk daren daɗewa saina afkawa yarinyar nan saidai duk abinda zai faru ya faru ,
Zama Hafsa tayi tare da cewa nifa na ɗauka "yar hannu ce ! Ganin farko da nayi mata itace ta fara nunamin wallahi a tunani na ta tafiya ce , ashe ba haka bene nima duk ranar data shigo hannuna saina horata , hawan farko zanyi da ita saita koma gidanmu da zama....
Ido ɗaya Amisty ta kashewa Hafsa tare da cewa ashe kuwa za'a haɗa rigima dan dai kinsan my Sultana tawa ce ni ɗaya , kinsan haɗarin dana fuskanta akanta kuwa ? Nabar uwa nabar uba na dawo zama da ita ? Lumshe idanuwa Amisty tayi tare da rungume duka hannayenta a ƙirji tace wallahi idan har na samu Sultana na more duniya , zan rabata da kowa da komai na ɗauketa na tafi da ita ,
A ` i tace ki ɗauketa ki kaita gidan uwar wa ? Ai yadda kikayi kowa sai ya more Allah dai yaba mai rabo nasara, sun daɗe suna ƙullawa da warwarewa yadda zasu samu nasara akaina daga karshe dai suka yanke shawara zasu kaini gidansu Hafsa acan zasu baje kulinsu dani...
Tun daga wannan ranar na canjawa su Amisty fuska na daina cin abinci tare da ita , na daina kwanciya wuri ɗaya da ita , idan ta kwanta a katifa saina sauka ƙasa , gaba ɗayansu na rage musu fuska ko dariya na daina musu tunda dai na lura dukansu iskancinsu ya girmi nawa ,
Amisty kuwa muguwar tare tayiwa su Nana A ` i da Hafsa , ita kaɗai take zuwa gidan Asma'u basu sani ba ta shige mata sosai , har ta gane kwanakin da mijinta yakeyi a gidanta da ranar da baya gidanta ...
Yau mijin Asma'u ba'a gida zai kwana ba tunda Amisty ta shigo gidan taƙi ta fita , har dare yayi sosai , gajiya Asma'u tayi dan taso Amisty ta tafi ta rufe gida , kasa haƙuri tayi tace wai nace ko yanzu zaki tafi dan kwanta ne bacci nakeji,
Murmushi Amisty tayi tare da cewa ai yau nine zan tayaki kwana , Asma'u tace haba ai babu wani damuwa ni ɗaya ma nake kwana nan babu komai , ajiyar zuciya Amisty tayi tare da cewa ai nasan bakyajin tsoro tunda duk girman kwanakin da kikayi kina kwana bani nake tayaki kwana ba., Asma'u tace Eh kawai karki damu kya iya tafiya...
Lemun dake gaban Amisty ta ɗauka tasha a bakinta sannan ta miƙe tsaye ta tunkari inda Asma'u take tsaye , Asma'u ganin Amisty a wani irin yanayi yasa taɗan ja baya , yaudararren murmushi Amisty tayi kamar yadda ta saba idan hankalinta ya tashi akan mace,
Asma'u tana ƙoƙarin ƙara ja baya Amisty ta fizgo ta , Asma'u tace haba Amina miye haka ? Tayi tambayar tare da fizge hannunta ta ƙara yin baya , binta Amisty tayi har takai maƙurar bango maida hannayenta tayi duka ta baya ta dafa bango dasu ta tsaya tana kallon Amisty ,
Da duka hannayenta ta riƙe ƙugun Asma'u sannan tace wai miye duk kika wani firgice ? Kwanan da nine bakya so ko miye ? Asma'u tace ba haka nake nufi ba , ƙara fizgo ta tayi jikinta sosai sannan tayi magana mai tattare da ɗaukar hankali tace tou miye ? A wurin Asma'u ta sandare ta kasa cewa komai , sakin ƙugunta tayi ta jawo hannenta ta ɗora su a saman ƙirjinta sannan tace mu kwana tare ko ? Tayi maganar cikin rarrashi , kai kawai Asma'u ta iya ɗagawa Amisty , murmushi Amisty tayi sannan taja Asma'u ta zaunar da ita saman kujera , kamar ɗakin uwarta itace taje ta rufe ɗakin dan dama gidan rufewa sukeyi sai an ƙwanƙwasa take buɗewa, a inda tabar Asma'u a wurin ta dawo ta sameta , kusa da ita Amisty ta zauna sannan ta jawota jikinta tace miye ? Ko kinajin babu daɗi ne ?
Cike da kasala Asma'u tace tsoro nakeji , ƙara jawota Amisty tayi sosai a jikinta sannan tace wane irin tsoro bayan gani ina tare dake ! Riƙo fuskar Asma'u tayi ta kalleta ido cikin ido sannan tace kin taɓa ? Asma'u tace a , a Amisty tace a kaina zaki fara kenan ? Jinjina kai Asma'u tayi alamar Eh , Amisty tace tou muje ciki ,
04/09/2019
*JAMILA MUSA...* 🧚🏻♀
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
Sannun ku. Na ga maganganu daga mutanen da suka riga sun sami lamunin su daga lamuni na tsarkakakkiyar zuciya sannan na yanke shawarar neman aiki a karkashin shawarwarinsu kuma 'yan awanni kadan da suka gabata na tabbatar a cikin asusun banki na kaina jimlar $ 50,000,00 wanda na nema. Tabbas wannan babban labari ne kuma ina mai ba da shawara ga duk wanda ke buƙatar rancen gaske don neman aiki ta hanyar imel ɗin su (jamesmichaelloanservices@yahoo.com) ko Whatsapp +16314912234, Ina mai farin ciki yanzu da na samu rancen da na nema
ReplyDelete