Ina fitowa daga wanka na wuce palo inda kayana suke ajiye , ɗagasu nayi ɗaya bayan ɗaya naga babu wata ƙura da kayan sukayi nidai a gani na dan an lulluɓe su da towel , zani da hijabi kawai na ɗauka na koma ciki ,
Zanin na ɗaura wato ɗaurin ƙirji , na saka hijabin na nufi palo dan naga Al ' Ameen yana waje har yanzu bai shigo ciki ba , inda kulolin abinci suke naje na buɗe na zuba abinci naci na ƙoshi sannan na dawo ɗaki nayi kwanciyata !
Babana ne yazo ya tsayamin a rai gaskiya ina cike da kewarshi soyayyarshi ta hanamin zaman lafiya , duk duniya ban haɗa soyayyar Baba da kowa ba , ko ina yake ? Ko a wane hali yake yanzu ? Yana tunani na ko shima bayayi... ? Haka nan naji hawaye sun cikamin ido cike da rauni nayi magana a bayyane ina kake ... ?
Murmushi nayi mai cike da ɓacin rai zuciyata cike da kudurirrika akan Dikko duk runtsi duk wahala komai daren daɗewa sai Dikko yayi nadamar sani na , yanda ya takura ma rayuwata nima saina takura ma tashi rayuwar saina mishi zargen da bazai iya warware kanshi ba , da wannan tunanin bacci ya ɗaukeni.
Su Dikko kuwa sai 12:30am suka dawo hayaniyar shigowar motocinsu ta tasheni daga bacci , tunda suka fara fitowa daga cikin mota suke gaddama har suka shigo palo , bayan kuma sun shigo haya² ƙarar filets da cokula kowa yana zuba abinci amma har yanzu banji maganar Dikko ba danshi baya da ƙoƙari wurin magana saidai dariya itama sai yaji mugunta yakeyi...
Zuwa wani lokaci kuma palon yayi shiru bakajin maganar kowa sai ƙarar tv dan sun fara cin abinci , bayan wasu mintuna kuma naji wani yana cewa kai ubangiji ya fishshemu tsaka mai wuya , gaskiya na tausayawa kaina na tausayawa Saminu wallahi , Dariyar Dikko naji yana cewa niko wallahi bai bani tausayi ba aishi ya siya tsautsayi da kanshi maganin ganganci da rayuwa kenan kaga garin neman gira an rasa ido , anso ayi suna sai aka samu matsala...
Hayani taci gaba da tashi , yayin da wasu ke cewa wannan tashin hankali da suka gani yau basu iya bacci , Dikko yace badai anan gidan ba ku gama cin abinci kowa ya kama gabanshi wallahi yau babu mai kwana a gidan nan , dariyar wani daban naji yana cewa sai An mata , Dikko yace koma "yar tsohuwa ce sai kunbar gidan nan ,
Kusan mutum biyu suka haɗa baki wurin cewa wai da gaske akwai mace yanzu haka a gidan nan ? Dikko yace mai maganar zaka tambaya dan nima dai ban sani ba , wai wace ce ita An matan nan ni na daɗe wallahi inaji Dikko yana kiran An mata ko itace ɗiyar ɗan... Sai naji kuma yayi shiru , murmushi nayi nace ɗiyar ɗan caca ,
Duk yanda akayi wani ya dakatar dashi ta hanyar hanashi yayi maganar shi , gaba ɗaya kuma palon yayi shiru har suka gama cin abincinsu babu wanda ya sake magana , bayan sun gama suka fara saɓewa ɗaya bayan ɗaya , bayan kowa ya gama fita naji Al ' Ameen yana ma Dikko sai da safe , banji abinda Dikkon yace mishi ba , ya fice kuma da motar Dikkon ya fita ,
Bayan Al ' Ameen ya fita daga gidan Dikko ya fara kirana , ban ansa ba na taso na fito palon daga bayanshi na tsaya nace gani , shima bai juyo ba yace kinajin yunwa ne ? Nace a , a me kikaci ne ? Nace ba komai , a , a ƙarya kike yarinya me kikaci dai ? Nace maka ba komai , tou zo nan yayi maganar a daidai lokacin da yake kwanciya saman kujera ,
Gabanshi naje na durƙusa cike dajin haushin shi , bai kalleni ba dan hankalin shi nakan tv amma dan tsabar ya ɗaukeni kidahuma yace kinmin kyau fa , zanyi magana ya tsareni da idanuwanshi tare da cewa bafa ina nufin kina da kyau ba ko kin birge ba kawai dai dan bakyajin yunwa nace da kyau , kallonshi nayi amma yanayin fuskata ya nuna banji daɗi ba , murmushi yayi tare da taɓe bakinshi ya kauda kanshi gefe guda yana ci gaba da cewa ni mace mai kyau haushi take bani , dan mafiya yawansu jakuna sunyi yawa a cikinsu kalloni yayi yana tambayata ko nayi ƙarya ?
Kallon da yayi mani yasa nace a , a , murmushi yayi yace ɗaukomin report inki , tashi nayi jiki suku² na fara tafiya , tallabo kanshi yayi da duka hannayen shi yana kallona , zuwa can kuma yayi tsoki wai ji mace na tafiya , babu wani tsari mai jan hankali babu wata zarra mai burgewa a tattare dake , shi sakaran waccan rana kome ya gani a tattare dake zance har 12ndare , ya gane sarai banji daɗin abinda yake faɗa a kaina ba , naje na ɗauko report in na kawo mishi ,
Ansa yayi tare da tashi zaune yana kallona , yace wallahi kina burgeni sosai saboda kina da kyau , murmushi nayi tare da kallonshi , gyara zama yayi yaci gaba da cewa kyawawan idanuwan ki inajin natsuwa yayin da kika kallene ni dasu saboda kyawunsu da sheƙinsu ko a duhu kikayi kallo dasu abun ɗaukar hankali ne , ƙarajin daɗi nayi tare da ɗanyin wasa da idanuwana dan ina so inji an yaba surar da Allah yayi min , kyakkyawan murmushinki yana tafiya da hankali na a duk lokacin da naga kina cikin nishaɗi dan yanayin yana sakani cikin wani irin shauƙi mai wahalar misultuwa , ƙara yashe bakina nayi inajin daɗi , hankalinshi nakan report in yace kike ta wani kwashe baki da ita fa nake ba ke ba , ɗan kama kaina nayi sannan nace wace ce ? Matata mana dan tafi ki haɗuwa yayi maganar tare da ɗaure fuska yaci gaba da kallon report in..
A dibarance na kalleshi shi kuma hankalinshi yana kan report yana kallo ko kyaftawa bayayi sai gemunshi dake motsawa a hankali saboda taunar cingom in da yakeyi cikin kwarewa da salon ɗaukar hankali...
Naɗe takardar yayi tare ɗago ƙafarshi ya takamin kafaɗa yana wasa da report in yace tunanin me kike a makaranta ? Kin rame , kuma cikin ku 20 kika yo na 20 , tunanin me kike ? Duƙar da kaina nayi ƙasa ina wasa da kafet banyi magana ba , jijjigani yayi da ƙafarshi yace baki ji wai ina magana ne ?
Cikin ladabi nace babu komai , to ko aure kike so ne ? 😳 aure kuma ? na tambayeshi tare da zaro idanuwana ina kallonshi , wani irin kallo yayi min mai tsarga zuciya wanda saida tsikar jikina ta tashi naji wani irin yanayi mai wahalar fassarawa na kasa daina kallon idonshi ,
Ɗan kauda kanshi yayi cewa tou daina kallona haka nan , gyara bakina nayi na sauke idona daga fuskarshi , yaci gaba da cewa zan miki haƙuri na yau saboda bance miki kar kiyomin na 20 ba , ban faɗa miki irin position in da nake so ki kawomin ba , amma zan faɗa yanzu..
Kalloni yayi sannan yace wallahi ׳ nayi rantsuwa kuma bazanyi kaffara ba , idan har kika sake kawomin 20 bazan dakeki ba , kuma bazan zageki ba haka bazan sakeyin fushi ba , kinga gidan nan dagani sai ke , sassauta muryarshi yayi ƙasa² yaci gaba da cewa babu wanda zaiji kuma babu wanda zai gani , duk lokacin da kika zo min da na 20 nasan abinda kike tunani , duk lokacin da naga 20 ni kuma zan sakaki a ɗaki irin abinda nayi miki a gidanmu ai kin tuna ko ? Ba tare da ya jira na bashi amsa ba yace tou wallahil azim irinshi zan ƙara miki ,
Kinga idan baki so in miki sai ki dage kiyi karatu , idan kuma kina so sai ki sake kawomin na 20 ni kuma ina ganin 20 tou sai mu shige daga ciki in rufo ƙofa in baki abinda kike tunani kuma ince karki sake ki faɗawa kowa...
Lallai Dikko digirarran ɗan iska ne kuma baida kunya ko kaɗan , kasa haɗa ido ma nayi dashi naci gaba da kallon kafet , komawa yayi ya kwanta tare da cewa kashe tv n can kije ki kwanta , simi² na tashi naje na kashe tv in na wuce ciki ,
Tun daga wannan rana Dikko ya zama siriki na , nafi sati ɗaya ban yadda mun sake haɗuwa dashi ba , idan basu nan zanje in zuba abinci inci , idan kuma yana nan saidai in yini kuma in kwana da yunwa , da kuma naji maganarshi ya shigo ƙaramin palo zan gudu bayi in zamana , idan kuma akayi sa'a ya shigo ɗakin dan ya jira in fito ya ganni to shi da kanshi zai gaji da zaman jirana ya fita , ni kuma idan zasu fita daga gidan zan laɓe jikin window inyi ta kallonshi wallahi bana gajiya da kallonshi kwata²
Gidan kuma kullum sai ya cika da maza suci su asha suyi ta gaddama mara amfani , amma zaiyi wahala kaji bakin Dikko , idan sun gama sun tafi kuma zaiyi kwanciyarshi ne kawai a palo , dan yanzu gidan yake kwana tun ranar da abokinshi yace wai da gaske akwai macen dake zama a gidan nan ? Amma naji ranar nan yana waya da wata wai yaushe zata dawo zai kawo mata amanar wata ɗiyar tsintuwa , nidai haka naji daga nan ban sake jin maganarshi ba , shin nice ɗiyar tsintuwar ko kuma wata ce daban oho...
Kwance nake saman katifa sai juyi nakeyi saboda azabar yunwa , na rasa inda zansa kaina cikina sai zafi yakemin har na gaji da kwanciya kuma gashi duk yau Dikko bai fita , yanzu haka palon ya cika da mutane kuma wallahi ko jiya babu abinda naci tun daga kalacin safe.
Na rasa inda zan tsoma rayuwata inji sanyi , sai hamma nakeyi ga bacci inaji amma yunwa ta hana inyi bacci duk jikina ya mutu bana iya tsinana uwar komai sai kwanciya nake kamar ruwa ,
Ta dubu nasha na fita ƙaramin palo na zauna ko Allah zai kawo min Dikko , amma mi har 11:30 bai shigo ba kuma babu wanda ya fara tafiya har yanzu dan naji sun tashi daga firar kwallo sun dawo labarin "yan danbe , har yanzu banji maganar Dikko ba kila baya gidan gaskiya ,
Daga firar "yan danbe suka faɗa maganar Saminu , wani ne yace bawan Allah Saminu wallahi ana maganar danben nan shi ya faɗo min a rai , me ya sameshi ne ? Wani daban ya tambaya , cikin muryar jimami yace bakaji ba ? Yace wallahi banji ba kuma ban sani ba miya faru ? Yace wallahi tsautsayi da rabon ayi , yaje kallon danbe .
Dariyar Dikko naji yana cewa babu wani tsautsayi kuma babu rabon ayi , kawai ka faɗa mishi matar wani ya nema , kuma dan hauka ya tashi ya bita har gidanta , Allah yasa mijinta ya ritsasu shine yayi ma Saminu shegen duka har saida idonshi ɗaya ya fita , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wannan masifar Dikko kema dariya ranar da na dawo daga makaranta kenan ?
Shima mutumin da ake ba labari salati yakeyi , Dikko yace wato mu mutane muna da wani hali na daban , kai da kanka zaka siyawa kanka matsala sai kace wai Allah ya kawo maka ? Ko ƙaddara ne ko meye ne , kaje ido ya fita wurin zina , kuma abin takaici ma Saminu matanshi biyu amma saboda masifa sai ya nemi mata , waye ya aike shi ? Wa ya saka shi ? Waye ya sashi neman matan aure ni wannan masifa da ta samu mutane bansan irinta ba , wannan tsautsayin dai Saminu shine ya kawo ma kanshi abunshi ba wani ba ,
Mai tambayar yace wa Dikko ina suka haɗu da matar tou ? Dikko yace an faɗa maka kallon danbe yaje , dariya sukayi dukansu , yace nifa ban gane kallon danbe ba , dariya Dikko yayi yace nanfa aka tsaya , wurin kallon danbe suka haɗu ,
Shima naci gareshi mai tambayar yace don Allah wai ya wurin danbe suka haɗu ? Tasowa Dikko yayi ya taho ciki , yana shigowa ya ganni zaune saman kujera yace baki bacci ba kenan ? Yayin da naji "yan palo sun ɗauki ihu duk yanda akayi an fassara kalmar dambe ,
Ba tare dana kalleshi ba nace Eh , zama yayi kusa dani yace mene ne tou ? Nace yunwa nakeji , kallon agogon hannunshi yayi sannan yace kuma wallahi banajin sun rage abinci amma bari su fita mu gani , nace to , wayarshi ya ciro daga aljihu ya ƙura mata ido yana danne ² yayin da nakejin kamar in tambayi Dikko miye dambe ? Dan ina so naji yanda labarin yake tiryan² kuma gashi palo labarin suke amma zuwan Dikko yasa banaji ,
Haka dai rayuwata taci gaba da tafiya zamana tare da Dikko , kullum da tunanin Babana nake kwana dashi nake tashi , bani da wata damuwa ta rayuwa dan Dikko ya shigo cikin rayuwata sosai kuma babu abinda na nema na rasa ,
Daren yau kuwa da kanshi yake tayani haɗa kaya saboda gobe zan koma makaranta idan Allah ya kaimu , sai nasiha yakemin cikin lallashi cike da tausayina da kuma nuna tsantsar soyayyar a gareni , kamar ya buɗe kaina ya zubamin ilimi haka yakeji bawan Allah , saida muka gama haɗa kayan muka fitar dasu ƙaramin palo , duk yanayin Dikko yana nuna bayajin daɗi zai rabu dani , duk inda na motsa zai tsareni da kallo mai tattare da tsantsar ƙauna da shaƙuwa.
Murmushi yayi yace idan kika koma makaranta zaki riƙa tunani na kuwa ? Ya mutsa fuska nayi tare da taɓe baki nace wai ni ? Na nuna kaina ! Yace Eh , nace Allah ya sawaƙamin mema zaija min nayi tunanin yin tunaninka ma ? So ya bani ansa , murmushi nayi tare da cewa tirr Allah ya sawaƙamin in faɗa Soyayyarka , wani irin kallo yayi min mai tsarga zuciya harsai da naji jikina ya mutu sannan yace ke komai sai kinyi wasa ni banajin daɗin haka ,
Jan hannuna yayi muka zauna saman kujera ya tattaro duka natsuwarshi sannan yaci gaba da cewe , ni ina sanki , da sauri na tashi tsaye nace me ? Dikko yace ƙwarai ina sanki kuma kema kina so na wannan shine gaskiya ina ta ɓoyewa kwarai , ya faɗi maganar tare da kauda idonshi daga kaina , dariya nayi tare da cewa wasa kakeyi ne ? Yace a , a da gaske ne fa , ba yanzu na faɗa soyayya dake ba tsawon lokaci , duk lokacin da nazo kusa dake sai inyi ta zuba miki ido wannan ai soyayya ce ,
Idan kina magana ni kuma kawai sai nayi shiru natsaya nayi ta kallonki inajin daɗi wannan shima ai soyayya ne , dakatar dashi nayi ta hanyar ɗaga mishi hannu ya isa , ya isa haka :•
Abinda ka bayyana wannan shine ƙimar matashi kamar ka ? Ba shi bane ba , tsawon wane lokaci muka ɗauka da zamu fuskanci juna ? Fari yaro da yarinya ko wannen su yasan damuwar ɗan uwanshi wannan shine so , sannan fahimtar juna ,
Dikko yace sani da kuma fahimta da kike san ko bakya so kina da damuwa ko bakya da , yayin da kika samu wannan sannan ki so ni ? Wannan shine so ? Soyayya fa ita ba tsarata akeyi ba kawai faruwa takeyi , kinyi waya kuma kina saka mata kati ki siya data sai ta baki duk abinda kike buƙata kinga faruwa hakan yakeyi ba shiryawa akeyi ba , tou wannan shine so , bana so na rasa damata yayin da nace kece sarauniyar mafarkina , kina da damuwa kuma kina da riƙe abu a ranki ,
Duk da haka inayinki , ina sanki , tsoki nayi tare da cewa kayi haƙuri Dikko ba kamar yadda kake tunani bane ni banma yadda da soyayya ba tun daga farko ma kenan , soyayya tana faruwa ne cikin wani lokaci mai gushewa da wurwuri wannan shine tabbataccen hasashen da babu irin shi , ina kaiwa nan na juya na shige ɗakina ,
Murmushi Dikko yayi bayan tafiyar Sultana yace yanzu ta gayamun abinda zanyi kenan , duk da abinda na faɗa mata saida tayimin gaddama ta yarinta na faɗa soyayyarta yawancin abubuwa sukan zo da aibi ku tsaya ku gani zata faɗa soyayya ta da wurwuri.......
24/09/2019
*JAMILA MUSA ...*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 40
Miƙewa yayi bayan ya gama surutanshi ya fita babban palo maƙulin motarshi ya ɗauka ya fita , ina tsaye a jikin window ina kallonshi har ya shiga mota ya bar gidan da gudu bansan inda zaije ba , kuma ga dukkan alamu bazai kwana gidan ba , murmushi nayi tare dayin magana ƙasa² nace sauka lafiya.
Yana fita na dawo na kwanta saman katifa naja bargo na lulluɓe na rufe idanuwana ina jinjina irin wulaƙancin da Dikko yayi mana shi mai kuɗi , "yar madara dabbace amma duk lokacin da naji an kira sunan mage ko na ganta sai magena ta faɗon min a rai da Dikko yabi ta kanta da mota bataji bata gani ba ,
Wulaƙancin da yayi ma Babana a ranar daya wankemin ubanda yafi ko wane uba a wurina da ruwan taɓo , lokacin daya bugamin kanshi har na suma , uwa uba ƙarshen wulaƙanci daya keta min mutuntaka ta , idan ma har zuciyata ta bari ƙiyayyar Dikko ta goge a cikinta ban yafewa kaina , ɗaukar fansa ƙudirina ne kuma muradi nane ko ba daɗe ko ba jima saina kafawa Dikko tarihin da bazai taɓa gogowa a rayuwarshi ba ,
Maganar cewa idan na kawo mishi na 20 zai rufe ƙofa dani nayi masa rata har abada nayi masa nisan da bazai iya kamoni ba , yanda Annabi ya gagari arna haka na gagareka Dikko sa'a ɗaya kawai nake nema fita daga hannunka amma da zaran na zare tou kwankin hararka sun soma...
Dukan sitiyarin mota Dikko yayi a daidai wannan lokacin yace wallahi ƙarya kike , dan tunda ya fito daga gidan zuciyarshi tana faɗa mishi Sultana tana sanshi tabbas kuma akwai wannan soyayya domin yaga soyayyashi kwance a cikin idanuwanta !
Da safe tunda nayi sallah asuba nayi wanka na shirya cikin kayan makaranta , jakata na ɗauka da sauran kuɗina da ban kashe ba nayo babban palo ,
Na daɗe dan nafi ƙarfin awa ɗaya amma babu Dikko babu alamarshi kuma babu mota ko ɗaya a gidan , tun ina zama na marmari har na fara gajiya na kwanta saidai na kalli agogo nayi tsoki dan gani ma nake lokutan basa sauri , raina fa ya gama ɓaci sosai dan har nayi tunanin kila bayau zan koma ba ,
Ƙarfe 9:46am ya shigo gidan , a kasalance ya fito daga cikin motar ya nufo palo , kallo 3 nayi mishi kafin ya iso na kauda kaina , kamar yayi kuka dan yanayin fuskarshi ya nuna rai a haɗe kamar hadarin tsakar dare ,
Da sallama ya shigo palon bai ko kalli inda nake ba ya wuce ciki , na ansa sallamar na gaishe shi bai ansa ba ya wuce , murmushi nayi a zuciyata nace kila matarshi taci ƙaniyarshi , mugu kenan sai lahira a gane halinshi...
Yayi fata² da awowi biyu sannan ya fito tunda ya fito ƙaramin palon ƙamshin turarunshi ya fara zagaye cikin gidan nan lungu da saƙo bana tunanin akwai inda ƙamshin bai kai ba , ƙamshin turare mai daɗi mai jefa mutum cikin wani irin baƙon yanayi mai wahalar mantawa ,
Bayan kamar minti biyu ya iso cikin babban palo , wallahi dole tasa na juya dan yanda naji ƙamshi inga wace shiga yayi haka ? Dan nasan bazaiyi wannan ƙamshin a banza ba , yanayin ƙamshin nasan yanayin haɗuwar da zaiyi kuma ba'a magana , dan duk yanda zan musulta muku kyawun Dikko zakuga kamar shiri ne abun , gaskiya Dikko yana da kyau fiye da duk yanda mutum yake zato , tunda nake a rayuwa ban taɓa ganin wayayyen namiji ɗan gayu mai saurin shiga rai kamar Dikko ba , ko ta ina babu inda mutum ya isa ya kushe shi saidai wani halin daban dan ɗan adam 9 yake bai cika 10 ba , Dikko yana da aji yana da natsuwar da ko mace tayi natsuwarshi taci Allah buɗa ,
Baida yawan dariya haka kuma bai cika murmushi ba , idan kuma yaji mugunta ya fara dariya kai kanka sai abun ya burge ka domin dariya tana mishi kyau , haka kuma murmushi ke ƙara ƙawata kawunshi , kuma yanayin ɗaure fuska ma dai yana mishi kyau gaskiya !
Idona na sauka kan idonshi gabana ya yanke ya faɗi , yasha ƙananan kaya abunshi yayi kyau cikar zatinsa da ƙwarjinsa ya ƙara fitowa sosai , bai kalleni ba ya yayi kamar ma bana nan saida yazo dai² inda nake zaune yace muje ,
Ajiyar zuciya na sauke na ɗauka jakata nabi bayanshi dan shi tuni ya fice daga palon , lokacin dana fito harya shiga mota , ina buɗe murfin motar zan shiga baya zaune naga shine zauna , fuska a haɗe kamar an aiko mishi da sauƙon mutuwa ,
Kawai dai naji babu daɗi yanayin yanda yake ta haɗe rai duk na kama kaina haka nan naji duk na takura , jakata na fara sakawa sannan na shiga na rufe na kalli wani gefe daban ba na driver ba kuma bana Dikko ba , yau an sako Al ' Ameen wani mai girman kan bala'e ne , kamar jira yake na rufe ƙofa ya bige mota kamar zai tashi sama ,
Saida muka fara biyawa Alheri clinic acan matar Dikko take shi kaɗai ya fita yaje ya dubota bai wani daɗe ba ya dawo yana gaba wata kyakkyawar budurwa tana biyoshi baya har suka iso wurin mota ,
Buɗe motar yayi ya ɗauki wayoyinshi daya bari lokacin da zaije wurin Sadiya , gaba ya koma ya zauna ita kuma ta shigo baya , kallona tayi ƙasa da sama sannan tayi tsoki tare da faɗin wata kalma da turanci amma ko miye tanayin maganar da zafi ne ,
Ɗaga kaina nayi na kalli cikin madubi inda Dikko yake kallona , sam yau idonshi hankalin shi da tunaninshi baya wuri na , da gudu driver ya sauko daga inda aka tanada dan ajiye motoci ya ibi hanya yaci gaba da falfala gudu babu ji babu gani ,
Saida mukayi tafiya sosai sannan ta sake faɗar irin kalmar data faɗa daga farko tana hararata , shiru nayi banyi magana ba , bayan wani lokaci tace au na manta ashe da daƙiƙiya nake magana jahila karuwar banza karuwar wofi , wani irin ɓacin rai na haɗeye dakel lumfashina ya fara yawo tsakanin duniya da lahira , taci gaba da cewa karya wacce iyayenki suka kasa baki tarbiya balbaɗaɗɗiya dake ɗiyar ɗan caca ,
Murmushi nayi mai cin zuciya amma banyi magana ba dan na fahimci tana da sauran magana , ci gaba tayi da cewa ni sweetheart baya ɓoyemin komai ni nace yayimin rainonki zuwa ranar da za'a ɗaura mana aure zaki dawo gidana kuma gidan mijina da zama a nan zan fara baki azabar tausayin da yasa kika shigo rayuwata Sadiya ma da tamin hawan ƙawara ya kikaga lamarinta ya ƙare ? Zata tafi duniyar mutuwa babu jimawa ,
Murmushi nayi tare da gyara zamana na kalleta sosai sannan nace idan kin isa ki sake maimaita abinda kika faɗa daga farko ! Nace jahila , nace ni ba jahila bace dan abinda na sani ko uwarki bata sanshi ba , ina da ilimin addini sittin ce a kaina sakara izihinki nawa ke ? Tayi shiru nace tou kinga ɗan caca tun nan ya nuna tarbiyarshi tafi irin wacce babanki ya baki ,
Da kika cemin karuwa tabbas ni karuwa ce bazaki shaida hakan ba saina kasa tallata a bakin titi uban naki idan ya gani zai kwasa , ni da kika gani kamar ɗan silif nake ko mutum baici ba saina burgeshi idan kuma harya taɓa kwanon zai taɓo cikin idan baici ba saiya lashe hannu , tabbas zan nuna miki kaidina da kuma illar kirana da karuwa da kikayi ,
Matsalarki da Sadiya ba tawa bace amma tabbas sai ubanki ya taɓa nan da nan ya kuma maida miyanshi , na faɗi maganar tare da nuna mata wuraren da idonta ke iya gani sannan nace dake da Dikko duk nafi ƙarfinku kuma kinyi ganganci shigowa rayuwata abun harina ya koma biyu daga yanzun nan zanci gaba da hararki kuma in hari Dikko , mari takaimin , nima na rama daga nan muma cakume da kokowa daga zaune ,
Da sauri Dikko ya juyo yace miye haka kuma ? Cikin ɓacin rai nace ban sani ba baƙin munafiki dakai , zaro ido yayi yace ai bake nake tambaya ba , cike da masifa nace nima ai bakai nake ba ansa ba , Ashiru yi parking inji Dikko , da sauri ya gurji gefen titi ƙayyyyy yayi parking har lokacin bamu daina bige² ba ,
Ni Dikko ya fara fiddowa tunda ni nake saitin daya buɗe murfin motar yana fizgoni ya mareni yace nine munafikin An mata ? Kafin ya sauke hannunshi nima na zabgaga mishi mari nace kaine mana munafiki dama akwai wani bayan kai ?
Da sauri Ashiru ya kauda kanshi , murmushi Dikko yayi yace An mata ni kika mara ? Nace waye kai ? Dikkon banza Dikko wofi , fitowa tayi daga cikin motar ta kamani da kokowa duk da banda ƙarfi na firgice sosai dan na tsani inji an aibata Babana , kokowa mukaci gaba dayi Dikko ya riƙeni na sake fizgewa mukaci gaba da faɗa , ya ƙara riƙeni sosai hannun damarshi ya riƙo min ƙuguna dashi hannun haggunshi kuma ya ɗagomin fuskata kowa yana kallon kwayar idon kowa ,
Cikin maganarshi maisa natsuwa yace An mata yau kuma Dikkon ne na banza da wofi ? Ni An mata ? Kinmin adalci kenan ? A gaban mutanen dake ganin girmana zaki tozarni ? Mi yasa bakimin jiya ba ? Me yayi zafi haka haba An matana.... Ya ƙarasa maganar kamar zaiyi kuka , cikin kuka nace cewa fa tayi Babana ɗan caca kuma kaine kace mata ni karuwa ce kuma karya fa 😭 jahila fa 😭daƙiƙiya balbaɗaɗɗiya fa wai Babana bai bani tarbiya ba irin wannan shedar zakuyi ma Baba ?
Tsareni yayi da idanuwanshi masu ɗaukar hankali sannan yace tou kiyi haƙuri , rufe idanuwana nayi nace inyi haƙuri a aibata min Babana ? Dikko ya ƙara cewa kiyi haƙuri , buɗe idanuwa na nayi tare da cewa wallahi Babana bai kasa bani tarbiyya ba kuma kai zaka sheda haka wata rana sakeni , sakina yayi baiyi kaddama ba mota na koma na ɗauko jakata nazo gabanshi na zazzageta nace ga jakar ka nan ga sauran kuɗinka nan idan naje gida zan bada cikonka a kawo maka ,
Ina faɗin haka nayi gaba , Dikko yace ina zaki je ? Juyowa nayi cike da ɓacin rai nace zanje gidan ubanda ya hafeni ne , nasan darajar ɗan caca kuma nasan mutuncinshi , kallon inda budurwar take nayi nace sunana MARYAM ALIYU MUHAMMAD BINNA { Sultana } ki fara kuka tun daga yanzu domin kwanakin baƙin cikinki sun soma daga yau , mafita ɗaya kawai shine ki mutu ki huta amma tabbas bazan goge kuɗina akanki ba wallahi ׳ ,
Kamar sakarai haka Dikko ya tsaya yana kallona , nunasu nayi dukansu da ɗan yatsa nace gata nan gatanan ku , goge hawaye nayi nai gaba cikin ɓacin rai , Dikko ya sake cewa wai An mata miye kikeyi haka ? Tsayawa nayi amma ban juyo ba nace idan ka sakemin magana saina tona maka asiri.......
25/09/2019
Kuyi haƙuri don Allah wallahi banajin daɗi wannan ma dakel nayi shi ,
*JAMILA MUSA...*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 41
Dariya Dikko yayi mai shiga zuciya yace tou miye ribarki idan kin tunamin asiri ? Ai asirina da naki a haɗe yake ki tona tunda ban riƙe miki baki ba , amma ki sani idan kin tonashi sai ki fara neman hanyar da zaki rufeshi saboda tabbas wata rana zaki zama ni , ni kuma zan zama ke , kije abunki amma duk abinda zaki kiyi na hankali da tunani , cikon kuɗi kuma da kike magana bake ba da wani abu ya shiga tsakani dake nake ganin mutunciki da ƙimarki saboda kina da wani matsayi na musamma a rayuwata da zuciyata wanda ta dalilinshi kuma nake ɗaga miki ƙafa , duk abinda ya fita hannuna na gama dashi har abadan abada ,
Kuma zuciyata ta faɗamin cewa ko kin tafi sai kin dawo bata taɓa faɗamin ƙarya akanki ba duk abinda ta faɗamin gaske ne , idan akacemin An mata ta mutu ina da yaƙini zuciyata tacemin a , a tou tabbas idan nazo zan ganki kina numfashi , sauka lafiya amma banda kukan dare dan ina buƙatar bacci a wannan lokacin kiyi kuka da safe kiyi da rana amma idan har kikayi kukan dare gani nan zan dawo ,
Kallon budurwar yayi ya nuna mata da hannu ke koma mota muje , shiga tayi mota shi kuma ya biyo bayana , gabana yasha yace An mata karki zo kiyi abunda zai zama matsala a rayuwarmu , ki manta da abinda ya faru baya mu fuskanci sabuwar rayuwa ,
Cikin kuka na kalleshi nace har ƙarshen numfashi na bana fatan na sake kasancewa dakai wallahi , kuma zuciyarka ta faɗa maka gaskiya tabbas zan dawo amma ɗaukar fansa zata dawo dani ,
Murmushi yayi tare da cewa haba yarinya , Dikko ne fa ! Kin manta nine na koya miki ? Nine nayi kuma nine na fara baki idan daɗi kikaji ko zafi duk nine dai , ruwa idan da rabonka cikin sa ko ka zuba a kwando bai maka yoyo , ni ba abin farautarki bane zaki duk jarumtatai yana ganin ƙimar mafarauci a wancan karon suma kikayi , wannan karon ma haka zata sake faruwa dake ba suma ba har jinya sai kinyi , idan kin dawo ɗauka fansa zaki gane Dikko ba sa'ar wasanki bane domin saina baki azabar da sai kinyi fitsarin wahala bayan kin dawo daga duniyar suma , tsoro na zai shigeki a lokacin da kika kasance dani a shifimɗa ɗaya , idan kuma Dikko baya nan zakiyi kuka bacci ya gagareki gidan biki ko suna Dikko yana tare dake a zuciyarki domin zan zame miki garkuwa , da hannun damarshi ya daki na haggu yace wallahi jarumi ɗaya ake a ƙarni nine jarumin wannan lokaci , Dikko jarumin maza ne kuma ke da kanki zaki faɗa keje ki dawo ina nan ina jiranki ,
Idan kuma soyayya ta dawo dake , ƙasa ya kalla yana nazari bayan wani lokaci ya kalloni yace tabbas zaki zo zuwa gareni kina roƙon na baki soyayya ta , nace wa ni ? Yace tabbas ranar zata zo , nuna kaina nayi tare daci gaba da cewa yi haƙuri Dikko ka manta da wannan wasan kwaikwayon naka har abadan duniya hakan bazai yuwu ba , murmushi yayi tare da taɓa daidai saitin zuciyarshi yace ina da tabbacin zaki soni kamar dai yadda na faɗa , ko kina da tabbacin cewa baza ki taɓa so na ba ? Nace Eh har abadan abada , murmushi yayi yace ƙarya kikeyi , nace da gaske nake , yace zaki gani nima nace zaka gani , girgiza kanshi yayi yace jeki abunki ,
Ci gaba nayi da tafiya har yanzu yana tsaye a wurin dana barshi , motoci masu komawa katsina nayi ta ɗagawa hannu har Allah yasa na samu masu ragemin hanya shiga nayi na nufo katsina yayin da Dikko ya shiga suka kama hanyar abuja ,
Budurwar Dikko kuma ga wayarta a hannuna , domin dana koma mota dama ba jaka na koma ɗaukowa ba waya na ɗauko abinda yasa na fito da jaka dan karsu zargi ni na sace kuma nasan idan sukayi gaba zasuyi tunanin wurin fitowa ta yada ita , Baba da Mama da kowa nata yana cikin waya...
Tunda Dikko suka tafi yake kukan zuci daren jiya da An mata tasan irin matsalar daya fuskanta akanta da bata baɗa mishi ƙura ba , abinda ya faru tsakaninsu sirri ne babu wanda ya sani sai shi sai ita sai Allah , yana bata mutuntukar mutuncinta daya ɗauka amma yarinta ta hanata kusantowa gareshi !
Abinda ya faru jiya , bayan Dikko ya faɗawa An mata yana santa tafiyarta kawai tayi ta barshi palo zaune kamar wani sakarai , bata daɗe da shiga ɗaki ba Dady yace yana nemanshi duk abinda yakeyi ya barshi yazo , shine ya tashi ya fita babban palo ya ɗauki makullin mota ya fita kuma a gaban idon Sultana yabar gidan...
Bayan yaje gida a palon Dady ya samu Al ' Ameen gurfane a gaban Dady , kallo ɗaya yayi mishi ya ɗauke kanshi tare da samun wuri shima ya zauna can nesa da Dady , bayan ya zauna ya gaishe da Dady ya ansa shima Al ' Ameen ya gaishe da Dikko , Dikko bai ansa gaisuwar ba , kallon Al ' Ameen Dady yace ya kira mishi Ummar ,
Miƙewa Al ' Ameen yayi kafin ma ya fita daga palon Umar ya shigo saboda dama tuni an kirashi bai samu isowa da wuri bane , bayan kowa ya zauna Dady ya kalli Al ' Ameen yace ga Babana nan ka sake faɗar abinda ka faɗa , shiru Al ' Ameen yayi , Dady kuma ya kalli Umar bayan Al ' Ameen yaƙi magana yace Umar wace yarinya ce take zaune da Baba ?
Da sauri Umar ya kalli Dikko amma shi basu yake kallo ba yana kallon wani wuri daban , cike da fargaba Umar yace wallahi Dady nidai ban sani ba , Dady yace tou aini Al ' Ameen yace min ya ajiye mace gidanshi na goroba road bayan ni nasan Babana baya huɗɗa mata shi yasa hankalina ya tashi , Umar sake kallon Dikko yayi amma har yanzu Dikko fuskar nan tashi dai kamar yadda take kullum kuma har yanzu baya kallonsu kawai dai yana saurarensu.
Dady yace ƙarya zakamin ne ? Ya tambayi Umar , Umar yayi shiru , Dady yace ma Al ' Ameen yanzu ina yarinyar take ? Tana gidan har yanzu ? Al ' Ameen yayi shiru , gyara zama Dikko yayi yace tana gidan Dady , amma lokacin dana fito na barta tayi bacci , nayi kuskuren rashin sanar dakai amma da Allah kayi haƙuri nayi amfani da maganar ka ne da kace na zama mai kyautatawa duk wanda naga rayuwarshi tana buƙatar taimako ,
Yarinya ce ƙarama shekarunta bazai wuce 18 ba kuma na baka labarinta kwanakin baya itace yarinyar da mukeyin faɗa tou yanzu mun daina faɗan ne , a tsawace Dady yace ɗiyar ɗan caca ? Karuwar Babana ? Cikin ladabi Dikko ya sauke kanshi ƙasa tare da rufe idanuwanshi , Dady yaci gaba da cewa duk ƙoƙarin kare martabar ka da nake maka ni zaka ɓatawa siyasa ka ɓatamin suna har cikin jahata ? Ni zaka zubarwa da mutunci ? Ka ɗauko karuwa ka ajiye a gidanka ka bar matarka kaje ka kwana da "yar iska mara tarbiya wacce tafi ƙarfin iyayenta itace wacce kake ganin kaine zaka gyara mata rayuwa ?
Masifar da tasa iyayenta suka yada ita ba ƙarama bace kai shine kaje ka ɗauko ka dawo da ita rayuwarka kai sarkin imani da tsoron Allah ? Kana siyasa zaka ɓatawa kanka suna , ka zubar da mutuncinka a idon duniya ina amfanin mu'amula da karuwa ? Ko zaka dafa Al ' Qur'ani kayi rantsuwa kace baka neman yarinyar nan babu wanda zai yadda , da yarintar ka baka bi mata ba sai yanzu da shekaru suka fara hawanka ? Tou idan dan rashin lafiyar matar ka ne Momynka ta nemo maka auren ɗiyar yayarta shikenan na kashe maganar...
Murmushi Dikko yayi tare da cewa gaskiya Dady ban tsara zama da mace 3 ba a rayuwata itama Sadiyar haƙuri nayi kawai na ansa amma ni gaskiya mata 3 sunmin yawa wannan karon bazan ansa ba kuyi haƙuri , ciki ɓacin rai Dady yace wallahi idan dai ina lumfashi a duniyar nan baza ka auri karuwa ba sakaran banza da baka san macen da ya kamata ka aura ba , shi aure daka ganshi yana buƙatar cancanta mutuntaka asali da nasabar mace , banda kake sakarai ka rasa wacce zaka so sai karuwa ? Karuwar kake tunanin zata zama uwar "ya "yan ka ? Ni wallahi ko jirgi zan siya bana buƙatar na hannu sai sabo shi yasa bazan iya auren zawara ba amma kai dan baka kishin kanka har kake tunanin auren karuwa , wallahi da kasan kanka ko mace baka nema ,na tsani wani yayi amfani da abu nayi amfani dashi saboda tsanar da nayi ma abun yasa bana sauka hotel , duk jahar daka gani babu inda banda gida babu ƙasar da ban mallaki gida ba dan na tsani wani ya shiga a wuri na shiga sakarai wawa dakai idan baka fita harkar yarinyar nan ba zaka haɗu da fushi na ,
Dady kayi haƙuri kasan.... Tsawa Dady yayi masa yace nasan me ? Ko zaka mutu banajin komai Babana , Dikko zai sake magana Dady yace fita bana san ganinka , jiki a sanyaye Dikko ya miƙe ya fita , ɗakin mom inshi ya nufa itama faɗa ta mishi sosai domin Allah kaɗai yasan abinda Al ' Ameen ya faɗa akan Sultana ,
Itama wata yayarshi da isowarta kenan nigeria tazo ganin Sadiya ta sako bakinta tayi ta ma Dikko faɗa tare da cewa kadaiji kunya wallahi kuma kayi asara ka rasa wacce zaka so sai ɗiyar ɗan caca , abun kunya duk nasabarka da mutunci gidanku kaje ka auro mana ɗiyar marasa asali , jiƙar matsafi ɗiyar ɗan caca karuwa tou ka faɗamin ita me zata haifa ? Kalli yadda tazo ji yadda take tata rayuwa wace irin tarbiya zata ba "ya "yanta ? Gaskiya Dikko ka bani kunya da ina alfahari dakai amma , Dikko ya tareta da cewa amma yanzu kin daina ko ? Tou kije kiyi ta daina warki kuma ki fitar da bakinki idan ba haka ba kuma duk abinda nayi miki ke kika jawa kanki ,
Momy tace rufemin baki mara kunya ko itama halin karuwanci zaka nuna mata ? Dikko yace tou ta ƙara aibata ta kiga yanda zanyi da ita ! Wallahi saina zane mata jiki tas idan kuma tana ganin zaki hana na daketa ta fito waje wallahi saina bi ta kanta da mota na wuce , wani irin mari Momy taimishi dan tasan halin Dikko da kafiya idan dai yace zaiyi sai yayi idan kuma ya rantse akan abu ko za,a mutu baya kaffara saiya aikata wallahi ,
Kallon Yayarshi yayi yace akanki aka mareni ko ? Jinjina kanshi yayi tare da miƙewa yace zan haɗu dake , tace ni ba'a kaina aka mareka ba akan karuwa dai , cikin ɓacin rai Dikko ya nufi wurinta Momy tace idan ka taɓata ban yafe maka ba shanyayye , dariya yayar tashi tayi tare da cewa aikin san karuwa koba asiri akwai bariki mai wahalar goguwa a zuciya , wallahi Dikko ka daiji kunya ɗiyar daka isa ka haifa ai ko baka haihu ba ka kalli ɗan abokinka , fita Dikko yayi daga ɗakin dan idan ya tsaya komai zai iya faruwa ,
Wurin motarshi ya samu Umar , kuma Umar shine ya faɗawa Dikko cewa Al ' Ameen yazo ya faɗawa Dady komai kuma ya ɗora da cewa idanma aure mai gida zaiyi ga ɗiyar yayarshi , shine ya kawota gidansu Dikko kuma tayi sati tunda tazo Dikko bai taɓa ganinta ba sai yau , kuma Dady shine ta tursasa Dikko yaje asibiti ya ɗauketa ya tafi da ita ya ajiyeta kaduna , tunda tazo itace take kula da Sadiya , tana kyautatawa kowa na gidan ,
Ita kuma Momy ta riga data yanke shawara kawai Dikko zai auri autar ɗiyar yayarta , kuma duk zagin da yarinyar nan tayiwa Sultana wallahi Dikko baiji ba , baisan sunayi ba dan hankalin shi baya wurinsu yana can ya tafi duniyar tunani , bige²nsu kawai yaji , amma wallahi baiji zage²nsu ba , Al ' Ameen shi yasan komai akan Sultana kuma shine ya bawa ɗiyar labari yace ta faɗawa Sultana tace Dikko ne ya bata labari , amma tayama Dikko zai fara wannan sakin layi ? Bayan bai haɗa Sultana da kowa ba ,
A gajiye na iso anguwarmu tafiyata babu jimawa anguwar ta samu ci gaba sosai , tun daga farkon layin hannun da Dikko ya sissiye har zuwa gidan dawankashi an bugeshi anyi wani irin zuƙeƙen gini babu wani maƙoci daya raɓeshi baya tare da kowa sai gidajen dake kallon gidanshi , waje kawai aka gyara aka ciccina mishi fulawowi ciki kuma aka watsa dawakuna da wasu irin lafiyayun karnukan turawa masu kama da kuraye , an ƙawata gidan da wasu irin fitulu wanda idan dare yayi aka kunnasu haskensu zai gauraye ko ina da ko ina ,
Gidanmu na shiga da sallama , Nana tana gani na ta tashi da gudu ta shige ɗaki , Babana na gani kwance saman tabarma yanajin magana na ya karkato da kanshi dakel ya kalleni ,
Kowa ya tsaya yana kallona babu wanda ya ansa min sallamar da nayi , wurin Babana na nufa na durƙusa na kamo hannayenshi nace meke damunka ? Kallona yayi cike da tsantsar ƙauna sannan ya buɗe baki dakel idonshi ya cika da hawa yace shine kika tafi kika barni....? 😭
Murmushi nayi tare da goge mishi hawayen nace ai gani na dawo ? Kana tunanin zan tafi na barka ne ? Bayan bana iya rayuwa saida kai ! Dare da rana safe da yamma yanayin farin ciki da damuwa halin yunwa ko ƙoshi babu kowa a zuciyata sai kai , farin ciki ya dawo rayuwar kunci da damuwa zata kama gabanta ,
Har yanzu babu wanda yayi mana magana ga gida cike da jama'a yayin mutane suka fara janye "ya "yansu , matar Baba ƙarami ta kira "yarta gefe tace ki wuce ki tafi gida annoba ta dawo ,
Wane yaro ne ya shigo gidan cikin farin ciki yana barka da dawo uwar ɗakinmu , ban kalleshi ba kuma ban saurareshi ba ina kallon yadda jama'a suke tsame "ya "yansu saboda zuwana , jinjina kai na nayi tare da cewa wane yaro a kawomin abinci da Allah , saida ya saramin caucau Allah dai ya kare miki sharri yayi maganar cikin muryar dabanci , nace Amin shi kuma ya fice...
Fitar wane yaro nabi duk wanda ke gidan da kallo , sannan nace duk sannun ku ? Na dawo ya mai jiki ? Babu wanda ya bani ansa , murmushi nayi na zauna gefen Babana , ban gama zama ba Amisty ta shigo , fitowar Nana daga ɗaki shigowar wane yaro da kwanon abinci , Hafsa A ' i Saude Zalifa Karima sai kuma wata daban wacce nake tunanin itace suke zuwa gidanta wato Asma'u ,
Murmushi nayi tare da miƙewa tsaye nace dama nasan ranar nan tana zuwa shi yasa na taho gida na dawo kuma a tafe nake da sabon salo na baya ba komai bane ba , ga Sultana ga Amisty ga kuma Hafsa ku kaɗai nake da damuwa daku sauran kuma banma sansu ba , ....
26/09/2019
*JAMILA MUSA....*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 42
*_AHUMAGGAH yadda kika fara lafiya ubangiji yasa ki kammala lafiya , ku nemi naku karku bari ya wuceku daga alƙamin SURAYYAHMS haziƙar marubuciya mai tafiya dai² da zamani yana nan yazo..._*
Kallon wane yaro nayi nace kai muje ƙofar gida kaji , na faɗi maganar ina nufar hanyar fita , riƙoni Amisty tay ta baya tana cewa babu wani wajen da zakije anan zamu ci uwarki , ban kalleta ba na kalli inda ta riƙeni nace sakemin hijabi , Hafsa tace baza'a saki ba kina nufin mu zaki ɗauka wasu ƙolaye mu barki kuma , murmushi nayi na kalli Hafsa nace sakarar banza ba ƙolaye ake cewa ba kuzo muje ƙofar gida , saboda bana so ayi wulaƙancin a gaban Babana da kuma sauran jama'ar dake gidan gani na ma kawai yasa sun kora "ya "yansu ina kuma ga anyi wannan maganar a gabansu , duk a zuciyata nayi wannan nazarin ....
Babana ya karkato cikin yanayin jin jiki yace Uwar masu gida me ya faru ne ? Nace ba komai Babana , a kadarance Amisty ta kalleshi tace ai kasani , a wahalce ya kalleta yace me na sani ne Amina ? Nace Baba da Allah ya isa haka kayi bacci abun ka kada a ruwa ai sarki ne kaja bakinka kawai kayi shiru domin ni wutar kara ce ba'a kwana dani ba saidai idan ba bacci ake ba !
Mamana..... Ya faɗa tare da lumshe idanuwan shi yace mene ne ? Kallonshi nayi cikin ɓacin rai nace wutar da aka daɗe da kashewa ni kuma nake so yanzu ta ruru , cikin hayaga ga , nace ɗaukar fansa da ramuwar gayya a cikin jininka yake Babana , baka gada ba ni kuma na gada ɗan koyo da ɗan gado dukansu idan suka tashi sai sun zarta ,
Na rantse da ubangiji da ya bani aron lumfashi da rayuwa dawowa ta sai ta zame ma kowa tashin hankali saina firgita kowa saina jinyata duk wanda ya shigo rayuwata , wallahi ׳ Amisty da Hafsa kun sake toƙalowa kanku masifa idan baku kiyayeni ba uwar kowa a cikinkun nan , na nuna su da ɗan yatsa na jinjinashi nace kuma nayi rantsuwa...
Da sauri Hafsa ta kalli Amisty suka kalli juna cikin firgici , komawa nayi na zauna tare da cewa har kun firgita kenan ko ? Jinjina kaina nayi tare da cewa baku ga komai ba furtawa kaɗai nayi kuma ban faɗa muku abinda zan aikata ba amma tabbas wani abu zai faru , kallon wane yaro nayi nace kai bani abinci kaji , gabana ya ajiye abinci nace muci shi tare , babu ɓata lokaci yasa hannu mukaci gaba dacin abinci ,
Kallo Babana ya bini dashi na wani lokaci sannan ya kalli Amisty yace mi ya haɗaku da Uwar masu gida ? Amisty tayi shiru tou maganar dai bata faɗuwa da kunya tace tsiraicin Babanta na ɗauko , tayi shiru ta kasa magana , lashe hannuna nayi tare da cewa bara kaji abinda ya haɗamu Babana ,
Kafin in ɗago su Amisty sunyi layar ɓata domin dai bansan ta inda sukabi suka fice ba , murmushi Babana yayi mai nuni da yana alfahari dani , kallon wane yaro nayi nace jeka idan Allah ya kaimu jibi ka dawo ina neman ka , godiya yayi ya fice daga gidan , ni kuma ɗakina na nufa ina zuwa na cire kayana , alwallah nayo nazo nayi sallah azahar har saida nayi la'asar sannan na tashi ,
Komai na ɗakina yana nan yanda yake babu abinda aka taɓa har kuɗin dana sata a jakar Amisty duk suna nan , wanka nayi na saka kaya na fice daga gidan , a napep naje gidan su Mamy wacce muka haɗu da ita a wurin saloon , ban sameta gida ba , saidai nabar saƙo idan ta dawo ace mata Sultana tazo mu haɗu gidanmu jibi idan Allah ya kaimu ,
Kasuwa na shiga nayi "yan hidimomi na har katifa na siyowa Babana da sabbin zannuwan gado 3 sabuwar ledar tsakar ɗaki sai ƙaton bargo saboda yanayin sanyi ² dake shigowa da labulaye masu kyau , bayan na gama da kasuwa naje na siya sabon sim card na wuto gida...
Ɗakin kusa da ɗakina na share na shinfiɗa leda na saka katifar na rataya labululluka na shinfiɗa zanin gado mai kyau a saman katifa , ɗakina na koma na ɗauko fulaluwa nazo na saka musu rigarsu irin na zanin dake saman katifar , ruwan zafi na dafa na kaiwa Babana bayi yaje yayi wanka ,
Kafin ya fito na ɗauko mishi kayan da zai saka dan naga kayan a gefen katifar ɗakina , ɗakinshi nakai mishi da turare shima a kusa da kayanshi na gani turare mai shegen tsada da ƙamshi , yana fitowa ya saka kayanshi ya shafa turare sannan yayi alwallah dan magrib ta gabato , abin sallah na shinfiɗa mishi ya hau sama , nima na fito nayi alwallah na wuce ɗakina...
Duƙe yake saman bayan kujera ya ƙurawa waya ido yana kallon hotunan Sultana , murmushi yayi a bayyane yace da wannan kyakkyawar zan kere sa'a na kasace na daban abina , amma dai ya kamata na bata shawara ta daina ciki baki akan cewa baza ta taɓa so na ...
Zagayawa yayi ya zauna saman kujera yana cewa dani dake yau zanga waye tunani zai hana bacci , kwanciya yayi saman kujera ni na kwanta kuma bacci zanyi ya ƙarasa maganar yana murmushi , saida ya lumshe idanuwanshi yace ki kasance cikin farin ciki na barki lafiya....
Saida na gama duk abinda nakeyi na kwanta saman katifa a gajiye , a hankali naja bargo na lulluɓe tare da ƙurawa wayar dana ɗauko ido kira sai shigowa yakeyi babu ƙaƙƙautawa , uhum murmushi nayi tare da kashe wayar gaba ɗaya na rufe idonuwana danyin bacci....
_Ƙarya kike..._
Wannan kalmar itace ta fara zomin a cikin kwalwar kaina , ɗan jujjuya kaina nayi a hankali na gyara kwanciya ta ,
_Zuciyata ta faɗamin cewa ko kin tafi sai kin dawo , bata taɓa faɗamin ƙarya akanki ba duk abinda ta faɗamin gaske ne_
Murmushi nayi har yanzu idanuwana a rufe nace tou ya akayi ban dawo ba ?
_Zaki zo zuwa gareni kina roƙon na baki soyayya ta , tabbas ranar zata zo , murmushin shi yazo ya tsayamin a rai kalmar ƙarya ta sake dawomin a zuciyata..._
Da sauri na tashi zaune nace wallahi ƙarya kakeyi na tsaneka....
Murmushi yayi ya gyara kwanciya , nasan baki tsaneni ba ɓacin rai yasa kike faɗar wannan kalmar , idonshi a rufe yayi magana ...
Wallahi a daren ranar banyi bacci ba , tun daga ranar dana fara ganin Dikko har zuwa yau da muka rabu ko ta ina Dikko ya zargemin zuciya , nayi juye² wallahi bai fita ba , ganin dai baccin bazai zo ba yasa na haƙura na fita nayo alwallah naci gaba da sallah !
***
Yau laraba kuma itace jibin da nake jiran zuwanta , bayan hantsi ya ɗaga na dafa ruwan wanka wa Babana , kafin ya fito na gyara mishi ɗakinshi na share na goge fess na zuba mishi turaren wuta , bayan ya fito wanka ya shirya cikin shiga ta kamala ya baɗa ƙamshi ,
Sama ² ya yagi abin kalacin dana kawo mishi , bayan ya gama ya umurceni dana fitar dashi ƙofar gida saman dakali , ɗakina na koma na ɗauko kafet na naje na shinfiɗa mishi sannan na dawo na kamashi dan har yanzu yanayin abu irin na wanda yasha jiya harya gaji ,
A hankali muka fito dani da Babana muna lallaɓawa , saman dakalin na samu Amisty zaune ita da Hafsa , ko inda suke ban kallaba na taimakawa Baba ya zauna , a dai² lokacin da Umar yake tsugunniya a gaban Baba yana gaishe shi cikin girmamawa tare dayi masa sannu da jiki ,
Naji daɗi sosai dan haka nima na gaishe shi , ya ansa cikin kulawa tare da cewa wurina yazo ya faɗi maganar yana miƙewa , bayanshi nabi mukayi nisa da Baba , bayan mun samu madakata yace mai gida ya aikoni wurinki , kallonshi nayi banyi magana ba , wayarshi ya ciro daga aljihu ya kira Dikko bayan ya ɗauka yace mai gida gata , ya faɗi maganar tare da miƙomin wayar ,
Cikin jin daɗi na ansa na kara a kunne na tare dayin sallama , ansawa yayi cewa ya kike ? Lafiya qalau kaima kana lafiya ? Alhamdulillah , tun shekaran jiya nake so nai miki ya hanya Umar yace yazo ² bakyanan ina kike zuwa ne ? Banje ko ina ba , tou da kyau , na sake cewa banje ko ina ba , yace ai shine nace hakan yayi kyau sai anjima , shiru nayi dan bana so wayar ta tsaya hakanan , shi kuma kashe wayar yayi abunshi...
Miƙa mishi wayarshi nayi , shi kuma yace min yana zuwa , mota ya koma ya ɗaukomin wata "yar ƙarama leda mai tambarin waya a jiki yace gashi yace a kawo miki kuma akwai layi a ciki anyi mata caji ,
Uhum ni da zanma Dikko cikon kuɗi saina ɓige da ansar waya , cikin farin ciki mukayi sallama da Umar , ban koma wurin Babana ba nayi cikin gida ina zuwa na shige ɗakina na zazzage ledar na ciro "yar kyakkyawar wayata na dudduba bansan sunan wayar ba anma an rubuta a jikin wayar , ban damu da sanin sunanta ba nidai tamin kyau kuma ta burgeni sosai , ajiyewa nayi na koma ƙofar gida wurin Babana dasu Amisty dana baro waje ,
Ina fitowa a daidai lokacin da Mamy ta faka da tsadajjiyar motar ta , tasha wani irin dakeken gilashi wanda ya cinye kaf rabin fuskata , karuwa ce data ansa sunanta karuwa , ba karuwar muje mu dawo ba , ba karuwar wahala ba , ba karuwar ya zanyi ba ? Kana ganin zubin iskancinta kasan karuwanci takeyi mai aji kuma mai matsayi ba iskanci cini inci tuwo ba ,
Tana fitowa ta fara bi bi biyyy 👍🏻 cikin yanayi mai nuni da "yar hannun ce , murmushi Babana yayi cikin jattako da gogewa , wata alama yayi mata da ido irin tasu ta "yan bariki , dariya tayi tare da cire gilashinta tace *BINNA* 👍🏻 , Binna kaci dubu ka binne dubu , binna zaki binna kura binnan ƙarshen ƙarni binna ka taushe ..... Sai kuma ta fasa ƙarasawa !
Dariyar "yan duniya Babana yayi tare da ɗan kauda kanshi gefe cikin jin kunyata , Mamy ta sake cewa Binna wuta , wuta na wurina.... Ba tare daya kalleta ba yace ga Mamana nan da nake baki labari ku gaisa , gaba ɗaya tabi mu da kallo dani da Amisty da Hafsa a wani irin yanayi tace wace ce Uwar masu gida ?
Kakkaɓe idanuwa na nayi nace nice , ƙwalalo idanuwa tayi tana kallona sannan ta sake kallon Babana tace Binna Sultana ɗiyarka ce ? Jinjina kai Babana yayi alamar Eh , ƙara kallona tayi sannan ta sake kallon Baba ta juyo ta tsareni da ido....
Kusa da ita na matsa na duƙa ƙasa² nace matsayin kura daban amfanin labule sirri , huɗɗakir da Babana daban nima tawa dake daban ,
Murmushi tayi tare da kallon Amisty tace Amina kuma tsaf ta kira sunan Hafsa , tace ke kuma Sultana ? Nace sosai suma mu'amular ki dasu daban nima har yanzu nawa daban da nasu.....
Kallon Babana tayi shi kuma yayi murmushi tare da cewa mijinki ya dawo ne ? Miji kuma ? 😳 wane irin miji na tambaya a bayyane , kallona Mamy tayi tare da cewa ya dawo ya koma ta ƙarasa maganar tana murmushi , Babana yace sai kuma yaushe zai dawo ? Har yanzu ni take kallo tace harsai na kirashi.... !
Dama kina da aure ne ? Na tambayeta tace Eh amma auren jeka nayi ka kawai idan yazo miji idan baizo ba sauka lafiya , ƙara duƙawa nayi nace ina kika san Amisty da Hafsa ? Wurin Babanki na sansu , Babana kuma kamar ya ....?
Dariya tayi tare da cewa amfanin labule sirri yanzun nan kika faɗa Sultana , saboda haka a sake labulen muje ciki inji neman da kike min ,
Amisty tace Aunty Mamy amana don Allah , cikin rashin fahimta na kalli Amisty nace amanar uwarki .... Dariya Mamy tay tare da cewa ai kinsan ba haka nake ba , kowa da wurinshi ,
Murmushi nayi na nuna mata da "yan yatsuna biyu manuni da mai bi mishi 🤞🏻 kamar ina datsa abu nace kema ...? { lesbian } Tace ina yaran wata ƙawata ne , nace baƙar magana kika faɗamin kenan kikace wurin Babana kika sansu ko ? Tace wallahi tare da Babanki nake ganensu kullum rana ,
Kallon idonta nayi tare da cewa kuma fa da gaske kike ba ƙarya kika faɗa ba , tou amma idan na gano akwai wani abu tsakaninsu da Babana tabbas zaune da tsaye bata ƙare ba , murmushi Mamy tayi tare da cewa ki kiyayi Binna duk macen da kika ga tana manneshi ki mata uziri idan ya gaji da kanshi zai wulaƙansu wallahi babu asiri ba komai idan dai kika faɗa tarkonshi fitarki sai Allah , matan yanzu da kansu suke bibiyarshi , kuma duk mutanen da kika sa nayi musu vidio kwanaki kinsan ko su wayen Babanki ne ?
Nace sai kin faɗa , jinjina kanta tayi tare da cewa gaba zaki sani amma Allah yasa dai wani abu bai shiga tsakaninki da Baban Hafsa ba , ni babu abinda ya taɓa haɗani dashi saidai munayi waya ana maganganu dai irin na gyaran kasuwa , so ɗaya kawai ya taɓa rungumeni ya bani cake a bakin partyn birthday ina , Mamy tace gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zama *KWARATA...*
Cikin rashin fahimta nace su waye ahali ɗayan ? Murmushi tayi tare da cewa wai dani da mijina shima neman matan bariki yakeyi , murmushi nayi nima dan ban taɓa daukar akwai wani abu ba , saidai tacemin da Baban Amisty da Baban Hafsa na fita hanyarsu tsohuwar motace su koda mai sai an tura , na gane karatunta kalami ne na matan bariki ,
Kallon inda su Amisty suke suna fira da Babana cikin tsantsar soyayya akwai soyayyar Babana mai zafi a cikin kwayar idon ko waccensu , sun tsareshi da ido daga gani sunajin daɗin kallonshi dan Babana yana kyau sosai gaskiya kuma ɗan gayu ne ƙirƙirar farko yana da aji kuma yanayin komai nasa cikin tsari da burgewa , tabbas saboda Babana su Amisty suka ƙyaleni amma da ba haka ba idan duk katsina dangina ne babu wanda ya isa ya kwaceni a hannun su Amisty...
Cikin gida muka nufa da Mamy amma zuciyata tana tamin tariya akan maganar Mamy ,
_Gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zama *KWARATA...*_
Juyawa naji kaina nayi kwalwata na zakuɗawa wasu abubuwa sunamin yawo a cikin kai da sauri na rufe idanuwana jikina ya fara kyarma lokaci guda zufa ta ketomin kaina da tunanin da nake dashi da wani sauran sani ya juye kwalwata ta sake toshewa , na sake tashi wata kidahuma ta karfi da yaji.....
Gaba ɗaya saina manta maganar da nayi da Mamy nayi ² na tuno amma sai zuciyata tacemin bamuyi wata magana ba , duk yanda naso na tuno wallahi gaba ɗaya komai ya goce daga cikin kaina , amma ban manta na fitar da Babana waje ba kuma na riƙe nabar su Amisty kuma na tuna nayi waya da Dikko amma sauran maganganun sun ɓacemin ,
Ina ƙofar ɗaki tsaye Mamy ta miƙomin waya cewa ana kiranki , da sauri na ansa na ɗauka , An mata Dikko ya kirani a cikin wata irin murya yace meke damunki ne ? Ba komai na bashi ansa , yace karki min ƙarya meke damunki ne ? Tunani na fara yi , sassauta murya yayi yace me kikeyi yanzu ? Ba komai , kina yanayin tsayuwa ko zama ? Nace tsaye nake , An mata zaki iya faɗamin ko wane iri ne Dikko ? Shiru nayi ina tunani , yace tuna ² An matana , har yanzu kaina juyawa yakeyi , yace kin tuno ko wane iri ne Dikko ko ?
Wallahi Dikkon ma ya ɓacemin , An mata tsaya kiji kin tuna nine mukayi fada dake har kika mareni , kin tuna ? Eh na ganeka , amma me yasa kamin wannan bayanin ne ? Murmushi yayi tare da cewa kawai mafarki nayi wai kin manta dani shine nayi sauri na tashi a baccin na kiraki dan Allah kimin adalici karki manta dani kinji An mata , nace tou yawwa An matana..... Muah yai sumbata , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya na kashe wayar....
Ɗaki na shiga na ɗauko wayar budurwar Dikko ina zama kusa da Mamy nace ciro layin ciki ki saka a wayar nan.....
27/09/2019
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 43
*_Ina miƙo saƙon ta'aziyya gareki HALIMATU SADIYYA MUHAMMAD { Leema } Allah ya bada haƙuri ya jiƙanta yasa ta huta mu kuma ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo..._*
*_Don Allah dan Annabin rahma kuyi haƙuri yadda labarin yazo min kenan haka nake rubuta shi_*
Me za'ayi da layin idan an ciroshi ne ? Shine tambayar da Mamy tayimin , kallo nabi Mamy dashi yayin da nima nake tambayarta wane irin layi kuma...? Mamy tace kina miƙomin waya ne kince na cire layin ciki na saka a wannan wayar shine nace meye ?
A ni ban wani faɗa ba ko dai kin fara ƙarya ne Mamy ? Nifa bana san ƙarya da kika ganni ƙatuwa dake bakyajin kunyar Allah bare kunya na kike nema kijamin sharri ko ? Tou tashi fitar min ɗaki , kamar sakara haka Mamy ta tsaya tana kallona , a hayagagance nace fita....... Da Allah malama , na faɗi maganar ina nuna mata hanyar fita , kallona Mamy tayi sosai tace ke Sultana anya kina da lissafi kuwa ?
A , a banda shi sai ke kika iya malamar lissafi , kila ma kece makarantar boko gaba ɗaga ko ? Murmushi Mamy tayi tabi Sultana da kallo cikin yanayin tausayawa , shi yasa ramuwa ga ramuwar abinda akayi maka babu kyau ka rama sharri ga sharri , Binna kuma idan har na faɗa mishi komai tabbas rayuwar yarinyar nan zata ƙare a gariri ne kawai , tun farko da bai anshi buduricin matar Bello a daren farko ba duk da haka bata faru da tilon "yar shi da ya ɗauki soyayyar duniya da ƙauna ya ɗora mata , dogon tunani Mamy ta tafi , tunanin abinda ya wuce shekaru da yawa shine wani sashe na daban yazo mata a kanta...
_Cikin farin ciki Binna ya shigo gidansu , dan dashi da Bello kowa baya ma kowa iyaka da shiga gidan kowa , kowa kai tsaye yake shiga..._
_Bello yana zaune tsakar gida Binna ya rungume shi cikin farin ciki da in ina yace kai banzan abokina an haifomin balarabiya yanzu na aihu a duniya duk na gaba hoton banza ne , kaga yarinyar kuwa ? Kyakkyawa da ita gata fara , burina akan ta zai sauka , itace Uwar masu gida dama nace sai an haifomin mai kyau zansa sunan mahaifiyata , zan gina mata rayuwa mai kyau dan ina so inyi alfahari da ita..._
_Murmushin yaƙe Bello yayi tare da cewa wane irin farin ciki kake ji a yau ɗin nan ? Binna yace baya musultuwa , Bello yace yanzu alal misali yarinyar nan sai kawai ayi mata fyaɗ...... Ai bai gama faɗa ba Binna yakai mishi wani irin duka harsai da Bello ya suma , duka ɗayan da Binna yayi masa yasashi tafiya duniyar suma , da gudu Mamy ta ɗauko ruwa ta yayyafawa Bello ya dawo , kallon Binna yayi tare da cewa alal misali fa kawai nace ! 👌🏻 Binna baiyi magana ba sai huci yakeyi kamar ɗan matashin zaki , jinjina kai Bello yayi tare da cewe hakan ya nunamin irin soyayyar da kake yi wa yarinyar nan , tsoki Binna yayi ya fice daga gidan..._
_Fitar Binna Bello yayi dariya tare da kallon Mamy yace wallahi tabon da Binna yamin yana nan bazai taɓa gogewa ba , shi a tunaninshi yaci banza , ya amshe min budurci mata a daren farko kuma yake tunanin zai gujeni , kyaleshi nayi kawai ni da kaina naje na bashi haƙuri duk da ni yayi ma laifi , na lallashe shi muka dawo muka koma ɗaya , tun kafin Binna yai aure yake bada labari akan zuwan Uwar masu gida , yau tazo kuma ta faɗo a dai² lokacin da Bello ke jiranta , ɗaukar fansa ba'a kan "ya "yanshi yake ba akan zuciyarshi yake wato Uwar masu gida mu tafi wasan daga yanzu Binna dani dakai wanda ya fasa shi ba ɗan iyayenshi bane ba..._
_Mamy tace haba dan Allah wai harsai yaushe zaku daina wannan ɗauke ²n fansar naku ne ? Ya kamata abu ya riƙa wucewa a wurinku don Allah , kayi haƙuri don Allah karka cutar da yarinyar ku daina jefe² da tsafe²n nan Bello , Bello yace na rantse da ubangiji daya aiko annabi da gaskiya sai yarinyar nan tayi karuwanci , shine abinda ya tsana tayi , kuma sai tayishi wallahi , namiji ɗaya ne zai buɗe mata ƙofa daga nan zata firgice ,kuma yaci buri akan sai ta zama malamar asibiti wallahi har a busa ƙaho ita da ilimin zamani , zan cuɗanya "yan uwa su halaka zan ɓata zumuncin su ,.... !_
Murmushi Mamy tayi tare da kallon Sultana tace tou zan wuce , kallonta nayi nace kai tun yanzu ? Haba dan Allah karki tafi ki zauna muyi magana , Mamy tace ba komai zan dawo zuwa asabar in Allah ya yadda , ansar wayata tayi ta sakamin numberta , tace kinga number na nan , idan kika tuna abinda zaki faɗamin to ki kirani kinji ko ? Jinjina kaina nayi alamar gasuwa , zan wuce ta sake faɗa , miƙewa nayi dan in mata rakiya...
Har ƙofar gida tayi sallama da Baba tahau motar ta tayi tafiyarta , wurin Baba naje na zauna dan Amisty bata nan kila tana gidan Asma'u , kallon Hafsa nayi dake muguwar matsoraciya ce kamar ni , nace da Allah ba mutane wuri zasuyi magana da Babansu , babu gaddama ta miƙe itama ta wuce gidan Asma'u...
Kusa da Babana na matsa sosai ina kallonshi nace Babana , yace Mamana ya akayi ne ? Runtse idanuwana nayi kwalwata tanamin wani irin zafi kamar zata fita daga cikin ƙoƙon kaina , hawaye ya cikamin idona cikin kuka na sake cewa Baba , riƙeni yayi tare da cewa wai miye ne Mamana ?
Buɗe idona nayi tare da cewa zaka iya misulta irin soyayyar da kakemin ? Murmushi yayi tare da kafeni da idanuwanshi , faɗamin Baba , hannunwashi ya buɗe kamar zai rumgumi wani abu , kallon yanda ya buɗe hannuwan nayi nace ɗan haka Babana ? Ƙara buɗewa yayi na sake cewa wannan kaɗai ? Murmushi ya sakeyi tare da buɗe ko wane hannu saida ya taɓa bango iyakar buɗewa sannan yace ina miki soyayyar da bata da farko bata da ƙarshe ,
Murmushi nayi tare da kamo hannayenshi na riƙe nace nima ina sanka , ina kuma tausawa rayuwata ranar da za'a waye gari babu ɗaya a cikin wa'annan masoya , idan na rasa ka zanyi kuka Babana harsai na haukace , idan kuma na rigaka mutuwa nasan kaima zaka zare kamar dai yadda zanyi idan baka duniyar nan ....
Murmushi yayi tare da cewa haba Mamana idan har na mutu karki sake kimin kuka kimin addu'a itace kawai zata tabbatarmin da irin soyayyar da kikemin , tou mudaina maganar mutuwar nan Babana...
Yace tou an daina , nace to wai Babana ina kasan Mamy ? Yace tsohuwar matar Bello ce , murmushi nayi tare da kallonshi nace kaima ka zagaya zawarci ba .... ? Na ƙarasa maganar ina nunashi ina dariya , dariya yayi shima cewa ita dai tayi zawarci na , tou mi yasa baka aureta ba ? Ba tsari na bace ba , ya bani amsa , murmushi nayi nace to wai kuma da gaske tana da aure ? Eh mana tana da aure hada yaranta amma bata aihu da Bello ba , tou Baba amma kuma naga kamar karuwa ce ! Yace Eh me yasa kika ce haka ? Shiru nayi dan dai babu dama na bashi labarin abinda ya faru tsakani na da ita akan iyayensu Amisty ,
Share maganar nayi da son nayi mishi maganar su Amisty amma sai kawai zufa taci gaba da kwararomin , kaina ya ci gaba da tafasa zuciyata tanamin wani irin zafi , lokaci guda kuma ɗimuwar tunani ta sake zuwa min , kallona Baba yai yace ya akayi kuma kinyi shiru ? Saboda hijabi ne jikina da yaga irin zufar da nakeyi...
Miƙewa nayi kawai na koma cikin gida , ina shiga Nana ta nufoni tana magana ko saurarenta banyi ba bare insan abinda take cewa , ina zuwa ɗaki na faɗa saman katifa na dafe kaina wai meke faruwa dani ne......?
Gaskiya Bello baka da mutunci kuma kaci amanar amintaka Allah bazai barka ba , Mamy ke faɗawa Bello magana dan daga gidansu Sultana wurinshi ta nufa kai tsaye , dariya Bello yayi yace umm dama nasan sai kin hallara ai mayya , wai me yasa kike san Binna da yawa haka ne ?
Murmushi Mamy tayi tace duk abinda yasa ma nake maitar tashi ka sani kuma maitarshi yanzu na fara , dariya yayi yace iska na wahar da mai kayan kara kuma wallahi kika sake dawomin da hannun agogo baya saina shafe babinki a saman doron ƙasa ... Dariya Mamy tayi sannan tace ina jiranka , tana faɗin haka taja motar ta tayi gaba...
Ranar juma'a da daddare bayan na gama sallar isha'e na fito da makullin mota ina sauri dan jirana Baba yakeyi sai kira yake kwalamin , ina fitowa Nana tace Alaji yazo nemanki bansan kina nan ba aka ce masa bakya nan , ko inda take ban kalla ba , muka fita daga gidan dani da Baba majalisarsu zan ajiye shi yacemin yanajin sauƙi naje na kaishi yaga abinda ake ciki ,
Ina ajiyeshi na dawo gida ban biya ko ina ba , ko parking ban gama gyarawa ba na hango wata mota a gabana kamar ana kokowa a ciki sakamakon haskasu da nayi da fitilar mota ta , da sauri na fita daga cikin mota ta na tun karesu ina zuwa na buɗe motar wai in rabasu , me zan gani.... Haka ?
Ƙanwata na gani ana iskanci da ita a cikin motar watanni biyar na bata da aihuwa , kallon saurayin nayi sannan na kalleta nace me kukeyi haka ne ? Babu damuwa ko fargaba a tare da ita sukaci gaba da abinda sukeyi , jiki a sanyaye na rufe musu ƙofar na koma motata na zauna ina jiran su gama ,
Hawaye naji ya cikamin ido nasan duk yadda akayi kila ta nemi wani abu ta rasa kuma ta tambayi Baba kawai zaice taje saurayinta ya bata , kwantar da kaina nayi saman sitiyarin mota ina goge hawaye , zata fito zan mata faɗa nace duk abinda take so ta faɗamin zan riƙa bata ,
Ai ban gama tunanin ba kaina ya juye , zuciyata tace karki wani yi mata nasiha kinga kin samu ƙarin fasinja daga nan zaki samu tayo miki yaƙi da "ya "yan gidan Baba ƙarami kawai kuci gaba da sha'aninku tunda kun rabu dasu Amisty , murmushi nayi tare da cewa tabbas haka za'ayi...
Dama ranar dana dawo naga kowa sai janye ɗanshi yakeyi karna gurɓatashi , zuciyata tacemin Eh kiyi ƙoƙari ki yaƙi duk wanda ya kyamaceki kinga idan kowa ya zama ɗan iska abun zai miki sauƙi wurin gori ,
Haka ne fa , ina ƙoƙarin fita a mota shima yayi parking in tashi daga bayana ya riƙa wasa da fitilar motarshi , ta kashe ta kunna , rufe mota ta nayi na nufi saman dakali inda zan jira fitowar "yar uwata ,
Ina zuwa dai² motar zan wuce ya buɗe murfin motar ƙamshin shi da sanyi a c suka lulluɓemin kaf ilahir ɓargon jikina , a kasalance na tsaya tare cewa ashe kaine ? Ey mana nine nazo gaishe shi , murmushi nayi na kunna fitilar wayata dan idanuwana sun ƙagara suga fuskar Dikko , haskashi nayi yaɗan shanye idanushi saboda hasken fitilar...
Sai ya ɗan rufesu ya buɗe su yayi haka yakai sau biyar sannan yace kinasan ki ganni ne ko ? Bara na kunna miki fitila ki ganni sosai , da sauri na kashe fitilar wayata na taɓe baki nace wa ni ? Tirr Allah ya sawaƙemin me zan kalla fuskarka , a dai² lokacin daya kunna fitilar motarshi yana cewa kinfi kowa sanin abinda kike kallo....
Murmushi yayi tare dayimin wani irin kallo yace ya kika gannin ne ? Ya ƙarasa maganar yana kashemin ido ɗaya , juya mishi baya nayi ina murmushi cikin jin kunya , gyara zamanshi yayi yana cewa bari in tafi zuwana kenan nace saina fara ganinki yakai hannunshi ya kashe fitilar daya kunna ,
Harararshi nayi tare da cewa kuma bakai kyau ba , dama banda abinki meya haɗa namiji da kyau ? Kece dai mai kyau kuma daga yanzu idan na kiraki saima na riƙa cewa ya kyau ? Zan tafi yayi maganar yana rufe motar , shiru nayi banyi magana ba dan bana san ya tafi kuma shima ya gane haka ,
Sauke gilashin motar yayi ya kwatar da kanshi saman murfin motar yana kallona ta sama yace ko kar in tafi ne ? A , a , a , a kawai kaje abunka , cikin sigar zaula yace kedai....... In tsaya ki ƙara gani na ko ? Matsawa nayi ina cewa wuce , murmushi yayi tare da cewa to na wuce sai Allah ya kaimu , nace amin , ɗage gilashin motarshi yayi ya fice da rubos tun daga ƙofar gidanmu har bakin titi , yana fita yaci taya ya ɓace abunshi , murmushi nayi komai na Dikko burgeni yakeyi ,
Cike da soyayyarshi na isa bakin dakali na zauna , ban daɗe da zama ba ta fito zata shige gida nace yaki Hamida , zuwa tayi tace gani , cikin tausayawa na kalleta dan itama babu uwarta a gidan , nace Hamida kin tambayi Baba wani abu bai baki ba ko ?
Shiru tayi tana kallon ƙasa , nace kimin magana kinyi shiru , yanayin ta ya nuna bata san ta faɗamin abinda ya faru dan sunsan bana san laifi Babana , tou tun yaushe kika fara wannan harkar ne ? Tace an daɗe gaskiya , nace yanzu har kinsan daɗin namiji kenan ko ? Daga gefenmu naji maganar Fa'iza na cewa wai na cikin masai ke cewa na waje ya taka kashi , nawa kike Sultana ? Kema kinsan daɗin namiji bare ita ko an faɗa miki ita dutse ce ba mutum ba ? Duk yadda kikeji itama irin abun takeji , ko nufin ki kiyi mata nasiha ? Keji Sultana da buƙulu zatama yarinya baƙin ciki ,
Ba tare dana kalleta ba nace ke kuma ina ruwanki da firarmu ? Da ruwana mana idan bata samo kuɗinta ba kece zaki riƙa cida ita ne ? Fita sabgar Fa'iza nayi nace nawa ya baki ne ? 150 zaro idanuwa nayi nace 150 sai kaci yaci yaɗi ? Fa'iza tace waike Sultana ina ruwanki da rayuwarta ne ? Ko ke wani ya shiga taki sabgar ne ? Banma Fa'iza magana ba naci gaba da cewa aiko kina karuwanci wahala gaskiya , janyeta Fa'iza tayi tana cewa kyaleta idan kika biye mata sai yinwa ta kamaki a gidan nan , tunda Allah ya baki kin samu na kalacin safe...
Suna gaf da shiga gida nace Hamida idan zaki iya huɗɗa dani kizo zan kaiki inda zaki samu kuɗi karki kuskura ki bari a koya miki toya awara a ƙofar gida hayaƙi ya kashe miki ido , kizo in haɗa da wani Alhaji ki biya buƙatarki kuma ga tulin kuɗi , Fa'iza tace naje na toya awarar dan uwarki , dama habaici ne nake mata kuma taji haushi tunda ta tanka , Fa'iza taci gaba da cewa kuma ita bata bin manyan Alhazawa ta bar miki kije kija , nace kece shedar inaja tunda kinga motar da nake hawa , danni ba sakara bace bana barin namiji ya hauni ya a banza ya sauka ni kuma in tashi a 150 ko doki namiji zai hau sai bada kuɗi da yawa bare kuma mace mai daraja....
Idan dai ka murza tou tabbas nima saina murje aljihunka fess , janta tayi sukayi shige gida , dariya nayi nima nabi bayansu , ina cewa 100k idan kin shirya ki sameni ɗakina...
29/09/2019
*JAMILA MUSA....*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 44
Ina ƙoƙarin shiga ɗaki Nana ta taho wurina a firgice jikinta yana kyarma tace Uwar room zo kiji wani abun tashin hankali , a firgice na kalleta nace kai miye haka har kin bani tsoro wallahi , magana ƙasa² tace zo muje ƙofar gida tayi maganar tana jan hannuna har muka fito waje...
Muna fita ta fara waige² irin yanda magulmata keyi idan zasuyi kilbibi , bayan ta tabbatar babu kowa tace da Amisty da Hafsa suna asibiti , a nutse nace meya samesu ne ? Ƙara matsowa kusa dani Nana tayi kamar zata koma cikin cikina tace gidan matar da suke zuwa...
Meya faru a gidan ? Nana tace mijinta yazo ya samesu suna maɗigo , { Lesbian } Asma'un tana ganinshi ta fara kuka ashe sun manta basu rufe ƙofa ba ya rutsasu duk sun haye mishi mata , Asma'u tace ya rufa mata asiri tana cewa ita wallahi ba halinta bane cutarta kawai akayi tana bashi haƙuri ,
Bai mata magana ba ya koma ya kulle ƙofa , bayan ya kullo ya dawo yace kiyi haƙuri my wife ba wani abu da zai faru sukadai yi miki haka ko ? Tace Eh yace tou koma gefe yanzun nan zan rama miki abinda sukayi miki , wayarshi ya ciro daga aljihu ya fara kiran abokanshi yana cewa suzo gidanshi yanzu akwai babban aiki kuma kowa ya shawo ta dubo ya taho dan yau a gidanshi za'ayi kwana ana wasan *DANBE...* shagon mada da shagon gwaggo zasu buga babbar lamba...
Bayan ya gama waya ya hunce tare da jawo ƙarfar Hafsa yace kece kika sha mata nan ko ? Ya ƙarasa maganar tare da taɓa inda yaga tana ma matarshi , cikin kuka Hafsa tace dan Allah kayi haƙuri tsautsayi ne , mijin Asma'u yace ai nima tsautsauyin zan nuna miki , Hafsa zata sake magana ya haɗe bakinshi da nata , wata irin ƙara Asma'u tayi ba tare daya kalleta ba yace Swry madam rama miki zanyi....
Cikin kuka Asma'u tace dan Allah kar kayi , har yanzu bai kalleta ba yace tou ni banza ne inzo in samu wasu na ƙwaƙulemin mata in barsu su tafi a haka ai wallahi ko waccensu saina bata tukwuici , kowa a cikinsu sai taji nauhi na , ihu Asma'u takeyi tana ba mijinta haƙuri baya ji kuma baya gani , kusa dashi ta matsa ta riƙoshi wani irin mari yayi mata wanda yasa tayi zaman dirshen dole a katsa ,
Haka ya farke Hafsa tas kuma bashi ne farko ba shima akan hanyar wani yabi ya wuce , bayan ya gama ya jawo Amisty itama ya kaita , yana gamawa da Amisty ya sake jawo Hafsa saidai ya zagaya ko waccen su so 3 sannan abokanshi suka shigo suma sukaji yanda kowa keji , bayan sun gama yace itama Asma'u suyi mata , ke a gidan dai haka aka kwana bala'e ana zagaye ² har gari ya waye , da safe kuma ya bawa Asma'u saki 3 gaba ɗaya , kai naga cikakkin *KWARATA...*
Wato a gabanki akayi komai kenan ko ? Na tambayi Nana , tace a , a ina ni ayi a gabana ? Ita Amisty tamin waya na taro musu mai napep , dani dasu Zalifa mukaje dan har muka isa asibiti Hafsa bata farko ba , itama Asma'u taji jiki sosai dake Amisty jar wuya ce ita bata wani damu ba ,
Shiru nayi ina kallon Nana zuwa wani lokaci nace mata miye wasan *DANBE... ?* Nana tace wani sabon iskanci ne maza ke zuwa su saka kuɗi a jera musu layin mata , ko wane namiji zaibi mace goma wanda yakai ba tare daya gajiya ba kuma ya gamsar da ko wace a cikinsu tou dama kuɗi ake zubawa , idan ko wace ta samu biyan buƙata kuma namiji bai huta ba tou wannan miliyoyin kuɗin nashi ne shi zai lashe su , tou ai irin *DANBEN...* mijin Asma'u yakeyi, shine sana'arshi...
Haka nan naji raina ya ɓaci wato Dikko kallo yake zuwa shima shi yasa naji yana cewa Saminu a wurin wasan danbe ya haɗu da wata ya bita baisan matar aure bace ba ,
Cike da ɓacin rai na koma cikin gida , ina shiga ɗakina na ɗauki wayata na fara kiran lambar Dikko , na kirashi yafi sau a irga amma bai ɗauka ba , zuciyata tacemin yana can kallon Danbe , raina ɓace na koma ƙofar gida na ɗauki mota ta na ibi hanyar goruba road , dan nasan irin wannan lokacin suna can suna kallon kwallo , 10:29pm na isa , inayin horn aka buɗemin get na shige...
Motoci sunfi goma a harabar gidan , dama nabar wasu a waje ma , cike da ɓacin rai na sauko ko ganin gabana banayi na tun kari palon , ashe ina fitowa mota ya ganni dan haka ya taso da sauri dan ya tareni , a bakin ƙofa ya tsaya ya raba hannunwa shi ya tare ni , kwantar da kanshi saman kafaɗarshi ta dama yace An mata lafiya ?
Cikin ɓacin rai nace ashe kai ɗan iska ne , da sauri ya buɗe bakinshi cikin yanayi mamaki yace me kuma yayi zafi haka ? Nace ban sani ba , ɗan buɗe idanuwanshi yayi sosai yace tou ai kin bani dunƙule bansan abinda nayi miki ba , kince ni ɗan iska ne nace me akayi kuma kince baki sani ba ,
Rufe idanuwana nayi hawaye na zubowa nace ashe danben ranar nan da kake magana iskanci ne , dariya Dikko yayi tare da sauko hannayen shi daga inda ya ɗorasu , jan hannu na yayi muka koma cikin mota ta , bayan mun zauna yace waye ya faɗa miki ? Banyi munafinci ba na kwashe kaf na zayyanawa Dikko labarin da Nana ta bani , dariya yayi sosai yace tou ni bana zuwa kallon danbe ban taɓa zuwa ba , ina da labari dai kuma abinda yasa kikaji nayi maganar danben a waccan rana shi Saminun abokina ne , kuma shine ya kirani yake faɗamin abinda ya faru dashi , kuma nace kizo muje kikace baza ki ba , da wannan abun yasa kika taho ? Da Allah baisa na ganki na tareki ba da haka zaki zo ki ɓara maganar gaban mutane ?
Tou ni ban taɓa kallon danbe kowa ba sai nawa da naki , kuma ina addu'a ubangiji ya tabbatar min dake a matsayin mata ta naci gaba da miki kina alfahari dani , yanzu kin yadda kinajin soyayya ta ko ? Ya ƙarasa maganar yana leƙo fuskata , kauda kaina nayi saboda kunya , Dikko yace kinga kinyi kuka dan kina tunani DK n ki yana zuwa kallon danbe , ki kwantar da hankalinki Dikko naki ne ke ɗaya da izinin ubangiji , ni bana zarginki har abadan duniya anma dan Allah karki sake ki bari zuciya da sharrin shaiɗan yasa aimin wasan danbe dake , ni ɗaya tak na isheki bana gajiya kuma bazan taɓa gajiya dake ba har ƙarshen numfashi na ,
Kwantar da fuska ta nayi saman sitiyari nace to me yasa gwamnati baza ta hana wannan saɓon ba ? Dikko yace tou waye yasan sunayi ? Bayan sun ɓoye babu wanda yasan inda suke sai su kaɗai , muna tare dasu muna cuɗanya bamu sansu ba tunda ba rubutawa akeyi a jikin mutum ba , yanzu dani dake da muka ɓoye mukayi waye ya sani ? Babu wanda ya sani daga ni sai ke sai Allahn daya haliccemu kuma kullum ina neman ya gafarta min kuma ai kin yafemin An mata ko ?
Shiru nayi banyi magana ba , kallon agogon hannunshi yayi yace kizo ki tafi gida dare yayi ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin fita daga motar , nidai bana so ya tafi banƙi mun kwana muna magana ba , dan wallahi maganar Dikko daɗi gareta ga sa natsuwa wani irin harshe yake amfani dashi wurin magana nidai tunda nake ban taɓajin irin yanayin maganarshi ba , amma shi na lura baya san yana daɗewa tare dani , ƙara maido maganar baya nayi cewa ,
Tou baka san Saminu ba , yace An mata ƙungiya ce fa , kuma daga jin irin kuɗaɗen da ake zubawa ai kinsan ba talakawa bane ba , can matsalarsu suyi rayuwarsu muyi namu rayuwar manta da sha'anin wasan danbe kin fara so na yanzu ko ? Shiru nayi , yace tou nidai ina sanki kuma kullum saina faɗa ,
Maganar abokinshi naji yana cewa DK wace "yar yarinya ce ka ƙurmusa a mota ? Fita yayi yana cewa An mata ce zo ku gaisa da ita , a tadai zo ta gaisheni baka faɗa mata ni yayanka bane ? Ya ƙarasa maganar yana zama saman bayan mota , ba tare daya bashi ansa ba ya maidai fuskarshi kamar yadda take wato ya ɗaure tare da rufe murfin motana yana cewa Allah ya tsare hanya ,
Kunna mota ta nayi zan fita , gaba ɗaya mazan dake palon suka fito suna cewa mai gadi karka buɗe yau sai munga "yar matan da yake ɓoyewa , cikin ɓacin rai Dikko yace kai buɗe mata hanya ta wuce , da sauri ya fara ƙoƙarin buɗewa su kuma suna cewa idan ka bari ta fita bamu ganta ba wallahi ubanka zamuci , Dikko yace wai da Allah mi yasa kukeyin abu wani iri ? Koma ce mana kayi mahaukata wallahi sai mun ganta ,
Dikko yace ashe kuwa zakuyi kaffara , kallon mai gadin yayi cikin tsananin fushi yace na rantse da girman Allah ka buɗe get in nan idan kuma baka buɗe ba na rantse da wanda rayuwata ke hannunshi saina taka ka da mota in take ka mutu kamar ɓera kuma babu abinda za'ayi na kashe banza , sanin hali yafi sanin kama , da sauri ya buɗe get in duk zagin da ake mishi ni kuma na fice da da gudu...
Sultana tana fita sukayi kanshi suna zagi dan ubanka ba cewa mukayi karka buɗe mata ba ? Mu da bama bi takanka da mota ko ? Faffala mishi mari kowa yayi sannan suka bi bayan Dikko daya koma palo ya kira Sultana yace karta sake zuwa idan tana san ganinshi zaizo ya sameta ko tana ina , tace insha Allah , bayan ya gama wayar yace hmm An mata ta rainani , bata ganin girmana ko kaɗan , tacemin ɗan iska munafiki hada mari , idanma ban auri yarinyar nan ba ai ta gama dani duk lokacin data ganni tana min kallon sakarai na nasha dakai , duk borinki na waje ne bari dai in lallaɓaki kizo hannu zaki gane ruwa ba sa'ar kwando bane...
Saida na biya ta majalissa akacemin Babana sun tafi wasan caca , raina ya ɓaci naji banji daɗi ba ace daga fara fitowarshi harya fara zuwa caca , ƙaraurawar kaina ta buga dan haka na manta da ɓacin rai nayi gida abina...
Washe gari ranar asabar tunda safe Mamy tazo gidanmu , kuma har yanzu Babana bai dawo ba , da murna na tareta muka shige ɗaki abunmu , bayan mun gaisa ta tambayeni na tuno abinda zan faɗa mata ranar laraba data zo ? Nace mata Eh , wayar na ɗauko na bata nayi mata dukkan bayani amma ban faɗa mata Dikko bane ba ,
Layin kawai ta cire daga cikin wayar ta bani wayar ta saka layin a jaka , nace da Allah Mamy wai da gaske kina da aure ? Tace ina da aure Sultana , nace keko me yaja miki bin mazan waje ? Bayan ga naki a gida ? Naga wasu ma basu samun ƙoshi ɗaya a bayan wasu shekaru { wanda basu da mazaje , basu da masu kwantar musu ko sauke musu sha'awarsu } kuma sunayin haƙuri keko naga kamar kin girtse da yawa...
Kici abincin gidanku kuma kici na gidan wasu , murmushi Mamy tayi tare da cewa aike yarinya ce bakya gane inda aka dosa gashi kuma kwalwarki tana tafiyar ɗimuwar rabin sa'a , murmushi nayi tare da cewa gaskiya ne inajin ƙaraurawar hauka tana bugamin duk bayan wasu "yan mintuka , Mamy tace da yanda idanuwanki da zuciyarki suke ganewa haka kanki ke ja da anyi alfahari dake , kauda kaina nayi gefe nace kwantar da hankalinki ina da ayyuka ne a gabana amma nasan komai zai warware ,
Mamy tace Allah yasa , zatayi magana kiran Hafsa ya shigo wayarta , ɗauka tayi tare da cewa Hafsa ya jiki cikin murna Hafsa tace Aunty ai jiki ya warke matar Dikko ta mutu , shegiya an gaji da ƙwaƙwar duniya an tafi anya mayyar matar nan baza tayowa mutane fatalwa ba ,
Mamy tace innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , ke waye ya faɗa miki ne ? Tace Mom ina taje ganinta safiyar nan tana can ma ta rasu amma tace Dikko yaji mutuwar saboda yana zaune kusa da ita tana bashi labarin abinda ya faru da ita bata gama bashi labarin ba ta zuge gilashi ta kama gabanta ,
Tou Allah ya jiƙanta ubangiji yasa mu cika da imani ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo amin , Hafsa tace yanzu tashin hankalina kuma ɗaya kinaji saura sati ɗaya a daura mishi aure , Mamy tace Hafsa bari anjima zamuyi magana , tana faɗin haka ta kashe wayarta ,
Wayoyin mutane ta fara kira tana tambayar da gaske ne matar Dikko ta rasu ? Abunka da masu jaha magana ta karaɗe kaf gari , kowa Mamy ta tambaya sai yace mata Eh ta rasu , kallona Mamy tayi tace kodai maganar mutane ta tabbata ? Nace me mutanen suke cewa ne ? Ƙasa² da murya tace kinsan kuɗin gwamna suna firgita al'ummar , ɗanshi kuma ya taso da ƙarfin dukiyar da ubanshi kanshi abun tsoro yake bashi ,
Anyi itifaƙi kaf gwamnonin nigeria babu mai kuɗinshi , danshi tunin duniya dama yayi kuɗinshi ba'a siyasa ya samesu ba , siyasa daya shiga kawai neman suna yasa ya shigeta amma badai kuɗi ba , to shi kanshi daya haifi Dikkon yana tsoron dukiyar shi , mutane cewa akayi wai ɗan nashi matsafi ne , dama tunda matarshi ta fara rashin lafiya akace ya tsafeta mutuwa zatayi ,
Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji , yayin da zuciyata tace ki rufe idonki ko sau ɗaya ne kiyiwa Dikko adalci Sultana , rufe idona nayi gaba ɗaya a halin Dikko babu ɗaya na zaɓe , Mamy tace da zan baki labari amma gaskiya tashi zanyi na sake dawowa , nace tou , har ƙofar gida nayi mata rakiya saida ta tafi na dawo gida ,
Tunda Mamy ta tafi nake saƙawa nake warware , me yasa Dikko ya zaɓi tsafi ? Me zaiyi da kuɗi dattin duniya da za'a koma ga Allah a barsu a duniya ? Tsikar jikina sai tashi takeyi ,
Har akayi kwana bakwai da mutuwar Sadiya ban daina tunanin maganar nan ba , Dikko kuwa ya kirani har bansan adadin kiran ba amma naƙi ɗaukar waya , daga ƙarshe ma kashe wayar nayi gaba ɗaya ,
Marecen yau kuwa ina ƙofar gida duk abin duniya ya dameni na rasa ina zan saka rayuwata naji sanyi , tunani ya dameni na babu gaira babu dalili , tsayuwar mota a gabana tasa na ɗago kaina da sauri dan a tunani na Baba ne , Dikko ne dan haka na tashi da sauri a daidai lokacin daya sauko daga saman mota , yana fitowa na taga ƙafa ina ƙoƙarin rugawa , a zuciyata nace an cuci sunna gaskiya ga gemu ga tambarin sallah wallahi ka ɓata kyanka ,
Ya kusa isowa inda nake na ruga da gudu ina wayyo Allahna......
29/09/2019
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 45
Tsaye yayi yana kallona , ni kuma da gudu nayi cikin gida har na kusa faɗuwa , a mamakince Dikko yabi Sultana da kallo a ranshi yana cewa ko lafiya ?
Mota ya koma ya gyara parking , yayi zamanshi ciki bai fito ba ranshi ɗauke da tunani daban ² , ga zafin mutuwar matarshi ga ciwon auren da za'a ɗaura mishi wanda rasuwar Sadiya yasa aka ɗageshi , ga iyayenshi sam² sun rufe idanuwansu akan aurenshi da Sultana...
Ya ɗan rame har yayi duhu saboda damuwa da tunani , a gajiye ya fito daga cikin motar ya nufi gidanshi , kafin ya ida shiga Baban Sultana ya faka tashi motar daga can gefe dan kar yayiwa Dikko laifi...
Dikko yana ganinshi ya dawo suka gaisa , bayan gaisuwa yace am dama ina san ganin wannan yarinyar ne , cikin damuwa Baba yace ta sake janka ne ? Fuska dai a murtuke babu fara'a yace a , a zanyi magana da ita ne kawai !
Baba yace tou Allah dai yasa lafiya , a ɗan rashin jin daɗi Dikko yace ba komai fa , shi baya so yayi ta nanata magana kuma anajinsa amma a kasa fahimta ,
Cikin gida Baba ya nufo zuciyarshi cike da damuwa , tunda ya shigo gida yake kwalamin kira kamar ranshi zai fita daga jin yanayin maganarshi babu daɗi a zuciyarshi ,
Da gudu na fito ina tambayar Baba lafiya , cikin faɗa yace me ya sake haɗaki shiga sabgar yaron can mara mutunci kuma ? Ɗan iskan yaro da baya ganin kowa da mutunci , ya raina arziƙin duk wani mai farin gashi dake doron ƙasar nan , fitinanne yaro dako bakin duniya baya tsoro ga rashin mutunci da masifa kamar kishiyar ɓarauniya...
A ruɗe nace ni babu komai , dakamin tsawa Baba yayi yana cewa babu komai inji waye ? Gashi can ya kafe mota ƙofar gida yana ɓacin rai duk abinda nace bana so sai kinyi Mamana kina so dai ki samin ɓacin rai idan na mutu kin huta ,
Hannuwa na duka biyu na ɗaga alamar bada haƙuri nace a , a Babana kayi haƙuri don Allah , dan bana so naga Baba yana fushi akan komai bare kuma ni daya ɗauki soyayyar duniya ya ɗoramin ,
Sassauta murya yayi cikin tausayi yace tou kije ki bashi haƙuri nidai bana so kina jawoshi faɗa uwar masu gida , nace tou Baba , a tsorace na fita ƙofar gida gabana sai faɗuwa yakeyi ,
Dikko yana tsaye ya jingina da mota , da gudu na isa inda yake na riƙe hannayen shi , na irin gani karka kasheni , kallona yayi cikin sigar so da ƙauna yace tou kin kama min hannaye ai gara ki riƙeni gaba ɗayana tunda abin har yakai ga riƙe hannu ,
Sakin hannuwan nashi nayi na ɗaga kaina na kallo cikin kwayar idonshi , wani irin kallo yayi min kwayar idonshi tana motsawa a hankali wanda idan baka iya saka ido ba baka gane motsi takeyi ,
Hmmm me yasa kika gudu da kika ganni ? Ko na zama dodo ? Bansan abinda yasa bana iya ma Dikko ƙarya ba amma da nauhi wannan kalma mai muni ta fito daga bakina ,
Tou tunda baki da abun faɗa ni zan faɗa nawa , shiru nayi ina saurarenshi , yace zanyi tafiya kuma bana tunanin idan na tafi zan dawo yanzu , bana so na shiga haƙƙinki da yawa dan ina baƙin ciki kiyi damuwa a rayuwa , ina so miki farin ciki bana so kiyi kuka haka kuma bana so ki kasance cikin damuwa ko ƙunci ,
Na baki daga yau zuwa jibi kwana biyu kenan ko ? Ya tambayeni , ina kallonshi banyi magana ba , yace tou kije ki natsu kiyi sharawa da zuciyarki shin kina so na ko bakya so na ?
Cikin yarinta nace ni bama sai nayi shawara ba gaskiya bana sanka , kallona yayi sosai yace karkiyi ƙarya An mata zakiyi nadamar hakan wata rana , nace wai ni ? Na ƙarasa maganar ina masa kallon rainin wayau nace Allah ya sawaƙemin ai baka cikin tsarin mazan da nake so , cikin damuwa yace .
Kina da matsaloli fa daban ² An mata , saurara samar da farin ciki a domin ɓatawa wani ba dai² bane , haka zafin murmushi a yayin da wani yake baƙin ciki da takaici hmm baya da amfani , karki damu kawai cewa zakiyi ina sanka , shi kenan fa babu wani wahala , uhum kana ba kanka wahala kaji , ince ina sanka ? Allah ya sawaƙemin ,
Murmushi Dikko yayi maicin rai yace tou ni kuma na san a cikin kwanaki biyu da wannan taurarin idanuwan naki zaki zamo masoyiyata babu jayayya , zaki zo ki rumgumeni , numfashinki zai shiga kwalwata, zaki kalli idanuwana , ina sanka , idan har baki faɗa kina so na ba , shiru yayi yana kallon fuskata , zuwa wani lokaci yace sai kin faɗa , yana faɗin haka yayi tafiyarshi ya barni a wurin...
Cike da damuwa na koma gida yayin da zuciyata ke shawarta ta ince ina san Dikko wata zuciyar tace karki sake ki faɗa ko zaki mutu ki barshi kawai kuje a haka , kina mace kice kina san namiji haba ai kinci ƙasa ,
Lokacin da kwana biyu ya cika zuciyata ta gama tabbatarmin da bata san Dikko , dan haka kuma na yanke shawarar sanar dashi bana sansa yayi haƙuri ,
Da daddare bayan yazo ya aiko aka kirani dan har yanzu ban kunna wayar ba tunda na kashe ta ban sake buɗewa ba , bayan na fita muka gaisa dashi , bayan gaisuwa yace ina saurarenki , nace gaskiya ansar dana baka tun farko itace har yanzu ,
Shiru Dikko yayi , bayan wani lokaci yace , wannan rana ta kasance min ranar juyayi ne , bana fatan wannan ranar ta sake zomin , ranar ƙarshe kenan banda wani ƙwarin guiwa , An mata ce kaɗai abin alfaharina , umm abinda bana so ya kasance duk lokacin dana runtse idanuwana nakan iya ganin kyakkyawar fuskarki , bansan mace ba sai a kanki idan har na taɓa san wata mace a rayuwata to kece An mata ,
Zan tafi idan har naci gaba da ganinki to zan ɓata miki , kiyi haƙuri bazan sake kiranki ba , haka ma zuwa ba zaki sake ganina ba An mata , kin daɗe kina ƙonani inajin kamar na rasa wani abu , me zanyi ? Bazan iya koda dariyar ƙarya ba , jawoni yayi ya rumgumeni duƙowa yayi ya kwantar da kanshi saman kafaɗa ta , cikin wata irin murya mai tsayawa a zuciya yace sai wata rana , ki yafemin don Allah karki riƙeni zan fita daga rayuwarki dan ina so kiyi farin ciki , zan tafi ki huta koda kuwa ni zan shiga halin damuwa ,
Bayan wani lokaci ya ɗago ya kalleni , cikin kallonshi mai ɗaukar hankali yaɗan ɗauki lokaci yana kallona sannan yazo dai² bakina lumfashin shi yana fitowa saman fuskata , gashin gemunshi yana shafar dai² saitin bakina , lokaci guda jikina ya canja tsikar jikina ta tashi ban taɓa jin irin wannan yanayi ba , bafa haɗa bakinmu yayi ba , daga waje ya sunbace ni wani abu naji ya shiga jikina da gudu saida ya gama zagayawa ya dawo zuciyata ya shiga da ƙarfi , ajiyar zuciya na sauke yanajin nayi ajiyar zuciya ya sakeni da sauri daga jikinshi yaɗan turani baya yace ki tsaya da kyau karki faɗi , zan bada saƙo Umar ya kawo miki kafin in wuce ,
Kasa magana nayi nabi shi da kallo da sauri ya shiga mota ya bar ƙofar gidanmu da gudu , har ya fita daga anguwarmu ina tsaye a wurin daya barni , yana ɓacewa na kyalkyale da dariya , na zabgaga wani irin ihu , daga cikin gidanmu Zainab ta fito da gudu tana tambayata lafiya ?
Sai dire² nakeyi kamar anyi ma doki allura ƙarfi , Zainab tace wai miye yake faruwa haka ? Goge hawaye nayi nace har yanzu na kasa yadda da wannan , Zainab tace miye ne kika kasa yadda dashi ? Nace masoyina ya faɗamin dukkan na kasunsa , shi da yace zan rungumesa sannan na faɗa masa cewa ina sanka DK ,
Zainab tace waye DK murmushi nayi nace baki sansa ba , Zainab tace tou ki faɗa masa kina sansa mana , nace ke jinan ya nunamin yatsansa yayin da yake ƙalubalanta ta cewa a cikin wasu kwanaki zance ina sansa , murmushi nayi tare da rufe idona , nace kamar dai yadda yace naji ina sansa , ƙara ɗaga murya nayi ina sanka mutumi na , ina sanka , Zainab tace to me yasa baki faɗa a gabansa ba ? A , a , a , a , idan na faɗa masa tou zaiyi ta jamin ƙafane har abada , Zainab tace zakiyi duk abinda kike so amma kuma idan kika makara a soyayyarshi fa ? Nace sam ² ki rabu dashi kawai yayi kuka na wannan daren nasan bazaiyi zuciya ba da safe zai sake zuwa , ni kuma yana zuwa zance barka dai DK idan ba tare dakai ba ina ne zanje .....?
Cike da farin ciki na shiga gida , Zainab ta rufomin baya , alwallah nayi na shige cikin ɗakina ina farin ciki ,
Dikko kuwa yana isa gidanshi wanka yayi , bayan ya shirya ya ɗan faffaka abu mai mahimmanci ba kaya ya ɗauka ba , wasu takaddu ne kawai ya tattara , layinshi ya cire ya ajiye , dube² yayi na irin banyi mantuwa ba kuwa ? Sannan ya fita daga cikin ɗakin ,
Wajen da aka tanada dan ajiye motoci ya samu Umar kamar yadda yace su haɗu , Ashiru a gefe sai Al ' Ameen , duk gaisheshi sukayi cikin girmamawa , bai ansa ba , makullin mota ya miƙewa Umar tare da nuna mishi mota yace ka kaima yarinyar nan akwai kuɗi a but in tasha mai , Umar yace mai gida wace yarinya ? Yarinya nawa kasan ina tare da ita ? Haƙuri ya bashi tare da cewa tou ai naji bakace An mata ba , murmushin baƙin ciki Dikko yayi a zuciyarshi yace tace bata so na , kuma fa ba'a soyayya dole Allah ma yasa bansha wahalar shawo kan kowa ba dasai nasha wahala na shawo kan iyayena tace bata aurena , gara kawai na haƙura nayi nesa da rayuwarta na barta ta huta , Umar kallon motar yayi Al ' Ameen ma ƙwalalo idanuwa yayi cikin tashin hanki yace mai gida wannan motar zaka bata ?
Cikin ɓacin rai yace Ey ita zan bata , cike da hassada yace ko ka manta nawa ka siyota ne ? Dikko yace kila babanka ya nemomin kuɗin shi yasa na manta , dan wani irin haushin Dikko yakeji kuma Dady yace idan yayi masa wani abu bai yafe masa ba , Al ' Ameen ya kalli motar ya ƙiyasta kuɗinta tou ai wallahi kaf garin katsina wannan motar ita ɗaya ce tak , bazai manta ba lokacin da Dikko ya siyo motar wallahi ganinta ake zuwa yi ana mata hoto ko wata motar batayi ba kuma Dikko bai taɓa hawanta ba , shine zai ɗauka ya bawa karuwa ? Kai amma yarinyar nan ta shanye mai gida da yawa , motar miliyoyin kuɗi haka ?
Kaf ma'aikatan gidan nan suka haɗu suna ma Dikko addu'a Allah ya tsare , wallahi game da kyauta dai Dikko baisan darajar kuɗi ba , yana kyauta maisa mutum ya kasa gane bacci yake ko idonshi biyu ? Bayan ya gama sallamarsu ya shiga mota Ashiru yaja suka bar gidan ,
Al ' Ameen kuwa sai ƙara kallon motar yake hada kukan baƙin ciki ina ma ɗiyar "yar uwarshi ta samu wannan mota ? Mai gida baisan abunshi haka nan yake neman kuɗin baisan darajarsu ba wallahi , yo wannan mota ai daya sani siyar da ita yayi ya sayi gidaje masu kyau kawai ya ɗauki mota ya ba shegiyar yarinyar da Z bata tantancewa , lallai zaima Yayarshi waya idan har Mai gida ya dawo nigeria Haneefa taje Abuja wurinshi...
Daga gidanshi gidansu ya wuce kai tsaye , danyi musu sallama , momy tace idan an ɗaura aure matarka zata isko ka , cike da biyayya yace tou , bedroom ta koma ta ɗauko maganinshi tace gashi nan saura idan ka tafi ka yadda shi , ansa yayi ya saka a aljihun wandoshi , addu'a tayi mishi tare da mishi fatan alkairi harya fita , Dady kuma baya nan ,
Cike da soyayya tabi bayanshi da kallo , haka nan taji dai bari ta mishi rakiya , bayanshi tabi har inda ya ajiye motarshi , saida zai shiga mota yaga Momy ta biyoshi , kallonta yayi yace inzo ? Murmushi tayi tace a , a , kusa dashi ta matsa tace karka zo rakiya nayi maka , taci gaba da mishi addu'a Allah ya tsare tana ɗaga mishi harya shiga mota suka tafi ,
Tun a mota ya goge hotunan Sultana , bayan yayi musu kallon ƙarshe dayi mata addu'a Allah ya bata miji na gari , ya kuma sa ta yafe masa karta riƙeshi a zuciyarta , shi kuma Allah ya bashi haƙuri da dangana akan ta...
Bayan ya gama goge ²nshi da addu'a shi ya anshi tuƙin motar dan gani yakeyi Ashiru ma baya sauri , tuƙin ganganci da wauta Dikko na fama da iskanci cike da kwalwarshi , ga raini ga rashin ganin mutuncin mutane amma yana da tausayi da taimakon wanda baya dashi ,
10:09pm suka isa kano , anan aka canja abokan tafiya , saida jirginsu Dikko ya tashi Ashiru ya juyo katsina bai kwana ba , sauka lafiya mai gida Dikko Allah ya tsare....
Cikin farin ciki na wayi gari kuma nayi alƙawari yau zan faɗawa Dikko nima ina sansa , duk wanda ya ganni yasan inajin daɗin wannan rana , saida hantsi ya ɗaga na sheƙaƙa wanka na , naci gayuna dan nasan yau Dikko yayi kwanan haƙuri nasan ya ƙagara gari ya waye zai fara zarya ganin dokuna ,
Cike da farin ciki nayo ƙofar gida na zauna ina jiran isowar jarumina , har lokacin zuwanshi yazo ya wuce babu Dikko babu labarinshi , gida na koma na ɗauko wayata na kunna , bayan ta gama kunnuwa na fara neman layinshi , amma dai inajin maganar ɗaya ce kodai wayar tana kashe ko kuma babu kuɗi a wayata ,
Gida na koma nasa aka dubamin ko banda kati , kowa sai yacemin akwai idan nace nawa ne sai su kasa lissafomin , Babana na bashi ya dubamin yace akwai kuɗi , nace nawa ne Baba ? Yace dubu ɗari biyu ne , nace tou kiramin wannan lambar na ƙarasa maganar kamar zan faɗa masa ,
Duba sunan da akayi saving in number yayi yai murmushi tare da cewa iye Mamana ta fara soyayya ya ƙarasa maganar yana kallona kuma cikin zaulaya yayi maganar , cikin jin kunya na zauna kusa dashi ina dafa kafaɗarshi nace aini bana soyayya , yace ai ba wani ne ya bani labari ba nine na gani da idona , tou me yasa kace haka ? A dai² lokacin da yacemin wayar a kashe take ,
Cikin rashin jin daɗi na anshi wayar kaina ya fara min ciwo haka nan naji ɓacin rai ya lulluɓemin zuciya , cike da damuwa na fito tsakar gida , amma sai naga gidan kamar yana juyawa , Baba kuma yana min magana daga bayana wallahi kwata² banajin abinda yake faɗa ,
Wai ance ana kiran Sultana , da sauri na fara kakkaɓa idona daya cika da hawaye inayin dariya cikin farin ciki , nayi ƙofar gida da gudu Babana ya fito da sauri ya biyo bayana yana lafiya ? Turus na tsaya ganin Umar , nayi tunanin zanga Dikko babu shi , sake cika da hawaye idona yayi nace ina yake ? Miƙomin makullun mota yayi a dai² lokacin da Baba ya fito yace gashi yace a kawo miki kuma akwai kuɗi a but wai kisha mai , sai ki bani tukuwici in wuce , nace tou ina shi Dikko yake ya aiko ka ? Umar yace yayi tafiya ,
Kallona Baba yayi yace waye ya kawo wannan motar ? Hawayen da suka taru a idanuwa na suka samu damar gangarowa daga saman kumatu na , da sauri na juya na rumgume Babana ina kuka , ɗagoni yayi daga jikinshi yace wai miye ? Waye ya baki wannan motar ?
Cikin kuka nace Dikko ne , kallon motar Babana yayi sannan ya kalli Umar yace wai wane Dikko ne ? Da hannunshi yayi mishi nuni da doki , kallona Baba ya sakeyi yace meke tsakaninki dashi ? Goge hawaye nayi na anshi makullin na buɗe but in motar , bandir in "yan dubu² ne guda goma , guda biyar na ba Umar nayi godiya , shima godiya yayi ya wuce abunshi...
Umar yana tafiya Babana yace wai Mamana ke ya akayi ya baki wannan motar ne ? Nace shi yaga dama ya bani ita ba roƙarshi nayi ba , kallon motar Babana ya sakeyi yace aiko wannan motar bata hawuwa wurinki garin nan saidai a siyar da ita kuma duk ma garin nan bana tunanin akwai mai siyenta shima ƙuruciya tasa ya siyeta , { ba rashin kuɗi baba yake magana ba da yace baya tunanin akwai mai siyenta } babu dai wanda zai ware wannnan kuɗaɗen ya siyi wannan motar kawai dan dai ya hau , murmushi nayi kaɗan nace baza'a siyar da ita ba gaskiya ,
Baba yace ki hauta ace miki wa Mamana ? Nace idan na hauta kaji yadda za'a kirani , tou ina zaki ajiye wannan mota ? Nace gidan dokunanshi zata riƙa kwana ... Allah ya tsare Babana ya faɗa , na ansa da Amin ,
Da kaina nakai ma masu gadin gidan ajiyar mota , suma kansu mamaki ya kamasu ya akayi motar mai gidansu tazo wurina ? Saboda kowa ya sani tashi ce shi ɗaya yake da ita duk kaf cikar faɗin garin katsina , dan anyi surutun motar sosai a lokacin daya siyota kuma har yanzu ba'a gama ba , wannan ansa basu da mai basu ita....
Na shiga cikin ɗimuwar rayuwa nayi kukan rashin Dikko nayi harna gode Allah , na rasa ina zan saka kaina naji daɗi , "yar jakar daya bani a lokacin da muka kama shago dasu Amisty na ɗauko na zazzage , cingom in daya bani nashi na ɗauka nayi ta ci ina haɗiyewa , saida naji zan mutu na haƙura na tattara sauran na mayar ,
Na faɗawa iska ina san Dikko bansan adadin kalamai nawa suka fita daga sautin bakina ba , baida wani amfani dan Dikko dai baya nan kuma bazaiji ba , nayi kukan rashin Dikko har tsawon sati ɗaya ina zubar da hawaye duk nabi na rame na susuce , na kira wayarshi kullum dai maganar ɗaya a kashe , duk lokacin dana kira wayarshi naji kashe sai nayi kuka kuma bazan daina kukan rashin ka ba Dikko har abadan duniya....
Bayan wata ɗaya ,
Abubuwa da dama sun faru , Babana ya warke tas kamar bai taɓa wani rashin lafiya ba , su Amisty kuma an ƙaro iskanci domin dai suma a anguwarmu suka sayi gida ,
Ta siyi motar hawa ta baro iyayenta tana zaman kanta , Nana ma ta tashi daga gidanmu ta koma nasu Amisty , Saude A ` i Zalifa Karima ma duk sun tare a can , Hafsa ma nan take yini amma bata kwana , itama Asma'u anyi mata register kuma suna faɗa cewa yanzu zanga yanda ake shugabar duk wani ɗan iska daya kwana a katsina suna da masaukinshi , idan inajin nima wata ƙwaro ce na kafa manya ²n karuwai kamar nasu...
Lokacin da naji saƙon su Amisty dariya nayi , bana san komawa ruwa dan naji kwata bana sha'awar karuwanci dan zuciyata bata da lokacin sauraren kowa saboda Dikko yabi ya mamayeta da soyayyarshi , kafin inyi wani nazari na yanke hukunci naji gam × ³ a cikin kaina , kamar wacce aljannu yake shiga jikinta haka jikina ya fara fizge² idanuwana sunamin zafi sosai , kaina ya juye , nace tabbas zasu san nawa ba kalar nasu bane mu zuba mu gani dani dasu.
A wannan halin Mamy ta sameni , bayan mun gaisa ta fara rattafomin bayani akan Baban budurwar Dikko , wacce mukayi faɗa da ita a mota.....
30/9/09/2019
*JAMILA MUSA....*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 46
Tsare Mamy nayi da ido na kasa magana duk saida ta gama buɗemin komai ta ƙare da cewa harma ta gayyato shi zaizo katsina jibi , har ta gama kallonta nakeyi saida takai nunfashinta ƙarshe nayi murmushi amma har yanzu idona akanta yake , kuma banyi magana ba ,
Mamy taci gaba da cewa tou ya kike ganin za'ayi idan yazo ? Zance gaki ko kuwa ? Shiru nayi na ɗora wayata a saman goshina na rufe idona na dama ina nazari ,
_Kije abunki amma duk abinda zaki kiyi na hankali da tunani ,_
_Ni bana zarginki har abadan duniya anma dan Allah karki sake ki bari zuciya da sharrin shaiɗan yasa aimin wasan danbe dake , ni ɗaya tak na isheki bana gajiya kuma bazan taɓa gajiya dake ba har ƙarshen numfashi na,_
_Jarumi ɗaya tak akeyi a ƙarni nine jarumin wannan lokaci , Dikko jarumin maza ne kuma ke da kanki zaki faɗa kije ki dawo ina nan ina jiranki....!_
Hawaye ya gangaromin daga cikin ido nace a ina kake jirana inzo ....? Murmushi Mamy tayi tare da cewa soyayya ? Shiru nayi ina hawaye , dariya tayi sosai tace har kin bani tausayi Sultana uban waye ya shiga zuciyarki har kike kuka ?
Saida nayi shashshekar kuka sannan na kalli Mamy da ido ɗaya nace ni kike tausayi ? Tace Eh ai soyayya babu abinda ke cikinta sai wahala da dana sanin da bashi da amfani , murmushi nayi mai ƙuna nace gara ki tausayimin dan a halin yanzu banma san a babin da nake ba ,
Yana so na har yanzu ko ya goge ni daga zuciyarshi banma sani ba , dama yace idan bana sansa zai tafi kuma bazai sake dawowa ba , yazo a lokacin da bansan waye shi ba , kuma ya tafi ya barni a dai² lokacin daya koyawa zuciyata soyayyarshi , bazan gaji ba , ba kuma zan daina faɗa ba har kalma na ƙarshe a duniya , ina sanka ׳ Na ƙarasa maganar ina goge hawaye ,
Tsoki Mamy tayi tare da cewa yanzu kinji abinda na faɗa miki , sai magana na gaba , akwai wani mijin ƙawata yaga wata anan anguwar yana so ya ɓata dare ɗaya tak da ita , tou na biyota bayan nayi bincike sai akacemin matar aure ce , dana faɗa mishi sai yace min dama matar auren yake nema shin zaki iya kawo mishi ita ? Akan wane farashi ? Na tambayi Mamy , tacemin 50k nace kai haba zunubin fa akwai girma , yadai ƙara wani abu...
Mamy tace Sultana haka zai baki , kallonta nayi ido cikin ido nace gaskiya ƙarya kikeyi ke kika rage kuɗin da za'a bani , Sultana ni nake ƙarya ? Nace yo wace ce ke da baki ƙarya ? Mamy tace dama naga kin raina ni ko girma na baki bani ? Murmushi nayi da gefen baki na , nace babu wanda ya kawoni bariki ni na shiga da kaina , bana ƙarƙashin kowa ina bisa ƙarƙashin ikon zuciyata ne , banda uwar ɗaki haka kuma banda ubangida , bana nema wurin kowa dan kowa baida abin bani , wannan harkar ra'ayina ne yasa na shiga badan ra'ayin kowa ba , abuna yana jikina naki yana jikinki , tayuwu ke ki bada naki a baki 1k wannan ra'ayinki ne kuma kinji kina iyawa ne , niko babu dalili na buɗewa namijin banza ƙafata ya hauni ya sauka ya bani kuɗin da bazasu kashemin kwarnafi ba ,
Ban kawo ki bariki ba baki kawoni ba ,baki koyamin ba haka nima ban koya miki ba , a rana tsaka muka haɗu kin gama gogewarki nima idona biyu kika ganni ba bacci nake ba , tuni na bushe fitilar idona , banda Aunty banda Yaya banda Mama haka kuma banda uwar ɗaki a bariki wallahi , ta yuwu ma kila namiji ɗaya ya nemu a tare yana gamawa dake ya jawo ƙafata , wane girma gareki a wurina ? Sana'ar fa iri ɗaya ce , uwar data haifeni ma data ga bata iyawa kayanta ta tattara ta kama gabanta tou bare fa ke banzar bazara kashi a masai , na faɗa kuma zan sake maimaitawa idan bakiji ba kiji , idan kuma kin manta ki sake fahimta ,
Matar aure bana kawota a dubu 50k wallahi idan dai yana so tou dubu ɗari biyar zai bani nayi miki alƙawari kuma ki mishi albishir a cikin sati ɗaya tak zan kawota babu asiri babu bori , idan haka yayi miki to idan bai miki ba a daina cinikin dan bana san rainin hankali da yawa....
Shiru Mamy tayi tana kallona ni kuma naci gaba da gwada layin Dikko , can kuma tace tou za'a baki rabin kuɗin idan an gama sai a cika miki , ba tare dana kalleta ba nace ni bana da sasshen jikin mutum , Mamy tace kamar ya kuma ? Nace tou kamar yadda zaki bani rabin kuɗi ! Me zan ciro na fara kawo mishi ? Mamy tace Sultana zan baki rabin kuɗi idan aka gama na cika miki , tsoki nayi nace kinga da Allah ki tashi kina ɓatamin magana a banza , kije idan kun shirya ansar mace kuzo da dubu ɗari biyar na gama magana....
Jakarta ta buɗe ta ɗauko dubu ɗari biyu tace gashi zan cika miki anjima , ai banma da lokacinta bare kuma tayi tunanin naji abinda tace , can kuma tace kin cika kafiya gasu bara na ranta cikin kuɗin ƙawata idan naje banki na cire ita saina bata , da gefen idona na kalli kuɗin , miƙomin tayi na ansa na tusasu fes sun cika , hoton matar ta turamin a wayata tace gata nan kuma bama so sai tazo tayi ta wani noƙe ² nace inki so kije abunki ,
Har zata fita nace , maganar mai zuwa katsina kuma jibi akwai Hamida akwai yaran gidan Baba ƙarami ki taimakamin suma su shigo sahunmu tafiyar zatamin dai² , Mamy tace baki da damuwa , godiya nayi mata ta wuce abunta , ni kuma naci gaba da nazari akan hanyar da zan fiddo matar aure a kaita wurin mijin da ba nata ba kuma banma taɓa magana da ita ba ina dai ganinta tana wucewa !
*America...*
Mai gida Dikko ne kwance a gefen gado , ya ƙurawa waya ido ko kiftawa bayayi , daga can ƙarshen gado kuma amaryace sanye cikin wata irin tsadajjiyar alkebba , mutum biyar suka kawota kuma kwanansu biyu yau suka juya bayan sun ƙara gyarewa ango amarya suka shiryata cikin shiga ta alfarma da ɗaukar hankali , bayan tafiyar "yan rakiyarta ta dawo ɗakin da take tunanin nan ne ɗakin mijinta ta tsareshi da kallo kamar kwarton namiji yaga wawan zama..
Tafi minti 15 zaune bataji yayi magana ba , dan haka ta tashi tsaye ta zare alkabbar ta ajiye a gefen gado , cikin gogewa da buɗewar ido ta fara tafiya cikin natsuwa ta zagaya inda Dikko yake kwance.
Kafin ta iso Dikko ya tashi da niyar shiga toilet , da sauri tasha gabanshi tace haba ina ne kuma zakaje ne bayan kayi wanka , kallonta yayi sannan yace zan tsaya kiyi ta kallona ne kamar banda aikin yi ne ? Haba Yayana aiko kaine kake da aikin yi a gabanka , nuna kanta tayi daga sama har ƙasa tace mai wannan zundumemiyar mace inashi ina bacci a daren nan ? Ga kallo kuma ga aiki , kasan yanzu ba'a sake da miji mai mummuna ma ta tattala abinta ina gani mai tsadajjiyar fuska da ƙira mai ɗaukar hankali kamar ka ? Ai banga ta zama ba aiki ya sameni harsai na goge tambarin ɗiyan ɗan caca a zuciyarka...
Wace ce ɗiyan ɗan caca ? Dikko ya tambayeta yana mata kallo mai nuni da zaici ubanta ! Haba Yaya DK kana tunanin bansan komai ba ? Kaf labarinta a hannuna yake , me zakayi da wannan yarinyar ? Yarinya mara tarbiya , marar asali jahila da bata gane komai sai karuwanci..
Murmushi Dikko yayi maicin rai dan duk duniya ya tsani a famo mishi ciwon tunanin An mata , haka kuma ya tsani a soketa , cikin ƙunar rai yace ni na sanki tun baki san kanki ba , haka kuma nasan waye ahalin babanki ciki da waje , idan har zan duba girma da tsatson ahali da tarbiyar iyaye ke ko matsayin mai aikin gida na baki ba , da cancanta aka bimin wurin auren da aka yomin ke kinsan baki kai cikin layin matan da zanbi hanya ɗaya dasu ba , An mata bata sanki ba kuma baki gabanta dan bata san da zuwanki ba , tana can tana rayuwarta bake ba ko ni bata da lokacina bana san munanan kalamai yana fitowa daga bakin ki akanta , ba ƙoƙarin gogeta zakiyi ba domin bata gogowa har abadan duniya a zuciyata , idan dai zaki iya kiyi ƙoƙari ki kafa soyayyarki a zuciyata shine abinda zakiy farko kenan ,
Sassauta muryarshi yayi sannan yaci gaba da cewa , tana da tarbiyya , nine zan bada wannan shedar , asalinta kuma yana tare da asalina , tabbas bata gane komai sai karuwanci , nine na yanka mata tikitin karuwanci nace ta koyo dan tamin riƙo da bazan taɓa tunani wata mace a duniya ba sai ita , ta shafe kaf illahirin zuciyata , tabi cikin kwalwata da jinin jikina , yarinya ƙarama mai tafiya dai² da irin rayuwar da nake so , zan bata labarin ki , kuma ince kina mata gori itama ta goranta miki tunda dai uba baifi uba , sa'arki ɗaya ma da mamanki ta haɗo da momy ai da ina ganinki sai nayi amai...
Goge maganar tayi dai tare da nunawa Dikko ya bata haƙƙinta , shareta yayi ya shige toilet, bai daɗe ba ya fito da alama alwallah yayo , itama shiga tayi tayo alwallah ya gabatar da komai kamar yadda yayi a daren farkonsu da Sadiya cikin natsuwa , bayan sun gama suka koma gado anan Dikko ya farke sabuwar amaryarshi kuma ya sameta a cikakkiyar budurwarta ,
Yayi farin ciki dan a tunaninshi yadda take ta nuna haɗama tana zalama baiyi tunanin zai sameta a cikakkiyar mace ba , komai yaji gaskiya amma Dikko yace gishiri yayi yawwa , { tasha kayan mata sosai } dan shi Allah ya bashi ilimin gane tsurun mace idan ta haɗa da "yan dubaru ya sani , amma wallahi An mata itadai ta dabance...
Sai kukan kissa matar Dikko keyi , cikin nuna tasha wahala , Dikko kuwa ɗan jirgiwa yayi ya kifar da kanshi saman katifa tunanin yadda darenshi ya kasance da Sultana yakeyi , wallahi ya cuci budurcin An mata daya karɓa ta ƙarfi da yaji , ƙaramar yarinya da ƙananan shekaru ya saki ƙarfinshi ya haɗa da magunguna yaje mata a gigice , bata taɓa gani ba kuma bata taɓa ji ba sai a gareshi , me yasa ....?
Me yasa? Me yasa haka ta faru ? Dole kice bakyasan Dikko saboda Dikko ya zama mugu a wurinki , An mata da kinyi haƙuri kin bani dama a karo na biyu da kinyi alfahari dani , da bazan barki kiyi kuka ba , bazan barki kiyi baƙin ciki ba , shi kenan kin fita a hannuna zaki tafi wurin mai rabo ya ɗaukeki ya dasa wasan sa daga inda na tsaya...
A hankali ya lumshe kyawawan idonuwanshi a bayyane yace Allah ya sanyaya miki zuciyarki , a tunaninta da ita ake tace amin mijina , har yanzu idonshi a rufe yace kin yafemin kenan ? Ummm ai bakamin komai ba ma , kenan babu zafi ? Umm umm , to me yasa ki key kuka ? Ba komai , sai yanzu ya gane bada Sultana yake maganar ba , buɗe idonshi yayi da sauri ya ganshi kwance akan sabuwar amaryar shi , kuma "yar uwa a gareshi...
Ko tsakar dare dana farka haka naci gaba da gwada wayar Dikko wanda ya zamarmin kamar hauka dan ƙaranci ban kira wayarshi ba a rana na kirashi sau 200 da wani abu ,
Ina zaune tsakar daren nan ina ta aikin neman wayar naji maganar Baba ƙasa² daga bayan ɗakina dake daga tagar ɗakin sai a fice zaure a fita ƙofar gida , bana iya jiyo abinda Baba yake cewa saidai naji maganar Amisty cikin shagaba tana cewa nidai Dady don Allah... Ta ƙarasa maganar kamar tana kuka !
Da sauri na haska fitila na duba agogo naga 3:45am cikin sauri na miƙe na sake matsawa da kunnena jikin window naji shin da gaske Amisty ce ko kuwa dai wata ce daban ! Wallahi Amisty ce dan duk duniya babu mai irin wannan muryar sai ita , me suke cewa ? Me ya haɗa Amisty da Babana a wannan salasunan daren ? Me ke tsakanin Amisty da Baba ? Duk wannan tambayar banda ansoshinsu nayi yunƙurin yin wani abu tunani na ya tsaya cak domin kaina ya riga da ya juya...
Buga kaina nayi da ƙarfin bala'e a jikin bango na kurma wani irin ihu duk wanda ke cikin gidan saida yayo waje saboda ƙarfin ihun da amonshi ni kuma na fito da gudu nayo hanyar fita , babu Amisty domin tuni ta fice , ina ƙoƙarin fita Baba ya riƙeni da ƙarfi yana lafiya ? Fizge ² na farayi na kwace nayi waje , da gudu ya bini ya riƙoni nafi ƙarfin riƙonshi domin na sake zuƙewa daga riƙon da yayimin , cikin tashin hankali zugar gidanmu suka yo kaina dakel suka kaini ƙasa suka daddanne ni na birkice gaba ɗayansu na watse su , na yanki santa , yayuna maza suka taimaka aka kamani aka mayar dani cikin gida ,
Kowa tambayar abinda ya sameni yakeyi ? Murmushi nayi mai ciwo na kalli Baba nace ina ka ɓoyeta ne ? Cikin rashin fahimta yace wa ? Kafi kowa saninta me takeyi a gidan nan a wannan lokacin me tazo yi me take nema...? Baba yace wai wace ce ? Ga sunan Amisty a zuciyata amma ƙiri² ya gagara na faɗa a baki na , nace ita mana ita wace ce ? Kai ji nan na nunashi da ɗan yatsa nace tana ina karfa ka ɗaukeni mahaukaci nasan abinda nake ina ka ɓoyeta ne ?
Amma Baba sai ya fara tofa min addu'a yana cewa aljannu sun kama uwar masu gida , a taimakamin da addu'a , inaji ina gani Baba yasa aka mayar dani mahaukaciyar ƙarfi da yaji , kowa yayi ta tofamin yawu , banda yanda zanyi dole nayi shiru amma wannan abun bai gogemin daga zuciya ba kuma saina bi salsala na gano abinda ke tsakanin Baba da Amisty , maganar Mamy ta dawo min a kaina kamar yanzu take faɗamin maganar...
_Gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zaman *KWARATA...*_
Lallai akwai alamar tambaya a wurin nan amma waye zai fiddo maganar daga cikin zuciyata ? Waye ? Waye zai taimakeni ne ? Wai wace ce ni ? Anya kuwa ni mutunce ? Mutane kuwa suna gani na ? Wai meke damun rayuwata ? Me ke damun kwalwata ? Wannan wane irin masifa ne ? Wace irin rayuwa nakeyi ? Ina mahaifiyata wai me Baba ya ɗaukeni ? Me nene ׳ na ƙarasa maganar ina ɗaga muryata wanda ina tunanin duk mutumin dake anguwar nan yaji irin hayagagar da nakeyi...
Fashewa nayi da wani irin kuka nace tabbas ko wace ce ni da sanin wace irin rayuwa nakeyi amsar tana wurinki , kuɗin da Mamy ta bani na ɗauko na irga suna nan yadda ta bani su , maidasu nayi na aje , amma a zuciyata nayi alƙawari zan bautata mata tiƙuru kuma zan bata girmanta kamar yadda take so zan nemo matar nan kuma zan kaita zan bawa Mamy kuɗinta kuma zanci gaba da farauto mata duk wanda take so adalci ɗaya zatamin ta warwaremin sirrin rayuwata wannan shine kawai mafita....
Gari na waye nayi wanka yau ko inda Babana yake ban kalla ba kuma ban gaishe shi ba , makulin mota ta na buƙata ya bani amma sai yacemin wai anci motar a caca , kallonshi nayi nace ni bansan caca ba mota ta kawai na sani kuma sai ka biyata ,
Mamana ni kike cewa saina biyaki mota ? Kaine ka siyata ne ? Ai ko ban siya ba naci albarkacin haihuwarki da nayi , ka maidani ciki idan kaji munin maganar amma sai ka biya wannan motar babu gudu babu ja da baya kuma ba abinda ya dameni na baka daga yanzun nan zuwa bayan sallah isha'e ... Ina faɗin haka nayi waje abuna na barshi ta tagumi...
Ina fita na shiga maƙota na nuna hoton matar da Mamy ta turomin a wayata nace da Allah ina neman gidanta , matar tacemin lafiya dai ko ? Nace lafiya qalau gwamnati tace a taimakawa masu ƙaramin ƙarfi wanda suke shan wahala a gidan aurensu , an ɗauko jaddawalin sunan ko wace macen aure da ƙaramin katin hotonta , sai naga ita kamar tafi kowa shan wahala shine nake so ita a taimaka mata da yawa , mata da kuɗi sai Allah kuma nayi haka dan in rubzata rami itama , ta haka zanji wane irin hali matar take nasan komai nata kafin na isa gidanta , !
Murmushi matar tayi tare da ɗaukomin kujera na zauna tace amma Sultana kunsan kuna da hanyar taimako shine mu ba'a saka sunanmu ba ? Jakata na zuge na fiddo damen "yan dubu² nace kin gansu nan kowa da sunanshi ai bansan kuna buƙata ba , itama banda tabbacin da zataje ko bazata ba ,
Tace zuwa kai , muje na rakaki gidan ta amma don Allah nima kisa a rubuta suna na don Allah , nace baki da matsala , saman ƙyaure ta ɗauko hijabinta tana ba yaranta umarni karsuyi mata ɓarna idan Babansu ya shigo ta shiga maƙota baza ta jima ba ,
Ta gaban gidan Amisty muka wuce gaba ɗayansu suna ƙofar gida hada Asma'u an saka kujeru na roba Amisty kuma tana ta tofi da hayaƙin sigari , yayin da wata tantiriyar "yar iska ke shan shisha tana murza hayaƙin cikin ƙwarewa da gogewa a cikin harkar ,
Har mun wuce naji bana iya haƙuri na dawo da baya , dai² Amisty na tsaya na ciro sigarin daga cikin bakinta na kasheta a saman goshinta , wata irin ƙara tayi saboda zafi ta riƙo hannuna na , da hannun damata na riƙe hannunta saboda dana haggun na kashe mata tabar sannan nace na rantse da Allah duk ranar da hasashena ya zamo gaskiya yadda na murje wannan sigarin a goshinki haka zan murje miki rayuwa..
Gaba dayan su sukayo kaina suna kee.... Nace heeee ku saurara na kaso daku sannan ku ɗauka domin yanzu babu sauran muradin ɗaukar fansa a zuciyata ina neman rayuwata ne amma idan kuka bari na ɗauki zafi anbaliyar wuta zan fara hattaranku domin ni fetir ce kuma sai cikin wuta nake amaina !
Kallon Amisty nayi nace ki fara addu'ar kuɓuta daga sharrina domin na yanzu ba irin na baya bane , na yanzu maciji zansa ya cinye kwansa { uba ne zai kwanta da "yar sa } ki kiyayi haɗuwa ta da ke domin abin bazai miki kyau ba ,
Sakinta nayi na kalli matar nace mata muje... Wuce su mukayi muka tunkari gidan matan , da sallama muka shiga , ta amsa mana cikin sakin fuska tare da shinfiɗa tabarma tace ku zauna sannunku da zuwa ,
Zama mukayi , baiwar Allah ta dama ɗan kokonta da ɗumamen tuwo suna ci ita da yaranta tana ma Allah godiya , amma dole tayi haƙuri domin Sultana ta shigo mata rayuwa , mijinta ya fito daga cikin ɗaki muka gaisa dashi ita kuma tabi bayanshi danyi mishi rakiya , wayyo bawan Allah kayi haƙuri Sultana tazo yanzu zan firgita maka iyalinka ka kasa gane gabanta bare bayanta...
01/10/2019
*JAMILA MUSA....*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 47
Cikin sakin fuska ta shigo cikin gidan bayan ta dawo daga rakiyar mijinta , a mutunce ta zauna kusa damu saman tabarmar da muke aka gaisa a mutunce suka ɗan taɓa fira a tsakanin su da matar da muka zo tare mai nuni da akwai sanayya mai girma tsakaninsu ,
Bayan sun gama gaisawa da Maman Sadiq itace wacce muka zo da ita , ita kuma mai gidan naji Maman Sadiq in tana kiranta da Ummu Affan , Maman Sadiq tace tou Sultana wannan itace kike nema ko ? Murmushi nayi cikin jin kunya nace itace , kallona matar tayi tace lafiya dai ko ? Nace lafiya lau , Ummu Affan tace ya akayi ne ?
Nace dama ƙungiyace gwamnati ta buɗe domin taimakawa matan aure marasa ƙarfi , an ɗauki sunayen wasu matan da kuma yawan "ya "yansu , mai girma gwamna ya bada izini dan gyara siyasar shi , shin kina da wata sana'a da kikeyi ko bakya da ?
Ummu Affan tace gaskiya bana sana'ar komai , tou mi kike buƙata wannan gwamnati mai adalci ta taimaka miki dashi wanda zaki taimaki kanki da kuma iyalinki a cikin gida ba tare da kinsha wahala ba ? Tace Eh tou gaskiya idan dai san samu da gaske za'a taimakamin a siyamin injin markaɗe da kuma injin taliya domin shine abinda yayi ƙaranci a wannan anguwa tamu , tou amma bashi za'a raba kayan ko kyauta ?
Nace haba wane kuma da gaske Ummu Affan ? Kinga ai ban taɓa zuwa gidanki ba sai yau , kuma duk mutumin daka gani a gidan ka ai da dalili , gwamnati tsaye take a kan ƙafafuwanta dan ganin ta taimaki talakanta , idan zaki amince ma ai sai a naɗaki shugabar ƙungiya ki tattaro mana matan aure waɗanda suke san taimako kinga ke sai ki zama shugabarsu idan yaso sai a baki kuɗin da kuma kayayyanki da gwamnati zata bayar ke kuma saiki riƙa raba musu ya kika gani ?
Maman Sadiq tace to ni me za'a bani ne ? Nace ke kuma sai a naɗaki matemakiyar Ummu Affan amma ban sani ba ko mazajenku zasu riƙa barinku kuje wurin taro ? Dan naga duk lokacin da ake taro dubu goma ² ake bawa duk wacce ta halacci taron , Maman Sadiq ta zaro ido tare da cewa dubu goma ? Nace sosai ma idan ma gwamna yazo wurin taron dubu ishirin ake rabawa ga duk mace ɗaya ga lemu ga ruwan roba hada naman kaji ga abinci mai kyau kici ki ɗaurowa yaranki a leda...
Ummu Affan tace dubu ishirin ? Nace sosai ma , tace idan dai taron bana dare bane wallahi sai muje ko ƙawata ? Suka kashe da Maman Sadiq , Maman Sadiq tace aini ko na daren ne wallahi ina iya zuwa uwar me ake baka auren ƙaddara auren ya zanyi ? Auren cida kai ? Kana gida zaune kullum kamar mai takaba babu wani ci gaban rayuwa sai tsofewa kakeyi kai baka mori rayuwarka ba kazo a wahala ka rayu a ƙunci ka koma a alakoro , nidai gaskiya ina zuwa ,
Nace tou ki bari muji ta bakin shugabar ƙungiya mana ? Na ƙarasa maganar a dai² lokacin dana zage jakata na fiddo irin kuɗin dana fiddo a gidan Maman Sadiq dubu biyar² naba ko wace a cikinsu nace idan kunyi shawara ku neme ni , gaba ɗayansu dubu biyar² ta ruɗasu dan yanayin fuskarsu ya nuna haka , ina basu nayi sallama dasu na wuce gida abuna...
Fitar Sultana daga gidan sukaci gaba da tattaunawa yayin da Ummu Affan tace ni zan faɗawa Abbu Affan idan ya yadda , Maman Sadiq tace ki rabu dashi kinsan mazanmu baƙin ciki garesu su kaɗai suke so su ƙaru da sunga hanyar da zaka samu sai su nemi bulo da suminti su yaɓeta , kiyi shirunki kici gaba da sabgar gabanki gaki shugabar ƙungiya kinga idan aka baki kayan ki raba kina iya danne abunki kice ance za,a kawo amma har yanzu bai iso ba , idan kuma kina ganin zai hana taron sai a riƙayi a gidana , ni nafi ƙarfin mijina dan bai tsaremin ci 3 a rana ba bare ya juyani wallahi.
Ummu Affan tace tou idan kuma akace an ganni a wurin taron fa ? Tsoki tayi tare da cewa banda kike banza ai niƙaf zaki saka waye ya isa ya ganoki ? Ey fa haka ne , tou Allah yasa karta juya tunaninta akanmu ta samu wasu daban , Maman Sadiq tace ai gobe idan Allah ya kaimu sai muje gidansu muce munzo gaisheta sai mu sake tuna mata muce karda ta manta damu , Ummu Affan tace haka ne zanzo , bara na bada a siyomin cefane yau a gidan nan miyar ja kowa zai sha... Dariya sukayi tare da cewa sai sun haɗu goben ta fita a gidan...
A ƙofar gida na samu Babana yana zaune ya zagba tagumi ga dukkan alamu akwai abinda yake damunshi , gaskiya ina san Baba kuma wallahi yana bani tausayi bawan Allah , daga nesa dashi na tsaya nace mike damunka kake tunani kamar macen data rasa miji ? Ba tare daya kalleni ba yace ba kince saina biyaki motarki ba , nace idan nace sai ka biyani mota kuma sai ka zauna ? Ka tashi kaje ka nemomin kayata , nifa saidai kawai in siya miki wata tunda ba ɓacewa tayi ba nace miki a caca aka cita ,
Kiyi haƙuri Mamana , nace idan na ƙyaleka baka biya motar nan ba gobe gidan zaka saka shima a cinyeshi sai mu koma kuma muna raɓe² tunda cacar ta daina yinka basai kayi haƙuri ba ? Baba yace insha Allah nama daina cacar daga yau idan dai hakan zai miki daɗi , zanyi magana naji ƙaraurawar kaina ta buga da ƙarfi , addu'o'i naci gaba dayi dan na fara fahimta sheɗanci na yana cikin kaina ,
Ƙarfin hali nayi cewa daka hutama kanka ina faɗin haka nayi cikin gida , ina tunanin anya kuwa kaina ɗaya ? Koma dai miye Allah yana tare dani ,
Al ' Ameen durƙushe a gaban mai girma gwamna yana gulma , Allah ya taimake ka har yanzu mai gida bai rabu da yarinyar nan ba , kai kace in saka ido sosai kuma duk abinda yake faruwa a tsakaninsu in faɗa maka , tou wallahi wannan motar daya siya kayi mishi faɗan siyenta ita yama ɗauka gaba ɗaya ya bata ita , kuma hada kuɗi yace tasha mai amma kuɗin bansan ko nawa bane ,
Dady yace tou ai ya kyauta ni bansan yadda zanyi dashi ba , mai ɗaki shi yasan inda ruwa ke zubar mishi sai yaje yayi ta tarayyar da ita , ƙara duƙar da kai Al ' Ameen yayi yace Allah ya taimake ka a gani na bai kamata a zuba ido abarshi da ita ba ya kamata a sake dakatar dashi kafin abun ya wuce misali , Dady yace idanma gidansu zai koma da zama yaje ya koma tunda ba yaro bane shi ai yasan abinda yakeyi ,
Al ' Ameen yace ranka ya daɗe ai bazaka so a kaishi a baroshi ba , gara a tari abun tun wuri basai yayi nisa ba a kasa taroshi ba , Dady yace wai ba Dikko bane ba ? Yace Eh , yace tou ka ƙaleshi tasu ta haɗosu kasanshi baida gwani ka basu wasu kwanaki zakasha mamaki , ba haka Al ' Ameen yaso ba amma baida yadda zaiyi dole ya haƙura amma zai faɗawa Momy ita kaɗai zatayi maganin Sultana , daga nan shi kuma ya samu ɗiyar yayarshi ta shigo babu ɓata lokaci ,
Da daddare bayan na gama abinda nakeyi Alaji na kira { Abbu Afsar } ya kaini gidan Mamy tunda banda mota , motar da Dikko ya bani kuma ba yanzu zan fara hawanta ba akwai tanadin da nayi mata nasan duk ranar dasu Amisty suka ganni da ita sai sunyi hawan jini ,
Da sallama na shiga gidan , daga cikin ɗaki ta ansa min sallamar tare da cewa shigo Sultana har ta ɗauki miryata , nace tou ɗakin na shiga da sallama na samu wuri saman daka²n kujerunta na zauna , bayan na zauna na gaisheta cike da biyayya sannan na gaishe da wani mutum dake zaune yanacin abinci , kallonshi Mamy tayi cewa tou ɗauki abinci ka koma waje zamu tattauna da baƙuwa , yace tou Hajiya ya ɗauki abincin ya fita daga ɗakin...
Bayan fitarshi nace Aunty kiyi haƙuri da Allah akan abinda ya faru dani dake jiya , nayi miki rashin kunya wanda haka bai kamata ba kuma ba tarbiya bane ɓatawa na gaba da kai ba , kiyi haƙuri kuma insha Allah bazan sake ba , jakata na buɗe na fiddo kuɗin data bani nace kuma gama kuɗinki na dawo miki dasu , maganar matar kuma zan kawota kiyi haƙuri bazan sake ba ,
Murmishi Mamy tayi tace ba komai Sultana ni dama banji komai ba , Allah ya haɗani dake kuma yasamin soyayyarki a zuciyata kuma nayi ɗamarar taimakonki in Allah ya yadda ,
Godiya nayi tare da matsawa gabanta zan ajiye kuɗin , tace ki barsu ki riƙesu , nace a , a Aunty ki barsu wallahi , tace bani nace ki barsu ba ? Bana so muna jayayya dake ki maida kawai a jaka , nace tou , jakata na buɗe na saka kuɗin , daga nan muka ɗan taɓa fira har take cemin kece kike mamakin ina da aure ko ? Murmushi nayi amma banyi magana ba , mutumin data fitar yanacin abinci shine ta kira , bayan yazo tace tou kinga mijina nan ,
Kallonshi tayi tana cewa wai mamaki take ina da aure , cike da biyayya yace Allah sarki , Mamy tace tou jeka tunda ta ganka , kamar sakarai kuma ya juya ya fita , a kunyace nace tou Aunty ya maganar baƙonmu na gobe ne ? Tace zaizo yanzu ma muka gama waya dashi , nace tou ya maganar yaran gidan Baba ƙarami ? Mamy tacemin komai ya tafi dai² karki damu amma ina ganin tunda ita Hamida tahau layi kawai mu fita safgarta , nace da ina so ta samu kuɗi , Mamy tace manta da "yan gidanku domin dama su tuni suna cikin sahun *kwarata...* tuni sun daɗe a harkar bariki tunda sune suke kula da kansu ki rabu dasu kowa yayi sabgar gabanshi , nace tou ,
Mamy tace yawwa akwai wani Uncle Al ' Ameen lokacin dana saka layin da kika bani yana ta kira babu ƙaƙƙautawa , gajiya nayi da nacinsa na ɗauka waya , bayan mun gaisa yacemin da Allah wannan wayar ta doughter inshi ce aka yadar da ita , ko ina zai sameni ya ansa ? Sai nace masa ni ba waya na samu ba layi na tsinta ,
Gaskiya da nayi niyar mu haɗu na bashi layin dan naji shima yacemin a katsina yake , abinda yasa na fasa yamin burga da cewa zaisa a kamani , nace masa shi ɗan uban waye a garin katsina shine yacemin daga gidan gwamnati , nace gwamnan ya tsaya maka ko waye ? Shine sai yacemin layin wayar matar ɗan gwamna ne , cika bakinsa yasa na saka number a wayata na duba ta whatsapp hoton Dikko ne na gani a d pn inshi , abinda na fahimta wato shi yaron Dikko ne , amma idan na tuna da labarinki kuma idan na fahimta Dikko shine kukayi faɗa a motarshi ! Me ya haɗaki dashi kuma miye tsakaninku ?
Ajiyar zuciya na sauke tare da gyara zamana nace tou kila sato wayar tayi amma ita wannan ai bata taɓa aure ba , shi kuma mai maganar yace miki layin wayar matar Dikko ne , ko kin manta matar Dikko ta mutu ne ? Tace min haka ne kuma fa , nace gaskiya shiri ne abun , naci gaba da cewa yanzu wayau ɗaya zamuyi mishi shine kice masa ya turo miki lambar wayar da za'a iya samunta , domin akwai wasu tambayoyin da zamuyi ma mai layin idan ta bada ansa za'a bata wayarta da layinta wannan shine mafita , nayi haka ne dan na samu ta hanyar da zan turawa yarinyar nan vidion da zamu ɗauki ubanta , naƙi yadda kuma na faɗa mata nasan Dikko saboda gudun bita da ƙulli , bayan kuma Sadiya ta rasu babu wanda yasan Dikko yayi auren ...
Miƙa hannuna nayi tare da cewa Mamy inga hoton , miƙomin wayarta tayi bayan ta kamomin hoton Dikko a wayarta tana cemin yanzu lambar wayar yarinya zansa shi Al ' Ameen in ya turo mana kenan ko ? Banajin ta domin hankalina da duk natsuwa ta ya tafi wurin kallon kyakkyawar fuskar mutumina ,
Wallahi bana gajiya da kallon kyakkyawar fuskar Dikko , yayi min kyau sosai a hoton kuma yayi hoton a cikin yanayin fushi ya ɗan soɓaro leɓonshi na ƙasa , yayi kyau sosai kuma shima Al ' Ameen in yasan hoton ya haɗu shi yasa ya sakashi a whatsapp inshi , idona ya cika da kwalla a zuciyata nace shine dai kayi fushi dani ko ?
Kiran waya ya shigo a wayar dan haka na miƙawa Mamy wayar na miƙe ina cewa sai mun haɗu goben idan Allah ya kaimu , tace tou Allah ya kaimu ki gaida gida , banyi magana ba na fice buzum² zuciyata namin babu daɗi ,
A gajiye na isa gida , koda Alaji ya ajiyeni kawai ce masa nayi saida safe dan banajin daɗi kwata² kuma yaso na tsaya muyi fira na nuna masa bana buƙatar hakan ,
Ina shiga gida ɗakina na shige , saida na kwanta sannan naci gaba da tunanin Dikko , inayi ina hawayen baƙin ciki naci gaba kuma da kiran layinshi , har na gaji nayi bacci....
Washe garin ranar kuwa tunda safe Maman Sadiq da Ummu Affan a gidanmu suka bayyana , lokacin ko baccin safe ban tashi ba , dan tunda nayi sallah asuba na koma bacci , zuwansu ya tasheni , saida na fita na wanko fuskata da bakina sannan nazo muka gaisa dasu , bayan gaisuwa Maman Sadiq ta fara cewa dama cewa nayi bari muzo muji yaushe ne taron ?
Shiru nayi tare da tsaresu da idanuwa dukansu , bayan na gama fahimtar wani abu daga garesu nace gaskiya shugaban ƙungiyar munyi magana dashi yacemin in ƙyaleku danshi baya san azo a samu matsala dan basaso a ɓatawa siyasar su suna , matan aure basa iya basu gudumawa yadda ya kamata akwai matsalar mijina yace karna fita , ko kuma ina zan bar yarana ? Ko kuma ni bana zuwa hotel ko kuma inane za'ayi taron ?
Saboda jiya bayan na rabu daku naje wurinshi nayi masa bayani yadda mukayi daku bayan na nemi alfarma dan yaɗan ƙara muku wani abu saboda na lura iyali sunyi muku yawa gashi babu wata sahihiyar sana'a kuma yaran naku duk basu kawo ƙarfi ba , na samu dai yayi muku ƙarin budu goma tunda kune shuwagabannin ƙungiya ,
Sai yace na kawo mishi shugabar ƙungiyar ya gani shine nace ai matar aure ce , kinji faɗa ? Yace mi yasa kika naɗamin shugabar ƙungiya matar aure ? Bayan kinsan meeting na gaggawa zai iya tashi na kirata tacemin bata shirya ba ? Nidai ki mayar min da budurwa ko zawara , dakel dai na bashi haƙuri yace min ai matsalar matar aure wai kina iya zuwa kice aike bakya zama wuri ɗaya da mijin da ba naki ba , bayan dole zaku riƙa ɗan warewa ku tattauna abinda ya shafi ƙungiya ,
Ummu Affan taji zance kuɗi dan haka tace anyi ma aikin kishiya bare na uwar miji ? Daga magana sai mi kuma ? Nace kinsan wayayin maza basa so ayi ta wani dunkumewa a hijabi kinsan "yan boko basa san suga ana sha''ani da hijabi ,
Tacemin ai bansan wurin taron ko za'a nuna a talabijin ba , nace a , a ba'a sakawa a TV , Maman Sadiq tace tou Sultana ai sai mu tafi tare kice nice matemakiyar Ummu Affan , nace kibi sannu duk za'aje da kowa , tace a , a abari ya huce fa shine ke kawo rabon wani , nace aiko bai hucen ba idan rabon wani ya shiga tun yana kan wutar wani zaizo , kinga kuwa ai dole zakuci tare ko ? Tace haka fa , nace tou kudaije ku sake tunani shin zaku iya huɗɗa da maza ? Dan duk zama ɗaya ko wace zata tashi da dubu ishirin idan kuma gwamna yazo ko wace tana da dubu talatin idan kuma kin iya gogayya da maza zama ɗaya ma da hamsin zaki tashi ,
Zasu sake magana wayar Mamy ta shigo , nace tou anyi ma sa'a ga shugaban nan yana kirana ku jira muji me zaice ne ? Ɗaukar wayar nayi bayan mun gaisa da Mamy tacemin in shirya gata nan zata taho , nace tou , sai nace yawwa Alhaji maganar matan auren nan ina dai ƙara baka haƙuri yanzu haka ma muna tare dasu kuma sunyi alƙawari babu wata matsala , shiru nayi bayan wani lokaci nace dubu ɗari da keken ɗinki ? Allah ya ƙara arziƙi wallahi godiya suke , kallon juna sukayi suka ƙyarawa junansu ido , ni kuma na sake shiru bayan wani lokaci kuma nace kai Alhaji dani da ita zamuje har a gaban mai girma gwamna ? Tou muna godiya sai munzo goben , nagode ׳ , yawwa sai anjima na kashe wayata , Mamy kuwa cewa tayi kai wannan yarinya batajin magana ,
Ummu Affan har sauri take wurin cewa wai waye za'a ba keken ɗinkin da dubu ɗari ? Nace shugabar ƙungiya wai cewa yayi idan Allah ya kaimu gobe duk shuwagabanni zamuyi zama da mai girma gwamna shin zaki samu damar zuwa ko kuwa yadai ?
Tace zuwa ma kai zanje , nace tou kidaiyi shiga mai kyau dan kinsan shiga gidan gwamnati bana yara bane , kiyi wanka ki ɗauro kallabi ƙarshen layi kizo muje amma kuyi shiru da bakinku karku sake ku bari wani yaji idan ba haka ba "yan zidaƙuiy zasu zo su anshe ma ɗan tama doki , Ummu Affan tace haba wallahi bama faɗa , nace tou yayi kuje sai mun haɗu goben , Maman Sadiq tace ai wallahi baku bari na wannan ai baƙin ciki ne taya ni na rakaki gidanta kuma a gabana aka haɗa komai sai ku tafi gidan gwamnati ku barni dan baƙin ciki ? Nace kema hada ke za'aje , tace tou yanzu naji magana , murmushi nayi tare da cewa kuje zan shiga wanka ,
Maman Sadiq ce ta fara fita ɗakin dan haka na riƙo hijabin Ummu Affan nace karki faɗa mata ƙarfe biyu na rana zamu tafi , idan ba haka ba keken ɗinkin nan da dubu ɗari tare zaku rabasu , tace bazan faɗa nace tou ku gaida gida ,
Kwando na ɗauka naje nayi wanka , bayan na fito na fara shiri ina saka kaya Mamy ta iso , bayan mun gaisa nake bata labarin yadda mukayi da matan aure , na ƙara da cewa kinga goben idan mukaje sai muyi ta zama ace gwamna yana meeting , ni kuma ina ci gaba da gyara hanya cikin sauran kwana shiddar daya rage har an kaita an baro ta ,
Mamy tace gaskiya ne , nace tou shi mutumin saiki faɗa masa idan munje muka tashi tafiya ya bata dubu hamsin kinsan ita mace da kuɗi ake tafiya da imaninta , Mamy tace haka ne karki samu damuwa nace dama banda ita ,
Bayan na gama shiri na ɗauki jakata da abinda nake shafawa mutane su tafi bacci , saida muka fita ƙofar gida nake tambayar Mamy ko Al ' Ameen ya turo lambar yarinyar ? Tace yace babu waya a hannunta sai dai ta Mamanta take amfani dashi kuma ya turo nace shikenan magana ya ƙare mata tacewa mijinta shege..........
02/10/2019
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 48
Ni naja motar muka tafi Mamy kuma tana gefe na tana waya , dama ta shigo tanayin abunta kuma har yanzu bata gama ba , hanya na iba ɗoɗar saboda ta nunamin hanyar da zanbi da hannunta ta kuma nunamin kawai in tafi miƙe kar in kwanta ,
Munyi tafiya mai nisan gaske sannan Mamy ta gama waya , sawa tayi nayi parking ta anshi tuƙin motar mukaci gaba da tafiya har muka iso inda muka zo Mamy bata sake magana ba ,
Get in gidan buɗe yake dan haka muma muka samu damar antayawa daga ciki , tun kafin Mamy tayi parking Allah ya nunamin Al ' Ameen , haka nan naji gabana ya yanke ya faɗi gaba ɗaya sai guyawuna sukayi sanyi nama kasa fitowa daga cikin motar , ni kaɗai nasan Al 'Ameen Mamy bata sanshi ba , sannan kuma numbershi da ta saka a whatsapp inshi ba shine ba Dikko ne ,
Dogon nazari na shiga to me ya kawo Al ' Ameen wurin nan kuma ?Tunani nayi sosai firata da Mamy ta daren jiya ta dawo min , to duk yadda akayi yarinyar da mukayi faɗa da ita kenan tana da alaƙa da Al ' Ameen ? Na shiga tunani sosai amma na kasa fahimtar ya abun yake ,
Mamy kuma fita tayi daga motar tabar harabar gidan ta koma ƙofar gida , bayan wani lokaci kuma ta dawo ita da wata matashiyar yarinya shekarunta da kamanunta duk bana iya ganewa saboda ta saka niƙaf ta lulluɓe fuskata , ciki suka wuce ta barni zaune a mota kamar mage na dakon tsuntsu ,
Shiru² babu Mamy ba labarinta , ni kuwa sai sassada kai nake ƙasa dan bana so Al ' Ameen ya ganni , gashi ina so na fita nima na shiga amma dole banda yadda zanyi saboda Al ' Ameen zaune yake kuma baida alamar tashi ,
Har su Mamy suka gaji da daɗewarsu suka fito , yarinya bata shigo motarmu ba ficewa tayi Mamy kuma ta shigo mota taja muka tafi , saida mukayi nisa nace mata wai mutumin dake zaune a wurin nan shi kuma waye ? Ko gadi aka sashi ne ? Mamy tace ƙanin matar Baban yarinyar ne , jinjina kaina nayi sannan nace tou wace ce da niƙaf kuma ? Tace "yar uwarki ce da kika ce na farauto ,
Nace Hamida ? Tace ɗiyar ƙanin Babanki ce , dariya nayi sosai nace tsakaninki da Allah tace wallahi kuwa , tou ya akayi kika farauto ta da wuri haka ?
Mamy tace wallahi ina zaune gidana Allah ya kawo minsu ita da ƙanwata , ashe ita ɗiyar ƙanin baban naki aure zatayi ? Mamy ta tambayeni nace mata Eh Safiyya ce zatayi aure , Mamy tace to ai kinsan "yan matan zamani sun saka kansu ƙarya basa haƙuri da abinda iyayensu sukayi musu , basa da gashin wance sai suce dole zasuyi kitso irin nata ,
Ƙanwata tacemin tana naima wa ƙawarta aiki a ƙarƙashi na , na taimaka wannan ƙawarta ce zatayi aure iyayenta basuyi mata wani abun kirki ba na kayan ɗaki , shine ta kawota wurina ko zan taimaka na ɗauketa aiki ita kawai talabinjin in bango da kayan sautin ta take so ta siya sai labulaye masu tsada ta gyara palon ta dan bata so ƙawayenta su raina mata gidan aurenta ,
Saina tambaye su bikin kwana nawa ya rage ? Shine tacemin wata 3 nace tou yarinya banda abinki wata3 taya zaki samu kuɗin da zaki sayi talabinjin in bango da kayan sautinta ? Kona ɗaukeki aiki na baki kuɗi da yawa a wata baifi na baki albashin 3k ba , kinga 3k sau wata3 ya kama 9k ba talabinjin ba ko labule bazai siya miki ba ,
Tacemin haka ne , tou bayan nayi bincike naji daga inda ta fito kuma naga kina nemansu da karuwanci ruwa ajallo yasa nayi mata tayin karuwanci bayan munyi ciniki dashi baban ƙawar faɗan taki akan zai bayar da dubu hamsin , nayi ² ya ƙara wani abu akai umm lusarin a haka ya tsaya , bayan mun gama ciniki dashi ya kafe kai da fata haka zai bayar ,
Kodai yane tunda na samu an farketa shikenan kinga ta tsaya zaman jiran talabinjin dan ubanta saidai kawai taji a salansa tamin hauka akan na bata kuɗi ga vidio na ɗauko ta ƙarasa maganar tana dariya , nima dariyar nayi tare da cewa yaro inya iya ruwa ai bai iya laka ba , dariya Mamy tayi sosai tare da tambayata meye ruwan kuma miye lakar ? Nace zancen sai wanda ya kwana a bakin gabi.... Mamy tace ina ne gabi kuma ? Nace wata matattara ce ta karuwai dake can wajen gari !
Haka dai mukayi ta taɓa fira har muka iso ƙofar gidanmu , bayan Mamy tayi parking ta fara kiran wayar Maman budurwar Dikko da mukayi faɗa da ita wacce bayan an ɗauki wayar naji Mamy tana cewa da Allah Momy ko Mardiyya tana kusa ne ? Eh tana nan Mardiyya kizo anyi miki waya ,
Tazo ta anshi wayar , bayan gaisuwa Mamy tace mata kin gane ɗiyar ɗan caca wacce kukayi faɗa da ita a motar saurayinki akan haryar ku ta zuwa Abuja ? Wacce bayan kunyi faɗan tayi zuciya ta barku a hanya ta samu mota ta dawo katsina kin tuna har kikace mata jahila daƙiƙiya kidahuma jaka kin tunota ? Tace Eh na ganeta ya akayi ne ? Mamy tace yawwa dama cewa tayi ki riƙe wayar Mamanki a hannu ki duba ta whatsapp zata turo miki saƙon ta tashi daga jahila ta koma ma... Da sauri na anshi wayar daga hannun Mamy nace.
Mai ilimi barka da tsakiyar rana , barka dai ta amsa a daƙile , nace suna na *SULTANA ALIYU MUHAMMAD BINNA...* ina miki albishir da mummunan gani , salona ne yin albishir da mummuna ga abokin gaba sai kuma nayi albishiri da kyakkyawa ga masoyina , idan baki manta ba a waccan ranar nace mutuwa kaɗai zaki ki huta da ganin baƙin cikina , tou yanzu muka fara ki fara yininki da wannan anjima ma zan turo miki na kwanciya bacci kisha kallo lafiya...... Gashi nan zuwa , ki gani ke ɗaya idan uwarki ta buƙaci gani itama ki bata ta gani muna da maganin ciwon zuciya na hausa idan kina buƙata kallon Mamy nayi tare dayin dariya nace masu magani kasuwa ta buɗe ....
Ina faɗin haka na kashe wayar , Mamy kuma ta ansa ta tura vidion data ɗauko kuma hada Safiyya a cikin hoton tana ta kwarara ihu saboda azaba yayin da Baban Mardiyya ke kwarara wani irin gurnani kamar kura tayo kamu , na raka vidion da voice note cewa mi yasa ya faɗa ruwa bai iya iyo ba ?
Dariya mukayi dukanmu , saida muka tabbatar an buɗe saƙon kuma ya ɗauki lokacin da ya isa Mardiyya ta gama gani sannan naba Mamy Umarni data goge shi daga wayar mamanta , wato ta saka delete 4 everyone , bayan an goge duka hada voice note in da nayi nasa Mamy ta rubuta cewa ta kawo kuɗi masu yawa sai mu goge idan kuma ba haka ba ta tara a tashar yanar giza gizo.
Bayan mun gama nayi sallama da Mamy na wuce gida akan sai mun haɗu gobe idan Allah ya kaimu , tace Allah ya kaimu lafiya , a gajiye na shiga gida dan haka ruwa na watsa kawai nayi sallar la'asar na kwanta ina hutawa.
A ɓangaren Ummu Affan da Maman Sadiq kuwa fitarsu suka yanke shawara cewa idan na kaisu so ɗaya bazasu sake tafiya dani ba dan abinda suka fahimta zan riƙa ci musu aljihu , ma'ana idan aka basu zan riƙa ragewa ni inci da yawa su abasu kaɗai , ummm kuji ɗan adam butulu ,
Yayin da Maman Sadiq ke bayar da shawara cewa suyi wayau muna zuwa su lallaɓa su anshi lambar shugaban ƙungiyar sai suce masa idan ana taro ko yana nemansu karya kira Sultana ya nemesu kai tsaye , Ummu Affan tace gaskiya haka ne , dan kinga idan aka bamu dubu ɗari zata saka rai a cikin kuɗin ta, ga, tunda itace ta haɗani dashi zata jira na bata wani abu a cikin kuɗin , Maman Sadiq tace haka ne , ai tana nuna mana hanya mun gama da banzar , haka dai suka yanke shawarar su ,
Bayan sun rabu kuma kowa ya yanke shawarar saiya koro abokin tafiyarshi dan kowa yaci shi ɗaya , yayin da Maman Sadiq take tunani idan gwamnati ta bada mai da sabulu da magi da rigunan siyasa da ake rabawa zatayi samayya fiye da tunanin mai tunani ,
Itama a ɓangaren Ummu Affan haka ne dan har ta kasafa dubu ɗari yadda zata kaya mata tun kafin akai inda za'aje har sun yada Sultana a gefe , Ummu Affan ma tana tunanin yadda zata yada Maman Sadiq yayin da itama Maman Sadiq in take tunanin yadda zata kora Ummu Affan taci ita ɗaya ba tare data samu mai tayata ba.
Washe gari kuwa tun 7:22am Ummu Affan ta bayyana a gidanmu , tasha wanka ta ɗauko jagira irin ta zamani sai baɗa ƙamshi takeyi anci jaka da takalmi masu kyau ta ida rufe wankan da wani irin tsadajjen gyale tayi kyau fa abunta ,
Tana zuwa ta ganni ban shirya ba , tacemin da Allah muje kafin wacce mayyar tazo , nace tun yanzu ? Tace Eh na samu na ajiye yaran a maƙota muje mu dawo , nace tou ki bari itama Maman Sadiq in tazo basai mu tafi tare ba ? Tace nidai karmu jirata da Allah ki tashi mu tafi , nace tou yanzu gwamna ma kanshi ai bai tashi bacci ba , tace haba ai da a jiraka gara kai ka jira , dan Allah ki tashi mu tafi , nace kai gaskiya ni ko shara banyi ba , kuma ban wanka ba , tace jeki kiyi wankan ni kuma sai in tattara miki ɗakin kafin ki fito , nace to amma mi yasa bakya so aje da Maman Sadiq , na tambayeta ? Danni dama bana so aje da ita ,
Ummu Affan tace kinsan mutanenmu da baƙin ciki sai kaja mutum inuwa ƙarshe kuma yakai ka rana , nace tou ba aminiyarki bace ba ? Tace wa ni ? Ta nuna kanta sannan taci gaba da cewa ba aminiyata bace ba kawai dai muna gaisawa cikin anguwa , nace tou ina kika cewa mijinki zakije da wannan safiyar ?
Saida tayi murmushi tace tambaya kamar "yar jarida , ce masa nayi ƙawata bata lafiya za'a tafi da ita asibitin zariya zanje na dubata kafin su tafi , nace to misali idan mukaje bamu samu ganin gwamna ba fa sai akace gwamna abubuwa sun mishi yawa mu dawo gobe tou sai muka dawo idan zaki fita goben sai mijinki yace baza ki fita ba tou ya zakayi ?
Tace ina ai dabara ma bazata ƙare ba , idan yace bazan je ba nasan hanyar da zan biyo masa , nace Allah ya taimaka ina faɗin haka nayi waje dan inje inyi wanka , kafin in fito wankan ta share ɗakin tas ta goge shi ta shinfiɗamin zani a katifa , ina fito na shirya a gaggauce ko kalaci banyi ba muka bar gidan kafin Maman Sadiq tazo.
A napep muka je gidan Mamy , a ƙofar gida muka same ta cikin motar wani namiji ga kuma wanda ta nunamin da sunan mijinta yana zaune saman dakali yana kallon ikon Allah , gaisawa mukayi dashi na umarci Ummu Affan da ta shiga ciki na nuna mata gidan tare da cewa shiga muna zuwa ,
Tana shiga ni kuma nayi wurin Mamy muka gaisa na gaishe da baƙon nata , bayan mun gama gaisawa Mamy tacemin in shigo mana , baya na buɗe na shiga bayan na zauna muka ƙara gaisawa ,
Shiru na wani lokaci sannan Mamy tace Sultana ga mutumin ki yaga mutuniyarshi kalli iskanci da yakeyi leƙo ta nan ki gani , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya nace ni basai na gani ba , tace dan girman Allah leƙo kiga yadda bironshi ki rubutu babu takarda , dariya nayi sosai nace nidai bana san gani , Mamy tace haba so ɗaya fa zaki gani kawai , nace ba komai idan ya rubuta a takardar zan gani danni bana gane rubutu bisa iska ,
Dariya akayi gaba ɗaya , bayan wani lokaci kuma mukaci gaba da maganganu dai na sakin layi , bayan an gama mutumin ya tambayeni yadda mukayi da sabuwar sheƙar tashi , na goga mishi bayani duk yadda mukayi da su Ummu Affan hada Maman Sadiq duk ban ɓoye masa ba !
Yace babu damuwa ba hamsin za'a bata ba dubu ɗari zan bata yanzu sai ince mata gwamna yaje Abuja sai jibi zai dawo , kinga tana dawowa jibin ke Mamy sai ki bamu aron ɗaki mintuna 30 sun ishemu sau ɗaya kaɗai zan sa mata hannu kuma in bata kuɗi daga nan da kanta zataci gaba da zuwa ana mata singing ,
Shiru nayi sukaci gaba da firansu da Mamy , bayan wani lokaci kuma ya juyo yace Sultana kirata na sallameta tafiya zanyi na ansa da to tare da fita daga motar na nufi cikin gidan babu jimawa muka dawo tare da Ummu Affan bayan sun gaisa yace mata gwamna yaje Abuja wurin shugaban ƙasa amma zai dawo jibi idan Allah yasa muna da rayuwa , tace tou Allah ya dawo mana dashi lafiya...
Ya ansa da amin tare da karkacewa ya fiddo bandir in "yan ɗari biyar² masu zafi ya bawa Ummu Affan da kwalin sabuwar waya yace kuma da akwai layi a ciki , ruɗewa tayi ta duƙe har ƙasa tana zabgaga mishi godiya tare da cewa Alhaji kasa min lambar ka a ciki ? Yace zan kiraki zuwa gobe yadda mukayi da gwamna zan faɗa miki , godiya tayi sosai kamar zata faɗa mishi sai ƙara godewa take godiya irin ta maroƙa ,
Wani irin kallo ya bita dashi yana lashe loɓonshi na ƙasa mai nuni da zan kashe wuta dake , Mamy kuwa fitowa tayi daga mota mukayi mishi sallama bayan muma yayi mana wanka da ruwan naira ya tafi ya barmu da ɗaurewa da ruwan godiya ,
Ai Ummu Affan kuwa cewa tayi bazata koma cikin gida ba lokacin da Mamy tace mu shiga ciki , juyin duniya nayi mu koma ciki tacemin tabar yaranta suna jiranta gida zata tafi , babu ko tayin kuɗin bare ta jira taji munce ko mun ƙoshi , haka ta saɓe abunta tabarmu da kuɗinta da wayarta tai tafiyarta , mu kuma muka koma gidan Mamy , gaba ɗayanmu a palo muka zauna inda Mamy take cemin Al ' Ameen ya kirata ya zageta fess dan Mardiyya ta kirashi ta faɗa mishi babu daɗi yace duk sai yaci uwarmu dagani har ke kuma ya faɗawa mai gida abinda mukayi ma matarshi kuma shi mai gidan yace duk sai an tattaremu an ɗauremu , ni kuma jin haka yasa na kira wannan mutumin na faɗa mishi tunda naga yana cikin gwamnati shima.
Nace to yanzu ya ake ciki ? Mamy tace sai munemi mafita , nace shi Alhajin ya yace miki ? Mamy tace yace mu jira idan anyi ƙararmu zai ɗaukar mana lauya , idanuwa na zaro nace wane irin lauya kuma na shiga 14 nidai gaskiya bana san huɗɗa da koto ƙarshe akai mutum gidan yari ni banda wanda ya tsayamin , kawai saina fashe da kuka , Mamy tace haba Sultana tou miye abun kuka muna fa da bakinmu ki barshi ya yanko sammacin kiga yadda alƙalin zaiyi idan yaga lafiyayun katifu ,
Cikin kuka nace shikenan kullum mai makon katifa tahau saman gado sai gado yai ta hawan katifa nidai na shiga 3 , Mamy tacemin da Allah ke banza ce ki kwantar da hankali babu abinda zai faru domin na sake kiran yarinyar nayi mata baraza na da zan saki vidion a social media idan Al ' Ameen ya sake magana kuma ta kama kanta sosai ,
Dakel dai Mamy ta lallashe ni ta kwantarmin da hankalina ta sake bani ƙwarin guiwa , a gidanta na yini saida nayi sallah isha'e ta kawo ni gida ,
Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya , yanzu tsawon watanni 3 kenan da kafa su Ummu Affan da Maman Sadiq a ƙungiya kuma tun daga ranar dana kaita bata sake bi takaina ba , yanzu tama ƙwace sosai wuta kawai takeyi abunta a cikin anguwa ,
Mijinta kuma tuni ta wanke ta bashi dan tunda ya taso ya fara hayagaga ta kwantar da banza da asiri , Maman Sadiq itama tuni an mata register amma bata ƙarƙashin ƙungiyata tana ƙarƙashin ƙungiyar su Amisty ne ,
Safiyya kuwa ɗiyar Baba ƙarami ciki gareta , gashi biki yazo Mamy ta hana talabijin bare labulaye , fitina sukayi ta rashin lissafi akan rashin talabijin da labulaye , ga rashin lafiya ya taso ta gaba tun Safiyya tana boyewa har abu ya fara damunta dan haka ta faɗawa Mamy cewa bata lafiya wata 3 bata ga jinin al'ada ba , kai tsaye Mamy tace ciki gareki sai kawai kije ki zago bedi ki saɓa kisha ,
Safiyya kuwa ta gaji da ɓoye ²ta rasa ina zata soka rayuwarta gashi Mamy bata , bata sahihiyar mafita ba , dan haka kawai ta haƙura ta faɗawa mahaifiyarta komai bata ɓoye mata ba , da Mamy da mahaifiyar Safiya akaci gaba da musayar harshe tsakanin Mamy da Uwar Safiyya , tashin hankali naƙin ƙari , ni ko kada Mamy ta faɗamin cewa nayi ai ba danneta akayi ta ƙarfi aka ƙwata ba lokacin da Alhaji yake bata tana ta tanɗewa tare da wa suka tanɗene ? Taje can taji da abunta sakaran banza tunda bata iya shan gishiri ba ,
Ƙarshen film in dai mahaifiyar Safiyya zama akayi aka sasanta suka fuskanci juna ita da Mamy daga ƙarshe dai a asibiti aka wanke cikin tass , ta tashi babu talabijin ba labulaye babu budurci kuma babu albashin kuɗin aikin da alhaji yayi , bayan wanke ciki da sati biyu aka ɗaurawa Safiyya aure , kwanata biyu a gidan miji ya korota tare dayi mata shegen duka rashin samunta da baiyi ba a matsayin budurwa , itama daga nan ta yanki nata tikitin na shiga sahun jerin *Kwarata...* kuma buƙata na ya biya.
Rayuwa mukeyi dai tsakanin ni dasu Amisty kowa naji haushin kowa , har yanzu ban sake ganinta da Babana ba , ta sake faɗaɗa ƙungiyarta da manyan mata masuji da duniya kuma duk matan aure sunfi yawa a cikinta domin yanzu kasuwar sutafi ja ba'a neman "yan mata kuma bata zawarawa akeyi ba matan auren dai ,
Ƙungiyar Amisty ta samu karɓuwa fiye da tunanin mai tunani ta samu kuɗi ta goge ta zama lafiyayyar hajiya , nima kuma inata bakin ƙoƙarina wurin ganin na kafa tawa ƙungiyar amma wallahi taƙiya daga ni sai Mamy a ƙungiyarmu , itama Ummu Affan ta kafa tata tana bada hayar matan aure ko a hanya ta ganni batamin magana saboda tana ganin tafi ƙarfina , al'amirin duniya ya fara bani mamaki dan haka na fara sanyi da rayuwata.
Mazan kuma nabi su² amma da an fara ciniki dai kalmar ɗaya ce 1k gani ni kuma haɗama gareni bana iya iba kaɗan sai in kantamo dubu ɗaruruwa , zuwa wannan lokaci kuma al'amura sunjamin baya sosai tun ba'ayi nisa ba duniyar ta ajiyeni bani ake yayi ba lokacin ba nawa bane na wasu ne , kenan tun kafin na ajiye bariki tana neman ta ajiyeni , dan har alaji su Amisty sunyi gaba dashi !
Ina cikin wannan tararrabi Allah ya kawomin wani zazzafan matashi maiji da kanshi ga kuɗi ga gayu amma matsala ɗaya wallahi mummuna ne ,
Naji daɗin zuwanshi kuma mun antaya soyayya shi ya wankoni daga talauci yayi ta yayyafin ya cidar hadarin naira da anyi tsawa saidai kiga yana ɓarin naira , cikin ƙanƙanin lokaci nima na farfaɗo na fara dawowa hajiyata ,
Naci gaba yanzu har hotel nake kwana amma matsalar ɗaya abunda na fuskata bayada alƙamin rubutu , kullum haka zanje in kwanta salaf in taso babu wani ɗan shafe² ko ɗan lashe ² ko ɗan tsotse² idan kuma na tashi tafiya haka zai bani kuɗi masu sa mutum ya kasa gano hanyar gidansu , abun a dameni dan haka na tambayeshi nace shin wai kai bakajin kanajin sha'awata ? Saidai yayi dariya yace yana da sha'awa in kwantar da hankali ranar hawa na zuwa ,
Ina kwance ina bacci a saman gadon hotel nayi guda² ina sararawa abuna idanuwana a rufe amma ba bacci nake ba , a tunaninshi nayi bacci dan haka ya tashi saf² ya fita daga bedroom in , wallahi haka nan naji tsikar jikina ta tashi jarr hankalina ta tashi ƙararrawa ta doka hayani ta riƙa tashi cikin kaina , da sauri na sauko daga saman gadon nayi bakin ƙofa ,
Da sanɗo na shiga palon ya bada baya yana waya cikin harshen turanci , hakanan na tsargu dan haka zuciyata tace kiyi masa vidio ko recording kamar yadda kika saba wannan da ganinshi baida gaskiya , da sauri na latso recording na fara ɗauka saida ya gama wayar tas sannan ya juyo da wata irin siffa mai ban tsoro dasa firgici tunda nake duniya ba taɓa ganin irin siffar ba , dakewa nayi banji tsoro ba kuma ban firgita ba naci gaba da addu'a nima na tsareshi da ido ,
A hankali siffarshi ta dawo siffarshi da nasanshi da ita , murmushi yayi yace ke matar aure ce ? Na girgiza kai da a , a , yace tou ki wuce daga yau karki sake dawomin matan aure muke nema , murmushi nayi tare da cewa ngode kuma na barka lafiya , ina faɗin haka nayi gaba abuna ko ciki ban koma ba bare na ɗauko gyalena , saida na fita daga ɗakin na ruɗe na firgice na kwarara wani irin ihu mai tada hankali ,
Hmmm
_Ƙalu bake gareku matan aure......_
04/10/2019
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 49
Gaba ɗaya na firgice na fita hayyacina kururuwar da nakeyi ta karaɗe kaf girman hotel in , hayagagata ya jawo hankalin mutane akayo wurina ana lafiya ? Duk wanda na gani sai inga fuskar mutumin nan gareshi wayyo Allahna na shiga 3 🙆🏻 na lalace shikenan mutuwa zanyi na bani ׳ na ƙarasa maganar tare da faɗuwa ƙasa ina burgima.
Baiwar Allah lafiya ? Meke damunki ? Shine tambayar da mutanen da suka zagaye ni sukemin amma maimakon naji maganarsu sai naji muryar mutumin cikin muryar tsoratarwa da firgitarwa yana cemin da hantarki da ƙodarki ko zuciyarki wanne kika bamu....
Da sauri na dafe cikina na tallabo saitin zuciyata amma har yanzu wayata na riƙe ram a hannuna , cikin kuka nace wallahi bazan bayar ba , nawa ne ni ɗaya , cikina ne da zuciyata hantana da ƙoda Allahna ya bani ba wani ba , kuma ubangiji bazai baku damar rabani da ko ɗaya ba , wata irin gigitacciyar dariya akayi tare da cewa kina nufin kinci kuɗinmu a banza ? Tou wannan kuɗin ki sani jinin wasu ne da wasu sassa na jikin ɗan adam dole ki bayar da naki kema domin a bawa dodo ya bamu kuɗi zuciyarki zata shiga kwarya , bankwana da duniya sai wata rana....
Gaggaɓewa akaci gaba dayi da dariya data gigitani a karo na biyu , addu'o'e naci gaba dayi da ƙarfi idan ina addu'a bana gama wata saina saketa na kamo wata , dai najin sautin muryar dariyar nayi sai sautin kuka har zuwa wannan lokacin ban daina addu'a ba , bayan wani lokaci kuma na dainajin sautin kukan gaba ɗaya...
Da sauri na miƙe ko jikina ban tsaya kakkaɓewa ba nayi gaba , mutane suka bini da kallo yayin da wasu ke tunanin ko ina da taɓin kwalwa ne , da gudu na fita daga hotel in , ina na fita na samu napep sai gidan Mamy amma har yanzu hankali na baya jikina gaba ɗaya a ruɗe nake , napep na tsayawa na fita da gudu nayi cikin gidan Mamy , bata nan sai yara na samu nace musu ina Mamarsu ? Sukacemin yanzun nan ta fita tace idan kinzo ki kirata ,
Jikina yana ƙyarma na fara laluben wayar Mamy babu ɓata lokaci ta ɗauka , gaisawa mukayi nace mata kina ta ina haka ne ? Sunan hotel in dana baro ta faɗamin tare da cewa wani sabon sauna ne na samu ki jirani na wankoshi cikin mintuna kaɗan zan dawo , kaina ya juya a gigice nace karki je , ki dawo hotel in nan akwai wani gahurtaccen matsafi daya bayyana karki shiga ɗaki ki dawo , Mamy tace wane ɗaki ? Nace ɗakin dana shiga wallahi matsafi ne karki shiga ki dawo akwai zama na musamman , Mamy tace tou lamba nawa ne ɗakin ,
Da sauri na dafe kaina duniyar ta riƙa juyamin kamar nahau shillo mai wanawa , gafa lambar ɗakin ina gani a idona bana iya faɗa dan na iya lissafin lambobi tunda dasu nake sarving numbobin mutane a cikin wayata , ganin na kasa faɗa kawai nace ....
Ki dawo........... Na faɗi ki dawo cikin wata irin murya hawaye suka gangaro daga cikin idona ina cewa nidai kawai ki dawo matan aure yake nema ko wane ɗaki bana so ki shiga ki dawo Auntyna bana san na rasa ki adaidai wannan lokacin ki dawo dan Allah na ƙarasa maganar ina durƙushewa ƙasa naci gaba da kuka , amma duk wannan maganar da nayi sam Mamy bata jini ta riƙa hello , hello idan kina jina kawai ki jirani , tana faɗin haka ta kashe wayarta ,
Da gudu na fita daga cikin gidan , mai napep in daya kawoni shi nace ya maidani inda ya ɗaukoni dan dama ban sallameshi ba , nace kayi gudun bala'e ka kaimin motar nan maleji karka tsaya kuma karka kauce ina so kawai na buɗe idona na ganni a hotel in nan kamar kyaftawar ido ,
Gudu mai napep yakeyi amma ce masa nake ya ƙara ina kiran wayar Mamy amma ba'a ɗauka , saidai na daki napep in nace wuta mai mota nace karka tsaya kaucewa ababen hawa muje kayi tuƙin nan kamar babu koma bisa titin nan saimu , gudu yake balbalawa na tashin hankali amma gani nake kamar baya tafiya , wayar Mamy kuwa saidai ta ƙari ringing inta ta tsinke amma ba'a ɗauka har muka isa hotel in ban daina kiran wayar Mamy ba kuma bata daina shiga ba haka kuma babu wanda ya ɗauka...
A harabar hotel in naga dandazon mutane , da gudu na tunkari inda suke kamar wata mahaukaciya na riƙa ture mutane , hasahsena ya zama gaskiya domin Mamy ce yashe a ƙasa mutane sun zagayeta ga "yan sanda har sun rigani hallara a wurin , jini ne kawai ke ɗiga daga cikin idon Mamy kamar babu ƙwayar idonta dan baka gani hasken idon ko sai jini dake ɗiga ɗis ² ,
A wurin mutane ke cewa yanzu wata ta fita itama tana ihu ita Allah yasa tana da sauran shan ruwa a gaba , goge hawaye nayi a zuciyata nace ba ni suke so ba matan aure , mutane sukaci gaba da cewe lallai akwai abinda yake faruwa , jiki a sanyaye na na isa gaban Mamy nace Aunty na ƙarasa maganar ina mai kamo hannuwanta , bata iya magana ma kwata² dan haka na rungumeta naci gaba da kuka , bayan "yan sanda sun gama bincikensu kuma basu samu wata sahihiyar sheda ba haka aka ɗauki Mamy da wayarta akayi asibiti da ita... Nima napep na koma nace masa mubi bayansu.
Bayan mun isa asibiti "yan sanda suka danƙamu a hannun likitoci babu ɓata lokaci aka shiga duba Mamy , tashin farko dai likitocin sun tabbatar da babu idon Mamy kuma har yanzu jini bai gama fita ba , ni kuma hankalina yafi karkata akan wayarta dan haka naje wurin ɗan sanda nace ranka ya daɗe wayar zaka bani na kira Babanmu ,
Kallona yayi sama da ƙasa sannan yace wace ce ke ? Nace ɗiyar mara lafiyarce ni , dan bana nan na dawo gida "yan uwana sukace Mama tace ta fita amma idan na dawo na kirata , bayan na dawo suka faɗamin na kirata mun fara magana da ita a waya daga baya kuma saita nunamin batajina , ka duba jerin kira kuma zaka gani dan daga baya nayi ta kiranta bata ɗauka ba ,
Miƙomin wayar yayi domin wayar Mamy ba'a buɗeta sai an zana pattern yace buɗeta tou tunda kince ta Mamanki ce , lafiya lau na zana na buɗe wayar domin kullum a gabana take zanawa kuma baida wahala , bayan na buɗe ya duba yaga kiran da nayi mata kamar dai yadda nayi masa bayani , yana cikin dubawa kira ya shigo dan haka ya ɗauka , bayan gaisuwa naji yace muna genaral , yana faɗin haka ya kashe ya miƙomin wayar ,
Babu wani daɗewa mijin Mamy ya iso asibitin , yasha kuka kamar ranshi zai fita duk iskancin da Mamy ke zubawa baya gani yana san matarshi , jikin gadon Mamy ya matsa cikin kuka yace Mamy Allah ya tsinemawa wanda yayi miki haka , Allah ya baki lafiya mata ta ubangiji yasa ki warke ,
A wahalce Mamy tayi murmushi ta lalabo hannun mijinta tace kayi haƙuri mutuwa zanyi amma ina roƙonka daka yafemin , cikin kuka ya rungume Mamy yace Hajiya baza ki mutu ba wallahi baki mutuwa , Mamy tace naji amma kawai kace ka yafemin , cikin in'inna yace na , na na ya.... Ya fe miki , godiya tayi masa tare da cewa naji muryar Sultana tana ina ? Yace gata nan hajiya ya kamo hannuna ya haɗa da nata ,
Umarni ta bashi cewa da Allah ya fita zatayi magana dani , cike da ladabi ya fice daga ɗakin , Sultana ta kira suna na , nace na'am tace dubamin babu kowa a kusa dani ? Babu Aunty na faɗa cikin girmamawa magana ta farayi bayan na tabbatar mata da babu kowa a wurin :•
Sultana ta kira suna na , nace na'am Aunty , tace tou ki saurareni dakyau , nace inajinki Aunty , Mamy tace kinga whatsapp in nan da kike ganinta ? Wallahi ba ƙaramin haukata mata takeyi ba , shiru nayi ban sake magana ba naci gaba da sauraren Mamy .
Aurena biyu a duniya , ina da shekara 39 akamin auren farko bayan nasha gwagwar mayar rayuwa , iyayena ba masu kuɗi bane suna dai da rufin asiri na ci da sha da sutura , mahaifina ba ɗan kasuwa bane kuma ba wani shahararen ɗan boko bane ba , yana aiki a ƙarƙashin kamfani wani attajiri ,
Matan Babana biyu daga mahaifiyata sai abiyar zamanta , muna da yawa sosai mu "ya "yan babanmu , cikin hukuncin Allah matan gidanmu suna auren mazaje masu rufin asiri , duka matan gidanmu saida aka aurar dasu kaf har ƙanne na ni ban samu mijin aure ba ,
Na tayar da hankalina sosai domin auren nake so ido rufe amma ban samu mai aurena ba , abin ya dameni sosai saina ma daina fita kwata ² kullum ina gida ko a familynmu daina shiga nayi domin na ganɗame sosai saina farajin kunyar shiga mutane ko baƙi akayi gidanmu sai in ɓoye ,
Ina wannan ɓoye ²n ne Allah ya kawomin Bello a rayuwata , Bello abokin Yayana ne duk duniya baida aminin daya wuce Bello shima Bello baida aminin daya wuce Yayana , kowa yana san kowa kuma kowa baya ɓoyewa kowa sirrin junansu , sun yadda da juna fiye da tunaninki domin dai Bello zai iya tarawa da matar Yayana shima Yayana zai iya tarawa da matan Bello ,
Tunda Allah yasa ya ƙyalla idonshi ya ganni ya liƙemin , nasan baƙin halin Bello sosai nasan illarshi kuma nasan miyagun halayyarshi dan haka koda ya furtamin kalmar so ban ansa ba nace bana sansa , shine ya faɗawa Yayana yana so na amma nace bana sansa , shine Yayan nawa yazo ya sameni yayi min kaca ² , nace ni bashi ne bana so ba halinshi ne bana so , kuma kaji tsoron Allah kai kanka baza ka iya bashi auren "yar uwarka da kuke ciki ɗaya , Yaya yace tou ko kinso ko kinƙi sai kin auri Bello idan baki aureshi don Allah ba zaki aureshi dan dole , saikin nemo Bello da kanki , yana faɗin haka yayi gaba abunshi ,
Tun daga wannan ranar sukayi ta kusatsamin asiri na firgice na fita hayyaci na da kaina nake nemo Bello , idan na fita ban ganshi ba ko zankai gobe ban dawo gida ba saina ganshi hankalina zai kwanta ,
A taƙaice dai Bello na aura aurena na farko , ranar da aka kawoni gidan Bello bayan mutane sun watse shima Bello ya shigo da abokanshi da suka rako ango ɗakin amarya kamar dai yadda akeyi ,
Kowa fatan alkairi yaimin da addu'ar zaman lafiya , bayan an gama Bello ya bayyanar min da abokanshi kowa ya faɗamin sunanshi , saida yazo kan *BINNA...* ya dafashi cike da soyayya yace kinga wannan nace Eh yace Binna kenan Bello baya rayuwa saida Binna kamar yadda mutum bai rayuwa saida lumfashi , ina san Binna fiye da yadda nake san kowa a duniya , Binna nawa ne nima nashi ne , murmushi Binna yayi cike da izza amma baiyi magana ba , gaskiya Binna ya shiga zuciyata kuma duk duniya ban taɓa ganin wanda nake so a daidai wannan lokacin ba kamar Binna ,
Sun ɗan daɗe dai suna fira amma har akayi firar aka tashi Binna bai saka baki ba har suka gama suka tafi , bayan Bello ya dawo daga rakiyar su yacemin na tsani Binna na nuna miki shi domin ki ganshi , hawaye ya cika a idon Bello yace tsinan Allah kawai ranar da zan zama ango Binna ya ɗauke budurci ya gudu , saboda kawai nayi ma yarinyar gidan da suka ɗaukoshi a bakin titi suna taimaka mishi ,
Nayi alƙawari saina ƙafa babban tarihi a zuciyar Binna saina tagayyara mishi rayuwa saina zama silar rushewar kaf ahalinsa wanda suka gabata da wanda basu zo ba , saina jefa ƙiyayya mara gogewa tsakaninshi da "yan uwanshi da suke uba ɗaya , nayi alƙawari kuma babu gudu babu ja da baya ko duniya zatashi saina cika muradina ,
Wani irin nishin wahala Mamy tayi har yanzu jinin bai daina ɗiga ba , a wahalce taci gaba da cewa....
Bayan Bello ya gama alkaba'inshi ya hawo gado babu wata sallar godiya ga Allah babu wani abunda ya shigo min dashi irin wanda ango yake zuwa ma amarya dashi a daren farkonsu , haka ya hayeni yaita sassaƙa kamar mai faskare ya samu babban bedi , haka kuma babu wata addu'ar tarawa da iyali ,
Sam banajin daɗin zaman aure da Bello dan na fahimta mugun atsabibi ne , babu sallah bare salati haka kuma bai yadda da ƙaddara ba komai dai malamin tsibbu , ina haƙuri dai ina zama amma sam bana sansa dauriya ce kawai ,
Tun daga ranar da aka kawoni ina amarya ban sake ganin Binna ba saida yazo faɗama Bello an haifeki ,
Duk ƙudirin da Bello yayi akan Sultana da burin mahaifinta akanshi ta faɗawa Sultana , tace wannan shine silar abinda ya rabani da Bello domin na nuna ban yadda ba ya aiwatar da ƙudirinshi akan Binna ba domin gaskiya ina sansa kuma bazan bari a cutar masa da rayuwa ba ,abun yayi ma Bello ciwo dan shine ya sakeni ,
Bayan mun rabu nayi ² Binna ya aureni yaƙiya ina sansa kuma ina sha'awarshi dan haka nayi masa tayin kaina kuma Allah ya taimakeni ya ansa , da sauri na runtse idanuwana , Mamy bata gani na dan haka taci gaba da cewa kullum ni nake isko Binna ko ya nunamin baida buƙata sai nayi yadda za'ayi ya kwanta dani danni kaɗai nasan yadda nakeji idan ina kwance dashi ,
Har na shekara 2 ina zawarci Binna fa ya kame akan bazai aureni ba , dole na haƙura na samu miji nayi aure , tunda nayi aure na daina zuwa wurin Binna , ina zaune da mijina lafiya babu abinda na nema na rasa , saidai zaman kaɗaici yana damuna , wannan dalili yasa na saya babbar waya na fara chating..
Banda friends sosai a whatsapp dan haka dana duba naga wanda ke online saina dameshi da surutu , idan nayi magana sai mutum ya ɗauki tsawon lokaci bai bani ansa ba , na gaji dai nacema wata ƙawata wai sai inyi magana kuyi kamar baku gani ba , dariya tayi sannan tacemin haba hajiyata yaushe rabon duniya da ayyaraye , ni bana cht da mutum prvt ina can group inmu na mata masu duniya , wayayyin mata masu aji masu faɗa a gidan aurensu aji ina ƙaruwa ina zan tsaya saurarenki.
Koda na tambayeta me ake koyawa a group in sai tacemin bara tayi adding ina gani ya kori ji , nace tou , bayan tayi adding ina ta gabatar dani tare da tura hotona , kowa dai yaimin fatan alkairi , a hankali dai nake rayuwa da "yan group in ina fuskantar su ,
Basu da aiki sai turo style na ɗinki , idan sabuwar atamfa ta fito sai an turota , wasu takalman yayi masu zafi suma a turo jukkuna gyaluluwa "yan kunne tsarƙa , bawai na siyarwa bane ba , a , a sune dai na zamani su matan idan suka gani zasuje kasuwa su siya ,
Mace kuwa idan tayi lafiyayen girki saita gama tsara abunta kaf a tebirin cin abinci sai ta ɗauko hoto ta turo a group , idan wanka kikayi kika kai ƙarshen adaka zakiyi hoto ki turo matan group in suna zugaki ,
Shin da Allah mace ta dafa lafiyayyen abinci komai yaji banda bala'e kina kallon yadda naman kaji ke wali ga lemuna masu kyau da tsada an jera ki faɗamin ke kinyi ɗan wake da miyar ƙuli ko kinyi zazafen tuwo kin ɗauka ki tura ?
Mace ta share ƙaton fili ga filawowi ta ɗauko hoto tasha kafirarriyar shadda ko wani ƙaton leshi ko super ke kuma mijinki baida halin ɗinka miki super atamfa rober yake da halin ɗinka miki kuma ita gareki shin kin ɗauka hoto ki tura a group in mata masu duniya ?
Banda ko sisi amma ina da style na ɗinkuna a wayata yafi dubu , duk wata jikkar da ake yayi ko atamfa sabuwar fitowa tana cikin wayata , banda sisi mijina baya dashi na manta da hatta yatsun hannuna ba ɗaya suke ba , duk lokacin da wata ta ɗauko hoton palonta ta turo sai ince ya zanyi na maida nawa haka ?
Kafin wani lokaci na fara tadawa mijina hankali cewa duk mazan duniya suna kishin matansu suna musu sutura sun wadatasu da komai amma duk lokacin da nayi maka magana sai kacemin kai babu ,
Idan yayimin nasiha ya bani haƙuri sai kuma in haƙura , kullum dai abu ci gaba yakeyi dan haka na fita daga group in , amma kash ina fita admin in ta biyoni prvt tacemin taga nayi left lafiya ? Ban ɓoye mata komai ba nace gaskiya ina ganin kayane hankalina yana tashi zuciyata tana min wasi² kuma mijina baida kuɗi shi yasa na fita , dan na lura idan aka turo kayan yayi duk wacce ta sawo idan ta ɗinka hoto takeyi ta turo kowa ya gani ,
Tacemin bara in kiraki nace tou , babu ɓata lokaci ta kirani bayan mun gaisa tacemin duk wanda na gani a group in nan matan aure ne , kuma yadda nake tunanin mijina ma baida hali yafi na wasu a cikin group in , kinsan yanzu ana zamanin rayuwar "yanci kina da aurenki amma kina da abokinki a waje , wanda zai ɗauke miki duk wata hidima taki ,
"Yanci shine babban mutunci da zaran kin rasashi taki ta ƙare , cikin mintuna biyar kacal abokinki zaiyi ya miki abinda mijinki da kike aure bazai miki irinshi ba , yanzu an daina duhun kawai rayuwar ƙyaunci ta gushe , ki riƙe babbar waya kici mai kyau kisha mai kyau ki ɗaura mai kyau ki gyara muhallinki babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani ,
Nace tou idan kuma mijina yace ina na samu kuɗin da nake wannan hidimar fa ? Tace dama ai kafin ki shiga zaki rufe banza a tulun ƙasa zaki riƙa juya rayuwarshi kamar remote sai yadda kikace dashi babu shi babu magana kuma idan "yan uwanshi sukayi mishi magana tou fa ko uwarshi ce zai iya rabuwa da ita akanki , nace tou abokinki me ake bashi yake bada kuɗi haka kuma a ina zan samu abokin , tace abinda zaki bashi yana nan jikinki samun shi kuma nine zan haɗaki dashi , nace tou zanyi shawara ,
Sati ɗaya ina neman mafita kuma kullum saita kirani ta ƙara bani shawara , ƙarshe dai na haƙura nima na antaya a duniyar kwaratanci , social media tana da amfani tana gyara amma illolin sunfi gyaratanta yawa kusan irin mutanen da kuke huɗɗa dasu , tari tayi sosai cikin yanayin wahaltuwa tace ki riƙe wayata a hannunki akwai wata ƙawata dana haɗa da Bello akwai wasu maganganu da nayi da ita akanki kuma na haɗasu domin ina so duk wani shiri nasa ya lalace ƙarshenshi tazo , naso na kafa rayuwa mai inganci a gareki amma lokaci ya ƙuremin , cikin kakari tace kuma Baban Hafsa da Baban Amisty da Binna ...... Daga nan lumfashin Mamy ɗauke ,
Shikenan Mamy tata , ta ƙare ina da tulin tambayoyi da zan mata amma ta tafi inda bazan sake ganinta har abadan duniya , me mutumin yayi mata ? Ya akayi aka ƙwaƙwale idonta ? Ina ƙawarta data haɗu da ita a sanadin whatsapp ? Ya akayi Babana bai aureta ba ? Cikin abokan Bello waye Yayan Mamy a ciki ? Ina iyayenta suke ? Wayyoni Allahna na shiga 3na , tou wai meye take san faɗamin data kira sunan Babana dasu iyayensu Amisty ? Wai ya rayuwata take tafiya a taltala ? Wani irin juyi kaina yayi na saki wani irin gahurtaccen ihu tare da faɗuwa ƙasa somammiya ,
Ihun Sultana yasa mijin Mamy ya shigo da gudu , da taimakon likitoci aka samu aka farfaɗo da Sultana daga duniyar sumar data tafi , a lokacin dana farko har an fita da gawar Mamy waje an sakata a mota ,
Mijin Mamy ya bani wayoyi duka domin duk firar da mukayi da Mamy yaji komai , yace min kije gida sai Allah ya kaimu gobe za'ayi jana'izar Hajiya , mai napep in da kika zo dashi na sallameshi kije kar a nemeni ,
Yana faɗin haka yayi gaba , kamar wata doluwa haka na riƙa tafiya irinta sakarkari har na fito waje , napep na samu na faɗa masa inda zai kaini , har na iso gida kuka nakeyi haka na sauka daga napep in nayi cikin gida abuna , shima Babana ya sallameshi ya tafi ,
Wanka na farayi har na fito kuka nakeyi , zuwa wannan lokacin kuma labarin mutuwar Mamy ya fara zagawa a cikin gari , har su Amisty sunji labari kowa so yake yaji dalilin da yasa aka ƙwaƙwalewa Mamy idanuwa , bayan na fito wanka ina zaune a gefen katifa na kunno recording in da nayo bana gane komai amma fa ga murya nan lafiya zaw kanajin komai , aje wayar nayi na fita nayo alwalla ina dawowa na saka kayana ban shafa mai ba , hijabi na saka nayi sallah la'asar da ban samu yi ba ina gamawa na maida magrib bayan na sallame na ɗauki alkur'ani naci gaba da karantawa dan har yanzu bana cikin natsuwata ga tsoron da naji daga farko ga kuma mutuwar Mamy da aka zare ranta a gaban idona ....
Tsaye yake gaban madubi yasha ƙananan kaya cikakken namiji kenan tsawonshi ma kanshi abun burgewa ne , sanye yake cikin farar riga da bakin wando rufaffen takalmi baƙi yasha stocking da bakin belt ƙamshin turare mai daɗi da dasa farinci mai jefa mutum yanayi marar gogewa a rayuwa sai tashi yake , murmushi yayi yayin daya fara sharce gemunshi yana cewa , sa'a da kanta take kwankwasa mana ƙofa ga duk nasarar namiji mace ce jigonshi , cingom yasaka a bakinshi saida ya ɗan tattauna yace gani nan zuwa gareki An matana......
05/10/2019
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 50
Cike da farin ciki ya juyo , amma me ? Sai yaga *Jiddah* tsaye ta zarge hannuwan ta , wayoyinshi ya ɗauka sannan ya tunkaro ta dan ta hanyar da zaibi ya wuce ta tsaya , cike da kissa tace haba Yaya daga dawowa kuma ina zakaje haka da daren nan ? Inda raina yake so zanje , haba Yaya gaskiya haka an shiga haƙƙina , kallon raini wayau yayi mata tare da cewa a haba ? Umm gaskiya ina so mu kwanta mu huta duk gajiyar jirgi tana damuna , ta ƙarasa maganar tare da san kwanciya a jikinshi , zamewa yayi da sauri ya karkata ya fice daga ɗakin.
Ni kuma bayan nayi sallah isha'e tunanin duniya yazo ya tokaremin zuciya , ikon Allah wato ita rayuwa haka take , Mamy bata taɓa tunanin mutuwa ba kwata ² a "yan wa'annen lokuta , hawaye ya gangaromin daga cikin idona nace shikenan anyi zamaninta an gama , duk saɓawa ubangiji da tayi saboda samun duniya kuma Allahn ya yaddar mata ta samu kuma ta tara , amma ta tafi ta barshi domin ansa kiran mahaliccin ta ,
Me ake ma haɗama a duniyar ? Bayan babu wanda yazo dashi kuma babu wanda zai tafi da komai , anan aka samu kuma anan za'a tafi a barshi , haba mata meke ruɗarmu a cikin duniya ?
"Yar uwa ko kunyi yar jejeniya da mala'ikan mutuwa ga lokacin da zaizo miki ? To kisani mutuwa bata sallama bata jira sai kin gama sharholiyarki wallahi zata iya riskarki a duk yanayin da kike ciki , ba ruwanta da kina aikata alheri ko akasin haka , ya ubangiji ka karɓi rayuwarmu muna masu aikata alkhairi ka sada mu da aljannar ka dan darajar fiyayyen halitta S. A. W , am3n.
Gadai Mamy nan an tafi neman duniyar amma an haɗu da mala'ekan mutuwa a hanya , kai ubangiji kasa muyi kyakkyawan ƙarshe , ko waye ma ya haɗa Mamy da wannan ibilishin ?
Ƙarar wayata naji a gefena a firgice na juya inda take na miƙa hannuna na ɗauko , lambar Dikko naga ta bayyana a saman screen in wayata , ajiyar zuciya na sauke da sauri na ɗauki wayar tare da miƙewa tsaye na karata a kunnena ,
Sai sauke wani irin wahaltaccen numfashi nakeyi mai nuni da nasha wahala , cikin muryarshi maisa natsuwa yace har kin fara bacci ne ? Kukana ya ƙara kwacewa ban bashi ansar tambayar shi ba nace shine ka tafi ka barni.... ?
Murmushi yayi mai sauti cikin murya mai kashe jiki yace in dawo ne ? Da sauri nace Eh , dariyar mugunta yayi yace An mata taji a jikinta tou fito gani nan ƙofar gida , da gaske ? Na tambayeshi sai kin fito zaki tabbatar da haka , da sauri ya ajiye wayata nayi waje da gudu ,
Dikko yana tsaye ya jingina da mota ya rungume hannayenshi a guje na isa inda yake tsaye da niyar in rungumeshi , a wayance ya matsa daga saitina ni kuma na ɗan sassauta gudu na saboda na iso ina ganin ya kauce nima na basar na rumgumi mota ,
Kauda kanshi yayi gefe tare da cewa ya kike ? Nima juya mishi baya nayi ina wasa da ƙasa da babban ɗan yatsana na ƙafa nace aini dana san kaine ma da ban fito ba , buɗe mota yayi ya shiga yana cewa ai dan nasan dama idan nine baza ki fito ba shi yasa nace miki ga Dikkonki ya dawo , ya ƙarasa maganar a daidai lokacin da yake zama a mota ,
Juyowa nayi dan a tunani na tafiya zaiyi , murmushi yayi yace ba tafiya zanyi ba banajin daɗin tsayuwar ne shigo mu tafi , da sauri na zagaya na buɗe mota na kame a gaba , ina rufe murfin motar ya taka motar muka shiga gidan dawakan shi ,
Kusa da motar daya bani yayi parking , ajiyar zuciya ya sauke tare da riƙe sitiyarin da duka hannayen shi biyu yayi miƙa cikin yanayin gajiya tare dayin hamma yace An mata na gaji wallahi yayi maganar cikin murya mai ladaftar da zuciya ,
Murmushi nayi amma banyi magana ba , dan idan inajin muryar Dikko sai inji tawa wata iri shi yasa ban cika magana a gabanshi ba , wayarshi ke ringing dan haka ya ɗauketa daga gefenshi daya ajiye yana cewa tou fa , karkace kaina nayi ina kallon fuskar shi yayin da hasken wayar ya haskaka fuskarshi dan duba mai kiranshi waya ,
Ɗan kallo yayi mai kyau yayin da idanuwan shi ke duba daga saman wayar zuwa ƙasa , zai ɗauka yace nifa bana san kallo da yawa , ki daina kallona haka nan tunda bakya so na , a dai² lokacin daya ɗauki wayar yana cewa inajin ka ,
Tou haka yace kuma ? A , a gaskiya bana kusa kawai kuje idan na dawo Ashiru zai tattaro minsu , ba komai fa kawai kaje abunka , to yayi kyau , ya kashe wayarshi ,
Bayan ya gama wayar ya juyo ya fuskance ni sosai yace An mata mi yasa kika bar mota tayi datti bakya hawanta ? Nace haka nan , hmm tunda bakyasan Dikko motar da ya baki ma bata burgeki ko ? Nace tana burgeni mana kuma ai nahau ta ma , Dikko yace haba An mata ai da kin hau wannan motar da naji a jikina , zansa a wanketa a daren nan ko baki so na ki hau motar nan don Allah inji daɗi kuma ko bakida inda zakije gobe kiɗan hau ta ,
Nace tou , yace yawwa ngode sosai , bayan wani lokaci kuma ya sake kallona yace An mata wai dan Allah mi yasa kike da kunne ƙashi ? Mi yasa bakyajin magana ? Nace me kuma nayi yanzu ? Bama kisan abinda kikayi ba ko ? Nace Eh , jinjina kanshi yayi yace yanzu ina amfanin irin rayuwar da kika koyama kanki don Allah ? Kullum baki da aiki sai ɗaukar tsiraicin mutane ,
Idan an taroki nan sai ki koma nan kina rayuwa kamar baki da kwalwa a kanki , shiru nayi banyi magana ba , cikin ɓacin rai yace ki kiyayeni ranar da nima zan miki tsirara in miki irin abinda kike ma mutane , bana san ɓacin raina akan ki saboda fushi na baida kyau idan har nace zanyi miki hukunci dai² da irin abinda kike aikatawa lafiyayen duka ɗaya zan miki ki mutu , cike da ɓacin rai nace tou ni yanzu waye kuma nayi ma vidio ,
Ƙanƙance idanuwa yayi yace Baban Mardiyya dama shine baƙin cikin da kike cewa zaki dasa mata a zuciya ? Ki bari bana so , nace tou , sake maimaitawa yayi cewa bana so ׳ idan kuma kuma kika sake zakiji babu daɗi , nace tou ,
Hararata yayi cikin salon so , yace to me kuma akayi miki kikayi kuka naga fuskarki duk sai a hankali , ban bashi ansa ba na canja maganar da tambayarshi wanda ya faɗa mishi nayi ma Baban Mardiyya vidio ? Cikin lallausar murya yace babu ruwanki da wanda ya faɗamin idan nace bana san abu kawai ki bari idan baki so mu ɓata , a ɗan zuciye nace tunda baza ka faɗamin ba bari in tafiyata , hannuna ya riƙo yace yi haƙuri An mata , tou faɗamin , yace ni bana san ɓacin ranki Al 'Ameen ne ya faɗamin , gaskiya An mata Al ' Ameen bai jitu dake ba kullum burinshi ya nemo aibunki ya faɗa a gidanmu duk da kince bakya so na ina so ki zama mai mutunci a idon "yan uwana da kuma iyayena kinga idan aka tashi bada labari cewa za'ayi ƙawar Dikko bata da hali mai kyau ni kuma kinga ai bazanji daɗi ba ko ? A kunyace nace Eh , yace tou da Allah ki baryin abu mara kyau duk ki barbaɗawa "yan baƙin ciki yaji a ido ya ƙarasa maganar yana kashe min ido ɗaya na dama , nace tou ,
Tada motar yayi yana cewa bari in ajiyeki haka nan kar ace kin ɓace , a dai² lokacin daya fara tafiya a hankali , yau da natsuwa yakeyin tuƙi yana ƙara jamin kunne na daina shiga sabgar kowa nayi rayuwata ni ɗaya idan banji bari ba kuma zanji hoho a jikina , a ƙofar gida ya ajiyeni yana cemin idan Allah ya kaimu gobe zai dawo , nace tou Allah ya kaimu ya kuma hutar da gajiya , ya ansa da amin ni kuma nayi cikin gida da gudu , murmushi yayi ya wuce cikin farin ciki ,
Yau zuciyarshi ta ƙara tabbatar mishi da akwai soyayyar shi a zuciyar An mata tunda har tasan idan ya daɗe bai zo ba idan yazo zata zo da gudu ta rumgume shi , kuma yace ko tana so ya dawo tace Eh , babu abinda ya kawo haka idan ba soyayya ba , yau kam yana cikin farin ciki.
Washe gari sai 9:30am na fita daga gida domin zuwa wurin jana'izar Aunty Mamy dan naji ance 10:00am za'ayi mata sallah domin kaita gidanta na gaskiya , doguwar hijabi nasa mai hannu ta saukar min har ƙasa mai ruwan jinin kare , dake ina da haske sosai sai hijabin ta matuƙar martabamin fuskata , babu abinda na shafa domin yau ranar ta jimami ce , makullin mota na ɗauka nayi gaba abuna ,
Ina fita naga su Amisty suma sunsha nasu hijaben cikin mota suna tahowa , ganin zan shiga gidan dokuna yasa Amisty tayi parking dan ganin abinda zanyi , a natse na shiga da jakata a hannuna saboda riƙon wayoyin zaimin yawa a hannu ,
A gidan na iske Dikko da kayan training jikinshi ya cire takalma rufaffi ya jiye a gefenshi ya naɗe kafafuwan wandonshi , silifas ne a ƙafarshi ɗorowo { Yellow } masha Allah shine abinda na furta lokacin da na kalli ƙafarshi , hutu dajin daɗi ya tabbata a gareta har wani hurhurun haske takeyi tsabar tasha madara ta ƙoshi "yar gayun ƙafa da ko mai ba'a shafa mata sabar hutawa , ga wani gargasa ya sauko saman ƙwaurinshi "yan yatsunshi masu kyau dan dani keda ƙafafuwan shi babu abinda zaijamin saka wasu takalmi idan ba irin silifas in daya saka a ƙafarshi ba domin yafa burge ,
Yana gani na ya tashi tsaye ya tare da ɗauko takalman daya ajiye a gefenshi ya tun karo inda nake yana cewa ina zaki tunda asuba haka ? Nace rasuwa akayi , Allahu Akbar Allah Allah ya sawaƙe , nace ba rashin lafiya ba mutuwa , yace Ey ai na sani ina nema ma ahalin gawar sauƙi ne , Allah ya kiyaye hanya nace amin , biyoni yayi bai sake magana ba shima ya nufi wurin motarshi ya buɗe but in mota ya watsa takalman ya rufe ya shiga motarshi nima na shiga wacce ya bani wanda yau itace ranar farko da zan fita da ita ,
Tasha wanki tayi kalar ɗaukar hankali , saida na shiga harna sauko daga inda na ajiyeta shima ya sauko yana cewa mintuna 15 na baki ki dawo , tsayawa nayi nace ya kuma minti 15 sai kace kai ka aikeni ? Ban aikeki ba amma wallahi kika wuce lokacin da nace saina ɓata miki rai za'a faɗamin lokacin da kika dawo ai , haba wai mi yasa kake yin haka ne ? Ki wuce lokacin da nace miki sai kiga dalili , cikin hayani nace aure na kakeyi da zaka tsaramin yadda zanyi rayuwata ne ?
Murmushi yayi ba tare daya kalleni ba yace ai da ina aurenki babu abinda zaisa na barki kije gaisuwar wacce aka kwakwale ma ido tirr ya ɓata baki tare da ficewa ya barni cikin mota kamar sakarai.
Da sauri na kalli agogo naga 10:19am , kenan zan dawo gida 10:34 ? Gashi kuma har naci minti 1 , ina da sauran minti 14 yaushe naje har nayi musu ta'aziyya na dawo ? Tsoki nayi kamar kar naje wata zuciyar tace kije kawai kina ɓata lokaci ,
Da gudu na fito daga gidan kamar zan tashi sama , su Amisty suka rufowa motar baya dan a tunaninsu Dikko ne a ciki , lokacin da suka fito bakin titi tuni na ɓace musu ko ƙurata basa gani , hanyar da motar tabi ta wuce suka gaza gano ta ina motar tabi ta wuce ,
Da nasan haka hawan motar nan zai jawomin tashin hankali wallahi da ban hauta ba , ni kuma na hauta ne kawai dan Dikko yayi farin ciki saboda tayi wata huɗu da "yan kwanaki da bani ita amma ban taɓa hawanta na fita sai yau ,
Ina isa ƙofar soro har an dawo daga kai Mamy dandazon mutane kamar ƙasa gaskiya Mamy tayi jama'a a hankali na shiga mutane suka riƙa darewa suna bani hanya duk wanda ya kauce saiya bi motar da kallo kowa ya ƙagara yaga Dikko ya fito dan nace muku lokacin daya siyo motar anyi ihunta a gari duk garin katsina wannan motar Dikko kaɗai keda ita ,
Daga Qerau zuwa ƙofar soro minti biyu kacal ya kaini shima dan nabi a hankali dan motar tana da tafiya sosai , nabar gida 10:20 , na iso ƙofar soro 10:22 harda parking da nayi , manyan mutane suka fara yayyaɓe motar dan cikawa Dikko sheda ba'a iya gane waye a motar saboda gilashin motar duhu gareshi , wa za'a gani ta fito daga motar ? Ɗiyar ɗan caca ,
Tunda na fito kallo ya koma sama a dai² lokacin dasu Amisty suka iso , banbi takan kowa ba na ɗauki jakata na wuce jama'a suka bini da kallo yayin da surutu ya fara tashi ƙasa² danni taron mutane baya hanani tafiya kuma bai ruɗani bai firgitani haka kuma yawansu basa gigitani kuma banayin tafiya inji kamar zan harɗe na faɗi ,saida nakai gaf da zan shiga gidan Mamy naga Bello , kallona yayi ƙasa da sama yace wai Sultana ce haka bakya ko gane mutane ? Murmushi nayi tare da cewa ya za'ayi lafiya ta kasa gane mai bata damuwa ? Magana ce na faɗa masa ina faɗin haka na shige abuna na barshi da dogon nazari ,
Gidan mutuwar sai koke ² akeyi yayin da tabarmin zamar gaisuwar suka rarraba kashi ² , dangin Mamy da tasu , sai dangin mijinta makota sai kuma wasu lafiyayun karuwai suma sunyi nasu mazauni , ahalinta na farawa ta'aziyya sannan "ya "yanta , sai dangin mijinta , ko inda karuwan suke ban kalla na miƙe zan fita wata mata tacemin nan zaki zauna ke ?
A dai² lokacin dasu Amisty suka shigo gidan , miƙewa nayi banyi mata magana ba , tace ke Sultana take ko wa ? Ta tambaya , aka ce mata Sultana , tace nan ne mazaunin mu , juyawa nayi da niyar feƙe mata uwa saidai banda isashshen lokaci dan ina so nayiwa mijin Mamy ta'aziyya , ina ƙoƙarin fita matar ta biyoni ta cakumoni ta baya tana cewa akace ina zakije ? Baki ga inda karuwai suke zaman gaisuwar su ba ? Ban mata magana ba na fiddo wayata daga cikin jakata nace ki duba zaki ga an rubuta Sultana itace lambar wayata ,
Kallona tayi sosai kuma kome tayi tunani Oho sai ta sakarmin hijabi ba tare data anshi wayar ba , ɗan gajeren murmushi nayi da gefen bakina na juya na fito ba tare dana sake mata magana ba , a ƙofar gida nayi ma mijin Mamy ta'aziyya da "ya "yanta maza Bello kuma sai kallona yake , murmushi nayi mishi na miƙe shima ban mishi magana ba ,
Tunda na fito daga barandar ƙofar gidan Mamy ake nunani nice nazo a motar Dikko , wasu kuma na cewa ni karuwa ce amma meya haɗashi dani bayan baya harkar mata , wasu kuma na cewa ɗiyar ɗan cacar nan ne shege mashayin giya ya haifo wannan kyakkyawar , wani yace ai yarinyar shegiya ce tana burgeni domin tanayin karuwancin cikin tako ne , kowa dai da abinda yake faɗa akaina abundai babu daɗin saurare ,
Murmushi mai ciwo nayi yayin dana tunkari mota ta , wato shi karuwanci babban tambari ne da baya gogewa har "ya "ya da jikoki kayi ƙoƙari ka zama na gari domin gori akan karuwanci ciwo gareshi yau mutane da sun san zasu taɓani su kwana lafiya inajin dasai sunci ubana kafin na fito , mota na shiga na karce duk wanda bai ga zuwa na saida yaga fita ta ,
Wuta ² na iso anguwarmu , a ƙofar gida naga motar shi , lokacin 10:33am kai tsaye inda na ɗauko motar na maida ta , lokacin dana fito ban sameshi ba kenan yazo da kanshi yaga lokacin da zan dawo ? Da sauri na wuce cikin gida dan inada abinda zanyi ,
Wuri ɗaya naje da mota amma yau gari magana ta kawai akeyi wata karuwa take tare da ɗan gwamna ta gama dashi ta tsafeshi har ya bata motar daya siyo ta miliyoyin kuɗi , duk inda ka saƙa a gari Sultana ɗiyar ɗan caca kafin wani lokaci kuma hotuna na sun fara yawo a social media da motar dana hau ɗiyar ɗan cacan da yafi ko wane ɗan caca sa'ar rayuwa ,
Al ' Ameen kuwa tuni yaje ya samu mahaifiyar Dikko ya faɗa mata halin da ake ciki dan yaga Dady yayi sanyi , Momy kuwa tayi zafi har ta wuce tafasashshen ruwa , matar Dikko data zo gaisheta itama ta cika ta kawo wuya , tace ma Al ' Ameen ya bari Dikko ya tafi a kamo Sultana zata ƙagi azabar da zata bata , Al ' Ameen yace ai ko yanzu ina iya kawota , Momy tace kudai bari yabar katsina dan koni baya so kamar yadda yake san mayyar yarinyar nan ,
Wane dalili yasa Dikko ya matsamin nahau motar daya bani yau ? Tabbas dan yasan za'ayi magana ne kuma haka yake so dama kowa yasan ina tare dashi shima yana tare dani dan idan babu wata alaƙa dani dashi mai girma me zai haɗani da motar shi.... ?
Yau kuma idan akwai wanda yafi *Jiddah* baƙin ciki bai wuce Momy ba kuma sun tanadin shaglin partyn wulaƙanta ni , Jiddah bata ƙara jin takaici ba saidai Dikko ya tura Ashiru ya maida ita gida , tace bata komawa , koda Ashiru ya faɗawa Dikko tace bata komawa cewa yayi ya barta idan ta gaji ta koma da kanta ,
Tunda naje gidan rasuwa ban sake komawa Dikko ya hanani , sai yau sadakar 3 yace inje amma yau mintuna 10 ya bani , Umar ya aiko ya kawomin kuɗi in bada sadaka idan naje , kuma har yanzu yana gari bai tafi ba saboda kullum rana muna tare ,
Ina ta shiri zan fita saiga Ummu Affan wai tazo min gaisuwa , bayan ta gama ta'aziyyar tacemin ashe kuma sai kikayi mota ? Murmushi nayi ban bata ansa ba naci gaba huɗɗar gabana kenan ba gaisuwar ta kawota ba dan kawai taji labarin mota , saida na gama shirina kaf nace tou zan rufe ɗakin , tace tou bari in tafi idan kika dawo na dawo , fita tayi nima na fita na rufe ɗakin .
Ina fita naga Baba zaune a tsakar gida duk yayi wani kalar ban tausayi , nace Baba baka lafiya ne ? Kallona yayi yace wallahi Mamana gabana keta faɗuwa , nace miya faru ne ? Yace nidai nayi miki alƙawari nabar caca har abadan duniya nace Eh Baba , yace tun daga ranar da mukayi maganar dake da na saka motarki a caca wallahi ban sake zuwa koda wurin caca ba haka duk abokai na bana tare dasu tun ranar ban sake shan giya ba haka kuma ban sake neman mata ba ,
Nace to yanzu meya faru ne ? Yace abun ya dameni ne tun ranar da nayi wannan maganar idan na kwanta bacci sai inga wani mutum tsaye a gabana yana cewa idan baka koma caca ba ajalinka ne zaici gaba da fuskantar ka , ka koma caca kaci gaba da neman mata kasha giya idan ba haka ba zamuyi maka kisan wulaƙanci domin zaka lalatamin duk wani tsari na ,
Shine nace bazan koma ba , jiya itace rana ta ƙarshe daya bani kuma yace yau idan banje gidan caca ba wallahi kasheni zaiyi , murmushi nayi nace Baba kenan wannan ai duk shirmen bacci ne , yace Mamana ba shirme bane da gaske ne dan har sunanki naji an kira a mafarkin yace shine ya toshe miki rayuwa wai ya rufe ƙwalwarki a bakin mataccen kwaɗo , dariya nayi sosai nace ji wani magana Babana ni na tafi saina dawo ,
Saida na fita daga anguwarmu zuciyata ta fara tabbatarmin da ba shirme bane , maganar Baba abin dubawa ce da tunani iri ² na isa gidan rayuwa , ban jima ba na fito bayan na basu kuɗin da Dikko ya bani duka ban rage komai ba ,
Jiki a sanyaye na dawo gida ban samu Baba ba , dan haka na shiga ɗakina kaina sai juyawa yakeyi , wayata na ɗauka na kira Dikko kaf na rattafa mishi abinda Babana ya faɗamin , yace baya nan yaje kano amma idan yayi magrib zai taho in Allah ya yadda , nace tou don Allah daka dawo kazo wurina , yace insha Allah An mata ki kwantar da hankalinki babu abinda zai faru sai alkairi , nace tom saida ya kwantarmin da hankalina sannan ya kashe wayar ,
Ina gama waya da Dikko wayar Mamy ta fara kuka , da sauri na ɗauki wayar ba tare dana san mai kirana ba , ina ɗauka nace Hello , mai magana a waya tace Mamy na samu duk bayanan da kike buƙata , kila bata san Aunty Mamy ta rasu ba , akwai wani kwaɗɗo da aka rufe gawarshi a kwalbar lemu kuma gawar kwaɗon saida aka zuba kwata a cikinta , akwai bokan dake gyara aikin kullum amma yace abu ya warware komai zai iya faruwa tunda har Binna ya fita a caca ,
Anyi ƙoƙarin juya al'ƙamin tsafi ya sauka akan yarinyar da kike magana bokan yace sai ta tsallake sallar isha'e da asuba idan har batayi su ba tana dai cikin tsarki ba jinin al'ada ba itace zata maye gurbin ubanta , yarinyar tana da addu'a gaskiya kuma bata wasa da sallah , kiyi sauri yanzun nan suka kira Binna zasu kashe shi.... Kwalbar da akayi asiri gata a hannuna , amma kiyi gaggawar zuwa gidan........ Ihun matar naji ina ta hello ׳ amma cikin wahaltacciyar murya tace kiyi gaggawa zuwa bayan gidan caca acan za'a kashe Binna ni kuma zanci da sauran....
A firgice na fara kiran wayar Dikko amma sai akacemin a kashe take , wayar Babana na fara kira sai ringing take amma ba 'a ɗauka , wayyoni Allahna na sake faɗawa wata rayuwar , me yasa Dikko ya kashe wayarshi ? Su waye suka kirashi ya fita ? Me akayi ma wacce nake magana da ita a waya ? Wayyo Allahna rayuwa me yasa zakiyimin haka ne .....⁉ 😭
06/10/2019
*JAMILA MUSA...* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 51
*_Godiya ta mussaman gareku ma'abota mutunci da mutunwa , ngode ׳ ina godiya sosai wanda idan nace zanyi ta rubuta ngode ² sai cajin wayana ya ƙare ban gama rubuta godiyar ba ,_*
*_Hassan 80k_*
*_Hassana Masko_*
*_Hafsat Sa'idu Galadima_*
*_Muhammad Musa Muhammad { Na Allah... }_*
*_Halimatu Musa { Uwa }_*
*_Gaba ɗayan shafin nan na yau sadaukar wane ga masoyana a duk inda kuke a faɗin duniyar nan ina sanku ina ƙaunarku kuma ina alfahari daku , fatan alkairi a gareku_*
*_Kuma na gaishe ku..._*
*_Abdulrahman & Ja'afar , Allah ya tabbatar da farin ciki da kwanciyar hankali a gareku ubangiji ya jiƙanku yasa ku gama da duniya lafiya , Am3n_*
Juyawa ɗakin yakeyi dani kamar anayin hajijiya dani , wayyo Allahna ina zan dosa ? Mi zanyi ? Ya Allah ka kawomin mafita ka tausayawa rayuwata kuma ka tabbatarmin da alkairin ka , banda zaɓi sai naka banda wurin gudu ko tsira sai yadda kayi dani ya ubangiji al'arshi taimakon ka nake nema bana san taimakon kowa sai naka , duk abinda ya faru da Babana dani haka yazo a rubuce kuma babu wanda ya isa ya goge,
Da gudu na fito daga cikin ɗaki ina cewa yaku taron "yan uwana kuzo kowa ya biyoni domin dai yau wata baƙuwar rayuwa tana tunkaro mu , ciwon ba nawa bane ni ɗaya , babu babba ba yaro ba matar Baba ba mace ba namiji yau tashin hankalin gaba ɗayan gidan ya tunkaro ku taho Baba yana buƙatar taimako !
Ina faɗin haka nayi gaba da gudu , namiji ɗaya ya biyoni shine babban yayanmu yana ke Sultana ina zaki ? Banda lokacin bashi ansa gudu nakeyi kamar taɓaɓɓiya shima da gudu ya biyoni ina fitowa bakin titi na samu napep nace muje , Yaya yana fitowa tuni mun tafi , shima dafe kai yayi tare da riƙe ƙugu , ganin hakan ba mafita bane yasa ya tari mai machine yace yabi mishi bayan napep inmu.
Muna isa tun kafin napep inmu ta tsaya na dire na tun kari inda nake hango mutanen da basu wuce su biyu ba , sunyi rami sun saka hannun takobi cikin ƙasa tsinin kuma yana sama , bayan sunyi wa Babana wani irin duka a kai ya tafi duniyar ɗimuwa jini sai bin jikinshi yakeyi , bana iya gane fuskar kowa a cikinsu saboda rufe take idanuwansu kaɗai ake gani ,
Mai napep yana ganin haka ya gudu babu shiri dan tsira da rayuwarshi yayin da ni kuma na tunkari wurin haiƙan ina cewa kai na rantse da Allah idan wani abu ya sameshi gaba ɗayanku sai tsinuwar Allah ta tabbata kanku , ku barshi me yayi muku ne ? Me rayuwar shi ta tsone muku ko kune kuka bashi aron lumfashi ne ? Ubangijin al'arshi shine ya bawa Babana aron numfashi kuma shine ya bashi lafiya ku ɗin nan banzaye da ku baku isa ku fitar da ransa ba sai Allah yaso ,
Dariya sukayi sosai tare da cewa tou Allahn ne yaso shi yasa ma ya kirashi kuma yanzu zai tafi domin ansa wannan kiran idan kina iyawa ki kamo ran ki dawo dashi cikin jikinshi , suka ƙarasa maganar tare da ɗauko Babana suka birkitashi saitin zuciyarshi suka ɗagashi sama suka dakoshi saman takobin da ƙarfi , sai kuma suka ɗagoshi suka juyashi yana kallon sama suka sake sokeshi...
Da gudu na isa wurin Babana na durƙusa saman guyawu na , nace Babana karka sake ka rufe idanuwanka babu abinda zai sameka kallarni gani nan nazo Mamanka Uwar masu gida jikina yana ƙyarma na fara ƙoƙarin ɗago Baba amma na ƙasa idan kuma nace zan juyoshi ina tunanin inda bai yanku ba ma zai yanku ,
Babu abinda ke ɗiga daga cikin idanuwan shi sai hawaye yana lunshe ido nace kar kayi bacci ka rufamin asiri karka rufe ido idan ka rufe ido tawa ta ƙare , waye ? Waye wai waye mutumin da kake gani a baccin ka ? Waye ya kiraka wurin nan ? Karfa ka rufe ido yi murmushi yimin murmushi Babana , dakel ya ɗago idonshi ya kalleni cike da soyayya sannan yayi murmushi da gefen bakinshi la'elaha illallah muhammadur rasulillah ya ƙarasa tare da rufe idanuwanshi , nice na ida da S. A. W ,
Kai........ Na shiga 3 na bani na lalace wayyoni Allahna wayyo rayuwa ina zan sa kaina , nace kar kayi bacci shine kayi bacci me yasa ? Me yasa kayimin haka haba Babana , shine zaka tafi ka barni ? Bayan kamin alƙawari baza ka tafi ka barni ba , shine ka tafi ka barni ? Ya ubangiji ka farkar dani wannan mafarki ka tausayamin badan halina ba dan darajar manzan tsira kasa bacci nakeyi ,
Isowar Yayana shima da gudu ya iso wurin cikin tashin hankali yaga Babanmu soke a saman takobi dan suna soke Baba suka gudu , shima wani irin ihu ya kurma hakan ya jawo hankalin jama'a , kafin kace me ? Wuri ya cika sai kuka nakeyi ina ƙarawa tare da cewa wai Allahna , wai Allahna , Allahu Akbar ,
Sauko Baba akayi daga saman takobin har yanzu murmushin da yayimin yana nan akan fuskarshi bai goge ba , kamar kace taso ya taso sai kayi tunanini bacci yakeyi , duk wanda yazo saiya haskashi saboda duhu yayi sosai , ganin ana ta kallemin Babana yasa na cire hijabina na lulluɓeshi a lokacin har Yayana yayi waya an kawo mota ,
Allah mai girma da ƙafafuwan shi yazo wurin nan amma gashi yanzu baya iya tafiya sai an ɗaukeshi , bayan an saka Baba a mota Yayana ya kamoni nima ya shigar dani duk muna zaune a baya yayin dana kwanta saman gawar Baba inaci gaba da kuka ,
Zuwan Mamy gidanmu na tuna ranar data zo ta samu Baba zaune a saman dakali tana bi bi biyyyy , murmushin da Baba yayi mata na tuno da alamar da yayi mata da ido , yau gashi daga Baba har Mamy duk basa cikin wannan duniyar , kai.... Wani irin ihu na sake kurmawa daga nan ban sake sanin abinda ya faru dani ba saidai na farko na ganni a ɗakina Dikko durƙushe a gabana idanuwan shi sunyi jajir Ashiru da Umar suna tsaye a bayanshi .
Tashi nayi cikin kuka na rungume Dikko nace me yasa ka kashe wayarka ? Kiyi haƙuri har yanzu wayar a kashe take banda caji , kauda maganar nayi da cewa kaga Babana ko ? Ranar da nayi faɗa dakai na dawo gida shine Baba yayi kuka yace Mamana shine kika tafi kika barni ? Ni na goge mishi hawaye da wannan hannun nawa na nunama Dikko hannun naci ga da cewa nace masa ai na dawo ,
Nace Baba kana tunanin zan tafi na barka ne ? Bayan bana iya rayuwa saida kai ! Dare da rana safe da yamma yanayin farin ciki ko damuwa halin yunwa ko ƙoshi babu kowa a zuciyata sai kai , farin ciki ya dawo rayuwar ƙunci da damuwa zata kama gabanta , cikin kuka nace shine ya tafi ya barni , ni in rayuwar ƙunci da ɓakin ciki wayyo Allahna , wai Allahna.....?
Inajina kamar inayin rayuwar da bana cikin sahun mutane yayin da farin ciki yake tunkaro rayuwata sai mutuwa tazo ta shafe wannan farin ciki , duk wanda yazo da niyar ya taimakeni sai a shafe labarinshi a duniya , bana so ka rasa rayuwarka ka tafi daga rayuwata kada kaima su kashe ka....
Juyawa Dikko yayi yace ma Ashiru ku jirani waje , fita sukayi , Dikko ya ɓanɓareni daga jikinshi ya zauna kusa dani yace ina Mamanki ne ? Cikin kuka nace ta gudu tabar rayuwata banma san ita ko "yar gidan wane ahalin suka haifota ba , ni ɗaya nake rayuwata a wannan ɗakin babu ruwan kowa dani nima banda ruwa da kowa babu mai so na sai Allah banda wanda zai nunamin kyakkyawa ko mummuna duk rayuwar dana ɗauko ita nakeyin abuna gani yau na zama marainiya.....
Kallona Dikko yayi yace ke ba marainiya bace Allah yana tare dake kuma Dikko yana tare da rayuwarki , duk wanda kika ga ya mutu kwananshi ne ya ƙare ki daina mishi kuka kiyi mishi addu'a , nace to , Dikko yana gidanmu shi ya tayani zama a ɗakina yana min nasiha sai 1:39am yabar gidanmu ,
Bayan tafiyarshi ma na tuna banyi magib ba bare isha'e , fita nayi nai alwallah nazo nayi sallah nayi karatun al'qur ani mai girma tare da roƙawa Babana rahma a wurin ubangiji , har gari ya waye banyi bacci ba kuma banje ɗakin da aka kwantar da gawar Babana ba ,
Tunda safe gidanmu ya fara ɗaukar mutane su Amisty da suka zo ɗakina suka sauka , suna shigowa ni kuma na tattara wayoyina da tawa data Mamy na fita , ɗakin da aka kwantar da gawar Baba na nufa , har anyi masa wanka an shiryashi yana kwance a mankara , ina tsuguniya abinda ya tunomin shine ,
Ranar da muna zaune dashi a ƙofar gida nace Babana ina sanka ina kuma tausayawa rayuwata ranar da za'a wayi gari babu ɗaya a cikinmu , murmushi yazo ya tsayamin a rai da maganarshi da yace min ai bazai tafi ya barni ba , a bayyane nayi magana cikin kuka nace shine ka tafi ka barni...
Naci gaba da kuka mai tada hankali , ina Allah ya jiƙanka ubangiji yasa ka huta , Allah yasa can yafiye maka nan Allah ya sadaka da mala'ekun rahma ubangiji ya kauda kai akan duk laifukan da kayi masa ya yafe ma ya gafarta maka ya baka aljanna dan arziƙin annabi muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wasallam....
Zainab ce ta riƙeni duk gidanmu Zainab tafi kowa tausayi na tana so na , tace Sultana kiyi shiru don Allah , cikin kuka na rungumeta nace don girman Allah ki tasheni daga baccin nan haka nan wallahi zuciyata ta kusa ɓarewa ,
Haƙuri kawai take bani , ina nan zaune a ƙasa kusa mankarar Baba sai kuka nakeyi , bayan wani lokaci kuma maganar Baba ta faɗomin a rai da yace idan har na mutu karki sake kimin kuka addu'a zakimin shine kaɗai zai tabbatarmin da soyayyar da kike min , shiru nayi naci gaba da gumji ina addu'a wa Babana ,
Misalin 08:50am gidanmu ya gama cika duk ta inda baka tunani , 09:00am aka ɗauki mankarar da Babana yake sama kwance za'a fita dashi domin salla tar gawarshi shi , shikenan Baba zai tafi inda bazan sake ganinshi ba bazan sake jin muryarshi ba har abadan abada duk soyayyar da yakemin ya tafi da gaske ya barni.... Sake ɗaukewa nayi na ƙara somewa !
Har akayi ma Baba sallah aka kaishi gidanshi na gaskiya Sultana bata san inda kanta yake ba , zata dawo² shiru har la'asar babu Sultana babu labarinta , duk wani taimako daya kamata ayi mata anyi amma har 5 na yamma bata dawo ba ,
Dan haka yasa Dikko yace a fito da ita a kaita asibiti , Zainab ce akan Sultana sai firfita take mata dama itace ta kula da ita a asibiti lokacin da Dikko ya farke mata mutuntakarta , da taimakon wasu matan aka fitar da Sultana aka sakata a mota da Zainab kaɗai aka tafi sai Ashiru dake tuƙi saishi Dikkon.
Asibiti mai kyau aka kai Sultana likitoci suka rufa akanta dan ceto rayuwata , amma duk yadda akayi saida Sultana ta kwana huɗu bata cikin hayyacinta , ga dai ido tana kallon kowa amma ƙiri² bata iya magana , bata ci bata sha sai kuka , hankalin Dikko idan yayi dubu ya tashi ya lallashi Sultana har ƙarfinshi ya ƙare amma Sultana taƙi tayi magana da kowa , da tsiya² Dikko ke bawa Sultana ruwan tea shima idan tasha saita amayar dashi ,
Zainab itace ta bawa Dikko shawara ko a riƙa ba Sultana fura duk tsiya dai ko tayi amai wata zata tsaya , Dikko yasa Ashiru ya samo fura ake ba Sultana amma ko tasha sai ta dawo da ita ,
Dikko yace haba An mata wai me yasa kikeyin haka ? Gaskiya banajin daɗin abinda kike yi ko nima so kikeyi in mutu shikenan sai ki huta ? Kiji tsoron Allah ki tausayawa rayuwata haka nan mana , ke shikenan abu baya wucewa wurinki ? Kina nufin ke Allah bazai jarabce ki ba ? Ko akanki ne aka fara rashin iyaye ? Ba'a fara a kanki ba , ba kuma za'a gama akanki ba , mutuwa tana nan tana zagayawa tsakanin rayuwar kowa kuma babu bararre a duniya duk wanda yazo sai ya koma , ina ilimin naki da kike alfahari kina dashi ? Wannan shine sakamakon da zaki sakawa rayuwa dashi ? Shi kukan mutuwa da kika ganshi ba'a gamashi kuma baya ƙarewa har sai ranar da rai ya ƙare kiyi haƙuri don Allah .
Murmushi Sultana tayi mai ciwo dan gani takeyi Dikko baima da hankali , ya za'ayi ta daina kukan rashin Babanta ? Ubanda ya ɗauki soyayya duniya ya ɗora mata , cikin "ya "ya sattin da wani abu itace kaɗai ya ɗauki duk soyayyarshi ya bata , taya ma zata manta Baba ? Taya zata daina kukan rashin shi ? Duk ma wanda yace tayi haƙuri ta daina kukan rashin shi wallahi mahaukaci ta ɗaukeshi ,
Banyi magana ba na sauko daga saman gadon na fice daga ɗakin , Dikko ya biyo bayana yana ina kuma zaki ? Banza nayi dashi ban juya ba kuma bansan abinda ya sameni ba bana iya magana sai hawaye , da sauri ya iskoni yasha gabana ina zaki nace ? Kaucewa nayi daga inda ya tsaya na tun kari hanyar fita asibitin ,
Zainab ma tambayata takeyi ina zanje duk banza nayi dasu nayi wurin mota na tsaya dan gida nake so inje , murmushi Dikko yayi mai nuni da baya san abinda nakeyi amma bai sake magana ba ya buɗemin mota na shiga na zauna ya rufe itama Zainab shiga tayi Ashiru ma haka amma yanzu Dikko yaja motar rashin a matuƙar ɓace ,
Har muka iso ƙofar gida babu wanda yayi magana , bayan yayi parking Zainab ta fita nima na fita Dikko kuma bai mana magana ba yaja motarshi yabar anguwarmu ranshi a ɓace , jiki a mace na shiga gida Zainab tana bina baya har ɗakina dan "yan gidanmu sai sharholiya sukeyi yadda kukasan ba mutuwa akayi ba , wayoyina Zainab ta kawomin tare damin bankwana tace Allah ya ƙaddara saduwarmu ,
Taci gaba da cewa yau kwanan Baba 5 da rasuwa ke kuma kina asibiti tunda aka ɗaga mankarar shi baki sake sanin abinda kikeyi ba , wannan gida naki ne babu maishi duk duniya saike tou a cikin kwanaki biyar da rasuwar Baba har sun siyar da gidan sun raba kuɗinsu an bani nidai gaskiya ban ansa ba , kuma wanda ya sayi gidan yaba kowa daga yau zuwa gobe ya tashi .
Murmushi nayi tare da jinjinawa Zainab kai , ansar wayoyi na nayi ta fice ɗakin , tashi nayi na dudduba , kayana masu kyau da tsada duk an sacemin su kaf har kuɗaɗene gaba ɗaya an dauke su , tsoki nayi na fita nayi wanka na wanko bakina nazo nayi sallah magrib na gamesu da isha'e , ƙarfe 10 na dare kuma Dikko baiyi zuciya ba yazo ,
A saman dakali muka zauna , ya ƙaramin gaisuwa tare damin nasiha yacemin kuma idan Allah ya kaimu zaije Abuja kwana biyu zaiyi ya dawo idan ya dawo zai tafi dani , cikin kuka nace to kuma kayi haƙuri ɗazu da nayi maka shiru , jawoni yayi jikinshi cikin sigar rarrashi yace ba komai An mata ai kinsan bana iya zuciya dake ,
Murmushin ƙarfin hali nayi cikin shashshekar kuka nace Allah yasa kaima kar a kashe ka , yace shima da suka kashe shi sai kuma ya kauda maganar da cewa tunda har An mata tayi rashin lafiya nima banajin daɗi ,
Bai dai wani daɗe ba mukayi sallama dashi har mota na rakashi ya bani kuɗi masu yawa yace in ajiye mishi nace ni sata akemin yanzu , yace idan an sace ba komai idan baki da kuɗi na arami ki , nace nidai bana ajiyewa haba yi haƙuri ki ajiyemin , nace kuɗin sunyi yawa bazan iya ajiyewa ba , kallona yayi yace tou ibi wanda zaki iya ajiyemin , nidai ko ɗaya bana iya ajiyewa ,
Tou ɗauka na baki duka , zaro ido nayi banma yi mishi magana ba na wuce da sauri gida , An mata zo , da Allah kizo kiji , ban dawo ba , murmushi Dikko yayi yaja motarshi ya tafi...
Jiya Dikko ya koma Abuja kuma munata waya dashi yana gayamin ya ƙagara gobe tayi ya dawo kuma yacemin yanzu idan zan koma makaranta Abuja zai tafi dani bazan sake makarantar kwana ba , yace shine zai riƙa kaini yana ɗaukoni wai sai muzo katsina juma'a da daddare mu riƙa komawa lahadi da daddare , bawan Allah shi kaɗai ke lissafin shi , haka dai ya ƙari surutunshi yamin saidai safe.
Muna gama waya da Dikko aka aiko kirana , dan haka na ajiye wayar na fita , Al ' Ameen na gani ƙofar gidanmu bayan mun gaisa yacemin mai gida yace nazo na ɗaukeki ki gano wani gida idan yayi miki yana so acan zaki koma da zama , murmushi nayi nace aiko yanzu muka gama waya dashi bai faɗamin zaka zo ba ,
Al ' Ameen yace nidai shine ya aiko ni , ni kuma nace tou bazanje ba na juya da niyar komawa gida , matan dake bayan mota suka fito kaca² muka fara kokowa har sukayi nasarar dannani a mota Al ' Ameen aja muka bar ƙofar gidanmu...
0 comments:
Post a Comment