*_Don Allah nidai ina roƙon alfarma wa mutanen da suke ɗaukar tsohon page ina suna saka mishi sabuwar number , abinda nake nufi misali sai a ɗauki page 1 a saka masa page 2 bayan ba labarin bane ba tou na roƙeki maimin haka dan darajar fiyayyen halitta S. A. W ki daina bana san haka idan Annabin ya isa dake ba danni ba._*
*_Attention , labari mara daɗi daya riskeni kusan kwana biyu da suka wuce bana san yawan ƙorafe² a jikin pages ina amma yau dole tasa ni sai nayi magana , cikakken suna na shine JAMILA MUSA , kuma ni haifaffiyar KATSINA ce iyayena da komai nawa yana katsina masoyana ku saurara kuji , yake "yar uwa me amfani da suna na kina maula to kiji tsoron Allah domin ko ba komai ƙarya haramunne inji manzan Allah S. A. W bazan ja miki Allah ya isa ba amma dai kituna zaki mutu kuma nima zan mutu dani dake duk zamu haɗu gaban Allah SW , bani bace nake waya daku cewa ku turomin kuɗi zan siya data zan yi kaza² ni JAMILA MUSA bani bace ba ƙarya ne kuma ƙarya take da suna na tana ansar kuɗaɗe a hannunku dan haka kuyi karatun tanatsu domin da kuɗin nake buƙata a hannunku bazan roƙeku ba sadai na siyar da littafin amma ba komai nasan ƙauna ne yasa yasa kuke bayarwa amma daga yanzu duk wacce tace muku itace JAMILA MUSA ƙarya takeyi 07016--78 shine farkon da kuma ƙarshen number na ngode sosai masoyana ina muku fatan alkairi...._*
Kaine Dikko ? Inna tayi maganar tana kallon idona ! Shima ni ya kalla yace ƙwarai nine Dikkon da kike magana , ai nasan kaima sunan ka Dikko bakai ba Dikkon gidan gwamna shi nake nufi , har yanzu idon Dikko a kaina yake ya ba Inna amsa cewa shine ai , kaine .....? Umm ya bata amsa , yanzu kaine ɗan iskan yaron nan daka raina mutane ? Murmushi Dikko yayi tare da cewa amma dai ai ke ban raina ki ba , wannan duk faɗar mutanen da basa so nane , na raina mutane bana ganin mutuncin kowa idan na taho bana kaucewa kaza² wannan duk labarin "yan uba ne Dikko ba haka yake ba kayane aka linke ta baibaya shi yasa ake ganin mununsu....
Kai da Allah rufe min baki ɗan iska mara mutunci na tsaneka duk duniya idan akwai wanda na tsana tou ka sani ba kowa bane kaine ...... , bana sanka yau ji nake kamar in yanke kunne na saboda ɓata lokacina da nayi ina waya dakai , har yanzu murmushi yake kuma bai daina kallona ba yace itama kamar yadda kikayi haka ta ɗauki zafi , nuna kanshi yayi cewa irin bakinmu ɗaya itama Momy wai bata san An mata kema baki san Dikko anyi anko kenan to amma ai dani da An mata kowa yana san kowa ke ko kin daina so nane ? Yayi maganar yana tambaya na da kanshi......
Nima murmushi nayi masa tare da bashi ansa ina sanka kuma saina aureka ko za'ayi ruwan bala'e da ƙanƙarar masifa a cikin familynsu wannan ni bai shafeni ba , duka zagi ko habaici baya gabana ko za'a mutu a dawo idan na kafe a hanya ɗaya tou wannan hanyar duk girman katsina babu wanda ya isa yasa na juya zuwa wata , nuna shi nayi sannan na nuna kaina Dikko ina sanka kuma saina aureka cikin amincin Allah da salama duk wanda baya maraba da auren nan tabbas canja maganar nayi cewa zai so ma...
Cikin ɓacin rai Inna tace fita....... Dikko fitar min daga nan , a , a Mama cikin hayani Inna ta fara turance Dikko shima da yaren da tayi magana yayi mata nidai na zama "yar kallo dan banajin abinda suke cewa kuma bansan yadda sukayi ba Dikko ya fita cikin damuwa , kafin na sauko daga saman gado Dikko ya fita daga ɗakin da gudu na fita lokacin harya shiga motarshi ya tada , cike da fargaba na isa wurinshi nace Dikko ka tsaya dan Allah , tsayawa yayi yana kallon can gefen cikin tsananin ɓacin rai.....
Kusa da motar na tsaya na dafa hannuna a saman glass ɗin daya rage bai ida saukewa duka ba , Dikko me Inna tace maka don Allah , dakel ya kalli gabanshi ya busar da iskar bakinshi a damuwance yace ba komai Sulthanah........ Dam׳ naji gabana ya faɗi sunan babu daɗi a bakin Dikko sai naji wani iri haka da ya kirani da Sultana tunda na haɗu da Dikko da rashin mutunci muka haɗu amma bai taɓa kamo tashar suna na ba sai yau lallai abun yaci tira karuwa ta tsira malam.
Ci gaba yayi da cewa mu ɗau haƙuri mu sanya haka ɗin jarabtace , kuma kowa akwai nashi a rubuce , babu wanda ya isa ya musulta ita ƙaddara idan ka rasa karka manta da Allah , ubangiji keda iko mu bayi "yan kallo ne ! Idan kinyi imani da Allah kuma kin yadda akwai samu akwai rashi , kuma idan har kinyi imani ubangiji yake bayarwa kuma shine yake karɓewa yadda da ƙaddara ki tuna wannan shi ake kira da imani , zumuncin mu yana nan insha Allah kije kuma ki ba Mama haƙuri idan har kinyi imani da Allah ki karɓi auren Sultan kuma ki zama mai biyayya wurin mijinki , kije Allah ubangiji ya albarkaci rayuwarki na barki lafiya , yana faɗin haka ya sulala da motarshi a hankali ya fita , bin bayanshi nayi yana fita daga gidan ya tafi da tuƙin shi mai burgeni......
Kai tsaye g r a ya nufa dan ya samu ya sauke damuwarshi , yayin da hotunan abinda ya faru tsakaninshi da An mata ya fara wuce masa ta gaban idonshi , a ranshi kuwa kukan Sultana yaji a ranar da yayi mata babbar kajin ƙauri , tana roƙarshi cewa { kaji tsoron Allah karka ɓatamin rayuwa ka rufamin asiri dan girman Allah , } goge hawayen idonshi yayi tare dayin magana a bayyane amma dake banaji shine banyi haƙuri ba saida nayi kaicon ka Dikko me kaji ? Da nayi haƙuri na barta duk haka bai faru ba nima kaina da ina nan zamana lafiya haƙuri yana da matuƙar kyau a rayuwa kuma yana da wahala babu wanda zaiyi haƙuri yayi nadamar yinshi , amma idan kaƙi haƙuri kayi abinda zuciyarka tace tabbas sai kayi nadama da zaran ka gama aikatawa , wani irin wawan burki ya taka tare da juya kan sitiyari ya nufi inda su Bello suke yau saiya kashe Bello daya kawo mishi An mata wurinshi ! Saiya faɗa masa dalilin daya sa saishi aka zaɓa ya ɓatawa An mata rayuwa ƙalu bale gareka Bello.....
Inna kiyi haƙuri don Allah zan auri Sultan , ko kiyi haƙuri ko kar kiyi babu gudu babu ja da baya aurenki da Sultan babu fashi wallahi , to Inna in Allah ya yadda , amma dan Allah Inna me kikace ma Dikko ? Ai na ɗauka da kika bishi ya faɗa miki na tsani Dikko sakarar banza ballagaza dake dama Sultan yacemin ko a asibiti tare kuke kwana idan har kika bari Sultan yace ya fasa aurenki ƙaryarki ta ƙare asirinki ya tonu.
Haka ya kasance dani ɗan uwana ya fito yayi hidima da rayuwata munyi soyayya mai tsabta auren zuminci shine al'adar familynmu amma tunda ake haɗa aure ba'a taɓa samun maso san junansu ba sai mu domin mu ba haɗamu akayi ba mune muka haɗa kanmu , biki ko suna komai da kika sani duk inda zanje muna tare , munayi ma juna soyayyar da ta zama abin sha'awa ga duk wani wanda ke ahalinmu dan wannan soyayyar ta kafa tarihi mai girma , amma lokaci ɗaya Binna ya shigo rayuwata yayi min karatun yaudara zama ɗaya na ɗauka kuma na kifa kaina ƙasa nace na fasa auren Umar , duka zagi anyi amma na kafe sai Aliyu....
Abun ya zama abun tashin hankali da jimami a ahalinmu , yayin da wani ɓangaren ake kallon abun kamar anyi wani babban rashi , duk wani ɗan uwana ko "yar uwata suka juyamin baya wannan bai dameni ba tunda dai Aliyu yana tare dani , Umar yayi kuka kamar ranshi zai fita wasu kuma suna cewa ko na fasa a aura masani dole , amma nace idan har aka ɗauramin aure dashi wallahi saina daɓa mishi wuƙa ya mutu , kaf ahalina suka juyamin baya bayan an ɗaura min aure da Aliyu kinga dai yadda rayuwar gidan Babanki take kuma nayi haƙuri duk nayi ta tsotse dafin wahalar gidanshi amma kinga daga baya saiya sakeni waishi baya zuwa bikon mace , dakel aka anshe ni a gidan nan Umar kuma baiyi zuciya ba ya dawo yayi aure amma ba auren zuminci ba.
Mazan basu da tabbas ko kace kana sansu daga ƙarshe sai sunyi maka tultular ruwan tsohon tulu suyi maka gori abu kaɗan kayi musu sai suce ka gagari iyayenka ka zaɓesu ka bar iyayenka , wanda ya gagari iyayenshi abun mamaki ne ya gagari mijinshi ? Ko a kuskure kayi abu sai sun goranta maka auno girma da rashin mutuncin Dikko Sultana , bani na faɗa ba duk garin nan kowa yasan halin Dikko ya gwane wurin rashin mutunci baya ganin ƙima ko darajar kowa koya aureki bazai riƙeki da amana ba , gashi yanzu ya faɗa cewa mahaifiyarshi bata sanki nima bana sansa , haka zakije ki fuskanci wulaƙanci da hantara a cikin zuri'arsu , kuma nayi imani wata rana saiya goranta miki yace miki karuwa kuma zai miki gori kinbar uwa kin zaɓi namiji , tazara mai nisa tako ina Dikko yayi miki asalinki da nashi ba iri ɗaya ba , tun ba'asan meye suna ba tunin duniya tasansu , mutane masu arziƙi da cikar asali sunyi kuɗi na tashin hankalin da kwalwarki bata ɗauka , sun nemi kuɗi kuma sun samu sun tarasu tun mutane na bacci , Dikko yafi ƙarfinki kuma yayi miki zarrar da baki kamoshi ki shafawa kanki ruwa ayi miki aski ,
Ke kina wasa da lamarin Dikko ko ? Hmmm dan girman Allah wata rana kije inda yake zama ki kalli mata masu siga da nagarta kamar ba mutane ba tsabar kyawunsu , Sultana har Dikko yana kallon dakakkin mata "yan gayun bala'e masu ilimi wanda suka goge masu aji zai saurareki ? Dan Allah kije wata rana kiga yadda mata kebinshi , ko yace zai aureki ƙarya yakeyi yaudararki kawai yakeyi dan nayi imani Dikko baya aurenki yafi ƙarfinki wallahi , kiyi haƙuri kiyi ma kanki karatun ta natsu ke ba ajinsa bace ƙarya yake ba sanki yake ba kaiki zaiyi kawai ya baroki , tunda dai abinda yake nema ya samu kuma tunda ya more kiyi haƙuri ki auri dai² ke shine zaman lafiyarki.....
Inna wallahi Dikko yana so na , ke yarinya ce Sultana baki san Dikko ba baki da labarin halinshi ne ganinshi kikeyi filinshi kika sani baki san ɓoyenshi ba , duk yadda za'a faɗa miki iskanci Dikko ya wuce inda bakya tunani , hausawa na cewa idan ruwanka baya iskarka wanka sai kayi alwallah ka tashi.....
Amma Inna Dikko baya neman mata kuma na zauna gidanshi har na gama zamana banga wata mace tazo ba , murmushi Inna tayi cewa ai kinji yarintar in banda abinki tunda kina nan taya zai bar wata macen tazo ? Ko an faɗa miki gidan da kika zauna nan ne kaɗai gidanshi ? Ai wayau sukeyi saboda siyasa basa neman mata a gida saidai su haura sauran jahohi su ƙwanƙwaɗi iskancinsu su dawo , shiko Dikko karuwanshi duk ba "yan nan bane ba zuwa sukeyi daga wasu ƙasashe kuma yana gama biyan buƙatarshi zai basu kuɗi su juya abunsu ba tare da wani yaji ko ya gani ba , kinga waye ya ganshi da mace anan bare yace shima manemin mata ne ? hmmm ke yarinya na kiyayeki da Dikko domin haɗarinshi yana girma.
Nidai haƙuri nayi ta bawa Inna kuma na haƙura har a zuciyata na yadda da auren Sultan kuma na bawa Inna haƙuri sosai ta kuma gode tare da sanyamin albarka sannan tabar ɗakina , tana fita na rufe ƙofa na kwanta ni bansan me yasa ba idan har zanga Dikko ko naji muryarshi sai in nemi hankalina da tunanina duk na rasa ina ya tafi amma insha Allah koya kirani bana sake ɗauka na haƙura dashi Allah ya bani dangana.....
Wata irin shaƙara Dikko yayi ma Bello cikin sanyinshi yace me nayi maka don Allah ? Me yasa ka haɗani da yarinyar da kukeyi rikicinku bayan ni bai shafeni ba ? Shiru Bello yayi baice komai ba , Dikko yace faɗamin ina saurarenka kadai lura ina cikin fushi ko ? Jinjina kanshi yayi cewa tou faɗamin kafin in ɓare maka biyu in kashe ka kuma na kashe banza sai ka zaɓa ga mutu ga kuma rayuwa......
Da sauri Bello ya dafa hannun Dikko , sakinshi yayi tare da cewa ina saurarenka , cikin kuka Bello ya faɗawa Dikko saboda yayi fyaɗe wa wata yarinya da suke gidan shine shima Binna ya rama akan matarshi , wannan dalili yasa ya kudiri shima saiya gurɓatawa Sultana rayuwa kasancewarta bugun zuciyar Binna , soyayyar da Binna yake mata yasa duk inda zata tafi yana tare da ita saboda baya so ta shiga cikin wata damuwa ko halaka , Binna baida tsoro kuma bashi da mutunci akan duk wanda ya taɓo masa Uwar masu gida saboda yana jinta kamar wata rayuwarshi , ni kuma ina nan haƙe dashi ina neman sa'a yadda zanyi na taɓo wannan rayuwarshi tashi dan huce raɗaɗin ciwon abinda yayi min , ƙwatsam sai Binna yazo min da labari cewa yau Uwar masu gida taso ta jawo masa fitina da kanta ta zagi ɗan gwamna yaro mara mutunci daya raina mutane dakel aka bashi haƙuri ya haƙura saina lura Binna yanayin maganarshi ya nuna yanajin tsoronka bayan shi kuma bayajin tsoro kowa.
Ganin haka sai nayi amfani da wasu mutane daya ci bashinsu nace musu Binna yace bazai basu kuɗin nan ba yace ya cinyesu idan suna da wani isashshe yazo ya karɓar musu a hannunshi , nine na tunzurasu sukayi ƙararshi aka kamashi kuma ni dakaina na bada kuɗi wa "yan sanda sukayi mishi lullusar fitar hayyaci , kuma nine naje na biya kuɗi nayi belin shi , saina bashi shawara za'ayi caca yazo yayi ya shiga tunda yana da sa'ar caca bai taɓa faɗuwa a caca ba idan yaci kuɗin saiya biya bashin , nasan baida kuɗin da zai saka kafin alƙalamin caca shine nace masa kawai ya saka Sultana , da farko bai yadda ba duk da saida nayi masa asiri kuma bokana ya tabbatarmin da zai sakata a cacar ya kuma bani maganin da zan zuba mishi a abun sha wanda zaisa yayi wasi² , haka kuwa akayi bayan dai Binna ya yadda ya saka Sultana a wurin caca na zuba mishi maganin wanda yasa yayi wasi² ya faɗi a wasa.
Ba wani abu kayi min ba na kawo ta wurinka ba saboda na lura Binna yanajin tsoronka kuma na tabbata ko tsafi yake kai kafi ƙarfinshi saboda kai ka zama dodon duniya kuma kai jan gwarzon maza ne dan kowa yasan ka gaji nagarta , duk wani ɗan ƙaramin tsafin shi bazai kamaka ba dan kai nari ne ko an jefe ka haka nan jifar zataje ta dawo kuma idan taƙamarshi yayi shari'a dakai kune gwamnati bai isa yaja dakai ,
Gwamnatin ubanka Dikko ya faɗa tare dakai mishi wani irin kyakkyawan halbi a baki saida yaci uban Bello da kyau ya kuma sake ɓare mishi haƙora sannan ya kashe Dady da mari yayi haukanshi sosai babu wanda ya bashi haƙuri dan babu mai riƙeshi sunci ubansu kuma suma yau sun ƙara saki da lamarin Dikko saida ya tabbatar sun tashi aiki ya nufi gidanshi cikin ɓacin rai !
Cikin farin ciki kowa ya wayi gari duk wanda ka gani a gidanan yau yanayin farin ciki , kowa sai hidimar gabanshi yakeyi yayin da ni kuma nasha wanka na tsuke cikin wani ƙaton leshi kalar launi mai kyau , nima dai duk da banajin daɗi hakan bai hanani nuna farin ciki ba amma na ciki yana ciki , Inna ma tana cikin farin ciki tana ta hidima da mutanen arziƙinta kai Inna gaskiya wayayyace "yar gayu kisan farko ga kyau ga hutu wallahi baka gajiya da kallonta.
Misalin ƙarfe 2:00pm aka ɗaura auren da taron dubun mutane suka halatta , ina ɗaki kwance ina ta kuka na rasa abinda yakemin daɗi Inna ta shigo ɗakin cikin tsananin ɓacin rai tasha kuka har ta gode Allah , kayana ta fara tattarawa tana kuka idan ta zuba a akwati sai ƙawayenta su ɗauka sukai waje cikin mota su dawo , duk abinda ya shafeni saida Inna ta tattarashi kaf ta ware lefen da aka kawo jiya ta ajiyeshi a gefe wayata ta ɗauka tare da jawo hannuna tana fizgata cikin ɓacin rai haka muka keto cikin taron mutane kowa yana kallonmu , Kaka ta biyo Inna tana cewa Fatima wai kedai ban isa in faɗa miki ba ? Bata bata ansa ba har yanzu kuka Inna keyi , haka Kaka ta biyomu har harabar gidan amma sam Inna bata saurara mata ba ta buɗe bayan mota ta jefani ta kulle da kanta taja motar kamar zatabi ta kan Kawu ta wuce ta fita daga gidan , sauran mutanen da suka zo mata biki suka biyo bayanta.
Har muka zo gidan Inna dake barhim estate Inna kuka takeyi , ƙaton gida ne da akayi mishi ginin zamani gidan "yan gayu an ƙawata shi da filawowi wanda suka ƙara martaba darajar gidan , tanayin parking ta fita nima fita nayi daga motar nabi bayanta ina kuka palo ta zauna tana goge hawayen idonta da tissue a haka taron ƙawayenta suka shigo suna ta bata haƙuri dukansu da turanci suke magana ni dai bansan abinda suke cewa ba saidai inaji lokaci² tana kamo sunan Dikko , haƙuri dai suke ta bata har wanda nake tunanin shine mijinta yazo kiranta yayi suka shiga ciki ƙawayenta suka ci gaba da tattaunawa akan abinda Yayar Inna tayi bata kyauta ba ,
Tayi ƙatuwar cin amana sukaci gaba da maganarsu da yaren da nake fahimta su kuma sun kasa gane saboda nine Inna take magana dasu da turanci tunda tasan ban iya ba , wai ashe ita Yayar Inna jiya itace ta faɗawa Sultan wai ni ina da cutar ƙanjamau lokacin da akayi min fyaɗe aka sakamin cutar shi yasa "yan gidanmu sukayi ta ƙyanƙyanmi na ko kofi na taɓa basa amfani dashi wannan dalilin yasa na shiga bariki kuma abinda yasa na amince da aurenshi wai ni nake faɗa zan yadda na aureshi ne dan na saka mishi cuta , kuma ni karuwar Dikko ce kuma kona aureshi wai ni na faɗa mata bazan daina bin maza ba , da Sultan ya faɗawa Kawu , Kawu yace ƙarya ne ka auri yarinyar nan zaka zauna lafiya amma sam mahaifiyar Sultan tace wallahi baya aurena , Kawu yayi faɗa cewa ya taro mutane daga wurare da dama zasu zo ɗaurin auren ɗansa saiya musu waya yace an fasa saboda wulaƙanci ? Shine Mami tace sai a ɗaura auren da ɗiyar ita Yayar Inna , yanzu da ita aka ɗaura auren duk Inna bata san wainar da ake toyawa ba saida aka ɗaura yau akayi ta mata habaici wai ta lulluɓo "yarta kura da fatar akuya taso ni na auri Sultan na goge masa cuta , sukayi ta faɗin maganganu marasa daɗi akaina shine Inna taji haushi kuma in banda munafirci jiya sune suka tunzurata ta nemo Dikko tayi mishi wulaƙanci , ashe su sunsan Dikkon shine Dikko ita kuma Inna bata sani ba tunda dai kawai shi wannan Dikkon ta ɗaukeshi matsayin ɗa yana girmamata ta gayyatoshi ne ya tayata tayi faɗawa wa Sultana sai kuma ya kira Dikkon gidan gwamna yayi masa concrete worning ya fita harkar Sultana , shine tayi rashin mutunci wa Dikko data gane shiɗin dai ne Dikkon da take nema tayi ma Dikko wulaƙanci a daren jiya sosai wanda kare baya ci ,
Ita ba rashin Dikko bazai auri Sultana ba dama tasan babu maganar Dikko ya auri Sultana gaskiya saboda ba irinshi bace ita , tanayin baƙin cikin zumincin data dagula tsakaninta dashi , sai kuma kukan abinda "yar uwarta ciki ɗaya tayi mata yanzu da bata raye haka rayuwar Sultana zatayi ta wurgegeniya babu mai taimakonta , ita kanta ta sani wato ta bada "yarta ita kuma Sultana ko oho ,.......
Sai dare kowa ya tafi daga gidan shima mijin Inna tafiya yayi ba'anan zai kwana ba , Inna tana cikin damuwa sosai ɗakinta ta shige ta kulle , tou banda abin Inna ita kuma Kaka meya shafeta a cikin wannan matsalar ne ? Wata zuciyar tace baki sani ba kila itama tace wani abu , tou amma me yasa inna ta haɗa hada Kawu ? Oho zuciya tace sudai suka sani domin sunfi kusa......
Duk gargaɗin da Inna tayimin akan Dikko saida na kunna wayata na kirashi , kamar jira yake tana shiga ya ɗauka ya gaggaɓe da wata irin dariya yace amaryar Dikko ai nasan wallahi dudduniya babu maike saini , yaci gaba da dariya cikin dariya yake cewa abinda yasa bana aurenka baƙin rai baka dariya ba fara'a doke² gaka mahaukaci sai aljannu kamar iccen tsamiya hahahaha ashe rabon mahaukaci ce lallai zamuga wasan kura An mata matar Dikko , ke kafiya ni kuma aljannu kamar iccen tsamiya , hmmm inzo Barhim ɗin zaki fito wurina..............?
Dan Allah kuyi haƙuri wallahi ina fama da matsalar rashin caji ne kuyi haƙuri da wannan !
06/10/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA.....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 72
Bazan fito ba na bashi amsa , dariya ya sakeyi kaɗan cewa he ƙarya ne fa gani nan zuwa , kasan gidan ne ? Ko na sani ko ban sani ba damuwa na ne ina zuwa kuma ki faɗawa Mama ina gaisheta kice mata nine zanzo dan na kirata waya bata ɗauka ba , da sauri na miƙe ina tunanin yadda zan shirya kafin yazo naji yana cewa bafa sai inyi wanka ba ina zuwa nan da mintuna biyar yana faɗin haka ya tsinke wayarshi.
Ɗakin da Inna ta shiga na nufa ina taɓa ƙofar najita a rufe , zan juya naji tace Sultana miye ? Inna Dikko ne yace zaizo , wane Dikkon ? Wanda kika sani , tou yanzu ya akayi ne ? Shigowa zanyi inyi wanka , duk kin san zaizo sai yanzu zakiyi wanka ? Nifa bansan zaizo ba Inna yanzu ya faɗamin yana zuwa , tou ki tafi ɗakinki mana , nidai Inna buɗemin don Allah , tsoki tayi tare da tasowa tazo ta buɗe ɗakin ta koma saman gado ta kwanta , bayanta nabi na shiga ciki har yanzu bata daina kuka ba !
Ban mata magana ba na cire kayana na shiga wanka , kafin in fito har Dikko ya iso sai kiran wayata yakeyi , Inna sai faɗa takeyi banda wawanci sai mutum yace zaizo na sirki wanka , ki fito ko baki gama ba , shiru nayi naci gaba da huɗɗar data shafeni , ita kuma Innar fita tayi taima mai gadi magana wai akwai baƙo a waje ya buɗe mishi ya shigo.
Da mai gadi yayi ma Dikko magana cewa yayi ai nan ma yayi suna da yawa ne basai sun shigo ba , mai gadi ya koma ya faɗawa Inna bataji daɗin haka ba , shi kuma Dikko abinda ya hanashi shigowa kar Inna ta sake feƙa mishi rashin mutunci kuma An mata tana fitowa ɗaukar ta zaiyi su tafi idan sun gama ya dawo da ita kar Inna ta fito ta tona mishi asiri cikin bainan nasi.....
Ina fitowa wanka na ɗauki kayana dana cire Inna tace ki ajiyesu dan ubanki ko su zaki maida ne ? Haba nifa ba su zan maida ba , da kika ɗaukesu ina zaki dasu ne ? Zanje in ajiyesu ne , da Allah aje ki wuce ga kaya can ta nuna inda ta ajiyemin kallonta nayi tare da cewa sannu ki daina kuka haka nan kar kanki yayi ciwo , idan yayi ina ruwanki naki ko nawa ? Allah ya baki haƙuri na nufi jikin madubi ina shafa mai sai powder tagumi Inna tayi ta bini da kallo har na saka kaya na shafa tutare kaɗan na ɗauki hijibin da Inna ta ajiyemin na saka na fita ,
Sultana tana fita Inna tayi magana a bayyane cewa wai Dikkon nan nawa ne don Allah ? Nifa na shiga rubibi dan har yanzu wallahi na kasa fahimta shin wai Dikko U DK shine yake zuwa wurin Sultana ko kuwa akwai wani Dikkon bayan shi Dikkon gidan gwamna ne ? Gaskiya ba DK bane tou ita Sultana ina ta samo wannan shi kuma .......?
Cike da zumuɗi na fito na buɗe gaba zan shiga naga ya ajiye filet a saman kujerar da kabeji anyi mishi yanka mai kyau sai cokali mai yatsu babu mai ba magi komai babu a ciki kuma Dikkon waya yakeyi rufewa nayi na koma baya na shiga na zauna , ina zama ya tafi yau bada su Ashiru yazo ba abokanshi ne suke tare , yana gama wayar ya ɗauke filet in yana cewa dawo nan An mata ,
Daga baya na tsallaka na isa gaba na rumgume Dikko sunbatar gefen fuskata yayi zan kwanta jikinshi motar ta fara lilo da sauri ya figi sitirayi dan kaucewa motar gabanshin daya kusa haye mata , zaunar dani yayi saman kujerar daya ɗauke filet in yana cewa zauna An mata karmu faɗi , ƙin zama nayi zan sake tasowa ya danne ni da hannun damarshi ya riƙe sitiyari da hannun haggunshi ya miƙa hankalinshi da natsuwarshi wurin tuƙi yana cewa da nace kar kiyi wanka saida kikayi badai zaki daina raini ba ko ?
Ni ? Waye yace maka nayi wanka ? Nayi wanka a ina ? Ko kana tunanin zanyi ne dan na burge ka ? Sauke hannunshi yayi daga riƙon da yayi min ya ɗauko filet in kabejin daga inda ya ajiyeshi ya ɗoro shi saman jikina yana gyara rigarshi yace ci , me zanci ne ? Koma miye idan kinci bakinki zai faɗa miki , wai kana nufin ni zanci kabeji kamar wata akuya ? Koma dai mece ce ke bai shafeni ba cewa nayi ki ci , haba Dikko ni gaskiya bana ci , cikin ɓacin rai ya kalleni yace ke..... Ɗauka kici , cikin sanyin murya nace haba kabeji ne fa har yanzu ni yake kallo yace kabejin ci ya ƙarasa maganar fuskarshi ba wasa.
Ina gunguni na ɗauki cokali na fara ci , a dai² lokacin da muka iso goruba , amma yau ba gidanshi yaje ba wata kyakkyawar santa suka yanka suka haɗa majalissar su a saman titi sun kashe hanyar ta yadda wani baya wucewa dan duk a saman titin suka ajiye motocinsu su ishashshi duk wani abokin Dikko da nasan yana majalissa a gidanshi na ganshi har dai Yazeed na gani kuma naga irin "yan matan da Inna ta bani labarinsu daren jiya , kallon Dikko nayi da hankalinshi yake kan wayarshi naci gaba dacin kabejin ina yunƙurin amai bai kalleni ba yace idan kikaimin amai a mota saina zaneki , to ai na ƙoshi babu daɗi , ai a ba daɗin zaki cinyeshi kisha ruwa gashi nan a gefenki ,
Salaf ne fa , salaf ɗin An mata cinye shi da sauri , maganin mi to ? Ra'ayi nane kawai na tareki da kabeji kuma ki rufemin bakinki na fara gajiya da magana , Allah ya isa na faɗa ƙasa² naci gaba daci saida na cinye kabejin nan duka , ansar filet in yayi ya duƙo kusa dani yace to me ne ne ? Ngode na bashi ansa to yayi kyau sha ruwa ina zuwa ya ƙarasa maganar yana fita daga motar da filet in yana fita wani ɗan cika sheda ya ansa , shi kuma aka ɗaukeshi a mota suka tafi..... Kuma na kirashi a waya bai ɗauka ba , raina ya ɓaci kuma na ƙufula da yawa.
Gaba ɗaya ɗakin yayi shiru kasancewar ƙarar saukar marin da Momy ta tsinkawa Dikko duk ƙannenshi dake wurin da gudu suka tashi , yayin da ita kuma Momy ke cewa saidai ka zaɓa ko yarinyar nan Dikko ko ni saboda ba so ɗaya ba biyu ba na rabaka da ita baka bari , kai da bala'e ma zaka rabu da ita dan duk duniyar nan idan zata taru bisa kaina bazaka auri karuwa ba sakaran banza da baka san inda duniya ta nufa ba yaushe ka koma sakarai ban sani ba ? Ina tantama anya ma kaine Dikkon dana haifa da ciki na ? Karuwa Dikko ? Me ka gani jikinta wanda harya gigita ka yasa kake neman ka zama wani zararre ?
Mom..... Ƙara yanka mishi mari tayi tace idan ka sake min magana saina shaƙeka ka mutu na huta da baƙin ciki tashi ka fita ka bani wuri kuma kaci gaba da yawo da ita a garin nan ana bani labari , duk ranar dana sake jin labarin ka ɗauki yarinyar nan a motarka saina je har gidansu naci uwar uwarta na faɗa maka sakaran banza marar kishin kanshi tashi ka fita ta faɗa a tsawace , jiki a sanyaye Dikko ya miƙe ya fito daga palon ,
A waje ya samu Nabeela tana ganinshi zata ruga yace ke zo nan , cike da fargaba tazo ta tsaya gabanshi ta fara kuka , kallonta yayi na wani lokaci sannan yace waye yace ya ganni da An mata ? Cikin kuka tace wallahi Yaya bansan waye ba ina toilet ina alwalla naji ta tana magana a waya tana faɗa , bayan na fito ne na sameta tana tura maka text ,
Amma a tunaninki waye ya kirata ? Yaya wallahi ban sani ba , na baki nan da mintuna 5 ya nuna da hannunshi yana ci gaba da cewa ki ganomin ko waye idan kuma ba haka ba zaki shiga3n ki.... Yana faɗin haka ya nufi wurin mota ya shiga abokinshi yaja suka bar gidan!
Lokacin da Dikko ya dawo har na fara bacci shigowarshi cikin mota ya farkar dani , ina tashi na ganshi nace sai in kiraka baza ka ɗauki waya ba ? An mata da Allah bazan ɗauka ba kiyi magani na mana , ai baka dai kyauta ba kuma haka rashin adalci ne ka barni a mota kamar sakara idan kuma na tafi kace na tafi saika shanyani ka kama huɗɗoɗin gaban ka ? Ke kalli idona , kallonshi nayi yace baki lura da yanayi ba ? Ai ni naga lura da yanayin yasa ka barni ni taya ma zan iya ganewa bayan duk yanayin iri ɗaya ne ? Rufe idanuwa yayi dan haka na kame bakina nayi shiru ,
Shi kuma idonshi a rufe yace na shanyaki sai zakiyi ya ya dani ne ? Shiru nayi ban sake magana ba dan yadda ya ɗauki zafin nan yana iya tsintsinka min mari , tafiya ya farayi da motar yana faɗa cewa ni bansan irin iskancinki gaba ɗaya na lura so kike ki mayar dani wani sa'ar wasanki wai me yasa ke kike san cin moriyar rauni na ne ? Kici gaba da haye man ƙaramar yarinya dake. Nidai ban sake mishi magana ba ,
Har muka iso ƙofar gidan Inna Dikko faɗa yake min yana cewa idan kinajin taurin kan ki sake magana kiga yadda zanyi parking nan in lalata miki fata , banza nayi dashi bance masa umm׳ ba , yanayin parking na fice da sauri bayan nayi mishi godiya kamar yadda yake so , har na kusa shiga gida ya kirani , dawowa nayi amma ban shiga motar ba , An mata kin yafemin ? Ya tambaye ni , da Eh na bashi amsa , tou zagayo nan kiji wata magana , zagayawa nayi saitin inda yake na tsaya ina kallon ƙasa.....
Idan Allah ya kaimu gobe zanje kaduna , Allah ya tsare hanya na bashi ansa , to bazaki tambayeni me zanyi ba ? Da kamar ince masa ai bani na aike ka ba , amma sai nace ɗin me zakayo ? Murmushi yayi yace An mata baiwar Allah ba kai tsaye zaki riƙamin magana ba na faɗa miki ki riƙa lanƙwasa min harshe wai ke ni haka nake miki magana ba sanyi ? A shagwaɓe zakice zakaje kaduna ka abarni ne , shiru nayi na kasa magana , ina saurarenki , ni dan Allah bacci nakeji , ai kowa ma yanajin bacci sai kin faɗa zaki tafi idan kuwa ba haka ba zamu kwana a titi , sai kin faɗa da shagwaɓa sannan zaki tafi , nidai kunya ta hanani kallon Dikko bare na maimaita abinda yasa na faɗa , text ɗin da Nabeela ta turo mishi yake dubawa bayan ya ajiye wayar yace ina saurarenki.
Ganin zamu dawwa a haka yasa na rufe fuskata na faɗa kamar yadda yace , buɗe fuskar ki , sauke hannuna nayi , matso nan , matsawa nayi kwantar da kanshi yayi samman murfin mota ya ƙara cewa matso , matsawa nayi da hannunshi ya nunamin nima na kwantar da kaina kamar yadda yayi , ɗaura kaina nayi ina kallon idonshi , shima kallon nawa idon yayi yace tou faɗamin ko baki so inji daɗi ? Ina so , kina so ko ? Eh , yimin magana a shagwaɓe yadda nace ki faɗa , dakel na iya faɗa cikin jin kunya bayan na rufe idona , buɗe idonki ba'a furta zancen so yayin da ido yake rufe ki faɗa a yayin da muke kallon idanuwan junanmu dan martaba soyayya , kallon idon abun soyayyarka yayin furta masa wata kalma da zaiji shauƙi yakan ƙara tabbatar da son mai magana a zuciyarshi , faɗa min kina kallon cikin idanuwana , dakel dai na faɗa , murmushi yayi tare da cewa jeki zanzo kafin in tafi badai haka yaso yaji ba , saida safe na faɗa tare da wucewa gida , saida na shiga gida Dikko ya tafi da tunanin wai me yasa yawancin mata basu iya magana mai tafiya da tunanin namiji ? Ba kallo mai burgewa magana mai laushi babu dai wani salo na tafiya da tunani wai a haka ma ita kunya ta takeji lallai yarinya kina da aiki kima tattara wannan kunyar gefe ɗaya ki ajiyeta saboda Dikko baya ma mace kawaici.
Dakel Dady yaja jikinshi ya leƙo yana ma mai gadin dake faman tsaron su babu dare kuma ba rana magana cewa da Allah ɗan sammin aron wayarka , ba wani damuwa ko tunanin abinda zai faru ya miƙa mishi waya , lambar matarshi yasa ya kirata , saida ya tsinke ya sake kiranta ana biyun ta ɗauka , ko gaisawa basuyi ba yace mata ɗan ƙawarki yana nan yana cin mutunci mu akan wannan tsinanniyar yarinyar dana faɗa miki tana san ta anshi kuɗin gadon su dan haka ki faɗawa ƙawarki tasa Dikko ya sakemu dan wallahi idan na ƙara biyu awurin nan mutuwa zanyi , cike da damuwa tace Dikko bai sanka ba ? Ya sanni mana ɗan iskan saida yacemin ma albarkacinki naci cikin kuka Dady ya ida cewa amma duk aya sanni yake ta ganamin azaba ba dare ba rana !
Maman Hafsa tace amma dai Dikko baida mutunci , bara zan kira Maryam ɗin dan na tabbata duk iskancin da Dikko keyi garin nan bata da labari ɗan iska mara mutunci dako bakin duniya bai kamashi , Dady yace dama banda abinki ya za'ayi bakin duniya ya kama irinsu wanda basu fito ba saida suka shiryama duniyar , ki kirata an fara kashedi kuɗin zai ƙare ya tsinke wayar.
Ina shiga gida a saman idon Inna na shiga kuma ta zageni sosai sannan ta shatamin layi karna sake bin Dikko fira idan ba'a ƙofar gida ba cikin palonta idan bayayi nan tou ya kama gabanshi , nace to na canja maganar da cewa kin daina kukan ne ? Dan bana so azo inda zata zagi Dikko , bata bani ansa ba dan haka nahau saman gado na kwanta kusa da ita ban daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗaukeni da tunanin rigimar Dikko.
Misalin ƙarfe 7:45am Momyn Hafsa ta kira Momyn DK tana ɗauka Momyn Hafsa tace tuba nake dai na tasheki bacci da safiyar nan dan Allah ina tare da damuwa ne nake ta Allah² gari ya waye , Momy tace ba komai , Mom Hafsa tace Hajjaju Dikko ne da mai gidana , Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un nan kuma ya dawo ? Eh , meya haɗa Dikko da mijinki Mariya ? Wata karuwars..... Ah ah Momy ta faɗa dan dakatar da Maman Hafsa tace Dikko bashi da karuwa ni kuma ban haifi mazinaci ba Allah ya tsaremin ɗana baya huɗɗar mata , me kuwa zai haɗashi da karuwa da har zaiyi riƙici da wani akanta ? Allah ya baki haƙuri ba haka nake nufi ba , Momy tace duk ma yadda kike nufi ki bari zan kira Dikko yanzu....
Kiyi haƙuri ki fahimci maganar tawa , Momy tace nafa fahimta kawai dai banji daɗi ba kike cewa wai karuwarshi kamar ba ɗanki ba ? Haba Mariya , haƙuri dai Mariya ta ƙara bawa Maryam sannan suka ajiye waya Momy bata bar Mariya ta gama maganarta ba , tsoki Momy tayi bayan ta tsinke wayarta , taci gaba da faɗa ita dai Dikko yana so ya kasheta ya hana mata zaman lafiya , idan ta rabashi da nan sai kuma ya koma nan Dikko ba ƙaramin yaro ba amma ya hana mata kwanciyar hankali , yanzu banda iskanci kuma meya haɗashi da mijin Mariya Jabeer , wayar Dikko ta fara kira tana faɗa amma sai Jiddah ta ɗauka tace mata tunda ya fita masallaci har yanzu bai dawo ba ,
Tun tsakar dare Bello ya fara tanɗar harshe kamar kwarton da yaga wawan zama , yana dariya ma Dady cewa saina tona maka asiri ׳ harararshi Dady yayi tare da cewa to ka tonamin dan wutsiyar gyatimin ka , dariya Bello yayi ta irin ya saki layi yana ci gaba da cewa saina tona maka asiri , a haka Dikko ya sami Bello yana ta abu kamar dai yaɗan zare haka....
Yana ganin Dikko yace Baba wannan Baban ne , Dikko rai babu haƙuri yayi ma Bello wani irin kallo yace nine Baban naka .....? Umm ya faɗa tare da gaggaɓewa da dariya yace ba kaine ka kamoni ba kayi man duka , kallonshi Dikko yayi tare da cewa ko kana so na ƙara maka ne ? A , a Baba na bari , tou me kayimin na dake ka ? Dan abinda shi Dikko ya fahimta kila kamar Bello ya tsorata da yawa yasa ya ruɗe , shi kuma Bello cewa yayi in faɗa maka gaskiya ? Da ƙarya ka faɗamin ? Inji Dikko , Bello yace wallahi nine nake so ta zama karuwa ,
Kuma nine na kashe Binna sa'ar caca na yana tafiya da rayuwar cacarsa dama boka yace zai haɗa sa'a tane a ta Binna danshi mai sa'a ne yacemin kuma idan har Binna ya daina caca shine komai zai lalace min bazan sake samun sa'ar caca ba kuma rayuwata zata zama kamar walƙiya idan har Binna ya daina caca , shine Binna ya fita a caca komai nawa yaja baya ,
Dana koma na faɗawa boka cewa komai ya taɓarɓare min kuma mutane suna gudu na , shine boka yace idan Binna bai dawo caca ba rigar da zan saka komai na rayuwa saina nema na rasa , dana ce Binna ya dawo caca ya ƙiya , shine na sake komawa na faɗawa boka shine ya tura aljannu suna bawa Binna tsoro a bacci ko zai dawo amma ya ƙiya.
Mafita na ƙarshe shine boka yace mutuwar Binna itace tsira da kuma salama a rayuwata shine na kashe shi , Dikko yace ai bashi ka kashe ba kaine ka kashe kanka , labarin kwalba ya akayi yazo wurinka ?
Malami karuwa da mawaƙi duk basu da amana , yayin da suka kama wani a lokacin suke watsi da duk wani mutunci dake tsakaninku , malamin da suka ba kwalbar ni malami na ne kuma nine na haɗashi da Mamy , da kwalbar tazo hannunshi shine ya kirani mukayi ciniki ita Mamy ta bashi naira dubu hamsin akan ya warware matsalar shine ya faɗamin ni kuma nace zan bashi naira dubu ɗari biyar ya bani kwalbar , shine nakai na anso ,
Aljannu goma ne a saman kwalbar suna gadinta daga nan har illah masha Allah , wannan sammu makarinsa ɗaya ne inji boka , saukar alƙur'ani mai girma tsawon wata ɗaya kullum sai an sauke alƙur'ani sau goma duk rana ɗaya a yanka raguna goma bayan an buɗe kwalbar kuma ba fasata za'ayi ba domin kwalbar itace matsayin ƙwalwar ita Sultana shi yasa akayi cushe² a cikinta an tosheta ta yadda iska baya shiga , buɗe kwalbar za'ayi a barta a buɗe daga ranar da aka san za'a fara sauka , sau goma za'a sauke fa kuma har tsawon kwana 30 za'a yanka raguna goma duk rana a raba ɗanyen naman sadaka.....
Yanzu ina kwalbar take ne ? Tana ɓoye a wani wurin sirri nine kaɗai nasan wurin , na ɓoyeta tun bayan lokacin dana anso ta daga hannun malam , fita Dikko yayi ya nufi gidanshi , bayan yaje yace Ashiru yaje ya ɗauki Bello ya kaishi gidanshi ya ɗauko saƙo , Ashiru yace to , Dikko ya wuce ciki.
Da wani irin ciwon kai yau Inna ta tashi ko motsin kirki bata iyawa tun jiya take kwarara amai kafin gari ya waye tayi laushi ko magana bata iyawa , ina zaune kusa da ita sai sannu nake mata bata min magana tadai bini da ido tana min kallo mai nuni da tanajin tausayin rayuwata ,
Mai gadi naji yana ta sallama daga waje dan haka na tashi na fita , nayi baƙi a waje shine abinda ya faɗamin , kai tsaye na nufi ƙofar gida wani mutum ne zaune a saman machine kusa dashi naje muka gaisa bayan mun gaisa ya ciro takadda daga aljihunshi yace gashi , nace ta miye ne ? Yace ki ansa ki kiranta mana , kaida ka kawota kaine zaka buɗe ka karanta , kallona yayi sannan yace sammaci ne ƙanin Babanki yana tuhumarki da sa hannunki a lalacewar tarbiyar "yar sa sai kuma maganar kuɗin gadonsu daya ji labari kin ansa kin handamesu.......
Kallonshi nayi amma ban anshi takaddar ba nace ina zuwa , komawa nayi ciki na ɗauki wayata na kira Dikko , saida kiran ya kusa ƙarewa ya ɗauka , fita nayi waje babu ko gaisuwa na fara rattafa mishi damuwata , shima yana cikin damuwa domin bayan ya koma gida Jiddah ta faɗa mishi Momy tayi waya , bayan ya kira Momyn ne tace yaje tana kiranshi , da yaje tayi mishi zagin girgizar "ya "yan magarya tare da faɗa masa cewa kashedi na ƙarshe tayi masa akan Sultana idan ya kuskura ta sake kiranshi akan Sultana zata mishi wulaƙancin da katsina bazata iya ɗauka ba , yana cikin tashin hankalin zagi da tunanin taya zaiyi ya rabu da An mata ita kuma ta kirashi tana faɗa mishi tata matsalar kuma shine take so ya sama mata natsuwa , ashe shine ma ya kamata ya koyi aje damuwa 2 a zuciyarshi ba An mata ba , damuwar shi , damuwar An mata , ajiyar zuciya ya sauke sannan yace kina ina yanzu ?
Ina Barhim , ina shi mutumin yake ? Yana waje , tou ki taho dashi mu haɗu daku wurin government house yanzu zan fito , ciki na koma na ɗauki hijabi na ko Inna ban faɗa mawa ba saboda na gani tana cikin damuwa bai kamata na ƙara mata wata damuwar ba amma nasan dole zan mata laifi tunda tace na daina bin Dikko kuma gashi zan bishi , kuɗin napep na ɗauka na fita waje ,
Ina zuwa wurin mutumin nace masa tou muje , ai ba yau ake nemanki ba sai sati mai zuwa zakije , Ey wurin Babana zamuje ka bashi kaga bai kamata ni na anshi sammaci a hannuna ba , kuma kaga daka zo bani ya kamata ka nema ba , iyayena zaka nema idan kuma ina da aure mijina , ina Baban naki ne ? Muje ai wurinshi zamuje yanzu , tada mashin inshi yayi yace in hau nace masa mu fita waje dai na samu napep.
Ina gaba yana bayana saman machine har muka fito wajen estate in , na samu napep na shige ko a napep mune a gaba yana bin bayanmu da machine har muka isa daga nesa na hango motar Dikko dan haka na sauka a napep bayan na bashi kuɗinshi...
Dikko yana hangoni ya matso inda muke tsaye , ta wurina ya tsaya tare da sauke gilashi , matsawa nayi kusa da motar ina cewa mutumin tou taho , ƙin tahowa yayi , ni kuma na sake cewa kazo ka kawo mishi yana jiranka ,tada machine ɗin shi ya farayi Dikko yace ya akayi ne ? Ya nuna kamar baima san abinda ya faru ba , wai kotu ake ƙarata wai ana tuhumata da lalata tarbiyar wata kuɗin gado duk ni ɗaya , a dai² lokacin da mutumin ya tashi machine ɗin shi Dikko yace kai zo nan , kashe machine ɗin yayi ya sauko dan yasa ko ya tafi zai bishi ne kuma idan ya bishi da damuwa.
Daga ɗan can gefe ya tsaya ya gaishe da Dikko , bai ansa gaisuwar ba yace ya akayi ne ? E dama ranka ya daɗe wai ita ake nema a kotu dan ansa wasu "yan tambayoyi , wane irin "yan tambayoyi ? Wani ƙanin Babanta ne yake ƙararta , biro Dikko ya ɗauko gefenshi ya bani yace miƙa mishi ya goge sunanki yasa nawa , ai ranka ya daɗe ba kai ake nema ba , Dikko yace wanda ya kira uwa ya kira ɗanta ne , haka zalika duk wanda ya nemi mata mijinta ya nema rubuta suna na ,
Ƙin ansar biron yayi tare da cewa tuba nake ranka ya daɗe , miƙo hannu Dikko yayi cewa tou kawomin , miƙomin takaddar yayi Dikko yace kai zaka kawota da kanka , matsawa yayi ya miƙa mishi , duba takardar yayi bayan ya ansa yace to jeka zamu zo rana irin na yau ko ? Yace E ba damuwa kuɗi Dikko ya bashi masu yawa godiya yayi sannan ya tafi...
Taho mu tafi , zagayawa nayi na shiga muka tafi gida , a hanya nake faɗa masa Inna bata da lafiya kuma tana ta amai tun jiya kuma na faɗa mishi kuka tayi sosai shi yasa bata lafiya , addu'ar neman samun lafiya yayi mata daga haka bai sake magana ba saini dana isheshi da surutu har muka iso gida , bayan munzo ne yake cemin ya fasa tafiya saboda wani uziri daya taso mishi ,
Sannan kuma ya tambayeni wai zan iya zama da Jiddah ? Ina zan zauna da ita ? G R A kinga ban gama aiki goruba ba kuma ni inaso muyi muyi aure , kallon gefe nayi nace idan munyi auren ka riƙa bani kabeji ? Murmushi yayi yace ke wallahi wannan kabejin nine nakecin shi a yadda kika jishi , babu daɗi ne ? Umm ba daɗi , zaki zaune da Jiddah ? Idan nayi maka laifi saika dakeni a gabanta ? A , a sai mun shiga ɗaki zan zaneki a saman gado kina so ko ? Tsoki nayi zan fita motar ya riƙoni yace An matana yi haƙuri kar kiyi fushi wasa nake miki fa , tafiya zanyi kar Inna ta tashi bana nan , naji zaki tafi amma kalloni , kallonshi nayi yace kin gode ? Ey , idan munyi aure ma idan kika zanu zaki gode ya ƙarasa maganar yanamin kallon tsakiyar fage.....
Fizge hannuna nayi na fita , dariya Dikko yayi yana An mata zo , ban dawo ba yace ki gashemin Mama zan dawo anjima ki ajiyemin abun daɗi kinji ko......? Ban juyo ba kuma ban bashi ansa ba na shige gida , murmushi yayi ya rufe ƙofar da Sultana ta bari buɗe sannan ya wuce , yana tunanin anya bazai bari ya gama aikinshi ba ? Kamar idan ya haɗa An mata da Jiddah zata sha wahala kuma gashi shi ba mazauni ba , wata zuciyar tace kawai cakuɗesu tayi hankali ma........
Mutumin daya kawo ma Sultana sammaci gidan Baba ƙarami ya nufa ,
08/11/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 73
Zaune suke ƙofar gida a saman dakali yana korawa Baba Ƙarami bayani cewa Dikko ne ya anshi sammacin daya kaiwa Sultana , gyara zama Baba ƙarami yayi tare da cewa ko shi gwamnan ne da kanshi ya ansa bai shafeshi ba shidai Sultana yake ƙara kuma koshi gwamnan ai yasan gaskiya in banda yarinyar nan ta gaji iskanci har tasan ta yadda zata haɗa wani da wata yayi iskanci ? Duk wannan bai isheta ba gidan da ni kaina ban sanshi ba amma ita taje ta ganoshi ta tattara kaf kuɗaɗen gado kuma tayi ruf da ciki dasu !
Amma kai waye yace maka ta anshi kuɗin gadon naku ne ? Jikar gidanmu ana ce mata Hafsa itace suka zo da wata yarinya ana ce mata Amisty , a saman wannan dakalin suka sameni cewa idan naga Sultana dan girman Allah inyi mata magana tasa a sako mata Dadynta , dana tambayeta abinda ya haɗa Babanta da Sultana sai ta koramin bayani ta kuma ƙara da cewa kuma ta anshi kuɗin amma har yanzu ba'a sako Dadyn ba shin saini in zura mata ido ta cinye duk wa'annan yawan kuɗin a cikinta ?
Kuma iskancin Sultana bai tsaya nan ba saida tabi hanyar da aka lalatamin tarbiyar yarinya , ita kaɗai taji tana ra'ayin iskancinta taje tayi babu wanda ya hanata amma akan me zata gurɓatawa wata da bataji bata gani rayuwa ba ? Abokin firar nashi dai bai sake wata magana ba saidai sauƙi daya nema tare dayi ma Baba ƙarami sallama ya tashi , Baba ƙarami kuma yaci gaba da bunbunai shi ɗaya.
A kwance na samu Inna tana waya da zani ɗaurin ƙirji da alama wanka tayi , gefenta na zauna ina tunanin rayuwar da zanyi a gidan Dikko idan har Allah ya ƙaddara na zama matarshi , zama dani da Jiddah ? Matar data zo har ƙofar gidan ubana suka ɗaukeni sukaje dani sukaci zarafi na ? Mahaifiyar Dikko ta tsaneni babu gaira babu dalili ga Al ' Ameen kuma tunda har mahaifiyar Dikko bata so na tou kuwa taya su "yan uwanshi zasu so ni ne ? Wace irin rayuwa zan fuskata ? Ya za'ayi idan har Jiddah tamin wani abu shin na iya ramawa ? Idan kuma na rama ta faɗawa Dikko ya goyi bayan matarshi ni ina zan saka tawa rayuwar ne ? Tunda dai nayi imani bazai goyi bayan ni bare ba ya yage bayan "yar uwarshi da sukayi auren zuminchie da mahaifiyar Jidda data Dikko uwa ɗaya uba ɗaya shin ya zanyi ne............?
Maganar Inna naji tana cewa ina kikaje ? Nan baya na zagaya na bata amsa dan bana san ina tunanin Dikko ana min magana wallahi , Inna tace ai kin kyauta ni tashi akwai ƙullun koko a palo nima yanzun nan aka kawomin shi yau da maitar koko na tashi a rayuwata saida na samu ƙullun nan hankalina ya kwanta kije ki dama min shi.
Inna ina zan dama miki wani koko ? Nan gidan mana , kinga karmu tsaya ba shari'a wahala ni ban iya ba Allah ya sani kuma Dikko yace yana gaisheki na faɗa mishi baki lafiya yace zai dawo anjima kuma a ajiye mishi abun daɗi..... Ya zo ne ? Eh , shine nace ina kikaje kika cemin kin zagaya baya ? Tayi maganar tana murmushi , nima murmushin nayi mata amma banyi magana ba.
Tashi tayi ta saka kayanta aka ɗan matsa turare aka kashe ɗauri ta fita palo , tashi nayi nabi bayanta a saman kujera nasameta zaune tana waya da mijinta , bedroom in na koma na kwanta nasan dai kafin in tashi bacci tasan "yar dibarar da zatayi wanda zamu ci ma cikinmu !
Biye yake da bayan Bello saf da ƙafa har cikin tsakiyar filin tsakar gidanshi , dakel Bello yake tafiya kamar zai kife Ashiru na biye dashi har cikin ɗakinshi , gaban wani ƙato bedsite Bello ya durƙusa a gajiye sannan ya fara ƙoƙarin turashi gefe ɗaya , Ashiru yasa hannu ɗaya ya janyeshi gefe Ashiru na janyewa Bello ya ɗafe wani bargo sai ya janye wani katako wani zurmemen rami ya bayyana mai tsananin duhu da matsakaicin zurfi.
Kwanciya Bello yayi ya zura hannunshi a cikin ramin ya jawo kwalbar kallo ɗaya Ashiru yayiwa kwalbar ya fara kakarin amai saboda yadda zuciyarshi ke tashi da tsikar jikinshi , bayan ya ɗauko ya miƙowa Ashiru yace kai kaci uwaka riƙeta muje , rungume kwalbar Bello yayi suka fita daga gidan.....
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un ta faɗa da wata irin ƙara mai tayar da hankali tare da tashi zaune saman tsakiyar gado tana sauke wani irin numfashin wahala , da gudu Inna ta shigo tana lafiya ? Wai , wai , wai tayi tare da goge zufar goshinta tana numfashi a wahalce , ke Sultana lafiya ? Har yanzu numfashin ta bai daidaita ba , Inna tace wai mene ne ? A tsora ce nace wani ne ya biyoni a bacci wai zai kasheni kuma idan inajin wasa idan na tashi naje Qerau yau zanga karuwa ɗaya ta mutu sanadin kwakwale mata idanuwa da yayi kamar yadda ya kwakwale idanuwan Mamy , cikin faɗa da ɗaga murya Inna tace ki koma baccin ki faɗa masa baki kasuwa kuma babu wanda ya isa ya kasheki , ta ƙarasa maganar tana kwantar dani ta lulluɓeni da bargo.
Wayyo Allah Inna da Allah bana so wallahi banayin bacci , cikin hayani tace duk abinda ya cimmiki nasara a bacci a zahiri sai yayi nasara a kanki babu wani maiyi sai Allah haka babu mai rayawa da kashewa idan bashi ba ki faɗa masa baki mutuwa sai kwananki ya ƙare..........................!
Saukowa nayi daga saman gadon jiki a sanyaye nace nidai banajin wani bacci , toilet na shiga na watso ruwa dan inɗanji ƙwarin jikina , ina fitowa ko mai ban shafa ba na zura kayana ina gama sakawa na wuce wurin Inna mukaci abinci tare...
Duk wani mahaluƙin dake anguwar Qerau yau kam yana cikin tashin hankali abu ba'a magana anguwar ta cika faful sakamakon alhinin safkar idanuwan wata matar aure duk inda ka leƙa gida ko bisa santa labarin akeyi bayan an cire idanuwanta aka zo aka yadda ita a saman santa....
Tun asuba aka tsinceta mutanen da suka fito domin zuwa masallaci sallar asuba sune suka fara ganinta dan haka a hankali labari ya fara zagawa cikin anguwa kafin wani lokaci kuma gaba ɗaya gari ya ɗauka ba'a kaiga kaita asibiti ba tace ga garinku nan ,
Wannan tashin hankali ya zama baƙon al'amari ga mutanen wannan anguwa anyi mutuwa maimakon addu'a ga mamaciyar sai zaƙule²n abinda ya kaita ga afkawa bariki akeyi , ita dai mamaciyar tana da aure da yaranta biyu kuma tana zaman lafiya da mijinta , bakin abinda Allah ya rufa mishi asiri yana riƙe da gidanshi bakin iya gwargwadon karfinshi.
Wannan matar aure dai ta samu damar antayawa a harkar bariki ne sakamakon gurɓatacciyar ƙawa data tsinta a saman yanar giza gizo , mamaciyar ta shiga harkar bariki ne a sakamakon ƙorafi wa ƙawar tata ta hanyar nuna gazawar mijinta a wurin riƙon gidanshi.
Bayan ta tsinci wannan ƙawa a saman iska sun ƙulla alaƙa mai girma ta yadda kowa baya iya ɓoyewa kowa sirrinsa , wani zamani ne wanda Allah ya kawomu wai sai kaga mace a duniyar nan duk abinda taci ko tasha saita ɗaukeshi hoto ta turawa wata , duk ƙawar da kike tare da ita ta fara miki wannan tsire²n na ɗaukar abinci ta turo miki shi ta waya wannan ba ƙawa bace ba maza kija mata layi ba abokiyar tarayya bace ba idan har tanajin ita mai kirkice to ta zobo abinci a kwano ta bada a kawo miki bawai ta turo miki ta waya ki gani ba , kina gani miyanki ya fara tsinkewa saidai ki kalla ki ƙara kallo kina aimu ansha damu mukam mata muka rako wasu sun more duniya muko dai gamu nan rayuwa har yanzu bata canja ba.
Abota ta ƙulle mai girma kowa yana ziyarta ɗan uwansa , yayin da suka shawartar junansu ta hanyar tura saƙo wa junansu ta whatsapp , ita dai mamaciyar tana tura ƙorafin mijinta ne idan yayi mata abu kaɗan , yake "yar uwata ki kwantar da hankalinki yatsun hannunki kawai kika kalla kinsan ba tsawonsu ɗaya ba wani yafi wani wani kuma bai kai wani ba , ita rayuwa bata yuwuwa ace kullum ke abinda kake so shi zaka samu dole , ita rayuwa juyawa takeyi wata rana asha zuma wata rana a lashi maɗaci haka rayuwar take tafiya duk wanda kika gani yana da tashi damuwar idan mai haƙuri ne ya ɓoye sirrin shi wa rayuwarshi da zuciyarshi ke kuma mai surutu jira kike a tara taron sabga biki ko suna duk inda kika zauna harshenki ake ji ke sarki matsalar gidan aure kullum an miki , kuɗin cefanenki bai kai ba , waya aikeki ? Waya sa ki ? Duk namijin da kika gani duniya babu namijin da yake so afi matarshi wanda duk baima iyalinshi ba baya da iko ne , idan ko maƙetacin namiji ne yana dashi ya ƙuntata miki barshi da Allah ja bakinki kiyi shiru ki lulluɓe aibin mijinki sai Allah ya lulluɓe miki naki....
Bayan ƙawance yayi girma ta waya sai aka fara ziyartar juna , mai mutuwa itace ta fara zuwa gidan rayayya tare da yaranta dan sada zuminci an tareta da shagali mai girma ta hanyar tara mata abubuwan motsa baki na zamani irin wanda bata taɓa ci ko sha a rayuwarta ba , an yini ana fira kowa yana faɗar irin rayuwar da yakeyi a gidan aure , yayin da ita wacce akaje gidanta take faɗo nata nasarorin rayuwar , mai mutuwa kuma ta hankaɗe zuciyarta taci gaba da tona asirin mijinta ta hanyar nuna gazawarshi wurin riƙon gida , bayan ta tashi tafiya ita wacce akaje gidanta ta shiga store ta ɗan tattaro mata kayan abinci ɗanye , irinsu shinkafa , taliya , makaroni , cuscus da dai sauransu ta haɗa mata da ɗan kuɗi bayan ta haɗa mata da kwancen kayan sawa....
Bayan an kwana biyu ƙawa tace itama zata zo , dan haka mai mutuwa ta hana ma kanta zaman lafiya ta faɗa maƙota neman rancen kuɗi wai ƙawarta zata zo bata so tazo ta raina mata , haka dai tayi ta faɗawa maƙota tana neman rance harta samo tazo itama ta haɗa irin tata ƙaryar , bayan ƙawa tazo ana fira ne tace mata amma yadda kike faɗar talaucin mijin naki kamar bai kai ba gashi komai na gani babu dai wata damuwa , hmmm "yar maular saita buɗe baki taci gaba da sana'ar nata tunda taga idan ta faɗi damuwarta kuɗi ake bata dan haka tace tou duk wannan da kika gani bashi na ciwo kuɗin a maƙota dan in fita kunyarki kindai san hausawa sunce abokin cin mushe ba'a nuna mishi wuƙa , taci gaba da ɗimi faɗi ba'a tambayeta ba , amma ni a gani na wasu matan sunayin "yar sana'a haka a gida dan su taimakawa mazajensu da abinda suka gagara yi musu.
Da ƙawa ta tashi tafiya taba mamaciya kuɗin da suka gigita mata lissafi tace ta biya bashin da ake binta ita kuma tayi ta zabga , haka dai akaci gaba da abota rayayya tana taimakon matacciya sosai , ganin ana yi mata hauka da kuɗi yasa ta gaji ta tambayeta kodai tana kasuwanci ne ? Tace bata kasuwanci bata siyar da fari ko baƙi tana da abokai ne dai masu taimakonta a waje , ta nemi ƙarin bayani aka bata sirrin abun dan haka babu wani tunani ko hangen abinda zaije ya dawo itama ta yanki kati ta faɗa harkar bariki yanzu yau wa gari ya waya.........?
Bello rungume yake da kwalba har suka iso inda aka ajiyesu ake basu horo , Ashiru kasa taɓa kwalbar yayi ya barta a hannun Bello yadai faɗawa mai gida sunje sun dawo , mai gida yace kawai yaje abunshi.....
Bayan sati ɗaya
Dikko yazo gidanmu a ranar da yace zai dawo kuma ciki ya shiga Inna da kanta ta lallaɓa ta nema masa abun daɗi kamar yadda ya faɗamin kuma yaci naji daɗi , daya zo kuma ya tanbayeni akan yadda akayi na saka Safiyya karuwanci nace ni babu ruwana kawai dai naji haushi ne sunamin gori na zama karuwa ranar da na rabu dashi a hanyarmu ta komawa makaranta mukayi faɗa na dawo gida ranar da suka ganni shine sukayi ta tura yaransu gida wai ga karuwa nan karna ɓata musu tarbiyar yara abin yamin ciwo shine na faɗawa Aunty Mamy daga nan bansan yadda akayi ba ,
Dikko yamin faɗa sosai kamar zai dakeni dan harsai da Inna ta kirani a waya dan a palo muke tana bedroom , ta tambayeni abinda ya haɗamu ban faɗa mata ba dan har Dikko yazo ya tafi Inna bata fito ba ,
A ranar ya sauke hidima wa Inna yayi jib da kwano na kuɗin da wallahi saida Inna ta ruɗe data gansu danni dama kyauta ta da Dikko biyu ce daga kuɗin daya bani a makaranta sai wanda ya sakomin a mota nasha mai da Umar ya kawomin wacce Al ' ameen ya ansa aka bawa Jiddah ita take hawa , sai kuɗin daya bani a ƙofar gidanmu ban ansa ba , ranar kam saida ya gigita Inna yasa mata mantuwar dole da manya kuɗaɗe a palo ya ɓaresu saman kujera ni kuma yayi fushi dani yai tafiyarshi saboda na haɗa Safiyya anyi iskanci da ita da baban Mardiyya duk da nace bani bace yace ba abinda ya dameshi bashi naci zamu bayan aure.
A ɓangarensu Bello kuma bai saki Dady ba amma tunda Momy tayi magana yasa aka sassauta bala'en da ake musu , an canja musu wurin zama ana basu abinci mai kyau shi Dady kuɗi kawai zai bayar ya kama gabanshi amma yace yana jiran wasu kuɗaɗe ne suzo saiya bayar ,
Tun washe garin ranar da aka ɗauko kwalba Dikko yasa aka tara manyan malamai yayi musu bayanin abinda yake so na za'ayi masa saukar al'qur'ani sau goma a rana har tsawon kwanaki talatin , tou an buɗe kwalba kamar yadda Bello yace malamai kuma suka ci gaba da sauka kuma ragunann nan goma duk ranar duniya idan akayi sauka haka ake yankesu ana raba naman sadaka.
Ranar da ya kama zuwa kotu banje ba lawyer Dikko ya tura bayan ya faɗa masa yadda kuɗi yake , idan kuma an gama shari'ar yana ƙarar baba ƙarami akan ƙazafin da yayi ma matarsa kuji wani neman rikici da rashin san zaman lafiya na Dikko kuma........!
Maganar Bello daya faɗa shine ya kashe Binna da kanshi nayi amfani da wata magana daya faɗamin a police station cewa , inji tsoron Allah in babu nan akwai ranar hisabi duk wanda yaci zalin wani dai² da ƙwayar zarra ubangiji bazai barshi ba , ki daina ganin kin samu dama ta taƙin lokaci yasa ki manta da rayuwar gaba , karki biyewa zuciya ki kafa abinda zaisa kiyi nadama wata rana , tunda har yayi imani da ranar hisabi bazan bar akashe Bello ba zamu haɗu ranar hisabin dani dashi da *BA BINNA* wannan shari'ar Allah kaɗai zaiyi ta.......
Hafsa kuwa tana tsaye wurin ganin ta gano inda kakar Ba Binna take kuma ta faɗawa Hajiya cewa idan harta ganosu saita faɗa musu itace silar mutuwar "yar su kuma tana roƙo Allah yasa masu zuciyane su kasheta kowa ya huta mai baƙin halin masifa kamar zuciyar fir'auna.
Tunda nayi mafarkin an kashe wata matar aure a Qerau ban sake ganin mutumin a bacci ba kuma ban faɗawa Dikko ba ,
Dikko ya riƙo wuta sosai ya matse lamba wa Dady a tura gidansu An mata , Dady yace tou kadai ga yadda Mom inka take hawa da rana ɗaya bata sauko ba abun nata kullum gaba yakeyi akan bata yadda ka auri yarinyar nan ba , Dikko yace Dady nayi nisa fa za'a samu matsala Dady yace yanzu ya kake so ayi ? Ka tura "yan uwanka kawai su an somin auren ta babu wanda yaji babu wanda ya gani ,
Idan kuma bayan anyi auren matsala ta shigo fa ? Babu damuwa Dady ni zanji da duk wata matsala , shiru Dady yayi yana nazari sannan yace daga neman aure idan abun ya warware ba'a ɗaura ba fa ? Dikko yace babu maganar neman aure kawai ɗaura aure za'ayi daga nan sai ayi duk wadda za'ayi , tou ina zaka ajiyeta Babana ? G R A tare da Jiddah , Babana yarinyar nan bata iya zama da Jiddah gaskiya , Dady nidai tare zasu zauna Allah ya bada sa'a kawai zakace , murmushi Dady yayi tare da cewa Allah ya tabbatar da alkairi Dikko ya ansa da amin tare da faɗa masa ranar juma'a ne , Dady yace Allah ya kaimu zai tafi da Momy ta rakashi ganin likita kafin su dawo anyi komai an gama...........
Dikko da kanshi yazo ya samu Inna sukayi magana yau duk laɓe²nta saida ya ganta kuma ya faɗa mata cewa ya tsaida ranar aurenshi da An mata ranar juma'a saura kwana 8 daga yau kenan , Inna tace ita gaskiya kwana 8 yayi mata kusa² tana da hidima sosai , Dikko yace shi baya buƙatar wuce wannan lokacin , kuma wane hidima gareta ta manta da yanzu An mata tayi aure da Sultan ? Ko sai nashi ne za'ace yazo da wuri ? Kodai har yanzu bata daina fushi dashi ba ? Shiru Inna tayi bata bashi ansa ba , saida ya ƙari maganarshi ya tashi yauma kuɗi ya safke mata na mamaki mai nuni da ko rashin kuɗi yasa kwana 8 yayi mata kusa² , baima saurareni ba kuma dana gaishi bai ansa ba.
Bayan tafiyar Dikko Inna ta shige ɗaki ta kira ƙawarta suka tattauna dan ita Inna kallon ɗan duniya take ma Dikko shi yasa ta fara neman hanyar da zata gyara "yarta gani take wannan hanyar itace mafita....
Da mijinta yazo ta rattafa mishi auren Sultana yau saura kwana 8 aurenta , waishi ba'a kyauta mishi ba ya za'ayi masa haka abu babu notice tace yayi haƙuri , kuma daya tambayeta wanda Sultana zata aura aure haka kwatsam , cewa tayi sunanshi Muhammadu , waye ubanshi kuma sun bincika halinsa har zata ɗauki Sultana ga baƙon fuska ta bayar tayi mata aure haka kamar ta gaji da ita ? Inna tace sanin ubanshi halinshi da komai nashi sa fuskanci juna idan anyi auren ,
Inna ranar jinta takeyi kamar ba ita ba , tana cikin farin ciki mara musultuwa cikin ƙanƙanin lokaci gidanta ya cika da taron ƙawayenta ƙasaitattun mata masuji da kansu a gidan aure tou wai ita Inna ina ma ta samu wa'anan ƙwanƙwasashin mata ? Suke ta huɗɗinsu Inna ta faɗa musu Sultana Dikko zata aura , amma bansan abinda yasa ta ɓoyewa mijinta ba ,
Bayan kwana biyu yadda Dikko yasa aka haukata gidanshi yasa Jiddah ta gane aure zaiyi dan haka ta fara ɓarin kaya tana ta hauka tana zage² gaba ɗaya ta tashi hankalin duk wani wanda yake da dalilin sanin Dikko zai aure , tou ai babu mai iya tunkarar Dikko da zancen dakatar da aure sai Momy kuma bata nan Dady yajata sunyi tafiya dan Dikko yayi hidimarshi ya gama saida tazo ta samu amarya ,
Jiddah bata gama tabbatar da Dikko zaiyi aure ba saida taga katin ɗaurin aure kuma Umar ne ya kawo mata shi , Dikko yana kwance yana bacci ta shigo ɗakin da gudu bayan Mardiyya ta tunzurota ta shigo tana ta ɓarke²n zagi tana aibata shi san ranta bai mata magana ba yayi kamar bacci yake dan yasan zafin da raɗaɗin da mata keji yayin da za'a musu abiyar zama , ya gani yadda Yayarshi tayi da akayi mata abiyar zama aurenta kamar zai rabu dan Momy ɗaure mata ƙugu tayi ta dawo gida , ba abinda zaice ma Jiddah tayi duk haukanta kila haka zaisa ta samu natsuwa idan kuma tayi ƙoƙarin keta iyaka zai nuna mata nashi haukan sai yayi mata dukan da har ya gama auren tana saman gadon asibiti saboda shi abu ƙalilin ke ƙufular dashi.......!
10/11/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 74
Yaye bargon da yake lulluɓe tayi taci gaba kuka tana ɓarke²n zagi tana ma Dikko gori wai yaji kunya ya rasa wacce zai aura sai karuwa ɗiyar ɗan caca jahila matalautan da suka kasa siyen gidan zama saidai gidan haya ai duk talaucin da yasa mutum ya rasa gidan zama wannan talaucin ya kai abun a duba matsiyatan banza da wofi ,
Me yake nema a wurin yarinyar nan ? Bayan ita tafi ta komai kuma su masu kuɗi gidansu Sultana fa ? Duk abinda ake nema ga mace Sultana basu da , duk abinda ya cancanta ka aureta saboda shi babu ko ɗaya da take dashi , jahila daƙiƙiya mace babu ilimi ai kwankwon ashana ce domin shi ilimi tushe ne mai nuna dogon zango , kaga tun nan abinda kake nema baka samu ba , halin kwarai jari ne , bata dashi , su kuma kuɗi jigone masu nuna isashshen iko a cikin abunda na lissafo wane take dashi ?
Ai ni ina da duk abinda kika lissafo ko ? Ai kaine kake dashi ba ita ba , to na bata ilimina na bata halina na bata duk komai nawa ke kinsan An mata kuwa ? Ki bari tun kafin raina ya ɓaci na fara maganganun da zakiji babu daɗi dan haka ki tattara mutuncinki ki barmin ɗakina !
Bana tafiya sai kayi maganganu akanta munafikin banza maci amana , murmushi Dikko yayi cewa nine munafiki Jiddah ? Maci amana ? Wace irin amana ne naci haka da har kikemin gori ? Ban sani ba baƙin munafiki , sauka yayi daga saman gado yana cewa Allah ya baki lafiya ya wuce toilet , ita kuma taci gaba da ɓaɓɓarka mishi zagi harya gama abinda yake ya fito Jiddah bata daina sokawa Dikko zagi ba.
Inda take tsaye yaje ya riƙota cikin rarrashi yace ni ne ? Kwantar da fuskarta tayi saman ƙirjinshi tana kuka cikin shashshekar kuka tace Yaya dan Allah bana san auren nan , tou muje saman gado saiki faɗamin kinsan ban cika jin magana daga tsaye ba , ni bazan hau gado ba , tou tunda bazaki hau ba fitarmin daga ɗaki idan ba haka ba zan hau dake dole kuma jikinki zai baki labari , da sauri ta sauka daga jikinshi tayi waje da gudu tana kuka , murmushi Dikko yayi yace matsoraciya.
Saman gado ta faɗa taci gaba da kuka a zuciyarta kuma jinjina irin muguntar Dikko takeyi macuci idan har yana jin haushin mace sai yayi mata ƙeta mamugunci nufinshi yashata basilla murmushin mugunta Jiddah tayi a zuciyarta tace badai Yaya bane ba ? Kije kin samu Sultana idan dai tsintuwar fatalwa riba ne.....
Inna da kanta taje ta faɗawa Kaka Sultana zatayi aure Kaka tayi murna sosai kuma tayi ma Inna da Sultana fatan alkairi , ta kuma ƙara da cewa amma me yasa saida aure ya rage kwana 6 zata faɗa mata ? Inna tace mijin ne ya zaɓi haka , Yayarta dage zaune tana saurarensu tace badai girin² ba tai mai , Inna ta gane ta maso habaici maso faɗa wanda ya tanka shi yafi tou bata da lokacinta ,
Tunda Dikko yazo ya tsayar da ranar aurenmu dani dashi bai sake dawowa gidanmu ba kuma kona kirashi waya ya daina ɗauka ma , Inna kuwa kullum bata da aiki sai kwaɓe²n kayan mata tana bankamin saidai tsareni tana zagina wani lokaci hada mari wai bana gane wannan gata ne sai naje gidan aure , tun ina sha ina amai har cikina ya haƙura ya riƙa riƙeminshi dan idan zansha so goma na amayar Inna bata gajiya zata sake kwaɓa masifa ta bani na kwankwaɗar wa cikina.
Labarin auren Dikko ya zaga kaf illahirin birnin garin katsina mutane sun fara canfashi ya cika aure² ya auri waccan ta mutu bai tsaya hutawa ba ya auro wannan duka yaushe yayi auren har yake tunanin sake auro wato ? Yayin da wasu kuma suke gani izzar kuɗi ce ke nuna ikonta shi yasa yana matashin shi zai aje mata biyu cikin shekara ɗaya....
Dikko kuwa babu abinda ya dameshi da labarin dake yawo a gari shidai zaiyi , tunda ya taho kuma yaga mai tareshi matsalar bai faɗa ba zaiyi amma da zaran ya yanke hukunci tou fa ko kanshi baya saurara ,
Duk "yan uwan Inna dasu ake hidima kuma hada yayarta kwansu da kwalkwata suna zuwa ba wanda aka rage tun bayan tsaida ranar auren da kwana biyu suka fara zuwa , kowa tambayar Inna yake tou ina maganar kayan ɗaki ? Saidai tace komai za'ayi , a kwana biyar za'ayi ? Inna tace Eh ,
Tou basu sani ba kayan ɗaki kansu da kayan kicin duk abinda iyaye kema "ya "yansu dan fitar dasu kunya Dikko yayi saboda tunda ya fara aikin gidanshi na goruba inda zai ajiyeni daga farko dama shine yake da burin zuba komai na gida tou kayan nan yasa aka sauke su a wani gidan mijin Inna sai idan za'aje jere Inna tasa aje a ɗauka a can yadda za'ace itace tayi.
Komai dai na hidimar auren nan cikin munafurci akeyinshi , dan ko lefe Dikko ne ya kawoshi da kanshi da daddare misalin 2:54am dashi da yaranshi bansan sunzo ba haka kuma banji tafiyarsu ba , saida safe na tashi naga wasu irin lafiyayyin akwatina masu tsinannen tsada da kyau na tashin hankali , akwatina 24 da wasu irin ƙattin jikkuna biyar babu wanda ba'a takeshi da kaya ba , wannan shine faɗawa mai zuciya biki ba mai tarin dukiya ba tou Dikko komai ya haɗa , nidai ban buɗe ba amma da Inna da mijinta saida suka zindire lefen nan kaf suka ganshi gaskiya naira wurin lefen nan taci bugu harta gode Allah wallahi komai na cikin lefen abun burgewa ne babu abu na banza komai baka isa ka raina ba saidai hassada.
Ƙawayen Inna "yan duniya lokacin da suka zo suka ga lefe sunyi ɓarin maganganu na isashshin mata wai Dikko dai ɗan gaye ne wayayye tebirin farko wallahi magana ya gayamin a lefe turaruka kamar suce wayyo Allah masu tsada abinda dai Dikko ke nufi yana san ƙamshi , wuraren daya kamata nayi amfani da turare suke faɗa duk abinda suka ɗaga a lefen sai sun faɗa fita nayi na bar musu ɗakin dan abinda na lura basu da kunya.....
Washe garin da aka kawo lefe akaje ganin ɗaki Jiddah tayi wulaƙanci tayi hauka marar ɗaura zani tayi bala'en daya tada hankalin duk wanda yaje ganin ɗaki Jiddah tace babu wata mace data isa ta zauna mata gida , wallahi wannan gidan tane daga ita sai mijinta , Dikko nata ne ita ɗaya babu maishi sai ita gidanta ramin kura ne daga ita sai jama'arta sai kuma "ya "yanta babu wata banzar ɗiyar ɗan caca data isa ta zauna mata da mijinta amma idan har Sultana ta shirya mutuwa ta shigo gaba ɗaya ma auren mamarta akayi wallahi , amma idan har Caca ta shigo zata goga da ita a kishi tou tabbas tana musu albishir kwanaki bakwai cas ta bawa Caca a gidanta zata dawo babu jimawa idan tana da sauran shan ruwa gaba kenan idan kuma bata dashi su tarbata a rimin badawa , sunan wata maƙabarta ne...........
Ta bubbugi ƙofofi ta rufesu ta hana ganin ɗaki tayi maganganu masu tsauri kuma kalamanta suna da kaushi ta fa barbaɗa rashin mutunci iyakar ƙarfinta guyawu a sace "yan ganin ɗaki suka dawo ba tare da sun samu damar ganin ɗaki ba , Inna da taji bayani kuwa cewa tayi to saidai ya raba musu gida , Inna ta yaba da masifar Jiddah baza ta yadda a haɗe Sultana da Jiddah ba dan cutar mata ɗiya za'ayi idan kuwa Dikko bazai raba musu gida ba ta yadda saidai a fasa auren nan, da ƙawayenta suka bata haƙuri cewa tayi har Sultana ma nawa take ? Ta gama haɗiye wani dafin zata fara kwankwaɗar na kishiya ? Masifa nawa zatasha ? Bazata laminta ba gara tasan abinyi tun kafin tabar nigeria idan zai yuwuwu ayi idan bayayi a barshi kowa ya samu natsuwa babu wanda zaisa ma "yarta ciwon zuciya........
Da daddare bayan kowa ya kama gabanshi Inna tayi ma Dikko waya tana san ganinshi , yace mata baya nan yaje kaduna amma yana shigowa katsina babu jimawa idan ya dawo zaizo insha Allah , fatan isowa lafiya tayi masa ta kashe wayarta , kallona tayi tace idan kin ga dama ki tashi kije kiyi wanka kin zauna bursunai² dake kamar an ƙwatoki bakin kura , ban kalleta ba nace ai ko ɗazu nayi wanka , dan ubanki yanzu ma sai kin ƙara wani , ai Dikko dai kike so ko ? Badai kin zaɓeshi ba ? Yanzu kika fara wanka tunda dai kina san Dikko kije kinsamu , Dikko da kike ganinshi ƙyalƙyal na rariya ne zamani ne da kanshi idan zaki iya ga fili ga mai doki , tun cikin mutunci nace ki rufawa kanki asiri ki auri Sultan kikaje kikayi ta hauka tun ina nida ke saida kika ɗaga murya aka jiyoki uwayen sharri suka kira ubanshi a waya suka faɗa mishi bakya san ɗansa sun nemi sharrin duniya sun ɗora miki hankalinsu bai kwanta ba saida suka ga an fasa auren nan , hmmm Dikko dai ko ? Bazan miki baki ba.
Da kin auri ɗan uwanki asiri a rufe babu wanda yaji ya gani amma dake ke sakarya ce baki san wanda yake sanki ba kin biyewa ƙuruciya da san zuciya ga yadda ta kaiki Caca ma take kiranki tsabar ta maidake jaka ta ƙarshen benci iskanci da rashin kunya kuma duk garin nan ba na gaba da Dikko , "yar uwarshi ce can zaki musu iskanci su haɗe miki kai suci ubanki nidai bazan fasa tafiya ba , india ba fashi wallahi saina bi mijina zan baki makullin gida idan bai miki daɗi ba kizo ki buɗe ki shiga ko ki tafi wurin ahalin ubanki gidan Hajiya dai yai miki tsururu cikin hayani tace ki tashi daga gabana in daina ganinki , da sauri na miƙe zan fita tace baza kije kiyi wanka ba ? Jiki a sanyaye na dawo na wuce ciki danyin wanka !
Cike da damuwa Inna ta miƙe taje ta nemi wasu magunguna ta damesu da madara tana damawa tana mita Dikko ɗan duniya idan ba'ayi shirin tashin bama²i ba ai za'aji babu daɗi , Inna a ganinta wannan shine mafita ta mayar da cikin Sultana kamar wata tsohuwar rijiya duk abinda ta kwaso a cikinta take juyewa saboda wannan garinka da take bankawa "yarta abinci ma kwata² ya daina ciwowa gareta , wata "yar duniyar ƙawar Inna kuwa ke dafo wata munafikar kaza wacce ba'acinta ma sai an kashe fitila kamar kazar tsafi , Sultana tabi ta rame ta ƙanƙance saboda masifar Inna da magunguna idan ma tace bata sha haka zata rufe ta da masifa sai tasha a karkaɗe kofi ,
Ina fitowa daga wanka na hango Inna zaune gefen gado da ƙofinta riƙe a hannu , gabanta kuma kaskon garwashi ne , a takure nake tahowa dan ida bayyana a cikin ɗaki a tsawace tace min kiyi tafiya kamar kina da rai garwashin nan zai siƙe kuma kin sani sarai dakel aka samomin shi tunda gabanki nake ta nemansa tun safe , Inna shi kuma wannan ɗin na mene ne ? Na ubanki ne , tayi maganar tana kunce haɓar zaninta ta ciro wata "yar farar leda ta kwance tana ki wuto kizo ki duƙa nan , matsawa nayi kusa da ita nayi yadda ta nunamin ita kuma ta zazzage abinda yake cikin ledar duƙa tana cewa da kinsan ko nawa na siya saikin yaba ma ƙoƙarina , ko inda take ban kalla ba haka kuma ban bata amsa ba har ta uwarce ni dana tashi , tashi nayi ta miƙomin kofin ansa nayi nasha ta zuba ruwa na girgije na haɗiye , ɗaukar kwaskon tayi da kofin ta fita ni kuma na ɗauki kayana na saka na kwanta dan bacci nakeji bana wasa ba.
Tana fita ɗakin mijinta ta wuce bayan ta ajiye kayan data fita dasu a kicin , ni kuma naci gaba da baccina , saida Dikko yayo mata waya yazo ta shigo dan taga ko na shirya ta ganni kwance ina bacci , cikin takaici ta tasheni bayan na tashi tace shine kinyi wanka ki iya ki shirya kika wani kwanta bacci ? Ƙara takurewa nayi da niyar komawa bacci tace ki tashi idan kin ga dama ki gyara jikinki kafin in gama magana dashi yana ƙofar gida , cike da farin ciki na sauko daga saman gado Inna kuma ta koma palo tana jiran shigowar Dikko....
Fuskata na wanke da bakina na fito , lokacin har Dikko ya shigo kuma Inna ta ratta mishi cewa saidai fa ya raba mana gida dan bazata yadda ba ɗiyarta tayi rayuwar takura , sundai yi maganarsu sun gama abinda dai naji Dikko yana bata haƙuri cewa shi babu macen data fi ƙarfinshi kuma gidanshi bai gagareshi yayi hukunci ba , inda yaso ya ajiye An mata bai gama aiki ba zaman na wani lokaci ne zasuyi kuma wani abu mara kyau bazai faru ba , Inna tace tou kai dole sai kayi auren ne yanzu ? Dikko yace ba dole bane ba lokaci ne yayi tunda ai ba yau naso muyi auren ba , Inna tace to gaskiya saidai ka bari idan ka gama aikin gidan sannan , mijinta ne yace ba'ayin haka idan bashi da ikon raba musu gidan ya zakiyi kenan ? Sai a fasa auren , ki daina haka ki musu fatan alkairi da addu'ar zaman lafiya , ba haka Inna taso ba dan na fahimci bata san gardama da mijinta , bayan sun gama ne suka shigo cikin bedroom in ita da mijinta , Inna tacemin kije ku gaisa farin ciki fal zuciyata na tun kari hanyar fita , zan fita daga cikin bedroom in naji mijin Inna yana cewa wai ba DK bane ba ? Inna tace waye kuma DK ? Bawan Allah cikin dai kokonto yace ba shi bane ba kamarsu dai tayi yawa wallahi shi wancan wanda nake magana bana tunanin ma zaizo nan , bata bashi ansa ba kuma sai suka rangaɗo suka biyo bayana suka fita daga ɗakin mijin Inna kuma yana ƙara kallon Dikko.
Cike da farin ciki na isa wurin Dikko na rumgumeshi rabon da in ganshi ko inji muryarshi harna manta nayi faraicin lallausan jikinshi mai kama da bayan zomo , maimakon yaji daɗi ko yayi fara'a sai yace ke kullum sai kin hawomin jiki kamar wata mage ina dai lissafi kuma da guda² duk saina rama , gyara kwanciyata nayi saman jikinshi saida naja gemunshi sannan nace yanzu ma ka rama mana nayi maganar ina kallon cikin idonshi , murmushi duniyanci yayi cewa a , a ni na isa inzo har gidanku in rama abinda kikai min ? Zaki isko ni har gida saurin me kike ne ? Murmushi nayi ba tare da na sake magana ba , shi kuma yace meya sameki naji kin rage nauhi , da nayi niyar faɗa mishi abinda Inna takeyi amma sai wata zuciyar ta haneni kuma gaskiya dai idan ba'ayi hankali ba saina faɗa mishi abinda akemin !
Shi kuma a ranshi tunani yakeyi kila fa itama An mata anayi mata irin abinda ake ma "yan gidansu idan za'ayi musu aure , jinjina kanshi yayi tare da cewa Allah ya sawaƙe idan kuwa anyi mata cutar yarinyar nan zaiyi da yawa , An mata kawo kunnenki in tambayeki , matsawa nayi tare da miƙa kunne ne saitin bakinshi cikin raɗa yace naji kin rage nauhi meya sameki ne ? Wata irin kasala naji ta lulluɓemin jiki na ƙara kwanciya sosai a lallausan jikinshi ban bashi ansa ba
Shi kuma yaci gaba da cewa Mama take baki wani abu ko ? Kaina na ɗaga mishi alamar Eh , ɗago fuskata yayi idanuwanmu suna kallon cikin idon juna yace ai na sani hada kaza ko ? Shiru nayi ban bashi ansa ba , yace ai mu na gidanmu ina kallonsu wallahi hada tattabaru ake basu mutum yazo ya kasa cin abinci nasan kema hada irinsu ake baki ai ni gaskiya wannan shigamin haƙƙin rayuwa akayi gaki an takura miki an ramar min dake babu gaira babu dalili saboda ɗaukar alhaki , ni babu wata kaza da nake ci , hmmm haba An mata aiko baki faɗa nasan komai miye baƙona a mata ? Ya fara lissafe²n kayan mata kamar wata tsohuwar karuwa bayan ya gama yace sune baƙin nawa duk abinda na faɗa nasan aikinshi idan baki sani ba , Allah dai ya sawaƙe ya kuma kyauta wahala saukar min daga jiki karki shanye daɗin ke ɗaya....
Murmushi nayi sannan na tashi na koma saman hannun kujerar da yake na zauna , mukaci gaba da firar duniya bana soyayya ba yana bani labarin abokin Yazeed da aka kama yace wallahi An mata fitinar zamanin nan yana bani al'ajabi saboda tsabar ƙazanta kina matar aure dan karnikanci kinabin mazan waje , ni na rantse da Allah da nine mijin idan nasa an kamashi Allah ya tsinemin , dariya yayi sannan yace dama ya sani yana riƙe banza yayi masa irin yadda akayi ma Saminu ya fashe idon dake ganin matan , nidai da nine ƙarya mishi wuya kawai zanyi ya mutu a rage annoba a ƙasa , dariya yayi yana kallona yace kiyi dariya mana , ƙinyin dariyar nayi kuma ban kalleshi ba , taɓoni yayi cewa An mata miye ? Ai kai dama baka iya komai ba daga duka sai kalmar kisa shikenan abinda ka iya faɗa , ke karfa ki raina min hankali , daga haka fira ya koma rigima wai wannan "yar maganar harya ɓatawa Dikko zuciya ni kuma bada wani manufa nayi maganar ba , tsoki yayi tare da miƙewa cikin ɓacin rai ya tunkari hanyar fita ,
Binshi nayi da ido harya fita daga palon , saida ya fita na tashi nabi bayanshi har ƙofar gida amma banyi mishi magana ba , ina fitowa duk su Ashiru suka gaisheni cikin girmamawa kaɗan na ansa gaisuwar nabi Dikko da aka buɗewa mota kafin a rufe na riƙe murfin motar nace kayi haƙuri idan kaji babu daɗi insha Allah bazan sake ba , ba tare daya kalleni ba yace na yafe miki , yawwa ngode na bashi ansa sannan na juyo da sauri na dawo cikin gida , murmushi Dikko yayi yace kura ta fara lafiya yau wace rana bata biye an tashi hankali ba , murmushi ya sakeyi tare da kwaikwayon maganar Sultana wai da haka zatace naje nace mahaukaci aljannu kamar iccen tsamiya ! Hmm jarumata kenan..... Ina komawa kwanciyata nayi naci gaba da baccina dan yau su Hajiya Inna ba'a ɗakin za'a kwana ba...
Inna da mijinta kuwa bayan sun fita daga palo mijinta ya tabbatar da Dikko ne dan haka yace ma Inna wane gigi ya kaita ? Shidai babu ruwanshi tunda dama tun farko ta ɓoye mishi wanda Sultana zata aura Dikko dai ba kanwar lasa bane ba , amma yana musu addu'ar zaman lafiya kuma bazaiyi binciken inda Sultana da Dikko suka haɗu ba tunda dama ba'a so ya sani.......
Duk iskancin da Jiddah ta zaƙula ma "yan ganin ɗaki bai isheta ba Mardiyya ta tirota tace idan ta saki ta tsaya sanya za'ayi babu ita ta tadawa Dikko hankali a daren nan ta hana mishi bacci , shi kuma a gajiye ya fito daga toilet ɗaure da rigar wanka a jikinshi dan baya buƙatar komai a halin yanzu sai bacci , da masifa Jiddah ta shigo ɗakin kallo ɗaya Dikko yayi mata ya ɗauke idonshi daga kanta ya matsa inda ya ajiye kayanshi na jersey ya ɗauka ya saka ,
Jikin socket ya matsa da niyar kashe fitila ta riƙe mishi hannu , kallon hannu yayi sannan ya kalli Jiddah na tsawon minti ɗaya yasa hannun haggunshi ya kashe fitilar ya koma saman gado ya kwanta , yana kwanciya ta kunna fitilar , jinjina kanshi yayi sannan ya sauko yazo ya kashe fitilar a karo na biyu , saida ta sake tabbatar daya kwanta ta sake kunna fitilar yanzu bai sauko ba yace kasheta , bazan kashe ba , ki kasheta nace , bazan kashe ba nace maka , rufe idanuwanshi yayi sannan yace ke........ Ki kashemin fitila nace , a ɗan tsorace Jidda tace bazan kashe ba , cikin wata irin murya Dikko yace na rantse da girman Allah idan har kika bari na sauko daga gadon nan wallahi saina takaita miki rayuwa zuwa ɗaya zan miki na tasheki aiki har abadan duniya , da sauri Jiddah ta kashe fitila tayi waje da gudu tana kuka....
Tsoki Dikko yayi tare da ɗaukar wayarshi ya fara kiran An mata , saida ya kirani so biyu ana 3n naji cikin faɗa yace wai ke An mata sai inta kiranki sai kin gama iskancinki zaki ɗauki waya , a sanyaye nace kayi haƙuri bacci nakeyi , nine baccin , kayi haƙuri bazanyi haƙurin ba duk kina nufin bakiji ina kiranki ba sai yanzu munafurci kawai , cikin ɓacin rai nace kai Dikko kaima munafurci , murmushi yayi sannan ya ɗaga idonshi dakel saboda baccin da yakeji yace nine munafurcin ko ? Haba kaima wallahi neman fitina gareka , tou yi haƙuri An matana raina ne ya ɓaci kuma bacci nakeji na fiso inyi bacci dake a raina kiyi haƙuri don Allah idan dake ne zanyi bacci idan bake bace wallahi bana iya bacci raina zaiyi ta ɓaci a banza kiyi haƙuri mu raba ɓacin ran kin yafemin ko ya ƙarasa maganar yana jan wani irin numfashi mai ɗauke tunani yace muyi bacci mai daɗi ki ga Dikko a baccinki jarumata ,
Shiru nayi banyi magana , a kasalance ya kira An mata cewa meye ? Dakel na haɗiye miyan bakina banyi magana ba har yanzu , An mata.... ? Na'am , Dikko ne ? Umm tou yi haƙuri kinji zanyi bacci na gaji saida safe ya kashe wayarshi , yana kashe wayarshi yaci gaba da baccinshi cikin natsuwa da kwanciyar hankali saɓanin Sultana da bacci ya gagari idonta ,
Dikko baida adalci gaskiya shi kanshi kawai ya sani , matarshi ta ɓata mishi rai akan me zai kira wata da bataji ta gani ba kuma bata san anyi ba ? Ita Jiddah me yasa bayacin ubanta yadda yake ma Sultana ? Danni nayi imani da Sultana ce ta kashe fitilar nan wallahi sai Dikko ya zaneta , amma ita Jiddah sai tayi kwance² ta ɗana iskancin ta amma Dikko baya zane mata jiki irin yadda yake ma Sultana me ne ne dalili ? Shin san Jiddah yafi ko kuwa .....?
Ranar da akaje jere ma Jiddah ta ɓara iskanci wanda yafi wanda tayi ranar ganin ɗaki , ta tara ƙawayenta ƙosashshin "yan iska kuɗin mota ta turama ko wace har naira dubu ɗari wai suzo su tayata tarar kishiya sun cika gidan ba masaka tsinke sai iskancin suke zazzagawa wallahi zaman jere bai yuwu wurin mata ba maza ne kaɗai suka tsaya dan kayan na ɗaurawa ne kunga kenan ba aikin mata bane na maza ne , ko iri ɗan tukuicin nan da ake badawa na jere duk Jiddah ta murjeshi ta hana , dama na ganin ɗaki ma bata basu ba , kai Jiddah riƙaƙƙar "yar iska ce mai tikiti lallai Dikko ya ɗauki alhakin Sultana da zai haɗata zama da Jiddah.......
Bayan tafiyar matan suka faɗa kicin ita da ƙawayenta wai wannan kulolin da duk wani abu da aka saka mata yafi ƙarfin sayen ɗan caca dan haka tasa suka kwashe duk abinda take so aka kai kicin inta , ita kuma Mardiyya an tsaida ita a kicin tana dafawa Dikko da baƙinshi abincin da zasu ci sai waya yakeyi a kawo , "yar kwalbarta ta jawo daga cikin breziya ta kakkaɓe maganin ta kaf a cikin abinci , hamdala tayi ga Allah bayan ta tabbatar ta gama zubawa.....
Banda faɗuwa babu abinda gaban Inna keyi ganin taron mata sun dawo suma kansu sunji tsoron Jiddah ina ita Sultana ? Ƙaramar yarinya wacce shekarunta bai kai na Jiddah ba gaskiya zalinci yasa Dikko zai haɗa mata "ya zama da Jiddah , da tsausayi ta kalli inda Sultana take tana shiri Dikko ya turo Ashiru ya ɗaukota ya kawota wurinshi bayan yace masa wai kar yayi tuƙin ganganci kuma karya biyewa kowa yayin daya hau titi ya ɗauka duk wanda ke saman titi mahaukaci ne shi kaɗai ne mai hankali , hijabi Inna ta bani na saka bayan na gama shirina , saida ta rakoni har bakin get ta koma ni kuma na fita na shige mota muka tafi....
Kallon kaina nakeyi a zahirance wai in banda abin Inna taya zata sadani da hijabi ? Wannan ma idan wani ya ganni ai sai a rainani umm to ya zanyi ? Haƙuri kawai zakiyi Maryama....
Tun daga ƙofar gida har cikin gidan motoci ne , sai dawakai da aka tara a wajen gidan da ciki ƙosashshi "yan gayun dawakai masu tsada wata irin haniniya sukeyi sun karaɗe kaf illahirin wurin da kuka , ciki Ashiru ya shiga ya samu wuri yayi parking sannan ya turawa mai gida saƙo isowarmu ,
Shima rubuto masa yayi wai mu shigo yana ciki bayajin daɗi cikinshi ke ciwo , da Ashiru ya faɗamin cewa nayi bazan shiga ba idan baya fitowa ya bari , a , a ranki ya daɗe kiyi haƙuri mu ki shiga , wallahi bana shiga idan bazai zo ba ya bari yasa an ɗaukoni tun daga gidanmu nan ɗinma bazai iya zuwa ba ? Idan yana zuwa yazo idan baya zuwa can shi ta matse mawa....
Tura masa yayi cewa bazan shigo ba , yace gashi nan yana zuwa , fita Ashiru yayi daga motar yana cemin ki jirashi yana zuwa , ya daɗe sosai sannan ya fito mutanen da basu gaisa ba suke gaisawa bayan ya gama ya taho wurin motar ,
Gaba ya buɗe kujerar mai zaman banza ya ziro ƙugunshi ya zauna a gajiye ƙafafuwanshi a waje bai rufe motar ba , kwantar da kanshi yayi jikin kujerar yace wallahi bansan abinda ya sameni ba cikina kemin wani irin ciwo kamar zan mutu , ai idan ka mutu ka huta , Eh na huta ke kuma taki ta ƙare juyowa yayi ya kalleni sannan yaci gaba da cewa ai nasan idan na mutu ɗan ƙaramin hauka zakiyi sai kin riƙa kwacewa ana riƙoki , tou ka mutum ka gani idan zanyi haukan , hmmm yarinya kenan kina wasa da lamarina An mata , nima kana wasa da nawa lamarin kedai kika sani , kaima ka sani dakel yayi "yar gajeriyar dariya tare da duƙar da kanshi ya riƙe cikinshi yace wai Allahna.....
Jikinshi yana wata irin kyarma ya kwantar da kujerar daya ke zaune kai yana cewa matsa daga nan ke , gefe na matsa yana cewa kin dai yafe ni ko ? Tou zan mutu in mutu ? Wata irin ƙara nayi cewa ban yafe ba Dikko dake duƙe ya riƙe ciki da sauri ya ɗago yace mene ne kuma ? Ajiyar zuciya na sauke na kalleshi murmushi yayi cikin ƙarfin hali idonshi ɗauke da hawaye kaɗan yace ya akayi ne wai ? Fashewa nayi da kuka nace mafarki nayi zaka mutu yanzu , murmushi ya sakeyi cikin jarumta yace ina nan zaune kikayi baccin ? ya ƙarasa maganar yana min wani irin kallo , tou amma na ganka ka kwanta kace zaka mutu , Dikko yace anan ɗin na kwanta ? Eh , ba kin ganni gani nan zaune ba ? Idan ba kaine ba waye ? To ni An mata ya za'ayi in sani ? Wallahi na ganka , hannunshi ya miƙomin na riƙe yace ke... wai mene ne ? Ko yunwa kike ji ne ? A , a , banajin yunwa kalli idona in ganki , kallonshi nayi shima ni yake kallo bayan wani lokaci yace ya isa haka fita muje ya fita........
Ƙin fita nayi ina tunani to wai idan ba Dikko bane ba waye ? A dai² lokacin daya buɗe murfin motar ya fiddoni yana cewa yunwa nakeji amma banajin zan iya cin abincin can gaskiya.......
12/11/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA...* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 75
*_Ga saƙon godiya Ummiee Zaria Jikar Lerawa Sultana tace a gaishe ki tana miki fatan alkairi..._*
Nifa bazanje ba kaje kawai zan jiraka a mota , da Allah wuce mu tafi banasan yawan magana ji nake kamar zan faɗi , nidai kaje abinka dan Allah , zaki wuce muje ko saina baki kunya , ai kaima zakaji kunyar , ni banajin komai idan ban ɗaukeki ba kice ba Dikko nake ba kuma idan na ɗaukeki saina fita ƙofar gida a tsakiyar mutane zan ajiyeki in dawo ,
Kaɗan ne daga cikin aikinshi dan haka nace muje badan halinka ba , naji muje dan naki halinki kuma da bakije ba yau da kinga yadda ake saɓanin igiyar ruwa , tafiya nayi na barshi a baya biyo bayana yayi yana cewa "yar raini magana fa nake kuma nasan kinaji na...
Kai aini yanzu na girma banda lokacin yarinta , dariya yayi yace ai nine zan baki girman kinga kina ƙasana har yau har gobe kullum ma kina ƙasa ina samanki yarinya kin gane abinda nake nufi yayi maganar tare da wucewa yayi gaba da ɗan gudu nima da sauri nabishi ina ƙarema gidan kallo gaskiya wannan gida ya haɗu masu kuɗi basu da aike sai bautawa ƙasar da bata da tabbas duk wannan ginin a kwana a tashi sai an tafi an barshi kuma ƙasar ce zata hiɗiye bata gajiya...
Wata "yar munafikar ƙara yayi "yar ƙarama yace wayyo cikina kuma bai daina tafiya ba nima ban daina binshi ba , gangarewa yayi ƙasa da gudu nima da gudun na bishi muka sauka muna sauka naga mun fito waje irin na farkon gidan amma ba inda Ashiru yayi parking ba , tsayawa nayi ina kallon wurin da mamaki jin ban biyoshi ba yasa ya dawo da sauri kamar za'a kamashi ya jani ta baya ina kallon wurin shi kuma yana jana da sauri , jinjina kaina nayi tare da cewa "yan gayu , ai kune gayun An mata mu "ya "yanku ne.......
Taho jirana akeyi , juyawa nayi na kalli gabana nace ina zamuje ? Can zamuje ai , ni gaskiya bazan je ba , ke da Allah wuce muje yanzun nan kika gama cemin kin girma ashe har yanzu An matance , nidai gaskiya bazanje ba , mi yasa ne ? Nifa tsoro nakeji , tsoron mi ? Da Allah wuce muje ke komai sai kinyi yarinta , ƙwacewa nayi nayo hanyar da muka fito da gudu , shima da gudu ya biyoni harna fara hawa matakal ya riƙoni yace wai me yasa kikemin haka ne ? Cikin kuka nace nidai bazanje ba , jawoni yayi kusa dashi yace tou in rungumeki sai muje ? Nidai bana so , yace um ummm Dikko ne fa ya faɗa tare dayimin kallon ƙauna , zo jikina kiji natsuwa An matana , a gajiye na sauka jikinshi cikin mutuwar jiki , yace tou ya kikaji akwai daɗi ko ? Eyy tou sauka muje babu wani abu da zai faru wallahi.... Ka tabbata na tabbata miki ya ƙarasa maganar yana duƙuwo dai² bakina na sumbaci gefen fuskarshi yace yawwa jarumata muje....
Yanzu bai riƙeni ba mukaci gaba da tafiya ta wata ƙofar gidan da ba'a rusa ba amma an fasa ƙofa ya shigo cikin gidan muka shiga shine a gaba ina baya kamar yadda yace nazo jikinshi zanji natsuwa na samu natsuwar banajin tsoro cikin dakewa nake binshi har muka shiga ciki...
Wani irin yagegen palo ne kuma an ƙawatashi da wasu irin mahaukatan kujeru masu kyau palon yana da girma maisa kaji juwa ta kamaka anyi masa ado dai² da zamani , mutane ne cike a wurin maza da mata "yan gayu ibar farko sai ƙamshin gayu ke tashi , muna shiga Dikko yace tou ga An mata nan ku gaisa ina zuwa yana faɗin haka ya wuce , binshi nayi da ido harya shige ciki ,
Dawo da hankalina nayi wurin "yan cikin palo nace sannunku , yawwa ki zauna mana , a , a zan wuce ne kawai ina faɗin haka nabi Dikko inda naga ya shiga , suka ce kizo ki jirashi ya fito , ko saurarensu banyi ba na wuce ciki , a gefen gado na sameshi durƙushe rabin jikinshi a saman gado idonshi a rufe hawaye na zubowa daga cikin idonshi , da sauri na isa wurinshi nayi yadda naga yayi sannan nace masa Dikko wai miye ? Ba tare daya buɗe idonshi ba yace An mata cikina kamar zan mutu haka nakeji , kace kanajin yunwa kaci abinci to , bana iya cin abinci a yadda nakeji na , to kasha magani mana , zan sha jeki palo ki jirani kinji ko ? Cikin kuka na matsa kusa dashi nace nidai zan zauna nan , a , a karki zauna kinji jeki ina zuwa yanzu , nidai , cikin hayani yace da Allah malama fita ki bani wuri nace kije ki jirani ki tashi kusa dani bana san numfashinki yana sauka a jikina , matsawa nayi na zauna gefen gadon nace tou zan jiraka anan ,
Wani irin kallo yayi min tare dayin dariya , murmushi nayi nima nace meya baka dariya ne ? Ɗaure fuska yayi sannan yace ba dariya bace fusata ce , da gudu na tashi nabar ɗakin , tsoki Dikko yayi yace kin rufawa kanki asiri dana yi miki maganin kafiya , cire kayanshi yayi ya shiga wanka a daddafe....
A palo kuma sai caccakar abinci sukeyi yayin da wasu kuma ke tacin ɗamara cikin shiga irin ta mahaya doki sai naɗa rawani sukeyi , wuri na samu na zauna bana kallon kowa zuciyata ce ƙawar firana tana haskomin Dikko da ɗabi'unshi , murmushi nayi ƙasa² nayi magana nace mutumine kenan....
A hankali mutane suka fara ragewa dan har yanzu Dikko bai fito ba abinda dai na fuskanta ko wane yana tare da budurwarshi ne ko matarshi ne nidai shine ban gane ba dan banga sunyi kama da masu zaman "yan ci ba , ina wannan tunanin ne Ashiru ya shigo hannunshi riƙe da kofi inda nake zaune yazo ya bani da girmamawa yace wai mai gida yace in baki ki kai mishi , kai tsaye nace bazanje ba , murmushi Ashiru yayi tare da cewa yi haƙuri kije ki daina haka babu kyau kinfa san halinshi sarai haba ranki ya daɗe ki riƙa mishi uzuri , ni bazanyi uzirin ba a cikin ni dashi waye ya kamata yayi uziri wa wani ? Kiyi haƙuri duk wanda yayi haƙuri bai iske ba kaɗan yayi ki ƙara haƙuri wata rana zai zama tarihi , wane tarihi kullum abu ɗaya ni na gaji wallahi , yi haƙuri ki ansa kinga gashi yana kira , ƙin ansa nayi na gyara zamana , ɗaukar wayar yayi yace E mai gida , tou gashi nan zata kawo maka ya tsinke wayarshi , yace dan Allah ansa ki kai mishi , ansar kofin nayi na tafi ɗakin kai tsaye !
Bayan ƙofa ya laɓe ina shiga ya kulle ƙofar da makulli , a ɗan razane nace masa gashi cikin girmamawa , kalli can ya nuna min gado , kallo nayi sannan na kalli Dikko da yanayin tuhuma , yace haka kika ganshi ɗazu ? Girgiza kaina nayi alamar a , a yace ai kin rainani ko ? Tou yau so nake mu fidda raini dani dake , da sauri na kalli kofin na sake kallon gadon ya gyareshe tas , meye a kofin ne ? Ya tambayeni bansan ko miye ba , tou shanyeshi sai in buɗe miki ƙofa ki tafi idan ba haka ba kuma in ɗoraki saman gado kema in miki yadda kika ganshi , nidai ka ansa tafiya zanyi gida , ai ba wani gidan da zaki yau yayi maganar tare da matsawa jikin madubi yana kallon kanshi saida ya shafa gemunshi da bayan hannunshi na haggu sannan ya fara cewa one , bayan wani lokaci yace tow , three , four , five , da sauri nace me zanyi ? A harzuƙe ya kalleni yace shanyewa zakiyi sai kizo ki dafa ƙafata kice kin gode , idan kuma kika bari na irga goma saidai kiji Dikko a saman ruwan cikinki....
Six yaci gaba seven , eight , nine ..... Da sauri na ɗaga kofin na shanye na riƙe moƙoshi na tare dayin wata irin ƙara sannan na fashe da kuka na jefar da kofin kamar nasha guba har a zuciyata kamar an kwaremin ita ƙirjina zafi maƙoshina kamar an tsatstsargar minshi , dariya Dikko yayi yace services gobe ma ki sakemin kafiya zo ki gode , da sauri na isa gabanshi kaina yana juyawa na dafa ƙafarshi ina kyarma nace na gode , to jeki Ashiru ya maida ke gida sai mun haɗu a ɗakina gobe idan Allah ya kaimu , da sauri na miƙe yace kimin addu'ar saukowa doki lafiya , har yanzu wuyana kamar zai fita nace Allah ya tsare yasa ka sauko lafiya , daure fuskarshi yayi yace yawwa kije ngode , yayi maganar yana tillomin makullin ƙofar , da sauri na ɗauka na buɗe na fita ina kuka....
A inda nabar Ashiru a wurin na sameshi nayi gaba cikin ɓacin rai yace ta nan zamu bi , banza nayi dashi na wuce , maganar Dikko naji da tunda na fito ya biyo bayana naji yana cewa ina zakije nan bakiji ana miki magana bane zo nan , ba tare da nayi magana ba na dawo da hannu ya nunamin yace wuce ta nan kuje kuma karki daina kukan zanzo da daddare ,
Kallonshi nayi , cikin tsawa yace ki daina kallona ki wuce marece yanayi sai ina miki magana kita kikkifa ido kina kallona , bayan Ashiru nabi har yanzu ban daina kuka ba , komawa Dikko yayi yaci gaba da shirinshi wai zasu hau taka ango duk wani abokinshi na nesa dana kusa idan dai yana da rai da lafiya yazo , yasa an ɗauko An mata da ya ɗorata doki amma ta ɓata mishi , kayan daya ajiye mata ta saka ma badasu zaiyi tunda batajin magana...
Abokanshi sunso ayi shagali amma Dikko yace a , a , sun tambayeshi dalili yace shi yasan dalili kawai bazaiyi ba , shine suka tsiro hawan doki dan tayashi murna kuma shima zai hau dan yana bawa hawan doki mutunci na musamman ,
Tunda muka taho kuka nake ina jinjina irin cuta da zalinci na Dikko , har yanzu wuyana bai daina maƙaƙi ba zafi yake daga ƙirjina har abinda ya sauko zuwa ramin zuciyata , goge hawayen da suka sake taruwa a idona nayi sannan na fara tunanin ya akayi Dikko ya kasu gida biyu ? To waye ya kwanta yace in matsa gefe ? Da nayi kuka kuma ya akayi naga banga na kwance ba naga Dikko ya ɗago ? Mafarki ne zuciyata ta tabbatar min da haka dan haka na manta da wani da na gani yana kwanciya a mota....
A ƙofar gida Ashiru ya saukeni ya wuce da gudu ni kuma na shiga cikin gida , duk sallamar da nakeyi babu wanda ya jini bare nasa ran za'a ansamin Inna da matan Baba ƙarami suke ta faɗa wai ni na koyawa Safiyya iskanci kuma naje na anshi gadon su Babana na lashe duk wannan bai isheni ba saida nasa Dikko ya ɗaure mijinsu sunga yadda za'ayi a ɗauramin aure , Inna tace aure anyi an gama ba fashi ko ƙarami ya ɗaura aure ko karya ɗaura sai an ɗaura auren Sultana idan Allah ya kaimu lafiya gobe kuma ko ni sai in fita in ɗaura mata aure tunda ba shegiya bace ba , shaggu ma an ɗaura aurensu bare Sultana , dama waye yake nemar a fasa aure ai jiki magayi dan hausawa kuwa cewa sukayi ko wattuna bara baiji daɗin bana ba , ai hangen duniya ne yasa kike harin bashi ɗiya ke haɗamammiya , Inna tace haɗama sai wanda ya isa yakeyi wani yayi yaga idan zai samu cusa kai babu ƙwarjini , matan Baba ƙarami sukace murnar mutuwa dai murnar banza yadda yayi ma mijinsu itama zai mata haka nan , banji abinda Inna tace ba na shiga ciki raina ɓace na fara kiran wayar Dikko....
Takalmi zanoty ne a ƙafarshi wando kamun ƙafa jawha milihi "yar gabas , babbar riga girken nufe yasha rawani mai bakin fara sai wuƙar hawan doki dake rataye jikinshi a jirge yadda dai masu hawan doki keyi , yasha kyau harya gode ma Allah sai hotuna ake ɗaukarsu a ɗan yamutse yake dan bayajin daɗi sosai komai cikin ƙarfin hali yakeyi...
Bayan sun gama ɗaukar hotunan suka ɗunguma suka nufi inda aka ajiye dawakan duk wanda zai hau doki sunsha ado sosai , gaban dokinshi ya tsaya da yasha ado da sirdi tunbas ajikin sirdin anyi masa kwalliya da bishiri guda huɗu , kayan azurfa gaban fuskar doki ɗan wuya ɗan gaba , ƙasan sirdi aka sa labbati mai kyau ɗan gabas da sha hirji... Yana ƙoƙarin hawa tsadajjen dokin kiran Sultana ya shigo....
Ɗauka yayi ya kara a kunnenshi tare da cewa inajinki , wai kai da Allah Dikko mi yasa bakayin abu da lissafi ? Tafiya ya farayi dan komawa ciki saboda wurin yayi taron mutane da yawa Sultana kuma taci gaba da cewa in banda hauka ƙanin babana zakasa a ɗaure ? Ai kinsan ni mahaukacin ne kika faɗamin damuwarki me yasa ke mai hankali bakiyi maganin matsalarki ba sai kin sako mahaukaci a ciki to ? Dana faɗa maka cewa nayi kasa a kulleshi ? Wanda zai ɗauramin auren Dikko ? Tou ai sai a fito dashi ya ɗaura auren idan ya gama saiya koma , cikin hayani nace kai mahaukaci..... Kafin in faɗi maganar da zan faɗa yace ai kinsan inda kika barni kizo ki sameni in nuna miki girman haukata shi baya san ke ɗiyar ɗan uwanshi ce ba yayi ƙararki duk sansanci da aka kasayi a gida to inda ya kaiki a can zasu sasanta nine nakeyin shari'ar ne ? Ko nine nake ƙararshi ? Yarinya dake kuma kece mahaukaciya ni ina da hankalina dokin Dikko kawai dake in hau kuma inyi sukuwa......... Yana faɗin haka ya kashe wayarshi !
Cikin ɓacin rai ya fita ji yakeyi baima ɓatama An mata rai ba dama yace saiya zaneta iyakar raini duk girman duniyar nan baiga wanda ya rainashi ba kamar yadda An mata ta rainashi ba , ta kalli tsabar idonshi ta kirashi mahaukaci ta faffaɗa mishi duk maganar daya zo bakinta baida wata ƙima a idonta amma zataci ƙaniyarta , da ɓacin ran An mata ya hau saman doki ya zakuɗa yadda sukeyi idan zasu gyara , bayan ya gyara yayi ma dokin diddige kowa yahau nashi suka wuce cikin tsari da gogewa irin tasu ta mahaya doki ango a gaba abokanshi a baya suna taka ma ango wannan shine ake kira taka ango zasu ɗan zagane inda sukaga ya kamata abunsu dai na manya.....
Dikko yana kashe wayarshi Inna tana shigowa , wuri ta samu ta zauna take tambayata abinda ya haɗani da Ba ƙarami , duk abinda ya faru dani bayan bata nan saida na zayyane matashi kaf amma ban faɗa mata zance Dikko yamin fyaɗe ba amma duk abinda nayi bayan na Dikko ban ɓoyewa Inna komai ba , bayan na gama tace yanzu inashi Baban Hafsa ? Bansan inda yake ba , shifa Bello ? Shima bansan yana ina ba , Hmmm Inna tayi cikin takaici sannan tace to dan uban ƙarami ya manta ni kenan ? Amma ina cikin gidan nan har aka kawo miki sammaci saboda Dikko ya fini mutunci kika saƙe a jikinki har kikaje kika kai mishi ina nan kwance Sultana ? Inna ranar baki lafiya bana so na tayar miki hankali , jinjina kai Inna tayi sannan tace naso ace ahalin babanki suka ɗaura miki aure amma nasan haka baza ta samu ba dan bana tunanin ƙarami zai iya ɗaura auren ki saidai "yan uwana su ɗaura miki aure...........!
Ba tare dana kalli Inna ba nace ba naki ahalin ba na Babana , Baba ƙarami ne zai ɗaura aurena da kanshi gobe idan Allah ya kaimu a ƙofar marusa ƙofar gidan su Babana haka na faɗa ma Dikko kuma haka yasa aka rubuta a jikin i v kuma a gidan za'a ɗauki amarya Inna dangi uwa sunyi kuma suna nuna soyayya mai girma da fifiko wa nasu akan ahalin uba kowa dai da nashi wurin , amma su ahalin uba garkuwar rayuwa ne gaba ɗaya daga zaran baka dasu tou fa ka koma liƙe² , Inna tace a jikin i v masallacin G R A za'a ɗaura aure haka aka rubuta ana gama sallar juma'a , kuma ko ƙarami ya ɗaura ko bazai ɗaura ba mijina zai ɗaura aurenki idan mai kowa mai komai ya bamu aron rayuwa da lafiya anan gidan za'a ɗauki amarya duk wanda bazai zo ba yasha zamanshi a gida.... Tana kaiwa nan tace in fito za'amin ƙunshi mai ƙunshi tun ɗazu take jiranki , wai duk girman kwana takwas sai yau za'ayi ƙunshin biki idan Allah ya kaimu gobe naje saloon sai kace auren wasan yara danni ina kallon abun kamar a mafarki ne....
Daren yau duk inda ka shiga a gari maganar su Dikko akeyi labari ya barbazu duk inda ba'a tunani ya dangane , sunyi hawa mai kyau da burgewa abokanshi sunyi mishi kara sosai wasu ma basu taɓa zuwa katsina ba sai dalilin wannan aure , dan duk auren da yayi duka biyun ba'a a katsina akayi ba , sai yau mutane suka tabbatar suka kuma yadda da wannan aure , hotuna sai yawo suke a social media , duk abin nan sai yau Momy ta samu damar buɗe wayarta , shi kuma Dady ya kira Dikko yace ya rufe kaf wayoyinshi karya tsaya duk inda wani zai ganshi tunda yace shi damuwarshi a ɗaura auren idan an ɗaura zaiji da sauran matsalolin , Dikko yace E fatan alkairi Dady yayi masa sukayi sallama ,
Dikko yaso yaje wurin An mata bayan sun sauko daga hawa amma baya iya zuwa ga gajiyan doki ga kuma ciwon ciki dake neman hanashi ya miƙe tsaye koda suka dawo a daddafe yayi sallar magrib yayi isha'e sannan suka shiga gida a saman kafet ya kwanta a wahalce ya kifa fuskarshi saman pilow shi kaɗai yasan azabar da yakeji , abokanshi kuma sun daɗe suna fira bayan sunci abincin dare ne suka fara tafiya wasu zasu koma gidanjensu anan cikin gari , baƙi kuma suna tafiya masauki ,
Bayan kowa ya gama tafiya ne aka rage Dikko dashi dasu Ashiru , wayar wani ya ansa a yaranshi ya kira An mata amma duk kiran da yayi ba'a ɗauka ba saboda tabar wayar a ɗaki tana waje ana mata lalle , gajiya yayi da kira ba'a ɗauka ba ya mayar mishi da wayarshi , yace ma Ashiru ya samo mishi fura yaji ko zata shiga , fura dai itace ya samu yasha abinci dai ya gagareshi yau , abincin saidai aka fitar dashi dan ya lalace....
Bayan ta saka layinta Jiddah ta fara kira ko "ya "yanta bata nema ba sai Jiddah ta fara taɓowa ɗiyar zumuncin Allah Jiddah da ƙawayenta suna zaune a palon Sultana dan neman magana saboda bayan an gama jere an rufe da makulli amma sai ta kira aka ɓalle mata ƙofar wai wannan kujerun sunfi ƙarfin siyen ahalin caca mijinta ne ya siya dan haka babu wanda zai mata iyaka da dukiyar mijinta , komai na ɗakin amfani sukeyi dashi kuma cikin ƙeta da mugunta shi Dikko baisan abinda Jiddah take ciki ba dan ko ranar da Inna tace saidai ya rabawa Sultana gida bata faɗa masa cewa Jiddah tayi iskanci ba tace masa dai kawai ya rabawa Sultana gida da matarshi dan ta fahimci kawai da damuwa , shine Dikkon yace gidanshi bai gagareshi ba kuma shi babu macen data fi ƙarfinshi....
Jiddah tana ganin number waje ta san Momy ce dan haka tana ɗauka ta ɓarke da wani irin kuka mai tada hankali , na shiga3 na lalace ƙaryata ta ƙare kece garkuwata da bakya nan na zama abin tausayi duka na safe daban na rana daban har tsakar dare bai barni na huta ba saboda kawai zaiyi aure , wane irin aure kuma ? Momy wai baki sani ba ? Aure zaiyi har anyi jere yau duk inda kika shiga a garin katsina maganar hawan taka angonsu akeyi yace yayi hawan barin tarihi a katsina tunda ya auro muradinshi ni matar sadaka ce shi yasa baiyi ba a aurena dashi , Momy tace wai waye zaiyi auren ne ?
Saida ta sake ɓarkewa da kuka cikin makirci irin ancucetan nan tace Yaya zaiyi aure har anyi jere gobe ɗaurin aure haka akazo jere jiya bakiji yadda sukemin habaici ba suna zazzagina nayi haƙuri na ƙyalesu Momy ina cikin matsala , wai wane Yayan zaiyi aure ? Inji Momy , Jiddah tace Ya DK , Momy tace wai Dikko nawa ? Ko wane Dikkon ? Jiddah tace shi , Dady dake zaune saman abin sallah yana lazimi ƙaddarawa yayi ma bata wurin , Momy tace wace ce zai aura ? Caca zai aura , Momy tace wace ce Caca ? Wannan karuwar , wata irin zufa ta ketowa Momy cikin tashin hankali tace Dikkon wai ? Jiddah tace Eh , kashe waya Momy tayi ta fara kiran wayar Dikko amma a kashe yake , Ashiru ta kira bayan ya ɗauka tace ya bata Dikko yasan da kwanan zance dan hakanyace mai gida yaje kaduna wurin wasan polo , haka Dikko yace duk wanda Momy ta kira a cikinsu baya nan yana kaduna tunda dama zaije polo saukar da akeyi ma Sultana shine ya hanashi zuwa , Momy tace shi da waye ya tafi kadunar ? Ashiru yace shida wani abokinshi , turomin number abokin nashi , har zata kashe waya taji bata iyawa tace ubanshi ne yahau doki yau zakacemin yaje kaduna ?
Ashiru yace nidai ban sani ba hajiya nasan dai mai gida baya nan bara na turo miki number abokin nashi , ina jiranka ta tsinke wayarta , gyara kwanciya Dikko yayi bayan Ashiru ya gama waya da Momy dakel ya fara karanta tsohon layin Sultana dake hannunshi , bayan ya gama faɗa Ashiru ya tura mata ,
Tana gama waya da Ashiru ta kalli Dady tace kaji wai Dikko zaiyi aure , Allah yasa alkairi , Dady ya faɗa , Momy tace wai har Dikko nawa yake zaiyi mata biyu ? Dady yace yo shi ɗin na wasa ne ? Karuwa fa ? Karuwar aini daya faɗamin zaiyi auren nan da banyi tafiyar nan ba , kunga tun nan Dady ya zame kanshi , Momy tace kaima bai faɗa maka ba ? Dady yace um umm , haka Momy tayi ta gwada number da aka turo mata amma batayi , cikin daren ta kira "ya "yanta mata tace idan Allah ya kaimu gobe lafiya suje gidan Dikko daga amarya har danginta suyi musu terere .......!
Hmmm tou waye ma zaije ya tashi rashin kunya har gidan Dikko duk girman mutum Dikko ya sauke mishi rashin mutunci , baka zo gidanshi ba kayi masa yaje ya isko ka har mazaunin ka ya gwagwaɗa maka rashin mutunci ina kuma ga ka hawo layinshi a cikin gidanshi................ ?
Ranar ɗaurin aure !
Tunda safe Inna da kanta ta ɗaukeni a mota ta kaini gidan Kaka hmmm wai ni za'ama nasihar zaman aure , murmushi saida ta ƙari karatunta Inna ta ansa itama tayi har miyan bakinta ya kusa ƙarewa sannan tayi shiru kuma duk maganarta akan Dikko ne , daga gidan Kaka ta ajiyeni wurin wankin kai tace zataje ta dawo ,
Har aka gama abinda za'amin Inna bata dawo ba , ina nan zaune ina zaman jiranta kiran Yazeed ya shigo wayata , ɗauka nayi bayan mun gaisa yacemin An mata kanki ɗaya ? Nace meya faru ne ? Ki rasa wanda zaki aura sai DK haba An mata me zakiyi da DK ? Wallahi ba baki nayi miki ba ko kinje sai kin dawo kinsan iskancin DK kuwa ? Kuma wallahi ba sanki yakeyi ba yaudara ce kawai bakiga auren naku duk a munafurce akeyinshi ba ? Duk auren da yayi babu wanda baiyi hidima da shagali na tashin hankali ba , duk matan daya aura wallahi lefe akwatina 200 yayi kinga banbanci biyu ya fito ko ? Ji naki babu wani shagali tun nan kisan baya maraba da auren saboda baya sabgar mata yake so ya moreki ya koraki bayan ya gama hora miki zuciyarki da soyayyarshi , banbanci na gaba lefe akwati 24 yayi miki , kuma zai haɗaki gida ɗaya da matarshi cewa yayi wai bazai iya ajiyeki goruba ba gidan yafi ƙarfinki kinji yadda yake aibata ki ? Hmmm uwa uba kuma ga duka kwata² baisan darajarki ba mahaifiyarshi bata sanki ga masifar DK gana matarshi "yan uwanshi da mahaifiyarshi ina zaki saka kanki ? Ya ganki "yar yarinya shi yasa ya liƙe miki yayi ta cin zalinki Dikko mugune na bugawa a jarida kiyi karatun ta natsu kuma ki cire number na a wayarki nasan zai sake miki sabon layi ne ki kirani da sabon layin zan baki shawara , jiki a sanyaye nace tou ,
Ina kashe wayata Dikko ya riƙa zuwamin a zuciyata , kyawun fuskarshi maganarshi da yakeyi cikin sanyi sai kuma tsadajjen murmushin shi mai ɗaukar hankali kallonshi mai tayar da tsikar jiki rigimarshi idan ya kafe yana faɗa dani da gaskiyarshi jina yake kamar wata sa'arshi , murmushi nayi a zuciyata nace mutumi na Allah ya baka lafiya , amma fa maganar gaskiya Dikko yana da cuta a rayuwarshi , horn in Inna ya dawo dani daga tunanin dana lula , jakata na ɗauka nayi musu sallama na wuce....
Lokacin da muka dawo gida gidan ya fara ɗaukar taron jama'a ƙawayen Inna wankakkin matan da suka san abinda sukeyi , kuma matan Baba ƙarami sunzo dan rashin kunya da "yan uwan Inna , ɗakin mijinta ta wuce dan itama gobe zasu bar nigeria , ko walima bata tsayawa ayi da ita shi yasa bata da wani ishashshen lokaci kula da mutane tana ta shirinta ,
Ɗakin Inna na shiga ƙawayenta suka sa ni nayi wanka ina fitowa suka rubdigarmin suna min shiri na musamman nidai sai yanzu jikina ya fara sanyi da lamarin Dikko tsoranshi naji ya kamani da maganar da yayi min jiya a goruba wai muje saman gado mu fidda raini , sai wayar da mukayi dashi wai nice dokinshi zaiyi sukawa akaina , sai maganar Yazeed da yace Dikko ya ganni "yar yarinya shi yasa ya liƙemin zaiyi ta cuta na ne , fashewa nayi da wani irin kuka mai tada hankali nace nidai wallahi bana sansa ,
Inna data shigo yanzu cikin shiga ta wayayyin mata tace wane ne bakya so ? Dikko , dariya ƙawayenta sukayi gaba ɗayansu cikin shaƙiyanci suka kalleni cikin yanayin wayyo muna tausaya miki , Inna tace kin manta daren ɗaurin aurenki da Sultan abinda kikace akan Dikko ? Aimu saidai muce Allah ya baku zaman lafiya...
Ƙara sheƙewa sukayi da dariya , kamar wata taɓaɓɓa haka nabisu da kallo ɗaya bayan ɗaya Inna tace ke da Allah ki rufe mana baki ko ki fita ki bamu wuri , wata ce tace a , a karta fita tazo nan ta zauna , saman gado na koma bayansu na zauna sukaci gaba da firarsu na tafiyar Inna...... !
Bayan sallah juma'a dubun mutane suka sheda ɗaurin auren *DIKKO U DK* da amaryarshi *MARYAM ALIYU MUHAMMAD BINNA...* akan sadaki naira dubu ɗari ɗaya lakadan ba ajalan ba , ɗaurin aure yayi albarka wanda manyan mutane da dama suka samu damar halakta daga jahohi da dama , Baba Ƙarami yaje amma yaƙi yadda ya ɗaura aure mijin Inna ya zama waliyin Sultana , ana gama ɗaurin aure Dikko ya buɗe wayoyinshi , yana buɗewa saƙon Momy ya shigo !
_Idan ka kuskura ka ɗauko "yar duniya ka watsa kanka ka watsa gidanka , kuma tunda bansan yarinyar nan ko ka aureta saika saketa.....!_
Murmushi Dikko yayi tare daci gaba da duba saƙonni , hada Yayarshi itama ta zazzageshi tass murmushi ya sakeyi sannan yace aike a cikin kayan miya ko matsayin ruwa baki kai ba sharar bakin kwata dake , na ɗayar Yayarshi ya duba itama dai abun babu kyan gani da daɗin ji , kanku akeji , saƙon Dady ya gani shi kaɗai ke masa fatan alkairi , bayan ya gama dubawa Ashiru yaba wayoyin yana gaisawa da mutane.
Wallahi Uncle na zuba , Mardiyya ce tsaye a gaban Al ' Ameen yace haba Doughter da kin zuba maganin nan idan an ɗaura auren nan niba ɗan Babana bane , tayi masa rantsuwa cewa ta zuba saidai idan bashi ne yaci abincin ba ko kuma baici ba , dan abincin sa daban aka zuba mishi , jinjina kai Al ' Ameen yayi tare da cewa aiki ya kwana uban gayya ya mutu , muna fama da Jiddah Sultana ta shigo , dolensu kowa zata kama gabanta amma Jiddah ce farko sai Sultana tabi bayanta , Mardiyya tace Uncle tare zasu tafi gaskiya , Al ' Ameen yace tabbas ki faɗawa waccan jakar boka yace azo a anshi saƙo gobe , Mardiyya tace to ta wuce ciki , tana wucewa Al ' Ameen yace zaki bani motarki da manki da kuɗinki inje in biyawa kaina buƙata.......
A wahalce Dady ya kalli Bello saida yayi nishin wahala sannan yace ɗan iskan yaron nan ma inajin ma ya mata damu ! Bello yace kaidai mu fita lafiya , Dady yace nidai jibi idan Allah ya kaimu za'a kawomin kuɗin nan na bashi na huta da wahala Dikko ɗan iskan yaro ne , dariya Bello yayi ta taɓaɓɓi yace mai naɗawa manya kashi....
Umar dai baya gajiya da gulma da kanshi yaje har gidan Amisty ya faɗa musu mai gida ya auri Sultana , Hafsa ita bata nan tana abuja wurin wata shaƙaƙƙiyar mata ta hawan kwakwa mai ranar bacci , Amisty tanajin labarin auren Sultana ta haɗa dabar karuwanta hada su wane yaro tace kowa ya shirya su tara gidan amarya amma kar a faɗawa Hafsa dan gudowa zatayi ta dawo kuma tayi zubin kuɗinta dan bata ɗaukar asara ,
Momy kuwa tana daga can ta tattara kan yaranta ta turasu gidan Dikko tace idan suka ragawa Sultana da duk masu rakota sai taci ubansu , dan haka suma suka taho ko wace kanta ɗure da iskanci suka iso gidan ,
Mardiyya kuma ta ɗora Jiddah saida ta tabbatar tafi jirgin sama tashi hankalinta ya kwanta , kuma faɗa mata Uncle zaije zaria boka yayi kira , Jiddah tace zasu haɗu da daddare.
Yazeed kuwa sai ƙara kirana yake yana jaddadamin na cire numbershi karna manta ya sanni da mantuwa , raina ya ɓaci dan haka kallo biyu nayi ma numbobin suka zauna akaina gaba ɗayansu.....
13/11/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA...* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 76
Ina ƙoƙarin ajiye wayata kiran Dikko ya shigo , fashe wa nayi da kuka naƙi ɗaukar wayar harya tsinke wani kiran ya sake shigowa ban ɗauka ba sai kuka nake mai tada hankali , wayata na yada na tashi da gudu nabi Inna ɗakin mijinta dawowar shi kenan yana labarta mata yadda ɗaurin aure ya kasance , wai kuma ana gama la'asar za'a ɗauki amarya ! Ina zuwa na rungumeta tare da ƙara ɓarkewa da wani irin kuka mai kama zuciya , da tausayi ta ɗagoni daga jikinta itama hawayen ne kwance a idanuwanta amma bai zubo ba , da yanayin ko oho tace wai meye haka ? Bana san iskanci fa , shi kuma kukan na mene ne ?
Inna na kirata tare da kallonta ina shashshekar kuka na kasa magana , murmushin ƙarfin hali Inna tayi ta jani muka fita ɗakin muka koma ɗakin ta , wata ƙawarta ce ta miƙomin wayata tace ana kiranki kuma har yanzu Dikko bai daina kirana ba , ina ansar wayar na kasheta gaba ɗaya...........!
Inna da ƙawayenta kuwa nasiha sukemin wallahi hankalina baya wurinsu kwata² banajin su kuma bana iya tuna abinda suka faɗamin har suka ƙari surutunsu suka gama a , a ciki bana iya tunawa , bayan an gama nasiha na tashi nayi sallah la'asar kuma har nayi sallah na gama hawaye ke ratata daga cikin kwarin idanuwana , ina gama sallah aka fara shiryani dan kaini ɗakin mijina.
Babu wani daga ɓangaren ango daya zo bikon amarya , duk maganar Inna batayi tsegumi ba ita burinta kawai akaini ta huta dan a ganinta aurena shine natsuwa a gareta dan tasan idan ta tafi ta barni yawo zanci gaba dayi tunda Allah ya kawo mai kwasheni sauka lafiya....
Babu abokin ango ko ɗaya duk motocin Dikko ne akayi amfani dasu wurin kai mutane gidan amarya , ni kuma a motar mijin Inna aka ɗaukeni dashi da ɗan uwan Inna sune suka kaini har gidan Dikko da kansu......
Da farin ciki masoyana suka shiga gidan tare da dabar su Amisty domin sun riga amarya isowa sai aka shiga a tare kowa dai da abinda yake faɗa irin dai abun nan namu na mata yadda mukeyi idan ankai amarya kun dai gane irin abun ai , Jiddah kuwa ta murza wani irin ƙaton wanka na tashin hankali kamar zata tashi duniya dan haɗuwa kai Jiddah "yar gayun bala'e ce kanta yana hayaƙin rashin kunya , wata irin guɗa ta rangaɗa ayyuri yuriiii........ Ƙawayenta suka ansa da barka da zuwa *CACA* ga caca ga tawagar karuwanta a baya fatan kunyo mana tsarabar kwalaben giya a cikin jikkunanku dan kunsan ba'a shiga kasuwa saida kuɗin siyayya amfani giya kenan sai ansha akejin muradin mace , giya mata caca sana'ar uban wata ƙawata ne , hehehe ram aka kashe kundai san iskancinmu na mata yadda yake.....
Yayyen Dikko dai turawa ne sun huta tunda banajin abinda suke cewa kunsan ajiboters basu iya faɗa ba haka kuma basu iya hayani ba daga zaune dai suke ta watso nasu kalaman cikin harshen turanci , kuma su ƙawayen Inna babu wanda yayi musu magana , Mardiyya ce naji tana cewa gashi nan Aunty zai shigo , cikin yayun Dikko ne naji wata ta turance abinda yasa na fahimta naji Mardiyya tace Dikko ne , kila ta tambayi Mardiyya waye ne tace shine , kowa dake palon yayi tsitt , murmushi nayi a zuciyata tare da cewa sannu da zuwa jarumina , ban ganshi ba amma na hasko yadda zai fito daga mota ,
Zaiyi parking cikin ɓacin rai , sai ya fito daga mota da yanayin shagwaɓa zai tunkaro palon cikin jarumta zaiyi mazurai da kyawawan idanuwanshi idan ya shigo , daddaɗar muryarsa zata bayyana yanzu , sallamarshi naji yayin da ake ƙoƙarin shiga dani hanyar da zata sadamu da inda aka bani mazauni da "yan uwanshi ya fara gaisawa sannan ya kira Jiddah suka wuce ciki.
Ƙarshen ɗaki aka kaini wato bedroom saman tsadajjen gadona aka ajiyeni a gefen gado , nasiha dai aka ƙara yimin an nunamin matsayin haƙuri biyayyar aure kauda ido akan ƙaramin abu danne zuciya yayin fushi , ba abun duniya baya duk girmanshi tsabta naga yadda abiyar zamana takeyi inyi ƙoƙari in wuceta a gayu , babu wanda ya zauna saboda yanayin hararar da ƙawayen Jiddah ke watsoma "yan kawo amarya abinda yasa ma basuyi yunƙurin yin wani abu ba dan Dikko yana nan , shima Umar ne ya faɗa masa za'a tashi bama²n masifa a gidanshi shi yasa ya taho , duk wani abu da za'ayi a wurin walima idan Allah ya kaimu gobe Inna ta ƙanƙare da dangin miji , tayi gara na fita kunya kuma duk Dikko ne yayi dan ya siyamin mutunci a wurin ahalinshi....
Amisty taso tayi magana dan na lura da bakinta amma ƙawayen Inna suka ce kowa yazo a tafi yanzu , amma tacemin akwai dawowa , inaji ina gani suka tafi suka barni , Oh saini ɗaya a ɗakina kamar mayya babu ƙawa ko ɗaya babu wasu "yan uwa da zasu kwana a gidana , jakata na jawo na fiddo wayata na kunna bayan ta gama kunnuwa na kira Inna , amma bata ɗauka ba ,
"Yan palo kuwa kowa cikinsa ɗure da iskanci a ƙagare suke Dikko ya fita su caccakeni san ransu amma yaƙi fita har aka kira magrib , suna tunanin zai tafi masallaci a gida yayi sallah , isha'e ma haka , Yayyen shi ganin bashi da niyar fita sukayi mishi sallama suka wuce , godiya yayi musu tare da cewa ku huta gajiya , amma sun ɗauki gudirin zasu dawo idan Dikko baya nan , Sultana ta samu ɗagin ƙafa na yau basa so suyi rashin mutunci Dikko yana nan idan ya birkice musu gano dai²nshi sai Allah.
Misalin 9pm ya kira Jiddah ɗakinshi ya faɗa mata cewa idan Allah ya kaimu gobe rai da lafiya duk wata ƙawarta data san tazo gidan nan to ta tattara ta kama gabanta har Mardiyya baisan ganin kowa idan kuwa ba haka ba za'a samu matsala , amma sai Jiddah tace ƙawaye na zasu tafi amma fa Mardiyya babu inda zataje wallahi tunda tuni Momy ta gama magana idan kuma dan kayi aure zaka tona min asiri saika haɗa hada ni ka koremu gaba ɗaya....
Cikin ɓacin rai Dikko yace Mardiyya ta tafi daga gidana Jiddah , wallahi babu gidan ubanda zataje , Mardiyya ta barmin gidana gobe kafin raina ya ɓaci , wallahi ba zataje ko ina ba idan saboda kayi amarya ne sai haɗa hadani ka sakeni kuma kake maganar ta bar maka gida ai bani nace ta zauna ba Momy tace saboda haka ka bari sai ta dawo , tana faɗin haka tayi gaba abunta , shima tashi yayi ya nufi ɗakin amarya Sultana...
Da ɓacin rai ya tunkari ɗakin Sultana yanajin tuƙuƙin maganar Jiddah da tace babu gidan ubanda Mardiyya zataje zaici uban yarinyar nan amma sai zuwa gaba dan yanzu duk idon jama'a akanshi yake yana iya mata wani abu ace daga yayi aure ya fara cusa mata damuwa , yana da cikin Jiddah duk ranar daya tashi haifeta zai wulaƙanta mata rayuwa yadda mai tunani baya zato, ina zaune a inda nayi sallah har yanzu ban tashi ba ina ta kiran wayar Inna ba'a ɗauka , babu ko sallama ya shigo ke An mata ni zakiƙi ɗaukar ma waya ne ? Dake kin ɗaukeni sakarai ma daga baya kika kashe wayar wai me kika maidani yana maganar yana shigowa cikin ɗakin , kai tsaye nace mahaukaci , kalmar hauka ya fita daga bakinki dan jiya ba yau bace doki , dokina ya ƙarasa maganar yana ɗaukata yaci gaba da cewa do ki , da iskanci yake faɗar do..... Sai yace ki , yana yin irin yadda akeyi idan an hau doki bari ki fara jin nauhi na sai ki fara kiyayata tun kafin mu fara wasan danbe ,
Dikko bana so , a , a ya maƙale ƙafaɗar shi irin yadda ƙananan yara keyin ƙiwya yayi maganar a shagwaɓe yana yin wani ɗan kukan shagwaɓa mai sa mutum yaji yana lilo tsakanin sama da ƙasa , cikina naji yana halbawa jikina yanamin wani yami² a dai² lokacin daya saukeni saman gado yana min wani irin munafiki kallo mai nuni da zakici gidanku sannan ya sake cewa do ki yayi min kyakkyawan murmushin shi mai fiddo mishi da ai nahin kyawun shi ƙuramin ido yayi sannan yace ai dokina ne ke ko An matana ? Rufe idona nayi cikin jin kunya nayi murmushi kaɗan!
Ina sanki , idona a rufe nace Dikko dan Allah kada kaimin komai , ke meye nace ? Cewa kayi kana so na , ke kuma meye kike faɗa ? Cewa fa nayi kawai ina sanki , to idan na faɗa nima bazakamin wani abu ba ? Naga alama dai idan banyi wani abu ba bazakiji daɗi ba dan na lura kina tsammani wani abu daga gareni , buɗe idona nayi tare da cewa , a , a , ido ɗaya ya kashe tare da ɗagamin gira yace sumbata ɗaya tak , ai nasan bazai tsaya a ɗayan bane , durƙusawa yayi a saman guyawunshi ya dafa hannuwanshi gefe da gefe ina tsakiya kallona yayi sannan yace kamar ya ? Cewa nayi nasan bazai tsaya a ɗayan bane ba , murmushi yayi tare da kwanciya saman jikina a gajiye buɗe bakinsa yayi kaɗan da ajiyar zuciya mara sauti sannan yace Oh to kenan kin yadda da sumbatar ashe ? To amma nasan bazaka tsaya a ɗayan ba , da hannunwanshi biyu ya riƙe kaina cikin kwantattar murya ya ɗora bakinsa a saman leɓuna na yace ɗaya tak ya faɗa da wata irin murya mai tayar da tsikar jiki , cikin mutuwar jiki nace amma dai karya wuce ɗaya , murmushi Dikko yayi tare dayin wata irin sukuwa a kaina cikin sigar mugunta kamar yadda yace sannan ya ɗagani yana cewa tausayinki nakeyi An mata nasan baki iya ɗaukar Dikko wahala zan baki "yar yarinya ta bara dai inzo muyi bacci kinji ko , yana faɗin haka ya fita da tafiyarshi ta sakakkin "ya "ya ,
Ajiyar zuciya na sauke tare da lumshe idanuwana ba haka naso wasan ya ƙare ba , me ma Dikko yake nufi yana nufin ido zai sakamin saboda nayi ƙarama kai kuji mugu fa , hmmm lallai Dikko ba baƙon mace bane ba , amma maƙetacin mace ne , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya kamar yana nan na rufe fuskata.
Shiru² Dikko zai dawo babu shi ba labarinshi , tsoki nayi tare da gyara kwanciyata , tun ina tunanin Dikko zai dawo harna fitar da rai yana wurin Jiddah a can ya sauke damuwarshi yayi baccinshi ya manta dani , haka na haƙura nayi bacci da tunanin Dikko...
Yauma nayi mafarki da mutumin nan kuma ya faɗamin ya ƙwaƙwale gobe saura ni tunda na shiga sahun ma'aurata , a firgice na farka tare da kwarara wani irin firgitaccen ihu wanda ya karaɗe kaf girman gidan gaba ɗaya duk mahaluƙin dake gidan babu wanda baiji ihuna ba , ina buɗe idona na nufo palo da gudu ban tsaya ko ina ba sai jikin firij na buɗe na ɗauka ruwa saboda wata irin ƙishirwa da nakeji kamar zan mutu , saida na shanye roba ɗaya ta ruwa , a wahalce na dawo da baya na zauna saman kujera ina goge zufa...
Jiddah ce ta fito sanye cikin wasu irin kafirawan kayan bacci idonta da yanayin bacci tace uban waye nan yake mana kuka ? Kallo ɗaya nayi mata daga nesa na fahimci fitina ne ya fiddota kuma uwarta zanci yadda nake haƙe da ita saboda kirana da tayi da caca , ubanki ne yake kuka na bata ansa a dai² lokacin da Dikko ya dafa ƙarfen bene daga sama sboda mu dukanmu a yanzu muna ƙasa kowa ta sauko , ni abinda yasa na fito palon ƙasa nasan bazan samu ruwa a palo na ba shi yasa na gangaro na ƙasa nasan zan samu , ita kuma Jiddah masifa ya fito da ita ni kuma yau zan sauke mata duk wata tsutsar iskancin dake cizar mata kwalwa , An mata ya akayi ne ? Dikko ya tambaya , ruwa nasha na bashi ansa ba tare dana kalli inda yake ba , Jiddah kuma tace Caca ni kike zagi ? Sai in takaita miki rayuwa na illahta banza ba abinda za'ayi , Dikko ne yace kinsha ruwan ne ? Ey nasha , tashi kije ki kwanta tou ,
Babu gardama na miƙe zan tafi Jiddah ta riƙoni ta baya ta fara zagina tana cewa ke "yar marasa tarbiya babana bazai zagu a bakinki ba danni Babana bai sakani a caca ba , shi Babana yasan darajar matansa yasan na "ya "yansa kaf zuri'armu bamu da "yan iska banza ahalin kwarata , Dikko ne yace An mata wuce kije ki kwanta kinji , tou na bashi ansa tare da ƙwacewa Jiddah ta sake riƙoni taci gaba da cewa...
Kuma ni babu wanda ya siye gidan hayarmu ya mayar da gidan kiwon dawakai karuwar banza karuwar wofi , murmushin takaici Dikko yayi tare da cewa An mata taho , ƙyale Jiddah nayi na tafi ita kuma taci gaba da cewa ƙaryar banza ƙaryar wofi ba ance ke wata shegiya bace ba da kin tsaya dana ciccire miki gashin kai , Dikko yace gashin kanta kike baƙin ciki dashi ? Dan a lokacin Sultana ta shiga ɗaki bata san wainar da suke toyawa ba , yaci gaba da cewa mace kenan An mata ta burgeta ina ga maza kuma kenan ? Wannan shine zaɓi na farko dana fara cankowa a rayuwata ƙatuwar banza da ƙanƙanuwar yarinya ta fiki tunani , yana faɗin haka yabi bayan Sultana....
Ai kaine ƙaton banza ko kunya bakaji kaje ka auro wannan "yar magen yarinyar idan ka isa kaje ka auromin min cikakkiyar mace wacce zata fito na fito itace kishiyata Dikko da zai shiga ɗakin Sultana yaba Jiddah ansa cewa wannan ma ta isheki yana faɗin haka ya shige , ita kuma taci gaba da cewa wannan yarinyar ni wallahi ba kishiyata bace ba "yar aiki ce ka kawomin kuma tayimin iskanci saina bata kashin bala'e , ƙawayenta suka fito suka jata suka koma ciki da ita suka ci gaba dayi mata huɗubar shaiɗan!
An mata kukan me kike a tsakar daren nan ? Ba komai na faɗa cikin ɓacin rai , kusa dani ya zauna ya riƙoni na kwace kaina tare da matsawa daga kusa dashi dan haushin sa nakeji baizo ya kwana dani ba , kuma ko "yar kazar da ake bawa amare ni bai kawomin ba , ƙara matsowa Dikko yayi zai taɓani nace da Allah ka ƙyaleni , tou na ƙyaleki amma kiyi haƙuri dan ma an sakaki a caca to miye ? Shi a tunaninshi inayin fushi ne saboda maganganun Jiddah tou inajin ciwonsu amma nafi jin haushin shi a yanzu ,
Gyara bakina nayi banyi magana ba , cire takalmin ƙafarshi yayi suba silifas ba kuma ba soso bane ba amma dai zubin slifas garesu , kwanciya yayi saman gadon yace tou taho ki faɗamin , yi nayi kamar banji ba , bai sake magana ba ya gyara kwanciyar shi yaci gaba da baccinshi hannunshi a saman cikinshi inajin har yanzu cikinsa bai daina ciwo ba , can nesa dashi na kwanta ina kallonshi ,
Haba Jiddah ina wayewarki ? Ina barikinki ? Ina feƙewarki ? Maza fa idan sukayi sabon auren kansu rawa yakeyi ya kasa tsayawa wuri ɗaya ki fita sha'aninshi da matarshi ba jibi zai tafi ya barku ba ? Jiddah tace Eh to ki bari idan baya nan ki riƙa ci mata uwa la'ada waje idan gaban idonshi ne saiki riƙa tattalinta kina nuna mata soyayya ko ƙararki takai masa zaice bata san zaman lafiya , kibi sannu ki zuge mata rayuwar uwa kamar iccen zogala karki sake ki barta ta huta idan azaba tayi mata yawa ita da kanta zata gudu , salon mugunta sanka² suka koyawa Jiddah....
Kiran sallah asuba ya tashi Dikko daga bacci ni har lokkacin banyi bacci ba saboda tsoro , da sauri na juya mishi baya na daina kallonshi , sauka yayi daga saman gadon ba tare da yayi magana ba ya fita daga ɗakin....
Cike da tausayin Sultana ya koma ɗaki shidai yana tausayinta gata "yar ƙararrama shi tayi mishi yarinya ji yake idan yayi jijjiga akanta kamar zataji ciwo , domin shi dai buƙatarshi tana da girma An mata bata iyawa dashi wancan ma da yayi mata yana nadama kuma har yanzu bai daina ba , shidai kawai ya aureta ne dan ya natsar da ita wuri ɗaya tunda kullum yana tare da ita , na biyu kuma ya aureta ne dan girmanshi daya sake mata yasan duk lokacin data ganshi zata riƙa hango abunda ya shiga tsakaninsu , tou waishi tayama zai fara hayema An mata gata duk ta rame ta zama wata "yar ƙarama shidai an cuceshi wallahi wannan ai ɗaukar alhaki ne , ɗan gajeren tsoki yayi sannan yace in taɓota kuma ta taramin mutane ma a gidan nan dana fita kowa yasan abinda nayi , ummm abundai ba wani sirri....
Dikko na fita masallaci Jiddah da zugar ƙawayenta suka shigo ɗakina hada Mardiyya , a saman abin sallah suka sameni tsaye zan kabbara sallah , Jiddah ce ta kama hijabina daga wuya ta yageta har ƙasa ta wurgar da tsumman ta cire kallabin kaina tana taɓa gashina , bayan ta tabbatar ban jiƙashi ba tace Allah ya rufa miki asiri da na rantse da girman Allah yau saina safke miki gashin kai banza ɗiyar ɗan caca tayi baya , Mardiyya ta matso tace ni nan da kika ganni nafi haɗarin jirgin sama kyan gani , ni haɗarina girma ne dashi domin idan nabi ta rayuwar mutum na fita tou fa lallai ya gama rayuwa har abadan duniya , na shigo gidan nan da niyar tarwatsawa ai kin tuna labarin dana baki a mota ko ? Daga haka bata sake cewa komai ba , ƙawayen Jiddah suka ci gaba da zuwa gabana ɗaya bayan ɗaya wasu su shafa fuskata wasu kuma su shafa gashin kaina , wata ma cewa tayi wannan ƙugun duk ke ɗaya ? "Yar yarinya dake da wannan babbar halitta ina kuma ga ni'imar aure ta tsargaki lallai Jiddah sai kinyi da gaske idan kuwa ba haka ba saidai tashin zance , haka dai sukayi ta daƙuna ni yayin da wasu suka riƙe ƙuguna suna jinjinawa , wasu kuma suna kallon gaban rigata dole Dikko ke birkicewa koni na samu wannan ai na gama da ko wace irin mace , dariya sukayi gaba ɗayansu banda Jiddah da Mardiyya ,
A ƙawayen Jiddah mutum 3 ya rungumeni ta ƙarshen itace ta warware gashin kaina ta rungumeni ta baya ta umarci wata cewa tayi mana hoto , ɗaukar hoton akayi da ƙarfi ta juyo dani ta sake rungumeni tace a ɗauka , sake ɗauka sukayi ana gama hoton tace ina sanki , murmushi nayi tare da kallonta nace ai tun baki faɗa ba na sani , gaba ɗayanku zan iya fitar da fetir zan kuma iya fitar da kalanzir a cikinku ,
Ku baƙin mata ne kuma baƙine a harkar lesbian ƙananan "yan iska , ke Mardiyya ke zaki basu labarin Sultana duk wacce tasan ta rungumeni a cikinku saina ɗauko mata hoton uwarta tsirara , ita Mardiyya furtawa kawai tayi ni na cika mata kalmarta ta hanyar ɗauko ubanta a cikin yanayi mafi muni a rayuwa , ke Jiddah kike ko wace ce ? Ni nan da kika ganni iskanci ne ɗore a cikin cikina da zaran kin latso wurin ƙaryarki ya ƙare ki kiyayi haɗuwarki dani , me kike tunani ne ? Tou idan baki sani ba a daren jiya Dikko maimaicin dahuwar dambu yayi min ko an faɗa miki ni ƙazamiyar mace ce mai kwana da janaba a jikinta ? Anyi an kuma an ƙara an ƙara ƙarawa kuje waje ku jirani kafiran banza da bakwa kallon alƙibla , tsoki nayi tare da naɗe gashin kaina na nufi hanyar toilet ,
Dariya Jiddah tayi tare da cewa burgar banza yo me yayi dake a daren jiya bayan tare ya kwana dani ? Ihun ki yasa ya fito banza duk abinda ya shiga tsakaninta da Dikko a jiya da magiyar da yayi mata dan da farko bata yadda ba haka tayi ta tonawa Dikko asari abindai bai kamata ba , jin kukan motarshi yasa suka fita daga ɗakina Jiddah naci gaba da basu labari suna dariya ,
Jakunan banza duk saina ci uwarsu in Allah ya yadda wallahi naji ciwon yadda Jiddah ta buɗe sirrin Dikko abun baimin daɗi ba amma zai dawo ya sameni saiya faɗamin abinda yasa ya aureni , wayata naje na ɗauka na kira Inna yanzu ma bata ɗauka ba ,
Wannan tafiyar ma dubu ɗari biyar Jiddah ta bawa Al ' Ameen bayan ta cika masa mota taf da mai ya nufi zaria , zuciyarshi na saƙa ƙeta iri² , su kuma ƙawayen Jiddah shatar mota sukayi bayan sun tabbatar wa Jiddah zasu dawo sati na gaba...!
Har yanzu ban daina kiran wayar Inna ba daga ƙarshe ma kashe wayarta tayi , tashi nayi na koma saman gado na kwanta ina kwanciya wayar Amisty tana shigowa , ɗauka nayi bayan mun gaisa take cemin Nana ta rasu , Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Amisty wace Nanar na tambaya idona cike hawaye , Amisty tace Nana wacce kika sani ? Me ya sameta ne ? Wallahi lafiyarta qalau tayi mana bankwana da dare ta fita asubar nan aka tsince gawarta an yadar da ita a bakin bola bayan an kwakwale mata idanuwa kuma an cire wasu sassa na jikinta babu nisa da wata maƙociyarmu itama haka aka cire idonta aka yadar da ita a saman bola bamu san abinda yake jawo hakan ba , wani irin ihu na kwarara tare da yada wayata ƙasa ina cewa na shiga 3 shi kenan sai ni yau zan mutu wayyo na bani na lalace shikenan ashe bazanyi tsawon kwana ba ,
A wannan yanayin Dikko ya shigo ya sameni , tambayana yayi abinda yake faruwa , kai tsaye na kwashe kaf na faɗa masa amma sai yacemin wai sheɗan ne yake zuwamin a bacci , haka ya lallasheni bayan ya faɗamin cewa shima da haka yakeyin irin nawa ko rashin lafiya ko wani zaiji damuwa duk abinda zai faru da wani a gidansu ko waye zai gani a bacci idan kuma ya tashi abin zai zama da gaske , wannan karki wani damu sheɗanu ne kuma zai daina , kallonshi nayi sosai sannan nace sheɗanu wane iri ? Aljannu mana , cikin tashin hankali nace wane irin aljannu kuma nayi maganar cikin mutuwar jiki na tsorata , cikin hayagaga yace ke da Allah ban sani ba ,
Nima cikin hayaniyar nace kar Allah yasa ka sani kuma ya toshe ilimin sanin naka , murmushi yayi tare da cewa tayi bakan damiyar nata saina kaiki goruba anjima naci ƙaniyarki "yar rashin kunya , sai kaje goruba zakaci me yasa anan baza kaci ba , anan ? A , a , ni bana taɓa ki a gidan nan ki ɓarewa mutane baki kiyi ta musu ihu saina kaiki can zan rufe ƙofa in baki wahala sannan na dawo dake , idan ka tashi karka dawo dani da raina ka kashe ni , babu wanda ya taɓa mutuwa kuma a kanki baza a fara ba amma zaki ci gidanku ƙaramar yarinya mai bakin tsiwa , badai kinci kaza ba ? Hmmm saina kulle bakin rashin kunya...
Sai kazo ka kulle , hmmm bakina waye ya isa ya rufemin tunda ba mutum ya bani abuna ba , juyawa Dikko yayi ya fita daga ɗakin bai sake magana ba , wayata dana faɗar ƙasa na ɗauka tare da cewa Allah ya jiƙanki Nana ke kuma taki ƙarshen haka yazo Allah na roƙeka ka taimakemu muyi kyakkyawan ƙarshe , da yanayin mamaki nace tou shi Dikko da yaga nashi sheɗanun ko ance za'a kashe shi ? Wayata na ɗauka na fara kiranshi , ƙin ɗauka yayi a bayyane nace kai ta dama , yana ramawa ne dan ya kirani jiya ban ɗauka ba , tou saina kira so adadin yadda ya kira bai ɗauka ba sannan zai anshi kiran nawa...
Da zullumin mutuwa a raina na koma bacci , wanda baiyi shawara dani zaizo ba , Dikko wanka yayi ya fice danshi Allah bai masa baccin safe ba , cikin bacci naji ni ina lilo saman ruwa da sauri na buɗe idona Jiddah na gani tsaye rungume da bokita a hamatar ta kaɗa kai tayi tare da nunamin inda agogo yake sannan tace an samu gado an wani mimmiƙe sauka kije kiyi aiki ko kina nufin nice zan girka miki abinda zaki ci ,
Kallon Jiddah nayi sannan na kalli inda ta jiƙa gadon sauran ruwan bai gama shiga cikin katifar ba nace ke zan dafa ma ko wa ? Ɗan ya tsina fuska tayi tare dayin wasa da bokitin hannunta cewa me kika iya wanda zaki girka ki bani naci ? Ai gidan ɗan caca babu cima , ƙanzo gari sai kuwa kwaɗon tuwo idan an samu kinga baki da ilimin dafamin abinda zanci , to me yasa kika tashe ni ne ina bacci ? Saboda baki isa kiyi bacci ba tashi zakiyi ki girkawa masu aiki abinci , saukowa nayi daga saman gadon nace aiko ubanda ya aifeki zanci , caca ubana yafi ƙarfinki mijina ma ya gagareki bare Babana ,ai saidai kici abinci ki miƙe a saman gado kafin Momy ta dawo taci uwarki ki koma inda kika fito , ni bana faɗa da kishiya saidai na kwace mijin ciwon zuciya ya kasheta , taya ma zan fara haɗa jiki dake in kwashi talauci ?
Ai an daina faɗan kishi saidai ayi a ɗakin miji , ido fa yana kallo wallahi saidai ki gani ki haɗe yawu lafiyayyen namiji mai kuzari wanda babu irinshi a bariki , jarumi ɗaya mai naɗawa mata duka naushin shi da daɗin kalamansa wurin yabo nada daɗin saurare Yaya yafi ƙarfinki , mamayata aurenki yayi tunda kin shigo saidai kici abinci kisha ruwa amma Dikko yafi ƙarfinki , daren farko na a america nayi shi , naci kaza nasha lemu keko ko ruwan faro ba'a baki ba , mijina ya kwaremin kayan jikina idonshi yana kallon nawa cikin soyayya ya lallaɓeni yayin daya kwanta dani , Allah yayi miki albarka Jiddah shine abinda ya furta lokacin daya jini sabuwar mota ce kin kawo min budurcinki ya faɗa cikin jin daɗi , gyara riƙon bokitin tayi taci gaba da cewa , a jiya kuma riƙeni yayi a jikinshi saida yayi min kirari uwar gida sarautar mata farar mace alkebbar amarya ni waccan jakar ban ɗauketa mace ba shi yasa na baro ta nazo gareki ki bani maganin damuwata tou ina soyayyar ? Ai dama a saman gado ake nunata ɗakinshi yafi ƙarfinki bare har kisa ran hawa saman gadonshi wannan ni'imar Jiddah kaɗai zataji ƙwalelenki Caca ,
Ngode sosai da saƙon ta'aziyyarku a gareni , Alllah ya bada lada ubangiji muma ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo am3n ,
Kuyi haƙuri idan har kunga banyi typing ba wallahi ina da ƙaton dalilin daya hanani kuyi haƙuri ni bana mantawa daku kuna raina kamar yadda An mata take a ran Dikko ,
*RABI MUSA* katsina zance ko kaduna ? Mrs Usman Abdullahi yau nayi typing sai a sakarmin mara inyi fitsari , mu duk muna miki fatan alkairi ubangiji ya ƙara zaman lafiya da kwanciyar hankali "yar uwata ,
17/11/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA ce....*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 77
Murmushi nayi tare da shiga toilet na ciko boket da ruwa nazo na sheƙawa Jiddah bala'e Caca ni kika jiƙa ta fara anbaliyar aman zagi na "yan tasha ban bi takanta ba na koma toilet na sake cikowa nazo na zuba a gado sannan na mayar da bokitin na fito har yanzu bata daina zagi ba , bayan na fito na matsa gabanta nace sa idonki a nawa wace ce ke ? Waye Dikko ? Anshe goruba a hannun kuturu ba wuya yake ba , makaranta guda gareni da na tara taron mata nake basu ilimin zaman gidan aure nice malamar , ke har kin isa Dikko a nawa yake ? Bare kuma ke da baki da lissafi balbaɗaɗɗa mai tona asirin mijinta , ni bana kuri haka kuma bana cika baki a zahirance nake bayyanar da saƙona , maganar Dikko da ɗakinshi rashin cin kaza ko ya kwana a ɗakinki ba damuwa na ne ba , amma zan nuna miki yadda ɗakin miji ke zai gagareki shiga sakarar banza , kuma daga yau idan kika sake cemin Caca saina caccake miki idon uwa.
Wani irin duka takaimin a fuska a wahalance na riƙe hannunta tare da cewa bani zaki daka ba ki koma wurin wacce ta faɗa miki saiki faɗa mata abinda nace idan ta baki ansar magana na kya dawo , kokowa ta kamani dashi ga sulbin tiyels da aka jiƙa kuma ai Jiddah tafi ƙarfina tunda shekarunmu ba ɗaya ba , bamu wani daɗe muna cakusawa ba Dikko ya shigo cikin ɓacin rai gaba ɗayanmu saida ya zazzabga mana mari sannan yace meya haɗamu ?
Cikin fushi na juya mishi baya ina kuka ƙasa² , itama Jiddah kuka takeyi kunsan "yan gayu basa san wahala tasha mari ni kuma dama na saba , ni kuma yunwa ce ta saremin guyawuna da kuzarin jikina , cikin kuka take faɗawa Dikko abinda nayi mata da turanci , raina a ɓace nace idan ba munafurci ba a faɗa da yaran dana sani mana , Dikko yace ma Jiddah ta tafi , juyowa nayi tare da cewa ina zatace ? Ai babu inda zataje kayi gulma kace taje kuma ? Allah dai ya haɗani da munafikin miji.,
Nine munafiki An mata ? Eh idan ba munafurci ba kaje kacewa Jiddah ka ƙagara Mom inka ta dawo ta wulaƙantani baka so na ni jakace shi yasa baka siyomin kaza ba , ita kuma a daren farkon ta taci kaza tasha lemu ni ko ruwan faro baka bani ba , itace farar mace alkebbar amarya , bazanje ɗakinka na kwana ba shi yasa ta jiƙamin jikina da gadona wai a gidanmu ba'a hawan gado zan kwanta a ƙasa sanyi ya kamani ɗakin miji yafi ƙarfina bare na fara tunanin hawan saman gadonka , kuma jiya a ɗakinta ka kwana kana mata magiya , Dikko yace nine na kwana a ɗakinki ? Yayi maganar yana kallonta ? Yaci gaba da cewa nine nace miki ina jiran Momy ta dawo taci mutuncinta ? Ni nazo ɗakinki ???
Fuuu Jiddah ta fita daga ɗakin , kallona Dikko yayi sannan yace kebaki gane sharrin mata ? Na rantse da girma Allah bayan na fita daga ɗakin nan naje zanyi wanka in dawo kuma kema haka nace miki ina dawowa , toilet ina na samu Jiddah tanayin waya , nazo zan shiga toilet sai.... Tsoki Dikko yayi tare da cewa bama zan faɗa miki ba ni nasan abinda yasa ban dawo ba kiyi magani na , kawai kadaiji kunya an tirka ka.
Kuma ni bazanyi maganin ka ba saidai ayita ta ƙare kawai ka bani tikitin saki nayi gaba abuna , danni bana iya zaman takura haka kuma bazanyi haƙuri da wulaƙancin dangin miji ba , wai ke ni zaki maida ƙaramin yaro , ina faɗa kina faɗa ni zaki maida kamar mace kina sakani a shirmenku nine aka turke? Tou ki buɗe kunnen ki da kyau ki saurareni idan har nasan zan sakeki a rayuwata da bazan ɓatawa kaina lokaci na auroki ba , da bana sanki ko kuma nasan zan auroki dan naci zarafinki dana barki a tare dani kawai na zamar dake karuwata , idan zanyi kawai zanyi ne idan banayi banayi kamar iska haka nake yayin dana taho babu wanda ya isa ya tareni sai nakai , ni bana lallashi kuma ban iya ba saidai idan kinmin yarinta zan zaneki ba abinda ya dameni ki dawo da hankalinki jikinki kuma kisan inda yake miki ciwo ,
Bawai zan zauna nayi ta kare miki faɗa ba dan idan yau ina nan gobe bana nan , ki koyi haɗiye damuwa da ba abun duniya baya dan ba komai kake nema ka samu ba a rayuwa , kuma bawai kullum zakiji daɗi ba abinda kike so bashi zaki samu ba , domin rayuwa juyawa takeyi kuma tana tafe da darussa da dama wata rana uwa zaki zama dole sai kin zama jaruma a gidan aurenki domin ta haka kaɗai zaki fuskanci rayuwa , idonki zaki buɗe sosai ki gano abinda yake tafiya a gidan nan kiyi maganin damuwa tun kafin ta dameki kiyi ƙoƙarin gusar da abin harin rayuwarki tun kafin ya gama farautar abun harinsa ya fara farautar taki rayuwa , duk wanda kika gani a gidan mijinshi yana da tashi matsalar , wata uwar miji , wata dangin miji , wata abiyar zama wata mijin ne gaba ɗaya , keda kina nufin kinzo zaki kwanta idan abin ya dameki ki ɗaga waya ki kira Dikko ya tare miki faɗa ? Ki gyara tunanin dan wallahi ko a gabana Jiddah ta faɗar dake sannu bazance miki ba , bana san zama faɗa da zage² tayar da fitina yana lalata arziƙin namiji kiyi haƙuri duk abinda tayi miki wata rana zai zama labari , baki yunwa baki ƙishirwa ba rashin sutura ko damuwar wurin zama , idan zaki kwantar da hankalinki ki zauna lafiya tou idan kuma kincemin yarinta ina da maganinki ,
Ita kuma Jiddah bata da lissafi tana tare da makashinta bata sani ba , nasan halinki sarai idan har na faɗa miki maganar nan kikayi gori wallahi idan naji saina zaneki da bulalar dukan doki , ni nace Mardiyya ta tafi Jiddah tace baza ta tafi ba , zagina fa tayi wai babu gidan ubanda zataje , tou idan baki sani ba Mardiyya ta turomin text , wai ga Aunty Jiddah can bata san zaman lafiya taje tana matsawa Aunty amarya , Aunty Jiddah bata san zaman lafiya ta cika tsatstsaga , amma zan faɗawa Jiddah dan tasan matsayin Mardiyya a wurinta dan ita tana ma Mardiyya kallon mai santa hmmm zata kaita ta barota domin duk ranar da haƙurina ya mutu zanyi ɓarna a gidan nan....
Ki fita harkar kowa kiyi rayuwarki tun kafin fushina ya shafeki , yanzu a ina zan kwana , cikin hayani yace ban sani ba , goge hawaye na nayi tare da matsawa can daga nesa shikenan kuma bazan ci kazar ba ? Fita yayi daga ɗakin bai sake magana ba , cire kayan jikina nayi na shiga wanka ina tunanin Mardiyya , tabbas a maganarta akwai lauje cikin naɗi , tana da wata manufa nata na daban , miye tsakaninta dani da har zata faɗawa Dikko ? Kuma har take goyon baya na ?
Ba kece damuwarta ba zuciyata ta bani amsa , yayin da maganganun Mardiyya suka fara dawomin a cikin kaina , Ni nan da kika ganni nafi haɗarin jirgin sama kyan gani , ni haɗarina girma ne dashi domin idan nabi ta rayuwar mutum na fita tou fa lallai ya gama rayuwa har abadan duniya , na shigo gidan nan da niyar tarwatsawa ai kin tuna labarin dana baki a mota ko ?
Lallai wani abu zai faru ko kuma yana faruwa , shi kuma Dikko yacemin idona zan buɗe sosai na gano abinda yake tafiya a gidan nan kiyi maganin damuwa tun kafin ta dameki kiyi ƙoƙarin gusar da abin harin rayuwarki tun kafin ya gama da abun harinsa ya fara farautar taki rayuwar , duk wanda kika gani a gidan mijinshi yana da tashi matsalar , ki gyara tunaninki dan wallahi ko a gabana Jiddah ta faɗar dake bazan miki sannu ba , wanka na naci gaba dayi ina tunanin duk amincin dake tsakanin Mardiyya da Jiddah shine take mata zagon ƙasa.......?
Jiddah ki farka idan bacci kikeyi Mardiyya bata sanki dan zata kaiki ta baroki , zata kaini ta baronin kai takai ta baro ne ? Tunda an ƙunsa ka a ɗaki an faɗa maka ƙarya da munafurci ai dole zakace bata so na , um umm ita ta faɗamin kuna faɗa da An mata wayarshi ya miƙa mata cewa duba ki gani , ansa tayi ta gani Dikko ganin ranta ya ɓaci yasa yace kindai gani ko ? Tou ki dakatar da ita domin da zaran na yanke hukunci tou fa ko kaina bana saurara....... Cikin ɓacin rai ta fita daga ɗaki ,
Daren jiya
An mata nasan baki iya ɗaukar Dikko wahala zan baki "yar yarinya ta bara dai inzo muyi bacci kinji ko ? Yana faɗin haka ya fita da tafiyarshi ta sakakkin " ya "ya.
Wayoyinshi ya ɗauka daga palo ya shiga bedroom , a gefen gado ya ajiye ya tunkari ƙofar toilet kai tsaye , magana yaji ƙasa² a dai² lokacin daya dafa handle in da niyar murɗewa ya shiga muryar Jiddah yaji tana cewa Al ' Ameen Mardiyya tace kana kirana shiru , bayan wani lokaci tace taya zan fito bayan gidan yana cike da mutane idan an ganmu tare mutane zasu ɗauka wani abu a tsakaninmu tunda bakwa shiri yanzu , shiru , wane maganin ? Na zuba ai , ɗakinta , a , a idan ya gano da damuwa nan zai birkice kuma kaga damuwa za'a samu , ba komai mu haɗu ta ƙofar baya misalin 3:15 sai in baka , ba damuwa , idan kaje ka haɗani dashi zamuyi magana , yawwa sai anjima , fitowa tayi taga Dikko a tsaye a wayance yace ranki ya daɗe kema kinyi wankan ne ? A , a , ta bashi ansa , murmushi yayi tare da rumgumarta suka koma toilet in tare da tunanin me aka zuba a ina aka zuba ? Kardai itama An mata kamar na Sadiyya zai faru da ita ?, an zuba , kuma an kira ɗakin ta shine bai gane ba , bayan sun fito wanka ne ya kulle ƙofa yace ma Jiddah tare zasu kwana ,
A damuwance yaja ta zuwa saman gado bayan ya gama shirin kwanciya bacci , Sadiyya tazo mishi a zuciya ta tsaya mishi wayayya "yar gayu tanayin abu irin yanayin na An mata itama ma'aboci hawan jikinshi ce kafin suyi aure ,
A asibiti.
Ranta ne ke ta kai kawo tsakanin maƙoshi da zuciyarta , hawaye yana zuba daga idonta tace ka yafemin kuma karka riƙeni a zuciyarka ka manta da abinda nazo maka dashi a daren da yafi ko wane dare farin ciki , amma sai ya zamar maka dare mafi muni a wurinka , na kasa sarrafawa bana iya danne sha'awata ka yafemin don girman Allah ta haɗa hannayenta biyu 🙏🏻tana kallon Dikko ,
Riƙe hannayen nata yayi tare da cewa na yafe miki nifa dama ban wani riƙe ba na faɗa miki na yafe miki² na yafe miki Sadiyya ya ƙarasa maganar yana kwantar da kanshi a gefen allon kafaɗarta yana ci gaba da cewa wai miye matsalar kukan nan ne haba Sadiyyata ki daina saka damuwa a ranki har abadan duniya wallahi na manta da wannan damuwar a raina , kayi min alƙawari ko bayan bana nan bazaka faɗawa kowa ba , nayi alƙawari bare ma kina nan bazaki je ko ina ba muna tare insha Allah , faɗamin meye ne ? Ya ƙarasa maganar yana ɗagowa ya ƙureta da kallo.
Fashewa Sadiyya ta sakeyi da kuka Dikko ya riƙeta da riƙo mai nuni daya martabata yace bana san kuka fa nidai sauri ƙufula gareni faɗamin meye raina ya fara ɓaci zanyi fushi cikin mintuna biyu , cikin ɓacin rai yace me ne ? Murmushi Sadiyya tayi tare da cewa Allah zai baka lafiyar damuwarka idan na ganshi bana iya ganeshi amma idan naji muryarshi a yaranka zan gane maganar shi saboda bana ganinshi waya mukeyi yana bada saƙo ana kawomin kuma da sa hannunshi a lalurarka ya haɗa kai da matan Babanka an gurgunta maka rayuwa akan naira miliyan biyu , yayi amfani dakai ya kai min rayuwata ƙarshe bashi da imani duniyar kawai yake so shi akan kuɗin zai iya koma miye....
Waye ? Dikko ya tambayeta , sunan sa da sanin waye shi ban sani ba , ke me yayi miki ne ? Sama lumfashin Sadiyya ya ƙarayi cike da soyayya ta kalli Dikko sannan taci gaba da cewa.
Na taso cikin soyayya da kulawa ta iyaye , iyayena shahararrin "yan boko ne suna da cikar arziƙi yahudawa ne sosai wanda basu damu da rayuwar yaransu ba , gani na a sake yasa nakeyin rayuwar data tari gabana bawai rayuwar iskanci ba rashin ji lanƙwasa gandar aiki bana aikuwa idan na shige ɗaki sai zanje makaranta nake fitowa , ɗakina babu mai zuwamin daga ni sai rayuwata sai kuma wanda naba izinin shiga.
Rayuwata ta samu matsala ne a makarantar kwana { boarding }, bayan nayi jss3 a makarantar jeka ka dawo wato day aka kaini makarantar kwana , ni bana san boarding saboda wahalarta , amma fur Hajiya tace sai naje , na shiga damuwa Yayuna maza sukace dama da makarantar kwana na dace haka sukayi ta zugawa tun Dadynmu bashi da ra'ayin haka harya amince na tafi boarding.
Ina shan wahalar makaranta yadda ya kamata domin dai ina bacci kamar a gida ina fita sch amakare kulle sai prefect sun zaneni , ni ban saba da wahala ba , kullum haka ake cimin uwa amma kullum saina makara kuma basa gajiya sai sun zaneni.
Yauma gani durƙushe a gabansu S P inmu ce tace karku daketa ke zo nan , tashi nayi naje gabanta na durƙusa wasa tayi da bulala a jikina sannan tace me yasa bakyajin magana ke jakace kullum ayita dukanki bakyajin zafi ne ? Kiyi haƙuri bazan ƙara ba , kullum haka kike faɗa kin raina nasu ko ? A , a , hijabina ta cire ta zaneni saida ta tabbatar ta farfasamin jikina sannan ta wurgomin hijabin tace tashi kije.
Yinin ranar kuka na yini yi , tun daga wannan ranar ta sakamin ido ko hostel bata bari na zauna lafiya nine ibo mata ruwa wankinta tsefe mata kai gyaran ɗakinta komai dai nice nakeyi mata banda lokacin kaina sai nata , wahala yasa na rame nayi baƙiƙƙirin ,
Tsugunne nake a ƙofar ɗakinta ina jiran fitowarta daga kwanar wata ƙawarta da gudu ta safko daga saman gado tana dariya tace ke ɗaukomun ruwan wanka nan , ɗauka nayi nabi bayanta har toilet , ajiye ruwan nayi zan fita ta riƙoni tare da cewa kwancemin towel ina , cikin jin kunya nace yi haƙuri Aunty , bazanyi ba kunce shi kafin ince ke zakimin wanka nan cire kar na sake miki magana , kiyi haƙuri don Allah , idan kika sake bani haƙuri saina ja miki sharri na hanaki zaman lafiya a makarantar nan kuma zan sakawa rayuwarki ido kuma saina miki fyaɗe zan lalata ki ne ba abinda ya dameni , zaro idanuwa nayi nace fyaɗe kuma ? Dama mace tana ma mace fyaɗa ? Dan Allah kiyi haƙuri , idan kika bari na sake magana zanci ubanki , rufe idona nayi tare da kai hannuna saitin da nake tunanin tana nan ashe baya taja , buɗe idona nayi dan ganin ko banyi saiti ba , daga can ciki na ganta ta sake wuri tana cewa ke nake jira ,
Cikin toilet in na shiga dan daga waje nake , shigo ki rufe ƙofa , dan girman Allah kiyi haƙuri, bana san haƙurin nan daga bakinki kullemin ƙofa nace , shiga nayi tare da cewa ai zan kunce basai na rufe ba , murmushi tayi tare da matsowa ta rufe ƙofa ta cire towel in jikinta babu kunyar Allah bare ni , ciremin hijabina tayi ta ɗora a saman inda ta ajiye towel inta tace kina so in daina dukanki ? Shiru nayi idona a rufe , bakyaji ina magana buɗe idonki mu fahimci juna , ƙin buɗewa nayi kuma banyi magana ba ,
Dariya tayi tare da ƙoƙarin fara ciremin rigata , riƙe jikina nayi da karfi ta yadda bazata iya cirewa ba , murya a sanyaye tace Sadiyya buɗe idonki mana , ƙin buɗewa nayi danni gaba ɗaya kunya ya kamani wannan ƙatuwar zata cire kayanta jikinta a gabana , hannuna ta kamo ta ɗora a saman ƙirjinta kamar wacce aka watsa ma ruwan zafi na janye hannuna , cikin rarrashi tace buɗe idonki mana bazan sake dukanki daga yau ba , kuma nayi miki alƙawarin wahala ya ƙare zanyi ta baki kulawa har na bar makarantar nan , zaki dawo ɗakina da zama zakiyi bacci kuma nice zan riƙa miki wanki komai da kike min ni zan miki natsuwa kawai zaki bani yanzu zan nuna miki yadda zakiyimin saki jikinki zan cire miki rigarki ,
Feƙaƙƙiyar "yar maɗigo ce tasan hannunta a harkar lesbian , tunda ta sameni ta tattara sabgar ko wace mace ta zubar saini , ta dawo dani zama ɗakinta bana wahalar komai kullum ina kwance tana nunamin soyayya fiye da yadda miji yake kula da matarshi ta iya tattalin mace kuma tana da karuwanta a met insu amma tunda ta sameni kawai ta zama mijina na zama matarta ko wanka bata bari na nayi da kaina kafin wani lokaci nima na goge a harka dan Yusra mayya ce akan mace ,
Karuwanta ganin ta zubar dasu hankalinta yana kaina yasa suka taso ma rayuwata ido , dan ta ɓata da kowa saini , duk inda zataje dani take tafiya a hostel lokaci guda nima na faso na zama gogaggiyar "yar lesbian ta ƙarshe , Yusra kishi gareta na tashin hankali wannan dalilin yasa take yawo dani lokaci guda suna na ya fara zagawa a makaranta dan Yusra azzalimar shugaba ce , taga dama yarinyar tayi mata laifi kafin ta sanni tace ta sameta ɗakinta da daddare yarinyar ta biya mata buƙatar ta korata , tunda ta sameni sai Allah ya fitar mata da san ko wace irin mace a duniya saini.
Karuwanta kuwa neman sa'a na suke suci ubana , wasa² nima na fara halbawa neman mata , idan mace ta taho haka zan tsareta da ido ina kallon ƙirjinta ƙugunta yanayin zubinta da dirinta abun yana neman ya zamar min kamar wani bakin iyaye dan ko a sch na tuno da yadda muke rayuwa da Yusra idan ban ganta ta rumgemeni ta ɗan jagulani banajin daɗi , maganar karatu kuma na daina bana ganin kowa bana gane kowa sai Yusra , ko kora ta fita kafin ta dawo na fara kuka banda natsuwa sai tana nan , tun abun yana burgeta harna fara tada mata hankali domin yanzu na fita jaraba , wani lokaci sai munyi faɗa zan riƙeta a yunwance dana gaji nace mata nidai tunda kin gaji dani ki sakeni kawai zanje na sake wata tunda kin gaji dani , haƙuri ta bani wai ita bata gajiya dani kawai dai in fahimta bawai kullum akeyin abun ba sai an huta taya ƙarfinta bai gama dawowa ba zata iya bani wata natsuwar , ko abinci ne ka kwakwafe ma ɗaya saiya fitar maka a rai , haka nayi ta roƙon Yusra tou ta fitar min da lokaci na ni ɗaya idan ba haka ba gaskiya zan barta nayi gaba ,
Na rabu da Yusra ne a lokacin da asirinmu ya tonu , abokan harkarta suka sameni a ɗaki da safe ita kuma lokacin ta fita dan dubo yara dake shara , sukayi min duka har suka sumar dani , da Yusra ta dawo ta sameni hankalinta ya tashi bayan na dawo dani daga suma ta tambayeni abinda ya faru na faɗa mata , duk wanda ya dakeni saida Yusra ta buɗe masa kai da sukundireba , wannan ɗanyen aiki da tayi shine yaja mana zuwa wurin shugabar makaranta , anyi case mai girma domin kowa babanta attajiri ne kuma saida aka tattaro iyayenmu tonan asirin dai babu daɗi , haka aka zane Yusra bugun bala'e akayi mata bayan an ƙwace kallabinta aka koremu dukanmu daga makarantar ,
Nidai a gidanmu Yayuna maza sukamin bugun leƙa lahira ki dawo , bayan komai ya kwaranye e aka maidani makarantar jeka ka dawo , haka nayi ta farauto yara ina kawosu ɗakina in basu kuɗi , ganin ban fita harkar mata ba yasa aka cireni daga makaranta kwata² gashi bansan garin da Yusra take ba banda number wayarta na shiga tashin hankali harna rasa ina zan shiga , haka nan na haƙura na koma neman abokan Yayuna bana wani jin daɗinsu nidai Yusra ita kawai nake so ,
Ana cikin wannan badaƙalar ne Allah ya kawoka rayuwata , tunda na ganka natsuwa tazo min na fara mantawa da Yusra saboda tunanin ka nidai ban taɓa ganin namijin daya shigomin rayuwa ya tsareta ba kamar kai , ina sanka kuma naso na zama rayayya domin kai namijin duniya ne ina ma macen data samu gwarzon namiji kamar ka murna , duk kuwa wacce ta sameka a matsayin miji damuwa ya ƙare mata kuma ta zama abin a yaba mata ,
Bayan kazo gidanmu zuwan farko ka tafi aka fara kirana da wata number mai kiran nawa yana da wayau kuma bai shigo rayuwata ba saida ya gama bincike ni kaf , yasan matsalata neman mata da neman maza na , kiran farko yacemin shi wani almajiri ne dana bashi sadaka nace ni bana bada wata sadaka bana ma fita , sai yacemin ka bada ka tuna ai sai matsiyata ka bada ka manta wannan shine cikar arziƙi , ko kin tuna ko kin manta nidai zan taimakeki , a ina ka samu number na ne ? Musulmin aljani daga saudiyya ya turomin yace na taimaki Halimatus Sadiyya zaki tafi gidan miji bayan kin gama lalata mutuncinki a titi na baki taimako saboda halinki na ƙwarai , idan har kikayi aure namiji ya sameki ba a yadda yayi tunani ba da damuwa , zai wulaƙanta ki haka yay ta faɗomin rayuwata kamar yana karatun littafi , banyi tunanin haka zamuje ba , a dai² wannan lokacin ne Momyn Hafsa ta shigo.
Sadiyya taci gaba da cewa shine ya aikomin da wasu layu yace nayi ƙoƙarin sakasu a ƙasan katifa kafin ka kusanceni , idan ka kwanta dani kaji ni a yadda kaji inyi kuka ince ka rufamin asiri , hmmm ya cuceni ashe ba'ayin kuka wanda ya bashi tsibbun yace idan har nayi kuka tou zanyi ta kuka har ranar da za'ayi kukan rashi na , bayan ya tabbatar da hakan shine ya sake kirana ya faɗamin zan mutu kuma a ranar aka cire layina daga wayata kwata² bansan waye ya cire ba , saida ta goge hawaye tace kuma yace zan tafi tafiyar da babu dawowa duk macen da tayi yunƙurin shigar Dikko haka zaiyi ta aikasu ƙiyama babu sassauci , kuma shine yake da sa hannu a damuwarka da taimakon matar uba , shiru Sadiyya tayi daga nan maganar ta ya ƙare , jijjigata Dikko yayi amma shiru domin yana da tarin tambayoyi da zaiyi mata , wannan dalilin ne yasa Hafsa tace yayi kuka kamar rashin zai fita , a cikin ku waye ne ...? Karku kashe An matana , tou ko kune take gani a bacci...... ?
Wannan dalili ya hana Dikko komawa ɗakin Sultana yaji an anbaci magani kuma ance ɗakinta tun a daren bai bacci ba har lokacin da Sultana tayi kuka a dai² lokacin da Jiddah ke dawowa daga wurin Al ' Ameen kuma ya fita ta kicin amma basuyi magana ba kuɗi kawai ta bashi ta dawo , shi yasa bai fito da sauri yaje wurin Sultana ba , ita tana hawowa ta ƙasa shi kuma daga sama yake saurarensu saitin ƙofar baya kamar yadda tace , haka yasa su biyun suka kasance a ƙasa shi a sama Jiddah da Sultana a ƙasa , kuma idonshi biyu Al ' Ameen ya kira wayarta kamar dai² lokacin da tace su haɗu , ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa yarana , to waye a cikin ku ? waye kai me kake so ne da rayuwata ?
Al ' Ameen ne gurfane a gaban bokanshi yace shi Jiddah ba damuwarshi bace ba yanzu Sultana itace matsalarshi boka yayi waje road da ita Mardiyya zataji da Jiddah.
Da kokowa Jiddah ta kama Mardiyya tana dan ubanki ni zaki ma munafurci yau sai kin bar gidan nan tunda ba gidan babanki bane ba , ni zaki kashewa aure Allah ya tona miki asiri kaza² , Mardiyya tace Aunty wai me akayi ne ? Kinje kin turawa Yaya text kince muna faɗa ke baƙar munafuka , cikin kwantar da murya Mardiyya tace Allah sarki Aunty ina tsaye ina tayaki kishi na ƙwaƙwafe a wurin ganin na ƙwatar miki "yan cinki amma bazaki gode ba , iyayena sai cewa suke na dawo gida amma ban tafi ba saboda ina so naga bayan Sultana daga gidan nan ta ƙarasa maganar tana fashewa da kukan makirci , tou a haka zakiyi ? Me yasa zaki tura text wa Yaya ?
Cike da ladabi tace Aunty dan ya yadda dani ya haɗani da kula da rayuwar Sultana ta haka zan shiga jikinta nasan sirrinta kafin ta ankara mai gamawa ta gama , amma kiyi haƙuri bansan abun zai miki babu daɗi ba , jakar bata gane komai ba sai tace tou kiyi haƙuri Mardiyya ai bansan haka kike nufi ba , wuri ta samu ta zauna Mardiyya taci gaba da kaita tana dawowa.
Lokacin dana fito wanka har an canja sabuwar katifa an goge ɗakin tas an sa masa turaren ƙamshi mai daɗi a gefe kuma wasu irin ƙatunan food flarks ne masu kyau a ajiye , wurin naje na buɗe dariya nayi tare da lashe bakina nace kajin ne ko me ne ne ? Koma dai miye zanci shagalina na gama na kwanta yarinya ta sake dawomin ɗakin ko tacemin caca saina kware mata fatar fuska.
Dikko kuwa daga wurin Jiddah wurin su Bello ya nufa , gaba ɗayansu sun zama abun tsoro sun saɓa kamannunsu abun dai sai Allah ya basu lafiya , Dady yaji uwar bari yasa an kawo kuɗi da takardun gonaye filaye da gidajen daya haɗa yayi handama da babakere , saida ya ƙara cin ubansu ya diddira musu yace ko a mafarki An mata ta sake ganin wani a cikinsu wallahi saiya takashi da mota yaja da'ira ya raba kowa da ita mai ƙararren kwana yazo , sunci uwasu har babansu sannan aka sakesu sai sun haɗu a wurin rabon gado , suka wuce shi kuma yayo gida.
Qerau cike take taf da mutane an zubar da gawar Nana a ƙofar gida ta zama abun kallo masu wayoyi sai ɗauka hoto sukeyi , abunda babu kyan gani mijinta kuwa mutuwarta ko jikinshi amma su Amisty sunji ta sosai , Hafsa kuma har yanzu bata dawo ba , yau zaman makoki da jimami a Qerau kuka da baƙin ciki yana wurin dangin gawa.
Saida naci na ƙoshi zuciyata ta fara tashi duk abinda naci dan na kwantar da tanzomar tashin zuciyar baya tsayawa kamar zanyi amai amma baya zuwa , toilet na shiga na wanke bakina na jawo amai amma yaƙi zuwa kam aiko sai kazo wallahi dan duk abinda naci ya tashi zuciyata fitarshi daga jikina shine natsuwa , saida na sheƙa amai hankalina ya kwanta , ina gamawa na gyara wurin na fita , hijabina na saka na fita dan samun abinda zanci dan gaskiya yunwa nakeji na tashin hankali.
Cikin yanayin gajiya na sauko na shigo palon da farin ciki , sai yanzu naji hayani , Aunty Suwaiba na gani zaune a saman keken guragunta a ɓangare ɗaya kuma ana riƙe Dikko yana saiya kasheta , yau kwata² baya riƙuwa duk wanda yaje kusa da Suwaiba dan ɗauketa sai Dikko yace kaima saina kashe ka , sai raba ido takeyi kamar karuwa ta tsare uztaz a ɗaki , ta sharara wani irin fitsari yafi liter goma ta ruwa , kallonta nayi sannan na kalli inda ake riƙe Dikko suna ta ƙoƙarin kaishi ƙasa amma yau sun kasa kwantar dashi , to me ya haɗa Dikko da Suwaiba kuma ? Kai.......... duk saina kashe ku...... dukanku...... yayi wata irin girgirza tare da zazzage su Ashiru ya ɓarar dasu ƙasa , ya nufi wurin Suwaiba idan har yaje mata a yanayin nan zai maida ita kamar damejin milcose , Ashiru ne ya riƙe ƙafar shi daga kwance wani irin ihu Dikko yayi mai tada hankali yace kai zan kashe kaina.............. Zan mutu saina kashe kaina.....................
18/11/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 78
Duk wanda ke gidan nan ihu Dikko ya tada mishi hankali wata irin zabura yakeyi Ashiru ya riƙe ƙafarshi dakel haka yaba sauran dake ƙasa kwance damar tashi suka nufo Dikko suna kamashi , duka ya farayi duka ɗaya tak yakeyi mutum ya tafi baccin wahala , cike da tausayi nabi Dikko da kallo to wai miye matsalar ne ? Cikin wata irin murya yace wai bana ce bana so ana riƙeni ba , saina mutu...
Jan keken da Suwaiba take zaune suka farayi dan fita daga palon , kai............. Wai , wai Allahna wayyo......... Kai....... Idan ta tafi saina kashe kowa a gidan nan duk saina kashe ku...... Riƙe keken nayi nace babu inda zakuje da ita sai Dikko ya bada izinin fitarta wallahi , Mardiyya tace gaskiya ki bari a fita da ita gudun matsala.
Kallon Mardiyya nayi sannan nace nabi matsalar da gudu , babu gidan ubanda zakuje da ita baƙaƙen munafukai duk sai Allah ya tona muku asiri ɗaya bayan ɗaya , Suwaiba hankalinta baya wurina kwata² jikinta ko sai kyarma yake idonta kuwa ya zubar da hawayen firgita bata san adadi ba , a dai² wannan lokacin aka kai Dikko ƙasa dakel bawan Allah har yanzu bai daina kuka ba idonshi yana ratata da hawaye hannunshi ya ɗago yana kallon inda Suwaiba take zaune aka zuba mishi magani ya ɗauke.
Ɗakinshi suka kaishi a ƙasa suka kwantar dashi saman kafet , bayan sun fito Ashiru ne yaja Suwaiba zai fita nace idan har ka bari aka gudu da ita wallahi saina faɗa masa , cikin damuwa ya kalleni ba tare da yayi magana ba ya fita da ita sai Dikko ya dawo daga hutun taƙin lokaci za'a zazzage sauran tashin hankali , yau wata zataci gidansu mudai ba ruwanmu , nidai kicin na wuce nayi abinda ya shafeni , ina tausayin kaina amma gaskiya ina tausayin rayuwar Dikko.
Kafin wani lokaci gidan ya anshi taron "yan uwanshi wanda suke uwa ɗaya uba ɗaya duk wacce tazo ɗakinshi take wucewa fuskokinsu babu daɗi , ina gama abinda nake ɗakina na wuce banbi takan kowa ba.
Da sauri na shiga bedroom dan kukan wayana da nake jiyowa , Yazeed na faɗa a bayyane tare da ansa kiran da sallama , gaisawa mukayi bayan gaisuwa yace bai canja miki layi ba har yanzu ? Eh zan kiraki anjima , ba damuwa na tsinke wayar.
Har yanzu Jiddah bata daina doke²n waya ba har Momy saida ta faɗawa ta tashi hankalinsu dan haka zasu tattara suma su dawo a cikin kwana biyu masu zuwa.
Al ' Ameen bai haɗa Jiddah da boka sunyi waya ba , yadai tattaro bala'enshi ya nufo katsina cikin ƙwarin guiwa ,
Tunda Dikko ya tafi wurin 2 na rana sai gab da magrib ya dawo kuma har yanzu "yan uwanshi suna nan basu tafi ba suna ta tattalinshi , kallo yabi su dashi bayan ya buɗe idonshi da salati , murmushi yayi wanda bai fito a saman fuskarshi ba , ƙanwarshi yasa ta miƙo mishi wayoyin shi , saida wayoyin suka zo hannunshi sannan ya tashi zaune ya jingina da gado ajiye wayoyin yayi a gefenshi ya tsare babbar ɗakinsu da ido.
Sannu tayi mishi , gyara bakinshi yayi cikin damuwa ya ɗan shafa gemunshi tare da dafe kanshi cikin ɓacin rai , gaba ɗayansu kowa sannu yake masa amma har yanzu ɓacin rai ya hanashi yayi magana , miƙewa yayi ya nufi toilet su kuma suka koma palo gaba ɗayansu , wanka yayi tare da ɗauro alwalla ya fito , yana fitowa ya ɗauki wayarshi ya kira Sultana , babu daɗewa ta ɗauka.
Ke ban lafiya kinfi ƙarfin kizo ko ? Magana tayi yace kizo ina kiranki , bayan tayi magana yace babu komai kiyi haƙuri , tou ya kashe wayarshi , Nabeela ya kira ƙanwarshi , ta ansa da na'am jeki kizo da An mata , yana faɗin haka ya saka kayanshi ya fara gabatar da sallar la'asar data wuceshi.
Itace da Jiddah suka ɗaukoni har gidanmu , kallo ɗaya nayi mata na ɗauke kaina , banda suke tsoron Dikko nasan da babu abinda zai hanata ɗuɗɗura ma uwata zagi dan yanayin fuskarta ya nuna tanajin haushi na kamar ta dakeni , shegiya ni kawai akace ta kira amma saida taje ta fara tura Jiddah sannan tazo ta kirani , banyi mata magana ba nabi bayanta har ƙaton palon da nake tunanin nan ne na Dikko.
Sallama nayi amma gaba ɗayansu babu wanda ya ansamin sallamar kowa ranshi a haɗe kamar yace kinci uwarki , ban sake magana ba nayi murmushi tare da murza ƙuguna na wuce inda nake tunanin nan ne hanyar da zata sadani da bedroom in na wuce ina musu tafiya mai nuni naci uwarku nasha ruwan kanwa maganin kwarnafin ciki.
Tsaye na sameshi a gefen gado yana ɗora hula saman kanshi ɗayan hannunshi wayoyinshi ya matsa jikin madubi yana kallon kanshi , da ɗan gudu na isa wurinshi na rumgumeshi , murmushi yayi amma bai taɓani ba yayi magana da fulantaci cewa , { dusudu kairu woni sudu ya nuna da hannunshi yaci gaba da cewa leso an min minwoni Dikko kuma inmin ɓilatama edow misudduma e guda miwaddanma fijo danbe ayidi koh ? Ya tamabayeni , } abinda yace wannan shine ɗakina nunawa yayi da hannunshi yana cewa gadona ni nine Dikko kuma nine zan ɗoraki a sama in lulluɓeki da bargo in miki wasan dambe ai kina so ko ? Rufe fuskata nayi a ƙirjinshi , murmushi yayi tare da ajiye wayoyin a saman madubi yace anshi.
Ɗagowa nayi na kalleshi , kallona yayi da salo mai tsuma zuciya wasa yayi da harshenshi tare da cewa bisimillah yana duƙowa dai² yadda zai kawoshi wurin bakina , riƙe wuyanshi tare buɗe bakina ya saka nashi a ciki , da hannu ɗaya ya riƙemin ƙuguna yana wasa da harshenshi a bakina , kyarma jikina ya farayi tunda uwar data kawoni duniya idan ba Alhaji mai gidan "yanci ba babu wanda ya taɓa shiga bakina sai Dikko , nashi kuma ba irin na Dikko bane ba dan salon na Dikko daban ne , me ye kike kyarma ? Ba tare daya cire bakinshi ba ya tambayeni ? Kaina na girgiza alamar babu , dafo kaina yayi ina kallon idonshi cewa bakya so ne ? Ina so na bashi ansa , cire bakinshi yayi tare da rumguneni saida ya ajiye ajiyar zuciya yace ba kin rainani ba , ni mahaukaci ko ? Zaki ga haukana a saman gado yarinya ,
Hmmm zan ɗoraki gadona badai kina so ki hau ba ? Shiru nayi ba magana , yaci gaba da cewa zaki hau yarinya kuma zakiji abinda kowa yakeji daga gareni , sakina yayi daga jikinshi yace ɗauko wancan makullin ki sanyo hijabi ki sameni waje , inda ya nuna makullin na ɗauka a lokacin harya fita palo yana gaisawa da "yan uwanshi , cikin farin ciki na fita ina mai jin daɗin yadda Dikko ya haɗamin bakinshi da nawa , hakan soyayya ne mai girma , wata munafukar ƙara nayi da murna na shiga ɗakina nima na zama mace naje ɗakin Dikko kuma ya rumgumeni da kanshi kuma ya sumbaci bakina wannan ranace mai daraja a gareni , saida nayi "yar rawa nace godiya nake mutumina.......
Bayan sun gama gaisawa yace ma Jiddah taje , Yayarshi tace ka ƙyaleta mana , miƙewa yayi tare da cewa ku gaida gida na gode sosai , yana faɗin haka ya fice abunshi , shi yana so yayi magana dasu dake su bahohi ne basa gane karatun kurma tou ya bar muku ita ku zauna tare ku dangi na kusa.
Dikko na fita suka fara zagin Sultana wai waccan "yar ɓeranyar yarinyar su take ma yanga ita mai ɗakin miji zataci ubanta , kan Jiddah suka juya haya² suke bata shawarar korar Sultana daga gidan Dikko , wai banda karuwanci kamar Sultana har ta iya yanga dan zata shiga ɗakin miji , Jiddah tace karuwa fa , Yayar Dikko ta ƙara ɗora Jiddah akan ta zage ɗamtse karta kuskusara tabar yarinyar nan ta huta har ta gaji ta bar gidan babu shiri , jakarta dake gefenta ta zage ta fito da wani magani na mata ta bawa Jiddah tace ki gwada wannan daga chaina nazo dashi bana ce miki komai ba labari sai naji ki a waya , haka suka ɗan ci gaba da ba Jiddah haske ga kuma ƙannensu da basu yi aure ba zaune suna ta sakin maganganu su haka suke tou ko Dikko yana nan haka zasuyi firarsu yana jinsu idan anyi abun dariya yaji yana iyawa yayi idan baya iyawa ya girgiza kai , ko kuma yace mata bakwajin magana....
Cike da zumuɗi na fita waje inajin farin ciki a zuciyata , rai a haɗe ya fito fuskar nan babu wasa , saida yazo inda nake tsaye yace muje yayi gaba nabi bayanshi ina rawar kai , kallona yayi tare dayin murmushin mugunta , yace shiga muje ya buɗe gefe ya shiga ni kuma na shiga mazaunin tuƙi naja motar da ƙwarin guiwa na fita daga gidan.
Ajiyar zuciya ya sauke tare da kwantar da kanshi jikin kujera a sakace yace goruba ya ƙarasa maganar yana lumshe idanuwan shi , cikin jin daɗi nace tou mai gida nayi yadda su Ashiru keyi , murmushi yayi tare da buɗe idonshi yayi min kallon gefen ido , murmushi nayi tare da ɗaga mishi gira , dariya yayi a ranshi cewa zaki natsu...
Saida na ibi hanya ya gyara zamanshi yace An mata na rasa abinda yakemin daɗi duniyar nan kamar zan mutu haka nakeji an dawomin da zuciya a bakin maƙoshi ya nuna saitin wuyanshi yana ci gaba da cewa an hanani na zauna lafiya kowa sai jifata yake kamar wani wanda yayi ridda , duk wanda ya raɓoni yasu² ma asiri suke ma junansu kowa so yake ya yafi ɗayan uwanshi a wurina , abun ya tashi ya koma jefe² mutane suna cewa wai duk wanda zai zauna dani sai yayi ɗamara da neman taimako idan ba haka ba yanzu akai mutum ƙiyama a dawo , ashe ma ba iya su suka tsaya ba nima ɗin so suke su kashe ni gaba ɗaya na zama kamar wani sakarai na zama wani ɓawon ayaba kamar bani ba haka nakeji na wallahi da raina ya ɓaci sai in zama wani zararre meke damuwana ? Dafa kanshi yayi yana hawaye yace ni kaina sai yanzu nake ganewa na zama mahaukaci na gaban feji wai wannan wane irin masifa ne ? Na rasa ina zansa rayuwata naji natsuwa , shiru nayi banyi magana ba , dan na lura yana cikin ɓacin rai na barshi ya sauke damuwarshi ko zaiji salama a zuciyarshi , ci gaba yayi da cewa abun bai tsaya a ni ba yana neman ƙetara iyaka , nafa gaji na gaji................. An mata wai meke damuwa na don Allah ,
Horn nayi aka buɗe get na shiga jikina a sanyaye , jiki a sanyaye ya jawoni jikinshi bayan nayi parking ya fashe da kuka yana riƙe kanshi da hannun haggunshi yace { surbajo waikowanna tayan gin Allah , a andi yaw an dunda in an huddi anduki min minajado , idume² gadaimi dun najabe gin Allah , ahn............ade'iti , to mirugga hugondube le ahan daga kuwanaibeyan e direba'en Ashiru en bedillai komoi rakkilayan mihoshsheta midillida emada midalai katsina misomi e masifa } abinda yake cewa An mata wai mike damuna don Allah , kinsan ciwo na tunda kece kika fara gane ni mahaukaci ne dame² nake yi na mahaukata don Allah ke.......... Kinyi shiru , tou zan kori duk wani wanda yake tare dani daga masu aiki direbobi su Ashiru kowa zai tafi ya bani wuri zan ɗaukeki nidai zan bar katsina gaskiya na gaji da masifa....
A tausaye na kalleshi nace kayi haƙuri Dikko ba'a kora maƙiyi kuma a cikinsu baka san waye yakeyi ba karka kora kuma karkayi nisa dasu , nasan wannan saboda Bello da Babana ka san mutane suke koya maka darasin rayuwa , ko maƙiyi ya tafi dawowa akeyi dashi karka bari maƙiyi yayi nisa da rayuwarka barshi kusa dakai kana karatunshi ta haka ne kaɗai zaka iya ganinsa sannan kuma kasan inda ya dosa , taya zan karantashi tunda na zama mahaukaci kuma ai kece kika ce ni mahaukaci ne , kayi haƙuri bazan sake ba insha Allah , meya haɗaka da Suwaiba ?
Da yanayin damuwa Dikko yace fita ki shiga ciki ina dawowa bai bani amsar tambayar da nayi masa ba , fita nayi , daga inda yake zaune ya koma kujerar dana sauka yaja motar kamar walƙiya ya ɓace daga gidan , ajiyar zuciya na sauke tare da juyawa na shiga ciki , ta inda yabi dani daren ɗaurin aure nabi na wuce har na isa ɗakin daya kulleni yasa nasha wani abu a kofi daya kira shi da service , a gefen gado na zauna nayi tagumi Dikko da fulatanci kuma shi naga Mamanshi buzuwa ce dan bata da hausa mai kyau shi yasa yakeyin wata irin magana shima hausar dai duk bata riƙe musu baki ba , Babanshi shine irin yarenmu amma baƙaƙen fulani ne sune na daji kenan amma bana tunani ya iya yare gaskiya tou a ina Dikko ya iyo yarenmu.............???
Zuwan Suwaiba....
Da gudu ya shigo gidanshi a dai² lokacin da aka fito da Suwaiba daga mota aka zaunar da ita saman keken guragunta , ita taji labarin auren Sultana ance mata ta auri wani matashi mai "ya "yan banki ta taho cin arziƙi bata san Dikko take aure ba , tou ita dai zata faɗa abinda ya kawota , bayan yayi parking ya fita da sauri dan hankalinshi baya wurinsu ciki zai shiga da ƙarfinshi saboda yasa abi mishi Al ' Ameen amma wanda yabi Al ' Ameen in yayi haɗari shine aka kira Dikko dan number Dikko ya bayar ,
Yana gaf shiga Suwaiba tace wayyo Allah na shiga3 ku maidani mota da sauri karku bari ya ganni kashe ni zaiyi , Dikko daya shiga da ɗan gudu ya dawo baya da sauri jin muryar ta , bayan idanuwanshi sun tabbatar mishi itace ya juya gaba ɗayanshi yace saina kashe ki.............
Kalmar kisa daya anbata tasa su Ashiru fitowa da gudu , dan baya faɗar kisan da wasa cikin yanayi mai tada hankali dasa tsoro yake furta kalmar , da gudu ya nufi wurinta yana saina kashe ki , wallahi saina kasheki...... Yau bazaki sake guduwarmin ba , kafin yaje wurinta suka riƙeshi kuma shi baya so suna riƙeshi yana fassara riƙon da an maidashi wani sakarai tou da an riƙeshi shine yake ida firgicewa yayi ta fizge² yana zabura yana faɗar saina kashe.....
Ina yake.......... Zaki faɗamin ko saina kashe ki , riƙe suke dashi sosai irin riƙon da sukayi mishi ya bashi damar yin tsalle daga jikinsu ya kai mata wani irin ɗimautaccen halbi tun a wurin tayi fitsari na farko , ƙara riƙeshi sukayi ya birkice , palo aka taho da ita , shi yasa da Sultana tace idan ka bari ta gudu saina faɗa masa , tou shi Ashiru shine ya kawota palon dan ayita ta ƙare....
G R A ya koma yana jiran isowar Al ' Ameen , amma har 12 na dare babu Al ' Ameen ba labarinshi domin Mardiyya ta mishi waya cewa Suwaiba tazo gidan karya dawo , kuma itace ta fita taje ta anso saƙo ta dawo shi kuma ya ɓace cikin gari abunshi da motar Jiddah , Dikko ganin Al ' Ameen bazai dawo ba yasa ya haƙura ya bar gidan kuma gashi zaiyi tafi idan Allah ya kaimu gobe amma idan harya kama Al ' Ameen na lahira saiya fishi jin daɗi , ita kuma Suwaiba a gabanta ya faɗa cewa idan har ta ƙi faɗar sunan mutumin nan injishi a ƙware mata fatar jikinta babu sauƙi , shi kuma yaron shi da yayi haɗari a wurin rijiya mai suminti an dawo dashi katsina yana asibiti , kuma Dikko yaje ya duba shi , saida ya gama abinda zaiyi a cikin gari ya nufi goruba.......
Da ɓacin rai sosai ya dawo goruba , tuni Sultana ta manta da tayi bacci , ajiye ledojin daya shigo dasu yayi sannan ya cire kayan jikinshi daga shi sai short nicker ya matsa ya fara tashin Sultana daga bacci , baccinta yayi nisa dan haka ta sake gyara kwanciya ta rufe idonta , jawota yayi bakin gado , buɗe idona nayi cikin yanayin bacci , Dikko na gani tsaye daga shi sai gajeren wando , da sauri na rufe idona na sake buɗewa , ɗan buɗe bakinshi yayi kaɗan yaja iska da wani irin yanayi yace tashi na dawo yayi maganar cikin raɗa.
Tare da matsawa wurin wayarshi da ake kiranshi , kai amma Dikko baida kunya in banda iskanci basai ya ɗaura zani ba sai kawai yazo ya tsaya haka ƙarere a gabana ko kunya bayaji , tsoki nayi tare da kauda kaina gefe ina kallonshi da wutsiyar idona , kunga bashi da ƙiba ko amma daya hunce yana da ƙirar ƙarfi irin nasu na masu ɗaga abun ƙarfi wanda suke motsa jikinsu , juyowa yayi ya zauna saman dressing mirrow inda ake jera kayan shafa yaci gaba da waya da turanci yana min wani irin kallo.
Ta saman idona na kalleshi shima yaci gaba da kallona da yanayin ido zai raina fata , yanayin kallon da yayi min yasa naji zuciyata ta karaya tsoro ya kamani lokaci guda jikina ya fara kyarma da sauri na sauko daga saman gado a tsorace nazo kusa dashi nace na bari , riƙoni yayi da ɗayan hannushi wanda baya waya dashi ya nunamin irin kofin ranar nan da idonshi , kallonshi nayi yayi min irin murmushin da nayi mishi a mota shima ya ɗagamin gira kamar yadda nayi masa ,
Zanyi magana ya rufemin baki da hannushi yaci gaba da magana a waya da idonshi ya nuna karkimin kuka , cire hannunshi nayi na koma saman gado na kwanta , har na samu damar komawa bacci bai gama wayar ba , bayan ya gama wayar ya kashe wayoyinshi gaba ɗaya ya nufi inda take kwance ya sake tashinta yana cewa ai yau bacci bai ganki ba , bake mara kunya ba , an turke ka mahaukaci munafikin miji sai kuma wata kalma data daɗe tana zugar min zuciya da kika faɗa ma Umar wai ni Dikko nine zaki gauraya dani ?
Tou ki tashi mu gauraya dani dake duk wanda ya raga ma wani shi ba ɗan Babanshi bane ba , badai kin rainani ba , tou na auroki mun zama ɗaya bana so ki tausayin min kuma idan kin ragamin baki haɗu ba ƙaramar yarinya dake tashi ga kazar nan ga komai nan na kawo miki ki anshi daren farko da ƙoshi a wurina ,
Abinda ya wuce bai kamata ana dawowa dashi baya ba , ni nawa ɗabi'ar kenan dawo da anjima yanzu inajin farin ciki yayin dana ke zalintar wanda nafi ƙarfi nakanyi murmushi ko dariya yayin da wani yakeyin kuka ko yake cikin halin tashin hankali , nidai nasan aka share miki fili dani nafi ƙarfinki a saman gadon ma nine oga hannunshi ya kawo yana ƙoƙarin cire min kayan jikina yaci gaba da cewa ki tashi ki gyara gadon nan kamar yadda kika ga nayi a daren aurenmu idan kin gyara kuma kije ki rufe ƙofa zanyi wanka na shirya nahau saman gado na jiraki kizo ɗaukar fansar shekaru biyun da kike jiran zuwansu yau ga abun ɗaukar fansar a gabanki ba tare da shekarun sunzo ba , kinga kin rufe ɗaki babu wanda zaiji kuka na ba bare in saka ran mai kwaceni a hannunki sai kinji tausayina kin kyaleni.
Ai ni na yafe maka , maƙale kafaɗarshi yayi cikin shagwaɓa yace ni ban yafe ba saifa an fitar da rainin nan yau hankalina zan kwanta zanyi tafiya ne shi yasa nake so ko a waya naji muryar gabana zai faɗi , kinga idan bana nan duk inda nake idan kika cemin Dikko kar kayi zan kiyaye saboda karki sake kulle ƙofa , a dai² lokacin daya buɗe ziff in rigata ya cireta daga jikina tare da saukoni daga saman gadon , na ƙwace da gudu na koma ina kuka , ke.......... Bana san wani kukan munafurci ba kinsan zaki gauraya dani ba kece ai kika faɗa da bakinki ba nine na matse bakin kika fada ba , nidai dan Allah bana san haka , cikin ɓacin rai yace sauko , Dikko dan girman Allah kayi haƙuri , na rantse da girman Allah bazanyi haƙuri ba yau sai kin gauraya dani , da nayi niyar ƙyaleki amma ɗazu da kikacemin munafukin miji shi yasa zakici kaza ki bada tukuici idan ba haka ba ni zan gauraya dake , ƙara fashewa nayi da kuka wurgomin makullin ɗakin yayi yace sauka ki kullo ƙofar , cikin kuka na sauka tare da ɗaukar hijabina , ki cireta tun kafin in sa ki sauke duk kayan jikinki , ajiyewa nayi zanja zani na sama yace ke........ Karfa ki bari na ɓaci.
Juyawa nayi na kalleshi ya ɗauke kanshi gefe yana murmushi hannunshi a saman kofin , kulle ƙofar naje nayi na kawo mishi makullin yace kije ki ɓoye abunki inda bana iya ɗaukowa kar inji wahala in gudu , banyi magana ba na ajiye a gefenshi na gyara gadon , bayan na gama yace zo ki sha , cikin ɓacin rai naje na ɗauka na shanye yau ma kamar na ranar ne cikin kuka na riƙe Dikko nace ngode , cikin iskanci yace a , a yau ba'a nan zaki gode ba bari sai kinji yadda nake a wasan danbe.
Juyani yayi na bashi baya ya kwantar da haɓarshi a saman kafaɗata yana sauke wani irin numfashi mai saukar da kasala ganin yadda na riƙe jikina yasa yayi wasa da gashin gemunshi a wuyana lokaci guda tsikar jikina ta mimmiƙe jikina yaci gaba da kyarma , cikin wata irin marainiyar murya yace ke kuma kazar auren naki da kuka zaki ci ? Banyi magana ba dan ina cikin yanayin damuwa ganin Dikko nake kamar bashi ba wallahi , ni duk abun a baƙunce yazo min ina hasko baya data wuce shi yasa nake kallon daren yau kamar a mafarki , duk ya zaneni da bulala mari halbi kuma yau zai kwanta dani.
Shima bai sake magana ba ya jani zuwa toilet , tare mukayi wanka kuma har akayi wanka aka gama idona a rufe yake dan Dikko bashi da kunya ko na misali , saida yayi alwallah ya fita ya barni a toilet in nima nayi na fito,
Nima dai kamar yadda yayi a daren farkon Sadiyya da Jiddah haka yayi a nawa , bayan mun gama ya miƙe tare da zare jallabiyar daya saka ya matsa jikin gadon yana cewa zoki nunamin yadda kike so na kasance , bara na baki satar ansa , mu ƙaddara wannan shine filin danbe an saka kuɗi masu yawa , dani dake mune "yan wasan kuma kowa yana jiran kowa sai aka haɗamu a wasa , da farko kafin ki shiga filin ki nemi albarka gado , sai ki hawo da ƙwarin guiwar ki , yadda ake wasan zaki riƙe kaina goshinki hanci zasuyi dai² da nawa , zakiyi magana da salon yarinta sai ki kalleni kallo ɗaya zakimin saiki rufe idonki ki fara tunano duk irin muguntar da kika iya ta yadda zakiyi nasara a kan abokin wasan naki , karki yadda ki faɗi idan kika bari na buga miki game over ta wannan hanyar zan riƙa horaki duk lokacin da kikayimin laifi , banza nayi banyi masa magana ba , yaci gaba da cewa daga lokacin na tashi daga Dikko zan koma ubangidanki a fagen jarumta , harararshi nayi cikin kuka ban masa magana ba har yanzu.
Murmushi yayi cewa ba damuwa , ƙudi yayi kaɗan mu ƙaddara abun da kowa yana jiran kowa ni dake , nine nayi miki irin raini da kikayi min aka haɗamu a wasan wane irin duka zakimin idan kika kamani , har yanzu banyi magana ba kuka nakeyi cike da soyayya ya kalleni yace karki damu nine ɗan wasan ai , ba damuwa bara in sakoki a filin Allah yaba mai rabo sa'a ya ƙarasa maganar yana dawowa inda ya barni ya ɗaukeni ya ɗorani a saman filin wasa........
20/11/2019 👇🏻
*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 79
Kifa kaina nayi saman katifa bayan ya saukeni a gado saboda kunya a raina kuwa ina jinjina girma da rashin kunyar Dikko , maganganun Yazeed ya fara dawomin sai kuma Inna da tace Dikko tantiri ne tunda kina so kin sama ga fili ga mai doki , wannan shine filin ni nice dokin kenan , zuciyata tace Allah sarki Sultana wallahi Dikko mugu ne.....!
Birkitoni yayi yana kallona yace yau zakiji idan ni Dikkon banza ne , kece zaki ba kanki labari idan niɗin na wofi ne ? Kuma yau zaki sheda niɗin ɗan Babana ne domin da bakinki zaki sa musu albarka da suka haifoni suka baki ni kyauta yau zaki tabbatar da na haifu kuma ni ɗin ɗane hada gyara , ya ƙarasa maganar yanamin kallon da bana so........
Kayi haƙuri , albarkoki wallahi "yar mata , dan Allah 🙏🏻, sai inyi haƙuri in zama munafukin miji ? Umm ummm wallahi sai an fitar da raini kowa yasan matsayinshi , kayi haƙuri fa , wai in ƙyaleki ? Nama zama sakarai kenan , duk haɗashi da Allahn da nayi fur Dikko yace bayajin yaren da nake magana dashi , cikin ɓacin rai nace tou kar Allah ya baka haƙuri kayi duk zalincin dan na baka haƙuri sai kake ganin kamar inajin tsoron ka ne ? Dariya yayi tare da cewa ai nasan wannan bakin tsiwar bazaiyi shiru ba , tsorona kuma daga yanzu zai fara ziyartar zuciyarki ko a waya kikaji muryata sai kinyi ladabi bare kuma ki ganni kamar haka , ya ƙarasa maganar yana tuɓe zanin dake jikina , da sauri na dafe ƙirkijina na matse cinyoyina , yanzu baya ko murmushi yayi min wani irin kallo tare da cewa taso ,
Cikin ɓacin rai na tashi tare da rufe idona na matsa inda yake durƙushe , riƙe fuskata yayi yace buɗe idonki , fashewa nayi da kuka nace Dikko na bari don Allah , rungumeni yayi a jikinshi cikin wahalalliyar murya yace ba abinda kikayi min An mata da farko dai ina baki haƙuri kiyi ƙoƙarin ɗaukata kinji jarumata , ina da masifa jarabata bansan irinta ba , ni ban haɗa mace da komai ba bana neman mata kuma bana sabgarsu ban taɓa zina ba saida ƙaddara ya ratsa min a kanki hankalina bai kwanta ba saida na auroki na samu natsuwa , kiyi haƙuri akanki nasan daɗin mace dake na fara kuma akanki na iya , ni bana kallon iskance² amma duk wani logo na mata a tafin hannuna yake bana da sauƙi , mace kuma ni kaina tausayi take bani idan na riƙeta a gado bana ma mace kawaici haka kuma bana lallaɓata zanyi ƙoƙari na murje shekaruna kafin su sauka dan wata rana inaji ina kallon mace bana iya mata komai , yanzu ko inajin ƙuruciyata ina da lafiya babu inda yakemin ciwo a jikina jini babu inda baya halbawa yaudai ina miki sannu da jiki ɗaukar fansa ko soyayya ? Shiru nayi naci gaba da kuka , bana san kuka bana san yagushi sannan bana san magiya duk idan kikayi zan ida warwarewa gaba ɗayana , kalli agogo , ƙin kalla nayi naci gaba da kuka , yace tou yanzu 1 saura kwata kinga dare ne karkiyi kuka da ƙarfi kindai san kin kulle ƙofa da makulli ya ƙarasa maganar yana latse gefe da gefen kumatuna da yatsunshi na buɗe bakina da sauri saboda zafi.
Dariya yayi tare da yin irin maganata yace Dikko mugu ya ƙarasa maganar yana haɗe bakina da nashi daga durƙushen ya fara hawa jikina yana sakin ƙarfinshi , a hankali nake tafiya ina sauka yana ƙara sakin nauhinshi har na kwanta saman gadon ya kwanta saman jikina sosai yana fitar da wani irin numfashi daga hancinshi mai sa jiki ya zama matacce , bakinshi a nawa yace ke buɗe idonki idan bana kalloki taya zan samu natsuwa ,
Buɗe idona nayi ganin Dikko a wani irin yanayi yasa na firgice , murmushi yayi tare da cewa idan kika sake rufe idon nan ke zaki nemeni wallahi kinji dai na rantse ya ƙarasa maganar yana ɗaure fuska yaci gaba da cewa ki kalleni da kyau kema ki koya , ƙara tura bakinshi yayi sosai a bakina yadda ko maƙoshina bana iya haɗawa nunfashina ya fara sama , ɗagamin gira yayi tare da dafe kaina cikin wani irin salo yaci gaba da sumbatata yana lumshe idanuwa , duk inda yasan idan ya shafo a jikina zai firgitani saida ya bashi haƙƙinshi cikin salo mai wahalar gogewa a zuciya motsin kirki na kasayi nakai matakin da nake buƙatar a fara buga wasan , haka Dikko yaita ranfa dani kamar mage ta kamo ɓeran daya bata wahala , kunsan sai ta gama wasa dashi ta bashi wahala ya suma ya dawo sannan take cinye abunta....
Saida ya gama ɗimautani sosai ya murgina ƙasa na koma samanshi yana sauke wani irin numfashi kamar wanda yasha gudu ya gaji , hannu na ya kamo nasan inda zai kaishi dan haka da sauri na rufeshi , dakel yayi dariya kaɗan yace misali idan nace bazanyi danbe ba a wannan yanayi ya zakiji ne ? Gabana naji ya faɗi a zuciyata nace daka ɗauki alhakina , jijjigani yayi ke bakiji na ne ? Idan kina so nayi sai kince don Allah kayi idan bakayi danbe ba zan mutu a shagwaɓe nake so da irin wannan kallon ya nunamin , idan ba haka ba yanzun nan zan saukeki daga saman gadon nan inyi bacci , yana faɗin haka ya juyamin baya ya lulluɓe da bargo tare da rufe idanuwan shi,
Fashewa nayi da kuka nace Dikko wai miye haka don Allah , ba tare daya juyo ba yace ba kuka zakiyi ba sai kin faɗa zanyi idan ba haka ba yau saida kiyi kwanan haƙuri dan na gaji ya ƙarasa maganar yana yaye bargon ya ajiye a gefe ɗaya yace kallarni fa , da sauri na kauda kaina gefe ɗaya ni kaɗai nasan abinda na gani , to kin huta yayi maganar tare da sake jan bargon zai rufe jikinshi , riƙe bargon nayi kallon raini hankali yayi min yace kina so ne ? A kunyance na ɗaga kaina , to zo ki rumgumeni sai ki faɗamin , kwanciya nayi a saman jikinshi jikina yana kyarma na nace don kayi haƙuri idan bakayi danbe ba zan mutu na faɗa a shagwaɓe kamar yadda ya nunamin da irin kallon daya gwadamin nayi mishi , riƙeni yayi a jikinshi yace fa'idar neman miji mutunci ne , ke kina ƙarawa kanki daraja da martaba a zuciyarshi , babu girman kai ko nuna kafi wani yayin da kake kwance da iyalinka , kuɗi mulki ko saurata duk basa aiki a dai² irin wannan lokacin kar kiyi tunanin nine zan riƙa nemanki daga yau kinajina ko ? Eh , kuma kullum idan ina nan banaso ki ragwantamin ko alwallah nayi ki bada himma ki warwareta naji zan canja wata , ina sanki ne so adadin yadda bazaki iya ganewa ba bana so wata mace ta fiki martaba a zuciyata ta fanni iya karemin haƙƙina a nan ida har tafi ki nan tasha dake , ki riƙe akalata sosai idan kuma kika kasa zan ƙara aure ne kawai tunda na lura duk lusaran mata natattara a gdan , ke ɗinma da nake tunani gara ke tun ban taɓaki ba kin ɓare baki kina mani kuka da wata ƙyarmar banza , tsoki yayi tare da nunamin yadda zanyi masa nidai baƙuwar maza ce iskanci nawa a baki yake , har yanzu jikina bai daina kyarma ba gaba ɗaya kunya ta dameni na ƙagara aje filin yaƙi dan inji irin tashi jarumtar.
Ya gane abunda nake nufi sarai amma dake ɗan iska ne sai ya basar yaci gaba da wani luguidani , kai wallahi Dikko kwallon ɗan iska ne , lokaci² yakanyi murmushi sai kuma ya ɗaure fuska yayi min kallonshi mai tsayawa a rai , can ya gaji yace tunda a haka za'a tsaya sauka ki ɗaukomin kayana , girgiza kaina nayi alamar a , a , tou ai naga karatun yaƙi gaba An mata , a , a ɗagoni yayi daga gefenshi da nake kwance sama ya ɗagani daga kwance har saitin cikinshi , da ƙafa ɗaya ya buɗe ƙafa ɗaya tawa bayan yayi addu'a ya sakoni a saman alƙalaminshi da ƙarfi ya shigar dani , wani irin ihu nayi shi komai nasa sai yayi cuta , jifa yadda ya shigar dani da ƙarfin tsiya babu imani ba zaibi sannu ba kuma yanaji ana dakatar dashi , ke rufemin baki ba kece kikace inyi miki ba muje , cikin kuka nace wai miye haka ? Ni bance miye ba saike dan baki da kunya ci gaba da nushi lokacin ki ya fara....
Ƙasa motsi nayi sai kuka nakeyi dan azaba ji nake kamar zan mutu wallahi , idonshi yana kan agogo ni kuma ina kwance a ƙirjinshi ina kuka , shafa bayana yayi yace karfa ki manta a filin wasa ake yayi maganar yana ƙoƙarin ɗagani na ƙara komawa na kwanta kamar wata doluwa , da hannunshi yasa dan ɗagani na ƙara komawa na kwanta yace munafukin miji fa , iyakar turkewar kenan ? Murmushi yayi tare da cewa lokacin ka ya fara Dikko.
Birkicewa yayi tare da jawo ƙafafuwana ya ɗora saman kafaɗarshi yayi min runfa da ƙirjinshi hannunwan shi ya ajiye gefe da gefe na sannan ya kalleni yace , nasan zakiyi ji mamaki ina magana da yarenki ko ? Tou ni bana sauƙaƙawa gaba duk ƙarantar ta haka kuma bana san raini duk wanda ya rainani saina sa ya raina kansa ,
Tun ranar da kika faɗamin zaki ɗauki fansa shekaru biyu hankalina bai kwanta ba saida na tabbatar duk wani logo na fulani na kamo tasharshi , ba'a fini iya mugunta ba amma ina da yafiya , nakan manta da ɓacin rai na fuskanci rayuwar gaba kuma haka na faɗa miki a ke a dole shekara biyu zaki ɗauki fansa ga abin ɗaukar fansar kin gagara ramawa , kinyi maganganu akaina marasa daɗi amma kamar yadda kikace abinda ya wuce bashi da kyau dawo dashi baya na barshi amma sai nayi hukunci hada marin da kikayi min wallahi.
Daga haka yaci gaba dakai nushi kaɗan² , har yanzu ban dainajin azabar saukar dani da yayi a alƙalamin da ƙeta ba , cikin kuka nace Dikko da zafi fa , Ey amma ai nushin yana da daɗi ki ɓoye hawayenki kila zasuyi miki amfani anjima yanzu sharar bage aka fara gyara kwanciya ki anshi hukunci , a wannan rana na raina kaina nayi ihu nayi kuka har muryata ta shaƙe nayi yagi Allah ya isa ban yafe ba na faɗa bansan adadi ba , a zuciyata kuwa ina tunani Alhaji mai gidan "yan ci baimin irin wannan muguntar ba , Dikko yace duk Allah ya isa ɗaya saina ƙara mata muntuna 20 akan duk awa ɗayar da zanyi , kuma idan kika sake yagushina saina rama baki fini haƙora ba bara ki sake cizo na kiga yadda zanyi dake saboda ba'a cizo ba'a yagushi a danbe ki bada himma kiyi nasara lokaci yana tafiya miki idan nayi nasara akan ki ƙaryarki ta ƙare....
Dole na haƙura na ƙyaleshi , a hankali yake tafiya yana ƙara murza totir lokaci yana tafiya yana ƙara yawan gudunshi a haka har ya warware gaba ɗayanshi , ya manta da ƙarantar da yake tausayi ya neman hanyar da zai sama ma kanshi natsuwa ya ƙanƙameni , wani irin kukan kissa yakeyi Dikko mai daɗin sauti da ratsa zuciya mai wahalar mantuwa a rayuwa , a hankali yake fitar da sautin kukan cikin sagwaɓa Dikko baijin magana wallahi jarumin namiji ne a fagen daga da iya jan linzamin mace a filin wasan danbe , lumshe idona nayi cikin wahala a raina nace tabbas babu mai irin jarumtarshi a mazan bariki Jiddah , ɗaya kawai na ɗana nasu wato Alhaji bansan yadda suke ba amma sai sun haɗa da "yan dabaru , duk namijin da baya iya sauke haƙƙin iyalinshi ya zama lusarin miji a wurin mace kuma ta samu kafar rainashi idan ba'ayi dan mai gona ba anyi da mai gayya , idan bata raga maka ta wani wurin ba tabbas zata martabaka da ƙoƙarin kare martabarta da kayi a fannin kare haƙƙin aure , ɓanɓare Dikko na farayi yi dan na kusa ɗaukewa , da sauri ya ƙara riƙeni a shagwaɓe yace wayyo ya faɗa tare da ƙarayi min kyakkyawan riƙo wai , wai Allahna a , a An matana ƙyaleni , ki ƙyaleni.......
Ya zalinceni iya zalinci ya cuceni ya nuna fin karfi yadda yayi min alƙawarin saiya sumar dani dan na kiyayeshi na gane shi ba sa'ar wasa na bane ya turani suma naje na dawo kuma tabbas tsoranshi ya shiga zuciyata kamar yadda yayi alƙawai , nayi kuka na bashi haƙuri amma saida ya tabbatar yayimin lullusar kece raini ya barni bayan yasa nayi masa godiya da addu'a Allah ya ƙara mishi lafiya a fagen filin wasa yayi ta nasara a wasan danbe ,
Yayi amfani da ƙarfinshi ya bani wahala ya zagaya a wasan farko kuma an faɗar dani , na biyu ma shine yayi nasara a na 3 akayimin game over 3/0 wasa ya ƙare kuma Dikko ya rainani daga yau kuma har zuwa wannan lokacin ban daina kuka ba dan ƙetar da yayi min , bai sake bi takaina ba yaci gaba sabgar gabanshi ko kallo na ba sakeyi ba , bayan ya tsarkake jikinshi ya saka jallabiyarshi ya ɗauki wayoyinshi da makullin mota ya tun kari hanyar fita ,
Ina zakaje ? Na tambayeshi , bai kalleni ba ya juya yace Al ' Ameen nake nema nasan yanzu ya gama iskancin guje²nshi ya dawo , nifa tsoro nakeji gaskiya , cikin masifa yace kije kiyi ta jin tsoron ke baki da kunya ma ni zaki faɗa ma tsoro ya ƙarasa maganar yana min wata irin harara gabana naji ya faɗi , da sauri na komar da kaina na kwanta , tsoki yayi tare da buɗe ɗakiya fice cikin ɓacin rai. Saida na tabbatar ya fita na sauka gado a gajiye ina gunguni cewa ɗan masifa tsakar daren ma ba'a hutawa da fitina Allah ya baka lafiya ,
Ina shiga toilet in na tunkari inda naga ya tara ruwa tare da tara hannuna ruwan zafi ne tsoki nayi tare da tsugunawa dan toilet in bashi da kwamin wanka kuma ba cikin ainahin gidanshi bane inda ya siya ne wurin ne kaɗai ba'a rusa ba gidan maƙota kenan.
Cikin ƙanƙanin lokaci ya isa G R A ko tsoron dare bayayi tunda ya tafi ranshi yake ɓace harya isa da wani irin tuƙuƙin fushin ci ma Al ' Ameen mutunci ya isa har yanzu bashi gidan motar daya fita da ita itama bai dawo da ita ba , ɗakin Jiddah ya nufa gaba ɗayansu daga ita har Mardiyya suna bacci saida ya gama kallesu tsaf sannan ya kashe hasken fitilar yaja ƙofa ya nufi ɗakin Sultana...
Sauke katifar gadon yayi tare da buɗe plow bed in duk abinda yake san gani babu , tsoki yayi tare da maida katifar ya nufi wadrof duk saida ya zubar da kayan ciki akwatinan lefenta ma haka ya zazzagesu ƙasa yaita janye²n kaya babu wani damuwa , palo ya koma nan ma babu wani sheda duk kayan daya zubar bai maida ba , Allah ya sawaƙe wahala ya faɗa tare da fita daga ɗakin.
Koda na fito daga toilet a gaban gado na durƙusa rabin jikina a saman gado naci gaba da baccin wahala , bacci yana ɗaukata na ganshi a gabana yana saina kwakwale idonki , a tsora ce nace wai mene ne damuwar ? Ka fita hanyata meye nasaba na dakai kullum ka kwakwale , me Nana tayi maka ka kwakwale idonta ? Me Aunty Mamy tayi maka ka kwakwale ? Kuma me yasa daka cire ake mutuwa ? Ansa zan baki ko kina so na fita rayuwarki ? Eh ka fita hanyata , tou ina wayar da kikayi min record , Dikko ya cire m card , idan har Dikko ya baki record in nan nayi miki alƙawari zan nuna miki inda aka binne asirin da akayi mishi , wani mutum ne yazo ya kamashi da kokowa yace idan ka faɗa saina kashe ka , kai ku riƙota karku bari ta gudu , wayyo na kwarara ihu tare da miƙewa a firgice a dai² lokacin da Dikko ya shigo , dakamin tsawa yayi wai wannan koken banzar ni ya fara isata , wuce kije ki kwanta , zanyi magana yace ki wuce nace bana san iskanci da Allah , fashewa nayi da kuka , yace mizanate , wai zai zaneni , ƙyaleshi nayi naje na kwanta ban daɗe da kwanciya ba na tafi bacci dan duk jikina wani irin ciwo yakemin.
Dikko kuwa gefen gado ya zauna yana latse² a waya , bayan wani lokaci kuma ya juya ya tsare An mata da kallo tana sauke ajiyar zuciya lokaci² ta kuka , murmushi yayi kaɗan yace An mata rigima ubangiji ya zaunar damu lafiya ya kare mana fitina Allah ya ƙara ninka miki soyayya ta fiye da wadda nake miki kunji irin san kan nashi fa.
Yau ko bacci ɗaya Dikko baiyi ba yana zaune duk abun duniya ya dameshe har lokacin sallah asuba yayi , da zai fita masallaci ya tashi Sultana ya wuce , ina gama sallah na kwanta a wurin na ci gaba da bacci ,
6:33am ya dawo kuma a lokacin muka bar goruba , a mota nake tambayarshi memory yace baisan ina yake ba , zan sake magana yace nayi masa shiru yanajin ɓacin rai , shiru nayi ban sake magana ba , shi kuma yaci gaba da lissafin tafiyarshi a zuciyarshi.
Zasuyi hannun riga da Momy zai fita katsina a daren yau su kuma zasu bayyana a gobe idan Allah ya kaimu har suka isa gida da abinda Dikko yake saƙawa kuma yake warwarewa , har ɗaki Dikko ya rakani kuma har yanzu Jiddah basu ma san gari ya waye ba amma gaba ɗaya duk wani ma'aikaci dake gidan maza da mata kowa ya tashi ya kama hidimar gabanshi , gidan cike kamar ana wata hidima saboda babu wanda ba'a gidan yake zama ba idan dai har a gidan yake aiki , ƙaton gida ne sosai saboda yafi gidan goruba girma bama a haɗawa kowa da ɗakinshi palo bedroom da toilet akwai masu dafa abinci a saman icce can bayan gidan a manya tukwane a cidasu kuma a basu albashi , ko ɗan uwa gareka ka kawoshi shidai Dikko babu abinda ya dameshi amma saboda fitinar Jiddah wai nice zan tashi nayi musu girki , suna fa cin daɗi domin abinci da nama baka isa ka raina ba gaskiya Dikko yana da cikar arziƙi ubangiji ya ƙara rufa asiri.
A harmitse na samu ɗakina kallo ɗaya nayi masa na nufi gado , Dikko yace a haka zaki kwanta kina ganin ɗaki a haukace , ban masa magana ba na haye gado saida na kwanta nace wanda ya ɓata zaizo ya gyara , da fushi ya nufoni na sauka gado da sauri kafin iso na nufi inda kayan suke na fara tattarawa ina kuka , dama kin bari na sameki a kwance.........
Yana faɗin haka ya fita yana faɗa , ɗakinshi ya nufa danyin wanka , saida na gyara ɗakin nan tas na shareshi na goge sannan na kwanta naci gaba da bacci.
Tunda ya fita sai bayan la'asar ya dawo tare da Nabeela , nima tuni nasha baccina na tashi nayi wanka na kame mutuncina cikin riga da zani na atamfa , yau Jiddah ita kuma fitina take ji tunda na fita take sunkuyawa iyayena zagi amma ban tanka mata ba sai Dikko baya nan zanci uwarta kafin ya dawo , tou ashe bani ɗaya ba har Dikko bata raga mishi kina jiyo hayaniyarta tana masa rashin kunya , ran Nabeela idan yayi dubu ya ɓaci kamar Yaya DK Jiddah kema rashin kunya wallahi ta sire mata kamar fitar tusar safe.
A palon ƙasa yabar Nabeela yazo ɗakina cikin sauri² yace zo ki gani , tashi nayi naje wurinshi nima na ɗaure fuska kamar yadda naga yayi , murmushi yayi ba tare daya kalleni ba hankalinshi a kan takaddar yace yau an raba an fitar da haƙƙin kowa , an bawa shi mijin ƙawar Momy na ɗakinsu domin alƙalin haka yayi rabo ɗaki² , na ɗakin su Baba aka bada shi wa wannan mutumin da yayi ƙararki , nasa an rabasu aka fitar dana gidanku kuma za'a ciccira su a fitar da kowa kema An mata da Allah ki yafe musu kuɗin nan yayi maganar yana kallona da damuwa kalli kiga ya nuna takaddar yana gwadamin yadda rabon gadon ya kasance ,
An fitar dana Kakarsu Hafsa ita da tayi takaba aka sake kasawa aka fitar dana ɗakinsu Dady saina ɗakin su Baba , an raba aka fitar wa da Baba ƙarami nashi gidanku yara 61 da mata 3 ni tafiya zanyi idan sun gama kasanfinsu sa ajiye miki naki ya ƙarasa maganar yana jawoni jikinshi , riƙe kafaɗarshi nayi da hannun dama na tare da kwantar da kaina a jikinshi.
Ni zan tafi ga Nabeela nan na taho miki da ita ta tayaki zama kema ki samu mai ebe miki kewa , bana san faɗa karki kuskura ki biyewa Jiddah kuyi faɗa kinji ko ? Nace tou , zan baki makullin mota kuma bana san yawo mara amfani na yaddar miki da izinina ki fita duk lokacin da buƙatar fitar yazo , shiru nayi banyi magana ba , ɗagoni yayi daga jikinshi yace a wl'a a yetti , tou baki ce kin gode ba , cike da damuwa nace miyyetti.
Shima da yanayin damuwa yace , midillidai e maraicimada , tomi tunitake emada minanai beldun wala miwonda e mada miwadai katunanimada kullum , jemmare keya idewdi mahimmanci sosai to a han idan tunitida jemmare keyah e dume ittata kewamada ? Abinda yace wai zan tafi da maraicinki , idan na tunaki zanji babu daɗi bama tare zanyi ta tunaninki kullum , daren jiya yana da muhimmanci sosai a wurina idan kika tuna daren jiya da me zaki ibe kewa ? Fashe wa nayi da kuka tare da sake komawa jikinshi na kwanta ina hawaye , dariya yayi sosai tare da saukeni daga jikinshi yace inzo muje ɗakinshi yayi gaba nabi bayanshi ina kuka.
Jiddah kuwa sai babbaka uwar ashariya takeyi bansan abinda akayi mata ba , Nabeela kuwa ɗakina tasa aka sauke mata kayanta bayan Dikko ya woner ta cewa idan ta kuskura An mata tace tayi mata wani abu ko taji wahalar zama da ita ko tayi baƙin ciki uwa uba tayi kuka zai kasheta ne ba ruwanshi , gabanta sai faɗuwa yakeyi ya wannan zaman zai kaya ne......... ?
Muna shiga ɗakin ya bani makulli wai in kulle ƙofa , zan ruga ya riƙoni cike da damuwa yace haba An mata , na Allah kiyaye fa zaki bani yi haƙuri don Allah yanayin maganar cikin nuna haɗama da zaƙuwa , zanyi magana yace yi haƙuri haba An matana Dikkonki fa cikin lallashi yakeyin maganar idonshi ya canja launi zuwa kalar jaraba , nidai don Allah ka ƙyaleni , cikin ɓacin rai yace bana san yawan magana zaki yi da arziƙi ko in danneki in kwata ta ƙarfi da yaji ne , a , a me yakai ta ƙarfi , to anshi , makullin ya bani yace rufe ƙofa cikin kuka naje na kulle ƙofar na dawo , bargo ya shimfaɗa a ƙasa yace jirani ina zuwa , wurin firij ya matsa ya fiddo wani ɗan madaidaicin galan ya zubo wani abu a kofi ya taho gabana ya durƙusa tare da zaunar dani yace tou sha , yana kai min kofin a bakina , wannan miye ? Da Allah sha malama kina ɓatamin lokaci , nidai kullum saina sha fa , Eyyy yauɗin ma zakisha idan ba haka ba zan ɗura mikishi ne ta hanci bata baki ba , one , two , three , tsaya zan sha , tou sha , ansar kofin nayi daga hannunshi nakai bakina miƙewa yayi ya fara kwance belt inshi.......
Shegiya butulu tsinanniya butulal cin amana kamar karuwar data zauna a garin legos aka zazzabga mata bulala , dariya Suwaiba tayi tare da cewa ko zaku kasheni bazan faɗa ba , ni har kun nunamin iskanci nida naci tsaye a gefen hanya nake miƙewa a bani tukuici ba'a katsina ba saida na tsalleke jahohi da dama naje iskanci daga ƙarshe na tare a ƙarƙashin gada can legos kaga kuwa rashin kunya ta tafi duk yadda kuke tunani , Ashiru yace ku barta mai gida zanje in ɗauko yanzu yana faɗin haka ya juya Suwaiba tace Ashiru kar muyi haka dakai zan faɗa ko saurarenta baiyi ba ya fice , Suwaiba ta darkaka wani irin ihu mai tada hankali tasan Dikko hankali wala.....
Daƙel na dawo ɗakina da bargon da Dikko ya kwanta dani a samanshi , ya bani makullin ɗakin goruba wai idan na samu lokaci inje in gyara ɗakin sai makullin mota da kuɗi , Nabeela na gani zaune a palona sallama nayi na wuce ciki ina kuka , tasowa tayi ta biyoni matar Yaya me akayi miki ne , banyi mata magana ba na hau saman gado na kwanta tare da tura fuskata a bargon naci gaba da kuka , gefena ta zauna wai inyi haƙuri idan naji babu daɗi kuma me akayi min nake kuka , maganar Dikko naji a palona dashi da Jiddah yana cewa bari in anso in baki ni An mata bazata biye miki ba , kuma idan tayi miki wani abu wanda bai miki daɗi ba ki faɗamin zan rama miki , ni nafi ƙarfin in faɗawa miji ya kare min faɗa saidai inci uwar yarinya , tou ni kuma kika taɓata zakiji da ɗaci.
A tare suka shigo yace An mata ina makullin motar dana baki , ba tare da nayi magana ba ko na ɗago na miƙa mishi , ansa yayi yace gashi na kashe fitina , ke An mata anshi na mota ta , wallahi bazata hau motarka ba saida ta anshi ta hannun Al ' Ameen dole , Dikko yace na rantse da girma Allah baza ta hau motar nan ba yadda tayi gwanjonta wa ke ta gama da ita har abadan duniya bata maimaici da mota tunda tana da ni , ai itace take hawan ta tun farko ka mayar mata kayarta , bazan mayar ba kuma yanzu bata hawanta , tou saidai ta fasa fita sai ta zauna harsai ka dawo , sai ta fasa uzirinta saboda bana nan ? Sai ta fita inda ranta yake so idan ke kike aurenta sai in gani , ba abinda ya dameni wata mota ce dai bata isa ta hau gidan nan ba saita hannun Al ' Ameen danma ta samu an bata motar a gidan ubanta ai a nepep take zuwa duk inda take zuwa , gidan mijinta ne yadda na saka sadaki na auroki haka na biya na aurota , nan ba gidan Babanta bane gidan Dikko ne kuma Dikko bazai bar matarshi tayi yawo a nepep ba wasu ma sunyi rawa bare ɗan makaɗi hannuna ya riƙe tare da cewa kiyi amfani da wannan motar kafin in dawo idan kuma kika bari ta anshi makullin ta baki motar Al ' Ameen zasu kaiki su baroki.
Yana faɗin haka ya fice , Nabeela da Jiddah suka bi bayanshi dan rakiya nidai banje ba , Jiddah bansan abinda ya firgita ta ba , saida suka dawo daga rakiya Nabeela ta wuto ɗakina , Jiddah kuma sai ɓaɓɓarka zagi takeyi saita kamu sunan Dikko ta luƙaƙa mishi zagi , wai gidan Dikko shine auren ƙaddara tana da saurayinta wanda yafi Dikko komai akaje aka cuci rayuwarta ana "yar murya da yanzu tana can ƙasar waje tana rayuwarta mai daɗi , sai ta kashe auren Dikko marar zuciya nace ya sakeni ɗan jaraba mayen mata yaƙi ya sakeni ,
Nabeela ta fita da gudu tace ke jaka har kin isa ki kira auren Yaya ƙaddara sakarar banza jaka dake , wace ce ke ? Ƙazamar banza bakisan halinshi ba ne amma idan kika sake zaginshi uwarki zanci ɗanyaɗanyarta bazan gasa ba , masifa ta cakuɗe tsakanin Nabeela da Jiddah sukayi ta masanyar kalamai nidai ban fita ba saboda sunfi kusa tunda da Maman Dikko da Maman Jiddah uwarsu ɗaya ubansu ɗaya ni ina ruwana ?
Duk wannan faɗan Mardiyya saida tayi musu video ta turawa Dikko , Nabeela ta dawo ɗaki tana ta zage² ni lokacin ma har na fito wanka ko inda take ban kalla ba dan abinda na lura yarinyar bata da kunya ko na misali , kayana na saka na fita dan sama ma cikina abinda zanci.
Bayan sati 3
Gaba ɗaya yanzu Sultana ta kwanta ta samu wata irin natsuwa ta musamman ta rage rawar kai domin an kammala saukar da akayi mata dan warware sihirin da Bello yayi akanta , yanzu zuciyarta ta natsuwa ta daina bata umarni akan muguwar ɗabi'a sai shakkun Dikko da takeji ko waya ya kirata a ɗaɗɗare takeyin waya dashi bata sakin jiki kamar can baya duk bayajin daɗin hakan.
Momy ta dawo , a ranar data dawo ranar tazo gidanmu ta yalyaɗa ruwan rashin mutunci ta zageni tai mani gori ta mareni tai mani ƙwanya kuma tace tana nan tana jiran dawowar Dikko ko zai mutu saiya sakeni ai dan yasan zata dawo shi yasa yabar ƙasar , tafa zuba ruwan rashin mutunci na wuce misali haka Jiddah kuma tasa an ƙwace makullin motar Dikko an bani na wanda Al ' Ameen ke hawa , Umar kuma ya buga ya faɗa mishi ya kirani yace kar in sake in hau motar nan idan zanje wani wuri in faɗa masa zai turo akaini ,
A ɓangaren Inna har yanzu bata nemeni ba , kuma ni bansan number da take amfani dashi ba a can india , ƙawayenta dai sukan zagayoni lokaci² kuma suma wai basu da number Inna ,
Zama na da Nabeela banajin wata damuwa zata dai shata surutunta iya iyawarta banda lokacinta danni bana fira da yarinya gudun raini ta raina mutane "yar iska ce ta gaban jarida , bata da kunya yarinyar kwata² danni ko wuri ɗaya bana kwanciya da ita dan nasan tana zaune dani kuma tana karatun rayuwata ne shi yasa nake kiyayewa dan nasan banda haƙuri.
Yazeed ya kirani kuma yace min yana san gani na wai zamuyi magana mai muhimmanci duk abinda nake nayi ƙoƙari mu haɗu gobe , nace masa zan duba,
A ɓangaren Bello yana so yayi wani abu amma bashi da wadatacciyar lafiya dan tunda suka fita daga hannun Dikko gaba ɗayansu basajin daɗi ta lafiyarsu sukeyi a halin yanzu bana gabansu !
Hmmmm a daren yau ƙawayen Jiddah suka bayyana a gidan..... Dan sunso zuwa tuni Jiddah ta dakatar dasu wai sai Dikko baya nan , to sunji ya tafi sun zo kuma kowa ta ɗuro iskanci cike da kanta sun taho..........
0 comments:
Post a Comment