Duk ya ruɗe ya rasa yanda zaiyi da ita, sai girgiza jikinta yake yana cewa "tashi Saude, na daina fa" ita kam kukanma ya daina zuwa,
Sai can ya tuna da ruwan zafi fa ake shiga a wanke jiki, da sauri ya tafi ya duba babu ko wanda babu sanyi sosai, haka ya ɗaura ruwa cikin darennan, ya haɗa sannan ya ɗauketa ya shiga kewayen da ita, bayan ya gasa mata ko ina, har wankan soso ya mata ya wanketa tass, sannan ya taimaka mata tayi wankan tsarki, ya fito da ita ya kwantar da ita saman katifa, tana kwanciya sai barci,
Washe gari cikin nishaɗi ya farka, sai yau ma yake jinshi kamar Angon, sai wani annuri yake fita a fuskarshi, bai tasheta daga barcin da take ba, shiya haɗa mata break fast, da duk abunda zata buk'ata ya ajiye mata, yakai hannu ya shafi fuskarta, zazzaɓi harya sauko mata, gashi baison ya tasheta, ya ajje mata magani inda zata gani sanda zai fita, har yakai k'ofa yana waiwayenta, taa k'ara yi mishi kyau sosae, don dolene kawai zaije wurin aikinnan, anma idan sonshi ne ya zauna kawai yayi jiyyarta.
Tana jin yaa fita ta buɗa idonta, daman taa daɗe da farkawa kunyarshi ce ta hanata buɗa ido, ga yunwa tanaji anma bazata iya cin abinci ba, maganin daya aje mata ta gani, ta ɗauka tasha, sannan tayi kwanciyarta.
Duk da babu inda ke mata daɗi a jikinta, haka ta tashi da taga rana tayi, ta ɗaura mishi girki, tun kafin ta gama ta fara jin k'arfin jikinta, sai dai zafinda bata daina ji ba, tana gamawa sai gashi, yau da wuri yazo, tana gyara inda tayi girki, baima kula da ita ba saida ta amsa sallamarshi.
Ya juya yana kallonta abun mamakin Saude bai k'arewa, sai kallonta yake yace "Saude maiya fito dake kuma?" da sauri ta bar abunda take, a inda take ta durk'usa tana kallon k'asa,
"Sannu da dawowa"
"Yauwah ya gida" a can ciki ta amsa, duk ta takura da kallon da yake mata,
"Bana hana yawan aikinnan ba Saude? Keda bakijin daɗi ai kamata yayi ki kwanta ki huta"
"Ai naji sauk'i"
"Ban yarda ba, ki ajje aikinnan muje ki huta" tace "tohh" ta mik'e tana sauri ta k'arasa aikin, zuwa yayi ya kamo hannunta ta mik'e tsaya, yana rik'e da ita har cikin ɗakin, sai k'asa take dakai, kamar k'asa ta buɗe ta shige kawai, wani irin kunyarshi takeji,
Saida ya Zaunar da ita, sannan ya buɗe laidar daya shigo da ita, fresh milk ne da naman balango mai zafi sai k'amshi yake,
"Ki zauna kici, naga bakiyi break fast ba, zan tashi in watsa ruwa kinji"
"tohh abincin fa?"
"a ina aka samu?"
"Girkawa nayi,"
Rasa me mezaice mata yayi, "yanzu dai a k'oshe nake, k'ila anjima" ta gyaɗa kai, yana fita ta fara cin namanta, saida taci sosae har taji ba wuri, sannan ta kora da fresh milk ɗinta.
Ba laifi Saude ta samu kulawa daga wurin Yasseer a ranar, duk da bai wani san yanda zai tarairayeta ba, yana zaune gida, anma sai yawan yi mishi waya ake, duk dai maganar tafiyarshi ce,
Tun cikin dare yake haɗa kayanshi, ita dai har tayi barci bai kwanta ba, duk ta shiga damuwa, batason ya tafi ya barta, ita da tanada damar hanashi ma bazata bari yayi tafiyar ba, sai dai kawai k'ok'arin dannewa da take,
Da asuba bayan tayi Sallah ta kwanta, tana jiyoshi ya dawo daga masallaci toilet ya shiga yayo wanka sannan ya shigo ɗakin, tana jinshi yana shiri, saida ya gama ya fara tashinta, ta buɗe ido kamar mai barci,
"Yi hak'uri naa tasheki, yanzu zan wucene"
Batasan sanda tace "tun yanzu?"
Tsadajjen murmushinshi ya sakar mata, "Tohh ai garinmu ne da nisa, shiyasa zan tafi yanzu k'ila in isa kafin magrib"
"Tohh Allah ya yarda"
"Ameen"
Ta mik'e zata ɗaukar mishi jakar kayanshi ta rakashi, ya kama mata suka fito har soro, har lokacin gari da sauran duhunshi,
Suna tsaye sai wasa take da yatsun hannunta, ya sunkuyo dai dai fuskarta, ta lumshe ido, "Yadai?"
Idanunta a rufe tace "ni bansan mezan baka bane, idan ka tafi ka ringa tunawa dani"
"Saude kenan, tafiyar kwana biyun? Ai abinda kika bani ma ya isa har k'arshen rayuwatah bazan manta dake ba" da sauri ta juya jikin bangon tana ɓoye fuskarta,
"tohm baka faɗamun sunan garinku ba"
Cikin wasa yace, "tsoro kikeji kar in gudu in barki?"
"A'ah inason sani kawai" ta faɗa tana dariya,
Har yanzu cikin zolaya yake mata magana "A k'asar katsina nake"
"Uhmn nasan ai ba jaharmu ɗaya ba"
"Hakane fa, garinmu yana can hanyar wani gari, idan anje kusa da wani gari, anma dai muna kusa da babban birnin tarayya, garinmu babban birni ne,"
Shiru tayi dai duk bata fahimci maganarshi ba, ita tunda take banda k'auyensu babu inda ta taɓa zuwa, ko k'auyukan mak'wabtansu bata sani ba.
Wayanshi ce tayo ringing, ya katse kiran sannan yace "lokaci nata wucewa, karna rasa mota, ko zaki rakani gari saiki dawo?"
"A'ah za'aita yimun surutun na fara fita ai, Allah ya kaika lafiya ya maido dakai lafiya"
"Ameen saina dawo" ya juya ya tafi, har yayi nisa tana mishi addu'a, sai k'ok'arin shanye kukanta take, tana daina ganinshi kau ta duk'e wurin ta fara kukan da babu mai rarrashinta.
BIRNI
Da marece sosae Yasser ya isa garin nasu, kai tsaye gidansu ya wuce, babban gidane, mai kyau da tsari, duk yanda kyanshi yazo muku a rai, ya wuce nan, idan kaa shiga bazaka taɓa tunawa a k'asarnan kake ba
Daman zaman jiranshi suke, sosae suke nuna farin ciki da zuwanshi, sai da ya nutsu ya zauna sannan suka k'ara gaisawa da momiensa,
Husna data kasa sakin jikkarshi duk ta rirrik'e tace "Yaya tsarabanah fa?"
Momie tace, "In banda abunki Asma'u wanne tsaraba ne a k'auye?"
"nidai inaso momie, ai shine yamun alk'awari"
"indai tsaraba ne gaki gashinan, inda abunda zaki iya ci"
"zanci indai bazai ɓatamun ciki ba"
"kin daiji dashi" yace mata
Kiran wayarshi da akayine ya sakashi mik'ewa,
"Bara in shiga in shiga ciki momie, idan Daddy ya shigo a kirani plz" yana kallon husna ya k'arasa maganar,
Dariya take rik'ewa da yayi hanyar ɗakinshi, "tohh yaya, abincinka nananma, yaa daɗe yana jiranka"
"Yauwah k'anwar"
Yana tafiya ya ɗauka kiran, muryarta ta sauka a cikin kunnanshi,
"Hakanan jikina ya bani yau Masoyina ya dawo"
Yasseer ya saki murmushi kamar tana ganinshi, "Kin canka dai dai, yanzunnan ban daɗe da dawowa ba"
"Aina sani, kuma shine baka faɗamun ba?"
"Yi hak'uri Masoyiyah, nayi laifi"
"Zan hak'ura anma sai kaazo na ganka"
"Insha Allah gobe zaki ganni"
"Ban yarda ba, nidai yau zan ganka"
"Kinsan na shawo gajia fa, gashi dare yayi, goben idan nazo har saikin gaji dani"
"nidai A'ah, wata uku fa ban saka ka a idanuna ba"
"tunda kinyi hak'urin wata uku, ki k'aramin en awanninnan mana, nima fa naso in ganki"
Suna cikin maganar ya isa ɗakinshi, duhu yaa fara ta ko ina yakai hannu zai kunna fitila, sai kawai ya jiyo an rungumoshi ta baya, zai juyo ta saka hannu ta rufe mishi fuska.
©Rabiatu sk msh
[3/7, 12:13 AM] +234 703 962 5239: ♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
41-45
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Rik'e hannuwanta yayi yana shafawa, sannan yayi murmushi,
"Rabi'ah?" sautin dariyarta ne ya fita sannan ta sakeshi, bayan sun katse wayan.
"Haba ko baki rufemun ido ba, ina shigowa gidannan jikina ya bani kina ciki"
"Hhm ba waninnan, kaida kace bazakaje ka ganni ba, ni kaɗaice na damu da ganinka ma"
"A'ah ai don nasan kina gidanne"
"Hhm ka cika wayau"
"Faɗin Gaskia dai"
Sannan takai hannu ta kunna hasken,
"Da alama kaa gaji Masoyi, bara in jiraka a fallo ka watsa ruwa"
"aini nama manta da wani gajia fa tunda na ganki"
"hhm tohh shknan, kayi sauri dai banso ka zauna da yunwa"
Yayi daria "tohh ko zaki tayani?"
Sai data tsaya tana ɗan tunani, sannan ta ware ido "I wish i could, anma ai akwai lokaci" tana mayar mishi da murmushinshi
Rabi'ah kenan, k'awar Husna ce tun suna sckul, harsun zama tamkar en uwa, suna gari ɗaya anma har kwana tanayi a gidansu Husna saboda Yasseer, tunma kafin su fara soyayya, har yaji shima tayi mishi ya bayyana mata sirrin zuciyarshi, ba wani ɓata lokaci ta amince mishi, yanzu haka babu wanda baisan da maganar soyayyarsu ba, itace ma wacce zai aura.
Cikin mintuna kaɗan ya gama wankan ya fito, sannan ya zura kaya, zaune ya tardata saman carpet ta jera abincin tana jiranshi, lokacin an kira Sallahr Magrib, ya wuce masallaci itama ta shiga toilet ɗinshi tayo alwala.
Bayan yaa dawo anan suka baje falo, tana zuba mishi abinci, ya kalleta sannan yace,
"Da alama akwai magana bakinki"
"Kuma akwai damuwa a zuciyana ba"
"Duk meya kawo hakan?"
Ta k'ara ɓata fuska, da alama abun na damunta sosae,
"k'auyen can mana, Allah banison zamanka k'auyennan, daga bazaka daɗe ba, harfa cewa kayi bazaka zauna ba, anma shine kayi daɗewarnan"
"to ai gashi naa dawo, duka wata nawa ya ragemun in gama duka?"
"Hakane anma nidai don kak'i, anma wallahi tun farko da nayima Abba magana an barka nan"
"A'ah ni nafison inyi bautar k'asarnan inda aka turani"
"Saboda ka ringa ganin en matah ba"
Ita maganarshi ma dariya ta bata, "K'auyene fa Rabi'ah"
"k'auyen basu da idanune? Na tabbata ko duk makafine ka wuce ta inda suke dolema suji sunason mallakarka, kana dakyau Yayanmu, ka mallaki duk wani abu da mace zataso a wurin namiji, en k'auyen daka raina nasan suma rububinka suke"
Har yanzu dariyar yake mata "kedai kin cika kishine kawai, anma plz ki daina wahalar da kanki akan en matan k'auye, ina laifi ma kiyi kishi da wayayyu en birni?"
"Indai a kanka ne ban raina kishi da kowa ba, ina sonka da yawa ne, ni kaina bansan kalar son da nake maka ba dahar nakejin idanna rasaka zan iya rasa raina, kuma da inyi kishi da wata a kanka, k'aramun in rasaka, don bansan kuma halin dazan shiga ba"
Mummunar faɗuwar gabane tazo mishi, shi sai yanzu ma ya tuna da yana da wata mata, yaya kenan idan Rabi'ah tasan shifa yanzu mai aurene? Gaba ɗaya jikinshi yayi sanyi, zufa duk taa jik'a mishi riga, bai iya bata amsa ba, sai dai yayi shiru kawai yana tura abincin dak'yar.
Washe gari kowa yaa hallara a dinning suna break fast, Momie, Daddy, Husna, da Rabi'ar Yasseer, suna cin abinci sai satar kallonshi take, tana so su haɗa ido, anma ko kallonta baiyi ba, ganewa ne kawai Rabiah batayi ba anma tun jiya Yasseer cikin damuwa yake, ta k'asa ta sanya k'afa tana zunguroshi, ya ɗaga kai suka haɗa ido, murmushi ta sakar mishi, da sauri ya maida kanshi yana ci gaba da wasa da cokali,
Murmushin mugunta tayi, sannan ta haɗa yatsunta biyu na k'afa, ta kamo yatsarshi ɗaya ta matse, har saida yaso yayi k'ara, ya ɗago kanshi da sauri ta tuntsure da daria, Husna naa lura dasu, daria take ciki-ciki, sannan ta shanye tace,
"Wai yaya har yau naji shiru, nifa na k'ara biki yazo musha shagali, Gani k'anwar Ango kuma k'awar Amarya"
Wani kallo ya watsa mata, "Ke! Ina wasa dake?"
Can ciki tace "to ni ba k'awar budurwarka bace"
"Kika ce?"
"Ba komai, kawai ina tunanin Yaya Najib ne"
"ai saiki bishi makarantar"
Ta turo baki zata k'ara magana Daddy ya katsesu, "Ya isa hakanan!" ya kalla momie, "Daman maganar da nace miki inasonyi dashi kenan idan yaa dawo, tunda dai bautar k'asar ake jira ya k'are, sai a saka lokaci wata ɗaya bayan yaa gama"
"Hakanma yayi Alhaji, Allah ya kaimu"
Daɗine ya kama Rabi'ah, da gudu ta tashi ta tafi ɗakin Husna cikin jin kunya,
"Ameen, kinga tare dana Husna kenan" itama tashi tayi tabar wurin, Daddy ya ɗaga kai yana kallon Yasseer daya haɗiye abincin daya saka baki dak'yar,
"Bakace komi ba, hakan yaa maka dai-dai?"
"eeh yayi"
"Yauwah toh abinda nakeso ka gane, yarinyarnan tana sonka sosai, amanah ce a wurinka, don haka kaci gaba da rik'e amanarta, ban yarda da abinda zakai mata ka ɓata mata rai ba"
Momie tace "Gaskia ne Alhaji, an riga an tsayar da magana a tsakaninku, ban yarda da wata doguwar magana ba daga baya, kowanne zama ɗan hak'uri ne, don haka komai ya faru tsakaninku, kuna dai daitashi basai kowa yaji ba"
"Insha Allah Momie, Daddy zan kiyaye" ya faɗa dak'yar, yana k'ok'arin ɓoye tashin hankalin daya shiga. Robar ruwan Faro mai sanyi ya ɗauka ya kafa a baki, saida ya shanyeshi tas baima sani ba sannan ya sauke robar, ko kan abincin bai k'ara bi ba ya wuce ɗakinshi yana tunani,
Saude MATATAH CE, anma ko kaɗan banijin sonta a raina, Rabi'ah itace Masoyiyatah, kuma wacce ta dace dani, itace nake burin na k'are rayuwata da ita, anma abunda zai faru idanta gano ina da wata matar bamai kyau bane, banson na rasa Rabiah, itace burin zuciyatah, anma ya zanyi da auren Saude?
K'AUYE
Daren Ranar da Yasseer ya tafi, dak'yar Saude ta iya barci ita kaɗai, sai rungumar filo take, tunaninshi kawai ya hanata ta runtsa, ji take daman yana tare da ita, ta k'ara lumshe ido tana rik'e da filo kamar yana tare da ita,
"harda wani cewa kake 'Saude abunda kika bani ma ya isa har k'arshen rayuwatah bazan manta dake ba' Hmm ni kuma saika bani yanayin da bazan taɓa iya rayuwa babu kai ba, ka daure ka dawo da wuri, ina buk'atarka" tayi murmushi, ita kaɗai tasan yanda takeji akan Yasseer, cikin kewarshi barci ya ɗauketa,
Tunda Safe bugun gidan da ake ya tasheta, ana dukan k'ofar kamar za'a ɓallata har saida ta tsorata, ta mik'e ta tafi tana tunanin ko waye? Tambaya tayi "Waye?"
"Uwaki ce" saida gabanta ya faɗi da taji muryar Gwaggo Bilki, ko tunawa da itama batason yi, jikinta na kyarma ta bangajeta ta shiga gidan,
"Lallai, kin samu wuri ko tunawa bakiyi damu, duk yacce zakiyi dai baki da kamarmu, shegiya mai bak'in hali," ita dai bin bayanta kawai tayi suka shiga gidan, ko gaisuwarta ma bata amsa ba, ta shige ɗakin,
"naji ance mijinki yayi tafiya, abunda ya bar muki zaki ɗauko ki bani"
"ai ba daɗewa zaiyi ba, babu abunda ya barmun"
"k'arya kike! ni zakima k'arya? Tun kafin kiyi wayau muke ciyar dake, ke kinyi gidan miji zaki gujemu ko" sai faɗa take tana ɗage ɗage duk ta watsa en kayan dake cikin ɗakin, ta hankaɗa katifa bata samu komi ba, da taga dai babu kuɗin da take nema, ta buɗa kwalayen da kayan abinci suke ta kwashi son ranta,
"idan kin hana kuɗi ai bazaki hana wannan ba" bata tanka mata ba, ta ɗauka hartaa fita ta dawo data tuna bata duba k'asan laida ba, tana ɗagawa kuwa sai ga kuɗi, ta ɗago tana kallon Saude,
"Hinyeh! Munafuka, ni zakima k'arya ko?" takai mata rank'washi, sannan ta k'irga kuɗin,
"Duk dubu Ukun ma zan tafi dasu, tunda ba daɗewa zaiyi ba kin gane" ta kalleta k'walla suka zubo mata, ta k'ara kai mata bugu "kin tsuramun k'attan idanunki kina kallona, muna fuka" ta gama zazzaga mata, sannan ta kaɗa buje tai gaba,
©Rabiatu sk msh
[3/7, 12:13 AM] +234 703 962 5239: ♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
46-50
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Kwana biyun da Yasseer ya mata alk'awari, bai k'ara ba ranar sunday da dare harma ta fidda rai da dawowarshi taa kwanta, ta jiyo bugun gidanshi da sauri ta tafi ta buɗe,
Tsayawa tayi tana kallonshi cikin hasken farin wata, er tafiyarnan da yayo harya k'ara komawa ɗan gayun fiye da daa, kyanshi yaa k'ara fitowa, ga wani haske daya k'arayi, tama rasa ta inda zata bayyana mishi farin cikin da taji da dawowarshi, kamar ta rungumeshi takeji sai kallonshi take tana washe baki,
Shima tsayawa yayi yana kallonta, wai nan mijintane ya dawo anma batasan yanda zata tarbeshi, Rabiah ya tuna dako igiyar shanya bata taɓa shiga tsakaninsu ba ballantana ta aure, anma data ganshi zata rungumeshi cikin farin ciki tana faɗa mishi daɗaɗan kalamai, anma ita da take matarshi batasan yanda zata tarbeshi ba, wani haushinta ma ya fara ji, tun farko meya kaishi aurenta? Er k'auye da ita duk taa canja mishi lissafi,
"Sannu da dawowa"
"Yauwah sannu da gida" ya wuceta ya shiga cikin gidan, tabi bayanshi yana zama ta kawo mishi abinci ta ajje.
"A'ah na k'oshi da abincinnan, a gajiye nake kwanciya ma zanyi"
Tace "tohh" sannan ta koma gefe ta zauna, ya gama rage kaya ya tashi ya shiga ya watsa ruwa, sannan ya dawo ya saka kaya mararsa nauyi duk tana zaune tana jiranshi, ya haye gado ya kwanta, itama bata matsa mishi ba ta raɓa gefe itama ta kwanta babu wani dogon magana a tsakaninsu.
Washe gari ma tunda wuri ya fice, bayan ya bata kayan tsarabarta, da abubuwan daya sawo mata, yana fita ta fara buɗawa tana murna, ɗinkuna ne masu kyau kalar na birni dai dai jikinta, kala biyar da hijabbai harda takalma, ita kaɗai ta ɗinga murna a gida.
Ta buɗa sauran kayan mayukan shafawa da kayan wanke kai, harda kayan abinci, tsarabar birni kala-kala, babu ma wanda tasan amfaninshi,
Saida ya kusan dawowa ta shiga wanka bayan ta gama aikin gidan, cikin kayan Gwanjon daya sai mata ta zaɓi wanda tafiso a ciki ta saka, sannan ta zauna shafa, tana cikin shafa mai yayi sallama ya shigo, ta amsa.
Yana yaye labulen yayi tsaye yana kallonta,
"Menene kike shafawa Saude?"
"Man shafawan daka kawomun ne"
Ya k'arasa shigowa ɗakin duk takaici yaa cika mishi zuciya, "Yanzu Saude blue band ɗinne man shafawa? Abun da akecin bread ne fa"
Ya duk'a yana shinshina kanta jin warin Shampoo da takeyi, k'amas babu ruwa a jiki, duk taa tsorata ganin yanda ranshi ya ɓaci, ya kama hannunta yana shinshinawa,
"Dame kikayi wanka?"
"Wannan sabulun mai ruwa"
"wanne irin sabulu kuma?"
Tashi tayi daga inda take ta ɗauko mishi shampoo ta mik'a mishi ya saki baki yana kallonta, duk ta marairaice da ita,
"Saida naji k'amshin sabulu gareshi nasan wanka za'ayi dashi, kuma kumfa gareshi sosae har saida na k'ara watsa wani botikin ruwan sannan kumfan ya fita"
Tana k'arasa maganar ya kwashe da dariya, donshi dariyama ta bashi, saida yayi mai isarshi sannan yace ta ɗauko kayan ya fara nuna mata yanda zatayi amfani dasu.
Bayan Wata Biyar.
Saura wata ɗaya ya gama bautar k'asa, zamansu ba yabo ba fallasa, tana matuk'ar girmamashi, shima yana k'ok'arin kyautata mata, yanzu yaa daina daɗewa baije gida ba, kuma duk sanda zai dawo da sabuwar damuwa yake zuwa, gashi yanzu ya kusan gama bautan k'asa, baisan yanda zaiyi da Saude ba, don bama zai iya tunkarar gidansu da ita ba,
Cikin watan ne ta fara laulayin ciki, wahala yake bata sosae, ya koma kusan komai ma shi yake mata, duk tayi yaushi ta rame, abunda ke k'ara mishi damuwa kenan,
Sauran sati ɗaya ya gama bautar k'asa ya ɗauketa suka tafi gidan Kawu Ado, daman daga ganinsu shida Gwaggon suka ɓata rai, ko shimfiɗar tabarma ba'a musu ba, saidai suka tsuguna kan k'afafunsu suna gaishesu, babu wanda yayi amsawar kirki a cikinsu,
Yasseer ne yayi magana "baba dama zuwa nayi in faɗa muku na kusan komawa gida insha Allah"
"tohh naji, sai akayi yaya?"
"maganar Saude ce, zata zauna anan tunda har yanzu iyayena basu san da auren ba, idan na samu lokaci zan dawo insha Allah"
Tunda ya fara magana take kallonshi, ita batasan da maganar zai tafi ya barta ba,
"Idan ka barta anan sai yaushene zasu san da auren naku? Ni duk wannan bai shafeni ba, Saude dai na samu na aurar da ita, don haka babu sauran wani abu tsakanina da ita, duk yanda kaso kayi da ita, anma karka sake ka kawomun ita nan"
Hularshi ya cire saboda zufar data karyo mishi, "Akwai matsala ne idan naje da ita Baba"
"Aini nafison a samu matsalan idan kunje, anma bazaka bar Saude anan ba, ka ɗauka matarka ku fice, idan zasu saka wuk'a su gutsuttsura ta bai dameni ba, babu sauran alak'a tsakanina da ita, don haka banma ce ku k'ara zuwa inda nake ba"
Su duka kasa motsi sukayi, anma Saude daɗi taji sosae da Kawu yace da ita Yasseer zai tafi,
"ku tashi ku tafi nace" kawu ya k'ara daka musu tsawa, jiki a sanyaye Yasseer yayi hanyar fita, itama ta tashi ta bishi.
Tun daga ranar itama ta fara shirin tafiya, kullum cikin zumuɗin tafiyar take, saboda murnar tafiya birni ma ko lura da fushin da yake da ita batayi ba, ko kaɗan ya daina sakar mata fuska, bala'in haushinta yakeji, gashi kullum bata lafiya,
Ana gobe zai tafi tana kwance tana barci, yayi tagumi yana tunanin wannan k'addararren aure, bazai iya sakin Saude ba, kuma bazai iya tafiya da ita ba, bai tanaji kalmomin dazaiyima iyayenshi, iyayen Rabiah da itama Rabiahr bayanin matsayin Saude a wurinshi, Saude Matarshi ce kuma harda ɗanshi a cikinta, ta yayama zasu tsaya harya musu bayanin er k'auyen daya aura daga zuwa bautar k'asa?.
Yana Zaune har akayi kiran Sallahr farko, ya kalli inda take kwance tana sharar barci, kallonta yake cikin tausayawa a fili yace,
"Kiyi hak'uri Saude, ki yafemun anma bazan iya zuwa gaban iyayena dake ba, bani da zaɓi ne bayan wannan, kiyi hak'uri ki raini ɗanmu har girmanshi, bazan taɓa mantawa da zaman da mukai ba" jin da Yasseer yayi hawaye nason zubo mishi, ya mik'e da sauri ya ɗauka jikkarshi ta tafiya, a hankali ya buɗe gidan ya fita cikin duhun Asuba.
****
Cikin mafarki ta ganta cikin daji, gudu take iyakar k'arfinta, tana tafiya tana waiwayen baya, gaba ɗaya duhu take gani ta ko ina, batasan sanda k'afarta ta faɗa cikin wani zurmemen rami ba, ta k'walla ihu.
Cikin ramin wani tsananin rayuwah ne ya baibayeta, ta ko ina ji take rayuwar ta juya mata baya, sai kuka take tana neman agaji daga Mahaliccinmu, tana hawaye tana rok'on Allah ya kawo mafa ɗauki.
A hankali taga haske ya fara bayyana ta cikin ramin data faɗa, har wurin yayi haske sosae, ta ɗaga kanta tana kallon wajen ramin, idonta yayi tozali da kyakkyawar fuskar Yasseer yana mata murmushi, hannu ya mik'a mata alamar ta taho, da sauri ta tashi cikin farin ciki ta mik'a mishi hannun ya rik'e gam, wani farin ciki da bata taɓa ji ba ya ziyarceta, sai murmushi take tana murna,
Yana cikin fiddota daga ramin data faɗa tana cikin jin daɗi, sai kuma taji ya saki hannunta ta koma ciki, tana shiga duhun ya k'ara lulluɓeta. A firgice ta farka tana Addu'ah a ranta, ta duba inda Yasseer yake kwance babushi ba alamarshi.
©Rabiatu sk msh
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
51
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Cikin tashin hankali Saude ta tashi ta fara waigen ɗakin bata ga Yasseer ba, a ruɗe ta tafi k'ofar toilet ko yana ciki anma bata jiyoshi ba, kamar kaɗangaruwa ta ringa bin bango harta lek'a ciki bainan, tsananin tashin hankali batasanma sanda ta fita daga gidanba, tafiya mai nisa tana nemanshi har wurin masallaci duk da ba'a shiga ba, haka ta daure ta dawo gida,
Sai lokacinma ta duba duk kayan Yasseer bai bar komi ba, katifarnan kawai ya bar mata da kayan amfani, tana ɗaga filo sai gaa mak'udan kuɗi nan yaa bar mata, sai lokacin ta ida yarda lallai Yasseer yaa barta, wani irin kuka ne yazo mata na tausayin kanta.
Ta saka hannu tana shafa cikin jikinta cikin muryar kuka tace "Shikenan mahaifinka yaa tafi ya barmu, ya tafiyanshi, ya gudu ya barni dakai kaɗai" ta k'ara fashewa da wani kuka,
"Lallai sai yau na k'ara yarda ni marainiyah ce, kayi kuskure Yasseer, kayi kuskure daka shigo rayuwatah ka cutar da wannan raunanniyar zuciyar tawa, kaa riga kaa gama da zuciyatah, tunda ka koyar dani yanda zan soka, kuma ka gudu ba tare daka nunan hanyar dazan daina ba" kuka yaci k'arfinta, tana dukan bango tana kuka, komai na duniyar gaba ɗaya yaa daina mata daɗi.
Gari naa fara haske ta zari mahafi sai gidan Kawu Ado, shi ɗinne dai komai zai mata bata da inda zata kai kukanta daya wuce can, idanunta duk sun kumbura, duk da rufe fuskar da take en k'auyen sai binta suke da kallo. Harta isa gidan da sallamarta ta shiga, sunyi shimfiɗa tsakar gida suna cin ɗumame, duk suka saki baki suna kallonta.
Tun kafin tayi magana Gwaggo bilki ta mata tsawa "Yau kuma da wacce tsiyar kikazo mana? Halan kinyi bak'in halin da mijin naki ya fasa tafiya dake?"
Munanan tambayoyin da suka dira kunnanta kenan daga bakin Gwaggo, anma da yake hankalinta a tashe yake saita k'ara fashewa da wani sabon kukan, "Guduwa yayi, yaa gudu yaa barni"
"Tohm yanzu waya aika kiranki anan da kikazo kina faɗa mana? Ko sakinki yayi?"
"A'ah Gwaggo bai sakeni ba, don Allah ku taimakeni"
Sai yanzu baba Ado yayi Magana "Taimakon k'aniyarki? Lallai duk shekararnan ba'a rainamun hankali ba irin haka, mu ga yaranki ko, mu ringa zagaye gari gari muna nemo mikishi ko ya kikeso ayi? Yaron da bamu taɓa ganin kowa nashi ba bamusan daga inda ya fito ba, koko so kike ki dawo mana nan da zama?"
Yayi shiru yana mata wani irin kallo, "Tohh ko ɗaya bazai yiwu ba, shi kanshi bazai iya da bak'in halinki bane shiyasa ya gudu ya barki, don haka tunda muma mun samu kinyi nesa damu ki kiyaye ni, aradu na k'ara ganin ko sawunki ne hanyar gidannan sai naayi bala'in saɓa miki"
Gwaggo tace "k'warai kuwa malam, don kokai kaa yarda ta zauna ni bazan k'ara zama da ita ba, mijinta ma yaa gujeta ballantana mu"
Wani irin kuka ta fashe dashi tana rok'arsu, "Don Allah Kawu ka taimakeni, kai kaɗai ka rage gatana, bani da kowa a duniya sai kai"
"ni ɗinma fiddani a lissafinki, indai ni kike kallo a matsayin gatanki tohh bakki dashi, don haka ki tashi ki ficemun nace"
Kuka taci gaba dayi tana rok'arshi anma yayi biris da ita, da yaga bata da niyyar tafiya ma icce ya ɗauko ya rakata har waje a guje, ya tsaya yana ci gaba da masifa, tsabar kuka Saude har sik'ewa take, dak'yar ta iya kai kanta gida.
Lallai babu mai laifi a cikin rayuwar data tsinci kanta kamar kawu Ado, yana sane da cewa basu san asalin Yasseer ba, basusan kowa nashi ba suka bashi aurenta don tsanar da suka mata, da sun samu wani wanda yake garin komai talaucinshi komai nakasunshi yafi mata wannan auren k'addarar da suka ɗora mata, maganar Yasseer ce ta ringa dawowa mata kullum ta tambayeshi garin da yake,
"Kina tsoran kar in gudu in barki ne?" sai yanzu ne ya tabbatar mata da abunda yake nufi, duk da yarda dashi da tayi bata taɓa sakawa taa kawo hakan a ranta ba.
Bayan wata bakwai...
Rayuwar Saude har tafi ta daa muni, tana gida ita kaɗai sai abunda ke cikinta, ko waje batason lek'awa don da an ganta ne za'a fara mata wak'a irin tasu ta k'auye, ana sakar mata habaici, har yara gulmanta suke idan zata wuce, mijinta yaa gudu yaa barta, ita kam kullum cikin saka ran dawowar Yasseer take, don shine yasan inda take, tana saka ran duk daɗewa zai nemeta.
Wata rana tana zaune ita kaɗai tayi tagumi cikin watan haihuwarta, cikinta ne ya fara murɗawa, nak'uda tazo mata gadan-gadan, gashi babu kowa gidan sai ita kaɗai, daman babu mai zuwa inda take, ta dinga ihu tana neman agaji, tayi matuk'ar galabaita,
Cikin sa'a saiga k'awarta Hanne zata wuce ta shiga gidan, daman ita kaɗaice koda tana gidansu Gwaggo takejin tausayinta, ba ɓata lokaci ta tafi tazo da unguwar zoma, lokacin harta fara fita hayyacinta, ita ta taimaka mata harta haifo k'atuwar yarinyarta jajir kamar babanta. Farine kawai ta ɗauko na Babanta anma komai nata na mamantane, kamarsu ɗaya da Saude kamar tayi khaki.
Unguwar zoma da Hinde ne suka taimaka mata suka gyarata da jaririyar tata, zata tafi ta ɗauko kuɗin sallama ta bada ta tafi tana ta godia, Hinde ita ta samo maiyi ma Saude wanka da erta, idanta samu lokaci tana zagayota, da en tsirarun en k'auyen masu zuwa su bama idonsu abinci, su gwaggo dai ko lek'e har akayi suna.
Cikin kuɗin da Yasseer ya bar mata ne, ta saima yarinyar kayan sakawa, tasa aka yanka ma yarinyar ragon suna, taaci suna Hafsat, saboda yanda takeson sunan, kuma babu dai wanda zai zaɓa ma er tata suna bayan ita.
Kwanci tashi babu wuya wurin Allah, Hafsat ta fara girma, taayi wayau ita ta zama abokiyar firar Saude, ita take ɗebe mata kewar mahaifinta, ko wasanta take da Saude tayi shiru tana tunani zata rarrafo ta tafi inda take, tana ɗaukarta tayi ta wangale baki.
Zara dai bata barin dame, hafsat nada kusan shekara biyu komai ya fara fin k'arfin Saude, duk kuɗin dake hannunta sun k'are tunda daman ba juyasu take ba, harta fara siyarda kayan amfanin gidan, rayuwar hafsa take tausayamawa, batason ta tashi cikin k'uncin rayuwa ta saba da babu da yunwa, idanma ta zauna a haka ai saidai yunwa tayi ajalinsu tunda babu mai taimaka mata, sannan kuma wacce amsa ma zata bama hafsat idan taa girma ta tashi tambayarta waye mahaifinta? Taa rasa sana'ar da zatayi, gashi k'auyen ba kowane ke bada aikatau ba, kowa baison fidda kuɗi.
Wata matar dake ɗaukar en aiki takai birni taje ta samu ta faɗa mata buk'atarta nason ta samar mata gidan aiki inda za'a dinga biyanta koda abincin da zataci ne,
Baba haja ta nisa tace "Anya Saude zaki iya kuwa? Nifa banan kusa nake kai en aiki ba, can birnin Abuja nake zuwa"
"koma a inane zan iya zuwa wallahi baba Haja, wake gareni a k'auyen da bazan iya tafiya ba? Ai yin nesan ma shine zaifimun Alkhairi"
"tohh Allah yasa hakan, daman akwai wata Amaryah ce don ko haihuwa batayi ba, tace in samo mata er aiki, Allah yasa ta amsheki don basu cikason en aiki yara ba"
"Ameen baba, ni indai zata amince wallahi aikinta ko yakai girman me zan iya mata"
"Tohh ai shikenan, sai kije ki fara shirye-shirye idanna tashi tafiya zan nemeki"
Tayi ma baba Haja Godia sosae sannan ta tashi ta tafi.
Tana shirin tafiya tana tunanin yanda Yasseer ya mata, saida ta gama shiri ya tafi ya barta, ita yanzu tama fidda rai da dawowarshi, don indai bai manta da ita ba tsawon lokacinnan yaa isa ya nemeta.
Ko sati biyu ba'ayi ba, baba Haja ta aiko mata tafiya taa tashi, en kayanta da suka rage daman duk taa sayar, ta tattara en kuɗinta suka tafi, bayan taje tayima mai gidan hayar da suke godia, don daman cewa yayi kuɗin da Yasseer ya biyashi ko zata shekara biyar a ciki bazasu k'are ba, ta bar mishi dai ta tafi.
Wa yaga Saude a Abuja😄 ita da ko k'auyensu bata taɓa bari ba, nima dai naa tafi in shirya don dani za'aje Abujar nan😃👯👯
©Rabiatu sk msh
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Arewa hausa novels
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)
WHATSAPP NO:
+2347039625239
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
51
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Cikin tashin hankali Saude ta tashi ta fara waigen ɗakin bata ga Yasseer ba, a ruɗe ta tafi k'ofar toilet ko yana ciki anma bata jiyoshi ba, kamar kaɗangaruwa ta ringa bin bango harta lek'a ciki bainan, tsananin tashin hankali batasanma sanda ta fita daga gidanba, tafiya mai nisa tana nemanshi har wurin masallaci duk da ba'a shiga ba, haka ta daure ta dawo gida,
Sai lokacinma ta duba duk kayan Yasseer bai bar komi ba, katifarnan kawai ya bar mata da kayan amfani, tana ɗaga filo sai gaa mak'udan kuɗi nan yaa bar mata, sai lokacin ta ida yarda lallai Yasseer yaa barta, wani irin kuka ne yazo mata na tausayin kanta.
Ta saka hannu tana shafa cikin jikinta cikin muryar kuka tace "Shikenan mahaifinka yaa tafi ya barmu, ya tafiyanshi, ya gudu ya barni dakai kaɗai" ta k'ara fashewa da wani kuka,
"Lallai sai yau na k'ara yarda ni marainiyah ce, kayi kuskure Yasseer, kayi kuskure daka shigo rayuwatah ka cutar da wannan raunanniyar zuciyar tawa, kaa riga kaa gama da zuciyatah, tunda ka koyar dani yanda zan soka, kuma ka gudu ba tare daka nunan hanyar dazan daina ba" kuka yaci k'arfinta, tana dukan bango tana kuka, komai na duniyar gaba ɗaya yaa daina mata daɗi.
Gari naa fara haske ta zari mahafi sai gidan Kawu Ado, shi ɗinne dai komai zai mata bata da inda zata kai kukanta daya wuce can, idanunta duk sun kumbura, duk da rufe fuskar da take en k'auyen sai binta suke da kallo. Harta isa gidan da sallamarta ta shiga, sunyi shimfiɗa tsakar gida suna cin ɗumame, duk suka saki baki suna kallonta.
Tun kafin tayi magana Gwaggo bilki ta mata tsawa "Yau kuma da wacce tsiyar kikazo mana? Halan kinyi bak'in halin da mijin naki ya fasa tafiya dake?"
Munanan tambayoyin da suka dira kunnanta kenan daga bakin Gwaggo, anma da yake hankalinta a tashe yake saita k'ara fashewa da wani sabon kukan, "Guduwa yayi, yaa gudu yaa barni"
"Tohm yanzu waya aika kiranki anan da kikazo kina faɗa mana? Ko sakinki yayi?"
"A'ah Gwaggo bai sakeni ba, don Allah ku taimakeni"
Sai yanzu baba Ado yayi Magana "Taimakon k'aniyarki? Lallai duk shekararnan ba'a rainamun hankali ba irin haka, mu ga yaranki ko, mu ringa zagaye gari gari muna nemo mikishi ko ya kikeso ayi? Yaron da bamu taɓa ganin kowa nashi ba bamusan daga inda ya fito ba, koko so kike ki dawo mana nan da zama?"
Yayi shiru yana mata wani irin kallo, "Tohh ko ɗaya bazai yiwu ba, shi kanshi bazai iya da bak'in halinki bane shiyasa ya gudu ya barki, don haka tunda muma mun samu kinyi nesa damu ki kiyaye ni, aradu na k'ara ganin ko sawunki ne hanyar gidannan sai naayi bala'in saɓa miki"
Gwaggo tace "k'warai kuwa malam, don kokai kaa yarda ta zauna ni bazan k'ara zama da ita ba, mijinta ma yaa gujeta ballantana mu"
Wani irin kuka ta fashe dashi tana rok'arsu, "Don Allah Kawu ka taimakeni, kai kaɗai ka rage gatana, bani da kowa a duniya sai kai"
"ni ɗinma fiddani a lissafinki, indai ni kike kallo a matsayin gatanki tohh bakki dashi, don haka ki tashi ki ficemun nace"
Kuka taci gaba dayi tana rok'arshi anma yayi biris da ita, da yaga bata da niyyar tafiya ma icce ya ɗauko ya rakata har waje a guje, ya tsaya yana ci gaba da masifa, tsabar kuka Saude har sik'ewa take, dak'yar ta iya kai kanta gida.
Lallai babu mai laifi a cikin rayuwar data tsinci kanta kamar kawu Ado, yana sane da cewa basu san asalin Yasseer ba, basusan kowa nashi ba suka bashi aurenta don tsanar da suka mata, da sun samu wani wanda yake garin komai talaucinshi komai nakasunshi yafi mata wannan auren k'addarar da suka ɗora mata, maganar Yasseer ce ta ringa dawowa mata kullum ta tambayeshi garin da yake,
"Kina tsoran kar in gudu in barki ne?" sai yanzu ne ya tabbatar mata da abunda yake nufi, duk da yarda dashi da tayi bata taɓa sakawa taa kawo hakan a ranta ba.
Bayan wata bakwai...
Rayuwar Saude har tafi ta daa muni, tana gida ita kaɗai sai abunda ke cikinta, ko waje batason lek'awa don da an ganta ne za'a fara mata wak'a irin tasu ta k'auye, ana sakar mata habaici, har yara gulmanta suke idan zata wuce, mijinta yaa gudu yaa barta, ita kam kullum cikin saka ran dawowar Yasseer take, don shine yasan inda take, tana saka ran duk daɗewa zai nemeta.
Wata rana tana zaune ita kaɗai tayi tagumi cikin watan haihuwarta, cikinta ne ya fara murɗawa, nak'uda tazo mata gadan-gadan, gashi babu kowa gidan sai ita kaɗai, daman babu mai zuwa inda take, ta dinga ihu tana neman agaji, tayi matuk'ar galabaita,
Cikin sa'a saiga k'awarta Hanne zata wuce ta shiga gidan, daman ita kaɗaice koda tana gidansu Gwaggo takejin tausayinta, ba ɓata lokaci ta tafi tazo da unguwar zoma, lokacin harta fara fita hayyacinta, ita ta taimaka mata harta haifo k'atuwar yarinyarta jajir kamar babanta. Farine kawai ta ɗauko na Babanta anma komai nata na mamantane, kamarsu ɗaya da Saude kamar tayi khaki.
Unguwar zoma da Hinde ne suka taimaka mata suka gyarata da jaririyar tata, zata tafi ta ɗauko kuɗin sallama ta bada ta tafi tana ta godia, Hinde ita ta samo maiyi ma Saude wanka da erta, idanta samu lokaci tana zagayota, da en tsirarun en k'auyen masu zuwa su bama idonsu abinci, su gwaggo dai ko lek'e har akayi suna.
Cikin kuɗin da Yasseer ya bar mata ne, ta saima yarinyar kayan sakawa, tasa aka yanka ma yarinyar ragon suna, taaci suna Hafsat, saboda yanda takeson sunan, kuma babu dai wanda zai zaɓa ma er tata suna bayan ita.
Kwanci tashi babu wuya wurin Allah, Hafsat ta fara girma, taayi wayau ita ta zama abokiyar firar Saude, ita take ɗebe mata kewar mahaifinta, ko wasanta take da Saude tayi shiru tana tunani zata rarrafo ta tafi inda take, tana ɗaukarta tayi ta wangale baki.
Zara dai bata barin dame, hafsat nada kusan shekara biyu komai ya fara fin k'arfin Saude, duk kuɗin dake hannunta sun k'are tunda daman ba juyasu take ba, harta fara siyarda kayan amfanin gidan, rayuwar hafsa take tausayamawa, batason ta tashi cikin k'uncin rayuwa ta saba da babu da yunwa, idanma ta zauna a haka ai saidai yunwa tayi ajalinsu tunda babu mai taimaka mata, sannan kuma wacce amsa ma zata bama hafsat idan taa girma ta tashi tambayarta waye mahaifinta? Taa rasa sana'ar da zatayi, gashi k'auyen ba kowane ke bada aikatau ba, kowa baison fidda kuɗi.
Wata matar dake ɗaukar en aiki takai birni taje ta samu ta faɗa mata buk'atarta nason ta samar mata gidan aiki inda za'a dinga biyanta koda abincin da zataci ne,
Baba haja ta nisa tace "Anya Saude zaki iya kuwa? Nifa banan kusa nake kai en aiki ba, can birnin Abuja nake zuwa"
"koma a inane zan iya zuwa wallahi baba Haja, wake gareni a k'auyen da bazan iya tafiya ba? Ai yin nesan ma shine zaifimun Alkhairi"
"tohh Allah yasa hakan, daman akwai wata Amaryah ce don ko haihuwa batayi ba, tace in samo mata er aiki, Allah yasa ta amsheki don basu cikason en aiki yara ba"
"Ameen baba, ni indai zata amince wallahi aikinta ko yakai girman me zan iya mata"
"Tohh ai shikenan, sai kije ki fara shirye-shirye idanna tashi tafiya zan nemeki"
Tayi ma baba Haja Godia sosae sannan ta tashi ta tafi.
Tana shirin tafiya tana tunanin yanda Yasseer ya mata, saida ta gama shiri ya tafi ya barta, ita yanzu tama fidda rai da dawowarshi, don indai bai manta da ita ba tsawon lokacinnan yaa isa ya nemeta.
Ko sati biyu ba'ayi ba, baba Haja ta aiko mata tafiya taa tashi, en kayanta da suka rage daman duk taa sayar, ta tattara en kuɗinta suka tafi, bayan taje tayima mai gidan hayar da suke godia, don daman cewa yayi kuɗin da Yasseer ya biyashi ko zata shekara biyar a ciki bazasu k'are ba, ta bar mishi dai ta tafi.
Wa yaga Saude a Abuja😄 ita da ko k'auyensu bata taɓa bari ba, nima dai naa tafi in shirya don dani za'aje Abujar nan😃👯👯
0 comments:
Post a Comment