Tafiya kawai suke babu wanda kema wani magana, duk a takure take, shikam ko a jikinshi kamar baisan tana a motan ba.
Dai dai wurin wani babban wuri taga yayi parking da batasan ko ina bane, ya fita ya barta a motan, bai daɗe ba saiga wata kyakkyawar budurwa ta fito wurin tana ta karairaya tasha Makeup harya mata yawa.
Tana daga ciki suke maganarsu har suka gama, sai dai ya buɗe mata yace ta fito, kallonsu dai kawai take, budurwan ta kalleshi tana wani lumshe ido.
"zan maka waya idan an gama, don zai ɗauka lokaci gaskia"
"ba komai, idan an gama inanan ina jira"
"owk, muje ko Saude?" ta kalleta tana murmushi, maida kallonta tayi kan Najib duk a tsorace take, ya ɗaga mata kai, sannan ta juya ta bita.
Hannunta ta sak'ala cikin nata, suka shiga wurin tana binta a baya sai da taga mata da yawa wurin hankalinta ya kwanta, wasu ana musu kitso, wasu gyaran gashi, wasu Make up, wasu gyaran fuska, kowa dai da abunda ake mata.
Wurin mai gyaran jiki takai ta, wani ɗaki ana ma wata an kusan gama,
"Aunty Nainah sannu da zuwa, keda kanki kuma?"
Bata tsaya bata amsa ba tace "ko waye a layi, dakin gama wanda kikema ga sistatah, ki mata gyaran jiki mai kyau so nake idanna dawo bazan ganeta ba"
"tohm shikenan Aunty an gama" Saude tana zaune kamar tayi tsalle don murna, duk ta matsu a gama itama ai mata, sai bin mutanen wurin take da kallo tana murmushi.
Gyaran jiki, fata, k'afa, fuska, gashi, baki, wuya komai lungu da sak'o na jikinta babu wanda ba'a gyara ba, wata haɗaɗɗiyar doguwar rigane red colour, Aunty Nainah ta kawo mata, ta shiga ta saka, sannan aka mata Makeup, ita da kanta ta naɗa mata gyalen rigar, sannan taja hannunta,
"Zo muje" tabi bayanta har gaban Mirror, tsayawa kawai tayi baki buɗe tana kallon kanta, wai itace nan a haka? Kamar wata jinsin larabawa masu masifan kyaunnan, ita kanta saida tayi k'ok'ari wurin gane kanta, Maganar da Yasseer ke faɗa mata kullum itace ta faɗo mata a rai.
"Saude ke mai kyau ce" jin maganarshi kawai take a matsayin yabo, ko kuma yana faɗi don ya sakata farin ciki, inama ace yau yana tare da ita yaga yanda Saudenshi ta koma? Tsananta tunaninshi da tayi ne kawai hawaye suka fara zuba a idanunta.
Aunty Nainah ce ta dafa kafaɗarta "Yadai Saude?" share hawayenta tayi duk da bata iya ɓoye damuwan dake fuskarta ba,
"Ba komai Aunty, Na gode miki sosai"
"Bani badai, Najib shiya biyamu kuɗaɗe da yawa donmu muki gyarannan, bansan yanda kuke dashi ba, anma Allah yasa yana da muhimmanci a gurinki kamar yanda kike wurinshi"
Maganarta taa ɗaure mata kai, harma ta rasa me zata ce mata, hannunta ta sake rik'ewa.
"Muje yana jiranki tun ɗazu" suka tafi har kusa da wurin ta rakata, sannan ta mata bankwana don tafiso ta k'arasa ita kaɗai.
Shi kaɗai harya gaji da jira, anma bai nuna alaman k'osawa ba, ta daɗe a tsaye, bai buɗe ba hankalinshi ma sam bai kanta, ta saka hannu taɗan k'wank'wasa k'ofan, sauke glass ɗin yayi kaɗan, ya kalleta yana sauraren k'arin bayani.
"Daman an gama ne" tace tana wasa da yatsun hannunta, ya taɓe baki donshi tsakaninshi da Allah bai ganeta ba.
"an gama me?"
"Aunty Nainah ce ta rakoni" sannan ya ɗaga kanshi yana kallonta sosai, donshi ko kallan mata bai cika yi ba, sai kuma ya ware ido bakinshi ɗauke da murmushi.
"Saude??" ta saka hannu biyu ta rufe fuskanta tana daria, "Naam" ai saiya buɗe mota ya fito, hannu ya saka ya janye mata hannun data rufe fuska dashi, yana k'arema kyakkyawar fuskarta kallo.
"I cant believe dis Saude kece kika koma haka?" dariya kawai take, ya ɗaura hannunshi saman kafaɗarta.
"Kinyi kyau, kinyi kyau Saude, ke mai kyauce"
Gabanta ne yayi mummunar faɗuwa, duk fara'ar da take ta kauce saboda k'ara tuna mata Yasseer da yayi, ta kalli kafaɗarta inda ya ɗaura hannunshi, ya ɗauka abunda ya ɓata mata rai kenan da saurinshi ya janye.
"Meya faru kuma?"
"ba komai" ta k'ak'aro murmushi, yace "Selfie?" yana ɗaga mata gira cikin wani irin salo mai burgewa.
Batasan me yake nufi ba, sai dai ya janyo waya, kusa da ita ya tsaya anma bai taɓata ba, ya dinga musu pics masu kyau, sannan itama ya mata, mutane sai kallansu suke ba k'aramin burgewa sukai ba,
Daganan wani k'aton boutique ya kaita, ya dinga jidar mata dogayen riguna masu kyau da masu wando, harda kayan barci duk wanda ya burgeshi ɗauka yake ya zuba kawai, kamar mai shirin buɗe kanti, kuɗi masu yawa taga ya zaro ya mik'a.
Basu gama ba har dare yana yawo da ita, wuraren shak'atawa ya dinga kaita, sunsha yawo sosai, wani iri takejin ranar daban da sauran ranakun da tayi a baya, duk da ba wani magana suke a tsakaninsu ba, shi miskili ita kuma sarkin kunya, saima ta maida fuskarta gefe tana shak'ar sanyayyar iska da yake glass ɗin a sauke yake, wani irin farin ciki na k'ara shigarta, ga wani kiɗa mai taushi dake tashi.
Kaɗan kaɗan zata waiwaya ta kalleshi, tanason mishi magana anma kunyarshi taa hana, hankalinshi gaba ɗaya yanakan tuk'i, shima wani irin nishaɗi yake ciki, wak'ar koredo bello ne yake bi a bakinshi kamar shine ya rairata, yana lura da duk wani motsinta.
"Ina zamuje?" ta tambayeshi cikin fargaba, batasanma yaji ba saida ya bata amsa,
"Gida, ko akwai inda kikeson zuwa?"
Ta k'ara k'asa da kanta tana wasa da hannunta, kallonta yake anma tak'i magana.
"kinyi shiru, karki goge zanen lallen mana"
Da sauri ta ɓoye hannunta tana dariya, "Daman..." kuma sai tayi shiru.
"ehen..."
"Zamuje gidan Aunty Husna?"
"Me zakiyo?"
"ba komai"
Ya duk'o da kanshi yana kallon fuskarta,
"zaki nuna mata kwalliyar ne?" ta girgiza kai duk ta takure jikin k'ofa, shi kuma ya wani shige mata.
"eeh mana kedai faɗamun" wani irin zaro ido tayi tana nuna mishi gabanshi,
"Gabanka yaya Najib" da sauri ya koma kan tuk'unshi baiga komai ba, ya kalleta sai dariya take mishi.
Ya ɓata rai "kekoh" itama duk saita marairaice fuska ta ɗauka haushi yaji.
"yi hak'uri"
Sai sannan shima ya fara dariya sosae, "kinfi kyau a haka" kallonshi kawai take.
Mutum mai faɗa da birkitaccen hali idan baka fahimceshi ba, anma mai sauk'in kai da son mutane, ga wanda suka zauna dashi, ya iya zama da mutane sosae ba tare da yaa ɓata musu ba, matsalanshi kawai kar a mishi katsalandan.
Sanda suka isa gidan har Momie ta dawo tana shirin kwanciya, suka shiga ɗakin da kaya niki-niki, ba k'aramin daɗi taji ganin Saude a haka ba, ta dinga saka musu albarka, ita da kanta ta dinga mishi godia, ta mishi addu'ah sosae.
Shiya ɗaukarma Saude kayan har ɗakinta, tana tsaye jikin madubi don bata gajia da kallon kanta, sai murmushi take ita kaɗai, daga bayanta ya tsaya tana kallonshi ta cikin madubin, sai kuma taji kunya da sauri ta rufe idanunta.
Saitin kunnanta yake mata magana "bansan me nake tunani ba Saude, anma yau ranace ta musanman a gareni, naji daɗin kasancewarki cikin farin ciki" yasan bazatayi magana ba, yana gama faɗa ya fita sannan ta buɗe idanunta,
"Nagode sosai ta sabuwar rayuwarnan daka bani Yaya Najib" ta faɗa kamar yanajinta, bayan taji fitarshi
©Rabiatu sk msh
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
59
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Ranar Monday kenan washe gari da wuri ta farka, barcinta kaɗanne, ta kasa mantawa da abubuwan da suka faru, kayanda ya kawo mata ta dinga ɗagawa tana gani, taji daɗinsu sosae.
Tunawa tayi da yau fa zai koma, gashi har rana tayi k'ilama ya tafi, dirowa tayi daga saman gadon tayi hanyar ɗakin Momie, tama manta da riga da wandon kayan barci ne a jikinta, tana sauri ta koma ta saka hijabi sannan ta tafi.
Da yake sauri take saida ta faɗa ciki ma sannan tayi sallama yana Zaune da Momie suna magana, shima jallabiyace a jikinshi da alama ko shirin tafiya baiyi ba.
Kasa magana tayi tana tsaye dai tana kallonshi, komai ya sakama kyau yake mishi, idan ta ganshi cikin k'ananan kaya saita ɗauka duk sunfi mishi kyau, idanta ganshi a manyan kaya ma haka, yau da ta ganshi da jallabiya ma ba k'aramin kyau ya mata ba, ta manta ma da Momie a wurin. Saida ta tuna a kunyace ta gaisheta, tace
"kinyi mamakin ganin yayanki bai koma ba ko?"
"eeh Momie, meyasa?"
"saboda ke" ya riga momie bata amsa, waro ido tayi tana daria, sannan ta kalla Momie.
Ɗaga mata kai tayi "nima dai haka yacemun"
"Daddy so yake ya sakaki a makaranta, kinason karatu?"
"eeh inaso sosae"
"Yauwa ki shirya yanzu ya kaiki, daman a garinku ai kina makaranta ko?"
"A'ah banyi nisa ba, anma dai...." kuma sai tayi shiru idanunta ya kawo k'walla.
Momie cikin tausayawa tace "kawu Ado ko?"
Girgiza kai tayi, "Mijina dai yana koyamun a gida"
"ki daina kuka Saude idan kin tunashi, addu'ah zakina mishi, abinda mamaci ke buk'ata kenan"
Share hawayenta tayi "Insha Allah Momie" Najib tashi yayi ya fita kawai, Momie tace "tohh yi sauri kije ki shirya, sai kizo ki break fast"
Da wuri suka isa makarantar, tsadajjiyar makaranta ce a garin Abuja, sai yaran wane ne ke a ckul ɗin, akwai ɓangaren nursery, primary, junior and senior secondry ckul. Kai tsaye ɓangaren shugaban k'aramar makarantar suka wuce (junior), cikin girmamawa ya amshesu, bayan sun gaisa Najib ya mishi bayanin daya kawosu.
Kallon saude yayi ta cikin gilashin daya saka, "what's ur name?"
"My name is Saude" ta bashi amsa cikin wani dadaɗan turanci kamar wata baturiya, yaci gaba da mata en k'ananun tambayoyi na en primary duk kusan taa haye, na sec ɗin daine take cewa batasan wannan ba, wanda ta sani kuma ta bashi amsa.
"congratulations Mr. Zamu ɗauka Saude a aji uku (J.s3) duk da yayi mata girma, anma nasan insha Allah karatun bazai mata wahala ba don da alama tana ganewa, sai dai kuma a samu wanda zaina koya mata a gida"
"Insha Allah, wannan ba damuwa bane, nagode sosae"
"jin daɗinmu ne"
"Saude wa za'a rubuta mata jikin admission ɗin?"
Kallonta yayi, "ya sunan babanki?"
"Saude Yasseer za'a sakamun"
Yamutsa fuska yayi, "Yasseer ba sunan baban Hafsat bane?" ta ɗaga mishi kai, wani irin haushinta yaji, cikin muryar ɓacin rai yace,
"sunan babanki nace ki faɗamun" duk sai taji ba daɗi da yanayinshi ya canja,
"Muhammad"
"Saudat Muhammad za'a saka mata" saida ya tabbatar an gama mata komai daya dace, ya biya kudaɗe da yawa, sannan suka tafi ko kallan inda take baiyi, wani irin haushinta yakeji. Anan ckul ɗin aka bata unifoam da littafai, suka wuce gida washe gari zata fara zuwa.
Har sukaje gida yana fushi da ita, yanayin parking da sauri ta buɗe ta fita, don karma ta k'ara ɓata mishi rai, sauri take taa kusan shiga ɗakinta taji taji ya kira sunanta.
"Saudat!!" saida ko ina ya amsa sunan cikin kanta, har k'asan zuciyarta takejinshi da kuma yanayin daya faɗa, bata taɓa sanin haka sunanta yake da daɗi ba sai yau daya k'ayatar dashi, saida ta rumtse ido tama kasa juyawa, ta kasa ci gaba da tafiya sai dai ta tsaya wuri ɗaya.
"Saudat!" ya k'ara kiran sunanta, still dai bata waiwaya ba, ya ɗanyi tafiya gab da inda take, magana yake mata yanda ita kaɗai zataji.
"Yau zan tafi, ko kaɗanne kina sakani cikin tunaninki, plz a sanmin wurinda za'a dinga tunawa dani cikin inda ake tuna baban Hafsat"
Jinshi gaf da ita ya saka ta jawo mayafinta ta rufe fuska, ta kasa bashi amsa tana jiran ya tafi, zagayawa yayi inda take yana lek'en fuskarta ta cikin mayafin da sauri da rufe wurin, ya juya ɗaya bangaren nanma ta rufe, haka suka dingayi saida taji kamar ya tafi ta buɗe fuska, da sauri ta zaro ido data ganshi gaf da ita.
"Zan tafi ko damuwa bazaki ba ko?" girgiza mishi kai tayi,
"banda amsa ko?" shiru ya juya zai tafi, a hankali tace "Yaya Najib" ya juyo yana kallonta, "Allah ya dawo dakai lafiya"
Ya sakar mata murmushi, "Ameen".
A ranar ya wuce kaduna, bayan ya tabbatar da ya samar mata mai lesson da drivern dazai kaita ya ɗaukota.
Page ɗin yau yayi kaɗan na sani, plz kumin uzuri donma banso ku jini shirune, na gaisheda duk wani Masoyan littafinnan, k'aunarku da nake batta da iyaka❤
©Rabiatu sk msh
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
60
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Su Saude, Aww Saudat😄 anci gaba da zuwa makaranta, kullum mai mata lesson yana zuwa bata gajia da karatu, tanason ckul d'inta sosai, a can kowa so take tayi k'awance da ita, gashi ba iya shiga mutane tayi ba ko k'awar kirkima bata da ita.
Ahmad ne rik'e da wayar Najib hannunshi yana kallon hoto duk ya yamutsa fuska, hotan Saude yake gani wanda tana er k'yauyentane sosai.
"Waida wannan ce Sauden? Gaskia Abokina ka badani, haba idan kana cemun er k'yauyece duk ban d'auka taakai haka ba, gaskia wannan bata dace dakai ba, inaa wannan in mukazo biki ma ai sai abokanmu suna mana dariya"
Yana cikin maganganunshi, Najib ya gano mishi wanda tayi a er birninta,
"Tohm ga Saudat kuma"
"wacece Saudat d'in?"
"Gani da kanka"
"wow Aboki, wannan irin had'uwa haka, ashe daman abunda ka dad'e kana b'oyemun kenan, kullum maganarka baka tashi soyayya yanzu ba, ashe kasan tanajin da kayi, ita kuma wannan ina ka samota?"
"Saude ce"
Coffee daya kurb'ane a bakinshi ya furzar dashi har yana k'warewa,
"Saudence ta koma haka?" ya d'aga mishi kai fuskarshi d'auke da murmushi.
Hotanta na k'yauye da wannan ya ringa comparing, donshi duk bai yarda ba, ya ringa kallon hotan.
"Kai Matan Aurece fa kake mata irin wannan kallon"
"hhh ni kuma abokin mijinta ne"
"wallahi ita d'ince fa, gashinan komai iri d'aya, sai yanzu na lura ana k'yauyenma ashe kyaune da ita sosae, kai Aboki kaayi babban kamu fa, ashe akwai abinda ka gano a bazawarar er k'yauyennan"
"Kaa cika surutu"
"aina kasa tsaida maganata ne, plz indai kaa fasa by any chance, let me know"
"Kayi me dan U***ka, kaifa Namamajo ne"
"Indai na samu kamar wannan aina daina kula kowacce mace, nasan kana son Saudat, anma dai zan k'ara fad'a maka ka rik'eta amana, karka cutar da zuciyarta ta kowanne hanya"
"ina son Saude da yawa Aboki, Soyayyar da ko kaina banayi mawa, ko wani ya b'ata mata rai sai nawa yafi b'aci, Soyayyarta bazata tab'a bari na mata wani abu da zataji ba dad'i ba, Idan harna rasa Saude bani da sauran jin dad'in rayuwa, ita na fara so, kuma da ita nake burin k'are rayuwatah".
"Allah yasa ta soka kamar yanda kakesonta, sai yaushene zaka fad'a mata?"
"saita fara sona"
MOSCOW
Yasseer ne kwance yana barcin rana, wani irin mafarkin Saude yake mai razanarwa, a firgice ya farka yana fad'in.
"MATATAH CE! MATATAH CE!! MATATAH CE!!!" duk ya Had'a zufa don ba k'aramin firgita yayi da mafarkin ba, ada idan yana mafarkin Saude cikin kuka take zo mishi tana neman taimakonshi, anma yanzu cikin farin ciki yake ganinta wani na neman k'wace mishi ita.
Ana gobe zasu tafi moscow saida yaje k'yauyensu Saude cikin dare ya isa da niyyar da safe zai d'aukota ya maida birni ko bada sanin danginshi ba, baije gidan ba saida safe don yaga kalan murnar da zatayi idanta ganshi, sai kuma ya had'u da bak'in labari wai a safiyarnan tabar garin, yasha nemanta harya gaji, ya hak'ura dai ya koma gida kuma a ranar yabar k'asar da maraice, ita kuma a daren ta isa gidansu Yasseer d'in.
Ta bayanshi ta kwanto tana sumbatar wuyanshi ta ko ina, rumtse hannunta yayi cikin nashi ya d'an juyo da fuskarshi yana lumshe ido, muryarta a sark'e tace "waye yace Rabi'ah ba matarka bace? Ni taka ce, sai dai ka k'ara jaddada musu"
Ta had'a bakinta da nashi tana sumbatarshi hannunta akan k'irjinshi, duk taa fara rikitashi, dak'yar yakai hannu ya shafi cikinta a kunne ya rad'a mata,
"Yaushe ne zamu sama baby? Inason yara Rabi'ah"
Buge hannunnashi tayi, "Ba yanzu ba, duka yaushene auren namu? Kuma ko ckul ban fara ba, saina gama gaskia, raino wahala"
Ya jawota jikinshi, "Plz Rabi'ah" tureshi tayi, ta mik'e zata tafi,
"Zan kawo wacce zata haifamun idan ke yana miki wahala" da sauri ta dawo tana huci, ta nunashi da yatsa
"karma ka fara, kai nawane ni kad'ai, babu macen data isa ta rabani dakai" shi dariyama take bashi idan tana nuna kishinnan,
"bazan b'oye miki ba Rabi'ah, hak'urina ya fara k'arewa, inason yara" maganar taa fara gundurarta, ta mik'e ta bashi wuri, yabi bayanta da murmushi kawai.
Rabiah rigima, matsalanshi da ita kawai rashin haihuwa, anma in akazo b'angaren abun ko gajia batayi, kuma yana samun kulawa sosae daga gareta.
Saude ce ta fad'o mishi rai da yaron cikin daya barta dashi, ko wanne hali suke ciki? Dukan k'irjinshi ya shiga yi, ko zaiji sauk'in bugawar da zuciyarshi take mishi, shi kanshi yasan bai kyauta ba, kuma kullum zuciyarshi cikin azabtuwa take da rashinta, 'Ya Allah ka nunamin Saude, da abundata haifa, ya Allah kasa tana tunawa dani kamar yacce koda yaushe take cikin tunani nah'
Tunawa yayi da Rabi'ah fa fushi tayi, yaja tsoki ita abun b'acin rai bai mata wahala, kitchen ya tafi ya sameta, ya kwanto ta bayanta.
"Me ake girka mana duk k'amshi ya cikamun hanci" tureshi tayi ba tare da tace komai ba, ya k'ara kwantotah, ta k'ara tureshi,
"Shikenan, ni daman duk sona da kike cewa nasan ba haka bane tunda kina fushi dani" ya juya kamar zai tafi, da gudu ta tafi ta fad'a mishi tana kuka.
"Plz hniee ka dainamin maganar kishiyarnan, Ina sonka da yawa karka saka zuciyatah ta fashe"
D'ago da fuskarta yayi "ke miye na kuka? Nifa wasa nake miki, banson ganin hawayennan plz" ya saka hannu ya fara share mata, tayi murmushi, "tohm kaima ka daina"
"na daina, bara inje wanka" ta d'aga mishi kai.
Suna zaune dinning ta zuba mishi abinci yanaci, cokalin farko kawai yakai tunanin Saude ne kawai ke dawo mishi, ko tana ina? Wanne hali take ciki? Ita tamaci abincin kuwa? Ji yayi bazai iya ci gaba da ci ba, a yanzu tunanin Saude duk yafi damunshi, ya ajje cokalin kawai ya tashi zai tafi, ta kalleshi duk ta marairaice fuska.
"Bazaka ci abincin ba?"
"zanci sai anjima"
"kodai bai maka dad'i ba?"
"kawai banjin ci ne" yana fad'ar haka ya wuce zuwa d'akinshi, har dare baida wani sukuni, baima k'ara fita ba a ranar, da wuri yayi shirin barci ya kwanta.
Saida ta gama duk abunda take ta shigo d'akin, ta kunne haske idonshi biyu anma da alama tunani yake, ta kashe sannan itama ta haye gadon, shiru bataji ya tanka mata ba kamar baisan da shigowarta ba, ta matsa inda yake ta saka hannu ta fara yawo dashi wurin wuyanshi, jin bai hanata ba ya sanyata komawa samanshi wani fitinannan kiss da dinga binshi dashi, tana aika mishi sak'onni, anma ko motsi baiyi ba, ita kad'ai ke kid'inta da rawarta, wani irin haushinshi taji, takai mishi duka a k'irji.
"koba komai ai saika fad'amun u're not in d mood" jin baiyi magana ba ta k'ara kai mishi wani dukan, ko a jikinshi, tashi tayi ma tabar mishi d'akin.
"Plz Saude ki dawo rayuwatah hakanan, kece farin ciki na"
Yau da gobe a kwana a tashi su Saudat har lokacin fara jarawa (J.S.C.E/J.L.S) yayi, kullum bata da lokaci saina karatu, bataso ta bama Najib kunya, sai dai kuma yawan tunani dake damunta, kullum cikin tunani.
Ranar laraba suka fara exam, tunda wuri take shiri bayan ta gama duk aikin da zatayi, cikin hanzari ta shirya ta tafi makarantar, lokacin da taje har an shiga, ta ajje littafinta harta tafi ta dawo ta k'ara dubawa sannan ta tafi da gudu ta shiga, malamin dake dubasu ne ya tsayar da ita.
"Saudat muhammad! Sai yanzu kike zuwa exam d'in don baki d'auketa serious ba?"
"M srry sir" ta tafi zata wuce sumi-sumi, ya k'ara kiranta.
"ki jira anan, yanda bakizo da wuri ba bazaki fara da wuri ba" idonta kamar zatayi kuka tace "pls sir" hannunshi ya d'aura saman bakinshi, sannan ya nuna mata inda zata tsaya, duk ranta ba dad'i.
Saida suka dad'e da farawa sannan ya mata alamar taje ta zauna, cikin dubara ta share hawayenta taje ta zauna, lokacin daya rage baida yawa, aka mik'a mata question paper ta fara dubawa, amsar data sani baida yawa a ciki nanta fara k'ok'arin tuna hardar da tayi anma kamar wacce akama satar k'walwa, komai ta kasa tunawa, bata rubuta komai a takardarta ba har aka amsa takardar, tun anan ta fara kuka.
Da gudu ta shiga falon Momie ta tare ta,
"Lafiyanki?"
Ta duk'e gabanta tana wani irin kuka, Momie ta dafa kafad'arta tana lallashinta,
"meya faru dake a makarantarne, kukanme kike?"
Ta k'ara fashewa da kuka,
"Nayi karatu Momie, wallahi nayi karatu sosai"
"ni kaina shaidace, fad'amun meya faru?"
Cikin kuka ta bata labarin duk abunda ya faru a wurin exam, sannan ta k'ara da cewa "wallahi nayi karatu momie"
"ki kwantar da hankalinki kinji, yanzu yaushene zaku k'ara wata?"
"friday"
"kinga kina da lokacin karatu sosai, ki daina damuwa nasan zaki iya, nasan bazaki bamu kunya ba"
Ita dai duk hankalinta bai kwanta ba, ta tashi d'akinta tana kuka.
Da Najib ya kira waya Momie ta fad'a mishi, yace a bama Saude wayar, shima kuka kawai ta saka mishi ya ringa lallashinta dak'yar ya samu tayi shiru, sannan ya tambayeta,
"Baki gane lesson d'in da ake miki ne?"
"nifa nayi karatu, komai saida na hardace ina zuwa na manta"
"nasan kinyi karatu, anma daman waya kaiki harda? Indai kika maida hankali kika gane basaikin harda ba kinji ko"
"tohm"
"Yauwah zan dawo gobe, sai in tayaki karatun"
Sannan tayi dariya, "Da gaske gobe zaka dawo?"
"ai naji ko murna bakiyi, nama fasa"
"A'ah dad'inne har yamun yawa, Allah ya kawoka lafiya"
"Ameen k'anwata"
"Ina Hafsat?"
"ta tafi tahfiz"
"tohm bani labari"
"labarin me?"
"komai ma, bani na kanki dai, yau me kika saka? Nasan kinyi kyau sosae"
"umm"
"umm kuma? Fad'amun zakiyi" Momie ta kalla, ba kallonta take ba anma tasan da tayi magana zataji.
"mezan girka maka gobe?"
"kunyar Momie ta hanaki bani amsa ko? Ni saikin fad'amun"
Tashi tayi daga d'akin Momien sukaci gaba da waya, bai k'yaleta ba saida ya tabbatar hankalinta ya kwanta bata da sauran damu, sannan ya yarda ta ajje wayar.
©Rabiatu sk msh
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
61
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Kamar yanda ya mata alk'awari, goben nayi sai gashi da wuri, tayi murna sosae da ganinshi saboda ba k'aramin kewanshi tayi ba, yanzu akwai shak'uwa sosae a tsakaninsu. Abinci kawai ta barshi yaci ta kwaso littafanta ta zube mishi.
Cikin sauk'i yanda zata gane ya dinga mata bayani, ba k'aramin burgeta yayi ba yanda yake mata bayani daya bayan daya, rik'e take da littafin anma shi kawai take kallo hankalinta ma ba saurarenshi take ba, saida taji yayi shiru tace "Kayi shiru"
"kina kallona ne"
"sorry na daina"
Yaci gaba da koya mata sosae takejin dadin karatun, Sallah kawai ke tadasu, saida ya tabbatar ta gane sannan ya barta taci gaba da karatun inda bata gane ba ta tambayeshi, har dare ko motsin kirki batasonyi, ta saka littafi tana ta karatu ko abinci tak'i taci.
"wai bakyajin barci?"
"zan kwanta, gobe fa ne exam d'in"
"tohm ai karatun ya isa haka, ga abincinki tun d'azu kink'i kici"
"ni nafa k'oshi ma, ka barni in k'arasa karatunnan plz Yaya Najib"
"me? Tun dawowa na banga kinci abinci ba, ajje karatunnan hakanan" rufe idanunta tayi tana maimaita abunda ta karanto, ya taso zai k'wace littafin, da gudu ta canja kujera, haka suka ringa zagaye falon tak'i yarda ya ansa littafin, tana gudu tana karatunta, saida ya gaji ya tsaya.
Sannan ta zauna, ya d'aukar mata abincin har inda take, ta wani marairaice.
"Plz ka barni inyi karatunnan"
"ai ban hanaki ba," ya deb'o a cokali, ya nufi bakinta dashi.
"bud'a bakin" ta waro kyawawan idanunta, ya d'aga mata kai, kwantar da kanta tayi tana girgazashi, ya d'an rausayar da kanshi yana mata alamar eeh da idanunshi,
Littafin ta saka ta kare fuskarta, ya sunkuyo ta k'asan littafin, babu yanda ta iya ta bud'a mishi ya bata a baki, "ko kefa, dana hana karatun exam d'innan" tak'i ma kallonshi taci gaba da karatunta, a haka yake bata abincin.
Suna cikin ci ta bud'a baki zai bata kawai taji babu komai ta tauna cokali, ya kyalkyale mata da daria, ta aje littafin duk ta b'ata rai tana harararshi, sai dariya yake.
"nama fasa cin abinci"
"Sorry na daina"
"nidai bazanci ba tunda hakane"
"da gaske bazan k'ara ba" ya rik'e kunnuwanshi da hannayenshi biyu, sannan ta hak'ura yaci gaba da bata, saida ta kusan k'oshi duk hankalinta na kan littafi, taji ya cika mata baki da abinci, batasan sanda ta saka littafin ba ta fara dukanshi, shikam dariyarshi kawai yake.
"kaje ka kwanta dukka hanani karatuna"
"nak'i, tare zamu kwanta"
"ni ba yanzu ba"
Ya ware hannuwanshi, "nima haka" ya k'aro wani abincin zai bata, ta girgiza kai, "ni bazan k'ara ansa da cokali ba, da hannunka zaka bani" ya fad'ad'a fara'arshi harda nad'e hannun riga.
"shi yafi komai sauk'i" tana mishi dariyar mugunta, yana saka mata hannun ta cijeshi, da sauri ya janye yana k'ara, ta mik'e da gudu tabar wurin tana mishi daria.
"Saida safe"
Haka suke karatun kullum cikin nishad'i, idan tana tare dashi mantawa ma take da wani auren Yasseer dake kanta, duk wani damuwarta kaucewa take ta bata wuri, kullum bata da wani buri daya wuce zama da Najib, idan tana tuna zamansu da Yasseer da ko abinci bata iya ci a ganshi, idan yana d'aki ita zata tsaya a wajene ko nesa dashi, bai jata a jikinshi ya nuna mata abunda yakeso ba, bai koyar da ita kalan soyayyar birni ba ballantana ta mishi a matsayinshi na mijinta, soyayyar kwanciyar aure kawai ya koyar mata yanda zata mishi, da kuma soyayyarshi daya gina a zuciyarta ya tafi ya barta da k'aton tabo, zaman shekara biyu tayi da kwanaki a k'yauye ba tare da yaa nemeta ba, kuma shine yasan inda take, ya manta da jaririn cikin daya tafi ya barta dashi, da kuma igiyoyin aurenshi dake kanta.
Idan ta zauna ita kad'aine take tunawa dashi, sai dai tayi ta sharan k'walla kawai, bada son ranta take kuka ba idanta tunashi, don batason bama zuciyarta dalilin da zataji haushinshi, domin shine mutum na farko daya fara nuna mata soyayya da kulawa a rayuwa, shine mutum na farko daya nuna tausayinshi a kanta, ta dad'e tana mishi uzurin butulcin daya mata kasancewarshi d'an adam kuma ajizi.
K'aran dukan k'ofan Najib ne ya fito da ita daga d'akin,
"wai ko shirin exam d'in bakiyi ba? Halan har yanzu karatun kike"
"A'ah unifoam kawai zan saka"
"tohm ina jiranki" har ya juya kuma ya dawo, "kuka kikayi ko?" girgiza mishi kai tayi, "ki fad'amun gaskia"
"Da gaske ba kuka nayi ba"
"tohm kije ki shirya" ta juya zata tafi, ya k'ara tsayar da ita "Saudat!" cak ta tsaya,
"bansan meye damuwarki ba, anma ina jinta har cikin zuciyatah, kullum burina ki kasance cikin farin ciki, bazan tab'a bari kiyi kuka ba inda muna tare," kai kawai ta d'aga mishi, tana toshe baki ta shige d'akinta da gudu,
Tana shiga toilet ta k'ara fashewa da kuka, “shima haka yace, 'kindaina kuka indai muna tare, hawayen farin ciki kawai nakeson gani a fuskarki (Yasseer)' yanzu gashi ya tafi yaa barni, banda wani dalilin kuka yanzu bayanshi, shine kawai silar damuwatah!!
Cikin lokaci kad'an ta gama shiryawa ta fito, ko littafi ma bata d'auka ba, daa ko toilet zataje da littafi, ko brush take tanayi tana dubawa har dare ya raba tana karatu, anma yanzu yaa zauna mata, data amsa question paper lokaci kad'an ta gama rubuce ta, ko wani abu ya shige mata saita tuna da lokacin da Najib ke koya mata muryarshi na dawo mata yanda yake koya mata cikin k'warewa duk yanda zata gane. Shi yake kaita exam ya d'aukota ko wurin aikinma yak'i komawa sai dai yaje ya dawo, Momie har fad'an batason zaryarnan take mishi, sai dai ya bata hak'uri ta barshi na sati d'ayane kawai.
Gobe zata gama exam d'inta, suna d'akin Momie ita har Najib d'in, wayanta ta d'auka tana kiran wani layi, da yake hankalinta nakan karatu bataji mai take cewa ba saida ta gama ta fara fad'a.
"Yau naaga d'an banzan yaro, kai shikenan baka da lokacin danginka baka dana Mahaifiyarka, kullum kai aiki dai, matarka dai"
Najib yace "Momie broz ne?"
"shi mana, shikenan kullum aka mishi waya sai yace yana busy zai kira, kuma shi bazai d'auka waya ya kira mutane ba, ya kwashi mata sun tafi k'asar turawa ya manta damunan, barni dashi azuminnan yazo bai dawo gida"
"Momie broz Yasseer ya kusan dawowa?"
"ai dolenshi ma ya dawo, shekaranshi nawa a can? Azumi saura wata d'aya na fad'a mishi su dawo anan za'a fara dasu, idan kunyi waya dashi ka k'ara jaddada mishi don ba k'aramin sab'a mishi zan ba ya wuce lokaci"
"an gama momie, gaskia nayi murna da dawowarshi sosai" shi yake murnarshi, anma Momie fad'anta taci gaba dayi, ita dai Saude iyakarta saurare, ita dai ko son ganin Yasseer d'in Momien ma batayi, don tuni mai irin sunanshi ya gama b'ata damarshi a wurinta, anma dai ta lura gidan suna sonshi, Najib ma yana yawan mata firarshi.
Ranar da zata gama exam, Najib zai kaita ckul, suna hanyarsu ta zuwa sai firarsu suke cikin nishad'i, yace "yau zaki gama junior ckul d'in, akwai maganar dazan fad'a miki anma saikin fito exam".
"tohm shikenan kaimun addu'ah in fito lafiya"
"Ameen dear, best ov luck"
Tayi murmushi "tnx" sukaci gaba da firansu har suka isa.
©Rabiatu sk msh
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
62
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Sun gama exam suka fito, anata bankwana kamar an tafi kenan, wasu nata hotuna, itama ta d'auko wayanta Iphone7 da Najib ya bata aro don kawai tayi pictures, nan aka dinga zuwa aro kowa sai so yake tayi dashi, daga k'arshe ma ta bar musu suyi kawai. Tana tsaye gefe wata class mate d'inta tazo inda take.
"Alhmdlh! Saudat muhammad Allah ya taimakeni baki tafi ba"
"tohh Allah yasa dai lafiya"
"Da sauk'i dai, tunda ciwon daga zuciyatah ne, number Yayannan namu nakeso ki bani"
"Yayanmu kuma? Wa kenan?" ta tambayeta kamar bata gane.
"Plz ki gane mana, wannan kyakkyawan dake kawoki makaranta yanzu"
"Yaya Najib ne yake kawoni, karma in tsaidake ni bani da waya"
"haba wancan Iphone d'in fa? Nifa numbershi kawai zaki bani"
"tashi ce ba tawa ba"
"Yazo da sauk'i, sai ma in saka mishi tawa, in kira inga numbern"
"ke babu fa simcard a ciki"
"Yau ni ya zanyi? Ki jirani plz ina zuwa" ta tafi da gudu tabar wurin, Saude ta bita da kallo tana tab'e baki, tana daina ganinta ta amsa wayarta tasan yana can yana jiranta, ta kusan kaiwa wurinshi sai gata ta dawo da gudu, tana kawowa inda take ta fara tafiyar yanga.
Takarda ta mik'a mata
"plz ki kai mishi" hannu kawai tasa ta amsa, sannan ta wuce tana mata godia, duk taa b'ata rai ta shiga motan. Saida ya tada ta mik'a mishi.
"Ga sak'onka fa"
"Sak'ona kuma?"
"wata er class d'inmu tace in kawo maka"
"Shiyasa kike ta b'ata rai kenan?"
Harararshi tayi, "Meye na b'ata rai kuma daga sak'o? Ni gajia nayi"
"tohh yarda ta"
"me? Ai tunda na amso saika karanta ta"
"nikam bazan amsa ba, ki d'auka in kina so"
"inaso mana, bara ma in karanta" ta bud'eta ta fara karanta.
“zuwa ga kyakkyawan saurayin da yafi kowanne namiji kyau a doron k'asa”
Ta k'yalk'yale da daria "wao!"
"ke ita ta rubuta hakan?"
“bansan meke faruwa dani ba aduk lokacin dana ganka, zuciyatah sai ta dinga bugawa da sauri, dole akwai wani abu na musanman tattare dakai dake sanyani jin hakan a koda yaushe"
"Ciwon zuciyah ne da ita"
Saude ta k'ara tuntsirewa da daria, "Sirrin zuciyah dai"
Tana dariya taci gaba da karantowa
“bana tunanin komai sai naka a kullum, ko yaushe cikin tunaninka nake ko abinci bana iya ci”
"taje asibiti kota nema maganin zafi"
"ba wani Asibiti, kai dai..."
"me kikace?" ya amsa takardar ya cukuikuye ya jefar da ita, "komai saikin karanta kenan? Cikin jin dad'i har wani daria kike"
"kaifa ka bani ya zaka anshe?" ta fad'a cikin dariyar.
"ni ba ruwana da wani er ajinku,"
"tohm shikenan na daina, saura maganar da kace zamuyi"
"aina d'auka kin manta" ya jawo wata linkakkiyar takarda a hannunshi ya mik'a mata.
"naga yau karatu kikeji, ki karanta wannan ma duk abinda zan fad'a miki yana rubuce a ciki"
Ta amsa ta fara karantawa a fili.
“You are so funny, you are so nice,
You are the girl with whom I fell in love twice.
The first time was love at first sight,
The second time I feel for you was when I got to know you,
I realized that this was love, because the feeling was completely new.
I will never ever let you go away and leave me.
I will hold your hand and stand by you forever,
I will always be your Man, will leave you never!
I love you today and for always!”
Tana fara karantawa ta daina fad'a a fili, ya kalleta yana d'auke da wani murmushin dake tafe da wasu sak'onnin, "nasan dai yanzu kin gama karantawa, abunda ke zuciyatah ne na fad'a miki, ina fatan zuciyarki zatayi maraba dani.
Bai lura da yanayin data shigane tun sanda ta fara karantawa, gaba d'aya ta shiga tashin hankali, anya kuwa abunda takeyi dai-dai ne? Itafa matar aurece tayama zata fara tarayya da wani? Anya ta kyautawa Najib kuwa data b'oye mishi mijinta yana a raye?
"Ina saurarenki, Allah yasa ba lokaci zakice in baki ba, domin kuwa nayi hak'uri da yawa, bazan iya jure lokacin da zaki d'auka kina tunani ba, idan har kina sona, baki buk'atar nazari akai, ki fad'amun abunda ke zuciyarki game dani, plz ki fad'amun da sauri Saudat"
Kamar yasan abun da zata nema kenan a wurinshi, lokacin da zatayi tunani, idan har tace batason Najib tohh tayi babbar k'arya a rayuwarta, bata da wani buri yanzu saina kasancewa dashi, anma idanta amincema soyayyarshi anya kuwa taa kyautawa auren dake kanta? Wata zuciyarce ke mata tuni da cewa wanne irin auren? Yanzu k'ilama ya gama mantawa dake, ke kad'aice kika damu dashi, ki manta da Yasseer kiyi sabuwar rayuwar dake jiranki a gaba.
Ba tare da wani dogon nazari ba, itama takarda ta samu mai kyau ta tsara mishi rubuta ta ninketa sannan ta bashi, murmushi yayi a motan ya bud'e ya fara karantawa shima a fili, lokacin yayi parking, ta bud'e da gudu ta fita.
“You make me feel so special every time. There is not a single moment when I am with you and I don't smile. So many lovely moments with you and so many memories that we make is all imprinted in my heart. I am so lucky that I have someone like you in my life. I love you a lot”
Yana gama karantawa yayi murmushin jin dad'i har saida ya sumbaci takardar. Daganan nasu labarin soyayyar ya fara.
Tun daga ranar gaba d'aya Saude ta manta da Yasseer a rayuwarta ko tunashi ma ta dainayi, soyayya suke ma junansu fiye da kowanne Masoya, Momie idan tana ganinsu a haka ba k'aramin dad'i takeji ba, babu inda Najib ke kunyar nunama Saude soyayya, ko yaushe yana tare da ita, kulawa ta musammam yake bata, shiyasa gaba d'aya ta manta da duk wata damuwarta.
Yanzu tashin hankalinta d'aya Momie tace bayan Sallah zasuje k'yauyensu ayi maganar aurensu da Najib, gaba d'aya damuwarta yanzu idan Momie taje k'yauyen aka fad'a mata cewar itafa matar aurece, mijinta nanan da ranshi guduwa kawai yayi ya barta, a wane matsayi zasu ajeta ita da Najib?.
Watan Azumi ya kama, har yayi tsakiya babu Yasseer, Momie gaba d'aya tayi fushi dashi ko kiranshi ta daina d'agawa, kullum cikin yima Najib waya yake ya tayashi bata hak'uri.
Masoyan guda biyu Saude da Yasseer, kullum suna tare, idan ya farka zaiyi sallar tsakar dare saiya buga mata k'ofa ya tasheta, kullum asuba a falo suke zama yana k'ara mata karatun Qur'ani, shiya zama malaminta a b'angaren addini ma, yana k'ara mata sani akan sauran littafan, idan kuma suka tashi soyayyarsu sunfi kowa iyawa.
Tare suke zuwa siyayyar sallah, komai kala d'aya yake sai musu, ko atamfane ya sai mata saiya sayi yadi kalan, kaya masu tsada ya dinga sai mata kamar baison kud'in, kowanne da takalminsu, jikka, da gyale duk kalar masu tsadar gaske, Momie ma tayi mata kayan sallah masu kyau, ita har rasa bakin godia take ga wannan mutanen.
Anata shirye-shiryen Sallah saura kwana uku, Yasseer yama Najib waya gasunan zasu baro Moscow, koda ya fad'a ma Momie bata wani yarda da gaske yake ba don tafi kowa sani k'aryarshi kullum zaizo kuma ba zuwan yake ba, sai dai d'a da mahaifi, duk da tana fushi dashi saida tasa aka shirya musu abinci kala kala, tarba dai ta musamman.
Suna sauka yayi ma Najib waya gasunan fa a tura musu driver, "Haba ina garin zakace driver, ganinan tafe yanzu bruz"
"Tohm sai kazo" daman a shirye yake yana jiran wayarshi, su Saude ma an zuba ido tanaso taga wanene wannan Yasseer d'in nasu Najib?
©Rabiatu sk msh
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
63
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
Wannan Shafin sadaukarwa ne gareku Masoya littafinnan, Hafsat rano, hafsat faruq, hafsy hafsy, fatima sidi, mrs emir, meenert, princess da kuma bilkeesu Muhammad, Nagode sosae Allah yabar k'auna😍
Jiya kunjini shiru ina can murna Momyn Muhseen taa biya mana Makka😊 lol, munyi fama da matsalan ntwk ne ban samu postn ba, Nagode sosai da kulawanku,
# One Love
www.babymsh.blogspot.com
Saude na zaune gefen Momie bayan ta aika kiranta, saiga Najib ya shigo yana fad'a mata su Yasseer sun sauka yanzu zaije ya d'aukoshi, tsayar dashi tayi.
"da yanzu zan tura Saude gidan Husna da driver, anma tunda zaka fita saika wuce da ita, anma ka hanzarta tana jira"
"Gidan Husna kuma? Me zatayi?" ya tambaya Momie cikin mamaki.
"Wai aikin azumi ta fara, taa kasa k'arasawa kaasan yanzu tayi nauyi (cikinta ya tsufa) shine zataje ta dinga tayata"
"kuma sai Saudat d'inne zata tayata dole?"
"kasanta dai batason er aiki, shiyasa ta nema taimakon k'anwarta, sauri fa zakayi taa cemun girkinta nakan wuta" ya k'ara b'ata rai duk baiso ba, "yaushene zata dawo?"
"idan ta haihu mana, nikam Daddy bansanka da haka ba"
"ai dole in damu Momie, tunda zatayi nesa dani"
Kunya ya bama Saude ta mik'e, "bara inje in had'a kayan dazan tafi dasu,
Momie ta tsayar da ita, "Daddy zai kai miki daga baya, ki d'auko mayafinki dai"
"tohh" ta tashi ta tafi, ba don yaso ba ya hak'ura ta koma gidan Husna.
A hanya suna tafiya duk sunyi shiru, ta d'an karkad'a mishi yatsunta biyu ya jiyo.
"wai bazakace komai ba?"
"Nama rasa mezance Masoyiya, tunaninah kawai yanda zanyi rayuwa koda na rabin awa ne baki a kusa dani"
"kana magana kamar wacce zata bar garin ko zata maka nisa, nasan ai duk inda nake zaka kasance tare dani"
"Hakane fa, don yanzu zama gidan Husna ya kamamu" dariya tayi, ta bud'a baki zatayi magana dai dai lokacin sun isa gidan, ya shiga da motan yayi parking harta bud'e zata fita ya kalleta.
"Sai sauri kike ki barni ko" da sauri ta d'aura hannunta saman leb'enta.
"babu wannan kalmar tsakanina dakai, ni taka ce, bazan tab'a barinka ba"
Murmushi yayi "nima duk da wasa nake miki, anma saida harshena yayi nauyin fad'a"
"Yayanmu fa yana jiranka a airpot, kayi sauri plz"
"Aww! Nifa ina tare dake mantawa da komai nake, saina dawo" tana murmushi take d'aga mishi hannu harya fice sannan ta shiga gidan.
Tayi sallama sannan ta shiga gidan, Husna na zaune falo ta baje da gani ta tara gajia, ta amsa sallamar Saude.
"Sannu Aunty Husna"
"Yauwah Aunty Saudat" ta fad'a tana tsokanarta.
"yau dai zan saka Matar yaya aiki"
"Aunty Husna zolaya ko? Yanzu dai dame zan fara? Lokaci ya kusa"
"komai yananan kitchen na fara na kasa k'arasawa"
"Tohh Aunty bara inje" tana tafiya hanyar kitchen d'in Husna ta mata magana da d'an k'arfi yanda zataji.
"Yaya Yasseer ya dawo kuwa?" saida gabanta ya buga yanda takeji kullum aka ambaci sunanshi.
"A'ah yanzu dai yaa tafi ya d'aukoshi"
"Wlhy naso aje tarbansu dani, anma dai duk jikina ba dad'i nakeji"
"Ayyah! Aikam yaronnan yazo duniya fad'a zanyi dashi tunda yana takura Auntyna"
"tohh bara Abbanshi yazo in fad'a mishi" tana dariya ta k'arasa shiga kitchen d'in, "ba ruwana fa wasa nake" itama Husna dariyan take. Ta shige kitchen ta fara aiki, ba wani mai yawa bane, kafin a kira Sallah taa kammala komai, ta wuce d'akin da Husna ta nuna mata ta zauna.
Kamar ba abunda ya faru, Momie ta tarbi su Yasseer hannu biyu sai nan-nan take dasu, Rabi'ah sai wannan shisshigema Momie take ita mai suruku, sunje bud'a bakima a kusa da ita ta zauna sai fira take mata kamar ba surukarta ba ko er kunyarnan babu. Shidai Yasseer sai d'ari-d'ari yake don yasan ya b'ata ma Momie rai da yawa, sai da ta koma d'akinta yaje ya sameta jikinshi a sanyaye, ya d'uka saman gwiwoyinshi kamar zaiyi kuka.
"Na sani ni mai laifi ne, kuyi hak'uri Momie hakan bazata sake faruwa ba, don Allah karkiyi fushi da d'anki"
"Kaga alaman ina Fushi dakai? Damuwata na rashin zuwanka gidane daman, tunda na ganka kuma sai hankalina ya kwanta, ai babu wata uwa dake fushi da d'anta" rarrafawa yayi kusa da ita cikin farin ciki ya kwantar da kanshi saman cinyarta, "Hakan bazata k'ara faruwa ba insha Allah, nagode Momie" murmushi tayi tana shafar kanshi kamar k'aramin yaro. Magana takeson mishi akan jikokinta da bataga alamansu ba, anma taa rasa ta inda zata fara mishi.
Rabi'ah ce ta shigo d'akin,
"Momie ya zaki barshi kamar k'aramun yaro? Kaifa nake jira hniee"
"Ki barni inji d'umin mahaifiyatah mana, yaushe rabon da in ganta?"
"Oh! Tohm ai bakai kad'ai keda ita ba, nima Momien tawace" ta k'arasa shigowa d'akin itama zata kwanta cinyar Momie tana musu dariya tace "Maza dai ku k'arasa er tsohuwar tun kafin jikokina suzo", cak Rabi'ah ta tsaya duk ta b'ata rai, ta d'auka wayarta dake gefen Gadon Momie.
"Yanzu zan wuce gida Momie, sai Allah ya kaimu"
Baki bud'e Momie ta bita da Kallo, "Allah ya kaimu" Yasseer ya mik'e da sauri, "Bara inje in kaita Momie" sai kuma ya lura da yanayin da take ciki.
"nima haka nake fama da ita Momie duk sanda na mata maganar haihuwa" kad'a kai kawai Momie tayi, har suka tafi.
A tsakiyar falo suka had'u da Najib ya sab'a Hafsat a kafad'arshi,
"broda sai ina?" ya juyo muryar Yasseer ya tsaya sannan ya juyo, "Gidan Husna zanje"
"Daa kuwa aron Motarka nakeso zankai Rabi'ah gida"
"tohh ai sai in d'auka wata" yana zaro mishi mukullan a aljihu, ya saka hannu ya shafi fuskar Hafsat.
"Ina kuma ka samu kyakkyawar babynnan?" da sauri ta fizge fuskarta daga hannun Yasseer,
Murmushi yayi da wasa Najib yace "Tawah ce".
"aifa da shekarun da nayi bananan sunkai shekarunta a duniya, tohm bazanyi tantama ba don kuwa komai naka ta d'auko" inji Yasseer
Najib yace "haka aketa cewa yanayinmu d'aya, shiyasa nakeji da d'iyar Momien nan, Hafsat bazaki gaida Uncle ba?"
Zumb'ura baki tayi ta kauda fuska gefe kamar ta sanshi, "Sunan Momie kuma kuke kiranta dashi ko sayawa bakuyi?"
"ai Momie ta hana a b'oye sunan"
"Mai kyau da ita, Inama kuka samota?" Najib ya bud'a baki zai bashi amsa suka jiyo muryan Rabi'ah, "Hniee kaifa nake jira" ya juya zai tafi kuma ya dawo ya mik'a mata hannu.
"Hafsat zaki rakani?" mak'ale kafad'a tayi, Najib yace "anma dai nayi Mamaki, Hafsat bata tab'a yima wani haka ba, akwaita da sakin jiki da Mutane"
"aini bak'one a gareta, zamu saba ko Hafsat? Hakanan ina son yarinyar sosae"
"ai haka take da saurin shiga rai" ya juya ya tafi. Shima wasu mukullan ya d'auko sannan suka fito, cikin irin fushinta na yara ta cema Najib, "ka fad'a mishi karya k'ara tab'ani"
Cikin mamaki yace "Sabodame Hafsat?" shiru ta mishi, har sukaje gidan yanata tambayarta tak'i ta amsa, ya k'yaleta kawai sannan ta saki jikinta. Can ta wuce cikin gidan wurinsu Husna da yake ta saba dasu sosae, har so suke tazo musu yini, Masoyan biyu kuma suna can waje ta musu shimfid'a suna fira.
Sai da dare yayi sosai basuma sani ba, har Hafsat tayi barci, sannan sukai sallama zai tafi ya ciro sabuwar waya a kwalinta ya mik'a mata, ta amsa tana murna ta bud'a, Iphone7 ce komai irin tashi, sai murna take.
"ni banmasan ta inda zan fara nuna maka farin cikina ba, babu abinda zan biyaka dashi da soyayyar da kake nunamin"
"ai kin riga da kin gamamin komai tunda kika mallakamun soyayyarki, kici gaba damun Addu'ah karna rasaki Saudat"
"bazaka rasani ba, ka kwantar da hankalinka Saudat takace"
"zai kwanta dai, anma sai sanda kika k'arasa zama tawa d'in" murmushi tayi, "ka d'aukama na zama" ta ciro wayan daga kwalinta, a kunne take da simcard d'inta,
"Allah yasa dai ka faramun saving numberka, don ita zan fara sakawa"
"Abunda na fara yi kenan ranki shi dad'e"
"gaskia nagode sosai dear" harararta yayi cikin wasa, ta rufe bakinta da hannu, "Sorry na daina, wallahi dad'ine har yamun yawa"
"Kin rik'eni da yawa, so kike Momie tace nayi dare gobe ta hanani fitowa?"
Yanda yayi maganar saida ta bata dariya sosae "Momie bazata hanaka ba" ta gano Camera a wayanta.
"first selfie?" ta kanne mishi ido, ta matsa inda yake ya duk'o zasu d'auka hotan, ya d'aura yatsanshi d'aya saman yatsanta mai d'aukan hotan, sannan suka d'auka a tare su duka suna dariya.
Sunyi kyau su dukansu, nan take ta mayar dashi wallpaper, "Haka zaiyi zamanshi" shima a wallpaper d'inshi ya maidashi, sunyi kyau sosae, ba don sunso ba sukai bankwana, sai da ta daina ganinshi, ita kuma ta shige gida tana nunama Husna wayanta.
Yana mik'a Hafsat wurin mai kula da ita, kai tsaye d'akinshi ya wuce don yasan Momie tayi barci yanzu, Yasseer harya kwanta, da yake daman d'akin nasu ne su biyu
"Big bruz harka dawo?"
"Kasan kuwa lokaci yanzu?"
"anma dai tashi zakayi ka bani labari, yau babu barci"
Girgiza kai Yasseer yayi, "So nake in kwanta da wuri, gobe da safe akwai inda nakeson zuwa"
"Haba bruz daga dawowanka? Ina zakaje kuma?"
"K'yauyen da Naje Bautan K'asa, akwai abinda na barone mai matuk'ar mahimmanci da nakeso inje in duba, abun yana raina bazan iya k'ara lokaci banje ganinshi ba"
"Tohh ka bari ka k'ara hutawa zuwa jibi sai muje tare, anma yanzu ga azumi ga gajia"
"jibi daren Sallah kenan mu dawo ranar sallah? Ba komai fa kasha zamanka, namafiso inje ni kad'ai, kai dai kamun addu'ah Allah ya bani sa'ar abinda zanje nema"
"Ameen d'an uwah, Momie dai taa barka ko?" cikin wasa yace "ai aikin lallashin ta barni zuwa nayi tun dawowatah daga gidansu Rabiah" dariya sukayi,
"Yaka baro Saudat d'in?" Yasseer ya tambayeshi
"ya akai kasan wurinta naje?"
"Momie ta fad'amun mana, ko wacce mai sa'ah ce ta iya samun zuciyar little bruz har haka?"
"Saika ganta zakasan nima mai sa'ahne sosae dana sameta"
"kana sonta da yawa gaskia"
"sosai kuwa bruz, ina sonta fiye da rayuwatah"
"gaskia naso ganin wannan Saudat d'in taka, da alama Momie ma tana ji da ita, anma ai zanje ganin Husna"
"yanzu ma bara in nuna maka hotunanta"
"karfa in ganta tafi kyau a hoto akan zahiri"
Dariya yayi "Saudat ganinta ai yafi jinta"
Folder da yake ajje hotunanta ya shiga, sannan ya mik'a mishi wayar bayan ya gano mishi hotunanta.
©Rabiatu sk msh
♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
64
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
Ta ina zan fara? Ban sani ba sis domin kuwa kalmomi sunyi kad'an su bayyana mahimmancinki a wurina, ko yaushe kina bani k'warin gwiwa, nasan godia tayi kad'an a tsakaninmu, sai dai addu'ah Allah ya bar zumunci, wannan shafin nakine Sis ```waliyya wally```
www.babymsh.blogspot.com
Yasseer ya mik'a hannu zai amsa wayan kenan kiran Saude ya shigo a wayan Najib, murmushi yayi,
"Halan ita ke maka waya?"
"itace fa, Bara inje in amsa"
"ai naga alama kam tunda kake murna, wani lokacin naga hotan"
"tohm shknan bruz"
Falo Najib ya koma ya amsa kiran Saude, kusan raba dare sukai suna waya, lokacinda ya koma d'aki Yasseer har yayi barci, tunda safe kuma ya wuce k'yauyensu Saude.
Tafiya mai nisa sosae yayi kafin ya isa k'yauyen, yasha bak'ar wahala sosai ga gajia da zaman mota, dak'yar ya iya gano gidansu Saude inda su kawu Ado suke, a waje ya tsaya aka mishi sallama dashi.
Saiga Kawu ya fito yana washe baki, da sauri ya koma kawo mishi tabarma a soro ya shimfid'a mishi, sannan suka gaisa.
"Sannu fa da zuwa Yaro"
"Yauwah baba, baka ganeni ba ko?"
"eeh tohh gaskia bangane ba"
"Yasseer ne mijin Saude" ya fad'a yana sunne kai. Nan take Kawu Ado ya d'aure fuska.
"toh toh, toh naji sai akai yaya?"
"daman zuwa nayi inji kota dawo ko kuma an samu labarin inda take"
"babu abunda ya shafemu da Saude da labarinta, tunda muka baka aurenta muka gama fita sha'aninta, yanzu wama yasan inda take? Oho! K'ilama tana can yawon karuwanci, ko kuma namun daji sun cinye namanta!"
Cikin k'ara Yasseer yayi magana har saida ya tsorata kawu, "na rok'eka kawu karka danganta Saude da wannan maganganun naka"
Kallonshi kawu yayi yana tab'e fuska, "da rayuwar Saude, da mutuwarta bata da wani banbanci a wurinmu, karka k'ara zo mana da maganar Saude, bamusan inda take ba, itama in tana da sauran hankali bazata nememu ba, don bazamu tab'a sonta ba"
"zan koma, anma don Allah idanta dawo a sanar dani"
Juya mishi baya kawu yayi bai k'ara cewa komi ba, ya zaro kud'i Aljihunshi masu yawa ya mik'a mishi, hannu ya zuro ya warce kamar yana tsoran karya maida, haka ko godia bai mishi ba harya tafi.
En k'auyen ya shiga tambaga ko akwai wanda yasan inda Saude take, anma babu wani labari mai dad'i, gashi baba Haja bata cika zama k'yauyen ba daman babu wanda yasan takai Saude birni, har dare yana yawo k'auyen babu wani nasara.
Duk ya gaji ga yunwa da kishirwa, sai da duhu yayi sannan ya hak'ura ya koma cikin gari, wani d'an k'aramin hotel ya kama ya kwana, washe gari ma ya koma k'auyen, babu dai labarin Saude haka ya hak'ura ya koma Abuja.
Cikin wani irin yanayi ya isa gidansu, d'aga k'afa kawai yake anma baisan inda yake sakata ba, cikin sa'a babu kowa a falon, kai tsaye d'akinsu kawai ya wuce, kamar yanda ya zata Najib bainan, ya fad'a saman gado kawai dafe da kanshi. Momie taji shigowarshi anma shiru bata ganshi ba, duk ta damu ta ganshi daman, kuma tunda taji shiru tasan ba lafiya ba, ta tashi ta nufi d'akin nasu.
Yana zaune ya had'a kai da gwiwa, sautin shesshek'ar kukanshi ne kawai ke tashi, ta tsaya bak'in k'ofa tana kallonshi cikin mamaki da tashin hankali, kuka yake sosae yana dukan kanshi kamar wanda yaji sak'on mutuwa, a rikice Momie ta k'arasa shiga falon ta rirrik'e mishi hannuwa.
"ki barni Momie, ki barni don Allah in hukunta kaina akan laifin dana aikata da har yanzu nake biyan bashinshi, qila hakan zaisa na rage zugin da zuciyatah kemun, Momie na aikata laifi, wallahi na aikata babban laifi a rayuwatah" ya k'arasa maganar yana fashewa da wani kukan.
"Subhanallahi! Yasseer wane irin laifi ne wannan dake ma farin cikinka katsalandan? Fad'amun wanne irin laifi ne wannan da har ya sakaka zubda hawaye haka"
"Bazan iya ba Momie, lokaci ya riga ya k'uremun, yanzu fad'a mikin baida wani amfani"
"nifa mahaifiyarka ce, kana da wacce ta fini ne?"
"babu Momie, shiyasa nakeso ki tayani da addu'ah, don Allah karki matsa saikinsan abunda ke damuna"
"tohh shikenan, Allah ya yaye maka"
"Ameen Momie, kaina ciwo yakemun sosai, jikina ko ina zafi, na rasa inda zan saka raina"
"ka sauk'ak'a zuciyarka Yasseer, komai yayi zafi, ka dage da Addu'ah, bara inma Najib waya yazo muje Asibiti"
"A'ah zanji sauk'i Insha Allah Momie basai munje ba"
"Tohh kasha magani dai, saika kwanta ka huta, zuwa anjima in bai bari ba sai muje asibitin"
"tohm Momie" dak'yar yake magana, hawaye kawai ke fita a fuskarshi, saida ta tabbatar ta d'an kwantar mishi da hankali sannan ta fita ta barshi.
Tana fitowa saiga Najib da Saudat sun shigo, sun dawo daga wurin k'unshi da gyaran gashi, ta taresu tanama Saude sannu da zuwa, har k'asa ta gaishe da Momie.
"Ya gajiyan hidima, ya Auntynki?"
"lafiya lau take, tace a gaisheku" taci gaba da wasa da yatsunta su duka sunyi shiru, sai Najib ne ya fad'ama "wai sannu da zuwa mukazo tayima bruz, munyi waya dashi yace yana hanya"
"Ayyah! Aikam bai dad'e da dawowa ba, baijin dad'i ya d'an kwanta ya huta"
"Allah sarki, Allah ya sauwak'e"
"Ameen"
Tsarabar Husna ta had'a mata, da kuma nata duk da bada sunanta aka siyo ba, tayi godia sosae, basu dad'e ba suka tafi don zata fara aiki, gashi daren Sallah, Momie tana ta sa mata albarka.
Suna fita Yasseer ya fito da shirin zuwa Masallaci, jikinshi duk ba k'wari daka ganshi yana cikin damuwa.
Bayan Sallah da kwana biyu, Yasseer da Rabiah sukaje gidan Husna bankwana sun kusa komawa, tunda yazo bai ganta ba ko sallah bata iya zuwa gida ba, kamar tayi me don murna da ganinshi.
Saude na kitchen ita da Najib, don har gidan Husna ma ko yaushe suna tare, cewa yake bai damu gidan k'anwarshi bane, ko ina yake Saudat kawai yake gani, kuma bazaiso tasha wahala ba.
Yana jinsu ya fita falon, suka fara mishi tsiyar yanzu har aiki yakema Husna kawai don Saude na gidan.
"ai ba don ita nake ba, Saudat nake tayawa, idan kuma aka matsa in d'auke matata mu tafi"
Rabi'ah tace "lallai mai Matah"
"eeh Aunty MATATAH CE Saudat, laifine don na fad'i?"
"A'ah mamakin yanda so ya canjaka nake, kamar ba Yaya Najib d'in da ko Motsa baki wahala yake mishi ba"
"Da kenan Matar Yayanmu"
Husna tace "Ai kad'an kikaji indai labarin soyayyar Najib da Saudat ne"
Yasseer na gefe sai faman duba Agogo yake, ta rik'o hannunshi, "badai tafiya ba?" ya d'aga mata kai, "kinsan dai sauri nake" a gabansu ta marairaice fuska kamar zata fad'a mishi, "nidai ka bari muyi yinin tare, saimu tafi"
"Zan dawo d'aukarki, nima ban gama gaisawa da sista ba"
Husna tace "Munata fira ma Yayanmu ko ruwa bakasha ba, bara a kawo muku" ta k'wala ma Saude kira, "Aunty Saudat, a kawoma su Yayanmu drinks" Najib ya mik'e, "yanzu wannan d'inma ita zaki saka?"
"Nikam dai Allah ya bani lafiya in huta da fad'a, ni don su gaisa da Yayan ma nasan itama har yau basu had'u ba"
A hanyar fitowa suka had'u da Saude, ya ansa na hannunta sannan ya juya yakai musu, ruwan roba kawai Yasseer ya d'auka, "ba'a k'inshan ruwan zumunci anma a k'oshe nake"
"Ai nasan Auntyna bata wasa da bama Yayana Abinci"
"kamar tafiya zakayi, ka jira Saudat tazo ku gaisa plz"
"Sauri nake, idanna dawo ma gaisa" suka fita da Najib ya rakashi, yana fita Saudat ta fito da kulolin Abinci.
Inayin read more d'aya, kukace yayi kad'an na koma biyu, shima wai yayi kad'an😭
Wani lokacin har uku nakeyi anma akwai masu cewa yayi kad'an, don Allah kuna yimun Uzuri, kullum fa nake postn, abubuwa da yawa nake bari in muku typin, don Allah kuna hak'uri da wanda ya samu👏🏻
0 comments:
Post a Comment