A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
Bismillahir Rahmanur Rahim.....
"Hakk'in mallakar Hajja ne, kar wanda yayi min sauyi a cikin sa please."
Page *1*
A makaranta.
"Uwani halilu?"
"Present sir.."
"Baraka lado?"
"Present sir.."
"Sahura Ayuba?"
"Present sir.."
"Indo malam Hamza?"
"Labbaika, present, sir, mah, nazo..."
Saurin kallon ta malamin yayi jin yauma a yadda ta amsa mai kafin ya zare glass d'in dake manne akan saman idan fuskar shi, ya d'ora dara-daran idanun shi akan nata da nufin ko zata ji tsoron sa sai yaga ta kafeshi da idanuwan ta tamkar zata cinye shi, yayi saurin wurga mata uwar harara ranshi a matuk'ar had'e yace mata cikin tsawa.
"Ke..! Baki da hankali ne...?!"
Indo ta mik'e tsaye tana gyaran hijjab d'in ta wanda yayi dikil-dikil da daud'a wuyan ya yage tun daga wuya har zuwa k'irjinta sannan tace,
"Da sauk'i dai malam..!"
"Naga alama ai koma gurinki ki zauna wawuya kawai.."
Ya fad'a ba tare da ya kalleta ba. Komawa tayi ta zauna sai faman soshe-soshe take yi akan ta wanda hakan da alama ba za'a rasa kwaron kwarkwata ba dan yadda take yi ya nuna hakan. sai da ya kammala kiran sunayen su tas! sannan ya mik'e ya fita yana jiran lokaci ya cika sai ya kuma dawowa yayi musu subject d'in turanci wanda aka sari basa fahimtar uban komai a ciki, idan kuwa yana son su fahimta toh sai ya had'a musu da yaren hausa sannan zaiji ruwan amsa da tambayoyi amma idan da turanci zai kwana yana yi sai dai su kafamai idanuwa tamkar zasu cinye shi.
Yana fita wajan mintuna biyar sai gashi ya kuma dawowa hannun shi d'auke da wasu littattafai manya da kananu. yana shiga ya tarar duk sun kaure da surutu yayin da ya kai idanunshi can k'arshen ajin ya hango INdo da wani yaro taci uwar d'amara da hijjabin ta suna dambe. Dorinar hannun shi ya d'akko yayi gurin. sauran yara na ganin shi suka fara watsewa aka bar INdo da lurwanu a gurin. yana zuwa ya fara tsulawa INdo dorinar ganin ita ce me fifik'arewa kafin ya tsulawa lurwanu yana cewa.
"Ke! Sakar mai riga wawuya kawai."
Axabar bulalar ne yasa ta saki amma da ba tayi niyar sakin shi ba sai ta fasa mai baki kamar yadda ta furta tun farkon fad'an nasu. Malam Sadeeq na kallon su yace.
"Me ya had'a Ku?!"
Idanu kwal-kwal zasu kawo ruwan kuka lurwanu yace.
"Malam itace..."
Caraf be k'arasa fad'a ba INdo tace,
"Malam wallahi k'arya yake shine ya fara..."
Shima lurwanu dan kar tamai sharri ya kuma tare zan cen,
"Wallahi malam k'arya take yi kawai na ajiye..."
"Billahillaxi malam shine ya..."
"Keep silent or something else's, sha-sha-shai kawai.."
Babu abin da suka fahimta a cikin abin da yace dasu sai dai yana yin yadda yayi musu maganar da kuma kalaman shi na karshe ya tabbatar musu da cewar fad'a yake musu hakan yasa suka yi shiru suna bin kyakyawan bakin shi da kallo ba kamar INdo da take tunanin ko alawace ji take kamar ta lasa dan yadda ya burgeta.
Komawa yayi wajan teburin shi ya zauna sannan yayi musu alamar suzo baki d'ayan, suka bishi INDO sai faman ture lurwanu take yi a haka suka k'arasa wajan da malam Sadeeq yake jiran su,
"Kai me ya had'a ku da ita?!"
"Malam itace kawai muna zaune sai tazo tana tab'ani da kafa nayi mata magana ta dena takani shine tak'i taci gaba har muka fara fad'a da ita."
Tun kafin ya bata izinin magana INdo ta fara tana hararar lurwana bakin ta har kumfar yawu yake sabida masifa,
"Kai..Kain uban can..! Na rantse da Allah malam shine ya d'alamin kaure a baya na shine na rama ya kuma yi min kawai muka fara fad'a dan shi masifaffe ne ya raina ni.."
"Ya isah haka kowa yaje ya zauna bana son surutun ban za."
Tashi suka yi suka tafi dama can karshen aji nan ne wajan zaman INdo dan haka ta tafi malam Sadeeq yayi saurin dawo da ita, tana zuwa yace da 'yan layin gaba suyi mata guri anan ta zauna cike da jin haushin malamin dan taga alamar baya son ta bare yabi bayan ta a duk cikin al'amarinta.
A haka ya kammala musu yabar ajin duk sun gundure shi ga haushin basa ganewa da turanci har sai yayi da Hausa. Ana tashi ya hau mashin d'in sa kai tsaye ya wuce inda ya sauka. Wanka yayi sannan yayi sallar azahar ya koma gefe ya zauna bayan ya janyo wayar shi, laluban d'an uwan shi ya fara yi cikin sa'a ta fara k'ara yana d'agawa yace,
"Hi twins ya gida ya gurin aikin naka?!"
Daga can 6angaran ya amsa cikin sanyin murya kamar yana rad'a,
"Lafiya lau all twins ya student's da fatan dai kana samun yadda kake so koh?!"
Shafa k'eya yayi tamkar yana ganin shi sannan ya lashi lips d'in shi yace,
"Nop! Twins ga baki d'aya makarantar bata yi ba wallahi, gashi nazo an wani bani formaster teaching kuwa sai dai nayi da hausa wata Kalmar ma ban san yadda zan fassara musu ba wallahi sai dai na barsu a haka."
Dariya yayi mai sauti ya san dole a bawa d'an uwan shi haushi duba da yadda baya son wasa a harkar karatu gashi an kai shi inda zasu samai hawan jini, cikin basarwa yace.
"Common Sadeeq ka sani ko anan ma girlfriend d'inka take, dan Allah kasaki ranka kasan 'yan kauye da son mutane za kaji dad'i kuma zasu soka kai dai kawai ka samo mana wifey d'in ka acan..!"
Kit! Sadeeq ya kashe wayan sam beji dad'in wayar da suka yi da d'an uwan nashi ba yau, a maimakwan ya lallab'a shima a'a sai ma yi mai fatan tsiya da yake yi na samo mata dan wulakanci. shi kam Abubakar murmushi yayi jin ya katse ya san haushi yaji sabida yayi mai fatan tsiya. zai samu yaje garin har gurin shi ya bashi hakuri yaga kuma yadda suke yi.
***
Bayan wasu awanni, Sauri yake yi ya k'arasa cikin masallacin dan gudun kar a tayar yana hanya, sai da yazo dai-dai wajan wata kwata zai tsallaka kawai yaji an kwararo ruwan kanzo gabaki d'aya aka b'ata mai wandon dake jikin shi. Bin katangar gidan yayi da kallo cikin wani mugun takaici kafin yayi wani yunk'urin tuni an fara zagaye shi abin takai cin ma harda d'aliban shi. sai sannu suke zabga mai tamkar wanda yaji ciwo.
"Kai subhanallahi Malam Sadeeq ya a kai haka?"
Kafin ya bashi amsa wanda yayi maganar ya kalli wani yaro tare da cewa,
"Kai yi maza shiga nan gidan kace a temaka mana da ruwa a buta."
Juyawa yaron yayi shi kuma headmaster ya kalli Sadeeq cikin jimami yace.
"Garin Yaya hakan ta faru Malam Sadeeq?!"
Da kyar ya samu ya tsaida takaicikin shi kafin ya kalli headmaster yana kallon inda aka b'ata mai yace,
"Wucewa zan yi zuwa masallaci, su kuma ba tare da suna kulaba kawai suka watso k'azanta sai kace a cikin gidan su duk ba wannan ba sun b'atan lokaci na rasa jam'i."
"Ashha-ashha malam yi hakuri kasan kauyan namu ne sai hakuri duk haka suke yi kayi hakuri dan Allah.
Dai-dai lokacin yaron da aka aika suka fito shi da INDO hannunta rik'e da buta gefen butar ya fashe sai da ta d'an kar-kata ta taho tana cewa,
"Waye yake neman ruwa a buta?!"
Karaf suka had'a idanu da shi da sauri ta dashare baki tana matsawa wajan shi ruwan sai zuba yake ta kalleshi tare da cewa,
"La'ilaha'illallahu Malam Sadeeq kaine a k'ofar gidan mu yau?!"
Banza yayi mata yana kallon butar ganinta jage-jage gashi duk ta fashe ya sashi yin saurin juyawa tare da kallon headmaster yana cewa,
"Rankashi dad'e bari kawai na koma gida naga nan duk b'ata lokaci ne na gode..."
Ba musu headmaster yayi mai sallama da sauri ya wuce sauran mutane na bashi hakuri ita kuma INDO tana fad'in,
"Malam ruwanfa? ko na biyo ka dahi koka ka fasa na maidahi gida?!"
K'in kulata yayi ganin haka yasa INdo ta murgud'a mai baki tamkar yana ganinta sannan ta koma gida tana mitar kawai yasa sunyi asarar ruwan su a k'asa bayan suma babu kala ne suke yi.
***
Yau kwana biyu kenan INdo bata zuwa makaranta, sai a kwana na uku taje tun daga bakin k'ofa zaka tabbatar da yau tazo sabida yadda ajin ya kaure da shegen surutu da hayani. yana shiga ya ganta zaune akan tabur d'in da malamai ke zama idanunta sanye cikin eye glass wanda idanun (glass) d'in suka ciccire ta rik'e pencil tare da d'ora kafa d'aya kan d'aya tana yin irin na Malam Sadeeq,
"Mary alto."
"Zuwaira jamilu."
"Mansur bawa."
Gabaki d'aya ajin aka d'auki ihu da shewa dan sam basu kula da zuwan shi ba. har INdo ta mik'e tsaye tana dariya tare da cewa,
"Alkur'an haka malam Sadeeq yake yi.."
Suka k'ara tuntsurewa da dariya ana cewa,
"Ohhh ke INDO...!"
Tsittt taji anyi hakan yasa ta waigawa bakin k'ofar dan ganin yadda kowa ke kallon wajan, karaf suka yi idanuwa hudu da malam Sadeeq wanda yayi kicin-kicin da fuska tamkar hadari tayi saurin komawa wajan zamanta wanda in dai shine a ajin toh anan take zama sai ya fita take komawa gurinta na ai na hi wato karshen aji.
Yana shiga duk aka tashi ana gaida shi kowa ka gani cikin tsoro yake dan basu san matakin da zai d'auka akai ba,
"Good morning sir..!"
Sai da ya samu guri ya ajiye register da sauran littattafan hannun shi sannan ya kalle su yayi musu alamar su zauna da hannu, gyara glass d'in idanun shi yayi sannan ya kalli inda INdo take zaune ta kwalalo mai idanuwa yace mata,
"You! come here.."
Tashi tayi cikin d'ari-d'ari dan babu wanda be san kalmar come ba, tana zuwa ya matsa mata tare da nuna mata kujerar gurin yace,
"Seat down..." (Zauna)
Zama tayi dan taga ne abinda yace sabida yau da gobe idan sun gaida malamai ana ce musu seat down so kuwa ya san kalmar, ta zauna sai wulkita idanu take. register ya d'akko tare da bud'ewa ya mik'a mata jan biro da blue tare da cewa,
"Oya started."
Tayi saurin kallon shi tare da cewa,
"Na'am malam.."
Keya ya salle mata da hannunsa tare da cewa,
"Ki fara kiran sunan idan ba haka ba zaki sha wahala dan naga alamar kin raina ni so ina son kiyi musu yadda nake yi nima na gani.."
Kallon register d'in tayi sam kasa gane yadda take tayi bare aje ga karanto sunayen ciki ba zata iya ba kuma nan J.S one, kallon shi tayi tare da marairaicewa ta fara ba shi hakuri.
"Malam dan Allah idan kana kaunar iyayanka kayi hakuri wallahi tallahi ba zan sake ba."
"Au ba zaki fara ba sai na zane ki...?!"
Ya fad'a yana gyara dorinar hannun shi, nan da nan INdo ta fara kuka dan tak'i jinin a doke ta da bulala. tayi saurin zamewa k'asa tare da sake bashi hakuri akan ya kyaleta ta tuba tabi Allah tabi shi.
Ganin duk ta gigice yasa shi ce mata,
"Tashi ki dawo nan kiyi naildown."
"Malam baka hakura ba dan Allah?!"
Ta fad'a tana matse idanuwa dan hawaye su fito amma ko d'igo, ganin yaje ya zauna ya fara kiran suna yasa INdo tashi taje tayi abinda ya sakata dan ta san ba hakura yayi ba. sai da ya kammala kiran sunan ya fara koyar dasu ya gama sannan ya kalleta yana nunata da yatsa yace,
"Idan kika sake yin abinda nake yi in dai ba na karatu bane sai na 6allaki kina jina?!"
"Eh malam ai baxan kuma bama."
"Yafi miki.."
Ya fad'a tare da kwashe kayan shi yabar ajin yana tunanin inda zai yi ya samu ayi mishi transfer ya tsani makarantar sam ba tayi mishi ba.
Bayan sati biyu ranar wata Monday Sadeeq na shirin tafiya class d'in shi ya d'auki duk wani abu da yake buk'ata yana shirin fita kawai yaga Abubakar twins d'in shi tsaye cikin kananun kaya riga seegreen me dogwan hannu da wando baki sai farin eye glass wanda yayi mai matukar kyau, sosai suke matukar kama babu ta inda zaka iya bambance su sabida tsabar kamannin su. kallon shi Sadeeq yayi cikin tsananin mamaki tare da k'arasawa ya kalleshi cikin mamaki yace,
"Yanzu muka gama waya da kai amma shine baka gaya min kana hanya ba why?!"
Kafad'a Abubakar ya d'aga alamar ba komai sannan ya shiga ciki ya zauna tare da cewa,
"Twin ko class zaka shiga ne?!"
"Eh but tunda kazo sai mu wuce gida ka huta gobe na shigar musu."
Yayi maganar yana k'okarin maida littattafan dake hannun shi, da sauri Abubakar ya mik'e tsaye yana tsayar dashi ta hanyar rik'e hannun shi yace,
"No kazo muje sai na tsayaka ina nan tare da kai har zuwa gobe."
Kafad'a Sadeeq ya d'aga sannan ya d'auka tare da juyawa yana fad'in.
"Toh muje."
Tafiya suke wanda ita kanta iri d'aya ce suke yi suna yi suna hira yara kuwa daga cikin tagogin ajin su sai lekowa suke suna mamaki da al'ajabi ganin malam Sadeeq guda biyu a haka suka k'arasa barandar ajin su INdo. Yauma kamar kullum cikin surutu suka gansu sam basu lura da zuwan su ba INdo suka hango a saman dest tana rik'e da kugunta sai gwada musu yadda malam Sadeeq yake tsayuwar shi take yi taji Uwani halilu ta janyota tare da nuna mata k'ofar ajin tana hango su ta shige k'ark'ashin benci cikinta sai kululululu yake sabida ta san yauma ta shiga uku.
"Goody morning sirsss..!"
'Yan aji suka fad'a baki d'ayan su tare da mik'ewa tsaye. ciki suka shiga sosai Abubakar sai kallon su yake su kuma sun rasa gane waye malamin nasu a ciki. Sadeeq ya k'arasa wajan bencin da INdo ke k'ark'a shi yace.
"Ke! Tashi ki fito ko na mareki.."
Jikinta na rawa ta d'ago ai tana ganin still biyu take ganin shi sai ta koma tana ihu tare da cewa.
"Wayyo Allah na higa uku malam nayi min fatalwa, wallahi tallahi ban yi niyar yi ba amma Maryam Aliyu tace nayi zata bani naira biyar dan Allah malam kadenayi min fatalwa wallahi ba zan sake yi ba idan na k'ara ka...."
Bata k'arasa ba taji an janyo kafar ta sai ganinta tayi a gaban allo tana d'agowa still ta kuma ganin su biyu kawai a take ta sulale a wajan ta sume sabida tsabar kad'uwa da shiga cikin rud'ani.
Ko gezau Abubakar beyi ba bare yayi yinkurin yin temako sai kallonta kawai da yayi yana mamakin ganin hauka irin nata, da sauri Sadeeq ya girgizata yana kiran sunanta cikin tashin hankali kar yaje ta mutu ya shiga uku 'yan aji kuma sai suka fara kuka cewar INdo ta mutu.
"Aisha! Aisha!! Ke Aisha!!! Tashi mana me aka yi miki haka...?!"
Sadeeq ya fara kiran sunanta ganin duk ya rud'e yasa Abubakar k'arasawa wajan ya dafa shi sannan ya kalle shi a hankali cikin rashin sonyin maganar shi yace,
"Sorry my twins ba mutuwa tayi ba suma tayi da ansa mata ruwa zata farfad'o.."
Shaf Sadeeq mantawa yayi da cewar d'an uwanshi likita ne sai da Abubakar ya samo ruwan wata yarinya a jarka ya shafawa INdo sannan ta farfad'o yana jin sanda d'an uwan nashi ya sauke ajiyar zuciya mai k'arfen gaske na farin ciki.
Tana farfad'owa idanunta suka sauka a kansu da sauri tayi baya jikinta na rawa, ganin haka yasa Abubakar dama shine wanda baya d'aukar raini ya buga mata wata uwar tsawa tare da zare mata idanuwa tsit INdo tayi jikinta sai faman rawa yake.
"Ke..! Karna sake jin bakin ki yayi mana ihu, wawuya baki san ana haifar 'yan biyu ba? Ko kinga munyi miki kama da mayu ko aljanu..?!"
Cewar Abubakar wanda ke tsaye akan INdo, da sauri ta girgiza mai kai cikin tsananin tsoro sannan ya ce mata,
"Tashi kije ki zauna na san yanzu garau kike ba kya buk'atar wani hutu."
Da sauri ta mik'a ta wuce gurin zamanta, mik'ewa Sadeeq yayi ya koma kan kujera tare da janyo d'ayar ya nunawa Abubakar alamar ya zauna. kallon kujerar yayi sannan ya kallo inda yake hango INdo cikin yatsina fuska yace mata,
"Ke..! Zo nan."
Da sauri ta k'arasa tare da zubewa a gurin shi tace.
"Gani malam."
"Karki kuma kirana da malam kinji ko? Ni ba malamin Ku bane..!"
Baki na rawa INdo tace.
"Toh sir."
Had'e rai yayi tare da tsuke baki cikin takaici yace,
"Waye sir d'in?!"
INdo tace,
"Kai ne sir. ."
Hard'e k'afa yayi yana kallonta cikin b'acin rai yace,
"Stupid...! Ya sunan namijin saniya? ya ake kiran shi da hausa?!"
Cikin sauri ba tare da takawo komai a cikin zuciyar ta ba tace,
"Sunan shi sah."
Abubakar yace,
"Ahha kin ga nayi miki kama da shi?!"
Da sauri ta girgiza Kai alamar a'a tana mamakin wannan abu, toh me zata ce mishi tace malam yace baya so tace mai sir yace ta kirashi da sunan dabba toh ko sunan shi yake son ta fad'a ko tace mai baba amma ai be haifeta ba bare tace mai hakan.
Jan baya yayi kad'an tare da cewa,
"Zoki gogemin kujerar da zan zauna."
INdo ta mik'e tana mamakin toh yau malam sadeeq mugu ya zama kokuwa ba shi bane dan har lokacin bata tantance waye malam Sadeeq ba cikin suba. kalle-kalle ta din ga yi ko zata samu wani kyallen da zata goge mai amma babu ganin haka yasa shi yin magana,
"Ke..! wai ba zaki yi aikin da na saki ba kin barni a tsaye fa."
"Mal.. Si.."
Ta rasa me zata ce mai kawai ta kalleshi tana turo baki dan ya gundire ta tace,
"Ai babu tsumma shi yasa."
Cikin rashin damuwa ya kalleta daga sama har k'asa ya tab'e baki sannan yace,
"Meye amfanin hijjabin jikinki ko d'ankwalin kanki su d'in ba tsumma bane?!"
Da sauri INdo ta kalleshi ya d'aga mata gira guda d'aya tayi saurin kallon Sadeeq dake zaune ga mamakin ta register ma yake bud'ewa ta kalli hijjab d'inta wanda duk ruwan kashu ya dafar dashi gashi wuyan ya yage tace mai.
"Ai hijjab d'ina ne bafa tsumma bane ba."
"Idan baki cire kin goge min na zauna ba ranki zai 6aci yanzun nan kinji na gaya miki."
Ya fad'a cikin tsawa wadda take a slow, ba yadda ta iya haka ta kama k'asan hijjab d'inta ta goge mai kujerar sannan ya zauna ita kuma ta koma wajan da malam Sadeeq d'in ya tanadar mata a gaba. Malam Sadeeq ya fara kiran sunaye sannan da ya gama yayi musu karatun da yake d'aukar su wato turanci, Abubakar dake zaune yaci dariyar zuci dan karma yayi a fili su raina shi ko idan yaji dariyar tayi mai yawa sai ya kara text book a fuskar shi yayi mai isar shi, lallai dole d'an uwan shi ya koka tab makarantun gwamnati sai addu'a yake ta fad'a a cikin ranshi har Sadeeq ya kammala musu sannan suka fita ana tashi suka wuce gidan da Sadeeq d'in yake haya a ciki.....
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:48 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
Page *2*
Bayan an tashi daga makaranta, su Indo ta k'ofar gidan da su Sadeeq suke suka biyo. lek'en su suka din ga yi su dai suna jin hayaniya da guje-gujen yara amma basu kula ba sai can Indo da Maryam Ali suka kuma kutsa kai suka shiga suna lek'a tagar wani d'aki karaf suka hango Abubakar zaune a bakin katifa yana danna laptop wanda daga shi sai 3quarter da singlet sam beyi tunanin cewar ana lek'an su ba sai da yaji motsin yayi yawa sannan ya d'aga kai yana kallon gurin.
Mamaki da al'ajabi yasa shi saurin mik'ewa tsaye su kuma suka zaro mai idanuwa kamar had'in baki su sam basu gane waye aciki ba kasan cewar kamannin iri d'aya ne. Suna k'ok'arin guduwa suka ga Sadeeq tsaye a bayan su ya rufe k'ofar gidan ya jin gina a jikin ta yana watsa musu wani mugun kallo. can Abubakar ma ya fito fuskar nan a murtuke.
“Wayyo Allah dan girman Allah dan annabi Muhammad s.a.w idan kuna kaunar iyayanku kuyi mana hak’uri.”
Cewar Indo tana faman tafa hannuwa alamun rok'o,itama Maryam tsugunnawa tayi tana magiya,
“Dan Allah kuyi hakuri wallahi Indo ce tace muzo mugani ko aljanu ne ku, amma wallahi ni banyi niyar shigowa ba.”
“Shhhhhhhhhhhhh..!”
Abubakar yayi musu bayan ya d'ora yatsan shi d'aya akan Lip's d'in shi suka had'a idanuwa da Sadeeq suka fara matsowa gurin su yayin da jikin su Indo ya hau rawa kamar an saka musu shock ai kuwa suka fara kurma musu ihu.
“Iiihuuu..! wayyo Allah a zo a temaka mana zasu kashe mu...!!”
Kafin kace mene har unguwar ta cika da mutane sai bugan gidan ake amma sunk'i bud'ewa, yaran da suka taho tare da su Indo ne suka yiwa sauran mutanen gurin bayani kan cewar ai su Indo ne suka shiga wai sai sun kallesu. wani dattijo ya kuma buga gidan jin su indo na ihu yayi magana da d'an k'arfi yace,
“Ku kuwa bayin Allah dan Allah kuyi hakuri ku bud'e su fito ba dan halin su ba.”
Sai da Abubakar yasa su kamun kunne wajan mintina goma sannan Sadeeq yaje ya bud'e su indo suka kwasa da gudu suka bar gidan,hatta wad'an da suke mak'otaka dashi Sadeeq d'in sai da suka tambaya waye Sadeeq a cikin su yace...
“Gani nan baba Al-hassan.”
Wanda aka Kira da Baba alhassan yace,
“Ikon Allah toh ai kud'in ne dole ku zama abin kallon jama'a sabida ba kasafai ake samun samarin matasa maza 'yan biyu masu matukar kama da juna ba. koni da Al-husain d'ina kafin ya rasu ana iya gane mu amma ko babu wata alama da zata sa a gane ku dole yara suzo kallan ku.”
Murmushi Sadeeq yayi tare da shafa k'eya yayin da Abubakar ya kalle su sai kuma ya juya tare da komawa cikin d'aki yana tausayin d'an uwan shi akan wannan aikin nashi daya zoyi duk babu sa'a, ba'a makarantar ba ba kuma a garin ba duk babu sauk'i haukan garin yayi yawa.
**
Abubakar da Sadeeq 'yan biyu ne wad'an da ba zaka ta6a iya banbance Hassan ko Husaini ba mudin suna tare sabida tsabar kamannin da suka yi. Hatta tafiyar su, dariyar su, yana yin maganar su sai d'abi'un su ne kawai idan ka zauna dasu zaka iya tabbatar da cewar sun ban-banta dana juna.
Engineer Alhaji Salmanu Haruna shine mahaifin su, yana da arzik'in shi dai-dai misali Matan shi na aure guda biyu ne Mama A'i itace uwar gida kuma mahaifiyar su Abubakar da Sadeeq sune yaran Alhaji Salmanu na farko sai kannan su da suke uwa d'aya su biyar Hawwa, Halima, Hamza, Amina sai Khalifa sai ta biyun Umma Fatu tana da yara uku Khaleel, Mubasshir da Rukayya. Gabaki d'ayan zuriar sun taso cikin tarbiya da ilimin boko dana addini dan Alhaji Salmanu tsayayyan mai gida ne da yake tsaye akan matan shi da yaran shi.
Wannan kenan..
**
Indo Aisha d'iya ce a wajan Hamza mai gyaran radio da Inna Mero sai kannanta guda uku Sagiru, Shehu sai Nafeesa. Malam Hamza ya dad'e yana gyaran radio dan da sana'ar yayi aure harya hayayyafa duk da suna matukar shan wahala dan wata rana ma basa samun na abinci sai dai su kwanta haka.
Indo yarinya ce k’azama ainun domin wanka ma se juma’a jum’a take yi,shima se an tilastata agaba bayan haka kuma gagarumar fitinanniya ce ga d'an karan tonan fad'a da shiga fad'an da bana ta bane,tana da son wasa hakan yasa koda aka bud'e musu wata primary aka sanyata bata kwaso komai ba sai k'arin fitina da rashin kunya a haka harta zana jarabawar fita daga primary ta wuce secondary yanzu tana aji d'aya ko sunanta da kyar take iya rubutawa shima a karkace cikin rashin tsari, kuma kusan duk haka ajin yake monita ne kawai mai iya rubata sunan shi complete sannan ya rubuta na wasu suma ba duka ba.
Gidan su na k'asa ne d'an k'arami wanda shi da kanshi Malam Hamza shi ya gina abunshi yayi d'akuna uku da makewayi katangar tasu gajeriya ce domin idan kai dogo ne to hak'ika idan kana tsaye sai an hangoka hakan yasa duk shirgin da suka kwaso suk'e iya cillashi ko su watsa shi ba tare da sanin koda mutum a wajan ba dan ansha fad'a dasu da mutanen unguwa amma sun kasa denawa har anyi shiru an zuba musu ido.
**
Da gudun tsiya ta shiga gida tana sauke wani uban nishi Inna ta kalleta tare da cewa,
“Ke kuma lafiya kuwa kika shigo gida bako sallama 'yar nan..?!”
Inna ta fad'a kasan cewar bata iya fad'in sunan Indo sabida 'yar ta ce ta farko kuma sunan surikar ta ne wato mahaifiyar malam Hamza. cire daddauhar hijjab d'in Indo tayi me tashin hamamin wari tare da cillar dashi a tsakiyar gidan su tace,
“Wato inna akwai abubuwan kallo idan mutanen cikin birni suka zo nan wai...!”
Tah fad'a tana zaro idanuwa, kallonta inna tayi cike da takaici ta rasa gane kan Indo tunda aka kawo malam Sadeeq kullum taje makaranta ta dawo da saban labarin da zata bata akan shi dan haka tasan tatsuniyar gizo bata wuce ta kok'i inna tace,
“Allah shi kyauta miki 'yar nan, tunda aka kaiki makarantar nan ban tab'a jin kinzo kina yin karatu ba yadda nima zanji dad'i ba sai dai tunda aka kawo sabon malamin ku toh babu ranar da zakije baki dawo da sabon labari akan shi ba sai kace shi aka ce kije ki koyo..”
“Kai inna ana baki kina k'in k'ar6a.”
“Eh ba zan k'ar6a ba bana so ki rik'e kayan ki.”
Indo ta kuma gyara zama tare da bugun kanta da alama kwarkwata ce tayi motsi,cikin son bada labarin tace,
“Aikuwa inna sai na baki labarin nan dan kuwa wallahi har suma nayi aka samin ruwa na farfad'o.”
Jin abinda ta fad'a ne yasa inna zaro ido tana dafe k'irji tace,
“Na shiga uku ni Maryama meya faru dake 'yar nan?!”
A take Indo ta kwashe labari tun daga wanda ta sani har wanda d'alibai 'yan uwanta suka gaya mata ta k'arashe zan cen da fad'in lokacin da suka shiga gidan su shine fa ana bud'e musu ta shigo gida da gudu.
“Ikon Allah kenan, toh ke dai babu ruwanki dasu..ah to karkije wata rana ki basu haushi suyi miki aika-aika su cuceki Allah ya tsare ba fata ba”
“Toh inna ai na fisu iya gudu wallahi.”
“Yi min shiru wawiya kawai an ce miki wannan muguntar ta gudu ce, ke dai babu ruwanki dasu na gaya miki.”
Da haka suka dinga magana inna na son fahimtar da ita sai dai kunya da kawaici yasa ta kasa sai faman kwana-kwana take yi.
Ita kuma wadda ake wa dama ba wani fahim ta ne da ita ba dan haka bata fuskanci inda maganar inna ta dosa ba.
***
“Other half gaskiya ya kamata ka nemi transfer daga wannan gajarabal d'in makarantar, ah!wannan school da kauyan ai sai kaima su maida kai kamar su dan wallahi rayuwa a irin wannan gurin tsab zasu canza ka su 6ata maka hobby d'inka.”
"”Kai twinnie God forbid wallahi sai dai ni na canza musu, ni sam basa yi min haka kawai zuwanka ne yasa dan sun ganmu mu biyu shashanci sai kace akan mu aka fara zuwa duniya mutum biyu iri d'aya...”
Abubakar ya kuma kallon Sadeeq shi tausayin shima yake dan ya san kawai yana zaune a garin ne ba dan yana jin dad'i ba,ta6e baki yayi tare da d'aukar laptop d'in shi ya koma cikin bedroom ya k'agara gari ya waye ya bar garin dan jin shi yake yi tamkar akan k'aya.
Mik'ewa Sadeeq yayi tare da d'aukar mukullin motar Abbakar d'in, fita yayi ba tare daya sanar mai ba yayi waje. Can cikin gari ya tafi wani restaurant ya shiga inda yake zuwa cin abinci yayi musu order mai rai da lafiya sannan ya siyo musu drink's masu sanyi ya dawo gidan lokacin ya tarar da Abbakar d'in ma bacci yake kasan cewar sun kunna inji akwai iskar fanka. kallon shi yayi sannan ya fito ya dawo parlor ya fara rubuta lesson plan har wajan la'asar sannan Abubakar ya farka yana fitowa yagan shi zaune gaban shi duk takardu ne da littattafai kawai ya kalleshi yace,
"Wai twinnie har yaushe ne ka koma haka? duk ka takurawa kanka ya kamata ka sauya makaranta dan kafi karfin koyar da irin wad'an nan school d'in."
Sadeeq ya numfasa tare da cewa,
"Meye abin fin k'arfi twinnie ? a gani na tunda teaching nake sha'awa ai be kamata nayi korafi ba."
Da sauri Abubakar yace,
"Ba anan ya dace da kai ba twinnie kamata yayi yanzu ace kana wata university d'in kana bada lecture's dan kafi can-canta da dacewa acan, amma nan wallahi tsaf zasu nakasa maka ilimin da kakeji dashi ya kamata ka duba magana ta."
Kallonsa yayi har ya shige cikin d'aki sannan ya sauke idanun shi, dama tun ba yau ba tun suna k'anana suke da ban-bancin ra'ayi wajan zab'ar samun gurin aiki sai dai shi Abubakar ya cika burin shi yayin da shi kuma Sadeeq be samu zama pilot ba sai aikin koyarwa a university of sokoto amma yak'i tafiya sai ya tafi ya samu a wani secondary school itama d'in a kauye, sai gashi sam baya jin dad'in ta.
Abubakar ne ya dawo ya zauna tare da janyo take away d'aya ya fara cin abincin shi, Sadeeq ya kalle shi tare da ture takardun gaban shi yace,
"Twinnie wai ya zancen Ummi kuwa ka kuma komawa kun dai-dai ta ko?!"
Abubakar yayi murmushi tare da ajiye spoon d'in hannun shi yace,
"Bari kawai twinnie ban koma ba sai aikowa gida da mahaifinta yayi wai ance angan mu a tsaye toh idan na shirya na fito. kaji fa? ni ai Ummi bata cika quality's d'in da nake da burin matata ta kasan ce ba dan haka nace a'a ban shirya ba ko ya ka gani?!"
Dariya Sadeeq yayi sannan yace,
"Kai ma ka tsaya ruwan ido meye ai bun Ummi tsakani da Allah, yarinyar nan fa yanzu s.s 1 zata shiga kuma gata kyakyawa to meye ya rage maka.?!"
"Gayu, twinnie ka san ina son mace 'yar gayu mai aji wadda koni idan ina mata magana sai taga dama zata amsa amma fa Ummi kana magana kafin kakai k'arshe ta mayar maka, no gaskiya akwai wata dai a cikin hospital din mu da suka zo sanin makamar aiki na ga kuma kamar type d'ina ce sai dai ba zan iya mata magana ba karma ta rainani."
"Rai ni kuma Abbakar? toh kenan idan kayi auran ma bashi da amfani tun da dole sai wani abun raini ya shiga tsakanin ka da matar ka.."
"Kasan kuwa wani sa'in ina jin tsoron yin aure, sabida wani sa'in sai naga ba shi da amfani."
"Ikon Allah."
Cewar Sadeeq yana yi mai kallon mamaki yayin da Abubakar d'in ya mik'e yayi waje yana son ya samu almajirin da zai wanke musu toilet d'in su.
Yana fita ya samu wasu yara zaune suna wasa ya kira wanda suka had'a ido da shi. yana zuwa yaron befi 10 years ba Abubakar ya kalleshi yace.
"Kai whats your name?!"
Yaron ya kura mai idanuwa kunnuwan shi sai bud'ewa suke dan beji abinda yace ba nan ya fara kwakular hanci har lokacin idanun shi na kan na Abubakar ganin kamar be gane ba yasa shi cewa,
"Ya sunan ka?!"
Ya dashare baki hak'oran nan yalaye kamar yasha d'orawa kafin yace,
"Suna na Sagiru Hamza."
Abubakar ya d'auke kai tare da kallon sauran yara, gaba d'aya kaf cikin su babu na za6a har garama Sagirun dan haka ya kalle shi yace.
"Zaka iya wanke mana toilet?!"
Da sauri Sagiru ya d'aga kai duk kuwa da cewar be gane abinda ake nufi da toilet din ba amma yaji ance wankewa yasan koma me ye zai iya wanke shi tatass.
"Toh shiga muje."
Abubakar ya fad'a yana komawa ciki, Sagiru ya juyo tare da yiwa sauran abokan nashi gwalo.
"Yauwa Sagir kaga ga klin da hypo shi zaka d'auka ka kwanke shi sosai."
Ganin inda ya nuna ne yasa Sagiru tabbatar da cewa ban d'aki ake son ya wanke, Abubakar na gama nuna mai ya koma cikin d'aki shi kuma Sagir ya shiga yana wankewa.sai da ya kammala tasss sannan Abubakar ya fito ya bashi naira d'ari biyu ai kuwa ya dinga murna sannan ya tafi gida da gudun sa yana murna tare da burin ramuwar abinda INDO tayi mai lokacin da tana da kud'in ta naira 50 ta dinga siyan awara tana hana su.
"INDO..! INDO...!! INDO..!! nima yau zoki ga kud'ina wallahi na samo.."
Sagir ya shiga gidan da gudu yana k'iran ta da k'arfi, da gudu ta fito daga ban d'aki hannunta rik'e da buta tana fitowa tayi wurgi da ita tana gyara kullin pant d'inta wanda yayi mata yawa sabida bud'ewar da yayi gashi kamar rai shi kad'ai gareta ta k'arasa kusa da Sagiru tana raba idanuwa.
"Wai kai dalla meye kake ta kwad'a min kira ne?!"
Be yi magana ba sai kud'in daya nuna mata yana tsalle, da sauri ta ware idanuwa cikin tsananin mamaki sannan tace,
"Kai Sagiru a ina ka sato ko kuma waye ya baka kud'i har d'ari biyu haka...?!"
"Yarinya wankin ban d'aki nayi shine aka bani ita lada."
"Ikon Allah a wane massalaci ne haka?!"
Sagir yace,
"Ba'a matsallaci bane a gidan malamin ku wannan mesa glass d'in nan."
"Tab d'i jam! toh Sagiru nawa zaka bani a ciki?!"
Wani banzan kallo yayi mata tayi kallar tausayi tare da cewa.
"Dan Allah kabani ko naira hamsin ce kaji kanina wallahi nima wata rana idan na samo zan baka."
"Uhh-umm yarinya ba zan bayar ba."
Cewar Sagir yana danna kud'in a cikin aljihun shi, ganin haka yasa ta cewa,
"Toh kuwa yaro dama Inna tana ta neman kud'in da za'a siyo daddawa da kuka sai kazo ka bayar tun da ai kaima da kai za'a ci tuwan."
"Ke wallahi ba zan bayar ba, ke rannan ba da naira goma a hannunki ba Inna tace ki kawo a siyo manja da ita ba amma kikak'i sai yanzu dan kud'in ba naki bane ba zaki ce na bayar a siyo kuka toh ba zan ba da ba."
Ganin bashi da niyar bata ko sisi yasa ta fara kwad'awa Inna kira, yana jin haka shi kuma ya zura da gudu yayi waje nan ya barta sai faman masifa take tamkar kud'in nata ne...
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:48 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
Page *3*
Da sauri ta fito ta biyo bayan sa amma ko kyallin sa bata hango ba,ta ciza le6anta tare da ficewa daga gidan gaba d'aya.Gidan su Maryam k'awarta ta wuce tana wak'ar ta da d'an tsalle wasa hankalinta kwance.malam Sadeeq dake k'ofar gida ya bita da kallon takaici ganin yadda tayi fururu ba wanka,sam bata kula dashi ba sai faman wak'a take tana cewa.
"Indo Aisha...ta zariya mai d'an kallabi..."
Har tayi kwana sai tayo baya ganin shi da tayi, shi kuwa yana ganin zata dawo yayi sauri zai koma cikin gida be kai ga k'arasa juya wa ba yaji tace.
"Wil dam malam. (Well done sir).."
K'in kallon ta yayi yana dan na wayar sa domin service yake nema.Ya gane abinda take son cewa so take ta gaida shi, ko me ya kawo well done a tsayuwar da yayi.dan haka Murya k'asa k'asa ya amsa mata,Indo ta washe mai baki tare da matsawa kusa da shi yayi saurin daka mata tsawa ganin yadda take shige mai.kallon sa tayi cikin mamaki ido waje ta kuma bin sa kafin tace.
"Malam Sadeeq baka gane ni bane?Indo ce fa ta makarantar gwamnati ta nan unguwar d'an Awaisu. Ka gane ni? Nan tsefawa fa gwamman sakandare sukul." (Tsefawa government secondary school).
"Ke! Naji me zan miki ne..?!"
Ya fad'a cikin k'ufula domin ta kai shi bango. Ita ma share shi tayi da masifar tashi da yake mata domin tana son yi mai tambaya wadda take son jin amsar su daga bakin sa dan haka masifar shi ba za ta d'aga mata hankali ba. kusa da k'afar sa ta k'ara sa haushin ta ya kuma zuwar mai wuya, tsoran sa d'aya kar 'yan kauyan suyi mai muguwar fahimta sai kauce mata yake amma ta kasa ganewa ya kuma had'e rai amma ko ajikin ta tace.
"Malam tsakanin ka da Allah gaskiya da gaskiya zaka gaya min, shin ku 'yan biyu ne, ko kuwa dai ni kake bawa tsoro sabida ina kwaikwayon ka a aji...?!"
Wata uwar harara ya narka mata dan yaga alamar kamar zata kawo mai rai ni shi kuma bezo garin dan su raina shi ba, wato ma k'arya yake mata shine zata zo ta k'ure sa dan tsabar ba ta da kunya. Fuskar sa a murtuke ya kalleta yace,
"You're very stupid."
Tana dariya cikin nishad'i tace,
"Sanki u malam Sadeeq, (thank you) wallahi shi yasa kake birge ni sabida ka iya turanci mai kyau da dad'i. Amma dan Allah malam ka d'an fassaramin abinda ka fad'a da hausa he nima in rik'e gurin na iya sosai..."
"Zaki bar gurin nan ko sai na 6allaki... mara kunya fitsararriya kawai.."
Ya fad'a cikin d'aure fuska. tayi baya-baya tana kallansa tare da kama ha6ar ta tace,
"Kai malam! masifa, daga tambaya sai cibi ya zama k'ari shi kuma k'ari ya zama k'ababa. na tafi kuma ba zan je makaranta ba a-he, sai ayi kuli-kulin tara sisi dani.."
Ta yi maganar tana tafiya da baya da baya har ta shige lungun gidan su Maryam. tsaki yayi ya koma cikin gida yayi kudurin sai ya gyarawa 'yan makarantar zama. kowa tayi wa dan ba ta je makaranta ba oho mata. yara sai rashin kunya basu san komai ba dak'ik'ai zai nuna musu shima bashi da mutunci. Ranar haka ya wuni yana kunci jefi-jefi yakan yi tsaki har dare yayi be fita ba sabida takaicin Indo da sanya idon 'yan gari domin fita dubu shiga dubu sai sun kalle shi gashi ya tsani saka ido cikin lamuran sa.
Washe gari da yaje makaranta Indo bata je ba yaga ashe da gaske take yi, still wata washe garin tayi nan ma babu labarin Indo sai ranar juma'a yana tsaye wajan black board yana koyarwa kawai yaji ana magana a taga, juyawa yayi sai yaga babu kowa domin da taga alamar zai ganta sai tayi saurin yin k'asa, dan haka ya cigaba da abinda yake yi. Can ya kuma jiyo kus-kus yayi a hankali ya kalli gurin caraf suka had'a ido da Indo tana cillowa Sa'ade wani abu a leda, dariya ta sakar masa ya k'arasa bakin tagar yana kallonta. Sanye take cikin house wear hannunta rik'e da faranti an jera kallik'ak'au da yajin masau da alama shi ta cillawa Sa'ade ya had'e girar sa tare da cewa.
"Zo nan..!"
Ita yake kallo amma sai ta juya wai ko zata ga wanda yake kira amma sai taga babu kowa sai ita, dashare mai baki tayi tare da d'an matsawa kad'an ba sosai ba tace.
"Gani malam."
"Jeki zaga yo ta k'ofa."
Ya fad'a, Indo ta tsuke fuska tare da cewa.
“Malam ai ba zuwa nayi ba yau d'in ma tallah nake yiwa mak'ociyar mu. Kasan idan na siyar mata mawa zata bani?”
Yayi mata banza ganin ita yake kallo yasa ta juyawa ta dafe abubuwan cikin farantin ta ruga da gudu dan ba zata yadda taje ya hana ta fitowa.
Kai ya girgiza tare da komawa ya ci gaba da yin aikinsa kuma a kwanaki biyun alhamdulillahi suna ganewa, tamkar dama Indom ce ke hana su rashin fahimta. Yana gamawa ya fita ya koma ofis haka ya dinga ci gaba da koyar musu har aka kusa fara jarabawa wadda daga ita zasu wuce j.s 2 amma Indo bata sake zuwa ba shima har ya manta da ita har ya Saba ma idan yana kiran suna ya samata absent.
Ana gobe za'a fara jarabawa Indo ta dawo makaranta. washe gari aka fara musu sai da suka yi jarabawa hud'u sannan a ta biyar d'in zasu yi English language wato subject d'in malam sadeeq. Kasan cewar tun da aka fara beje ajin ba sai yau da za'a yi tashi jarabawar kuma dole sai yabi aji-aji ya kuma yi musu bayani sannan. Tare da Abubakar suka shiga domin lokacin yazo abinsu gwanin ban sha'awa, zasu gaida su Sadeeq ya hana dan karsu yi hayaniya, can k'arshen aji INdo take ta duk'ufa sai satar amsa take yi cikin littafin Ayuba mati sabida ita bata da ma littafin bare tayi karatu.
Tsayawa Sadeeq yayi a gaban alo domin shi bema san ta samu damar zuwa ba ya fara musu bayani. Malamin dake tsare su yana zaune a kujera Abubakar yana tsaye ya hango wata ko d'agowa ba ta yi hakan yasa shi k'arasawa gurin da take ya lek'a yaga meke faru sai yaga ta bud'e littafi sai kwafa take yi har ta kusan cika shafin farko.
"Ke.....!"
Taji an fad'a dai-dai kunnan ta. tsoro da razana yasa ta sakin tusa burtt ba tare da ta shiryawa hakan ba 'yan aji suka kwashe da dariya ita kuma ta zaro ido ta fara rantse-rantsen kare kai.
"Malam wallahi tallahi...."
Da sauri ya kifawa bakin na ta mari tayi saurin toshewa da hannun ta. matsawa yayi tare da nuna mata hanya yace.
"Fito waje kafin na yayy-yaga ki a gurin nan 6arauniyar amsa.."
"Wallahi mal..."
Zata tsaya yi mai gaddama ya yi saurin fin ciko ta tare da tura ta gaban ajin tayi taga-taga zata fad'a kan tebur Allah ya temake ta tayi saurin sanya hannu. Kwal-kwal idanunta suka kawo ruwa zata yi kuka Abubakar ya k'arasa gurin yace.
"Shanye shi, idan kika bari hawaye suka fito sai na zane ki 6arauniyar amsa."
Maida hawayen tayi tana nan tsaye har Sadeeq ya gama yi musu bayani sannan ya kalli Abubakar hace,
"Twinnie bar yarinyar nan ko tayi ba dubawa zan yi ba sabida ta yaye kanta ba zuwa take yi ba tayi degree yanzu sai zuwa tallah."
"Ohhh! No-wonder ashe dak'ik'iya ce, amma baki yi halin asalin me sunan ba shame on you.. Kawo wannan ta hannun taki da kika sato amsar, ki d'akko sabuwar pepper kizo nan ina jiranki."
Tafiya tayi tana gunguni tare da murgud'a musu baki, sabuwar takarda ta d'akko tare da biro taje ya nuna mata gaban alo yace.
"Zauna kiyi anan."
Kallon gurin tayi sannan ta turo baki kai da kagani kasan zai yi fitsara tace.
"Toh malam ai babu abin d'orawa kuma yagewa takardar zata yi"
Ba tare da ya kalleta ba dama Sadeeq ya fita yace, "ki d'ora akan cinyar ki kiyi."
"Amma malam ai..."
Wata uwar harara daya yi mata ne yasa ta had'iye sauran maganar, zama tayi tana zumbura mai baki yace.
"Idan kika sake kira na da malam sai na fasa miki baki."
Bata sake kula shi ba ganin yafi malam Sadeeq zafi da saurin kai duka, har kowa ya gama ya fita INdo tana zaune a gurin sai raba ido take yi gashi bata rubuta komai ba sai jagwal-gwalo. Ganin bata da niyar kawowa ne yasa Abubakar k'arasawa wajan tayi saurin cukwaikuye takardar ya mik'a mata hannun alamar ta bashi amma taki,
"baza ki kawo ba mara kunya?" Baki ta kuma murgud'awa mai aikuwa ya sanya k'afarsa ya doke shi da takalmin sa. INdo ta kurma wani uban ihu tare da fad'uwa k'asa tana ihu tana birgima.
Sunkuya wa Abubakar yayi ya d'auki takardar ya sanya cikin sauran tare da bawa invigilator d'in, ko takanta be kuma bi ba sai ma tsallake ta da yayi yabar gurin.
Ihu ta kuma saki tana shure-shure har daddaud'an pant dinta ake gani sabida wandon makarantar ya yage d'alibai suka zagaye ta ana bata hakuri da kuma masu yi mata dariya amma bata fasa shure-shuren ba shima malamin yayi tafiyar Sa dan yasan INdo sarai hakan yasa be kulata ba.
"Allah ya isa ban yafe ba mugaye kawai anyi satar amsar, shi dama ba malamin muba yazo yana cin zalin mutane..."
"Hahaha INdo me tusa burtt..."
Uba Aminu ya fad'a yana nuna ta yana dariya, ai kamar jira take yi ta mik'e tare da cakumar sa suka fara fad’a. K'arfi ba d'aya ba shi namiji ya dinga gwarata da alo jikake k'um...k'um amma tak'i sakinsa sabida tsabar jaraba, can akaji Uba ya rushe da wani irin ihu mai had'e da kuka.
"Kai..kai...kai! Lafiya meya faru haka.?!"
Malam Zubairu daya zo wucewa yaji ihu ya tsaya yana tambaya.
"Malam fad'a suke yi."
"Waye da waye?!"
"INdo da Uba."
Ihu Uba yake yana hawaye gashi ya rik'e gaban sa, malam Zubairu ya kallesu ganin INdo na rik'e kugu yasa shi cewa "ku biyo ni ofis yanzun nan."
Abokan Uba suka kamashi suka kaishi k'ofar staff room, ita kuwa tahowa tayi tana bugun cinya alamar bala'in be k'are ba taje ta tsaya malam Zubairu yakai takaddu ya ajiye sannan ya fito dan jin kanun zance, be fara bawa INdo damar magana ba yace Uba ya fara yi amma ya kasa sai shasshek'a yake yi da kuka.
"Ke kuma gaya min gaskiyar abinda ya faru."
Dai-dai lokacin Sadeeq da Abubakar suka fito daga cikin staff room, tsayawa suka yi Abubakar na waya ta fara baya ni.
"Tonona yake yi shine muka fara fad'a."
"Sai kuma aka yi yaya..?!"
"Sai kazo kace mu biyo ka."
"Kai Uba me yasa ka toneta gashi ta saka kuka..?!"
"Malam cizo na tayi a anan."
Ya fad'a yana nuna gurin, duk wad'anda ke gurin suka zaro ido Abubakar dake waya ya zare ta daga kunnansa yana kallon INdo cikin tsananin mamaki yace.
"Ke mayya ce? Baki da hankali?ke wace irin yarinya ce ne da kika fitini kowa ne? Stupid,nonsense, what a fool wawuya kawai, mai wasa da maza karya.."
Haushin maganar sa da kuma turancin da yake yi bata jinsa yasa ta fara murgud'a baki tana motsa lab6anta alamar magana take yi, da sauri Abubakar yayi kanta zai ham6are ta Sadeeq ya rik'osa yana kad'a masa kai alamar kar yayi yayin da zuciyar Abubakar d'in ke tafasa yanajin wani tururi cikin ransa dan yaki jinin rashin kunya da k'in gaskiya. A hankali Sadeeq ya dafa kirjinsa yana kalon INdo wadda ta makure jikin karfe tana jiran jin saukar duka yace...
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:48 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
Page *4*
"Aisha zo ki bawa yaron hakuri."
Tamkar ba taji ba sai faman wasan ta take yi da k'asar gurin da d'an yatsan ta wanda alama ce ta baza ta bayar da hakurin ba ya kuma cewa.
"Aisha ba magana nake miki ba kika min shiru ko..?!"
"Malam fa shine ya fara tono na kuma sai na bashi hakuri ta6di jam.."
"Duk da haka ki bashi hakuri tun da kin yi mai ba dai-dai ba.."
"Hu’...uhm." Ta fad'a cikin k'asan mak'oshin ta, Abubakar yayi kamar zai wuce kawai yayi wuf ya dank'e ta, nan da nan ta fara ihu har wasu malaman suna sake fitowa ya damk'eta ta 6are baki tana ihu yaji wani sumumin wari ya fito daga bakin ta yayi saurin kawar da kai tare da hankad'a ta saitin Uba ta fad'i k'asa bata San lokacin da ta furta.
"Allah ya baka hakuri Uba kayi hakuri kaji ka hakura..?!"
"Eh." Uba ya fad'a yana share hawaye malamai aka yi ta yiwa Indo fad'a akan karta sake yin fad'a da Namiji sannan aka sallame su. Ana tashi daga makaranta babu wanda Indo ta kula tayi wuce warta, ba gida ta wuce ba kai tsaye ofishin 'yan agaji ta nufa tana zuwa ta sami ogan ya kalleta yace,
"Yarinya ya aka yi aiko ki aka yi..?!"
Tace "A'a shugaba k'ara na kawo dan ance shari'ar maita bata k'arewa toh wani malamin mu ya Ce min banza maiya jaka, toh ban yafe bane shi yasa na kawo k'ararsa abi min hakkina."
"Au ke cema kika kawo k'arar?"
"Eh sabida ance nan ake kawowa kafin akai kotu."
Sosai ya kalli INdo wadda take faman turo baki tana taunar k'asan hijabin ta da hak'ori.
"Toh naji yanzu shi malamin yana ina kuma a wacce makaranta yake koya muku duk da naga inifam (uniform) d'inki na makarantar tsefawa ne...?!"
"Eh Shugaba acan nake kuma ma shi ba malamin mu bane d'ayan ne malamin mu amma kaga ya mareni, yayi min kutufo da k'afarsa sannan yace min Mayya, ance shira'ar maita baya k'arewa toh yazo ya fad'a a ina nayi maitar."
Shugaban 'yan agaji na k'auyan ya sake kallonta sannan yace,
"Ya sunan ki...?"
Tace "INdo malam Hamza."
"Toh INdo yanzu abinda nake so dake nasan yanzu an tasheku ki bari gobe idan Allahu ya tahemu lafiya he muzo ki nuna mana hi malamin kin ji ko.?!"
"Kai! Shugaba, ai tafiya yake yi kuma idan an gama jarabawa ba dawowa zai yi ba a hanyar gidan mu suke kayiwa Allah kayi ma ma'aiki kazo muje ayi Mai jan kunne ya dena ce min mayya da dak'ik'iya."
"A'a bada ni zakuje ba bari nasa wani yabiki suje yaji abinda ke faruwa."
Ya d'aga murya yana k'iran, "Awaisu! Awaisu!!, zo dan Allah kabi yarinyar nan ta kawo k'arar wani malamin su." Awaisu na zuwa suka tafi suna tafiya suna hira tamkar dama sun saba har suka k'arasa k'ofar gidan su malam Sadeeq wanda shigowar su kenan dan sai da suka tsaya suka yi juyan bak'in mai.
"Kika ce nan ne gidan ko?"
INdo tace "Eh nan ne suna ciki."
Kwan-kwan-kwan, Awaisu ya fara buga k'ofar gidan yana kwad'a sallama. Malam Sadeeq ne ya fito sanye cikin jallabiya ya kalli INdo sannan ya kalli Awaisu cikin rashin fahimta da kuma sanin dalilin zuwansu ya fara magana.
"Lafiya dai ko bawan Allah."
"Eh toh lafiya ba lafiya, wannan yarinyar ce ta kai k'ara cewar kana ce mata mayya. Toh bata yafe bane yasa takai mana k'orafinta shine shugaban mu yace nazo naji dalilin da yasa kake fad'a mata wannan kalmar."
Mamaki da al'ajabi suka cika Sadeeq, sai yanzu ya k'ara tabbatar da hauka da rashin hankalin 'yan garin ya kuma kallon INdo wadda itama shi take kallo yayi shiru yasan Abubakar ne dan haka ya tsaya yana tunanin abin cewa yaji INdon tace.
"Awaisu ka tambaye hi idan shine idan kuma ba hi bane toh d'ayan ne ya fito dan tagwaye ne.."
Kallonta Sadeeq yayi ya sake tabbatar da lallai bata da kunya, shi kuma Awaisu sai d'aga kai yake yana kallon gidan ko zai ga wani ya fito amma ba kowa hakan da sadeeq ya gani ne yasa shi cewa.
"Naga alamar baki da kunya Aisha, toh bazai fito ba ki shiga ki fito dashi fitsararriya kawai. Kai kuma SS ne ko d'an sanda ko soja ko menene da ta d'add'ago ka kuka zo nan..?!"
"A'a mu mune 'yan kungiyar agaji na wannan kauyan kuma turo ni aka yi akan naxo naji abinda yake wakana dan tace bazata yadda ba."
Cewar Awaisu Sadeeq yayi tsaki cike da takaici sannan yace,
"Toh kaji abinda na fad'a idan ba maita ba waye zai ciji mutum a mafitsara? Kuma ma wai fad'a mace da namiji dan iskanci."
"Haka ne kam malam kana da gaskiya ke INdo baki da gaskiya dan haka zanje na sanar cewa ga abinda ya had'a dan haka sai ki tafi gida ki dena wannan halin."
Awaisu na gama fad'ar haka ya bawa Sadeeq hakuri sannan ya juya ya tafi INdo na kallonsa zuciyarta fal haushin sa. Da taga yayi nisa ta juya zata yi magana sai taga ashe shima Sadeeq din ya shiga ciki ta d'aga murya saitin k'ofar tace.
"Kujini da kyau ni ba mayya bace sai dai kunemi mayya, kuma an dena zuwa bokon ai ba aikin Allah bane rawawul ni INdo na dena zuwa tsefawar yo dan banje ba ai ba mutuwa zanyi ba kuje ku cinye makarantar..."
Suna jinta suka yi mata banza Abubakar ya shak'a iya shak'a Allah-Allah yake ya shirya yabar garin dan takaici. Ita kuwa tana gama fad'a tayi tafiyar ta gida tana zagin su tare da d'aura aniyar baza ta sake zuwa makarantar ba tunda ai sai taje zasu ganta har suyi mata maganar banza.
K'arfe 3:34pm Abubakar ya idar da alwalar la'asar yana jiran Sadeeq su wuce masallaci dan da sunyi sallah yake son dawowa ya wuce gida. Jerawa suka yi suna tafiya suna hira abinsu gwanin ban sha'awa mutane sai kallansu ake yi.
Sagiru dake tsaye a k'ofar gida ya hana INdo fita ya tsaya yana kallonsu, ita kuwa INdo ganin yace baza ta fita ba yasa ta komawa cikin gida. Dai-dai katangar gidan zasu wuce kawai Abubakar yaji an cillo wani abu ya rufe mai fuska suka tsaya ya cire yana dubawa yaga hijjab ne yayi dik'il-dik'il dashi ya yarda shi, kafin ya kuma yin taku d'aya yaji an kwad'o mai wani abu a gefen wuyan sa ya kalli k'asa takalmi ne d'an madina silifas yasha d'aurin leda a wajan sanya d'an yatsa suka kalli katangar da ake yo jifan kawai sai suka ga hannu hakan yasa ran Abubakar ya kuma 6aci sai ga k'afa can sai gata ta dirgo tim...!
Da sauri suka matsa inda take tana d'agowa ta gansu a tsaye a gabanta bata san lokacin da ta kuma kurma ihu ba tare da juyawa zata kuma kama katangar ta koma gida Sadeeq yayi saurin janyo rigar ta mutane suka taru yayin da INdo ke faman basu hakuri.
Gabaki d'ayan ta tsami take yi da zarni Abubakar ya tsinketa da mari tare da dungure mata goshi sannan Sadeeq ya sake ta Abubakar yace.
"Baki da mutunci ko?Ke mara kunya kinga abubuwan tsimmar da kika watsa min? Toh ki saita kanki idan ba haka ba kafin nabar garin nan sai na ji miki ciwo idiot kawai sai zarni kike yi mai fitsarin kwance jibe ki dan Allah da wani billanki a goshi kamar zanan one..."
Yana kaiwa nan yayi gaba yayin da Sadeeq ya harare ta shima yayi tafiyar sa suka shige masallaci. Mutane kuma suka k'arasa wajan INdo da tayi shiru tana kallon jikin ta.
"Kedai INdo wallahi kowa sai yace baki da kunya, suma bak'i har kin fara yi musu.."
Cewar Rabi bala wadda makarantar su d'aya amma ita a js 3 take, INdo ta harareta tare da cewa.
"Anyi d'in kizo kiyi kuli-kulin tara sisi dani munafuka kowa yasa dake.."
"Ke INdo dan ta gaya miki gaskiya shine zaki mata rashin kunya."
Wani yaro Bala ya fad'a ta kuma juyawa kanshi cikin masifa tace, "ji banza kai tunda ga kan sunanka ansan kai d'in bala'i ne banza Bala bala'i mtwww."
Nan da nan gurin ya kaure ita kad'ai su kuwa wajan mutum goma amma babu wanda ta ragawa, Sagiru k'aninta ya jata suka shiga gida sai da suka kai har tsakar gida sannan ta ture shi. "Dalla can ni kyale ni banza."
Ruwa ta kindima a buta ta shiga band'aki shi kuma Sagiru ya kuma fita waje yana cewa,
"Dama na barki sunyi miki shegen duka masifaffiya kawai."
Fitowa tayi jikinta sharkaf da ruwa wanda da alama wanka tayo amma ba a saka sabulu ba. Cikin d'aki ta shiga Inna tana sallah ita kuma taje ta sake kaya sannan ta d'an d'ibi man shanu ta shafa dama tana sato chuck ta d'auki d'aya ta daddaka tayi hoda da shi ta shafa tayi kwalliya jagirar nan har wajan kunne ta sanya kantakile a lab6anta sannan ta d'aura d'an kwali tayi waje Inna na ta faman kiranta amma ko waigowa bata yi ba.
K'ofar gidan taje ta zauna tana jiran su dawo, ana idar da sallah suka dawo gida tun daga nesa suka hangota kamar aljana dariya ta kusa kama Sadeeq ya daure yak'i yi a fili yayin da yace wa Abubakar.
"Twinnie ga tanan fa kayi mata gorin wanka tayo tazo ta nuna maka." Dai-dai suka je k'ofa Abubakar ya kalleta wani takaici ya kuma kamashi INdo tace.
"Gani yanzu kunsan abinda yasa bana kwalliya? Sabida mazan garin nan sun fiya kallona shi yasa amma ni bana zarni."
Ta fad'a tana bubbuga kanta tare da sosawa, mtwww "ke wai kinga sa'anki anan gurin ne?"
Kallon shi tayi tare da kura mai ido tamkar zata cinye sa ya d'aga hannu kamar zai bugeta tayi saurin matsawa tace.
"Yoo ni ina ruwa na wannan ai ba wasa bane kuma idan anyi duniya da manzo na dena zuwa makaranta wata za'a sake min irin ta 'ya'yan gidan kansilan mu."
Mtwwww Abubakar ya ja tsaki tare da shigewa gidan, itama ta doka cinyarta ta kalli Sadeeq tace "Duk haka kuke babu me imani."
Sadeeq ya bita da kallo yana tunanin k'ila tana da aljanu yace.
"Kije kiyi brush."
Abubakar daya fito da car key dinsa yace.
"Bakin ta kamar kashi. Kinga yadda ake son aga hakora ba irin naki ba kamar kina shan d'orawa."
Ya fad'a yana nuna mata hak'orinsa fari kal. Wucewa yayi gurin motar sa Sadeeq yabi bayan sa dan suyi sallama, suna kallon sanda ta wuce tana sanya k'asan hijabin ta tana goge hak'orin. Sallama suka yi abubakhr na sake bawa Sadeeq shawarar ya k'arbi transfer ya k'ara da cewa.
"Bazan sake zuwa garin nan ba sai dai na hakura har ka dinga zuwa can gida ma dinga had'uwa amma wannan garin beyi min ba."
"Insha Allahu doctor karka damu kayi min addu'ar abinda yafi alkairi."
"Toh amin ni na wuce."
Suka yi sallama ya tafi shima ya Shiga gida. Tunda ga ranar kuwa har aka yi hutu Sadeeq be sake ganin INdo a makaranta ba sai dai a unguwar su ya ganta suna wasa ko da farantin tallah..
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:49 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
Note:- Assalamu alaikum masoya wannan labarin, dan Allah adalci d'aya zaku yi min idan kuna so toh ku ringa adanawa. Idan nayi nisa kuka ce na turo muku sai na rasa yadda zanyi gashi wayar ba lafiya gareta ba dan Allah kuyi min wannan agajin please.🤭
Page *5*
Tafiya take tana dirzar hak’oran ta da k'asan hijjab ko zata samu suyi fari itama, ai kuwa da ta gogo zata duba jikin hijjabin taga gurin yayi yellow ta girgiza kai tare da cewa. "Kai...! Kuma fa da gaskiyar sa wallahi, dan gahi ina kankarowa yalo na fitowa, amma shi hak'oran sa har wuta-wuta suke yi sabida kyau."
Wani shago ta tsaya a nan kusa da gidan su Sahura ta kalli me shagon tace.
"Idirisu kana siyar da burushi da abin matsawa...?!"
Yace "A'a bana siyo shi INdo sabida ba'a siyan shi, sai dai kije kasuwa ranar laraba ki siyo."
Tsaki tayi tare da fad'awa gidan su Sahura, ita dai sam ba ta son zaman gidan su domin bata ta6a yin cikakkiyar awa d'aya sai ta fita, bata taya Inna da aikin komai sai dai da taji yinwa taje taci idan ba'a gama ba ta hau sababi. Sai kusan magariba sannan ta koma gida shima dan tana son tambayar baban su kud'i zata je mahad'a wato inda 'yan mata da samari ke had'uwa suyi hira.
"Baba sannu da gida."
Yana jin haka ya san akwai abinda zata tambaye sa dan haka yayi mata banza, ta kuma fad'a sai ya d'aga mata kai kurum ta ciza yatsan ta cikin ranta tace,
"Wallahi sai ka bani abinda nake so, kaji shi daga gani na baba yayi wani shiru."
Kusa dashi ta k'arasa ta zauna shi kuma da yake a kishin gid'e yayi saurin dan ne aljihun sa me kud'in a ciki dan ya san tun da ta fara wannan shisshige mai d'in toh rok'on sa zata yi shi kuma naira d'ari da sittin ne garesa kuma goma ba zai bata ba dan yau da kyar ya samu a gurin sana'ar sa. INdo ta cire hijjab d'in jikinta sannan ta kalli mahaifin nasu duk da ya had'e rai hakan besa taji zata fasa tambayar Sa ba, cikin rashin ladabin magana ta kallesa tace.
"Baba nera (naira) hamsin zaka bani anjima zanje mahad'a, daga can idan naje kaga zan siyo burushi harda abin matsawa sai kuma ka bani nera ashirin wadda zan siya abubuwa naci.."
"Bani da kud'i uwata yanzu, amma ki bari gobe idan na samu zan baki."
Kallonsa tayi da alama bata yadda da abinda yace ba, ganin tana kallan sa yasa shi kuma kishin gid'a kan aljihun kud'in yana k'ara volume d'in rediyon sa duk kuwa da yana jin ana k'iran sallar magriba amma ba shi da alamar ta shi yayi alwala.
"..'Yar nan zo kije kiyi alwala bana jin yauma ko sallar asubahi kinyi bare kiyi sauran." Inna ta fad'a tana kashe wutar kararen da ta gama tuwo. INdo naji ta turo baki sam bata kaunar taji ance tayi wani abun a harkar rayuwar ta abu in dai ba wasa bane ko kuma naci toh sam bata kaunarsa bare tayi. Bacci ma ban da 6arawo ne da baza ta dinga yi ba, ta mik'e tsaye ta shiga d'aki ganin baban nasu bashi da niyar bata ko sisi.
Garam-garam inna ta jiyo ta tana tatta6a mata kwanukan jeranta na d'aki, saurin bin bayan ta tayi nan taga sai faman bud'e-bud'e take yi mata cikin fad'a inna ke magana tana kallon INdon tace.
"Me kike nema anan? Ko kinyi ajiya a gurin ne zaki d'auka..?!"
INdo ta ajiye kwanon hannunta kana ta kalli Innar ta tace, "Inna fisabilillahi baba ba zai bani kud'i naje mahad'a ba, salan naje naga su maryam su sahura Sa sauran k'awaye na suna siyan abubuwa su yi min gori...?"
"Toh banda abinki baya ce miki babu ba idan ya samu zai baki, toh kiyi hak'uri mana nima kuma basu gare ni ba bare na baki."
K'ad..! INdo tayi da harshe alamar jin haushi sannan tayi waje fuuuuu babu wanda ya kula ta shima baban nasu yana ji ana k'iran sallah amma ba shi da niyar tashi yayi yana kishingid'e abin sa. Tana fita ta shiga gidan Rukayya wadda amarya ce aka kawo ta unguwar take yin kayan siyarwa su alawar madara, gullisuwa, k'alli-k'a-k'au, yajin masau da dai sauran kayan siyarwa na yara, shine INdo take zuwa ta kar6a tana siyar mata sai ita kuma ta ringa bata ladan nera talatin ko asshirin da biyar.
"Uhm su INdo sai yanzu aka ga damar zuwa ko..?!"
Rukayya ta fad'a tana kallan ta, zama tayi a kan tabarma tana dariya Rukayya ta idar da alwala tazo ta zauna kusa da INdon tana kallonta tace "Toh me ya hanaki zuwa yau da wuri gashi ma har an siyar sabida yau na samu 'yan sari duk sun siye sauran albishir kawai na naira tamanin.."
INdo ta zaro idanuwa tare da dafe k’irjinta yau kenan ba ta da kud'in siyan gyad'a, cikin karad'i tace, "kai Rukayya amma ko ki jira nazo ba komai tun da abin 'yar haka ce..!"
Rukayya tace "A'a INdo ina zan ta jiranki bayan har gidan Ku na tura kizo aka ce min bakya nan, sai kawai na zauna jiranki bayan ga kustoma sun zo.."
"Ai shikenan yanzu ki bani albishir d'in na tafi dahi.."
Shiga cikin d'aki Rukayya tayi ta fito hannunta rik'e da leda ta mik'a mata. k'ar6a INdo tayi ta lek'a cikin ledar sannan tayi dariya cikin ranta tana addu'ar Allah yasa yau ta had'u da Shu'aibu saurayin ta ya ce ta shanye ya biya kud'in. Mik'ewa tayi tasa takalma tana cewa Rukayya.
"Toh na tafi sai na dawo Rukayya kiyi mana adda'a (addu'ah).."
Tayi dariya tana gyara hijabi tace, "Toh INdo Allah ya ba da sa'a a siyar baki d'aya."
Tana fita ta d'auki guda d'aya tare da jefawa cikin bakin ta, zak'in ya gauraye mata bak'i ta lumshe ido tare da sosa cikin kunnanta. K'ofar wani shago taga malam Sadeeq hakan yasa ta k'arasa tamkar bata ganshi ba ta kalli me shagon tace.
"Wale kana sai da burushi da abin matsawa..?!"
Wale me shago yana k'ok'arin bawa malam Sadeeq klin da sabulon da ya siya yace. "Eh guda nawa za'a baki..?" INdo ta kuma kallon malam Sadeeq sai taga ko kallon tama baya yi sai kud'i da ya zaro yana k'irgawa zai bawa me shagwon ta ta6e baki. Yana sane ya zamar da naira d'ari k'asa as in be sani d'in nan ba sannan ya mik'awa wale kud'in sa ya mai da sauran aljihu. INdo na ganin kud'in tayi kamar zata d'auki dotse kawai ta d'auke d'arin ta maze sai mazurai take yi taji ko wani zai ce ya ga sanda ta d'auka, da taga babu wanda yace komai sai ta mik'awa wale kud'in tana cewa.
"Toh bani guda d'aya-d'aya ka bani canji na." Sadeeq na gani ya wuce yana mamakin ta ashe har sace-sace da d'auke-d'auke take yi, lallai yarinyar bata da tarbiya sam sai dai be san dalilin da yasa yak'i yi mata magana ba bayan ya san hakan da tayi ba dai-dai bane ba a cikin addini dama rayuwar ta gaba d'aya.
D'akko mata yayi sannan ya bata canjin naira talatin ta k'ar6a tayi gaba abinta. Cikin mararta ta tura brush da makilin d'in sannan tayi gaba tana d'aukar albishir tana sanyawa a cikin bakinta sai farin ciki take yi yau ta fito da sa'a zata yi brush ta basu mamaki gobe.
Tana zuwa zata sha kwana taji ance mata "ke zo nan." Ta juya tana kallansa ganin malam Sadeeq yasan ya ta rik'e kugunta tana girgiza jijinta tana harararsa "yes.." Ganin yadda take mai ne yasa shi kuma d'aure fuska yace mata "fito min da naira d'ari ta da kika d'auke ko kin d'auka ban ganki ba."
INdo najin haka ta gyara tsayuwar ta tare da sake danna brush d'in dan karya gani, cikin wayan basarwa tace "kai malam Sadeeq kud'in ka? yaushe na d'auka zaka ce in baka...?"
Matsawa yayi kusa da ita tayi saurin yin baya ya mik'a mata dogon hannunsa tare da bud'e mata tattausan tafukan hannun da nufin ta sako mai kud'in sa ta kallesa tana muzurai tare da tsuke baki cikin yake tace.
"Ni ban d'auki kud'in kaba, a inama muka had'u bare na gani na d'auka."
Ya kuma had'e rai sai taga yayi mata kwarjini k'irjin ta ya hau harbawa ta fara jin tsoron Kodai ya ganta, toh me zai mata ko ba malam Sadeeq bane d'ayan ne masifaffan. Ganin yak'i d'auke hannunsa yasa ta tabbatar da cewar lallai ya ga sanda ta sace amma ya aka yi be nuna ya ganta ba a gurin? Cikin borin kunya tace.
"Toh na d'auka abakacin kalamin herrin maita da kayi, ai dama nace ban yafe ba toh yanzu ka biya ni hike nan."
"Ki mik'o min kud'ina nace bana son maganar banza kina jina..."
Jin yana masifa yasa ta cewa "Toh na siyo burushi dasu ba kune kuka min wulak'anci ba, shi yasa nasiya nima na dinga yi wallahi a gobe zaku ga bakina sai yafi naku fari."
Tana kaiwa nan tayi gaba haushi da takaici suka cika Sadeeq yama rasa gane meye matsalar yarinyar sai dai yafi dan gana hakan da cewar k'ila tana da aljanu. Gida ya wuce domin so yake daya gama had'a result ya tafi gida tunda anyi hutu sai kuma an dawo wanda yake son kafin sannan ya samu canjin gurin aiki.
Cikin kwanaki uku ya kammala komai yabar garin sai farin ciki yake yi dan ba k'aramin takura yake yi ba da k'auyan.
_Fatan alkairi ga masu bibiyar wannan labarin, ina ganin sakwannin ku Allah ya bar kauna. Muje ga page d'in gaba wanda daga shi ne zaku fara gano sirrin cikin labarin._🤭
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:49 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
Page *6*
Zaune suke a cikin d'akin su, babban d'aki ne domin a da a matsayin sitting room yake lokacin da suka taso suka zama samari yasa abban su ya bar musu shi suka gyara shi aka sanya musu katifu guda biyu d'aya na gefen hagu d'aya na dama sai durowar kayan su ko wanne ya d'auki gefe d'aya domin kayan nasu ya bambanta. Abubakar shine yafi son sanya k'ananun kaya sa6anin Sadeeq daya fi son manya kamar su shadda boyal da sauran su.
Shiru Sadeeq yayi idanunsa a sama kai da ka ganshi kasan ya fad'a cikin zurfaffan tunani, kallan sa Abubakar yayi cikin ta6e baki yace.
"Twinnie ya aka yi ne kake wannan zurfaffan tunanin?"
Sadeeq ya numfasa tare da tashi zaune ya janyo kofin zobon da Maman su ta aiko musu dashi ya d'iba yasha sannan ya zuba wani ya mik'awa Abubakar yana cewa.
"Twinnie ina tuna nin maganar Mama ne ta jiya, kaga tace Abba zura mana ido kawai yake yaga dame zamu fara. Gaskiya ni yanzu na fara tunanin gara na fara yin gini na tunda ya riga ya bamu filayen kuma yace duk inda muka ga ya kakare mana toh muyi mai magana gara kawai nazo na fara dan ina son lokacin da zan fara neman aure toh ya zamto koda ban k'arasa ginin ba to ya zamana sauran k'arashe shi yasa kaji nayi shiru ina tunani."
Kai kurum Abubakar ya jin-jina sannan ya mik'e tsaye, shirin tafiya asibiti yayi ganin be ce komai ba yasa Sadeeq cewa. "Toh kai naji baka ce komai ba ka kuma tashi zaka tafi meke nan hakan da kayi..?!"
Shafa gashin kansa yayi tare da d'aukar turare ya fesa. "Karka damu twinnie da rashin maganata, kasan dole idan naga ka fara nima na fara har addu'a nake mana Allah yasa mu samu matan aure 'yan biyu kawai mu aure su, dan haka karka damu kai dai ka fara samo matar tukun na."
Sadeeq yayi dariya tare da komawa ya kishin gid'a, yana murmushi yake cewa. "Lallai kuma a ce mun had'a gida kuma kamar su d'aya like me n you, ta6 ai sai mu kasa ganewa haka kurum wata rana in dirfafi matar ka ko kai ka shigar min gona toh a'a.."
Abubakar ya kyal-kyale da dariya irin wadda be ta6a yi ba ya kalli Saddeq yana nuna shi da yatsa yace. "Amma dai my twinnie muguwar fassara gareka, babu abin da zai faru kai dai kayi mana fatan alkairi.."
"Toh ai gaskiya na fad'a ko kuma matar ka ta fito ta ganni tayi tunanin kaine tazo ta mak'ale min ni bazan hanata ba tunda jiki da jini, ko kuma tawa matar ta ganka tayi tunanin nine gaskiya twinnie ka dena yi mana fatan auran twins dan ni gaskiya ka san bani da kauda kai, shi yasa ma da Abba yace baxai bamu gida kusa da juna ba banji haushi ba."
"Hahaha twinnie ai ina tausa yawa duk wadda zata aure ka wallahi domin zata sha wahala, kana gani a yanzu ma baka da auran sai kayi dreaming sau uku hud'u bare kana ganin ta."
Murmushi Sadeeq yayi tare da gyara kwanciyar sa yace "twinnie kayi tafiyar ka kana yin late ga marasa lafiya can na jiranka ni bacci ma zanyi dan ban gama va ka tashe ni bye."
"Hmmm ka dai kore ni toh Allah ya baka mata a kauyan daka baro tun da baka son muyi iri d'aya."
"Wallahi ba amin ba, duk basu da hankali musamman ma INdo kai! wannan yarinya ba hauka ne yake damunta ba harda jahilci kasan shi yafi hauka. Gasu k'azamai tunda naje garin banga wayayye ko wayyayi ya ba wallahi, ba amin ba dan kamar yadda kake son nutsattsiyar mata haka nima nake so kuma 'yar gayu mai ilimin zamani da na addini.."
"Twinnie kad'auki zafi da yawa so sorry dan Allah, bari naje na dawo bye.."
"Ok sai ka dawo."
Da haka suka rabu sai da Abubakar ya shiga cikin gidan yayi sallama dasu Maman sa sannan ya fita, yayin da Sadeeq ya kwanta duk da cewar maganar da d'an uwan nasa ya fad'a tasa baccin ya gudu sabida takaici hakan yasa ya tuno da INdo yaja tsaki tare da mik'ewa ya koma cikin gida ko zaiji dad'in ranshi a gurin su Maman su.
*IHSAN MEDICAL CENTER*
Ahankali yake karasawa asibitin na ihsan medical center dake unguwar sultan road nassarawa gra agarin na kano,sanye yake cikin kananun kaya kirar suit blue tacikin kuma fara ce hannunsa rike da jakar laptop d’insa fuskarsa sakale da farin glass se bulbula kamshi yake haka yashiga harabar asibitin,yana shiga ya hango nurse hidaya k’ok’arin juyawa yake ta cinmashi da sauri,
“Welkm Doctor,Ina kwana..?!”
“Fine Alhamdulillah nurse hidaya..”
Yana gama fada yai gaba ya barta wajen
Office d’insa ya nufa inda sunansa ke rubuce boldly ajikin k’ofar office din
‘Dr Abubakhr’ kamar kullum Mani Cleaner ne aciki yana tsaftace office din se mopping terrazzo din yake dake ta shekin kyalli,da sauri Mani ya tsugunna yana kwasar gaisuwa
“Sannu da xuwa yallabai Barka da safiya”
“Barka dai Mani.”
Kan kujera dr abubkhr ya xauna yana dudduba files din kan tebur din one by one,har Mani yakarasa ya feshe office din da freshener,
“Yallabai na kammala”
“Yawwa Mani godia nake xaka iya tafiya”
Har Mani yakai kofa yadawo yana sosa keya,
“Yallabai anbani sako wajenka amma wallahi na sha’afa da sunan,nurse dinnan ce de da tai transfer daga Cotonou”
Sarai abubkhr ya gano wacece naccaciyar yarinyar data nace masa ce,
“To Mani ba damuwa tunda kamanta sunan kaje kawai”
Shiru Mani yai da alama ya zurfafa tunani be jima ba ya dago yana murmushi,
“Yallabai natuno nurse natasha ce da sassafe xuwana kenan tabani sako nabaka nikuma hartamin alkhairin Naira dubu yallabai”
“Toh madallah”cewar Abubkhr tareda shan kunu
Kyakkyawar farar takarda datasha xanen heart Mani ya ajiye akan tebur se faman sosa keya yake don wannan bashine karo na farko ba da nurses suka sabayiwa ogan nasa haka,cikin dakakkiyar murya Abubkhr yace
“Jeka Mani sena neme ka..”
“To Yallabai Nagode ahuta lapia..”
Mani nafita abubkhr yaja tsaki ko duban takardr beyiba ya mike don yin round na patients fitarsa kenan suka kusan yin gware da nurse Deexah uniform dinnan sun matse koina na jikinta ya bayyana se wani rausaya take tana karkada jiki,
“Dr..Pls”tace hakan cikin wata irin siga
“Please what ?!inada patients daxan duba pls..”yakarasa hade da kaucewa ta gefanta xe wuce tai hanxarin shan gabansa bayan tahada tafukan hannayenta biyu sama alamar roko,
“Dan Allah dr ka saurareni minti d’aya pls”
Allah data ambata yasanya shi tsayawa ba tare daya karasa tafiya ba amma bejiyo ba fuskarsa kan agogon dake daure a hannunsa yana jiran minti dayan ta cika,
“Ki magana kafin minti dayan ki tacika pls”
“Dr Meyasa kake mun haka? Kaso me sonka,ka agaxawa xuciyata kaceto ta daga fadawa kogin halaka,duk asibitin nan babu wanda na xaba amatsayin wanda zuciata take muradi sekai”
Karasa maganar ta yayi dede da cikar minti dayan data ambata don haka yai gaba abinsa yashiga bin round na patients sedaya kammala tsaf sannan yashiga office din abokinsa wato dr luqman,
Sundan taba hira sunayi suna tafawa sannan luqman yashigo da wata hirar,
“Nikwa Abokina nagaji da kawo korarrafin da ake kawomun akanka wlhy,yanxunnan nurse deexah tafita hawaye kwance shabe shabe kan fuskarta dukde akan ka,dama yanxun nake maganar koba ka shigo ba xanxo na sameka don nikam nagaji”
Murmushin takaici Abubkhr yayi cikin nutsuwa yace,
“Toh Aboki bani shawara shin mexanyi akai?”
“Ni Ina ganin kaxabi d’aya kawai ka aura kaga ai dole sauran su kyale ka ko?!”
Ajiyar zuciya Abubakhr yai kafin yace,
“Gaskia Aboki kabani mamaki wallahi domin bantaba saka a sahun mutanen daxasu bani shawarar naxabi d’aya daga cikin nurses dinnan na aura ba,karka manta duk wani namiji yana sone ya auro yarinya yar mutunci me dattako da sanin yakamata wadda ‘yayan daxata haifa ma xasuyi alfahari da kasancewarta uwa tagari,
To axahirin gaskia de magana d’aya ce xanyi wallahi duk cikin nurses dinnan babu wadda xan iya xaba a matsayin wacce xan dauka nakai ta gidana wai amatsayin matata ta aure,Kowa Allah ya hadashi da rabonsa kawai ko ya kagani?!”
Shiru dr luqman yai yana cin faratansa da alama yarasa tacewa,knocking akai a kofa har sau uku hakan yasanya abubkhr bada izinin shigowa bayan yace,
“Yess”
Shigowa tai sanye cikin abaya baka bakinta dauke da sallama hannuwanta rike da files cikin siririyar muryarta kamar anbusa sarewa tace,
“Gashi Doctor,duk nagama komai har room 13 dakace nayi mata inducing ruwan..”
“Okay nurse Mareeyah thank you..Xaki iya tafiya”
Dama abinda Mareeya ke jira kenan tai hanxarin ficewa abinta,baki galala abubkhr yabude yanabin k'ofar data rufe da kallo kafin yadawo da kallonsa kan Doctor luqman cikin sauri yace,
“Dr ai naxatan nurses d'innan sun gama aikinsu sun koma ya kuma Naga wannan?!”
“Oh mareeyah riketa mukai wallahi yarinyar ta iya aikinta ga hankali da nutsuwa wallahi ba ruwanta da shiga harkar mutane kullum ita kad’ai xakaga tana aikinta”
“Mareeyah..”Dr abubkhr ya maimata sunan
“Kwarai sunanta mareeyah..A’a kode kafada’a da...”ai luqman ne k’arasa ba abubkhar yai hanxarin ficewa
Cikin sa’a ya hangota tsaye a corridor tana shimfida sallaya xatai sallah,
“Salam alykm..”cewar Abubkhr daga bayanta..
“Wa alykm Salam”tabashi amsa tana k’ok’arin gyara mayafin data yafa
Ya salam,,abubkhr yafurta azuciyarsa Dakyar da lalubo salati yasamu ya saisaita kansa kamar bashi ba yace,
“Dama uhm..Idan baxaki damu ba magana nakeso nayi dake”
“Babu damuwa amma xanyi sallah de tukun..”
“Tohm shikenan take ur time xanjira”cewar abubkhr
Ya jima azaune sedata idar tai addu’ointa tukun sannan ta nannade praying mat dinta ta mayar cikin jaka,
“Ina jinka dr..”
“Okay.. Sunana Dr Abubkhr..”
“Allah sarki..Ni sunana mareeyatul qibdiyya.”
“Nice name qibdiyyah,”
Nande abubkhr yashiga gaya mata meke tafe dashi da abunda ke cikin zuciyarsa,itade mareeyah kawai kallonsa take tana mamakin dama yana magana haka?!Abubkhr be bar maareryah ba har seda ya tabbatar ya dana mata tarkon son sa tukun sannan sukai exchanging numbers zuciyarsa fes yakoma gidah,
Kullum de abinda ke faruwa kenan abubkhr har gidah yake xuwa xance wajen mareeyah ashema basuda nisa su su abubkhr suna unguwar Court Road ita kuma Mareeyah tana Hausawa,Sosai suke gwangwaje soyayya abun su shikuwa sadeeq har yanzu be samu wadda ta kwanta masa ba duk ya gwada amma babu sa’a ga cuku cukun transfer dayake nema amma yakasa samu haka ya hak’ura yafara shirin komawa makarantar tsefawa dake kauyen Sani a k’aramar hukumar sumaila..
****
Ranar asabar da safe sadeeq yatasamma titin sumaila bayan yasha adduoi daga mahaifansa da kuma dan uwansa abubkhr wanda sam be so komawar d'an uwan nasa kauyan kayayau d'inba,
Yana shiga cikin unguwar kuka sunan unguwar tasu kenan ya fara jiyo hayaniya sama sama be tabbatar da muryar ba seda yaxo daf da dandaxon jama’ar da suka taru suna kallon fadan da ake ta muryarta yagane kowacece siririn tsaki yasaki jin muryar INdo ce dan turmutsawa taron yai ya hangota sanye cikin kodadd'un kayanta se jurwayen fitsari riga daban xani daban d"ankwali kuwa ba'a xancensa se tumurmusar fad'a suke da wasu yara maza kuma duk itace me karfin ciki,wani daga cikin taron ne yace
“Ke y’ar nan kome sukai miki ki hak’ura ki kyalesu tunda ke macace dan allah”
Cikin turo baki had'e da k'ank"ace idanuwa tana girgixa kugunta data d'aure da shamilallan hijabinta tace,
“Ta kwarankwasa baxan hakura ba,Babban bala'in can,se in xauna gani sokuwa sumin lefin sannan na hakura wallahi babu xancen hak’uri a dishenari(dictionary)na ramuwa ta da ta taxama dole..”
Tana gama fada tacigaba da kokawar da take yu cikin xafin nama sadeeq ya k'arasa cikin su ya wanke mata fuska da mari hade da hankadata gefe yatsan sa yasa yashiga nuna ta,
“Ke wai wacce irin kidahuma ce ne eh?! Kina mace kike fad'a? fad'anma da maxa dandaxon mutane akanki ko kunya bakya ji? Tukun nama me akai miki da kika kamasu kina duka kaman wata tinkiya..”
Rike baki Indo tai tana kada Kai
“Kai ka Kai Kai Kai wacece tinkiyar?!”
“Kece tinkiyar”
“To wallahi ka bude kunnuwanka kaji niba tinkiya bace kuma kwarankwatsa ka kara cemin tinkiya seka gani. Haba nifa kana shiga rayuwata da yawa makaranta ce de nace ni INdo Malam hamxa nadena xuwa tsefawa inifam d'ina ma na yadashi amma saboda tsabar shisshigi da neman sani seka tsoma wannnan bakin naka a xancen da ba naka ba”
Tana gama fada ta shuri bokitan su ubale da idi na talla da suke fad'a tai gaba dasu tana sharara uban gudu,ganin haka yasanya su ubale binta a d'ari suna rokonta da tabasu bokintan tallansu da ta kwashe,
Karkad'a kai kawai sadeeq yai wani b'angare na zuciyarsa na tabbatar masa da lallai yarinyar nan ba aljanu bane kad’ai da ita Lallai babu shakku aciki kwakwalwarta ta tabu, da haka ya k'arasa gidansa yashiga bakinsa d'auke da sallama tamkar da mutane a ciki.
0 comments:
Post a Comment