Bismillahi Rahmanin Rahim
On the authority of Abu Hurairah, who said : The messenger of Allah said : "Part of someone's being a good Muslim is his leaving alone that which does not concern him." fine Hadith narrated by Termithi and others
Abu Hurairah (May Allah be pleased with him) reported: The Prophet (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "He who believes in Allah and the Last Day, let him show hospitality to his guest; and he who believes in Allah and the Last Day, let him maintain good relation with kins; and he who believes in Allah and the Last Day, let him speak good or remain silent."[Al-Bukhari and Muslim
****************************
Buckingham Palace, City of Westminster...
3 years ago....
A hankali ya bude idanun shi sai kuma ya sake rufewa da sauri. Haka yayita kifkifta ido har idunsa suka kai agogon bango dake cikin karamin Cubical dinsa.
Zumbur!! Ya mike tsaye tareda tangal tangal alamun zai faɗi kasa. Innalillahi wa inna ilayhi rajiun yayita nanatawa, “Shikenan na gama yin latti” ya faɗa tareda wucewa bayi.
A gurguje yayi wanka tareda saka kaya, Dukda bala’in lattin dayayi saida ya sha Coffee saboda baya wasa da breakfast. Acewarsa breakfast is the most important meal of the day.
Haka yayi ta sintiri cikin cubical dinsa har ya gama shirinsa tsaf sai ya rufu kofa ya fita zuwa inda za shi.
“Good Morning Miss Beckinsale?” ya faɗa ma next door neighbour dinshi Wanda zata kai shekara saba’in a duniya amma bata taɓa aure ba.
“Good Morning sunshine, How are you?” ta faɗa tana fari da ido. Dama haka take tsokanar sa wai batayi aure ba saboda dama tana jiransa ne yazo ya aureta.
Tanada bala’in fara’a kuma sau da dama yana rakata irin su cocktail ko Fund raising haka.
“I’m fine” ya faɗa tareda danna elevator ya shiga cikin azama sanadiyar lattin daya riskeshi yau.
Dama yadan kishingida ne bayan yayi sallar asuba domin yayi 5mins sleep to shine bai farka ba sai 8:45am.
Gudu yakeyi akan sidewalk babu k'akk'autawa, yana yi yana bige mutane tareda fadin "Sorry please" haka har ya kai wajen traffic, tsayawa yayi yana ganin yanda motoci ke wucewa da gudu.
Daya lura basuda alamun tsayawa sai kawai ya kutsa dukda ba'a nuna alaman Pedestrian su wuce ba.
Kuuuu kake ji wani mota ya kusan kadeshi, haka yayi kokarin komawa baya amma sai ya zame ya fadi wanwar a kasa, tsaki yayi tareda mikewa, shi kuma mai motan ya fito da sauri don yaga yanayin shi. Sai ya fada ma mai motan, "Sorry please, I'm in a hurry"
shi kuma mai motan yace, "Damn you Man, you can get urself killed with these attitude" sai yayi kwafi ya koma motarshi.
Ko ajikinsa tuni ya cigaba da gudu, yana yi yana duba agogo. "09:24 Insha Allah I won't miss the train" ya fada a fili.
Har ya kai subway yana gudu tareda tsallake stairs uku ko hudu. Ikon Allah train din bai tashi ba mutane sunata shiga tunda tafiya ta Subway yafi idan mutum yayi latti bcs babu traffic yasa baima fita da motarsa ba.
💦💦💦
Sanye take da wani multi coloured long chiffon gown mai guntun hannu, saita hadashi da karamin Blazer Silver mai stones wanda bazai kai cikinta ba, k’afanta kuwa Gucci hightop ne mai spikes kuma yana daukar idanu.
Headphones din Beat By Dre ke kunneta kuma ta rataye dogon Vintage jaka a gefen damanta. Hannunta kuwa wayar handset ne tana latsawa tareda yin murmushi.
A hankali take tafiya zata shiga speed train din, a sanya sanya take komai sai gashi yazo da gudu yana so ya shiga bcs in a minute train zai tashi. "Hello Miss can you hold the door for me please" ya fada mata.
Ita kuma Wanda tuni tana sauraron wani abu daga wayarta bata ma San yana yi ba, koda ta shiga kofa yana kokarin rufewa sai ya hada da jakarta.
Shi yaji dadin abin saboda zai iya kustawa amma bata nuna tana so tayi hanzarin cire jakarta ba balle ya wuce.
A hankali take abinta har ta samu ta cire sai kofan yayi karap ya rufe jirgi ya tashi.
Da gudu yabi jirgin yana fadin" Nooo no no no no" sai kuma ya tsaya ya soma boxing da iska tareda dukan k’arfen dake wurin da hannunshi, zafi yaji mara misaltuwa saiya soma ihu yana tsalle, daga bisani ya lura kowa kallonshi yakeyi, kwafa yayi sai ya kame a gefe.
"Dama idan za'a hada abu da mata sai rai ya baci" ya fada ma kansa. Abin haushi baiga fuskarta ba saboda tayi wrapping irin na Arabs, at least koba komai zai saka ta a list din mak'iyan sa bcs wannan hassada ce k'arara.
Haka yayita zama har 10mins later inda wani train din yazo suka ware. Victoria Tube Station ya sauka saboda shine nearest station to Palace din Queen Elizabeth II, tafiyan mintuna 7 yayi ya kai main entrance.
Tsaye take a queue din Palace din, dama dream dinta ne taga inda Queen Elizabeth take, Daddy ya fada mata idan CGP dinta yakai 4.80 zai kaita country of her choice for summer kuma ikon Allah ta buga 4.82
Tabi duk wani protocol din security saboda yau akwai wani gagarumin taro dat is significant to yan England, yaune Her Majesty zata bada yabon girmamawa ga best students din kowane University din country dinta.
Tana shiga ciki idonta ya hangi royal standard flag din wajen a sama, murmushi tayi tareda fadin "yes the Queen is around" saita shiga ta fara kalle kallen su statue din wajen masu bala’in kyau.
Shi kuma yana isa ya gyara kayan jikinsa, grey suit ya saka tareda farin riga sai kuma purple tie, yayi adjusting dakyau tareda mak’ala links din hannun rigarsa sai ya soma taku daya daya kamar bashi ke gudu dazu ba.
"Da zuwa da wur wuri gwara zuwa da wuri" ya fada yana murmushi. Sai yaje inda security yafi yawa zaiyi signing in.
Mika masu babban yastan shi yayi suka daura akan na'uran su saiga sunan shi ya fito. NAUFAL HUSSAIN BELI representing Oxford University, "that's correct" ya amsa masu.
Gaba ki daya suka ce "Congratulations Mr Hussain, welcome to the Great Buckingham Palace"
Tun dayake karatu bai taba zuwa wajen ba kuma bai taba tunanin zaije ba, yana tafe yana kare ma wajen kallo sosai. Furanni irin su hydrangeas, tulips, lily da kuma Roses tako ina ga kuma wasu anyi customizing sunar Elizabeth dashi.
Security din wajen sun saka Bearskin hat, riga mai Ja da ratsan blue sai kuma bakin wando. Da MI6 gasu birjik, suma FBI da CIA ba'a barsu a baya ba saboda John Kerry na America da dignitaries din England sun hallara.
💦💦💦
A cikin fadan kowa yana tsaye za'a fara taro, masu karban yabo na daga gefe, kid’a na tashi a hankali mai dadin ji irin na al’adar yan England.
Duke and Duchess sun fara saukowa daga wani katafaren stairs mai dumbin tarihi. Yaransu biyu suma ana saukowa tare. Kida ne ya chanza alamar a natsu Her Majesty zata fito.
Ta sauko an fara taro anata bada awards har an kai turn din Naufal, "For Oxford University we present the brilliant Naufal Hussain Beli from Bauchi State Nigeria"
Raf Raf Raf suka rinka tafa masa, shi kuma cikin natsuwa yaje wajen Her Majesty yayi bowing head dinshi tareda shaking hannunta "Thank you so much your Majesty, I'm really honoured" ya fada ita kuma tace, "The pleasure is mine Mr Hussain" saita yi murmushi wanda ya bayyana mata hokararta.
Ya juya zai koma wajen tsayuwarsa saiga wata yarinya idon shi ya hango mai, ya lura tafi kowa tafi a cikin audience. Murmushi ya soma yi yana tafiya tareda kara kallonta.
Yana wajen tsayuwarsa ne ya lura da headphones din dake wuyanta, a hankali ya rinka ware ido dan yaga ko zai ina gano kayan jikinta.
Zuciyarshi ta soma aiki da sauri sauri tana kokarin kawo mashi wasu tunani marasa amfani, wani siririn murya ta raya mai "kila fah yarinyar dazu ce..." da sauri ya kawar da tunanin tareda korar shedan saiya sake kallon bangaren ta.
Kaddara ta riga fata saboda anan yaga Multi coloured kayanta tareda jacket mai stones wanda keta walkiya.
anan take bakin cikin mara misaltuwa ya riske shi.
Kwafa yayi tareda juya kansa, "Bad luck! har nan kika biyo ni?" ya tambaya kansa rhetorically.
*Special shout out to my best friend turned sister, Aisha Sulaiman aka Momyn Jawahir. Allah ya kara dankwan zumunci*
*All rights reserved*
💥∂ιмρℓεs💥
[13/2 07:12] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 2✨✨✨
Abu Hurairah (May Allah be pleased with him) said: The Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "Do you know what is backbiting?" The Companions said: "Allah and His Messenger know better." Thereupon he said, "Backbiting is talking about your (Muslim) brother in a manner which he dislikes." It was said to him: "What if my (Muslim) brother is as I say." He said, "If he is actually as you say, then that is backbiting; but if that is not in him, that is slandering."[Muslim].
*************************
Haɗa girar sama dana k’asa yayi bai k’ara kallon inda take ba, Jira kawai yake a gama taro yaje ya sameta su gwangwanje. Bcs irin sanya sanya data keyi ba k’aramin wahala zata shaba musamman idan ta aure namiji mai gajen hakuri.
Ita kuma bawai tana wani concentrating bane, abu takeji a headphone dinta which she is addicted to Kuma shine wanda ya dauke mata hankali, idan taga ana tafi sai itama tayi. Sam bata lura da cewa nata yafi na kowa k'ara ba.
Ana gama taro kowa yana kokarin tafiya sai ta sidada ta wuce upstairs da sauri kafin a ganta, dama she is obsessed with paintings da kayan art works tunda Fine Arts take karantawa a Jami’a
Paintings din Van Dyck da Reubens ta fara gani a wani corridor, a hankali taje ta rinka kallonsu tana yabawa da structures ɗinsu. Yanda aka k'erasu ya bala'in burgeta. “I wish I can paint like this” ta fada ma kanta.
Daga nan sai ta soma touring cikin Palace din sai ga na Vermeer, poussin da kuma Claude. Ta tsaya a gaban painting ɗin tayi su selfie tareda bude snapchat dinta.
“HI Snapchat, I'm in the Buckingham Palace, look at these amazing priceless paintings” saita nuna paintings ɗin, haka ta rinka having fun abinta hankali kwance.
Bata bar wajen ba saida tayi su Instagram videos kuma tayi posting hotuna a whatsapp da sauran chats haka. Yanda take abinta a hankali kai zaka zaci yanga takeyi amma yanayinta ne kawai.
Komai a sanya sanya takeyi kuma abinda Naufal ya tsana kenan wajen mutane. He prefers swift individuals.
Ta hange wani daki wanda akwai sculpture ɗin Canova zata je gurin sai security masu Bearskin hat suka dakatar da ita tareda faɗin, “Sorry ma'am, restricted area”
Locacin yayi daidai da k’arar wayanta, ta saka hannu zata dauka “ahn ahn Ma'am, please no calls allowed” suka k’ara fadi. Kwafa tayi tareda murguda masu baki, tana tafe tana turo baki tareda Jan kafanta karap karap duk ta ishe kowa.
Kafin ta isa wajen building ɗin sai wayar ya tsinke, tsaki tayi ta fara neman signal tareda returning call ɗin. Har ya shiga an fara magana, “kiyi sauri ki bar wajen nan ki sameni a…..” bata k’arasa jiba sai ga yara sunzo da gudu da kites suna wasa, tureta sukayi komai ya tarwatse saida ta ɗuka tabi ta roro battery ɗinta da Sim card.
Shi kuma Naufal ware ido yayi yana kokarin yaga inda take a cikin hargitsin mutanen, amma bai ganta ba. Shifa bai dandara ba saboda ya riga ya sakata a black list ɗinshi.
1- Ya tsana mutum mai nawa.
2- Sai wani tafi take tana zak’ewa da aka kirashi sai kace ya santa.
“Shifa shishigi ne baya so”ya faɗa a ranshi. idonshi ya mayar Kan Electric door amma babu ‘Bad luck’ babu dalilinta. “Dama nasan cewa tana nan tana nawa ta wani bangaren bazan ganta ba”
Tsaki yayi ya koma wajen sauran awardees sunata raha tareda fadin zasu hadu a after party din da akayi don karrama su. Amma dukabinda sukeyi hankalin shi baya jikinshi.
Ya fito daga building ɗin zaiyi answering call, sai ya hangota daga nesa sai faman zuba sauri takeyi, daga alama zata tafi ne. “Ashe kin iya aiki da jiki” ya fada ma kansa. Sassarfa ya soma yi yana kokarin zuwa inda take.
“Excuse me Ma'am, you just dropped this” Wani security ne ya dakatar da ita yayinda ta zubar da passport dinta a kasa wajen fito da wallet ɗinta. Murmushi tayi tareda cire headphone ɗinta don taji mai zai fada da kyau.
“FADEELA ABBAS BELLO” abinda ya fada kenan bayan ya bude ciki, “Thanks so much, but I need to go” ta faɗa mishi tareda nuni da hannunta alamar ya bata. Bai bata nan take ba ya tsaya yana wasu dube dube, haushi ya kamata saboda bataga dalilin da zai yi mata bincike ba.
“Have a nice day Ma'am” ya fada sai ya mika mata tareda daga mata gira, ita kuma, “Thanks, you too” tace tareda murguda masa baki, mayar da Headphone dinta mazaunin shi tayi saita cigaba da tafiya cikin sauri wannan karon harda Sassarfa.
Dayaga security mai Bearskin hat ya tsayar da ita ba k’aramin jin dadi yayi ba, amma kuma sai ga ta yanzu ta soma gudu. “Excuse me Please” ya faɗa yayinda yake binta amma headphone ɗin kanta bazai barta taji ba.
“kila ma ba wani abun Kirki take ji ba” ya faɗa ma kanshi. Ita kuma tana isa bakin titi ta tare Cab ta shiga abinta, suka soma tafiya.
"Hello! hello!!!" yayita nanatawa amma bata jiba. Text din Momy ta gani "Na hada miki kayanki, ki same ni a airport" sai tayi murmushi tareda mayar da wayan jakarta.
Shi kuma Naufal dayake bai iya ɓoye frustration dinshi ba, “Nooooooo no no” ya rinka faɗi saboda yana isa titi cab ɗinta yana tafiya.
Sai kawai yayi kwallo da wani empty cup din coffee tareda naushin iska. Hannunshi yana Kan waist ɗinshi yana fuzgar iska mai zafi kamar mayunwaci zaki yana kallon yanda motar ke tafiya.
“Ma’am I think that guy was talking to you” Cab driver ya faɗa. Ita kuma ta juya don ganin wanene amma yana mata dishi dishi still bata San ko waye ba. “Don't worry I don't know him” ta faɗa tareda gyara zamanta.
“where I'm I taking you to?” ya tambayeta. “Home” ta amsa mashi. Kallonta yayi cikin rashin fahimta tareda faɗin, “And where is home?” murmushi tayi saita ce “Nigeria, sorry please. I meant to say Heathrow Airport”
*Hankali baiwa ce kuman idan Allah ya baka ka gode masa. Special shoutout to my triplets, Ummiee Rilwan (Fatimah), Ummiee Jafar(Faizah) and Ummiee Khaleel (Aisha)*
*All rights reserved*
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: 💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 3 ✨✨✨
On the authority of Abu Hurairah, who said : the messenger of Allah said : "Do not envy one another; do not inflate prices one to another; do not hate one another; do not turn away from one another; and do not undercut one another, but be you, O servants of Allah, brothers. A muslim is the brother of a muslim: he neither oppresses him nor does he fail him, he neither lies to him nor does he hold him in contempt. Piety is right here-and he pointed to his breast three times. It is evil enough for a man to hold his brother muslim in contempt. The whole of a muslim for another muslim is inviolable: his blood, his property, and his honor." Related by Muslim.
************************
*Bauchi....*
*Present day....*
Conference hall ne mai madaidaicin girma irin wanda kujeru zaici mutane akalla 24 sai wani katafaren brown table a tsakiya.
Babu abinda ke mosti sai TV dake manne a bango kuma shima yana mute ne. Sanyin AC yana sirara kuma ga kamshin room freshener tako ina.
Mutane bakwai ne zaune, fararen fata guda uku sai sauran bak’ake. Zaman mintuna 54 cifkenan da sukayi. Babu wanda yace komai, daga mai haɗa girar sama dana k’asa sai mai latsa wayar handset.
Tsaki ya buga a Karo na uku, “Please we need to get started” wani bature ya fad'a yayinda ya k'ara kallon Rolex wrist watch dake manne a hannunsa na hagu.
Sai wani bak’in fata ya chapke tareda faɗin, “Please be patient Mr Pearson, I'm sure Mr Hussain is on his way. He is not usually dis late”
Wani bature daban yace, ‘Mr Jibrin call him again bcs our flight is for today” sai yayi kwafa yana tattara takardunsa.
Aminu Jibrin yace, “Excuse me please” sai ya tashi ya fita tareda wayarsa a hanunshi. Ya fita chan wajen balcony yayi facing Kan titi yana danna wayarsa tareda ware ido ko zaiga zuwan Naufal.
Sanye take da wani Indian attire, wani shararren designer dinsu na chan mai suna 'Gaurang' yayi. Ta fito daga wurin Tailor dinta mai Suna Ismail a kasuwan Wunti.
Ranta a ɓace take tafiya cikin yanayinta na sanyi, tunani kala kala ke zuwa mata saboda ta dau alwashin idan suka haɗu sai tayi mashi rashin mutunci, Ankon course mate ɗinta da bakinta ya gabato nanda 8days amma yana mata hide and seek saboda bai ɗinka ba.
Tana tafe tana turo baki saboda ta bala'in jin haushi, yanda yan shagon Ismail sukeyi tasan cewa yana ciki kila ya ɓoye a cikin shargi ne.
Wak’ar ‘The weeknd’ na Starboy ke tashi kuma shine ringtone ɗin Naufal, yasan sarai wake kiransa amma bai dauka ba. Haka wayar ya gama rero wak’a ya tsinke.
Gudu yakeyi babu k'akk'autawa, baisan dalilin daya sa yayi muguwan latti ba, ko sallar asuba sai 9:30am yayi. Kunya abinma yaji dukda babu wanda ya ganshi sai mahillicin shi. Koh tie baiyi knotting ba kasancewar zasuyi meeting da turawa akan Merger kuma he is suppose to look smart and collected.
Haka gashin kanshi kacha kacha bai taje ba, a birkice yake yin komai saboda ko kwallan rigarsa tana mak'ale a cikin wuyarsa. K'arar wayarsa yaji, da gefen ido ya kalla yaga still Aminu ke kiransa, "idan kai maye ne, toh fah saidai Kaci yan gidan ku" ya fada, sai da wayar ta kusa tsinkewa kafin ya dauka, "Guy I dey road, no disturb me abeg" ya fada yana dariya.
Shikuma Aminu ya k'ulu sosai saboda baiga abin barkwanci akai ba bcs wanna shine biggest contract da kamfanin su suka samu tun buɗewarsa. Tsaki yayi saiya kashe wayan. Bai koma cikin conference room dinba yana tsaye yana haki kamar wanda yayi gudu.
Tana kokarin tsallaka titi shi kuma Naufal ya kauda kanshi for less than 3 secs don ajiye wayar shi. Kuuuuuuu ya taka barki yayin daya kusan kad'e wata baiwar Allah.
Ita kuma dama taga hanya babu kowa cikin yanayinta na Sanya Sanya ta shiga zata tsallaka. Earpiece ɗinta na fama yana kunnen ta yasa bataji zuwan mota ba.
Kawai wani faduwan gaba taji tareda juyawa, "dam" gabanta ya fadi data lura baifi taku uku mota ya nik'ata ba.
Salati ya rinka jerowa tareda addu'oi kala kala wanda ya dace da wanda bai dace ba, dama shi yanada tausayi sosai. Earpiece dinta ta cire daga kunnen ta tana kokarin mayar wa cikin jakarta.
“Bad luck” abinda ya fada kenan tareda tsaki, dukda three years ago ya ganta last amma bai mance da fuskarta ba. “Bazata bar saka wannan abun a kunnen taba koh?” a fusace yayi parking motarshi da kyau tareda fitowa. Dama ita ta koma baya inda ta fito bayan abin ya auko.
Jikinta yanata rawa zufa sai keto mata yakeyi, hannu na karkarwa duk ta fita hayacinta. Dama akwaita da bala’in tsoro kamar farar kura.
“Ke jakar ina ne?” abinda ya faɗa kenan yana nuna mata yatsa kamar zai tsokane mata ido, bata amsa shiba illa hawaye daya soma malalo mata daga fuska. A duniya tashin hankali ne abinda yafi ɗaga mata rai.
Dama tun yau tanata samun mood swings kamar mugun abu zai faru da ita, “Dake nake, nace ke wace irin gara ce da zaki saka Earpiece akan titi?” Ita bataga abinda yasa ya hasala haka ba yana wani tsuma, accident do occur besides da gangan bazata shiga ba.
“Ni jakar garin ubanka ne” ta amsa idonta kur a nashi. A fusace ya ɗaga hannu zai mareta. “kada ka kuskura ka taɓa ta idan ba haka ba zamu taru muyi maka shegen duka da sai ka raina kanka yanzu yanzu” wasu masu saida fruits suka fada.
Yanda yaga babu wasa a tareda su saiya mayar da hanunshi kasa, “ku dama masu kuɗi sai ku rinka tink'aho da titi kuna cewa kada kowa ya hau, toh bari kaji titi na gwamnati ne saboda haka dole muyi amfani dashi”
K’arar wayarsa yaji sai yayi tsaki ya koma wajen motarsa, 10 missed calls ya gani. Gabanshi yayi mummunan faduwa saboda ya shafa'a ya mance da conference ɗin yana nan yana so yayi faɗa da Bad luck.
Wani call din ya shigo sai ya ɗauka da hanzari, “I’m sorry man, abu ya tsayar dani but......” Aminu bai bari ya karasa magana ba yace, "Calm down, ka cigaba da abinda kakeyi saboda Mr Sutter yace ka raina shi kuma ya wuce Abuja” din din din abinda Naufal yaji kenan a kunnen sa.
Cilla wayar yayi cikin mota sai ya fara dukan motar da hannu da kafa, sai ya kuma kifa kanshi akan motar yana mayar da numfashi da sauri sauri. “Bad luck” ya faɗa da karfi daya tuna itace sila.
A guje ya koma wurin daya barta saboda yanzu babu mai kwatanta a hannunsa, sai yayi kas kas da ita. Idan ya gama sai sauran mutanen suma su dake shi.
Yana isa wajen babu ita babu dalilinta, “Bad Luck” ya faɗa da karfi saboda gaskiya ko wacece yarinyar nan duk inda taje saita jawo annoba.....
Jiki babu kwari ya koma motarsa, bai tada ba illa kifa kai dayayi akan steering yana tunani kuma zuciyarshi yana mai k'una. "wannan wani irin tashin hankali ne? Yanzu meye abin yi? Allah ya shirya ki idan zaki shiryu"
“Sam Sam baiwar Allah bakiji dadin halinki ba..... At all”
*All rights reserved*
💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 4✨✨✨
It was narrated that Abu Usaid, Malik bin Rabi'ah, said "While we were with the Prophet(), a man from the Banu Salamah came to him and said: " O messenger of Allah, is there anyway of honoring my parents that I can still do for them after they die?' He said: "Yes offering the funeral prayer for them, praying for forgiveness for them, fulfilling their promises after their death, honoring their freinds and upholding the ties of kinship which you would not have were it nor for them.'" (Hasan)
*****************
Wani na annabi ne ya taimaka ma Fadeela ya samo mata keke napep ta hau bayan Naufal yaje wajen motarshi. Tana tafe tanata kuka, still jikinta bai bar rawa ba, dukta susuce.
Ita abinda yafi ɓata mata rai bai wuce wai ita ce zatayi faɗa da namiji wanda ko mata bata gama yi dasu ba.
Dama daga shagon Ismail, Yelwa zan wuce inda makaranta mu yake watau ATBU, amma yanzu gida zan koma dukda inada test amma bazani ba bcs I'm too angry to write.
Muna isa GRA inda gidan mu yake nayi kuka har murya na ya fara dishewa, “Allah ya isa” na rinka faɗi a raina saboda bazan yafe mashi ba.
A daddafe na fito duk jiri na ɗibana saboda bana ko ganin gabana, “nawa ne kudin?” Ki barshi kawai Hajia ai naga abinda ya faru, Allah ya kiyaye na gaba. "Amin" na faɗa mashi kawai na wuce saboda banida energy ɗin wani magana.
“Assalamu Alaikum” na faɗa saina wuce upstairs, ko tsayawa na gaida Momy banyi ba, which ba d’abiana bane. “Wa'alaikumus Salam” ta amsa sai ta bini da ido tana karantan yanayi na. Har na kusan kaiwa karshen stairs saita ce, “Yaki dawo nan, lafia bakije school ba kuma kin shigo kina wani kumbure kumbure?”
Ban amsata ba saboda hawaye dake fito min, haka na tsaya kuma ban yuja ba. “Bada ke nake magana ba?”
kafin na amsata saiga Daddy ya fito daga ɗakin shi cikin black suit and grey tie daga alamun yanada court case Kasancewarshi na Judge.
“Ni matsa min daga hanya, mahaifiyarki tana miki magana kin wani kyaleta. Uwa dai ba abin wulakantawa bane!” Daddy ya faɗa yayinda yake saukowa. Saura kaɗan daya hankaɗe ni saida naja baya, nan take na fashe da kuka saboda duk laifin azzalumin mutumin nanne wannan abu ya faru dani.
Wucewa ɗaki nayi da gudu na kwanta a gado na dauko wani babin kukan. Sai ga momy ta shigo ta zauna akan gadon, janyoni tayi jikinta saita ce, "Auta waya taɓa min ke? Na hana shi sukuni a garin Bauchi”
Sarai nasan halin Momy kuma tanada connections, k'akalo murmushi nayi saina ce, “ Momy fault dina ne, naje tsallaka titi sai mota ya kusan bigeni” dariya momy tayi sosai kafin tace, “ Ho sarkin shagwaba, ni banga abin kuka ba. Anyway tunda kin dawo zo na aike ki gidan Jawahir kinsan Jiya mijinta ya dawo akwai sak'ona a wajen shi.
Momy kallon Fadeela takeyi saboda sam bata iya fushi ba, most of the time tana abu kamar goyon kaka aside rashin kunyar, “Allah ya bata mijin wanda zai rinka tausayinta”momy ta fada a ranta yayinda take fita.
💦💦💦💦
Shikuma Naufal wani dabara ya fad'o mashi, gwara yabi Mr Sutter Abuja ya basu hakuri. Haka kuwa yayi, zura gudu yakeyi akan titi yayi hanyar Abuja. Dama idan wajen gudu ne to fah ya kware saboda zaka sha drifting din motoci ne.
Yana isa Nicon hotel ya fito daga parking lot, tunani kala kala yakeyi tareda neman mai zai fada masu, yana so ya shiga reception din kenan saiya hango Mr Sutter, Mr Pearson da Mr Targeyan sun fito da kayansu zasu tafi.
Da sauri yaje ya sha gabansu, "Please I'm very sorry for my actions, I take full responsibility, please just consider this merger with my firm and I promise you will never regret it" hannun shi biyu yana rok'on su. Fuskarshi tsantsan nadama ke nunawa.
Mr Pearson yaji tausayinshi amma Mr Targeyan yafi zafin kai, juyar da fuskarshi yayi kamar baima san Naufal na wajen ba, dama tun farko baiso ayi abu da bak'in fata, a cewarsa basuda rike alkawari.
Mr Sutter ya kalle Mr Targeyan which har yanzu yaki murmushi, "since he owned up to his mistakes, I think we should consider him but this time around we will reevaluate the first contract. We will give you 6months trial bfr signing the agreed documents"
Murna mara misaltuwa a wajen Naufal, “wow dats what I’m talking about” ya fada yana shaking hannu su, kwata kwata baisan me zai faru dashi ba idan yayi losing deal din saboda anyi relying dashi a firm dinsu gashi uwa uba shine Bread earner(Mai tallafi) ɗin gidansu...
Okay let’s go inside and talk, Mr Targeyan ya fada wannan karon yana murmushi harda dafa shoulder ɗin Naufal. Bayan sunyi meeting ɗinsu suka had’a da lashe lashe, daga bisani kowa yayi hanyar sa.
Su suka wuce airport inda zasu tafi Newyork, shi kuma ya dauki hanyar Bauchin Yakubu saboda shi baisan kwana a wani waje idan ba gida ba. Daukar wayarsa yayi ya kira Miemie kanwarsa suka sha hira dukda shirme take zuba masa sanadiyar tanada psychotic disorder(Ciwon Hauka) but a duniya bashida kamar Miemie.
Farin cikin sa kenan, kuma duk wani zafin nema dayake yi saboda health dinta ne yasa ma bashida sha’awan aure. Acewarsa baya so mace tayi distracting dinsa while sister dinshi batada lafiya.
Ko yanzu ba maganar kirki sukeyi ba, babbaka dariya takeyi saboda tun shigowar wannan makon yan dariya suka motsa. Dama turn by turn ne, akwai yan dariya, yan shiru, da kuma idan ta samu lafiya kadan.
Jira yake ya koma Bauchi gobe su wuce Psychiatric Hospital na Kaduna. Dama idan deal ɗin baiyi working ba dole su canza mata asibiti. Bayan ya kashe wayan sai ya kira Aminu amma har ya gama k’ara bai dauka ba.
Murmushi yayi saboda yasan fushi yayi dashi. Text ya aika mashi na, “Calm down please, I know na ɓata maka rai but don’t worry everything is going to be alright. Ka mance nine Naufal?” saiya tura mai.
*Wanene Naufal?*
*Birthday shout out to my dearest Kawa Aysha kirya. Allah ya baki more meaningful years yasa muje har Isiala Ngwá(lol) musha biki..... Amin. Calm down everyone it's her birthday*
#NiDaDiyata
*All rights reserved*
💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 5✨✨✨
Abu Barzah Al-Aslami narrated that the Messenger of Allah (s.a.w) said "The feet of the slave of Allah shall not move [on the Day of Judgement] until he is asked about five things: about his life and what he did with it, about his knowledge and what he did with it, about his wealth and how he earned it and where he spent it on, about his body and for what did he wear it out." (Da'if)
*************
Naufal Hussain Beli matashi ne mai jini a jiki ɗan shekaru Ashirin da tara a duniya, kuma ɗan asalin Bauchi ne a wani gari da ake kira Shira.
RTD Engr Hussain Beli shine mahaifin Naufal kuma yanada mata biyu. Hajia Sarai wanda ake cema ‘Mama’ sai kuma Hajia Saudatu suna ce mata ‘Anty Saudah’.
Mama tanada yara biyar a duniya, Nabil ɗan kimanin shekara 32years kuma yana aiki a Airtel Networks a Abuja. Yanzu haka yana auren Safeena yar garin Katsina ne amma a Abuja take zama, sun haɗu sanadiyar supervising wani promo da akeyi a University of Abuja which a locacin ita student ɗin school dinne. Sunada yaro ɗaya mai suna “Mohammad Eemaad”
Daga nan kuma sai Naufal, sai kuma “Amatullah” yar kimanin 25yrs kuma tana aure a Gombe da yaronta guda daya “Abdulrahman” Amatullah tanada bala’in zafi bata daukan raini at all, kuma itama tanada raini sosai, ga kuma kyaman talaka musamman yanzu data aure mai k’unban susa.
Daga ita sai kuma Abla yar 22 years wanda yanzu take serving a NEPA, itace dai mai sauk’in kan ɗakinsu. Batada matsala at all saboda tanada daɗin sha’ani.
Sai kuma autan mama wato yan matan 100l ‘Bilqees’ itama footstep ɗin Abla take bi amma bata kai Abla kirki ba.
Anty Saudah tanada yarinya guda d’aya mai suna “Laurat” amma suna kiranta “Miemie” saboda sunan maman babane.
Bayan haihuwar Miemie da wasu shekaru sai suka lura tayi developing wasu strange ɗabi’u, an kaita asibiti shine akayi masu confirming tanada ciwon Hauka watau Psychotic disorder.
Ansha wuya wajen neman mata magani, sunyi zirya a Psychiatric Hospital Kakuri, Kaduna. Kuɗaɗe masu ɗunbim yawa ake kashe mata kuma still bata warke ba. Jefi jefi yake yi mata tuburan.
Hajia Sarai watau Mama ta tada bala’I akan bazata zauna gida d’aya da Mahaukaciya ba, dayake locacin Abba yanada k’umba susa, saiya siya wani gidan gona haka mai dan girma.
Duka yaran Mama basu ji daɗin abin ba saboda Miemie yarinya ce mai shiga rai, musamman Naufal da Abla, shi saida ya koma gidan da zama, jefi jefi yake zuwa gurin Mama. Yanzu haka Miemie tanada shekaru goma sha hudu a duniya, kamar yanda bature ke fad’in first impression matters, to haka rayuwar Miemie yake.
Idan kuka hadu for the first time ta nuna bata sanka, toh fa saidai kayi hakuri. Amma idan tayi maka fara’a zaku shirya sosai. Ana cikin yi mata magani sai Abba yayi retire daga wajen aiki.
Ko karatun Naufal bashi ya ɗauki nauyin sa ba, Gwamnatin jihar Bauchi ta bada scholarship ga yara masu hazaka, kuma cikin sa’a Naufal ya samu wannan damar. Shine yaje Oxford University inda ya karanta Architecture kuma yanzu haka yana cikin best Architects a Nigeria.
Kasancewar Naufal ya shaku da Miemie yasa ya dauki nauyin Medical bills dinta. A duniya yanzu bashida wani buri face yaga ta samu sauki bata tuburan ko doke doke, bcs idan lafiya ya ɗan zo mata har special school ana kaita domin tayi karatu.
Yanzu haka duk sati biyu sai an kashe mata 70k, yasa da ya kusan losing deal ɗinshi dasu Mr Sutter ranshi ya bala’in bace bcs baisan ya zaiyi bill din Miemie ba tunda sun samu ta rage hauka tuburan, saidai kawai tayita kyalkyala dariya ba gaira ba dalili.
Naufal tun fil azal yanada tausayin ɗan Adam, baya so yaga mutum cikin pain. Ko bai sanka ba ka rokeshi alfarma zaiyi maka koba duka ba. Abinda baya so a rayuwarshi shine “Nawa” da Sanya Sanya saboda a cewarshi “Time is money” He is very swift Idan zaiyi abụ yasa ake ji dashi wajen aiki, kuma idan yanayi bawai rawar kai yakeyi ba.
Bashida surutu sosai musamman idan bai sanka ba toh bazai ce uffan ba, daga eh saidai ah ah Har ku gama magana, gashi yasan addini daidai gwargwado kuma yana kokarin kare hakkin shari’a.
Bak’I ne sosai mara misaltuwa, amma bak’inshi yanada kyau kuma skin dinshi is fluffy. Yanada tsawo daidai misali ba jankala kok’I ba, gashin kansa yayi curly a matsayinshi na Fulde.
Yanada Emerald eyes which is very rare ma yan Africa, kuma idanun are not that bulging, sunje daidai da dogon fuskarshi. Bashida saje ko kaɗan saboda bai taba yiba, fuskarshi haka yake payau.
One good thing about him shine ya iya dressing thou mostly suits and tie ne na week days sai kuma T-shirts haka ma weekends. Idan kuma traditional wears ne toh fah saidai ya saka farin kaya da hula, baya sa wani colour at all. Idan yayi kwalliyar nan kuma Miemie tana daidai tana mishi lak’abi da “Yaya bak’i da fari” wai gashi baki amma yasa farin kaya.
Kuma he is very neat, koda yaushe yana fadin “Al naxafatu shaɗaral iman”
Wannan kenan!!!
1 week later...
Yaune bikin k’awata kuma aminiyata Hadiza, tun jiya muka fara su kunshi, Hajia Sumayya Gaya wanda aka fi sani da “India” tazo tun daga kano domin yi mana, Hadiza ta fito sosai sai san barka, nima ba tayar baya ba.
D’inkin da Isma’il yayi min ya fito da duk wani bangaren jikina har kunya nakeji, “gaskiya saina yafa gyale” na faɗa ma kaina tareda kara kallon madubi.
Haka na tsala ma kaina kwalliya tunda ni ma’abociyar shine kuma ina shiga YouTube da Instagram na kalle videos haka, mune ake kira da “Internet Makeup Artist”
Shi kuma Naufal tun yau yakejin Mood swings, gabanshi faduwa yaketa yi. Innalillahi wa inna ilayhi rajiun ya rinka maimaita wa.
Komai sukuku yakeyi, saiga Miemie ta shigo. Dama bata fiye magana ba tunda yanzu ‘yan maganar basa nan, hawa kan gadansa tayi ta kura mashi ido, “Ya Naufal bakada lafia ne?” shima karin kansa baisan meke damunsa ba.
“Halan baki iya gaisuwa bane?”
“Na iya mana, but please answer me”
Juya kanshi yayi gefe saboda bai san me zaice ba, gashi in an hour zai wuce wani dinner na friend ɗinshi Sadeeq. A hankali ya tashi ya wuce bayi yayi wanka tareda dauro alwala.
Ya gama ya fito kenan saiyaji kamar bai kulle shower da kyau ba, ya koma ciki sai yaga komai lafiya lau, juyawa yayi sai kawai yayi missing steps dinshi yana kokarin faɗuwa.
Sink, bango da k’arfen shower duk yayi kokarin kamawa but still saida ya zube a kasa, “tim” kakeji kawai.
Shiru yayi a k’asa zafin ya gama barin jikinshi, da tangal tangal ya samu ya koma wajen gado. Tsaki yayi kafin ya soma dressing, farar Boyel ya saka as expected.
Saiya murza hular k’ube wanda ake kira kwalba a kanshi. Fashe turaran Christian Dior yayi dana Ralph Lauren ko ina sai kamshi.
Ya juya zai tafi saiya lura Miemie tana kallonsa, “ashe baki tafi ba?”
“Ya Naufal zaka kashe arna yau, yan mata zasu rinka rububinka” ta faɗa tareda zurawa a guje.
Dama haka takeyi idanta faɗa abinda yafi karfin bakinta saita gudu shima ya bita ayita wasa. Amma Sam yau bazai iya ba saboda har yanzu bayan shi yana mashi ciwo.
Baiji haushin abinda ta fada ba saboda it’s true, ya saba yaje biki yan mata suyi masa cha a kai suna k’arairaya, shi kawai yasan cewa bai haɗu da soul mate ɗinshi ba har yanzu. Yanada feeling duk randa ya ganta he will know!
*All rights reserved*
💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 6 ✨✨✨
Narrated `Abdullah bin `Umar, Allah's Messenger (pbuh) said, "A Muslim is a brother of another Muslim, so he should not oppress him, nor should he hand him over to an oppressor. Whoever fulfilled the needs of his brother, Allah will fulfill his needs; whoever brought his (Muslim) brother out of a discomfort, Allah will bring him out of the discomforts of the Day of Resurrection, and whoever screened a Muslim, Allah will screen him on the Day of Resurrection . "
********************
Saboda yanda kayana ya matse ni, da ban na shiga hall ɗin batare da zugan amarya ba. Na samu wani seat a gaba na zauna tareda sauran friends ɗina tunda high table is just for bride and groom.
Kowa ya hallara da wanda aka gayyata da wanda ba’a gayyata ba, kowa yazo rangem yaci shinkafa.
Yana isa Zaranda hotel inda za’ayi dinner din, yawan mototin wajen ya bashi mamaki. Hall ya cika sosai kuma rabin gurin yan mata ne “Sunzo tallan kai” ya fada a ransa yana taku cikin k’asaita.
A wani table guda ɗaya dattawa uku ke zaune kuma duka aminan Alhaji Sulaiman ne(Baban ango).
“Ai ina gaya maku na rasa dalilin sa na kin yin aure gashi ba yaro ba” Engr Hussain ya faɗa fuskarshi duk takaici.
Alhaji Musa ya dauki samosa guda ya gatsa saiya buɗe roban Swam ya sha, “Kuma kace ya gama karatu koh?” ya tamabaye su.
“Yaron kirki mai taimakon iyayen shi, wallahi tun sanda Engr Yayi retire ya rinka daukar ɗawainiyan k’anansa, amma sam baya maganar aure” Alhaji Sulaiman ya chapke.
Saiya k’ara da cewa “ko dayake tare suka tashi da Sadeeq duk halinsu ɗaya na rashin san aure amma shi Sadeeq baida aikin yi sai 8 Months ago ya samu. Amma shi kuma gogan ya kusan shekara 3 dafara aiki kuma yanzu yana chaɓawa sosai a garin Bauchi”
Shi dai Alhaji Musa shiru yayi yana sauraron hirar da abokinsa yakeyi da amininsa. Kuma yaji ance yanada da halin rik’e mace ga kuma yaji ance yanada hankali da tausayi.
“wow!!! dude ɗin chan ya hadu, sai dai baki ne” Mansura ta faɗa. Ita kuma Sadiya tace, “wanga green eyes haka, naji ance idan dare ya tsala masu irin idon suna komawa mage” sai gabaki ɗayansu suka kyalkyale da dariya.
Ni ko jin abinda suke banayi saboda ina sana’ata na shan wak’a, Mansura ta fizge earpiece din “wai dalla meye haka? Inace Momy ta hana ki?” juyawa nayi na kalli left and right cikin isgilanci kafin nace, “banga momy anan ba, so bani abuna” saina fizga abina.
“Amma bansan guy ɗin, saboda yasan ya haɗu shine yake wani salo” Sadiya ta faɗa. Ni kuma na juya inda suke kallo naga waye amma naganshi a duke yana gaida wasu.
“Ashe yanada tarbiya” Mansura ta faɗa, har cikin raina ina so naga fuskarshi saboda yanda suke kod’ashi yayi yawa, inaso naga if he is worth kwace min earpiece ɗina.
Naufal ya cika yayi fam, tun shigowarsa yan mata ke kallonsa but nasu yafi bak’anta mashi rai. Mutum ɗaya ta kalleshi tayi magana sai sauran su kwashe da dariya ba karamin haushi ya bashi ba. Fatan shi ɗaya, wata tayi mashi ba daidai ba ya daketa tunda yanada saurin hannu.
Dama yazo wucewa ne yaga Abbanshi da baban Sadeeq, toh shine suke gaisawa while yan matan two table away sunata giggling suna kallon shi “Nifa raini ne banso” ya faɗa a ransa.
Su Mansura kuwa sai magana suke a hankali suna kallon Naufal, ni kuma tuni na fizge earpiece dina na mayar mazauninshi. Daukar Pepsi nayi na buɗe sai abin ya fara zuba. Da sauri na mike ina kokarin juyawa sai na bige mutum.
Shi kuma yazo wucewa ta gefen su sai wata daga cikin su ta bigeshi tareda watsa mashi Pepsi. “D’ankari” ya faɗa a ranshi. Ni kuma Dimples nace abin nema ya samu wai matar makaɗi ta haifi ganga.
Tasss ya watsa mata mari, sai ya k’ara dauketa da wani ta ɗaya bangaren, marin daya yanka mata mai sa fitsari a jiki ne kuma dole kaga taurari.
Ni kuma a razane naja da baya dana lura azzalumin mutumin dana haɗu dashi kwanaki ne, “dole a rina wai an sace zanin Mahaukaciya”
Dama suna bashi haushi sai ya lura “Bad Luck” ne a gabansa kuma ga earpiece a kunnenta yasa ko tunani baiyi ba ya watsa mata frustration dinsa.
Tabbas sukuku da mood swings dayake ta samu yau sanadiyar zaiyi gamo da ita ne, bcs duk wanda ya hadu da ita yayi gamo. Idanunshi suka kad’a bcs Bad Luck din dake binta yasa ya fadi ɗazu a bayi.
Karkarwa na somayi bakina sai rawa yakeyi, gumi nake tayi duk na jik’e hawaye sai malalo min yake kamar bakin teku. Baya na rinka ja ina kallon mai zai biyo baya, daɗin abin hankali mutane baya kanmu sabida sunata cin abinci.
“Yanzu dai na tabbatar a jakunan duniya, kinfi kowa jakanci” ya faɗa a hasalce. Tsuru tsuru nayi bance komai ba. Mansura ce tazo da sauri “Kayi hakuri Mallam, Fadeela is very clumsy” “Kambu” na faɗa a raina
Word ɗin clumsy data fada ya bani haushi, bata ganin ya mareni ne? Kuma shine zata bini da zagi “toh saime idan na watsa mashi drink? Yafi karfi ne” Na fada ina turo baki tareda juya idanu duk salon marasa kunya.
“kefa na lura karaman mara kunya ne, kuma samarinki masu fruits basa nan balle su tare maki” ya faɗa sai kuma ya cigaba da sababi “kisan me zaki rinka faɗa kafin ki yaba ma aya zakinta”
Wasu yara suna guje guje sai suka tureni na sake watsa mashi, tasssssss ya sake dauke nida mari saida naja baya. “Dama bakisan ina raga maki bane saboda ke sa’ar k’anwata ce, amma bari na koya maki darasi”
“Daga yau kin gama rashin kunya, ko a mafarki kikaga wasu zasuyi zaki kwaɓe su”
Idanun kowa a kanmu, kafin kace ‘Jack Robinson’ Kowa ya dauki wayar shi anata video. Anata posting a snapchat da Instagram, dama Mallam Bahaushe yace idan ba’a yi faɗa a biki ba baya armashi. Koba komai an samu abin tseguntawa.
Ja da baya na rinka yi hannu na biyu a kunci na, Shi kuma Naufal ya dauki alwashin sai ya shiga jikinta da duka sosai saboda saita yaba ma aya zakin tareda bambance zare da abawa. Abinda yafi bashi haushi ko Ango bai gani ba balle kawai ace ya juya gida.
Damkarta yayi ya k’ara watsa mata mari, “Idan ka kasheta sai ka bani gawarta na mayar ma iyayenta” Abba ya faɗa ranshi a bace.
Sai a locacin ya tuna dasu Abba, sakinta yayi ta faɗi kasa wanwar tana kuka. Hall anata kallonsa ana tsegumi, Sadeeq ya sauko daga high table rai a bace.
Kallon up and down yayi ma Naufal sai yayi nuni ma Amaryarsa da hannu alamar tazo su tafi. Ko k’ara kallon Naufal baiyi ba suke wuce.
Abba hannunshi harɗe akan kirjinsa ya k’ura ma Naufal ido, wannan ɗebo ruwa dame yayi kama. shikuma yana kallon k’asa cikin nadama.
Baban Sadeeq yaketa kallon Fadeela, ajiyar zuciya yayi kafin yace, “Naufal ka ɗebo ruwan dafa kanka saboda if I’m not mistaking wannan yarinyar Grand Kadi ce na Bauchi”
Jikin Engr Hussain yayi la’asar “Dan Kuka mai jawo ma uwarsa jifa” ya ayyana a ransa.
Bashi ba har Naufal cikinsa yanata kaɗawa saboda kowa yasan cewa ba’a taɓa yaran manyan mutane a zauna lafiya, uwa uba yarinyar Grand Kadi gaba ɗaya. Yanzu yanzu within minutes zasu iya mayar da life dinka miserable.
#NiDaDiyata
*Xeemee you are appreciated, Allah ya bar zumunci*
*All rights reserved*
💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 7 ✨✨✨
Abdullah It was narrated that 'Abdullah said: "The Messenger of Allah said to us: 'O young men, whoever among you can afford it, let him get married, for it is more effective in lowering the gaze and guarding chastity, and whoever cannot then he should fast, for it will be a restraint (wija') for him.'"
********************
Sheshek’ar kukanta da sukaji ya dawo dasu hayacinsu, Abba ne ya matsa dab da ita ya fara magana kasa kasa, “kiyi hakuri diyata, insha Allah sai anbin miki hakkinki, nine mahaifinsa”
A hankali na daga ido na kalle dattijon dake magana, kammanninsu ɗaya babu bambanci. Bance komai ba illa rage sautin kukana ina Jan magina a hankali.
Alhaji Sulaiman (mahaifin Sadeeq) wanda yayi shiru kamar wanda ruwa yaci, a sanyaye yaje wajen tubur dinsu inda suka bar Alhaji Musa, shi dama baisan abinda ya faru ba sanadiyar yana waje yana waya.
“Ranka ya daɗe dama wani ɗan matsala ta taso” shikuma Alhaji Musa yace, “Injin dai lafiya?” tare suka koma inda su Naufal suke. Gaban Egnr faɗuwa yayi daya lura da Fuskarshi yayi kama dana Fadeela. Nan kowa yayi tsuru tsuru ana inda inda.
A gurguje mahaifin Sadeeq yayi mashi bayanin abinda ya faru, shiru yayi kafin yace, “Yarinya tashi ki faɗa sunan ki dana gidan ku?” ita kuma Fadeela tana daga ido ta ganshi saita barke da sabon kuka kai zaka zata locacin ake marinta.
“Big Daddy kasheni yakeso yayi wallahi” ta faɗa cikin sigar kuka.
“yi min shiru please, ni shiririta ne bana so” ya fada mata. Tsit tayi bata kara cewa komai ba,
“Ai abin yazo da sauki tunda na gida ne kuma ba matsala sai mu tafi gidan Grand Kadi, though ni banga abin tashin hankali anan ba, tayi rashin kunya kuma ya hukunta ta”
“ Ah ah gwara aje ayi abu cikin mutunci”, shi Abba abinda yasa ya nace su tafi a warware komai baifi akan iyayen Fadeela ba bcs yanzu sai a hana mutum sakat. Yanzu yanzu yaji tace kasheta akeso ayi.
Fadeela ta shiga motar Daddy babba(Alhaji Musa) shi kuma Abba da baban sadeeq suna mota daya, sai Naufal dake baya yana bin su. Yana tafe zuciyar shi yana mashi k’una, wai fisabilillah gidan Bad Luck zaije ya bada hakuri, tun dayake bai taba jiba.
Daddy babba yana tuk’i murna fal a zuciyarshi, shi kaɗai yasan dalilin haka. Sun isa gidansu Fadeela wanda ke GRA, katon gidan wanda komai akwai. Daga su Garden, swimming pool da kuma karamin basket ball court wanda yake da double function as tennis saboda Grand Kadi yana san motsa jiki.
Daga Naufal, baban Sadeeq da kuma Abba saida suka jinjina tsarin gidan, sum sum suka bi bayan Alhaji Sani. Ita kuma Fadeela tun kafin mai gadi ya buɗe kofa ta fito daga cikin mota tabi k’aramin gate ta shiga “Ho sarkin shagwaba” Daddy babba ya faɗa.
Bata iske kowa a falo ba sai motsi dataji a kitchen, da sauri ta haye upstairs kafin a risketa a fara mata tambaya. Su kuma su Naufal da Abbanshi sannu a hankali suka rinka bin Daddy babba har cikin Main parlour. Suna isa ciki sunyi Sallama sau wajen uku saiga Mommy ta fito tana gyara zaman gyalenta tareda amsawa.
“Abbansu Fadeela Kaine tafe?” ta fada fuskanta dauke da fara’a. Shi kuma ya murmusa sai yace, “Eh nine Hajia, kuma tafe da manyan baki nake” sai a lokacin ta mayar da hankalinta wajen su Naufal, fuskanta a sake tace masu sannu da zuwa. Wucewa tayi kitchen ta jero abinci akan tray saita kawo masu suci. “Bismillah mana” Daddy babba ya faɗa, su kuma Naufal mutuwar zaune sukayi saboda sun tuna idan mutum zai cuce ka saiya bari kun sake kafin ya ɗana maka tarko.
Upstairs mommy ta wuce domin ta kira Daddy, basuyi minti 5 ba sai gashi sun dawo tare. Zama yayi akayi gaisuwan mutunci, shi dai Daddy babba baice komai ba, gabzan abinci ya rinka yi yana santi tareda jinjina ma girkin mommy tunda ta iya sosai a matsayin ta na professional Chef. Daga bisani yace, “Ai tare muke da Diyata” Grand Kadi(Alkalin Alkalai) ne yace, “wanne daga ciki?”
“Auta nake nufi, sarkin shagwaba” yana kaiwa nan ya fara dariya. “Ban masan ta dawo daga bikin ba” Mommy ta fada. Shi dai Big Daddy saida ya cika Gizzard dinshi kafin yayi gyaran murya, gaban Naufal ne yayi mummuna faduwa. Dama tun yau abinda yake samu kenan but na yanzu ya ninka sau dubu.
Gyara babban rigarsa yayi, falo yayi tsit kowa naso yaji mai zai faɗa, “Da Alheri nazo” murmushi yayi wanda shi kadai yasan ma’ana shi, kowa kawai kallonsa yakeyi. Naufal duk ya k’agu yaji mai zai faɗa, “Dama batun auren ɗiyata ne da mijinta gashi kuna kallon shi” ba su Daddy ba har Abban Naufal saida suka mayar da idonsu kanshi.
Shi kuma zare ido yayi yana nuna kansa da ɗan yatsa, da kyar ya iya bude baki yace, “Da ni kuma?” kwarai da gaske, kai muke nufi Alhaji Sulaiman ya chapke. Shi dai Alhaji Hussain baice komai ba, ya bar ma Allah komai. Idan auren zai zame mashi rufin asiri ba’a tozarta shiba to gwara ayi.
“Yanzu dama akwai wanda aka ajiye ma Fadeela ta aura amma shine ba’a sanar dani ba? Kun kyauta min kenan? NI DA DIYATA amma sai ayi abu ba’a shawarce niba. Idanun Mommy fal da hawaye take magana cikin k’aramin murya.
Grand Kadi zaiyi magana sai Big Daddy yace, “bazan canza magana taba, dole ayi bikin nan. Badun ina san Fadeela ba da nasa ayi bikin nanda 6 weeks but zan k’ara mata wani 6 weeks din kunga ya kasance 3 months kenan sai ayi proper gaisuwan iyaye da kuma biyan sadaki”
Shi dai Naufal tunda yake bai taba ganin something that is absurd ba Kamar yau, “ya mare yarinya, maimakon a hukunta shi sai aka bashi ita a matsayin mata. Bai taba ganin inda aka ɓare gyaɗa aka tsinci mota ba.
Daga alamu sun gaji da annoban data ke jawo masu ne shi ne ake so a mak’ala mashi, amma bazai yiwu asha fate ranar sallah ba” Ranshi a bace ya ɗaga green eyes dinshi wanda idan ranshi ya baci yana glimmering, zaiyi magana sai ga Fadeela ta fito tana kuka.
A kasa ta zauna gefen Daddy tana facing Big Daddy, muryanta k’asa k’asa ta soma magana, sai kayi da kyar kafin kaji abinda take faɗi. “Please alfarma nake nema gurin ku, kunsan cewa tun dana ke ban taɓa saɓa maku ba?
Ina kokarin fulfilling all righteousness a matsayina na yarinyar ku. Banida kamar ku a fadin duniya, dama daga Allah, Manzaninsa tareda sahabbai kune next danake bi.” Gyara zamanta tayi tare da durk’usawa, hannunta biyu a harɗe saita sunkuyar da kanta k’asa, “please kada kuce na aure……”
Tas…. Mommy ta dauketa da wawan mari, “halan nan gurin sa’anki ne ke zaune? don raini ina kokarin k’wato maki hakkin ki shine zaki watsa min k’asa a ido wai ga zance ga magana, dan ace nike sangartar dake”
Ya isa haka Hajia, “ai gwara ta faɗi ra’ayinta amma bazai canza komai ba saboda sai anyi” Big Daddy ya chapke. Ita kuma Mommy ranta ya baci saboda da Fadeela bata fito ba data san yanda zatayi ta ruguza abin, amma yanzu tana cewa kule za’a ce sun haɗa baki ne. Amma tabbas yau saita shiga jikinta da duka, tunda ta ruguza mata plan dinta bcs of her stupidity.
Fadeela tana Sheshek’ar kuka ta koma ɗakinta, shi kuma suka mayar da idan su kan shi, wanda baka ganin komai sai green eyes kawai, “Kanada ja ne?” Alhaji Sulaiman ya faɗa. “Gaskiya kuyi min afuwa, ni inada wanda zan aura kuma alamomin munafiki ne idan yayi alkawari ya saɓa” Mallam rufe mana baki, Abba yayi magana a karo na farko tun bayan sun gaisa.
“Nifa bazan aureta ba” ya fada tareda mikewa, kallonsa kowa keyi “Grand Kadi kayi hakuri akan abinda nayi ma yarka which nasan Baka sani ba, but bazan aureta ba saboda wasu dalili nawa”
wucewa yayi ya nufe hanyar kofa, “Naufal karka bar gidan nan batare da na baka izini ba” Abba ya faɗa mashi amma yayi kunnen uwar shegu yayi ficewarsa. Yana tafe yana haki, “wai Bad luck za’a haɗa ni da ita! Ta kashe ni kenan da bak’in jininta. Sam Sam bazai yiwu ba” yana tafe yana faɗa ma kansa har ya kai wajen motarsa.
Haka ya fito daga cikin gidan su Fadeela sai yayi shawara yaje gurin Mamansa ya shawo kanta ta mara masa baya dukda tana fushi dashi akan yawan zuwa wajen Anty Saudah tareda daukar ɗawainiyan Miemie.
Ya hau babban titi yana tsugaga gudu baji ba gani, kuuuu yayi kokarin taka birki yayin daya lura da ɗan ga ruwa yana tura amalanken sa. left Naufal yayi kokarin zuwa cikin tashin hankali tareda rankamo salati but ashe masu Fruits da kuma balangu suna wajen wanda shi baima lura dasu ba. Saisaita steering dinsa yayi a firgice but sai da yayi Karon rago dasu. Nan take ya sume sanadiyar buga kanshi daya yi.....
Su kuma mutanen wajen salati suka rinka jerowa, daɗin abin kowa ya kauce. Gaggawa aka je bashi, anata dambe da mota da kyar aka fito dashi. Tun sanda aka fara cincibarsa ya farka amma baice komai ba saida aka ajiye shi.
A hankali ya ware idonsa ya rinka kallon wanda suka ceceshi. “Ina fatan babu wanda yaji ciwo?”
“Alhamdulillah babu kowa ya kauce” wani dattijo ya amsa shi.
“Amma Mallam kai ɗan rainin wayo ne, dan wulakanci zaka hau titi kayi ta zura gudu kamar na ubanka” Wani matashi ya faɗa
“Toh wallahi ba zanyi asara ba, ko a bayani kuɗin Fruits ɗina kona tada zaune tsaye yanzu yanzu” ya faɗa yana zaro ido tareda lakwansa baki.
Shiru Naufal yayi saboda yasan duk me ya faru dashi laifin shi ne, iyaye ba abin wasa bane. Bazai disrespecting dinsu hankali kwance ba. Gaskiyar Mallam Bahaushe ne daya ce “Rashin bin maganar iyaye hatsari ne” gashi abin ya zama mai hatsari physically ba a baki kawai ba.
Su kuma su Abban Naufal shiru sukayi kunya sai ɗawainiya dasu takeyi. Mommy ce tace, “naji yayi maganar wani abu ya faru, halan lafiya?” Nan Abban Naufal da kanshi ya labarta masu daki daki abinda ya faru.
Mommy shiru tayi kada ta tozarta Daddy ace matarsa batada kintsi yasa bata k’ara cewa komai ba. Amma bazata yarda ayi auren nan ba, bata taɓa jin inda aka ɓare gyaɗa aka tsinci mota ba.
Su Engr bada hakuri suka kara yi kuma fuskar Grand Kadi a sake. Shi kuma Alhaji Musa yace hakuri ɗaya zaiyi idan aka sa Naufal yayi auren nan. “Kar ka damu, nima auren nake so yayi tuntuni amma yaki. Aiko gawarsa ne sai an daura” Engr ya jaddada.
Grand Kadi har mota ya rakasu ana raha. Shi dai bashida abin cewa, duk abinda Big Daddy yace shi za’ayi. Saboda matsayin shi yafi karfin haka a wajen shi, yayi mai hallaci sosai a baya saboda haka bazai watsa mashi k’asa a ido ba. Ita kuma Mommy idanta ya cika fal da hawaye, kullum addu’a take Allah ya ba Fadeela miji mai tausayinta amma gashi za’a haɗata da wannan gwaskar.
Haka Naufal ya wuce wajen motarshi domin ya dauko masu kudi. Dama yayi withdrawing kuɗin dazai lik’i ne. Dubu goma sha biyar yaba mai Fruits su rage asara, sai yaba mai nama dubu goma. Shi kuma mai ga ruwa aka bashi dubu ɗaya da ɗari biyar, sauran mutanen wajen su uku ya basu dubu ɗaya ɗaya.
Haka ya koma motarshi datayi damaging, glass sun farfashe handle din kofa ya lankwashe. Komai dai babu kyan gani, ya shiga ya fara tuk’awa sai motar tanata hayaki tareda k’ara kamar Vespa. Tafiya yakeyi kamar bayayi saboda bashida maraba da kunkuru. Kowa kallonsa yakeyi yana kwafa bcs duk ya ishesu.
Abban Naufal ya kira Anty Saudah a waya yaji ko Naufal na wajenta amma tace rabonta dashi tun kafin yaje dinner. Abba ya rasa a inda Naufal ya koya mugun ɗabi’a amma ya dauki alwashin anyi na farko anyi na karshe. Zuwa gida yayi ya wuce bayi kai tsaye yayi wanka, daya fito saiya saka wani Ash jallabiya haka.
Daukar jaridar Daily Trust yayi ya wuce Varenda yana jiran shigowar Naufal, zama yayi a kujerun wajen saiya ɗaura kafa ɗaya kan ɗaya. Baya ma gane jaridar kawai k’afarshi yana karkarwa.
Sannu a hankali Naufal ya rinka gungura motarsa har gidansu, k’aran ɓararan motan ya sanar dakowa gashi nan zuwa, ga kuma hayaki kamar ana gobara. Yana zuwa mai gadi saida ya leka ta karamin gate yaga waye kafin yagane Naufal ne.
Shikuma Naufal tunanin shi ɗaya yazai yi da annoban ta, wai ace daga zuwa gidansu har ya kusa mutuwa, ina ace inuwar su ɗaya.
Yana isa parking lot ya ajiye motarsa zai wuce BQ inda ɗakinsa yake. Sam baiyi tunanin zaiga kowa war haka daren nan.
“Mallam zo nan” Abba ya faɗa fuskarshi babu wasa. Sum sum Naufal yaje waje, tun yau abubuwa mara misaltuwa ke faruwa dashi, yanzu a gajiye yake yayi likis. Yana isa ya ɗuka kasa alamar girmamawa.
Abba baiyi wata wata ba ya wanka mashi mari kyawawa guda biyu. “Faɗa min daga inda kake ka shigo min gida cikin dare kamar ɓarawo?” kanshi duk’e baice komai ba, shiru kawai yayi yana tunanin irin marin da zai rinka dauke Fadeela dashi. Saboda aurenshi zai zamo mata bak’in canji a rayuwarta.
#NiDaDiyata
*All rights reserved*
💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 8 ✨✨✨
*A LESSON*
The Holy Prophet(SAW) said, "Stop doing everything during the ADHAAN(calling of prayer), even reading the Holy Quran, the person who talks during the Adhan shall be deprived of saying the KALIMATUSH-SHAHADA when he or she is about to die! May Allah guide us...
*********
“Dama na danyi wani k’aramin hatsari ne” Naufal ya amsa ma Abba still yana ɗuk’e a kasa. Shiru Abba yayi na wajen 5 minutes yana tunani irin halin Naufal. Ajiyar zuciya yayi abin duniya ya isheshi sai yace “Wato sabon alkawarin daka dauka ma kanka kenan koh?’’
“Yanzu bazaka barni na sha ruwa a garin Bauchi ba koh? Idan an hanaka mutuwa sai ka suma. Shi kenan yanzu dan na haife ka banida sauran kwanciyar hankali a tareda ni kuma. Kana abu kamar k’aramin yaro.”
“Wai tsakani da Allah Naufal mena rageka dashi da kake so bakin cikin ka ya kasheni. Haba mana! Bafa kai kaɗai na haifa ba balle kamin haka, idan ka gaji ne sai kayi min bayani na yafeka a cikin yarana then we can call it a day”
“Kayi hakuri dan Allah Abba Wallahi bai kai zafin haka ba, tsautsayi ne kawai aka samu. Kuma wanda nayi hatsari a gefen su ko qurjewa basuyi ba” Naufal ya faɗa yana tunanin yayi abin arziki. “Ai bakayi gwaninta ba, daka kashesu ne saina san ka cika namiji” Abba ya amsa.
Ita kuma Bilqees ta tashi karatun TDB saboda tanada test saita ji hayaniya a varenda. A hankali taje taga ta lek’a sai idonta yayi arba dana Abba. “Zo nan” ya faɗa ita kuma ta fara jan k’afa duk takaici tace a hankali “I don dieooo.... Meya kawoni wajen nan” haka taje wajen Abba ta durkusa “Gani Abba”
Kallon sama da kasa yayi mata saiya ce, “kije ki tada Abla da Maman ku sai kuzo ku sameni gabaki ɗayan ku a falo” ya faɗa tareda kallon Naufal alamar harda shi.
20 mins later....
Duk suna zaune a falon Engr, Mama da Naufal ke kan one one seater, su Abla ana k’asa ana turo baki. Mama tana ɗan jijiga kafarta ta cika tayi fam. Ita bata ga dalilin da za’a tasheta cikin tsakar dare ba? Wani zuciya ya raya mata ai aikin Anty Saudah ne. Tsaki tayi a ranta sannan ta faɗa “Nayi maki nisa mahaifiyar mahaukaciya”
“Abba gamu mun zo” Abla ta sake maimaitawa a karo na biyu. “Ai na ganku since niba makaho bane” shiru ya k’ara yi wanda Fallon baka jin komai sai motsin jaridar dake hannunsa. Kafarsa ɗaya akan ɗaya yana karkaɗasu, shikuma Naufal bai taɓa gajiya kamar na yauba. Kwakwalwarsa sai chaji yake yi a hankali don komai yayi masa zafi.
“Hajia Sarai” Na’am Alhaji ta amsa tana kallon gefe.
“Naufal” Na’am Abba
“Abla” Abba Na’am
“Bilqees” Na’am
Ya kira sunan su ko kallonsu baiyi ba still yana duba jarida. Ajiyar zuciya yayi saiya ajiye akan centre table kafin ya mayar da hankalin shi kansu.
“Wannan gidana ne bana wani ba! Saboda haka dole abi dokoki na. My house my rules”
“Bazai yiwu akawo min raini under my roof ba, akan me? Bari kuji daga yau an daina tozarta ni. Ban ɓata ma iyayena suna ba bazaku ɓata min nawa sunan ba, haba!”
“Hajia Sarai daga yau kin gama Kishi da Hajia Saudah, shekararmu wajen sha shida da aure amma kinki saka ma zuciyar ki salama. Daga yau sai yau bana so na kara jin kin takaleta ko wani abu makamancin haka. You are going to be nice to her and her daughter, Zaki rinka zuwa kina dubasu kuma zaki bar yaranki suje” yana kaiwa nan ya numfasa.
“Naufal! Dole ka aure Fadeela, kuma you will treat her nicely. Gobe zakaje kabama iyayenta hakuri da ita kanta. Zakayi auren nan cikin daɗin rai, yar mutunci zaka aura dole ka mutunta ta. Batun Miemie kuma banida abin cewa sai Allah ya saka da alheri” shiru Naufal yayi baice komai ba saboda duk gabobin sa yana mashi ciwo.
“Abla da Bilqees ku fito da mijin aure tun kafin nakai hoton ku masallaci, musamman ke Abla tunda kece babba. Kuma zaku rinka zuwa wajen Miemie kuna dubata”
Yana kaiwa nan ya dauko jaridar sa tareda fadin “Duk wanda yaga bazai iya bin abinda nace ba sai yayi hanyar gate yanzun nan or else kowa yaje ya kwanta”
Naufal ya fara tashi tsaye tareda faɗin “Saida safe Abba” saiyayi hanyar BQ. Sai mama ta tashi tayi hanyar ɗakinta. Su Abla suma saida safe sukace sakayi hanyar ɗakinsu. Murmushi Engr yayi saboda ya fara dawo da tarbiyan gidansa hanya madaidaciya.
“Nifa ban gane me ake nufi da Ya Naufal zai yi aure ba?” Bilqees ta faɗa. “Shine nima naji gashi kin sanshi yanada bala’in taste” Abla ta amsa
Bilqees tayi ajiyar zuciya kafin tace, “Fadeela! Ko wacece ita?”
WACECE FADEELA ?
Marigayi Mallam Bello ya haifa yara biyu tal a duniya. Musa da Abbas, ya rasu babban yaronshi yanada shekara 21 duniya. Dukda k’arancin shekarunsa bai hanashi rike mahaifiyarsa tareda kaninsa ba. Shiyayi jjigilarsa harya zama lawyer gashi yanzu shine Grand Kadi, yanzu Sam bazai iya musa masa ba akan alfarma saboda shine mahaifinshi.
Alhaji Musa wanda ake kira Big Daddy yanada yara biyar, Maimuna, Zainab, Hafsat, Safiya sai auta Mubarak. Sunar matarshi Hajia Rabi.Yanzu haka duka yaranshi mata na zaune lafiya lau gidan mazajen su thou Zainab aurenta na biyu kenan. Jikoki 14 Big Daddy yakeda.
Shikuma Grand Kadi Abbas yanada yara uku, Jawahir, Muhsin sai auta Fadeela. Jawahir tanada yara uku, Yanbiyu Abdulrahman da Abdulrazak sai Fauziya. Shi kuma Muhsin yana Masters a Dubai tareda Mubarak shi kuma degree yakeyi . Ita kuma Fadeela tana 400l a ATBU Bauchi tana karanta fine arts.
Fadeela dai yarinya ce mai natsuwa ga dadin zama, ta san ya kamata saboda ba’a yi masu wasa da tarbiya ba. Fara ce daidai misali, bazaka cemata kyakyawa ba amma babu muni a fuskarta, daidai gwargwado take Tabarakta mashaAllah.
Siririya ce kuma tanada ɗan tsawo. Gashin kanta yanada santsi amma bashida tsawo bai wuce cikin cokali ba. One good about her shine she is very classy, ta haɗu iya haɗuwa. Dressing A1 take ci saboda tasan fashion trends.
A duniya tanada bala’in san yara, domin ko a bus saita murmusa masu. Burinta ɗaya ta haifinata but gashi yanzu an haɗa ta da wanda ya tsaneta. AllahuMusta’an kawai take faɗi.
Matsalarta guda biyu ne.
1.Tana san shan waka kamar ibada.
2.Ta fiye sanya sanya da nawa ko wajen magana.
But dama dan Adam ajizine, dukda wannan bata san raini at all. Bataga dalilin da bazaku mutunta juna ba.
Wannan kenan!
*********
Daga ɗayen bangaren Fadeela ta koma ɗaki ta shiga cikin bargo ta duk’unkune sai kyarma takeyi, duk zazzabi na farad ɗaya yayi awon gaba da ita. Momy kai tsaye ɗakin Fadeela ta nufa saboda saita cin mata. Tana tura kofa taji abuɗe but wuta a kashe. “Gwara da baki rufe ba” momy ta faɗa da karfi.
“Dan rashin hankali uban waye sa’anki? Muna magana zaki shigo mana da zancen banza” sai Momy ta fizge blanket dinta. Yanayin dataga Fadeela ya bata tausayi sai ta mayar da duk wani abu data je dashi. Dama ita Fadeela bata iya fushi ba, abu kadan sai ta hau zazzabi.
Zama tayi akan gadon ta jawo ta jikinta, rau taji zafi kamar ana shirin soya kwai. A hankali ta soma magana “Yi hakuri auta, komai ya faru da mutum daga Allah ne. Kwantar da hankalinki. Gobe zani wajen Big Daddy na rok’esa alfarma, but idan bai yarda ba Please im begging you in kina gidansa I want you to show him how well trained you are.”
“Please Karki bani kunya, ki nuna masa ke yar halas ce kuma yar mutunci” haka Momy tayita rarrashinta tana mata nasiha har barci ya kwashe ta.
Washegari, 4:56am…..
Abba ne yake tafiya zuwa ɗakin Naufal domin tadashi su wuce masallaci sallar asuba, dama ɗabi’ansu ne muddin Naufal ya kwana a gidan. Ya mika hannu zai kwankwasa kofa sai ga Naufal ya buɗe zai fito, “Alhamdulillah ai ka hutar sheni” Abba ya faɗa yana murmushi. Shi kuma Naufal murmushi ya mayar masa sai suka jera suka yi hanyar masjid.
Bayan sun idar suna dawowa sai Naufal ya koma ɗakin shi, shi kuma Abba ɗakinsu Abla ya wuce direct yaga yanda suke. Bilqees ya gani tana karatun Al Quran sai Abla tana zura hijab da alamun sallah zatayi, baice komai ba ya wuce ɗakin Mama. Itama tana bayi da alamu alwala takeyi.
Tunani ya soma yi bcs iyalinshi na kokarin kare hakkin addini, kwata kwata baisan idan Naufal ya debo halinshi na jiya ba. “Maybe he is the black sheep of the family” wani zuciya ta raya mai. “Allah dai ya shirya shi” ya fada a fili. TV ya kunna ya kalle sunna TV inda ake hira da Bn Uthman sai wajen 6am ya koma NTA inda zai kalle AM Express.
6:30am…
Locacin ne Fadeela ta tashi, kasancewar bata sallah yasa ta ɗan kara barci. Da kyar take tafiya bata ko ganin gabarta sanadiyar kukan data ci which ya haifar mata da azabataccen ciwon kai mai sara kamar na gatari.
Tana tafe tana tangal tangal kamar yar k’waya, ruwan zafi ta watsa a jikinta saita soma samun kanta. A daddafe ta wuce ta haɗa ma kanta Espresso a PS Gucci Nespresso machine dinta dake dakin tunda ita ma’abociyar shan coffee ne. A yanayinta na sanya sanya ta wuce bedside drawer dinta ta dauki Paracetamol, Boska da Panadol extra duk ta hadiye. Saita jingina akan gado tana ajiyar zuciya.
Hawaye ke gangaro mata data tuna sabon rayuwar da zata shiga, within minutes life dinta yayi shredding into pieces. Dogon ajiyar zuciya ta yi saita ce “Alhamdulillah ala kullu halin” a fili saita mike tsam ta saka kaya. Wani valvet overall ne kuma yana cikin kayan zaman gidanta.
Dakin Daddy ta soma zuwa, a kan couch ta ganshi yana duba Alqur’ani da wasu takardu a gefensa da alamu yanada court case. “Assalamu Alaikum Daddy” ta faɗa a sanyaye tareda da zuwa gefensa ta zauna.
“Wa’alaikumus Salam, Auta kin tashi lafiya”
“lafia lau, hope kaima haka?”
Kallonta ya tsaya yi yanda bata nuna wani damuwa akan batun jiya ba, abinda yasa tafi burgeshi kenan a yaransa saboda batada riko kwata kwata.
“Daddy wat are you working on?” ta fada tareda daukar ɗaya daga cikin papers din kan table.
“kul ki ajiye” ya faɗa yana dariya
“Wannan aikin na manya ne”
Murmushi tayi saita ce, “me zan haɗa maka na breakfast?”
“Na hutarshe ki, matana chef ne so zata yi min gangariya” ya faɗa yana dariya. Ita ma dariya ta soma yi bcs a duniya parents dinta su ne relationship crush dinta. Yanda suke abinsu cikin mutunci da girmamawa yana burgeta sosai.
Kullum fatan ta itama ta samu koda rabine, idanunta suka ciko da kwalla data tuna Naufal, da sauri ta mike kada Daddy yaga yana yinta. “Daddy ayi aiki lafia, bari na duba Mommy” bata bari ya amsa ba tayi gaba abinta.
Share k’aramin kwalla daya soma gangaro mata tayi, ɗakin Mommy ta shiga which is adjacent to na Daddy. Tana tura ɗakin sai taga duhu alamun momy ta koma barci, itama zuwa tayi ta shiga bargon ta kwanta. Ido ta kafa ma Mommy kur, “kaza mai ‘ya’ya bata mai” Mommy tace tareda murmushi.
“watau baza’a barni nayi barci hankali kwance ba?”
“Mommy ina kwana?”
“lafia lau auta ya hakuri damu?”
Dariya Fadeela tayi sosai saita canza topic din, “Daddy yace zakiyi masa gangariya”
“Na sani Malama ba sai kin faɗa ba” sai Mommy ta kalle silver and black agogon bangon dake manne. “Innalillahi bari na tashi kaɗa na makara, today I’ve a lot of things da zanyi”
Ita Fadeela tana so ta tambaya Mommy ko abubuwan data keso tayi ya jiɓance zuwa gurin Big Daddy but ta kasa magana.
“Mommy please kada Kije wajen big Daddy kafin yace mun raina shi” ta faɗa idonta fal da hawaye. Kallonta Mommy tayi tana nazarinta kafin tace, “akan me Auta? Kin taba ganin inda mutum ya bude gyaɗa ya tsinci mota?”
“marinki fa yayi shine za’a aura miki shi ya kashe ki gaba daya”
“Mommy ba abinda nake nufi ba kenan, idan Allah ya kaddara auren babu abinda zamu iya and vice versa. Kawai bana so muyi forcing komai ne muyi ma Allah shishigi kafin muji kunya”
“Besides dan ya mareni is not the worst scenario that people meet their spouse, Wasu fah a social media suke haɗuwa”
Mommy shiru tayi tana kallon ɗiyarta, “Gaskiya hankali baiwa ne kuma idan Allah ya baka sai kawai ka gode masa” jawota tayi jikinta tana jin dumin ta. A hankali tace, “Nagode Fadeela” which is rare ake kiranta, anfi ce mata Auta har masu gadi da makwabta.
4:38pm…
Jallabiya ya dauko sabuwa fara sol ya saka, sai ya haɗa da bakin wando tareda bakin hula. Fashe kanshi yayi da turaren Yes Saint Laurent yana tafe yana shan kamshi, gashi kuma rana ya fara sauka so emerald eyes dinshi yana ɗan glimmering.
“wannan wanka haka? Ya Naufal sai ina?” Bilqees ta faɗa daga gani ta dawo daga School ne.
“Kinsan niba sa’anki bane?” abinda yasa yayi mata magana in a rude way baifi haushin zuwa wajen Bad Luck da zai yi, wanda har yanzu bai taba faɗin sunanta ba.
“Yi hakuri but please jirani na dauko kayana saika ajiye ni wajen Anty Saudah anan zan kwana yau”
Kallonta yayi baice komai ba, mamaki karara a fuskarshi sai kuma ya tuna Bilqees batada matsala probably Mama ke zugata, mai zafin kan gidansu bai wuce Amatullah ba kuma tana chan ta karata da mijinta.
“Karki bata min locaci” ya faɗa yayi hanyar motan Abba tunda ya kai nashi gyara.
Ya ajiye Bilqees a gidan gona saiga Miemie tazo da gudu, “Ya Naufal wai da gaske zakayi aure?” ta faɗa tana haki. Shi kuma yace “bakya so ne?”
“Ina so mana sosai ma kuwa, na gaji da Mommy kaga sai na dawo wajenta” ta faɗa tana waige waige. Shi yaso tace Ah ah amma ta bashi haushi kawai. Kwafa yayi “dama wayace na tambaya mahaukaciya abu?” ya faɗa a ransa.
Tun kafin ya kai gidansu Fadeela yake addu’o’I, shifa ya riga ya chamfa duk randa ya ganta sai wani mugun abu ya same shi. “La ila inna anta subhanaka inni kuntu minnal zalumin” yaketa maimaitawa while driving har ya isa cikin gidan…..
#NiDaDiyata
I'm really sorry for my silence, buki mukayi. Uncle Usman Allah ya baka zaman lafiya da amaryar ka Rahama.
*All rights reserved *
💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 9 ✨✨✨
It was narrated from Hakim bin Muawiyah, from his father, that a man asked the Prophet(): "What are the right of the woman over her husband?" He said: "That he should feed her as he feeds himself and clothe her as he clothes himself; he should not strike her on the face nor disfigure her, and he should not abandon her except in the house (as a form of discipline)." (Hassan)
*********
Ina kwance akan sallaya bayan na idar da sallar Asr, lazimi nake tayi harna gaji. Dama ni kaɗai ke gidan Mommy taje supervising wani catering services haka. Anty Husna ce ta shigo wai ana sallama da dani.
Shiru nayi bance komai ba, sai kuma na Mike zaune ina fuskantar ta tareda wani irin kallo. Saboda ni kwata kwata I’m not expecting any male visitor, though I don’t have plenty of them.
“Wanene?”
“Ina ganin yana cikin bak’in jiya” ta amsa mani.
“Oh!”
Na faɗa saina yi kwanciya na, nifa tukura ne banso. Watau shi har yana san auren kenan da har zaizo zance wajena. “mts” naja tsaki mai bala’in k’ara.
Ita kuma Anty Husna har takai stairs sai wani zuciya ya raya mata kamar fah Fadeela bazata fito ba. Juyawa tayi nan take ta koma ɗakin. Inda ta barta nan ta same ta.
“Auta kinyi bak’o shine kike kwance? Babu kyau wulakanci! Kije kiji mai zai ce mana, koba komai su Hajia basu ji dadi ba idan kika raina sa, kuma bakya tsoro kada ya rama idan an kai ki?”
Mai aikin mu Anty Husna ta faɗa, ni kuma shiru nayi sai daga bisani nace,
“Haba Anty wani irin wulakanci kuma! Wallahi bansan me nayi masa ba. Kwata kwata ya tsane ni, kamar ya sanni a wani waje. I just can’t figure it out. Kina ganin Idonshi zakiga tsanata a ciki karara”
Na faɗa idona fal da hawaye, kallona ta tsaya yi saita ce, “Kiyi hakuri, wata rana sai labari. Kinsan cewa mai hakuri yana dafa dutse harya sha romonta” miko min hannunta tayi saina kama tareda mikewa tsaye.
Drawer na wuce na dauki Swiss lace orange mai ratsan purple da silver. Saina dauki purple gyale wanda ake ce masa Aisha Buhari na saka tareda takalmin Zara.
Fuskana payau babu makeup sai pink lip gloss wanda ya kara ma pink lips ɗina armashi kafin yace ina sanshi yasa nayi masa kwalliya.
Shi kuma Naufal bayan yayi parking motarshi sai yaje wajen mai gadi akan yayi mashi iso da mai gidan, to anan ne aka faɗa mashi babu kowa a gidan illa Fadeela. Shiru yayi kafin yace to ayi mashi iso da ita.
“karshen wahala bai fi mutuwa ba, kila yau zata kasheni kowa ma ya huta” ya faɗa a ranshi. Haka yayita zaman jiranta tareda latsa wayarshi tunda shi ma’abocin Instagram ne. Yana cikin motarshi ya shafa’a ya mance da komai sai yaji kamshin turaren da bazai mance dashi ba.
“Chanel No 5” ya faɗa a fili yayin da ya ɗago green eyes dinshi. “Assalamu Alaikum” na faɗa da murya kasa kasa tareda tsayawa gefen motan. “Wa’alaikumus Salam” ya amsa mani sai ya mayar da hankali shi akan wayar shi.
Ni firgitani yayi, bashida maraba da mage. Ga Green eyes ga bakin fata, sunkuyar da kaina kasa nayi ina wasa da yastuna.
Bayan 45 mins……
Haka na cigaba da wasa da yatsuna ina regretting rashin fita da banyi da wayana ba, koba komai zan buga Candy Crush.
Shikuma Naufal kwata kwata ta birkitar dashi da kamshinta, turaren data saka irinshi Ex Gf dinshi Anastacia take sawa. Sunyi soyayya sosai a London sai daga baya ta guje shi wai bazata aure Musulmi ba.
Acewarta Muslims are terrorist. Yayi kokarin wayer mata da kanta about Islam amma ta kafe. Abin ya ɗaga mashi hankali sosai har ya kusan shiga wani hali da bai dace ba. Bayan aukuwan abin da 2 weeks sai yagane ashe Anastacia aure zatayi da Mayor din district dinsu.
Zuciyar shi ya fara mai zafi sanadiyar tuna Anastacia daya yi, duk wani assignments shi ke mata kuma har exams yayi mata amma ta guje shi. “Birds of the same feathers” ya faɗa tareda kwafa.
Shi yanzu tsanar Fadeela ya karu a zuciyar shi, dukda tanada kyau kuma she is hot but tana firgita shi gata kuma da bala’in nawa. Deep down yasan champi haramun ne a musulunci but he can’t help himself to blame her for all the bad stuff in his life. Yasa ya basar da ita baice mata komai ba thou yana ankare da every move dinta, ya lura sai kwafa takeyi tana girgiza kafanta.
“kaɗan ma kika gani” ya faɗa yana kallonta ta gefen ido. Haushi ya kamani sosai amma nayi kokarin controlling kaina. Insha Allah bazan nuna mashi I’m weak ba, saidai yayi ya gaji. Muna cikin haka ne saiga Daddy yazo.
Da sauri Naufal ya fito daga motarshi, nima naje wajen Daddy ina shagwaba. “Ashe Daddy’s gal ce…. Tabdi!” ya fada a ranshi. Mikama Daddy hannu yayi suka gaisa tareda risinawa.
Daddy da fara’arsa ya amsa. “wannan wani irin mutane ne da ake masu abu basa nunawa” Naufal ya sake faɗa a ransa.
“Ah ah Mallam Naufal kaine tafe haka?” sai kuma ya mayar da fuskarshi kan Fadeela “ya baki kai shi cikin ɗaki ba”
“Daddy tun fa dazu yazo yanzu ma tafiya zaiyi sai gaka ka dawo”
“oh! Allah sarki toh mu shiga mu kara gaisawa” haka suka wuce cikin falon Grand Kadi suka zauna. Naufal sai inda inda yakeyi.
Grand Kadi ya lura akwai magana bakinshi, saiya canza topic din tareda mashi tambayoyi akan aiki da sauran al’amura. Daidai gwargwado Naufal ya bashi amsa saboda ya lura audition Daddy yake yi akan auren ‘yarsa, shi kuma Daddy ya yaba da ɗabi’un sa, murna fal ransa saboda koba komai in sha Allah ba zasuyi zaɓen tumun dare ba, wannan shi Mallam Bahaushe ke cewa ‘wai faɗuwa ne yazo daidai da zama’. Har wajen 30 mins sunata zantawa sai Naufal ya mike zai tafi.
“okay sai Fadeela ta raka ka mota”Daddy ya faɗa. Daga Deela har Naufal babu wanda yaji dadin abin amma haka suka hakura. Rakiyar da nayi ma Naufal was the longest journey of my life, shuru mukayi bamu ce uffan ba har muka kai parking lot.
Motar mommy ya danno kai, tsayawa yayi da fara’arsa na munafunci yana jiran ta iso. Bayan ta fito daga motar ta saiya risina ya gaishe ta yana wani kunya kunya. Sai kuma yace, “Mommy nazo bada hakuri jiya, nasan ban kyauta ba”
“Allah sarki ai babu komai, dama zo mu zauna zo mu saɓa ne” numfasawa tayi kafin ta ce “Allah yayi maka albarka”
“Amin Mommy” ya amsa dashi. Sai Mommy ta wuce cikin gida tana yabawa da halin surikin ta. Shi kuma motarshi ya shiga saiya mika ma Fadeela bandir din 500 naira. “ka bar abin ka bana so” na amsa mashi.
Kallon up and down yayi min, duk ya firgitani saboda Magrib yayi gashi idansa yana glimmering. Ban ankara ba sai naji ya tada motarshi, har ya fara tafiya saiya cilla min kudin a fuskata. Saiya faɗa “Kece matsiyaci ya amma badai niba”
Sororo na tsaya kallonshi har ya ɓace daga haraban gidan mu. Tunda nake ban taɓa ganin makirci irin nasa ba. Oh ni Fadeela ! Meke shirin Faruwa dani? Dukawa kasa nayi na dauke kudin tareda wucewa daki. Akan mirror na ajiye sai na kwanta akan gado na dauko sabuwar babin kuka.
#NiDaDiyata
*All Rights Reserved*
💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 10 ✨✨✨
Malik relate from Nafi that when Abdullah ibn Umar sneezed and someone said to him, "May Allah have mercy on you," (Yarhamuka'llah), he said, "May Allah have mercy on us and you, and forgive us and you." (Yarhamuna'llah wa yaghfirlana wa lakum)
***************
17 days later.....
MIEMIE
Tafiya takeyi cikin sauri sauri, kallabinta tamke akan qugun ta. Dayake tanada tsawon gashi haka wasu suka bazu a fuskarta har yana tsone mata ido.
Bata cireba haka ta barshi tana tafiya abinta. Ta kai babban titi near Bauchi club dake kusada makarantar su na Special school. Tana kokarin tsallake titi amma dataga mota ya danno kai koda ta kai rabi ne kuma motar yayi nesa da ita zata pella baya.
Tsaye yake gefen mai gasa masara yana kokarin ya siya, baima lura da wasu halitta ba a wajen balle ita. “Amma anyi wawiya” mai gashin masara ta faɗa. Juyawa yayi tareda cire tabaransa ya kalli abin ake magana akai. Wata yarinya ya gani wanda bazata kai 15 yrs ba tana guje guje a titi. Tsaki yayi ya mayar da tabaransa ido saiya mika ma mai gashin masara dari biyu “Keep change” ya faɗa sai yayi hanyar motarsa.
Ta kara komawa baya da gudu a karo na uku kuma duk a Idonsa. Tsaki ya karayi ya soma danna wayarsa ko ajikin sa. Wasu samari su uku sukaje wajen ta suna mata surutai, Ita kuma bata kula suba. “Bada ke nake magana ba?” ɗaya daga cikinsu ya faɗa tareda chapke mata gashin kanta. Kara ta saka wanda ya mayar da attention ɗin kowa kansu.
Kwafa yayi saiya fito daga motarshi da saurin gaske, “Kai meye haka Mallam, kanwata ce fah” ya faɗa tareda janyo ta zuwa inda motarsa yake. Buɗe kofar gaba yayi saiya turata ciki. Shima ya zagaya ɓangaren driver ya zauna saiya kunna motar tareda fadin “Inane gidan ku na kaiki”
Bata amsa mashi ba illa kuka data keyi, tana jin alamar ciwonta zai tashi ne yasa ta gudu daga school ta fara gantali akan titi. Duk a hargitse take kamar bible din hausa.
Daya lura batada niyar amsashi saiya kira babanshi which shine IG din yan sanda. Bayan wayan da wajen 45mins haka saiga babanshi ya iso tareda escorts dinshi. Kallo ɗaya yayi ma Miemie yasan cewa akwai alamar tambayan hankali a tareda ita.
Tag dinta na suna dake rataye akan Wuyanta wanda shi guy din baima lura ba babanshi ya ɗaga ya karanta. “Bauchi Special School” ya karanta. Sai ya mayar da attention dinshi kan yaronshi tareda faɗin “Khattab ai ga komai a rubuce don ruɗewa shine ka kirani, gashi an rubuta Laurat Hussain Beli” sosa k’eya Khattab yayi tareda dariya saboda yasan he wasn’t really paying attention to her.
Nan take IG yasa wasu police suzo su tafi da ita station ayi documenting komai cikin protocol. Nanfa ta soma dambe dasu wai bazata bar motan Khattab ba, shure shure takeyi tana hambarin police din idan kuma fatan ka ya kusa da bakinta saita ganna maka cizo. Haka tayi biji biji dasu tayi masu jina jina, su kuma suna raga mata ne saboda ba lafia ga yarinta. Daddyn Khattab yace su kyaleta.
“Bakyaso ki bisu ne?”
Gyada kai tayi alamar eh
“Ina ne gidan ku?”
“Ni tareda YaNaufal Zan tafi”
“Waye YaNaufal?”
ɗaga idonta tayi saita nuna Khattab. Sai IG yayi murmushi tareda faɗin, “Ai sunan shi ba Naufal ba, bakiji Khattab nake kiransa dashi ba.”
“Na sani amma idan mutum yanada kirki toh YaNaufal zan kirashi” tafada tana Sheshek’ar kukanta.
Khattab ne yace mai zai hana aje school dinta tunda gashi rubuce maybe aga family member dinta.
Daga ɗayan bangaren Anty Saudah take zaune dirshan a gaban school din Miemie wai sai an fito mata da ɗiyarta. Tun sanda driver ya koma gida wai babu Miemie babu dalilinta saita saɓa gyale tawuce makarantan tanata kuka. Su kuma school din Naufal suka kira a matsayin Next of kin dinta. Duk an taro hankali a tashe kowa yayi charko charko, Naufal tunanin shi ɗaya ya zaiyi idan ya rasa Lil sister dinshi.
Duk zufa yakeyi ya rasa meke masa dadi, har police station yaje yayi reporting babu wani kyakyawan labari. Su Abla da Bilqees suma sun samu labari hankalin su a tashe, sai Abba yace suje gidan gona incase Miemie ta gane hanyar gida. Ita ma Mama bataji dadin abin ba sanda ta samu labarin, tasan cewa babu daɗi babba yayi ɓatan hanya balle yaro. Kawai addu’a takeyi Allah yasa a ganta.
Su Khattab sun nufa hanyar makaranta Miemie za’a mayar da ita. Shi dai baice komai ba illa tuk’a mota, ita kuma kuka take rusawa. A hankali ya furta “Sunana Khattab ba Naufal ba” ta gefen ido ta kalle shi saita watsar.
“Na sani amma banga dama bane” ta faɗa tana fyace magina da kwallar riganta. Nan take abin yaba Khattab kyama saida yayi kakarin amai, dama shi abu kadan saiya saka shi amai. Waigawa yayi don yayimata magana sai ya hange tasono mak’ale a hancinta, da sauri ya buɗe window ya tsida miyau.
Ita kuma Fadeela tana cikin kitchen ta dafa abinci, Danbun shinkafa tayi wanda yasha zogale da gyada ga kuma nama k’anana a ciki. Sai kuma tayi juice ɗin garin kuka wanda yasha pineapple da cucumbers sai ta haɗashi da Sambousah. Ta jera a wasu fararen Italian coolers komai yayi tsaf sai san barka.
Bayi ta wuce tayi wanka tareda jero alwala, tayi nafilfilon ta saita haɗa da sallar Asr. Ita kadai tasan meke damunta saboda a duniya rainin wayau ne ta tsana. Tsaki ta doka tareda faɗin “Karma kazo mana tunda dama ban gayyace kaba” tana cikin haka ne saiga Mommy tazo, “Har yanzu Naufal ɗin bai zoba?”
“Eh shine nima na gani”
“To kira wayansa mana kiji ko lafiya”
Shiru Fadeela tayi bata san mezata ce ba, saboda rabonta da shi tun ranar daya watsa mata kudi, itama Mommy a Pharmacy suka haɗu shine sukayi exchanging number. Toh a bakinta ne Fadeela taji zaizo sai Mommy ta tursasa ta akan saita mashi girki.
Maza ki saka wannan kafin yazo baki shirya ba Kinga babu daɗi, ita kawai kallon Mommy takeyi yanda take rawar kai akan Naufal, “Da kinsan true colors dinshi da kin daina haka” ta faɗa a ranta. Tsam ta mike ta dauki kayan, Sky blue cord lace da akayi mashi ɗinkin kimono. Batayi makeup ba saboda acewarta kanayi ne wajen burge mutum kuma ita tsakani da Allah bata sanshi kawai tasan cewa dole ta mutunta shi.
Su Khattab sannu a hankali suka isa school din Miemie, suna gaba su IG da escorts na baya. Kashe engines dinshi yayi saiya ce, “Okay sauka muje wajen Principal” bata kulashiba kuma bata nuna tanada alamar motsawa ba. Sauka yayi saiya zaga ta ɗayen bangaren. Dayake motarsa Range rover ne kuma it’s somehow high sai Khattab ya mika mata hannun sa ta kama ta sauko.
Aiko a idan Naufal akayi haka, da sauri ya karasa tareda cin kwallarsa “Ubanwa ya baka dama ka dauki k’anwata? Da harzaka sakata a cikin akwalan motar ka salan whitlow ya kamata”
Kafin Khattab ya amsa Abba yace, “Meye haka kake yi sai kace dage? Dalla sake shi” bai so ba saiya sake shi. Ita kuma Miemie kallon kowa tayi saita ruga motar Khattab ta dauke Masara a ciki ta fara gabza. Naufal ranshi yayi bala’in baci, “Zo nan Mallama bana hanaki barin school ba? Hawan jini kike so ya kamani na mutu koh? Shikenan na tafi naje na mutu” sai yayi hanyar motarshi. A guje taje tana bashi hakuri saboda a duniya ta tsani wasan mutuwa.
Su kuma su Abban Khattab yayi Introducing kanshi a matsayin Inspector General Hamza Aminu Danbatta. Anan sukayi gaisuwan mutunci shine ya zayyana masu yanda Khattab ya tsinci Miemie. Nan take Abba yasa Naufal ya ba Khattab hakuri, musabaka sukayi sai yace,
“I’m sorry man, I don’t know what my life will be Idan babu ita”
“Dont worry komai ya wuce bcs I don’t hold grudges.” Ita Anty Saudah saida ta rankwashe Miemie akai, ita kuma Miemie tayi dariya wai da gangan ta gudu wai saboda YaNaufal yace bazashi wajen amaryar sa da ita shine tace gwara kowa ya rasa.
Sai a lokacin ya tunada zancen wani Bad Luck, gefe yayi ya kira Mommy tareda bata hakuri akan rashin zuwan shi, yayi mata explaining Miemie ta ɓata ne but yanzu an ganta, in sha Allah within the week Zai duba ta. Jaje tayi masa tareda aika regards dinta wajen Miemie da Mamanta.
Wata sabuwa wai inji yan cha cha! Miemie ta kafe bazata shiga motar kowa ba saina Khattab, shi kuma Naufal yace bata isa ba, nan aka rinka Jani in jaka da ita saida Khattab ya durkusa gabanta yayi mata magana cikin raɗa kafin ta tashi ta shiga motar Naufal.
“Everything yayi daidai yanzu” ya faɗa saiya nufa hanyar motarsa. Naufal dabai iya boye abin mamaki ba saida yayi magana “Mai kace mata data hakura?”
Murmushi yayi tareda faɗin “It’s our secret”
Nikuma Dimples nace Iyye su Miemie yan mata.
Ita kuma Fadeela ana gaya mata bazai zoba tayi kwafa saita kwashe abincin kaf takai ma mai gadi tace masa yaci sauran ya bama almajirai.
“Daga yau na gama maka girki” ta faɗa yayin da take hayewa upstairs.
0 comments:
Post a Comment