Meena nata jan humaira da hira harta dan sake jikinta da ita, har dare meena na dakin har sukayi sallah sukaci abinci tare , bayan sunkare saiga anty amarya ta shigo, tace sunnuku kuta hira, tawoce toilet din dake cikin dakin , bayan wani lokaci tafito tace, humaira tashi kije kiyi wanka, tamike tacere kayan jikinta ta daura towel tashige toilet, anty amarya tabude akwatin humaira taciro wani yadi maikyau ta aje agefen gadon, tace da meena inta fito tasa wadan kayan, tajuya ta fita.
meena tana dan latsa wayarta saiga humaira tafito, bayan tagama shafan ne meena tadauki kayan ta bata tasaka, meena tace kai Anty kinga yadda kikai kyau kuwa. humaira tayi murmushi tace nagode. meena ce tasake cewa bari na tashi natafi karsu yaya su sameni. ta waigo ta kalli meena tace ina zaki kuma ba anan zamu kwana ba. a,a ba anan zan kwana ba amman gobe da sassafe zan shigo. tace wlh indai zaki tafi nima binki Zanyi. meena ce tamike tace to bari naje nadawo. to kiyi sauri karki dade.
meena nafita tayi dakin momy tagaya mata abinda humaira tace. momy tayi shiru tace gashi mijinta ba hankali gareshi ba bare yalallashe ta.suna cikin haka saiga faruk da abokan shi sun shigo nura ne agaba duk suka tsuguna furuk na gefe ya dukar da kai kasa nura ne yace momy munkawo miki ango ne kiyi mashi fada. tace nime zance mai aida gun hajiya kuka kaishi Allah dai yasa su zauna lfy kuma yaji tsoran Allah. daganan kuma sun kaishi hargun alhj shimdai fadan da yayi mishi kenan yaji tsoran Allah.
lokacin da suka shigo bacci yafara daukan humaira haniyar sune ya farkar da ita tadau gyalanta tarufa. sun shigo harciki suka zauna suta shakiyancin su , ita dai humaira ba fahimatan su takeyi ba ita bata masan waye mijin ba kuma badamu tasan shi ba. haka suka gama surutun su suka fita gaba dayan su. tana ganin sun fita tamike tayi daki momy, tatura kofar ta shiga bataga momy ba, sai meena dake bacci akan gado, danha tadau filo takwata akasa momy kuwa tana dakin alhj dan
yau itake da girki shikuwa faruk da yadawa daga raka abokan shi yarufe kofar falon su bekoma dakin humaira ba ya nufi dayan dakin yayi kwanci yarshi.
da subahi bayan alhj yatafi massala ci , momy ta nufi dakinta tatura kofar sai kawai taga yarinya kwace akasa tai salati ta sanar da uban gije ta matsa kusa da ita ta tashe ta, tashi kiyi sallah ta matsa ta tashi meena itama taji mamakin ganin humaira adakin. bayan alhaji yadawo daga sallah momy ta koma tagayawa alhj abinda ta gani.alhj yaji mamaki, yace turo min ita bayan tazo tagaida alhj yace matso nan ,yata taje kusa da shi ta zauna, yace faruk koroki yayine ? tace a,a nidaice nafito. yasan kinfito ? a,a ai lokacin sunfita . alhj ya girgiza kai yace ikon Allah kuruci dangin hauka
momy ce tace bari nakira shi . yace karki kirashi barni da shi kawai.
faruk ko tudda yadawo sallah yashige dakin shi yana sharar baccin shi saida gari ya waye yatashi yayi wanka yafito ko kallon dakin beyi ba yafice be nufi dakin momy ba falon alhj yanufa , yatar da alhj ya kishingida ya zauna yace abba ina kwana. fly lau yace dashi ya iyali .
faruk ya durkusar da kai yace lfy lau . ya baku fito tare ba jeka kirata . faruk yamike yafita, yayi sallama adakin yaji shiru yasa kai dakin bega Kowa ba, ya bude toilet bakowa , be tsora taba saida yaduba dakin momy beganta ba.
momy ce tace lfy kashigo bako sallama kana mana dube dube . yace yariryar nanne abba yana kiran ta. wace yarinya mu bamuga wata yariya ba anan. .yace momy kingane fa wadda nake nufi . bata da suna ne? ni sunan shige min yakeyi . to jeka bata shigoba .
faruk ya fara rudewa yarasa yazaiyi amma baiyarda da maganan momy ba, kasa koma yayi ya zauna afalo.
alhj yagaji da jiran faruk ya fito yasame shi afalo , kaikuma inajiran ka kazo ka zauna .
abba bangata bane adakin, kuma naje dakin momy tace wai fata shigo ba. alhj yace inataje to tun yaushe ne bata daki ? yayi shuru dakai fa nake magana, tun yashe rabonka da ita ? daddare ne ni ina daki basan sanda tafita ba.
ok irin rukun da zaka mata kenan gara da ka nunamin ban isa ba tunda da dai kai bakayi niya ba mu kuma bamu isaba to shikenan kayi duk abinda kaga dama kuma kaje duk inda take kanemo min ita. faruk yamike ya shiga dakin momy yace momy dan Allah kibar irin wannan, nasan tana wajenki karkisa Abba yayimin baki . nace maka ban gata ba, kawuce kabani waje. zabura yayi yanufi dayan dakin dake gefe , momy na fadin karka shiga min daki. ina ko sauraran ta beyi ba yana shiga ya ganta ita da meena zaune suna ta hira harda dariya yamika hannu ya kamata karo na farko da humaira ta fara sashi a idonta shima kuma haka dan haka da ya riketa itakuma ta rike meena tana kuka, ya daka mata tsawa ,saketa kukanta ne ya karu tana kira momy. yafara janta harya fito da ita yana rige da hannun ta momy ta tare hanyar tace saketa karfa kaji mata ciwo. be saurari taba saida yakaita gaban alhj ya saketa shikuma ya tsoguna yace abba dan Allah kayi hakuri ka yafemin kuma in Allah ya yarda haka bazata kara faruwa ba. yace to naji amman karka kara barita adaki ita daya daga yau .yace to nagode alhj yayi musu nasiha bayan ya kare faruk yamike yace mata tashi muje tamike suka fita, tana gaba yana baya kallonta yakeyi yariyar ba laifi yafada a zuciyar shi ga hannunta tunda yake betaba jin me taushin shiba suna shiga ban garen su yasake rike ta ke munafuka ce ko me aka miki kike kuka ya kama kuneta ya murde waye yace miki kifita, kinaso kihada ni da iyaye na ne ? tace a,a tana gargiza kai, dan kwalinta ya fadi , faruk naganin gashi yace yauwa yau zaki gane kuranki yasake kune ya kama gashin ya murde, saida tayi wujiga wujiga tafita haiyacin ta tukun ya saketa yace daga you karki kara fita daga dakin nan batare da kin gayamin ba
[6:34PM, 11/6/2016] +234 701 419 7556: 💞💞ZAKI GANE KURANKI💞💞
18 to 20
✍MMN YAZEED
Lokacin da furuk ya fahimci ta firgita da shi ,ya saketa ta tashige dakinta ta kwata tana ta kuka.
meena ce ta shigo dauke da abinci ta aje a falo, ta shiga dakin humaira tace ga abincin ku cen na aje a falo, tace anty humaira kuka kikeyi. humaira ta dago kai tace meena wlh yayan ku mugu ne.
meena takalli fuskar humaira data kunbura saboda kuka tace dukan ki yayi ? kinga yadda yake jamin gashi kamar zai kasheni ni wlh bazan iyaba zan kira abbana na fada mishi. meena ta rufe mata baki dan taji motsi a falo, tai kasa da murya tace mata karki gayawa abban ki, momy ya kamata ki gayawa wa xatamai fada zai bari, kiji.
kitashi kije kizoba mai abinci naji kamar ya fito.
nigaskiya bazanje ba meena tayi tayi da humaira ta fita tace bazata fita ba.
haka harta gaji da magana ta tashi ta tafi.
faruk ko yasaba dakin momy yake cin abinci gashi kuma yau anbiyu shi da shi. kuma masifar yunwa yakeji yarasa yarda zaiyi, hakadai ya daure , yace ke zo nan . afirge ce tafito ta manta ma kanta babu dankwali, tace gani. zuba min abinci . nanta tsoguna ta fara budewa. yace ahaka zaki ban abincin kanki ko dan kwali babu ke kazamiya ce wlh inhar naga gashi acikin abincin nan zaki gane kurenki.ta koma ta dauko dankwali tadaura sannan ta zuba mai . tamike takoma daki . yana cikin cin abincin aminu ya shigo shi da abdallah suka zauna suna ta hira da faruk abdalla ko dama yana shigowa ko gun faruk bejeba ya wuce dakin humaira , aminu ne ya gaji da jiran fitowan ta ya daga murya yace anty kifito mugaisa mana. tafito rike da hannun abdallah, hanun kujeran da aminu ke kai taje ta zauna ina wuni yaya yace lfy lau antymu. faruk ne ya dago ya kalleta yace waike baki da hakali ne zakizo kan mutun kizauna, da sauri ta sauka kasa ta zauna, aminu yayi ta jan ta da hira harta manta akwai faruk awajen sukaita hira suna dariya har abdallah ko kallon faruk basuyi ba shiko furuk hararar su yakeyi amma azuciyar shi cewa yake yarinyar nan dariya tana mata kyau . bayan aminu yayi musu sallama yatafi tamike tace zanje gun meena . yayi kamar bejita ba tagaji da magana takoma daki tayi tagumi .
hakadai zaman su yaci gaba da tafiya in dare yayi zaije dakin humaira ya kwana shi yana kujera ita tana gado inbanda tsangwama abinda yake shiga tsakanin su ,duk ta rame ta lalace dan haka aka maida ta makarantar da meena take zuwa drive ne yake kaisu ya kuma dauko so , humaira ta saki jikinta sosai ta saba da kowa agidan indai kaganta bata walwala to faruk na wajen ne har yan gidan suka fara ganewa da sungan shi saisu ce ga dodon humaira nan dan haka yafar dan sakar mata fuska agaban mutane anacikin haka tafiya ta kama faruk zuwa naija zaiyi wata uku bayan tafiyan shi humaira ta kara sakin jikinta duk inda meena tasa kafa sai tasa tata dakinta marufe shi tayi tadawo dakin momy ta tare, momy bata hana taba saima suje gidan inna su kwana buyu gidan yan uwa kuwa ba inda meena bata zaga da itaba humaira dai ta goge tayi kiba mulmul da ita faruk ya cika wata uku harda sati daya da tafiya suna waya da momy amman baitaba cewa aba humaira ba ko ya tambayi lfyr ta ba, meena da humaira suna zaune afalo meena tace tunda yau ba makaranta zo muje mutambayi momy sai muje gidan baba, to nima kafata kaikayi take. sun gayawa momy tace kuje amman karku dade, suka hau shiri yarda meena tayi shigar ta itama haka tayi baza ka taba cewa matar aure bace harma tafi meena haduwa, suka fito falo su hjy babba suna falon hjy tace sai ina kuma , gidan baba zamuje hjy tace amma dai humaira wannan gyalan yayi kadan . hjy beyi kadan ba nattare shine, to adawo lfy basu nemi drive ba suka wuce suka hau ta haya lokacin da suka shiga gidan nura da abokin shi suna zaune aharabar gidan suka karasa wajen suka gaida su suka wace ciki ,abokin nura ne yabi humaira da kallo ya nuna humaira yace nura wanan yariyar fa? kannai nane, eh nasan dayar ba meena bace kanwar faruk , dayar nake magana , kaifa kacika son matan to matar aure ce, nura wlh ba wasa nakeyi ba inasota wlh zan aure ta , nace maka matar aure ce matar wanin dan uwana ne , kai amman mijinta wawa ne wlh yana da mata haka yabar ta tana yawo ahaka, su kuwa su humaira tunda suka gaida mutan gidan suka dawa dakin bilkisu matar nura suta hirar ,suna cikin haka saiga nura ya shigo, yace ke shine kika biyewa meena kuna yawo, ke da meena fa kwai banbaci ke matar aure ce, yanzo da kika biwo ta wa kika tambaya ? wazan tambaya kuwa yaya banda momy, momy ce mijin ki, a,a mamata ce ni ai bani da miji, nura yayi dariya ba laifinki bane humaira to yanzu yaushe faruk zaidawo? ni bansani ba nama manta da wani faruk, lalai kinci ganye.
sai gurin mangariba suka baro gidan suna shiga Layin suka hango faruk da aminu zasu shiga masallaci faruk ne ya waigo ya kallesu yace da aminu dama su meena basa gida, eh suje gida baba baikara cewa komai suka shiga, itako mena tunda ta hango faruk ta rude tace mun shiga uku yaya yadawo, ni ina ruwa na da shi basai na koma dakin zaimin muguntan ba, suna shiga momy tace haka mukayi da ku ba nace muku karku dade ba, momy wlh wahalar mota ake , kun kyauta ke humaira je kishare dakin ki mijin ki ya dawo tayi kamar bata jiba ta shige daki, faruk ne ya dawo sallah dakin momy suka zauna har aminu dama abicin su na aje a gefe suka fara ci, ya waiga ga kalli su meena da suke cin abinci, yace ku baku ci abinci bane a inda kukaje gantalin, meena tace gidan baba fa muka je, ya daka mata tsawa ina magana kina mayar min, ya mike yayi fataili da abincin yaciro wayar redio ya fara tsula mata tana ihu aminu bece komai ba ,tayi waje da gudu tana kiran momy, faruk kuwa kan humaira ya koma ya fara tsola mata ta fasa kara da karfi yake dukan ta dan yafi jin haushin ta kuma ya tare hanyar bare ta gudu dan haka tayi bayan aminu ta rikeshi tam tana ihu shi ko faruk ganin inda ta rike aminu ranshi ya kara baci,
momy ce ta shigo aguje ,ta rike wayar tace sake .yaki saki jikin shi na rawa kamar mazari, dakai fa nake magana kasake min bulalar nace ko kasha kwaya ne. ya saki wayar yana huci, ita kuma humairar meta maka kake jifgarta kamar kasamo jaka, yawo taje kuma ai bai kamata adinga barin ta tana yawo a haka ba.
ubanta ne kai, kodan kana mijinta kuma sai kasa bulala ka zaneta ?
ai itama kanwa tace kamar yadda zan hukunta meena itama haka zan hukunta ta.
karya kakeyi ba kanwar ka bace matar ka ce karka sake fakewa da meena ka daketa akwai banbanci meena ta saba da bakin halinka ka tsaya kanta.
humaira ta sake alone tayi bayan momy tai kasa da murya tace kuma Allah ya isa.
faruk yayo kan momy gadan gadan kamar mahaukacin zaki yana fadi , ni kikewa Allah ya isa ni abokin wasanki ne, dan kinga ana daure miki gindi kina iskanci da kikaga dama wlh zanga wadda zai hanani dukanki yau.
momy na kokarin tare shi amma ina idon shi yariga ya rufe
[6:34PM, 11/6/2016] +234 701 419 7556: 💞💞ZAKI GANE KURENKI 💞💞
21 to 23
✍MMN YAZEED
Da momy taga ya nufi gurisu gadan gadan yasa ta daga hannu ta wanka mishi mari.ya tsaya cak yarike gurin.
momy harda duka kuma. eh kadan ma ka gani watarana ma tabarya zansa maka, bakai kana ganin kafi karfin kowa ba to muzuba dani dakai karyan rashin kunya kake.
yadade tsaye ya dukar da kai yayi shiru sannan ya juya ya fita. aminu ne ya durkusa yana kwashe abincin da faruk ya zubar .momy tace aminu barshi jeka wajan iyalinka zan kwashe bayan tagama gyara wurin tashiga toilet ta hadawa humaira ruwan waka ta fito tace humaira jeki ki gasa jikinki, zaki iya kuwa dan naga jikin ya tashi da yawa? zan iya, bayan ta fito tadau wata riga mara nauyi ta saka nan da nan zazzabi ya rufeta duk jikinta shedan bulala ne rudu rudu, momy ta dauko magani ta bata tasha ta kwanta, bayan alhj ya dawo ne momy ta shiga ta same shi da hjy babba da anty amarya tafara gaya musu abinda ya faru, alhj yace wani irin duka, wlh alhj inda kasan yana dukan yar shi, alhj ya daga waya ya kira faruk, momy ce ta mike zata fita, alhj yace ina zaki kuma , zanje na kwanta ne danni ko ganin shi bana sonyi, hjy tace matsala ta dake baki iya fushi ba nan sukai ta mata nasiha, faruk ne ya shigo tare da sallama, momy na ganin shigowan shi ta fita , alhj ne yace me ya faro ne naji ance kadaki humaira? yayi shuro kanshi akasa, ina sauraron ka, abba ita da meena ne, yawo suka je sai dare suka dawo , alhj ya rufeshi da fada ta inda yake shiga batan yake fita ba, faruk yau yaga bacin rai agurin alhj wadda betaba gani ba, nan ya tsuguna yayi ta bashi hakuri, saida su hjy sukasa baki tukuna alhj yabar fadan, tashi ka fita kuma kaje kaba mahaifiyar ka hakuri, lokacin da faruk yaje ya tarar ta riga ta rufe kofa dan haka ya wuce ya kwanta amman bacci ya gagare shi ya shiga dogon tunani , yaya akayi na bari yariyar nan ta rainani yariyar da batafi sa,ar meena bace take min Allah ya isa, kuma an hanani na hukunta ta itakuma momy harda mari na agaban ta hmm tunani da yayi tayi kenan besan sanda bacci ya dauke shi ba, washegari faruk ko wanka beyi ba, yatafi dakin momy domin ya bata hakuri , yasa meta itada su meena suna hira momy na ganin shi ta daure fuska, humaira kuwa mikewa tayi ta shige ciki, ina kwana momy, tayi banza da shi yaga kamar bata jiba yasake gaida ta nanma yaji shiru , itama mina mikewa tayi tabi humaira, faruk yaji dadin fitan meena dan haka yazo gaban momy ya tsuguna, momy dan Allah kiyi hakuri naga kindau abin da zafi bazan kara ba, har yanzo bata tanka ba, yayi ta surutun shi tayi banza da shi, haka ya gaji ya mike ya koma daki, kanshi yaji yana juyawa, dakar ya daga waya ya kira nura, nura na dagawa yace mishi akwai matsala.Allah yaraba mu da ita, menene ya faru daga dawowan ka jiya? nura komai ma ya faru , kadai zo dan Allah. a,a nikam ba inda zani yau ranar hutu ce gida zan zauna in huta da iyali na. wai inace ma matsala kana cewa zaka huta dan Allah kayi sauri kazo, nura ya fahimci tashin hankali atare da muryar faruk dan haka cikin hanzari ya taho, saida yafara shiga ya gaida muta nan gidan sannan ya woce gurin faruk ya same shi kwance a falo akan kujera ya rike kai, baka da lfy ne? a,a lfy ta lau ya kwashe duk abinda ya faru ya gayawa nura, gaskiya tsakani da Allah faruk abinda kakeyi be taceba yariyar nan tunda tazo kake nuna mata kiyayya ni banga laifinta ba tun tanaji tsoronka ga shi har ta iya mayar maka da magana ina amfanin irin wannan.
ai wlh bawai nabarta bane zan kama ta saita gane kurenta akanta fa momy ta daga hannu ta mareni tunda nake da wayo na momy bata taba sa hannuta ajikina da sunan duka ba sai akan wannan wawuyar yariyar, kuma ita momy da take cewa ba kanwa ta bace wai matatace to da izinin wa ta fita, kaga ma shigar da tayi ne .
to lefin waye lefin ka ne , ka nuna mata auren nada daraja agurin ka, kai da kayi biyayya da yanzu in robo ne ma ansamu.
wanne irin rabo kuma wannan yar tatsiyar yariyar ya zatai da ni.
ikon Allah kai dai mutun bazai taba gane kanka ba, bakai kace karama kake so ba.
ai da nace karama bance sa,ar meena ba.
to inaganin gaskiyar momy ce da tace baka da lfy, ga dukkan alama baka da sha,awa.
wlh inada ita nina ma fika lfy kawai dai ina danne wane.
a,a ni baka fini ba wlh da kafini da baka kawo yanzun baka da mata ba.
mubar wannan maganar yanzon kaje kaba momy hakuri, bana son ganinta ahaka. nura yamike yace amman gaskiya kana sani a uku.
nura ne yayi sallama dakin momy ya shiga. nura dama kana nan ai nadauka katafi. a,a bantafi ba inagun faruk, momy ya gayamin abida ya faro kuma ya amsa laifinsa dan Allah ki yafe masa.
nura kenan , kadai amsa masa laifin.
a,a momy shi da kansa yace inzo na baki hakuri.
to shike nan ya wuce amman da na dauka dambe zaiyi dani. a haba dai wane shi aibe isaba yayi kadan.
ya sake cewa ina humaira. momy da kanta ta daga murya takira humaira.
yaya nura dama baka tafi ba. eh ai ina dakinki inata jira kikawo mana abici naji shiru. caf na shigo ya bigeni.
saikace wani mahauka ci bazai bige ki ba, magana tariga ta woce karki kara tada ta, kuma ko wani abo ya faru atsakanin Ku karki kara cemai Allah ya isa. to shima kace mishi ya daina shiga harka ta. bazai daina shiga harkan taki ba, dama haka kike yanzu ne ma zai shiga harkar ki, daga yau karki kara zuwa ko ina , saikin tambaye shi. ta kwashe da dariya, au dariya na baki wlh ba wasa nake ba, momy kizama sheda wlh faruk be yadda ta fita bada izzinin shi ba. momy tace ku kuka sani niba ruwa na. bayan nura ya koma dakin faruk ya kara bashi sha warwari sannan ya nuna mashi mahim mancin kula da matar sa in kana mata haka nan gaba zaka iya kamuwa da sonta ita kuma ta bijire maka. nine zan kamo da sonta Allah ya kiyaye wlh. to shikenan tunda baka sonta, dama abinda yasa nace ka kula da ita wani abokina ya ganta jiya ya nuna yana sonta shiyasa nace.
kabari fa bana son irin wannan wasan ya fada a fusace. wlh faruk ba wasa na keyi ba inzaka kula da ita ka kula ni babu ruwana inhar baka bariba nan gaba karka kirani. bar wanan maganar wani dan iskan ne yace yana sonta, idon nan jawur
[6:34PM, 11/6/2016] +234 701 419 7556: 💞💞ZAKI GANE KURENKI💞💞
24 to 27
✍MMN YAZEED
nura ya kwashe da dariya, kace baka sonta kuma gashi naga duk ka wani rude. ba rudewa nayiba amma yaya za ayi yaga martar aure yace yana so .
to ai baka kula da ita ba in bakason ace anason ta to ka kula da ita, kana son yarinya kana wani basarwa. wai wa yace maka sonta nake. nura yayi murmushi ga kishin ta nan a idon ka. niba sonta nake ba, amma ai akwai aure na akanta . zama ka kadawo hanya ne, ni zanta tafi.
da daddare humaira tashigo dakin tana zunbura baki ta wuce faruk yana kwance rike da kai dan har yanzun kanshi bai daina ciwo ba , ta shige dakinta ,faruk nason ya shiga daki shi ya kwanta kuma yana tsoron karya shiga itakuma ta fita, tajamai wata maganar dan haka yatashi ya shiga ciki
washegari da wuri ta fara shirin makaranta , tana dakinta ta na kokarin sa rigar makaranta, taji anturo kofar ,ta sake kara da karfi. juyawa yayi yana fadin meye haka. to ya zaka shigo ma mutun daki ba sallama. yayi tsaki ya fara tafiya in kun gama shiryawa kimin magana na sauke ku, bejira yaji me zata ceba ya wuce itako humaira cewa take azuciyar ta wannan yana so yafara takura mana.bayan tagama shiryawa ta fito tasame shi zaune a falow ya juwo ya kalleta ya dauke kai, yasake juwowa ya kalle ta sosai, dama ahaka kike zuwa makarantar. eh
dawan nan dan siket din, karya kikeyi.tace nizan wuce zamu makara. kije ki canza ki sako wando kisame adakin momy. toni wani wando zansa haka fa kayan yake. to wlh saidai in bazaki makaratar ba yajuwa ya fita. bin ubayan shi tayi tana zunbura baki, momy ce tagan su sun shigo kowa rai abace meena ya hango itama da irin shigar humaira. ke kmeena kayan makarantar ku ba riga da wando bane.tace ancanza ne fa yaya. ya tsaya yayi shiru momy dai ido tabishi da shi can ya dago yace ke meena taso muje na sauke ki. momy tace humaira fa. ita zauna zan canza mata. me zaka canza mata, kana nufin zakiyi mata wasa da karatu , tana gaban iyayeta tayin karatun ta aka katseta kuma yanzun ta fara asake katseta wlh baka isaba. momy aiba lokaci zan jaba. kaidai wlh fitinanne ne bakaso kaga anzauna lfy, ni idai ba barin gidan kayi ba hankalina bazai kwanta ba. faruk rai abace yace jeki dauko hijab ki daura akai. yaceni bani da hijab. ko kallota beyi ba ya juya ya fita. momy tace ke humaira jeki dauko hijab din kizo kutafi. momy wlh bazan saba haka kawai ba me sawa saini. kidaina sauri rantsuwa humaira mijinki ne yafi kowa karfi akanki tashi maza. ai bani da shi. momy tayi murmushi meena dauko mata hijab dinki. meena ta dauko ta mika mata, takarba ta bude ta fashe da kuka momy yayi nmin yawa fa. kash kema taurin kan zaki min meena tariga humaira futowa dan ita tsoro yaya faruk takeji baya ta shiga tazauna humaira ta fito gaban motar tashiga dan shi ta gani abude bata daina kuka ba har sukai nisa, yajowo ke karki damemu tai banza ta shi tacigaba da kukanta harsuka kawo bata daina kuka ba, kukan humaira yafara dagawa faruk hankali ji yake kamar ya rungume ta ya lallasheta, dan haka yace meena jeki abinki, da saurinta ta fita ta shige makaranta. ya juya ya kalli humaira yana son yakara taba hannuta amman yana gudun karta raina shi gaskiya inbai taba ba hakalin shi ba zai kwanta ba dan haka ya wayance ya mika hannun shi yarike mata hannu , yana dan matsawa. ta dago da kanta tana kicikicin kwacewa tana fadin ka sake ni niba yar iska bace.tsaki yayi ya kara matsa hannun .tasake kara akwai zafi fa . haka ya saketa bawai dan ya gaji da taba hannu ba.
faruk fa ya jawowa kanshi dan tunda ya taba hannun humai hakali shi yaki kwanciya da taimakon Allah ya isa office ko da yaje be iyayin komai sai tunani yake shidai yasan basanta yakeyi ba amman ayau yaji yana son yadan taba jikinta kuma baya son ta raina shi in ma ya daure yasan yariyar ba yadda zatayi ba dan haka yafara tunani yadda zaiyi yabar gidan da ita dan haka yana tashi office ya woce gidan alhj ahmad, nura ya fara kira yace mai zomuje karakani, ina zan raka ka? gurin baba nura bai kawo komai aran shiba dan haka ya bishi suka shiga bayan sun zauna alhj yace babana kwana biyu shiru
wlh baba abu buwa ne sukayi min yawa .
inna ma tace fushi kake da ita, rabon da ta ganka ta manta, ina sane da ita ai zanje ne baba. bayan sudayi hira faruk ya fara magana baba dama inason na tare a gida nane. to ka shirya tarewa kenan to amma maizai sa bazaka bari tagama karatun ta ba.
baba ai zatayi acan .
yace to kabari zaga baban naka tuda shi yake zaune da ku .nura ne ya sako baki baba karku yadda ya tafi da ita wlh be natsuba . alhj yayi dariya yace da gaske ne wai baka natsuba . yace karya yakeyi baba. yaushi zaka tafi? jibi yafada atakai ce. kaje zakira shi zamuyi magana.
washegari da safe yaji kiran alhj , saida gaban shi ya fadi yana me ardu,a azuciyar shi Allah yasa abba ya yarda bayan ya isa dakin abba yace naji ance wai zaka dauki matarka ka kai abuja to kama cire wannan tunanin azuciyar ka , inka manta ni ban mance ba yau kwana nawa da ka zaneta acikin gidan nan adakin mahaifiyar ka, shine dan bamu da hakali zamu baka ita katafi da ita wane waje inkana son ka tafi da ita ka gyara halinka. haka ya koma jiki ba kwari . lokacin da ya shi ya samo humaira ta waya , tanata murna tana fadin ai zanzo suna. tana kashewa tamike da gudo tayi dakin momy , bata dade ba ta dawo, yaya faruk momy na kiranka, bece komi ba, ya tashi ya tafi, yana shiga yace gani.
ni ba nemaka nakeba waye yace ina kiranka? humaira baitaba kiran sunan humaira ba sai yau. tace au ita da nace ta tambaye ka shine ta turo ka, wai matar yayansu ce ta hai hu takeson taje suna, Kuma kaga ya kamata taje tunda tazo bata taba zuwa gidan bab. momy dan Allah kidaina cewa ya katama ba ruwan ku karma kusa baki.
ai baza abaku shawara ba? bahaka bane yanzun in taji kina fadan haka saitaga kamar dole ne.
da daddare banya suyi shirin kwanciya tana gado shiya na kujera yace yaushe ne sunan matar yayan ki ? da sauri ta sauko tace yau ta haihu , yaya zanje ne . ke da kike min rashin kunya baki jin magana ta. wlh yaya na bari bazan kara ba. duk abinda nace kiyi zakiyi ?eh tace dashi da sauri batare da tayi tunanin komai ba. to dama yau agajiye na dawo zo ki dan min tausa
[6:35PM, 11/6/2016] +234 701 419 7556: 💞💞ZAKI GANE KURENKI💞💞
28 to 31
MMN YAZEED
Mikewa tayi ta ja da baya , yaya dan Allah kiyi hakuri wlh ban iyaba, ta nufi kofa. ke ina zaki kuma ,zo kiji. ta kara matsawa, yaya wlh ban iya ba .
to naji baki iyaba zoki yi baccin ki. taki zuwa tamakale wa kofar, yata shi ya matsa kusa da ita , ba za kimin ba ko, ashe baki shirya zuwa gida ba. ni ashirye nake .to tunda bazaki yi min ba zoki kwata amma karki kara cewa zaki gida ,dan wlh bazaki ba . ni bazan kwata ba sai ka fita adakin . saina fita , saboda me zan fita? tsoron ka nakeji. wlh bazan fita ba ,bake kika sa akace dole sai na rinka kwanan ba, kuma yanzun dan munafurci zakice wai tsorona kikeji ,mezan miki , ko kina tunanin wani abu nake nema awajanki me kike da shi, yamike yafara takawo kusa da ita. tana ganin ya nufuta ta ruga da gudu tayi waje . dawowa yayi ya zauna yafara ganin laifin shi meyasa ma har ya mata magana, wannan yariyar da bata da sirri , yanzo ma kila harta gayawa momy.
momy na kwance taji anshigo aguje tana daga kai taga humaira na haki. ke lfy kuwa ? bakomi .
momy tamike tazo ta riketa ta , meya faru ? bakomi momy nazone na kwanta anan. a,a bazai yiwoba yazaki baro mijinki adaki kizonan ki kwata, ai ba haka akeyiba , yanzun kintaba ganin samira ta kwana adakin nan ? to momy zan koma amman kice ma yaya faruk ya koma dakin shi . momy tayi shiro can ta dago tace humaira kitashi kikoma dakin ki niba ni da damar da zance mai karya kwana adaki matarsa, ke meyasa bakice mai yakoma nasa ba. nacemai fa , yaki ta fiya ne. momy tayi murmushi ta kalli humaira tace bake kikace kinajin tsoron kwana ke daya ba ? ai yanzo na daina ji. suna cikin haka saiga faruk ya shigo, ya tsaya bece komi ba, momy tace tashi ku tafi . momy nifa inbai tafi dakin shiba saidai na kwana anan.
wai humara meyasa bakijin magana ne nace miki kitashi ku tafi, ba gobe zaitafi ba in ya tafi saiki dawo nan kitare . faruk ne yace momy rabu da ita , ki tashi kitafi dakin naki, kuma ko natafi ki zauna can ban yarda kidawo nan ba, yajuya ya tafi.
washegari da wuri faruk ya bar garin. humaira taji dadin tafiyan faruk taci gaba da har kokinta yadda ta saba , sadai yanzo momy ta takura mata da yawa bata barinta fita sai tace ki tambaye mijin ki , ni babu ruwa na ita kuma ko number sa bata dashi shima bayi da nata dan betaba kiranta ba, haka ta hakura da fitan dan bata da yadda zatayi da momy. shi kuwa faruk kulum da tunani humaira yake bacci sai yaji kamar ya kirata ko rashin kuyar ne tayi mishi sai kuma ya tuna bayi da number ta kuma abinda kunya yakira wani agidan yace abashi number matar sa. humaira ko tana ta shirye shiyen tafiya gida dan yau saura kwana biyu suna amma momy batai mata maganar tafiya ba dan haka taje ta same momy tace momy na hada kayana gobe zantafi ko sai ran suna.
momy ta ce yaushe kukayi da mijinki ?
bemin maganar ba har ya tafi. to ke me yasa bakiyi maiba?ni yanzun banda damar da zance ki tafi , yanzo sadai ki kirashi kiji me zaice. momy dan Allah ke ki kirashi. nikam bazan kira shiba. hakalin humaira ya tashi bata da yadda zatayi dole ta kira shi, dan haka ta nufi bangare samira tasame ta ita da aminu, yauwa yaya aminu dan Allah ka kira yaya faruk kace mai gobe zantafi suna. yace caf ai kunfi kusa, ke ya kamata ki kirashi.
nifa bani da number sa ne ,ya karbi wayan ya sa mata. samira ce tace ikon Allah mutun da mijin shi amman baki da number sa .aminu ya mike yana fadin ai wannan soyayyar ta manya ce, ya juya ya fita samira ce ta juwo ta kalli humaira tace dama inason naganki . tace to ai gani. wai faruk be taba kiran kiba ne ? anty me yasa kikamin wannan tanbayan .
tace naga tunda kika shigo gidan keki shishige ma momy duk kinbi kin likewa dangin miji har su meena duk an mallake mikisu amman ankasa mallake miki mijin yana can yana sheke ayarsa da yan matan sa, to dan Allah bari na baki shawara ki dan rage shishigi , tana maganar tana ya tsina baki . humaira ta gama sauraron samira, ta rasa me zata cewa samira dan magan ganu sun bata haushi mikewa kaiwai tayi ta fita tana kuka , dakinta ta nufa ta fada gado ta fashe da kuka saida tayi me isarta sannan tayi shiro sannan ta dauki alkawari duk ranar da samira ta kara yi mata irin wannan saita ji mata ciwo, bayan tayi sallah mangariba taji zuciyar ta tayi sanyi kuma har yanzo tunanin tafiyan ta gobe yanan azuciyar ta dan haka ta dauki waya ta dan, na number faruk, can aka daga. ina wuni tace da shi.
lfy, ya dauki muryarta amma sai yace waye ? humaira ce . yaya akayi ? momy ce tace na gayama gobe zantafi. kina da hakali kuwa ? ni lfy ta lau ,wata na 8 fa banjeba. to ni dai ban yarda ba, ko kofar gida bance kije kuma wlh inkika fita zaki hadu da bacin ran da biki taba ganin irinshi ba. kuka ta fara, faruk najin ta fara kuka ya kashe wayar . momy taji shiro humaira bata zoba tasan ba lfy ba dan haka ta nufi dakin humaira da kanta kuma wanne karo na farko data fara shiga ban garen su tana shiga ta sameta kwance fuska duk ta kunbura, subuhanallah humaira me yayi zafi haka . nan tara kuka ta fada mata yadda sukayi da faruk . momy ta lallashi ta takyar tayi shiru.
har washegari humaira bata hakura ba ta dinga kiran faruk yaki dauka har yamma kira takeyi amman be dauka sai can dare ya turo mata message da sauri ta bude. *ke kika jawa kanki da kibi umarni na da yanzu kina can*.
haka taci gaba da kukanta can tayi tunani bari ta kira nura ta dauko wayar ta ta danna number sa .ya daga da fara,ar sa. humaira ya akayi ne ? nanta fara kuka. ya sake cewa ya salam humaira kiyi shiru kiyimin bayani , faruk ne ko ? tace eh.
to kidaina kuka share hawayan ki ki gayamin me ya faru. nan ta fara gaya mishi abinda ya faru. to shikenan zan kira shi, amman meyasa inya ce kimai abu bakiyi ? yaya nifa ban iyaba ne , cewa fa yayi wai na mai tausa . nura ya toshi bakinsa yace to kiyi shiro karki kara gaya wa kowa . baya ya kashe waya
yayi dariya yace wlh faruk dan duniya ne. yasake daukan wayar ya fara kira faruk bugu daya ya dauka yana fadin sai yau ka tuna dani? shiko nura cewa yake yau asirin ka ya taunu, wato dan kace wa yarinya tama tausa taki shine ka hanata zuwa taga iyayenta. faruk yayi dariya, badai ta gayawa momy ba . oho ni ban saniba, yanzu dai koma mai kake ji dole ka ajeshi sai ta koya , muna fiki kawai. faruk ya kwashi da dariya wai kiran ka tayi ne ? ina ruwanka, yanzun dai zata tafi gobe. ai wlh ba zataba in kaga taje garin nan to haihuwa tayi
[6:35PM, 11/6/2016] +234 701 419 7556: 💞💞ZAKI GANE KURENKI💞💞
32 to 35
✍MMN YAZEED
Nura ya yace amma dai wlh baka da kunya, da wanne dan iskan zata haihu? mata ta ce fa.
ba wani matar ka kai dai kawai kace ka kamu da sonta. dama nasan haka zaka ce amman ni ba wai sonta nake ba, kasan me ne ne ? saika fada. daki daya fa muke kwana kuma kasan nifa ba dutse bane. au she ba dutse bane ni na dauka dutse ne , yan zundai ina neman alfarma kabarta taje. nura nariga narantse , ka rabuda ita wani lokaci zan kaita da kaina . nura yace to shikenan ka kirata ka bata hakuri, wlh ta ban tausayi tana ta kuka . to zankira. bayan yajiye wayar yafara tunanin yanzu yariyar nan haka zamuyi da ita ba sirri, yanzun har tagawa nura, Allah yasa bata gayawa momy ba" tsiyar karamar yarinya kenan babu sirri .
itako humaira har ranar suna tana jiran tsammani saida taga 3:00 sannan ta cire rai tare da alwashi wlh sai ya gane kuranshi haka taci gaba da harkokinta ba walwala atattare da ita ga bacinran abida samira ta mata gakuma bakin cikin faruk, dan haka ta rage sakin jiki agidan duk da dai momy na nuna kolawa kwarai agare ta ,haka sauran yan uwa sai yan kadan wa edda ba a rasa ba, faruk be kira humaira ba kamar yadda sukayi da nura sai ana gobe zai dawo taji ankira ta a waya , ta isa ta dauki wayar, MUGU ta gani kamar yadda ta daura akan number sa. saida tayi Kamar karta dauka , tadai daure ta daga, tana dagawa ko sallama bataiba tace, to me nene ? au ko gaisuwa ma bazan samu ba. akan me zan gaishe ka. matsayi na mijin ki. Allah ya kiyaye me zanci da tsoho" ke ni ne tsoho, barina na dawo zaki gane kuranki "kadawo din kaima zaka gane kuranka wlh " ni din ko ? eh kai. faruk da sauri ya kashe waya yace rashin kunyan yariyar nan babba ne, saina bita ahankali.
washe gari faruk ya kamo hanya bawanda yasan da zuwan shi agidan dan be gayawa kowa ba, humaira kuwa yau tasaki jikinta tayi kwalliya kamar me shinrin zuwa gidan biki tunda ta gayawa faruk magana taji zuciyar ta ta mata sanyi . tana zaune Itada meena , momy na gefe ta kishin gida , meena tace anty humaira wai fly kuwa naga kwana biyu baku cika magana da anty samira ba. bakomai meena kawai da yan maganan basanan ne" meena bata sake cewa komai Amman bata yadda da maganar ba , sai ta dauko wani zance , suna cikin haka sai suka ji muryar faruk yana gaida hjy babba"humaira zabura tayi ,tabi bayan momy tace meena kamar naji muryar faruk. tace ba kama bace shine. faruk yayi sallama ya shigo ya yauna , sallaman shi ya tada momy taga humaira rakube agefeta. bayan ya gaisar da mahaifiyar shi meena ta gaida shi tamike ta fita, humaira kuwa ko mutsi ta kasa yi , shikowa faruk ya kosa humaira tayi magana yaji zazzakar muryarta amman shiro harya gaji da jira yace , ke ba gaisuwa ? tayi banza da shi, momy tace humaira dakefa yake . ta waigo tace ina wuni . yace saida na roka, yamike ya fita .
momy tace je ki kai mai abinci tamike tana zunbura baki. lokacin da humaira ta isa bangaren su ta same shi a falo yayi wanka ya canza kaya taje ta aje abincin ta fara zubawa yayi maza yarike hannuta yace to gani na dawo , koda yake kince zan gane kure na ko? tayi shiru batace komi ba. me nayi miki kika daina gaishe ni? nan ma bata kulashi ba, nan yafara tunani wannan yariyar innayi wasa ko muyar da nake dan samo saiya zama aiki , shi ko rashin kuyar ne ma tayi mi shi yana so dan haka ya mike ya zagayo kusa da ita ya zauna yana rike da hannun ta. saida taga yayi kusa da ita sosai sannan tace ni wlh ka sake ni. yakara rike hannun yace kwantar da hankalin ki, niba wani abu zan miki ba, magana kawai zamuyi kinji, kisan me Nene ? ko kalloshi batayi ba , humara kiyi hakuri nasan nayi miki laifi ba nayi bane dan na bata miki rai bane, ni bana son kitafi ke daya ,ki bari da zarar na samo lokaci zan kaiki da kaina amma kema kidaina min abida kike yi min ki dinga bin umarni na nifa mijin kine, ko bikisa hukunci matar da take yiwa mijinta haka ba" yana maganar yana kara shigewa jikinta. tace nidai kasake ni. kuma wlh idai sai nabi umarnin ka zaka kaini gidan to na hakura da zuwa. haba humaira me yayi zafi haka. tafara ciki cikin kwace hannun ta, da taga bazata iyaba tasa bakinta ta gantsara masa cizo da karfi amma ko gezau beyiba saida wurin ya fashe harya fara jini sannan ya saketa . ta ,kwasa da gudu ta nufi hanyar waje , shima tashi yayi aguje ya tare ta, ta fashe da kuka tana ganin kashin ta ya bushe.
zo ki zauna ba abinda zan miki kinji, yanzo fa saikice dakin momy zaki ko, dan Allah humaira ki daina haka yanzun ba dama muyi abu adaki sai kinje kin gayawa momy, zoki zauna bazan miki komi ba. biyoshi tayi suka zauna sannan ya saketa , yace bari na wanke hanuna na dawo, ta kalli hannuta taga jinin faruk sosai ya fita har a kasa , dan haka tamike tace so yake ya dawo ya zaneni babu me cetona.
futowa yayi be ganta ba , beji dadiba dan beso momy tasani ba dan haka ya kasa zuwa dakin, yaneme guri ya zauna. zuwa can anjuma saiga anty amarya ta shigo da sallama, tasamu faruk yana shafa man zafi ahannu shi ga digon jini akasa, tace faruk wai me yafaru ne, ga humaira can taki magana sai kuka take. ya daure fuska kukan munafurci take anty , cizo nafa tayi . cizo kuma, kai humaira itama bata jin magana, ta juya ta fita, saiga momy rike da humaira tashigo tace karka sake kace zaka tabata yanzun haka mugunta kaje yi mata . momy magana fa kawai nake mata ta kamo hannuna ta ciza. to naji abar maganar ke humaira zoki bashi hakuri. tace Allah ya baka hakuri bece komiba ta shige dakin.
washe gari da safe nura yayima faruk waya bilkisu matar shi bata da lfy. dan haka yaje dakin momy yagaya mata sannan yace tama humara magana su tafi tare. bayan momy tama humaira waya bata bata lokaci ba, ta fito suka dau hanya, suna cikin tafiya ya waigo yace, baki cemin ya jiki ba kuma jiya da zazzabi na kwana. banza tayi da shi, yayita magana ya gaji yayi shiru ,yana kallon hanya, can taga ya tsaya ya dawo da baya , ya tsaya agaban wata kyakyawan yariya , budurwa ce amma zatai kanwa da humaira tana ta karai raya, yace sajjida ina zuwa haka dasafe ? wlh yaya makaranta zani gashi na dade tsaye anan. yace shigo na kaiki mana. ya juya ya kalli humaira yace humaira sauka ki koma baya
Enter your comment...
ReplyDeleteTO MUN FARA KARANTA "ZAKI GANE KURAN KI" MUNA BIN FARUQ MUGA YADDA ABU-BUWA ZASU KASANCE.