Bismillahi Rahmani Raheem!
"Alhaji dan darajar Allah kayi hak'uri ni bansan laifin da nai maka ba, mai ya kawo maganari saki"???
Cewar yar matashiyar matan dake tsaye a gaban wannan dattijon, wadda ta kasance ita ba fara ba ita kuma ba baq'a ba, shekarunta bazasu wuce 30 ba.
"Hajiya na fad'amaki cewan na' sakeki saki daya saboda hka idan Allah y baki miji kiyi aure"
Yana gama fad'in yaja rigarsa fuuu y wuce.
Kai kawea ta girgizah saboda tasan tabbas mutum baya tab'a wuce kaddararsa, hakan yasa ta koma d'akinta ta tattara kayanta a cikin jaka ta had'a ta dau mayafinta ta fito, zuciyanta cike da k'una da bakin ciki, tana kawowa tsakiyan gidan d'anta na dawowa dga makaranta, jakar makarantar shi ya yarda akasa, da gudu ya isa gareta.
"Mame tafiya zamuyi ne naganki da jaka a hannu"?
Rage tsayenta tai dea2 nashi tasa hannunta ta dafa kanshi
"Aliyu ba tafiya zamuyi ba, nidea zan tafie, kuma a nan zan barka, ina mai maka nasiha da kazama namiji, kazama mai hakuri da juirya akan duk abunda zai biyo bayanka"
"Mame dan Allah kada ki tafie ki barni, wallahi zan rik'a jin magana, bazan k'ara fasa kwano ko d'aya a gidan nan ba, zan rik'a share ko ina, mame dan Allah".
Rungumeshi tai tana zubar da hawayen rabuwa da d'anta, wanda yake shine sanyin idaniyanta.
"Aliyu ni wnnn duk baya damuna, ko wanne yaro haka yake, hasali ma ni kullum addu'ah nake maka akan Allah ya shiryaka, nasan kuwa Allah zai amshe addu'ahta"
Gyaran muryan da tajine ya katsie mata zancen da takeyi
"Kai zubairu amso min yaron chan" ya fad'a murya a fusace.
Zubairu dake kusa dasu, yasa hannu yana raba uwa da d'anta.
Zubairu ya amsheshi, hajiya ta juya ta nupie kopan dake fita gidan.
"Mame dan Allah ki dawo kada ki tafie, mame!!!".
Haka ta fice ta barshi a gidan zuciyoyinsu cike da tarin bakin ciki mara misaltuwa...
[7/29, 11:50 AM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((2))
©Kausar M Hassan
Ganin baida mafita sea ta Allah, yasa ya cigaba da huci kaman wani sabo zakin daya fito neman abunci, hannun zubairu ya garzawa cizo, wnda hakn yay sanadiyar sakinshi da zubairu da yay, da gudu y haura gidan saman, ya bud'e wani d'aki wnda da alama wannan shine d'akinshi, banka kopar yay ya maida y kulle da padlock ya hau kan d'an karamin gadonshi ya kwanta ya cigaba da kuka.
Alhj baiji dad'in kasantuwar hakan ba, shi kanshi baisan maisa yay hkn ba.
Cike da tak'aicin abunda ya aikata y kama hanyar shiga d'akinshi. Wata mata na hango fara tas da itah, iya inda akeso mace takai to ta kai, sanye cikin dogowan riga bak'a tasa dan k'aramin hijab, da baqaqen takalmi, chewing gum ne a bakinta tana tauna Karas_karas.
Ganin Alhj da tai yasa taja ta tsaya chack kaman gunkin da aka ajiye.
"Alhj ina hajiya salma"?
Shiru yay jim kad'an tukkuna ya nisa
"Na saketa hajjah rabi, kuma nace idan ta samu miji to tayi aure.
Kirji ta daka cike da nuna rashin jin dad'i fal a fuskanta
"Haba Alhj dan Allah, kayi hkuri ka dawo da ita mana mai yay zafi haka shi ba wuta ba"?
A fusace ya bata amsa
"Kinga na gama magana, kuma bana so a k'ara dawomin da ita farko"
Zatayi wata magana ya ra6ata ya wuce, kai ta girgizah tukunna ta qaraso tsakar gidan, ganin jakar Aliyu da tai yasa ta tabbatar da cewan ya dawo dga makaranta.
"Zubairu!!!" Hajjah ta hau kiran sunanshi
Jiki na rawa ya amsa kiran da take masa
"Na'am hajiya gani" ya karaso kusa da ita cikin ladabi.
"Aliyu y dawo dga makaranta ne"?
"Eh hajjjah ya dawo"
"Yana inane"?
"Yana d'akinshi hajiya"
Alama tai masa da hannu wadda ke nuna cewan ya wuce, da sauri y kama hanya y bar falon.
Hajjah rai a 6ace ta hau gidan saman, dai_dai d'akin aliyu taja ta tsaya, a hnkli ta fara kwan_kwasa kopar.
Aliyu daya riga ya hasala ya fara magana
"Wanene"?
"Aliyu nice mamanka ka bud'e kopan nan"
"Nifa ummi bazan bud'e ba sea abbi ya dawo min da mame"
Shiru tai tukkuna ta qara cewan
"Ka bud'e d'ana zan maka komai kake so kana so kasa mamanka kuka ne, kasan idan bana ganinka bana jin dad'i'
Cikin muryar shagwa6a ya bud'e baki
"Ummi zaki hana anty nana ta daken"
"Na maka alkawari bazata kara dukanka a gabana ba kaji aliyuna jan gwarzo zakin fama, ka bud'e dakin".
Tasowa yay ya bud'e dakin, da gudu ya fad'a jikin ummi, ummi ta rungumeshi sosai, a jikinta ya matuqar bata tausayi har a cikin zuciyanta"
"Yi shiru d'ana ka deana kuka, ga umminka nan tare dakai, zan baka dukkan gatan da mame dinka ke baka kaji ko"?
Kai ya d'aga tare da cewan
"To ummina"
Murmushi tai masa taja hannunshi zuwa d'akinta.
Tana isa ta tarar da nana zaune a d'akin, cike da hasala ta taso akanshi
"Ummi ya zaki shigo mana da yaron nan a d'aki sarai kinsan bayajin magana ynxn nan zai fara fasa mana kaya"
"Ke"! Ummi ta daka mata tsawa
"Bana son iskanci da d'iban albarka, ke kinsan da ya nai renonki ne, kowanne yaro haka yake, kurciya ce idan yay ta kuma zata wuce, komai lokacine"
Nana ta dubie aliyu ta dubie ummi
"Naji ummi amma gskya nifa...
"Kefa mi? Bazaki zauna da d'an uwanki lpy bane? Tsaya kiji wallahi nai maki iyaka da yaron nan, fice ki bani guri'
Baki ta tunzure ta kama hanyar fitah dga d'akin, yayinda ummi ta juya ta dubie Aliyu
"Kada ka damu kaji d'ana mamanka na nan tare dakai"
Mujie in baka chocolate"
Murmushi yay ya saki ranshi, suka wuce chan kuryar dakinta
Yayinda Nana tai d'akinta ta maida ta kulle, zuciyanta nai mata k'una sbd ita a duniya ta tsani aliyu, bata sonshi ko kad'an a cikin rayuwanta...
Meye dalilil"?...
®Kausar Luv💞
[11/15, 5:18 PM] Kausar~Luv: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((3))
©Kausar M Hassan
A chan bangaren hajiya salma kuwa tana fitah dga gidan kai tsaye taxi ta tsayar tasa jakarta a ciki.
"Malam mai taxi unguwar shanu zaka kaini"
"To hajiya"
Suka kama hanya sea unguwar shanu, suna isa dea2 kopan gidan da zata shiga ta tsayar da mai taxi di'n ta ciro kudi'nshi naira d'ari ta bashi, ta dauki jakarta, dea2 kopan ta tsaya tana kallonshi, rabonta da gidan tun ranar da aka sata lallen aurenta sea kuma yau datazo, kuma zuwan bana wuni ba na zama gabad'aya, hawayenta ta share tasa kafanta a gidan daya kasance matsakaici tare dayin sallamanta.
Yar dattijowan dake zaune akan kujera ta d'ago idanunta, ganin "yarta da tai yasa ta d'ago ta dubeta
"Salma ina Aliyu"?
Wannan shine tambyan da tafara yimatah
Kuka ta fashe dashi tai zaune dirshan akasa
"Mama alhj ya sakeni, kuma yace "idan nasamu miji inyi aure".
Dattijowan ta girgizah kai
"Bkomai salma Allah yasa haka shine mafi alkhairi, dauki jakarki ki shiga da ita dga ciki"
Hakan ko akayi ta dauki jakarta ta shiga dakin da rabonta dashi shekara goma shaa biyu. Rayuwa kenan.
Karfe takwas na daren wannan rana ta alhamis.
Aliyu ne kwance akan kafafun ummi, yana wasa da d'an super man d'in roba, anty nana ce ta shigo a d'akin ta zauna kusa da ummi.
"Ummi abbi na kira"
Ummi ta tashi zaune ta dubie aliyu duba na soyayya
"Aliyu ka jirani ynxn nan zan dawo, bance kai fad'a da kowa ba, kaji ko?
Kai y girgizah ya cigaba da magana dashi da super man dinshi kaman ynda yake daukan yanayi.
Ummi ta kama hanyar fita d'akin yayinda ya rage dga anty nana sea aliyu.
Kallonshi tai tun daga sama har k'asa ta watsar tasa hannu ta rik'e masa kunne
"Kai dan ubanka waye yace ka shigo d'akin nan"?
Shiru yay, yaja jinin jikinshi sbd tsabar tsoron nana dayakeyi.
"kana jina kayi shiru kasan cewa bana son ina magana ana kyaleni ko"?
Cikin rawar murya ya fara magana
"Anty nana mai nai maiki dan Allah? ynxn fa zaune nake banyi komai ba"
"Taras"! Kaji saukan mari a fuskan aliyu , wnda hakan yay sanadiyyan sakin mutum butumin super man din dake hannunshi ya kwallah k'ara saboda zafin marin dayaji.
Tashi tai ta kalleshi
"Dan ubanka ka sake ka fad'awa ummi sea na maka wnda yafi wannan"
Sheisheikar kuka ya hauyi sbda anty nana ta hanashi kukan, da gudu yay kuryan d'akin ummi kan gadonta ya cigaba da kukanshi
"Mame kina inane, dan Allah kizo plsss"
Haka ya dinga fad'a har bacci yay awon gaba dashi...
Wanene Aliyu?
Wanene Abbi (alhj)?
Wacece Nana?
Wacece mame?
Wacece ummi?
Ya ya alaqar su take a cikin gidan"?
Ku biyoni ni kausar M Hassan dmn jin wannan labari
®Kausar Luv💞
[11/15, 5:19 PM] Kausar~Luv: [7/30, 6:22 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((4))
©Kausar M Hassan
Aliyu haydar, d'ana ga Alh shuraihu isah shine dea d'anshi namiji a duniya d'aya tamkar da dubu, wnda ya dauki son duniya y d'ora masa, kasancewar, shi d'ayane d'anshi namiji a duniya, aliyu dea farine mai matsakaicin baki, dogon hancinshi ya k'ara masa kyau gashi da d'an jikinshi kadan dea2 misali, shekarunsa bazasu zarce tara zuwa goma ba ynxn haka yana primary 5 ne a matakin karatun zamani, a b'angaren addini kuwa yana karatunshi dea2 gwargwado kaman ynda ya kamata.
Wacece mame?
Ainahin sunanta salma, itace matar alhj, cewa da baban aliyu ta 2, yana sonta sosai, kasancewar itace ya aura bayan ya auri maman nana, aliyu ne kad'ai d'anta a duniyah, hajiya salma mace ce mai addini da son ibada, batada matsala a rayuwanta ko kad'an.
Wacece ummi?
Ainahin sunanta rabi'atu usman, wadda aka fisani da hajjah, itace matar alh shuraihu ta farko, tanada yara 2 tare dashi "Nana asma'u da kuma nafisa, nafisa tana gurin kanwar mamanta mai suna zaliha, a chan take karatu kimanin shekarunta 8 a duniya..
Ummi ta kasance mace mai kamar maza, kasancewar ta uwar gida ga Alhj shuraihu, ta tsaya tsayen daka gurin ganin tai hakuri da komai ke biyowa bayah. Duk da ba ita ta haipie aliyu ba tana matuqar sonshi da gskya, ko kusa bata daukanshi d'an kishiyarta, ta daukeshi tamkar d'anta data haifah...
Wacece Nana?
Nana asma'ah shuraihu isah wannan shine sunanta, kimanin shekarunta 18 a duniyah, idan akuy wanda ta tsana a gidan to bai wuce aliyu ba, sanadiyyar wannan kiyaya kuwa itace tana ganin mahaipinsu Alhj shuraihu y nuna masu banbanci tsakaninsu da d'anshi namiji wato aliyu a ynda take gani, nana fara ce, mai d'an matsakaicin jiki, da manya_manyan idanunta masu kama dana mage, ma shaa Allah nana Allah ya bata kyauwun fuska amma bbu kyauwun hali, tana s.s.3 a matakin karatun zamani..
wannan kenan.
Wanene Alhj shuraihu??
Alhj shuraihu mutum ne mai arziki, yana d'an shekara 25 yay aure, ya auri hajjah, shekarunsu 7 a tare amma Allah bai bata haihuwa ba, bayan wad'an nan shekarun ta haipie yarta ta farko mai suna jamila, bata jima ba Allah yay mata rasuwah, haka ta dinga haihuwa har sau hud'u tana jiro "ya "ya mata suna rasuwa tukkuna Allah y bata nana, bayan ta haipie nana sea da tai shekara 5 bata kara haihuwa ba, byn alhj ya auro hajiya salma ta haipie aliyu, bayan shekara 2 itakuma ta haipie nafisah. Wannan kenan....
[7/30, 6:23 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((5))
©Kausar M Hassan
Washe garin ranar ta kama juma'ah, bayan ummi ta shiryawa aliyu ta had'a masa kayanshi da lunch box d'inshi gaba da'yah.
"To aliyu sai ka dawo ko"?
Kiss ya manna mata a kumatu
"Bye ummi sea na dawo"
Murmushi unmi tai tukkuna tai masa hannu.
Da gudu ya ruga ya shiga cikin motan, nana ce a gidan baya, shikuma ya bud'e gidan gaba ya shigah, cike da murmushi ya gaidah driver d'in dke kaisu makaranta mai suna musa
"Ina kwana kawu musa"?
Murmushi yay ya amsa da
"Lpy qlw aliyu zakin fama, aliyu ikon Allah"
Harara nana ta aika masa mai rai da lpy
"Kai dallah malam kajamu ka kaimu makaranta ka tsaya kana yima mutane wani surutun banza"
Humm! Y fad'a kawea yaja motan aka bud'e masa gate suka bar gidan zuwa makarantarsu dake nesa da gidan sosai.
Suna isa yay parking suka fita, suka karasa kowanne yay 6angarenshi, kasancewar makarantar su primary and secondary school ne. School d'insu d'aya.
******
Hajiya salma ce zaune a d'aki bayan ta had'a karin komallo taci ta zauna gata ga mama, hajiya salma tayi shiru tana tunanin duniya.
Mama ta kalleta ta dubieta
"Salma dan Allah ki deana tunanin nan, kada ki sawa kanki hawan jini".
Juyawa tai ta dubie mama
"Mama bana tunanin komai a raina face d'ana aliyu, aliyu yana bani tausayi sosai sbd shi kad'ai na haifah, duk da nasan hajjah na kulamin dashi, amma ina tsoron nana, sbd nana batada kirki bata son yaron nan kuma bansan dalili ba"
Mama ta dafa kafad'anta
"Salma kiyi hkuri, kicigaba dayi masa addu'ah, Allah yana amsa addu'ar iyaye musamman ma ta uwa zuwa ga "ya "yanta".
"To mama" ta fad'a jiki a sanyaye..
Karfe 1pm aka tashi su aliyu dga mkrntah, jakarsa ya dauka tare da abokinshi mai suna shafi'u suka kama hanyar fita dga mkrntar, kasancewar ko sun tashi dga makaranta sea ya jira an tashi su nana sea azo a d'aukesu su dawo tare.
Shafi'u shine babban abokin aliyu a makaranta, koda yaushe tare kake ganinsu, abunda ya k'arwa abotarsu amarshi shine shima shafi'u yayarshi ajinsu d'aya da nana kuma k'awartace sosai..
[7/30, 6:23 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((6))
©Kausar M Hassan
Dea2 bus stop din skul din suka tsaya shida sauran wad'anda ke jira azo a daukesu.
Wasa sukeyi Yar boya, shida shafi'u, su nana suka fitoh, yana ganinta ya natsu abunshi ya daukie jakarshi ya daura a bayanshi.
"Tashi ka wuce"
Sim2 ya tashi y wuce, shida shafi'u, yayinda nana ta zauna itada kawarta siyama yayar shafi'u abokin aliyu.
Bayan sun zauna siyama ta kallie nana
"Haba nana wea mai yasa kika tsani yaron nan dan Allah"?
Nana ta d'ago idanunta ta dubie siyama
"Siyama kisani cewa mahaipina shi yaja komai"
Ta tashi tsaye ta kallie siyama
"Bara in baki labarin abunda yasa na tsani aliyu siyama a rayuwata"
" Abbi d'inmu mutum mai son jama'ah da mutane, gidanmu ya kasance babban gidah, gidan sama ne, d'aku nan dake gidanmu sunyi 10 saboda yawan bakin da ziyartarmu da kuma yan uwah, lokacin da mahaipiyata ta haifeni mahipina ya nuna min soyayya dea2 gwargwado, yana kula dani, hka ummi da kuma mame, bayan wasu shekaru Allah y baiwa mame ciki ta haipie Aliyu.
A lokacin mahaipina ya daukie son duniya ya daura mashi, komai yay baya laipie, sea in nema abu a gurinshi ya hanani ya dauka ya bashi, bazan manta ba tun yanada shekara 8 yake d'aukanshi suna yawo duniyah, yama manta da wata y"a wea ita Nana asma'u, kinji siyama wannan shine abunda yasa na tsaneshi, saboda da ba dan an haipieshi ba da banda damuwa"
Nana ta juya ta dubie siyama
"Kuma wallahi zan iya halaka aliyu akan hakan"
Siyama dake zaune da sauri ta tashi tsye tasa hannu ta dafa kafad'anta
"Nana kiyi hkuri ni banga wni abu gameda hakan ba tunda mahaipinku komai yanayi maki kuma shi ai namiji ne fa, dole ne ya rik'a daukanshi yana fita dashi"
Nana tai ajiyan zuciya
"Hmm siyama kenan kada ki manta a cikin Al_qur'ani mai girma Allah yana cewa "y'aku wad'anda kukayi imani kuji tsoron Allah kuma kuyi adalci a tsakanin "ya "yanku". Allah bai ban_bamta "ya "ya maza da "ya "ya mataba, dukkan mu "ya "yanshi ne da siyama...
Siyama ta nisa ta bude baki
"Buh amma...
Dea2 lokacin mai zuwa daukansu yazo hkn yasa siyama tai shiru, aliyu na hangoshi da gudu ya karaso inda suke
"Anty nana gashi mota tazo mu tafie gidah"
"Jeka gani nan zuwa" ta fad'a tare da watsa masa harara.
Jiki a sanyaye ya k'arasa cikin mortar ya bude gidan gaba ya shigah.
"Aliyuna har an tashi"?
"Eh an tashi kuma kasan next week zamu fara last exam dinmu a primary kaga sea in shiga secondary ko"?
Murmushi yay
"Allah ya bada sa'ah aliyu"
"Amin uncle" ya fad'a yana daria.
Nana tai d'an murmushin mugunta
"Yau aliyu ina fadamaki bazea kwana a duniya ba, ba dea ice cream yake shaa ba? Yui kuwa zaisha na ajalinshi, kada ki kashe wayanki dan zan kiraki in fadamaki cewan aliyu ya mutu"
Ta kyalkyale da daria ta kama hanya zuwa mota, yayinda siyama ta girgizah kai cike da tsoro take kiran sunanta, dan daukan take ta haukace.
Nana najin kiran da take mata tai banza da itah, hka ta shiga mota ta maida marfin motan ta rufe, kawu musa yaja motan suka karasa gidah.
®Kausar Luv💞
[11/15, 5:19 PM] Kausar~Luv: [7/30, 9:30 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((7))
©Kausar M Hassan
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un"
Siyama ta furta a fili, yayinda ta kira shafi'u ganin mai zuwa d'aukansu yazo.
Da gudu ya karaso suka shiga motan duk a gidan bayah, tunani ta hauyi na anya kuwa za'a samu irin wad'an nan mutanen a duniyah lallai kuwa nana ta tabbata batada hankali kuwa, amma ya zatayi tai saving din Aliyu gameda nana "?? Wannan shine tunanin data shigayi a hka har suka karasa gidah dukansu.
Suna isa aliyu da gudu yay kan abbi, abbi yaja hancinshi kad'an
"Ma boi an dawo skul ko"?
"Yes daddy and kasan kuma cewan ranar monday din nan zamu fara jarabawa, I need to read hard sannan kuma ynxn babu shan ice cream babu wasa, babu game"
Murmushi abbi yay
"Ma boi kenan, kaga kuwa abunda ya kamata ayi shine kana kammala primary dinka tunda akuy yaron abokina dake karatunshi a london shima secondary yake sea in had'aka dashi kaje chan ka kammala har degree dinka ka dawo ko"?
Aliyu daria yay
"Abbi ni bana son zuwa chann, America nakeso" ya fad'a cikin muryan shagwa6a.
Duk wannan abun dake faruwa a gaban idon nana akeyinshi, wani d'an guntun tsaki taja tukkuna ta haura sama tai d'akinta cike da takaici.
Abbi ya d'go kai ya dubie ummi dake tahowa
"Kinga d'anki nan wea nace na kaishi U.K yace U.S yakeso idan ya gama primary dinshi.
Ummi ta dafa kanshi tare da cire masa jakar makarantar dake goye a bayanshi.
"To alhj inda yakeso ba sea akaishi a chan ba, tunda dea d'ana ne, maza kaje kai wanka kazo kaci abunci sea driver ya kaika gurin mame ko".
Alhj shuraihu y d'ago kanshi
"Babu inda zashi yana nan tare damu"
Zatayi wata magana kawea ya haura sama yay d'akinshi, yayinda aliyu ya tafi ya aikata kaman yanda umme tace ya dawo da kanta take bashi abunci yana ci, har ya koshe ya tashi yay d'akinshi ya fara karatu kaman ynda ya fad'ah...
[7/30, 9:33 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((8))
©Kausar M Hassan
A chan bangaren siyama kuwa tun bayan komawarta gida tunani kawea takeyi, saboda tasan nana zata iya aikata abunda ya zarce wnda ta fad'a gameda duniyah.
Da wannan tunanin ta wuni har dare
Misalin karfe 8pm na dare, bayan sun kammala dinner d'insu, ummi taja hannun aliyu sukai d'akinta, tana zaune tana kallo, sea ga kira wayanta ya hau ruri.
Dauka tai ta kara a kunne tare dayin sallama
"Assalamu alaikum"
"Amin alaikum salam ummi, nice siyama kawar nana dan Allah aliyu nakeson yin magana dashi idan yana kusa"
Ummi ta kira aliyu, da sauri ya taso yazo
"Kar6a waya wea siyama kawar nana keson magana dakai, kayi magana ni zan tafie kasa in dauko maka lemo in dawo ko"?
Kai ya d'aga mata alamar to tare da amsan wayan ya kara a kunne.
Cikin muryanshi mai dadin sauraro ya fara magana
"Hello"
"Hy"
"Aliyu kana jina ko? Daga ynxn duk abunda nana zata baka kada kacishi"
"Saboda mi"? Ya fad'a a takaice.
"Saboda tace tana so ka rabaka da mame kaji ko"?
Kai ya girgizah tukkuna ya kara da cewa
"To anty siyama bazan ciba"
Ya maida wayan ya kashe.
Idonshi da zai d'ago sukayi ido 2 shida nana, ido ya ware, yayinda nana ta shigo a d'akin tana yimasa murmushi rike da ice cream a hannunta.
Da gudu ya hau kan kujera ya dauki remote ya chnza channel zuwa MBC 3 ya hade hannayenshi guri d'ayah.
Nana murmushi tai ta matsa kusa dashi ta zauna
"Aliyu na"
Ido ya d'ago
"Na'am anty nana"
"Ga ice cream na kawo maka, nasan kana son ice cream"
Kai ya girgizah
"Ni bazan sha ba anty nana, ummi tajie ta daukomin lemo"
Nana ta turnukie fuska
"Haba aliyu mai yasa bazaka shaa ba, kaga bazan kara dukan ka ba kaji ko"?
"Na fadamaki bana shaa ki kyaleni anty"
"Dan ubanka sea ka shashi ina maka magana kana kyaleni ko"?
A zuciye ta bud'e roban ice cream d'in ta d'ebo a cikin chokali ta fara mika mashi tare da murd'e masa baki, kokawa ta 6arke tsakaninsu.
"Hakan yayi dea2 da shigowan ummi
"Ke! Mai kike yine haka"?
Cikin rawar murya ta fara magana
"Ummie a'a... wea.. dama ice cream ne na bashi shine yace baya shaa"
"To ana dolene nana, tunda baya sha ki kyaleshi mana dan Allah, ki daukie kayanki ki shaa mana"
Ta karasa maganar da karasawa cikin d'aki taja hannu aliyu suka wuce ciki
A cikin zuciyanshi yake cewa
"Kin shiga 3 kuwa nana" yay mata gwallo😜
[7/30, 9:40 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((9))
©Kausar M Hassan
Washe garin ranar ta kama assabar tunda safe aliyu ya tashi ya tattaka zuwa kopar dakin nana, kasancewar masu aikin gidan da an kammala sallan asuba suke tsafatace ko ina da ko ina na gidan.
A hnkli ya daukie ruwa a cup, dea2 kopar d'akinta ya zubar dasu ya ruga a guje y koma d'aki ya kwanta.
Ba'a jima ba nana ta fitoh dga d'akin, taku 2 tai kajita kasa tim😂 kamar an zube kayan wanki, kugu ta rike ta fara waiyyo! Dkyar ta iya tashi tukkuna ta karasa d'akin aliyu ta kwankwas, tasowa yay ya bud'e tare da cewa
"Ina kwana anty nana"
"Lpy qlw aliyu, zo muje kitchen yau ni zan dafa maka abuncin daka fiso kaji ko"?
Murmushi yay suka kama hanya sukai down stairs, a kasan ta samu dogon towel ta d'aura ta cire kayan baccin ta shanya a igiyah suka shiga kitchen din, ta fara har_hada masa indomie, shidea yana zaune yana kallonta
Har ta kusan kammalawa ta dubie aliyu
"Jeka d'akina ka dauko min kaya na nan kan karamin drawer dina yi sauri"
Babu gardama ya haura saman, koda ya isa an goge ruwan, daria yay kad'an ya bud'e dakin ya shiga y dauko kayan kaman ynda tace ya dawo kasa.
Koda ya sauko ya tarar da ta had'a abuncin akan dinning.
"Yauwa aliyu kawo kayan nan zauna ga abuncinka nan na had'a maka"
Murmushi yay ya dubieta yaga tana yin yar daria
"Anty nana ina ruwa, kinsan bana cin abunci sea da ruwa fa".
Har ta bud'e baki zatayi masa fad'a sea ta fasa ta tashi ta koma kitchen, kapin ta dawo yay maza y chnza kwanon abuncin ya fara cin na gabanshi.
Tana dawowa ta tarar dashi yana cin abuncin, haka yasa tai murmushi ta ajiye masa ruwan kusa dashi, ta zauna ta fara cin nata, tana ci tana murmushin muguntah, shi kuwa aliyu sea cin nashi yakeyi.
Har taci abunda yafi rabin abunci sea taji cikinta ya fara murd'awah, da sauri ta rike cikinta, ta fara hawaye, aliyu ta kalla tagan lapiyanshi kalau, take ta kai k'asa, aliyu dake zaune da gudu ya haura sama ya kira ummi, tare suka dawo shida ummi a rud'e, da sauri tace "zubairu kiramana Dr bilal, haka kuwa akayi , kasancewar shi makocinsu da hanzari yazo gidan, yana ganin hakan yace "a bashi madara peak, da sauri aka shiga kitchen aka kawo masa, fasata yay yace "ummi ta rikata", haka ummi ta d'aga kanta ta bata madaran tasha, take sea amai, nan aka dauketa akai da ita d'aki, Dr bilal ya dubata bayan d'an lokaci kad'an ya dubie hajjah
"Hajja guoba ce taci a cikin abunci, Allah ma yayi mata arziki dan da ta kasheta"!
🙆🏾Nana u wan kill d lion😏?
Cike da mamaki hajjah ta amsa da
"Guoba kuma dr, kai aliyu waye y baku abuncin da kuke ci"?
Cikin sanyin murya y kalleta
"Ummi ita ta dafa fa kuma ita ta bani nawa da nata"
Ummi ta jinjina al'amarin
"Allah ya sauwaka, nan Dr ya basu tabbacin cewan zata farka zuwa wasu awowi, in shaa Allah kuma zata buqaci hutu sosai, ya kuma yi masu sallama.
Fitarsa keda wuya, ummi ta fitah ta bar aliyu a d'akin
Daria yay a fili ya furta
"Am back bakin samu na rika jin magana ba har ina jin tsoronki ba, to na dawo da asalin sunana na aliyu"
Dama chaan bana jin magana, haka nake wollah😂 sbd hka ki kuka da kanki... Nanuwa😏
®Kausar Luv💞
[11/15, 5:19 PM] Kausar~Luv: [7/31, 5:39 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((10))
©Kausar M Hassan
Nana bata farfado ba sea kusan la'asar tana nan tana bacci, yayinda Aliyu ya tafie makarantarsu ta islamiyya dake nan kusa da gidah.
Bayan nana ta farka dga bacci, a hnkli ta bu'de idonta chaan ta tuna abunda ya faru sea ta girgizah kai
"Yaro kaman aljani, nikam yau ai danayi mutuwan mazuru"
Tashi tai ta shiga toilet ta watsu ruwa, tare da d'aura alwala tai sallah.
Aliyu bai dawo ba sea karfe 6 dea2, yana shigowa sukayi arangama shida nana, jaa da baya yay kad'an tukkuna ya kalleta
"Anty nana ina kwana, ina wuni"?
Hannu tasa ta rike masa kunne
"Kai uban wa yace maka ka chnza kwanon abunci nan d'azu"?
Baki ya torou
"Nifa anty nana kinga ba ni naiba, kefa kika bani abuncin nan"
A kunne take fad'amasa
"To yayi aliyuna yi maza kaje d'akin ummi"
Murmushi yay
"Ok anty nana"
Kai tasa ta fita wajen gidan yayinda aliyu cikin sand'a yay dakin nana ya maida ya kulle. Kasancewar akuy wata kujera a d'akin da nana ke zama mai kamar ta karfe, kuma d'aurata akeyi mutum take zea iya kwance ta y kuma had'ata.
Aliyu daria yay, ya daukie kujeran ya kwance d'an abunda akasa aka d'aureta ya maida ya ajiye, ya lalla6a ya fitoh dga d'akin zuwa nashi d'akin ya cire kayanshi yay wanka ya chnza kayan jikinshi abunshi yasa takalminshi sandals ya fitoh.
Aliyu haydar kenan ba dea tsafta ba, ga son gayu kwata2 baya son k'azanta a rayuwnshi, gashi dea yaro amma kuma abokin manya sbd Kanshi na jaa...
Yana fitowa kai tsaye dakin ummi ya nufah, chaan ya tarar da abbi zaune kan carpet yana kallon CNN, yayinda ummi ke had'a lemun ginger.
"Assalamu alaikum" aliyu yay sallama
"Amin alaikum salam" abbi da ummi suka amsa
Da gudu yaje kusa da abbi ya zauna shima ya kurawa TV d'in idanu yana kallon news, duk da primary school yake amma yana jin turanci, irin wnda ba big2 grammars d'in nan ba.
Chaan kaman an ta6ashi ya dubie ummi
"Ummi ni gskya ki fad'awa abbi bana son america kuma, makkah nakeso"
Abbi dake zaune yay daria kad'an ya dafa kanshi
"Aliyu mai yasa kake son zuwa chaan Makkah"?
"Abbi saboda kaga chaan duk muslimi ne"
"Shekenan Alhj kaga d'ana yayi zabi mai kyau sea akai shi a chaan"
"Allah y kaimu lokacin"
Ummi ta amsa da
"Amin"
Yayinda Aliyu yay murmushi abunshi wnda ya k'ara masa kyau..
[7/31, 5:57 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((11)
©Kausar M Hassan
Karfe shida da rabi nana ta dawo dga inda ta'je, kai tsaye dakinta ta nupa, taja kujera ta zauna, zaunawan da zatayi kajita kasa rum,
"Waiyh Allah"
A daddafe ta tashi ta koma kan gado ta zauna, tana mamakin abunda ke faruwa, sea kuma ta tuna da cewan Aliyu fane, chaab!
Hka sukai spending ranakun karshen makon, tskanin aliyu da nana kuwah, duk tarkon data had'a masa sea ya ketareshi abun y koma kanta.
Yau ranar ta kama monday, sbd hka Aliyu da nana suka shirya zuwa makaranta, kasancewar yau itace ranar dasu zasu fara jarabawa yasa shi natuswa, hka suka shiga class din, da uniform din makarantar dark blue din wando da farar riga, da abun wuya shima dark blue, na matan kuwa duk hkne dfrnce din shine bbu abun wuya, sea farin hijab..
Hka sukai exams d'insu har ta tsawon sati 2 suka kammala.
Ranar da suka kammala akai hotona na bankwana, tare da malamai da kuma d'aliban makarantar.
Akuy wata yarinya a ajinsu aliyu mai suna Nadiya, ita dea aliyu yana matuqar burgeta, hakan yasa tai duk ynda tai sukai hoto su 2, sannan sukai tare da shafi'u..
Bayan kammala exams d'inshi, ya rage dagashi sea ummi ke zama a gidan, kasancewar nana tana zuwa makaranta yin waec, rayuwarsu sukeyi cikin jin dadi yayinda abbi yasa aka fara nemawa aliyu admission dinshi a wata makaranta dake nan gaein madina birinin manzo, brinin karamchi....
[7/31, 6:15 PM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((12))
©Kausar M Hassan
Bayan wata 3!
Yau ranar ta kama ranar juma'ah, yayinda ummi keta faman had'awa aliyu kayanshi na wucewa makarantar da aka sama mashi admission din a kasar madina.
Bayan ta kammala hada masa kayanshi tsaf, ta dubie abbi dake zaune yana kallonta yana murmushi,
Cike da tsoro da kuma fargabar abunda zai biyo baya ta fara magana.
"Alhj dama cewa nai mai zai hana akai yaron nan yaga mame dinshi kapin ya wuce makaranta, tunda yanzu idan ya tafie kuma sea ya jima bai dawo ba"?
Abbi dake gincire y tashi tsaye ya dubie ummi
"Ina wasa dake irin wannan ne? Kada ki koma yimin wannan maganar idan ba haka ba ranki zai bace a gidan nan"
Yana kammala fadar haka ya tashi ya zarce d'akinshi
Ummi binshi tai da kallon mamaki, a zuciyanta ta furta
"Ikon Allah ikon gskya, ynxn ni daga magana sea abu y dawo kaina? Ni ina laipiena dan kawea inaso kayi abunda yakamata, wannan ai baso bane kana kokarin raba uwa da d'anta, Allah ya sauwaqa"
Washe garin ranar ta kama assabar, ummi ta shirya ta fitah bikin wata yar kawarta da akeyi, aka bar nana da aliyu a gidan
Nana ce zaune a babban falo, tai zaune kan kujera, aliyu ne ya fara saukowa dga d'akinshi, idanunta da zata d'aga tagan shi yana kokarin yayou downstairs.
Cikin kakkausar murya ta kira sunanshi
"Aliyu kai"
D'agowa yay ya dubeta dan bashida idea akan abunda zata iya yi masa yasa ya sakko k'asan, kusa da ita yaje ya rage tsayenshi ya kafeta da idanunshi, hannu tasa ta zungureshi akai, ya dago idanunshi da sukai narai2 ya dubeta
"Kai zaka tafie saudi karatu ko"?
Ta d'aga hannu kenan zata mareshi sea ga sallama
Wadda wannan ba sallaman kuwa bane face na Anty zaliha, kanwar mamansu, tare da nafisa kanwar nana.
Hakan yasa ta fasa niyyan abunda zatai, da gudu nafisa ta rugu, duk daukan nana gurinta zatai sea taga tayi gurin aliyu.
"Yaa aliyu i miss u"
Murmushi yay kad'an
"Kanwata inace kin dawo gidah dea sbd nima a rika cemin yaya"
Nafisa ta d'aga masa kai
Aliyu yaja hannunta suka haura saman d'akinshi yayinda anty zaliha ta zauna kan kujera, suka fara tadie da nana, nan ta dauko mata ruwa da lemo ta kawo mata tare da kiran zubairu daya sanarwa ladidi mai aiki ta dora girki anyi bakuwa.
Zubairu! Shine babban yaron gidan Alhj, shine ya zaama tamkar d'an uwansu na jini da tsoka jiki da jijiya. Yazama kamar sarkin gidan, duk abunda ake a gidan yana sane, haka ya daukie aliyu tamkr d'an daya haifah..
Haka kuwa ya fice ya aikata kaman ynda ta fad'ah.
Ba ummi ta dawo ba sea bayan la'asar lis tukunna, nan suka gaggaisa da kanwarta ta kuma shaidamata cewan nafisa ce tace tana son dawowa gidah shine tace bara ta kawotah.
Bayan d'an lokaci kadan tai mata sallama tare da kama hanya zuwa garinsu wato Kadunah..
Aliyu da Nafisa kuwa wata shaquwa ke kara shiga tskaninsu, suna son junansu a matasyin yan uwan junah..
A wannan rana dea a d'akin ummi suka kwana dukansu.
Washe gari!
Da asuba aliyu yay d'akinshi yay sallah, ya zauna yana tunanin mamanshi, shi ko yama zayyi ya ganta bai sani ba.
Nana ce ta bud'e d'akin sad'af2 kaman wadda zatayi satan wani abu ta shiga, tana shiga ta maida kopan ta rufe...😳🙆🏾
Waiyyo dear little aliyu lion😰
®Kausar Luv💞
[11/15, 5:19 PM] Kausar~Luv: [8/1, 8:13 AM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((13))
©Kausar M Hassan
Tana shiga ta dubie aliyu, kan kujera ta zauna ta bashi umarni
"Oya fara tsallen kwad'o ka gama kuma kayi kamun kunne mazzah, kai ya d'aga mata jiki a sanyaye ya fara yi.
Nafisa dake kwance ta lalaba taji babu aliyu inda suka kwanta hakan yasa ta tashi ta mum_murza idanunta ta yaye abun data rufa dashi tabi hanyan d'akin aliyu, direct ta murd'ah kopan koda ta bud'e ta tarar da aliyu sea kuka yakeyi, da gudu ta isa gareshi ta d'ago kanshi
"Yaya aliyu mai yasa kake kuka"?
A hnkli ya d'aga dayan hannunshi na hago y nuna mata nana, da sauri nafisa ta fara magana cike da rud'u
"Anty nana mai yaa aliyu yayi maki da zaki dakeshi haka"?
"Nafisa tashi nan kada in hada dake wollah"
Nafisa tasa hannayenta ta rungumou aliyu cikin muryan kuka ta fara magana
"Ni wallahi anty nana sea dea ki hada dani amma gskya bazan yarda ki daki yaa aliyu ba"
Huci nana tai tare da yin tsaki a fusace ta wuce ta bar d'akin..
Aliyu a hnkli yaja da baya kad'an kan carpet ya fadie kasah, kanshi har juwa yake gani, saboda tsaban wuyan dayasha, hawayene keta faman zuba a idonshi..
🤔Rayuwa kenan wata rana sai labari.
"Yaa aliyu bara in tafie in fadawa ummi"
Har ta tashi ya riko hannunta
"A'a nafisa kada ki fadama ummi ki kyaleta kinji ko"?
Nafisa kuka ta hauyi itama saboda tausayin aliyu..
Hka aliyu ya wuni a wannan ranar jiki a sanyaye, kowa a gidan mamaki yakeyi, ita kuwa ummi ta d'auka cewan sbda zai bar gidane.
Shi kuwa aliyu abu 2 ke damunshi da azabar da nana ta bashi da kuma rashin ganin mame gashi har ranar tafiyanshi ta kama gobe...
Kasancewar akuy d'an abokin abbi da zasu tafie tare mai suna zayyanu shima a chaan zai fara karatun, duk kusan sa'an shi daya da aliyu lion.
Shafi'u ma yzo sunyi bankwana da junah...
[8/1, 8:13 AM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((14))
©Kausar M Hassan
Washe garin ranar ta kama ranar tafiyan aliyu, saboda hka ummi ta hada masa abunci, saboda bataso yaci abuncin jirgi, karfe 12pm jirginsu zea d'aga dga babban filin sauka da tashin jirage na margayi sarkin musulmi abubakar na 3 dake sokoto.
Tun wayewar gari, nafisa da aliyu suke tare, nana kuwa ta rasa abunda ke mata dad'i sea faman safa da marwa takeyi a d'aki.
Dad'ina da agogo aiki, haka lokaci ya buga karfe 11:50am, saboda go slow din kan hanya abbi yace "aliyu ya fito su tafie, tashi yay sukai sallama da dukan ma'aikatan gidan, nana ce kawea bata gurin, sun jima suna bankwana shida nafisa tukkuna abbi ya rika hannunshi suka kama hanya.
Sautin muryan da sukajie nayin sallama ne yasa abbi dakatawa y saki hannun aliyu tare da d'aga idanunshi, arba yay da hajiya salma.
"Ke mai ya kawoki gidana"
Cikin muryan tausayi ta hau yin magana
"Alhj nasamu labarin yau aliyu zai tafie makaranta shine nazo in ganshi muyi sallama"
Da gudu aliyu yay inda mame, ma'aikatan gidan kuwa har zuwa ummi sunji dad'in wannan gamuwa tasu.
Rungumeshi tai sosai tana hawaye
"Aliyu Allah yay maka albarka, kayi karatu banda wasa kaji ko"?
Murmushi yay ya k'ara laqamie mame, mame kada ki barni dan Allah"
"Ina tare dakai d'ana a koda yaushe, bazan tab'a barinka ba"
Zubairu!!! Alhj ya hau kiranshi
"Na'am alhj"
Yi maza ka karbomin aliyu saboda zamuyi late idan muka tsaya nan
Da hanzari zubairu ya matsa kusa dasu
"Aliyu alhj na kiranka"
Kara shigewa jikin mame yay.
Yayinda zubairu ya kasance baida zabie illah yayi kaman yanda alhj yace
Hannu yasa ya fara jan aliyu dga jikin mame
Kuka aliyu ya hau yi tare da kiran sunanta
"Mame! Mame dan Allah kice ya kyaleni, bana son tafiya ni gurinki nakeson zama"
Kuka aliyu ya hauyi har idanunshi sun kada sunyi jajir
"Mame! Dan Allah"
Ga aliyu a hannun zubairu ya rikeshi, yana kucce2 a hannunshi, iya karfinshi ya dage yana kiran sunan mame
"Mame kuka takeyi sosai sboda tausayin d'anta
"Aliyu!!!""
Ta kira sunanshi ta fashe da kuka.
Da karfi ya su6uce ga rikon da zubairu yay masa ya qara rugawa da gudu yay gurin mame ya rungumeta
"Mame! Pls ki daukeni mu tafie, mame pls"😭
Kanshi ta shafa itama din kukan takeyi..
Ganin hakan yasa alhj ya tako da kanshi ya rika hannun aliyu tare da janshi, ga kasa . Aliyu y fara bubbuga kafafunshi a k'asa yana kiran mame
"Mame!!!😭
kuka aliyu keyi sosai, har sun kai kopar fita falon ya kara ruguwa da gudu ya k'ara kankamie mame yana kuka yana kiran sunanta..
A falon bbu wnda bai zubar da hawaye ba saboda tsabar tausayin aliyu, illah nana data kasance tsaye ta dora hannayenta akan matar takalar stage din.
Abbi hasala yay da zuciya ya dirkako kan aliyu yaja hannunshi, ya dga hannu ya wanka masa mari mai kyau, wanda yasa aliyu natuswa lokacin da bai zta ba.
Hannu mutanen falon suka saa suka rike baki, ganin abbi bai tab'a daukar hannu ya dorawa aliyu ba sea yau.
B'acin rana kenan😕
Nikam ido na zaro ina mamakin wannan al'amari wea meye dalilin yin hakan na raba uwa da danta da kuma wannan tsanar data shiga tskanin alhj shuraihu da kuma hajiya salma...
Uwar d'ansa tilo namiji wadda kuma a cikin so ya aureta, tabbas akuy wata a qasa😱...
[8/1, 8:14 AM] Kausar Luv💞: *ALIYU_HAYDAR*
Page ((15))
©Kausar M Hassan
Idanu Aliyu ya d'ago sukai ido 2 da abbi, abbi yaja hannunshi suka kama hanyar fitah dga gidan, suna tafiya aliyu na waigen baya yana kallon mame tana hawaye tanai masa bye2, yyinda nana keta faman yin dariar jin dad'i, haka har suka bar gidan suka shiga motah.
Kawu musa ganin yanda fuskokinsu sukai yasa bayyi magana ba, kawea yaja motan sea airport.
Suna isa kuwah, yaron abokin abbi na zuwah, aliyu shiru yay baice da kowa komai ba, abbi na kallonshi ya bashi tausayi yama rasa da wanne baki zayyi rarrashin shi, hakan yasa ya barshi yayta huci
Abbi ka taba mana lion fa
Haka aka kirasu suka tashi kowa yaja jakarshi, da kuma jakar goyanshi suka shigah jirgi suka zazzaunah, aliyu da zayyanu guri d'aya suka zaunah. Zaiyyanu yay ta magana, aliyu yay banza dashi haka har jirginsu ya tashi dga Nigeria zuwa saudi Arabia...
Wani irin abu aliyu ke ji a cikin ranshi, baqin cikin dake ranshi yay masa yawa fiye da tsammani, har ynxn fuskan abbi yake kallo ynda ya rabashi da mame, mahaifiyanshi, sanyin idaniyarshi, gatanshi, nisful hayat dinshi...
Allah sarki Aliyu haydar😭😭
®Kausar Luv💞
0 comments:
Post a Comment