Mabaruka ta yi ajiyar zuciya
sannan ta daga dan yatsa ta
nuna shi ta ce.
"Idan kuma kana ganin da
takura, to ina shawartarka da ka
rubuta min takardar sakina
yanzun nan, sai ka hada naka ya
naka ka bar min gidana, amma
ka tuna daga lokacin ka daina
karbar albashin naira dubu dari
biyu ka daina karbar kudin da
mahaifiyata ta ke baka duk wata
ka kuma daina hawa motocina
kai hatta kayan da ka saya da
kudin mahaifiyata sai ka ajiye
min kayana kuma sai ka yi
sallama da fita wata kasa a
duniya domin na san a rashin
zuciya da lalaci irin naka da
wahala in zaka yi arziki a duniya
mutumin da ko sallah baya iya
yi!"
Anas ya yi tsaye sororo cikin
tsananin kaduwar da bai taba
irinsa a duniya ba. Wani abu mai
kamar gare-gare ya fara yawo a
cikin kwakwalwarsa, nan da nan
ya ji cikinsa ya murda kamar zai
yi amai
Cikin sauri ya dubi Mabaruka baki
na rawa ya ce
"Ki yi hakuri Mabaruka abin duk
bai kai da zafin haka ba." Anas ya
dada dafe ciki sannan ya dubi
Mabaruka.
Mabaruka ta sake fashewa da
kuka. Anas ya ji ba zai iya
daurewa kukanta ba dan haka
sai ya ruga bandaki a guje yana
zuwa sai ya fara keta amai. Bayan
tsawon lokaci ya gama zubar da
abincin da ya ci a wurin liyafar.
Daga bandakin yana iya jiyo
shisshikar kukan Mabaruka
hakan shi ya tuna masa da
guntuwar takardar da Ummi ta
bashi cikin sauri ya laluba
aljihunsa ya dauko takardar
sannan sai ya warwareta ya fara
karantawa......
.
Anas Tun da nake a duniya ban taba
sanin mene ne so ba domin ni
ko zance ma bana fita wurin
samari
To amma tun ranar da na dora
idanuna a kanka sai na ji duk
duniya bani da abin so kamar ka.
Na yi matukar farin ciki sa'ar da
na dubi cikin kwayar idanunka,
sai na tabbata kai ma kana
kaunata. Haka nan na yi bakin
ciki da ya kasance wannan
gurguwa ta yi min shigar sauri ta
aureka.
Wannan shi ya sa na yi amfani da
damar wannan liyafa domin na
isar da sakon zuciyata zuwa
gareka Na gode, zan tsaya anan,
idan har abin da nake zargi
gaskiya ne, na san zaka so mu
hadu.
Ga adireshina nan a kasa, zan
jiraka gobe gida tun daga karfe
bakwai na dare har zuwa goma
na dare...sai na ganka mai...
Ummai.
Anas ya kankame takardar a
kirjinsa cikin farin ciki sannan
kuma cikin tsananin rudewa.
"Daga yanzu duk inda za ka
muna tare zan manne maka
kamar cingam!"
Ya tuna da kalaman Mabaruka.
"Ina jiranka gobe a gida..."
ya kuma tuna da kalaman Ummi
na karshe.
Anas ya lumshe idanunsa,
sannan ya kara takardar wasikar
akan hancinsa, ya shaki kamshin
turaren jikin Ummi dake jikin
wasikar, cikin jin dadi.
Daga can falo ya jiyo gurnanin
kukan Mabaruka. Anas ya yi sauri
ya toshe kunnensa domin baya
son kukan ya bata masa farin
cikin da yake, kai da zai yiwu ya
gwammace ya kwana cikin
bandakin rungume da wasikar
Ummi!
Sidi mai jaka ya yi shiru lokaci
guda. Na dubeshi cikin kaduwa
na ce bakina na rawa.
"To mana Baba Sidi...ci gaba
mana ya ka tsaya bayan labarin
ya gama daukar dadi."
Sidi mai Jaka ya dubi kwanon
tubanin dake gabansa cikin
takaici, sannan ya dubeni da
kyau ya ce.
"Kada ka bari dadin labari ya
dauke ka, saurara da kyau ka ji
kiran sallah ake yi. Tashi ka je ka
yi sallah idan an idar da sallar sai
mu sako wani sabon zaren
labarin." Yana gama fadin haka
sai ya mike tsaye ya dauki
tsohuwar butarsa ta karfe mai
kwarin tsiya ina tsammanin
butar tafi shekaru arba'in.
Na mike tsaye cikin sauri na ce.
"Baba Sidi dan Allah...da na gama
sallah fa zan dawo." Baba Sidi ya
dubeni da murmushi ya ce.
"Idan za ka dawo ka tabbata ka
dawo min da karin tubani, domin
idan babu shi, to babu labari Nas,
na riga na fada ma ni da tubani
tamkar tsohuwar mota ce da
man fetur.
Ya juya cikin sauri da butarsa a
hannu ya nufi waje zai yi alwala.
***
Ban sami damar dawowa wajen
Sidi mai jaka ba sai bayan sallar
La'asar sakamakon tsayawa da
na yi a sake dafa min sabon
tubani.
"Kai dan nema, bana son
shakiyancin banza, me kuma
zaka sake yi da tubani. Na dauka
dazu-dazun nan na yi ma cikin
kwano guda?" Kakata ce ke fadin
haka. Na dubeta da dariya.
"Kin ga in za ki dafa min ki dafa,
in kuma ba haka ba yanzun nan
in baki takardar saki akan
tubani." Ta fashe da dariya.
"Amma kuwa da ka yi abin kunya
wallahi ka saki matarka saboda
tubani?"
Daga karshe bayan mun sha
cacar baki kusan mintuna
bakwai, na shawo kanta da kyar,
ta sake cika min kwano da
tubani, a wannan karon har sun
fi wadancan girma domin ba a
son ranta ta yi su ba.
Na riski Baba Sidi mai jaka zaune
akan tsohuwar kujerar
katakonsa yana jan carbi, tun
kafin na gama yi masa sallama ya
dago kai ya dubi kwanon dake
hannuna cikin fara'a, kamar
karamin yaron da ya yi ido biyu
da alewa mai tsinke.
"Tsohon alkawari a karo na biyu,
lallai Nas ka kyauta min." Ya ce
sa'annan ya mika hannu ya karbe
kwanon daga hannuna tun ma
kafin na ajiye shi da kaina. Sidi
mai jaka bai jira komai ba, sai
kawai ya bude kwanon tubanin
ya fara juya tubanin da yan
yatsunsa bayan wani dan lokaci
ya tabbata da cewa sun juyu
yadda ya ke so don haka sai ya
can ku wani kato ya jefa cikin
bakinsa sannan ya dubeni.
"Nas, ina fatan dazu kana biye
dani a labarin da na fara baka."
Cikin sauri na gyada kaina.
"Kwarai kuwa ka tsaya inda Anas
ya shiga bandaki ya fara karanta
wasikar Ummi harma take cewa
dashi tana son ganinsa a daren
washe garin ranar
Sidi mai jaka ya gyada kai da
murmushi.
"Wani lokaci ina son mutum mai
saurin rike al'amura a cikin
kwakwalwa nan da nan ba tare
da mantuwa ba." Na dubeshi da
murmushi a karo na farko na ce.
"Ai kuwa in ka dauke labarai
babu abin da kwakwalwata ke
iya rikewa domin koda sunan
mutane in ba dadewa muka yi da
kai ba sai ka yi ta zuwa ina
kiranka da kai!" Sidi mai jaka ya
fashe da dariya sannan ya canko
wani katon tubani ya sha ya ji
jajur dashi ga girma kamar
dankali ya miko min.
"Ungo wannan Nas jefa a bakin
ka." Na yi saurin girgiza kai cikin
kaduwa.
"Allah kuwa karbi baka jiba
yadda tubanin nan ya yi dadi.."Ungo wannan Nas jefa a bakin
ka." Na yi saurin girgiza kai cikin
kaduwa.
"Allah kuwa karbi baka jiba
yadda tubanin nan ya yi dadi har
ya fi na dazu." Na dada girgiza
kai. Sidi mai jaka ya zunkuda
kafada, "Ka cuci kanka Nas, ni
duk abincin duniya ban ga abin
da zai zo a na biyun tubani ba a
gare ni. Ya sake tsikaro guda ya
jefa a bakin salatinsa sannan ya
juya ya dubeni idanunsa na
zubar hawaye kamar kuturu.
"Nas, zaren labarin dana fara
baka labari dazu ya kare iyakarsa
kenan." Na dubi Sidi mai jaka
cikin kaduwa.
"Haba Baba Sidi, kai fa ka ce dani
Ummi ta ce tana son ganinsa
washe garin ranar, kuma yanzu
ka ce dani wai zaren labarin ya
kare."
Sidi Mai Jaka ya yi murmushi
"Haba Nas kai fa yanzu mun
zama jiki sai dai ka fadawa wani
ni, sanin kanka ne idan na ce da
kai zaren labari ya kare to ya kare
din tabbas, dole ne sai na sako
sabo sannan na jona ma shi da
bakin wannan tsohon labarin da
na saka. Ya dan yi shiru, sannan
ya sunkuyar da kai.
Nas ina son ka dauki zuciyarka
cancak ka maishe da ita can wani
lokaci, kuma wani zamani mai
dan tsayi na a kalla shekaru
ashirin da biyar da suka gabata.
Na dubi Sidi mai Jaka cikin
mamaki bani da abin cewa dan
haka sai na gyada kai na ce dashi
"Na mayar."
Sidi Mai jaka ya ce "Yauwa Nas
haka nake so da kai."
*
*
Shekaru ashirin da biyar da suka
wuce wani dogon mutum fari
siriri buzu-buzu balarabe-balarabe, ya sauka a garin nan dauke
da yar tabarmarsa ta kaba akai
yana neman inda zai sauka. Ba
don komai ba kuwa sai don
lokacin da ya sauka a garin nan
cikin dare ne tare suke da
matarsa ita ma kusan irin kirar
su daya to sai dai kuma
kyakkyawa ce ta gani a fadawa
sarki. Wannan mutum dogo fari
siriri babu komai a cikinsa sai
hanji domin rabonsa da abinci
kwana biyu kenan haka ma
matarsa. Haka nan kuma yadda
cikinsa yake hakanan aljihunsa
yake, karaf babu ko karfanfana.
Mutanen guda biyu mace da
mijinta suka shigo birni, mijin na
gaba dauke da tabarmar kaba,
ita ko matar na biye dashi a baya
dauke da wasu tsummokarai da
ita kanta bata san amfaninsu ba.
Me yiwuwa dai tana dauke da
tsummokaran ne don cika
umarnin mijinta, babu mamaki
kuma sabo da yi ne wai gawa da
gatsine. To koma dai mene ne
wannan mutane dauke suke da
muguwar yunwa ga kishi ga
gajiya, ga babu tabbacin gurin
kwana, sannu a hankali suna
yawo cikin birni tsakanin manya-
manyan gine-gine na alfarma can
sai matar ta jefar da kayan
tsummokaran dake kanta ta
durkusa, ta rike ciki.
"Wallahi...mai gida ni na gaji." Ta
ce cikin wata irin bakuwar
Hausa.
Mutumin ya ajiye tabarmar keson
dake kansa sannan ya dubi
dankareren gidan dake gabansu
wanda ke ci reras da fitulu kamar
rana. Ya dubi matarsa cikin
tsananin tausayi.
"Ban ga laifinki ba HINDATU, ai kin
yi ma kokari." Ya dan yi shiru
idanunsa akan katon gidan dake
gabansu.
"Gashi wannan gidan ma kamar
babu kowa a cikinsa, da sai in
karasa na barato mana dan abin
da zamu sa a bakinmu."
Matarsa Hindatu ba ta ce komai
ba, maimakon hakan ma sai ta
kwanta a kasa ta dora kanta
akan kullin tsummokaran ta
kurawa sararin subhanahu
idanu. Hankalin mijinta ya dada
tashi, ya san cewa dadin ta
yunwa ce kawai, duk wannan
mai sauki ne, domin sun riga sun
saba da jin yunwa, tun sa'ar da
yaki ya barke tsakanin buzaye
yan tawaye da gwamnatin
kasarsu basu kara samun damar
wani jin dadin rayuwa ba. Koda
yake can ma ba wani cikin
kwakkwaran jin dadi suke yi ba,
to amma akalla dai kafin
barkewar yaki suna da
kwanciyar hankali wannan da
sauran matsalalo halayyar yaki
marasa adadi su suka sa
wadannan mutane sabo da duk
wata irin wahala, a cikinsu har
da ma jimirin yunwa. Dan haka
abin da ya sa hankalin mijin
matar nan Hindatu ya tashi shi
ne, ya san tana da juna biyu,
akalla zai kai wata uku. Tun sa'ar
da ya ki ya barke suka fita gudun
hijira mutumin ya fitar da ran
cewa matarsa zata sami damar
haife cikin, kullum kwanan
duniya cikin zullumi yake, yana
sauraron zubewar cikin, amma
cikin ikon rabbana har zuwa
wannan lokaci matar bata ko
taba ciwon kai ba ballantana a yi
zancen zubewar cikin sai yanzu
da ta fadi a gabansa ta ce dashi
ta gaji ga kuma muguwar
yunwa.
Dogon mutumin ya mike tsaye
sannan ya sake duban matarsa
cikin damuwa kana ya dubi
sararin samaniya sai ya ga tuni
ya hade da gajimare an kuma
fara rugugin aradu haka nan
Walkiya sai haskawa take yi wal-
wal kamar tana daukar hotonsu.
"Sannu Hindatu dan jirani kadan
na karasa kofar gidan can me
yiwuwa idan nayi sa'a ko
masamu wani ya taimakomu da
abin da za mu sa a bakinmu."
Hindatu ta runtse idanu sannan
ta budesu cikin karfin hali ta dubi
mai gidanta ta ce.
"Kada ka damu je ka gani, Allah
baka sa'a." Cikin sauri na ban
mamaki idan aka yi la'akari da
rama da kuma bakar wahalar
dake jikinsa mutumin ya nufi
kofar gidan kai tsaye kirjinsa na
harbawa.
Har sa'ar da ya kai ga
tangamemiyar kofar me kamar
kofar gari bai ga motsin ko da
halitta daya ba a duk tsawon
kwararo sai wasu karnuka guda
uku dake can karshen kwararon
suna ta faman haushin babu
gaira babu dalilin kamar sun yi
ido biyu da aljan.
Mutumin ya matsa kusa da kofar
ya tsaya cikin shakka, domin bai
san abin da ya kamata ya yi ba
Shin buga kofar zai yi ko kuwa
sallama zai yi. To idan ma ya yi
sallama wa zai ji shi? Ya tambayi
kansa. Yana nan tsaye cikinsa na
kugi kamar tukunyar talge, sai ya
ji kamar dagacan sashen hagu
na katuwar kofar ana tabata.
Mutumin ya yi sauri ya dan ja da
baya lokaci guda kuma ya dubi
bangaren hagu na jikin kofar. A
lokacin ne to ya fahimci ashe a
jikin katuwar kofar akwai wata
yar karamar kofa daga hannun
hagu wacce akalla mutum guda
zai iya wucewa ta ciki, wannan
yar karamar kofa ita ce ake
motsawa ba a ko dade ba sai ta
bude. Wani dan matashin yaro
fari kyakkyawa ma'abocin
kyawun sutura da cikar hallita ya
fito daga cikin gidan sannan ya
kurawa dogon mutumin idanu
baya ko kiftawa. Dogon mutumin
ya dubi yaron, sai ya rasa ma me
zai ce masa. Domin da ido
mutum na iya tsammanin dan
saurayin yaron ya kai shekara
goma sha uku ko sha hudu, to
amma a gaskiyar al'amari yaron
shekarunsa goma cif-cif da
kwana biyu, domin shekaran
jiya-jiya din nan aka yi bikin cikar
shekarunsa goma da haihuwa.
"Sannu Malam." Yaron ya ce da
mutumin cikin ladabi.
"Yauwa dana, sannunka dai." Ya
dan yi shiru sannan sai ya dubi
yaron ya ce.
"Da Allah dan samari idan da hali
taimakon abinci nake nema duk
kankantarsa, wallahi mu baki ne
bamu san kowa ba, ga matata
can kwance akan titi, yunwa ce
ta hanata tafiya" Yaron ya dubi
mutumin na dan tsawon lokaci, a
zuciyarsa yana tunanin ja da
baya a guje ya rufe gida domin
me yiwuwa mutumin nan dake
tsaye a gabansa mahaukacine,
dubi fa kayan dake jikinsa, koda
yake dai irin kayan da yake gani
ne jikin buzayen dake gadin
gidansu, to amma shi wannan
nasa sun ji jiki da yawa.
"Ka ce abinci kake so?" Yaron ya
tambaya.
Mutumin ya gyada masa kai
sannan ya dada da cewa.
"Ko da kadan ne wanda zan
bawa matata da Allah a taimaka
min, so nake na bata ta dan ci
mu yi gaba" Yaron ya daga kai ya
dubi hadarin da ya mamaye
sararin samaniya, sannan sai ya
dubi mutumin cikin tausayi ya ce.
"Ina zuwa" Cikin sauri ya shiga
cikin gida. Ba a dade ba sai ga
yaron tare da masu gadin
gidansu mutum uku biyu buzaye
daya tsohon soja, hakanan kuma
da wani mutum dogo kakkaura
wankan tarwada sanye da
babbar riga amma kansa babu
hula, ko shakka babu shi ne ya yi
kama da mamalakin dankareren
gida.
Dogon mutumin dake tsaye, ya
dubi mutumin a tsorace, domin
ya tabbata kashinsa ya bushe a
tsammaninsa kamashi zasu yi a
matsayin barawo ko mahaukaci.
Tun kafin su karaso gurin
mutumin sai ya ji maigidan nan
na cewa sauran masu gadin.
"Wai wani mutum ne da matarsa
anan kofar gidan suke neman
taimakon abinci a gurin
Abdulmalik shi ne na fito da
kaina gara mu je mu gani ko
wane irin mutum ne, duniyar nan
yanzu ba abin yarda ba ce."
Dogon mutumin ya zube gaban
mai gidan ya gaida shi. Maigidan
ya dubi dogon mutumin ya ce.
"Malam kaine me neman
taimakon abinci?"
Mutumin ya gyada kai ya ce.
"Ni ne ranka ya dade, wallahi
zuwan mu kenan garin nan ni da
matata, ga ta can a bayan yunwa
ce ta kayar da ita ta kasa tafiya
kuma tana da ciki wata uku,
wannan shi ya takurani nake
neman wannan abinci kafin Allah
ya bani masauki, domin mu ba
mutanen wannan kasa ba ne
yaki ne ya koromu gudun hijira."
Kalamin dogon mutumin ya karya
zuciyar maigidan, nan da nan sai
ya ji tausayinsa ya kamashi,
musamman ma daya ji tare suke
da matarsa kuma tana da ciki
wata uku. Wannan shi ya fi tayar
masa da hankali. Domin yau
shekarunsa ashirin da yin aure,
tun daya auro matarsa Hajiya
Sa'adatu basu sami damar
haihuwa ba sai bayan shekaru
goma suka haifi Abdulmalik, tun
daga kansa kuwa basu kara
samun koda batan wata ba har
zuwa wannan lokaci.
"Yanzu ina matar taka take?"
Dogon mutumin ya nuna can
bayansa ya ce.
"Ga ta can yallabai" Mai gidan ya
dubi masu gadinsa guda uku ya
ce.
"Ku je dashi ku taho da matar, ku
sameni a tsakar gida." Sannan sai
ya kama hannun Abdulmalik suka
shige farfajiyar gidan
ma'abociyar shuke-shuken da
kamshin furanni.
Ba'a dade ba, masu gadin suka
shigo farfajiyar gida tare da.Ba'a dade ba, masu gadin suka
shigo farfajiyar gida tare da
dogon mutumin da kuma
matarsa Hindatu. Suna isowa sai
mutumin da matar tasa suka
zube gaban alhaji suka sake
gaidashi. Mai gidan ya dubi
tsohon sojan nan mai gadinsa ya
ce.
"A kaisu dakin nan na kusa da
injin bada wuta su kwana a ciki
yanzu zan sa a kawo musu
abinci ina son kuma a lura dasu
kaji ko?" Tsohon sojan ya rusuna
ya ce
"An gama alhaji" Sannan sai ya
dubi dogon mutumin da matarsa
ya ce.
"Ku biyoni mu tafi." Ramammun
mutanen guda biyu kyawawa
suka bishi a baya, gami da
godiya.
Mai gidan ya bisu da kallo cikin
tausayi yana tunanin abin da ya
kamata ya yi domin taimakonsu.
"Wallahi baba mutanen abin
tausayi ne dubi matarsa da kyar
take tafiya" Mutumin ya dubi
dansa Abdulmalik ya gyada kai,
bai ce komai ba.
Sidi mai Jaka ya yi shiru sannan
ya dubeni ya ce.
"Nas, ina fatan kana biye dani
akan wannan dogon zaren
labari" Na gyada kai cikin
kaguwa na ce.
"Ina biye da kai baba Sidi, sai dai
kuma ni wannan labarin duk
jinsa na ke yi kamar sabo daman
har yanzu ban ji alakarsa da
wannan ba"
Sidi Mai Jaka ya dubeni da
murmushi sannan ya dubi
kwanon tubanin dake gabansa
ya cafka daya ya jefa abakinsa ya
dube ni.
"Nas kenan, amma dai yanzu ai
ka isa ka baiwa wani labari,
sanin kanka ne in har na sako
sabon zaren labari to ko shakka
babu in Allah ya yarda sai na
hade shi da wancan na baya, shi
yasa ba ka gane alakarsu ba, to
amma ka jira sannu a hankali
lokacin da zaren labarin zai rikida
ya koma kan wancan su hade da
juna ba zama ka sani ba"
"Haka ne, ina to sauraronka" Sidi
Mai Jaka ya dada jefa tubani daya
a baki ya ce "Dadina da kai kenan
Nas, iya sauraron labari, ba ka
gajiya da saurare" Na fashe da
yar dariya. To ai labarin naka ne
wani sa'in dole ma a saurareka
domin sai kayi kamar kayi gabas
da mutum sai an jima can sai a
sameka a yamma" Baba Sidi ya
fashe da dariya sannan ya dube
ni ya ci gaba da cewa.
"Nas, tun daga wannan rana da
mai gidan ya sauki dogon
mutumin nan da matarsa basu
kara barin gidan ba, har sai da ta
Allah ta kasance a kansu." Na
dago kaina na dubi Sidi mai jaka
cikin sauri na ce dashi.
"Kada kace na tari numfashinka
baba Sidi, ina da tambaya."
Sidi mai jaka ya dubeni cikin
mamaki.
"Me kake son tambaya." Na
dubeshi na ce.
"Ni tun da ka fara bada sabon
zaren labarin, kake ta ambaton
wani dogon mutum, da kuma
mai gidan daya sauke su, gashi
dai ka siffanta su, kace sunan
matarsa Hindatu, sunan dan mai
gidan daya sauke su Abdulmalik,
to shi dogom mutumin da mai
gidan ya ya sunansu?" Baba Sidi
ya dan yi shiru na dan lokaci
sannan sai ya dubeni da
murmushi ya ce.
"Wani lokacin mutane kan bani
mamaki, wai idan kana basu
labari dole ne sai ka fadi sunan
mutunen," Sidi mai jaka ya danyi
shiru sannan sai ya ce.
"Sunan dogon mutumin
Saifullahi, mai gidan kuma Alhaji
Kabiru. Nas ina fatan ka gamsu."
Na gyada kai na ce "Eh, ci gaba"
Sidi mai jaka ya dora daga inda
ya tsaya.
Washegarin ranar da Alhaji Kabir
ya sauki bakin, tayi mutukar
faran tawa bakin rai, domin yasa
masu gadin gidansa sun
bincikesu daga karshe suka gane
cewa lallai da gaske yan gudun
hijira ne kuma ya ki ne ya koro
su. Dan haka sai Alhaji Kabiru ya
ce a ci gaba da basu abinci, daga
nan har zuwa ranar da matar
Saifullahi zata haihu. To amma
duk da haka sai da alhaji Kabir ya
gana da masu gadinsa a sirrance
ya ce suna fa kula da bakin nan,
domin mutum na yau ba abin
yarda bane domin sai ka dauko
mutum daga rana ka sashi a
inuwa, shi ko ya tura ka cikin
wuta
Sidi mai jaka ya dubeni cikin
mamaki
A haka Saifullahi da matarsa
Hindatu suka zauna cikin farin
ciki, a karshen watan da suka
sauka a gidan ne to wasu
sangartattun yan fashi suka
ziyarci gidan alhaji Kabir
A ranar da yan fashin suka zo tun
karfe hudu na yamma ake tafka
ruwan sama haka nan yan
fashin basu tashi zuwa ba sai
ana daf da fara sallar asuba
lokacin suka karaso ko shakka
babu sun rigaya sun gama sanin
abin da za su yi dan haka cikin
ruwan sanyi barayin su goma
sha tara kamar tururuwa suka
cafke masu gadin buzaye cikin
ruwan sanyi yayin da tsohon
sojan nan ya yi kokarin kawo
musu turjiya hakan shi yasa cikin
ruwan sanyi suka danne shi suka
yi masa yankan rago kai tsaye
kuma suka wuce inda Alhaji
Kabir yake shi da iyalinsa.
"A can bangaren hadiman gidan
Saifullahi ya ji idanunsa sun bude
ya farka daga nannauyan barci
sannan sai ya ji jikinsa ya fara
rawa babu gaira babu dalili cikin
sauri ya taba matarsa Hindatu.
.
Matar ta mike zaune cikin firigice,
ta dube shi a tsorace da yake har
yanzu razanar ya ki bata gama
saketa ba.
"Me...nene?" Saifullahi ya dubi
matarsa ya ce.
"Ji na yi haka kawai idanuna sun
bude, duk yadda aka yi wani
mugun abu ne ke shirin faruwa a
gidan nan." Ya dan yi shiru yana
saurare kamar zakara.
"Dauko min damarar layuna da
guraye na."
Cikin sauri na mamaki ga macen
dake da ciki wata uku da kuma
magagin barci jikinta, ta mike ta
nufi inda tsummokaransu suke
ta mika masa jakar gurayen. Cikin
yan mintuna Saifullahi ya daura
gurayen, sannan ya mike tsaye.
"Bari in je in gani." Hindatu ta
dubeshi da murmushin karfafa
gwiwa ta ce.
"To, Allah kiyaye bacin rana Allah
bada sa'a."
Saifullahi ya juya cikin sauri ya
fice daga dan dakin.
Hindatu ta bishi da kallo, ko kusa
ko alama bata fargabar komai,
domin ta yi imani da cewa in dai
ba karfin kaddarar karar kwana
ba, babu abin da zai sami
maigidanta, ta riga ta san sirrin
dake tattare da gurayen, ta ga
yadda suka ratsa ta tsakanin
sojojin yan adawa akan iyakar
kasarsu, suka tsallako ba a gansu
ba, ba a kuma samesu koda da
alburushin bindiga guda daya ba
duk kuwa da irin barin wutar da
ake yi.
Saifullahi ya matsa wata katuwar
laya mai kamar makami da ke
kwibinsa na hannun dama.
Sannan ya nufi cikin gidan, ya
tabbata a lokacin in ba Allah ba,
ko ifiritu bai isa ya ganshi ba.
Saifullahi ya hangi barayin daya
bayan daya har su goma sha tara
sun mammakale a loko-loko
guda biyar daga cikinsu tsaye a
kofar babban dakin shakatawar
gidam. Saifullahi ya zaro wani
bakin guru daga kugunsa wani
dogo mai kamar maciji ya zagaya
barayin dashi har sau biyu, nan
da nan barayin suka sankare a
gurin basa ko motsi kamar
itatuwa. Saifullahi ya barsu a
gurin, sannan ya ringa bin
barayin daya bayan daya yana
zagaya su da gurun ba tare da
sun ganshi ba har sai da ya
kamar dasu baki daya, sannan
sai ya nufi kofar falon, ya zagaye
barayin ya kwankwasa kofar
dakin shakatawar a hankali.
Shiru-shiru bai ji motsin komai
ba, Saifullahi ya dada kwankwasa
kofar da karfi, har sau goma.
Tswon lokaci, sai ya ji kamar
motsi an nufo kofar a hankali
kamar a tsorace.
"Alhaji ni ne...Sanifullah i."
Saifullahi ya ce cikin tattausar
muruya.
"Saifullahi...l afiya ina masu
gadin?" Saifullahi ya tausasa
murya ya ce.
"Yan fashi ne suka kama su, sun
kuma kashe tsohon soja." Alhaji
Kabir ya rike numfashi a tsorace.
"Yanzu ina barayin?" Ya tambaya
a tsorace.
"Gasu anan waje duk na kama
maka su."
"Kai kadai Saifullah?"
"Kwarai kuwa ai ikon Allah ya fi
da haka."
Tsawon lokaci, bai fito ba, can sai
ya leko a hankali a tsorace
sannan sai ya ja da baya saboda
mutanen da ya gani guda biyar
duk a sankare kamar itatuwa.
"Kada ka ji tsoro Alhaji, kana iya
fitowa, babu abin da zasu iya har
sai idan na ga dama da ikon
Allah, sannan zasu yi motsi."
Alhaji Kabir ya dubi Saifullahi
cikin kaduwa.
"Jirani to ina zuwa, bari na
bugawa yan sanda waya."
Mintuna goma bayan haka gidan
ya cika da jami'an tsoro. An kame
barayin gaba dayansu, tun daga
wannan rana sai Saifullahi ya
sami cikakken yanci, Alhaji Kabir
ya gama yarda dashi, ya kuma
bashi shugabancin masu gadin
gidansa.
Sannu a hankali watanni suka
shude, har cikin Hindatu matar
Saifullahi ya isa haihuwa, ran nan
da safe sai ta fara nakuda, Alhaji
Kabir da kansa ya bada mota a
kaita asibiti. Kusan sa'o'i biyu
suna jiran labarin haihuwa, a
cikin masu jiran akwai Alhaji
Kabir, matarsa Hajiya Sa'adatu,
Abdulmalik da kuma Saifullahi.
A cikin wannan sa'ar ne
abubuwa biyu suka faru, farin
ciki da bakin ciki, domin Hindatu
ta haifi wata kyakkyawar
budurwa, mai kyawu na ban
mamaki, ita kuwa Hindatu Allah
ya yi mata cikawa.
Tun daga wannan rana Saifullahi
bai sake samun lafiya ba. A ranar
da za a radawa jaririyar suna,
jikin mahaifinta Saifullahi ya
matsa, tun da sassafe ya sa masu
gadi suka roki Alhaji da ya zo
yana son ganawa da shi domin
ba zai iya zuwa da kansa ba.
Alhaji kabir ya zo dakin mai
gadin cikin gaggawa, Saifullahi
ya dago kansa da kyar ya dubeshi ya ce bakinsa na rawa "Alhaji, jikina ya tsananta min,
haka nan kuma bana jin zan
warke daga wannan rashin lafiya
tawa."
Alhaji Kabir ya matsa kusa da
mutumin cikin tausayawa ya ce.
"Ka da ka ce haka Saifullahi, ai ita
cuta ba mutuwa ba ce" Saifullahi
ya girgiza kai ya ce.
"Ba zan rayu ba Alhaji, domin na
ji a jikina, Shi yasa na kiraka
domin na baka abu daya da na
mallaka a duniya wanda da shi
ne kadai zan iya saka maka abin
da ka yi min a duniya" Ya dan yi
shiru yana mayar da numfashi.
"Alhaji a duniya bani da wanda
ya fi ka, na dauke ka a matsayin
dan uwa, amini, ka mutunta ni,
ka taimakeni a lokacin da nake
matukar bukatar taimako"
Saifullahi ya tura hannunsa cikin
wasu tsummokara dake gefensa
ya dauko wata tsohuwar jaka ta
bakin yadi ya mikawa Alhaji
Kabir.
"Wannan shi ne kyautar da zan yi
maka ta musamman, guru ne, da
layu guda uku. Sirri ne na tsarin
kai da mahassada, da su ne Allah
ya taimakeni na kama barayin
nan" Ya dan yi shiru sannan ya ci
gaba.
"Ga Yata nan jaririya, na baka ita,
ka taimake ni dan Allah ka rike
min ita, idan an jima in za a sa
mata suna, ka sa mata suna Nana
firdausi, domin sunan mahaifiya
ta ne" Ya fara tari, sannan sai ya
yi karfin hali ya dago ya dubi
Alhaji Kabir idanunsa na zubar da
kwalla.
"Alhaji wannan ita ce alfarmar da
nake nema, za ka yi min..?" Cikin
sauri Alhaji Kabir ya amsa masa.
"Na amince Saifullahi, in Allah ya
yarda zan rike ta kamar yar da na
haifa a cikina kuma ina fatan ma
Allah ya baka lafiya"
Washe gari da aka yi sunan
Firdausi mahaifinta Saifullahi ya
bar duniya, a lokacin kwananta
takwas kawai a duniya.
Bayan an binne Saifullahi, sai
Hajiya Sa'adaru ta fito dauke da
kyakkyawar jaririyar ta sami
maigidanta zaune a falo shi da
dansa Abdulmalik, ta zauna kusa
da maigidanta, sannan ta kurawa
jaririyar idanu ta ce.
"Oh, Allah mai yadda ya so, Allah
gwanin iya halitta, ka dubi
wannan kyakkyawar halitta, kai
wallahi Alhaji ina bala'in son
jaririyar nan, ba don komai ba.
Sai don irin maraicinta, da kuma
kasancewar sunan mahaifiyata
ne nima aka sa mata"
Alhaji Kabir ya dubi matarsa ya
ce.
"Ki riketa da kyau cikin aminci da
kulawa kamar yadda za ki rike
danki Abdulmalik." Hajiya
Sa'adatu ta rungume jaririyar ta
dubi maigidanta, sannan sai ta
dubi kyakkyawar fuskar jaririyar
ta ce.
"Daga yau kin zama yata, Allah ya
raya ki UMMI na"
Tun daga wannan rana ne sunan
Ummi ya bi wannan jaririya.
Sidi mai jaka ya juyo da
murmushi ya dubeni.
Ni kuma na dubeshi cikin bazata.
"Baba Sidi, kana nufin ka ce min
wannan jaririyar ita ce Ummi din
da Anas ya kamu da ciwon
Kauna?" Sidi Mai Jaka ya fashe da
dariya ya ce.
"Nas kenan, ai daman sai da na
fada ma sai na baka mamaki,
sannu a hankali zan dawo da kai
na jone ma bakin zaren labarin,
gashi kuwa tun ma kafin na jone
shi din har ka fara ganin alakarsu
da wancen tsohon zaren labarin
da muka saka" Na dubi Sidi mai
jaka cikin kaduwa.
"Wai Baba Sidi kana nufin ka ce
ita wannan kyakkyawar Ummi
din iyayenta ba ma wata tsiya ba
ce a garin nan" Sidi mai jaka ya
gyada kai ya ce.
"Kwarai kuwa Nas, dan ma ka
tari numfashina, domin har
yanzu zaren labarin bai kare ba,
bari in gama saka ma shi, idan na
gama zaka fahimci rudanin dake
cikin wannan labari" Na gyara
zama na dubi Sidi mai jaka cikin
doki na ce "Ci gaba, ina saurare"
Sidi mai jaka ya jefa tubani daya
a baki ya ci gaba.****
Sannu a hankali Nas Ummi ta
fara girma kullum ta Allah
kyawunta karuwa yake yi. Ba
mutumin dake ganinta a waje ba
lokaci-lokaci hatta Alhaji Kabir da
matarsa Sa'adatu dake ganinta
kullum suna mamakin kyawu irin
na Ummi
Wani abin ban mamaki shi ne
tun ranar da aka haifi Ummi
kullum a hannun Abdulmalik take
wuni yana yi mata wasa. Gashi
dai shi ba mace ba amma kullum
yana makale da jaririyar dan
haka har sa'ar da Ummi ta kai
shekaru goma a duniya, duk inda
zasu tare suke da Abdulmalik a
lokacin nan shi yana da shekaru
ashirin a duniya Amma duk da
haka kusan tsayin sa daya da
Ummi
Wani sa'in sai Abdulmalik ya
dauki Ummi a mota su yi ta yawo
kantuna-kantuna inda ake sayar
da kayan lashe-lashe da
makulashe idan sun je sai
Abdulmalik ya juyo ya kalli Ummi
cikin fara'a a tausashe ya ce
"Ummi, dauki duk abin da ki ke
so" Cikin farin ciki da kauna irin
ta dan uwa sai ta dubeshi ta ce
"Abdulmalik kana shagwaba ni!"
A duk lokacin da ta ce haka sai
Abdulmalik ya ji zuciyarsa ta dada
narkewa da begenta domin tun
ranar da aka haifi Ummi
Abdulmalik ya fara sonta tun ma
bai san mene ne kauna ba. Don
haka sannu a hankali shekaru na
shudewa har wannan son ya
juye zuwa kauna. To sai dai
kuma abin da Abdulmalik ya kasa
fahimta shi ne a duk tsawon
zamanin nan Ummi a matsayin
dan uwanta na jini ta daukeshi
domin bata taba sanin cewa ba
uwarsu daya ba ubansu daya ba.
Abdulmalik ya riga ya fi kowa
sanin cewa Ummi ba yar uwarsa
ba ce ta jini Domin shi ne ma ya
yi sanadiyyar haihuwarta a
gidan, to amma daidai da rana
daya bai taba nuna mata alamu
ba
A bangaren iyayen Abdulmalik
kuwa sun dade suna kallon irin
alakar mai karfi dake kulluwa
tsakanin yaran guda biyu, koda
yake ga zuciyar Alhaji Kabir bai
taba daukar alakar yaran a bakin
komai ba face kawai sabo da
kuma yan uwantaka.
.
To amma ranar wata laraba da
yamma sai matarsa Sa'adatu ta
dubeshi ta ce.
"Alhaji, wai kuwa kana lura da
al'amarin yaran nan?" Maigidanta
Kabir ya dubeta cikin mamaki.
"Kamar ya ya ina lura dasu?
Wannan ai dole ne domin kuwa
yayana ne." Sa'adatu ta dubeshi
cikin yar damuwa ta ce.
"Ba abin da nake nufi kenan ba."
"To me ki ke nufi?" Sa'adatu ta
gyara zama ta ce.
"Wato ni gani na ke yi kamar
Abdulmalik kaunarta ya ke yi."
Alhaji Kabir ya dubeta baki bude
cikin mamaki ya ce.
"Yau ga ikon Allah, to daman
mutum ba dole ne ya kaunaci
dan uwansa ba." Sa'adatu ta
girgiza kai.
"Abin ya wuce da haka ina
tsammanin begenta ya ke yi."
Alhaji Kabir ya kura wa matarsa
idanu na tsawon lokaci, sannan
sai ya yi kasa-kasa da murya ya
ce.
"Kada fa ki manta cewa, har
yanzun nan Ummi ba ta san
cewa ba mune iyayenta ba."
Sa'adatu ta yi murmushi.
"Idan ita ba ta sani ba, ai shi
Abdulmalik ya san ba yar uwarsa
ba ce ta jini. Kuma abin da ya sa
ka ji na fada ma haka shi ne,
yanzu da ka leka cikin dakinsa za
ka ga duk ya zagaye shi da
hotunan Ummi, kowannensu ya
rubuta (My love)
Alhaji Kabir ya
dada duban matarsa na tsawon
lokaci, akwai alamun tunani a
fuskarsa, can sai ya yi ajiyar
zuciya ya ce.
"To, sai mu bar wa Allah komai,
ya yi ikonsa, Allah zaba musu
abin da ya fi alkairi."
0 comments:
Post a Comment