A bangaren Abdulmalik, sannu a
hankali har Ummi ta kai shekaru
goma sha bakwai. Kullum wutar
begenta sai dada ruruwa cikin
zuciyarsa take yi, ita ko in ka
dauke soyayya irin ta yan
uwantaka bata dauke shi a bakin
komai ba. Amma duk da haka
nan dai kullum suna tare basa
rabuwa.
Wata rana da yamma Ummi ta
shiga dakin Abdulmalik ta ci
kwalliya, fes,fes, hakan shi ya sa
zuciyar Abdulmalik harbawa. A
ranar ne to Abdulmalik ya ji
kamar ya amayar mata da
boyayyen sirrin zuciyarsa, to
amma sai ya tuna kashedin da
mahaifinsa ya yiwa duk wani
mutum dake gidan inda yake
cewa.
"Kada wani daga cikinku ya sake
ko da da wasa ya fadawa Ummi
cewa mu ba iyayenta ba ne."
Wannan shi ya sa Abdulmalik
hadiye maitarsa.
Zuciyarsa na harbawa ya dago
kai ya dubeta cikin yabawa da
abin da ya gani ya ce.
"Kai, amma fa kin kara kyau
Ummi." Ummi ta dube shi cikin
dariya ta ce "Na gode yaya
Abdul." Ta dan yi shiru tana
kallon jeren hotunanta ko ina a
cikin dakin sannan ta dubi
Abdulmalik ta ce.
"Duk duniya babu yan uwan
dake kaunar juna kamar mu,
dubi fa Yaya Abdulmalik duk ka
bi ka wani shagwaba hotunana
kamar wata budurwarka.
Wannan ko budurwa ce ai ba
karamin kaunarta kake yi ba."
Abdulmalik ya sunkuyar da kai da
dan murmushi, wata zuciya na
cewa da shi, fada mata kawai
cewa ita fa ba yar uwarka ba ce
ta jini. To amma sai gargadin
mahaifinsa ya sake dawowa
zuciyarsa dan haka sai ya dago
kai ya dubi Ummi da Murmushi
ya ce.
"Ummi kenan. Ina za ki ne na ga
kin caba kwalliya haka?" Ummi ta
dube shi da murmushi sannan ta
ce.
"Ina zani, ko dai ina zamu, bikin
taya murnar ranar haihuwar
wata kawata zaka rakani."
Abdulmalik ya dubeta cikin
mamaki ya ce.
"Kin manta ne cewa ina da
jarrabawa ta karshe a
makaranta, kin san ina bukatar
karatu."
Ummi ta yi sauri ta rufe fuska
cikin dariya.
"Oh! Dan Allah Yaya Abdulmalik
ka yi hakuri, wallahi mantawa na
yi ashe kana da jarrabawa gobe."
Abdulmalik ya mike tsaye.
"Mu je na raka ki sai na dawo."
Ummi ta mike tsaye ta dube shi
ta ce.
"Wallahi nima dan muna bala'in
mutunci ne da MABRUKA da ba
zan je ba tun da kaima ba za ka
ba." Abdulmalik ya yi murmushi.
"Ai ba komai. Yaushe zaki
dawo?" Ummi ta lumshe idanu ta
dan daga kai sama. Abdulmalik
ya kurawa wasu siraran zane
guda uku da suka yiwa
kyakkyawan wuyanta kawanya.
"Nan da karfe tara na dare zamu
dawo."***
.
Sidi Mai Jaka ya dubeni ya ce ina
fatan kana fuskantar inda labarin
ya dosa da kyau? Na gyada kai
cikin sauri.
"Ina fuskanta." Sidi Mai Jaka ya ci
gaba.
A daren ranar da Ummi ta dawo
daga walimar bikin zagayowar
haihuwar Mabaruka ne to
Abdulmalik ya fara ganin canjin
yanayin karara a fuskar Ummi
Karfe tara na dare da yan
mintuna ta dawo, Abdulmalik ya
ji shigowarta babban falo dan
haka sai ya ji wani farin ciki ya
lullubeshi domin tuntuni ya
matsu da ya ga ta dawo domin
baya iya yin sama da sa'a biyar
bai ganta ba Wani sa'in ko a
makaranta yake sai ya yi ta bugo
mata waya duk bayan sa'a guda
dan kawai ya ji muryarta Don
haka sa'ar da ya ji motsin
dawowar Ummi sai ya ajiye
takardun bokon da yake
karantawa ya lumshe idanu yana
jiran shigowarta domin ya san
alkawari ne sai ta shigo dakin.
Tsawon lokaci shiru babu motsin
UmmiDomin ya san
alkawari ne sai ta shigo dakin.
Tsawon lokaci shiru, babu
motsin Ummi sannu a hankali
har mintuna talatin suka shude
bata shigo dakin ba. Abdulmalik
ya mike tsaye cikin tsananin
damuwa da mamaki domin a iya
saninsa da Ummi ko kayan
jikinta ba zata sauya ba sai ta zo
gare shi su yiwa juna Sallama
Cikin sauri Abdulmalik ya fita
daga dakinsa ya ratsa ta falo ya
nufi dakin Ummi. Abdulmalik ya
dan kwankwasa kofar dakin a
tausashe sannan sai ya yi sallama
ya shiga.
Ummi na kwance akan gado,
sanye da kayan da ta fita da su
walimar, ko cire su bata yi ba, ta
kurawa saman dakin idanu bata
ko kiftawa kamar mai kallon allon
sinima. Abdulmalik ya tsaya cak a
tsakiyar dakin kamar an dasa shi,
ya kurawa Ummi idanu cikin
tsananin mamaki da kaduwa
domin ya fahimci ashe Ummi
bata san ma ya shigo dakin ba.
"Ummi..." Ya sake maimaitawa a
karo na biyu kamar mai biya
karatu. Ummi ta juyo firgigit ta
tashi zaune akan gadon. Ta dubi
Abdulmalik.
"Tunanin me ki ke yi haka?"
Ummi ta dubeshi da murmushi.
"Ka yi hakuri don Allah
Abdulmalik wallahi ban san ka
shigo ba." Abdulmalik ya matsa
kusa da ita ya zauna daga can
nesa da ita a bakin gadon ya
kura mata idanu.
"Na ji shigowarki, ina ta jira ko za
ki zo, ba ki zo ba shi ne na ce
bari ni nazo da kaina na gani ko
lafiya." Ummi ta sunkuyar da kai
sannan ta yi ajiyar zuciya kana ta
dago kai da murmushi ta dubi
Abdulmalik ta ce.
"Lafiya lau Yaya Abdulmalik
bala'in gajiya na yi." Tun kafin ta
gama fada Abdulmalik ya san
karya take yi, domin alamun
damuwar dake fusakarta tamkar
bakin rubutu ne akan farar
takarda. Abdulmalik ya ji
zuciyarsa ta sosu, bai ji dadin
abin da ta fada ba, domi a duk
iya tsayin zamani, tun ranar da
aka haifeta ya fara daukarta, har
zuwa yau bata taba fada masa
karya ba sai yanzu.
Abdulmalik ya dubi Ummi cikin
shakka, ya girgiza kai ya ce.
"Kada ki ce haka Ummi, ba gajiya
ba ce kawai ke damunki akwai
matsala ta daban." Ummi ta
dubeshi da wani fatalwan
murmushi akwai alamun kunya a
fuskarta ta ce.
"Gaskiya ne Abdulmalik wallahi
akwai abin dake damuna, ka
kuma yafe min dan Allah ka san
ban taba yi ma karya ba sai yau..."
Ta dan yi shiru tana murmushi
sannan sai ta dada da cewa.
"Yau din ma kunya ce wallahi ta
sa ni yin karya." Abdulmalik ya yi
ajiyar zuciya kana ya dubeta cikin
shauki ya ce.
"Na yafe miki Ummi...ai kin san
duk laifukanki a gurina yafaffune
har ma da wanda ba ki yi ba."
Ummi ta yi dariya ta sake
sunkuyar da kai Abdulmalik ya
sake nazarin fuskar Ummi cikin
damuwa ya ce.
"Fada min sirrin dake zuciyar ki
Ummi me ke damun ki ne?"
Ummi ta dauke kai gefe guda na
tsawon lokaci, haka nan a duk
iya tsayin wannan lokaci akwai
alamun murmushi-murmus hi
da
kuma damuwa-damuwa a
fuskarta. Shi dai Abdulmalik ya
kura mata idanu cikin mamaki
bai tari numfashinta ba. Tsawon
lokaci, sannan Ummi ta juya ta
dubeshui, ta ce bakinta na rawa.
"Yaya.....Abdul malik...wallahi
irin
abin da nake yawan karantawa
ne a cikin littattafan labarai na
Hausa ya faru a kaina."
Abdulmalik ya ji gabansa ya fadi
ras! Ya dubi Ummi.
"Me ki ke nufi." Ummi ta dauke
kai gefe guda a kunyace ba tare
da ta hada idanu da shi ba ta ce.
"Wallahi...wani na gani a gurin
liyafar nan naga ya burge ni."
Abdulmalik ya ji zuciyarsa ta
harba.
"Har yanzu ban fahimce ki ba
Ummi, waye wani, kuma ya
burge ki kamar ya ya." Ummi ta
sake dariya ta ce.
"Yaya Abdulmalik ji na yi wallahi
ina masifar kaunarsa a zuciyata,
a yanzu din nan haka ji nake yi
kamar mun dade da sanin juna."
Ta dan yi shiru ganin Abdulmalik
bai ce wani abu ba sai ta dada da
cewa
"Za ka yi mamaki idan na ce da
kai Mabaruka ce kawai ta turani
na yi kiransa." Abdulmalik ya
dago kai ya dubeta da
murmushin karfin hali, amma a
badini tuni har zazzabi ya rufe
shi
"Ummi kenan. To yanzu ya ya za
ki yi kenan? Kin ga mutum kin ce
kina sonshi amma ba ki san ko
wane ne shi ba ba ki san inda
yake ba baki san ko da sunan shi
ba." Ummi ta matso kusa da
Abdulmalik ta ce
"Ma'aikacin otal din da aka yi
liyafar ne, na ji Mabaruka ta kira
shi da suna ANAS!" Abdulmalik ya
sunkuyar da kai Ummi ta
dubeshi cikin damuwa. A
tunaninta halin da ta tsinci kanta
ciki ne ke damun Abdulmalik
domin ta san irin yadda yayan
nata Abdulmalik ke matukar
sonta don haka sai ta ce dashi a
tausashe
"Ka da ka dami kanka Yaya
Abdulmalik na san duk abin da
ya shafe ni kai ya shafa. Ni dai
abin da nake so shi ne ka tayani
don Allah mu same shi ka ga
kaunarsa" Ta dan yi shiru
sannan sai ta dubi Abdulmalik ta
ce
"Kana jin kuwa zai iya
kaunata?"***
Sidi mai jaka ya yi shiru kana ya
dubeni da murmushi sannan ya
dubi tubanin Tubanin dake
gabansa cikin damuwa domin
tuni ya hadiye sama da kashi uku
bisa hudun tubanin
A zuciya ta na ce kai wannan
tsoho da cin
tsiya yake domin na tabbata
yawan tubanin da ya hadiya tun
daga rana zuwa yanzu ya ishi
katti goma su ci su koshi amma
sai gashi shi kadai duk ya
hadidiye su kamar rumbu
"To Nas ka ga abin da nake fada
maka tun farko ko? Sai da na ce
da kai ni ne mai saka labari
kamar injin saka, na hade ma shi
guri guda, gashi kuwa sannu a
hankali na nuna maka alakar
zarurrukan labarin guda biyu."
"Haka ne Baba Sidi." Na ce dashi
Sidi mai jaka ya canko wani
katon tubani mai kama da
dankali ya gutsiri rabi, sauran ya
fado a cikin kwanon
Sidi mai jaka ya dubeni ya ce.
"Nas, wannan shi ne karshen
wannan dogon zaren labarin,
yanzu abin da ya rage shi ne na
gaggauta na daura ma bakin
zarurrukan labaran guda biyu
kafin nan da sallar magariba,
domin bana son labarin ya kai
mu har bayan sallar magariba."
Na yi sauri na gyada kai na ce.
"Ni ma ai na fi son haka." Sidi mai
jaka ya gyada kai ya ce.
"To Nas, bari yanzu ne zan koma
kan wancan tsohon zaren labarin
da muka bari lokacin da zamu
tafi sallar azuhur, inda mauka
baro Anas yana karatun wasikar
da Ummi ta bashi." Ya dubeni ido
da ido.
"Ka tuna da gurin?" Na gyada kai
na ce.
"Kwarai kuwa, ba inda ka ce har
ma yana jiyo kukan matarsa
Mabaruka ba daga cikin
bandakin?" Sidi Mai jaka ya fashe
da dariya yace.
"Nas kenan, da ace yadda kake
rike labari a kwakwalwarka haka
nan kake rike karatu da ba
karamin malami za a yi ba wata
rana, to sai dai kuma na fahimci
kamar kwakwalwarka ta fi iya
rike labari fiye da komai." Nima
sai na fashe da dariya, na ce.
"Baba Sidi kena." Sidi mai jaka ya
yi gyaran murya sannan ya ce.
"Nas, dauki zuciyarka cancakat ka
mayar da ita cikin bandakin nan,
inda muka baro Anas dazu yana
karatun wasikar da Ummi ta
bashi."
"Na mayar." Na ce dashi.
Yauwa Nas. Anas ya ci gaba da
juya takardar a hannunsa,
zuciyarsa dauke da abubuwa
guda uku masu kama da kishiyar
juna. Ka ga na farko dai akwai
farin ciki, domin Anas bai san
abin da zai iya kwatanta farin
cikinsa da kalmar Ummi ba, inda
tana kaunarsa da kanta. Na biyu
akwai tsana mai tsanani cikin
zuciyarsa, domin a yanzu duk
duniya babu abin da ya tsana
kamar matarsa Mabaruka. Domin
tuni Anas ya riga ya san wannan
mummunar gurguwa ita kadai ce
katangar karfen dake tsakaninsa
da babbar masoyiyarsa Ummi.
Abu na uku kuwa dake dafe a
zuciyar Anas shi ne tsananin
fargaba, don Anas ya tabbata sai
dai ya zabi tsakanin mummunan
aski da sa kai a wuta, domin
muddin ya ci gaba da mu'amula
da Ummi, rabuwarsa da
Mabaruka ta zo kenan, shi ko ya
san a yanzu koma me yiwuwa
har abada Mabaruka ita ce
babbar rumfar da ta rufe kansa
da inuwa ta yi masa katanga da
zafin ranar talauci.
Wadannan abubuwa guda uku
su suka hadu suka cunkushe
zuciyar Anas, don haka yana nan
bandakin yana maimaita karatun
wasikar Ummi har sai da ya
karanta ta sau kusan talatin. Bai
tashi komawa dakin kwanan su
ba sai da ya tabbata a lokacin
Mabaruka ta gama fushinta ta yi
barci.
Anas ya nufi dakin kwanansu
cikin sanda, a lokacin kusan biyu
da rabi ne na dare. Ko kusa ko
alama baya son ya sami
Mabaruka ido biyu bata yi barci
ba, domin Anas ya gama gajiya
da ita, kai hatta muryarta baya
son ji. Murya daya ce kawai ke
yawo cikin kwakwalwarsa
muryar Ummi.
Anas ya yi boyayyiyar ajiyar
zuciya sa'ar da ya tura dakin
kwanan nasu ya shiga. Domin ya
ga a cikin duhu yake. Tabbas ta yi
barci, Anas ya ce cikin zuciyarsa
Sannu a hankali ya sauya kayan
dake jikinsa sannan ya lallaba ya
haye bisa gadon ba tare da ya yi
wani kwakkwaran motsi ba ya
kwanta haka nan bai ma yarda
koda jikinsa ya taba jikinta ba
Anas ya yi lamo kamar ya mutu
gashi dai baya ko motsi amma
idanunsa a bude yake garau
Zuciyarsa dauke da hoton
kyakkyawar surar Ummi Yana
nan kwance zuciyarsa fari fat
lokaci guda kuma yana tunanin
hanyar da zai bi a gobe ya
gujewa Mabaruka domin ya sami
damar ganawa da Ummi Anas
na nan cikin wannan haki can
sai ya ji agogo ya buga karfe
daya sannan ne fa ya ji abin da
yasa gashin jikinsa mimmikewa
tsaye
"Anas." Muryar Mabaruka ta ratsa
duhun dake dakin ta daki dodon
kunnensa. Anas ya zabura cikin
kaduwa Bai taba tsammanin
Mabaruka ba barci take yi ba.
"Mab...Mabaruka ...dama ba barci
ki ke yi ba." Mabaruka ta yi ajiyar
zuciya ta ce a sanyaye cikin
karayar zuciya.
"Ya zan iya barci Anas bayan
kana fushi dani." Hakan kawai da
ta ce sai Anas ya ji dan tausayinta
ya kamashi.Ya zan iya barci Anas, bayan
kana fushi dani." Hakan kawai da
ta ce sai Anas ya ji dan tausayinta
ya kamashi. Don haka sai ya yi
karfin hali ya ce.
"Ki yi hakuri Mabaruka...wann
an
duk wani al'amari ne na rudin
shaidan." Ga mamakin Anas sai
ya ji Mabaruka ta yi wani irin
nannauyan ajiyar zuciya, sannan
sai ta juyo shi ta rungume shi ta
kankameshi ta ce.
"Ka yafe min Anas, ka kuma
manta da duk abubuwan da na
fada ma na bakaken maganganu,
wallahi masifar kaunarka da
kishinka ne suka sani..." Ta yi
shiru tana numfashi sama-sama
daga nan bata kara cewa komai
ba, a haka barci ya dauke ta
hannayenta kankame da jikin
Anas babban masoyinta a duniya.
Shi ko Anas, yadda ya ga rana
haka ya ga dare bai runtsa ba. Ga
dai Mabaruka rungume da shi
cikin shaukin bege, amma shi ji
yake yi kamar a rungume yake da
kaya.
Washe gari da safe suna karin
kumallo sai Anas ya fuskanci duk
da yake dai ba cikin fushi
Mabaruka ta tashi ba amma babu
alamar walwala sosai a fuskarta
haka nan da kyar ta kai abinci
sau biyu bakinta.
Ka bi ta a hankali dan samari
wannan gurguwa ita ce babbar
inuwar rayuwar ka
Wata zuciya ce ke baiwa Anas
Shawara
Wata zuciya ce ke baiwa Anas
shawara. Anas, ya mike tsam
daga inda ya ke ya koma kusa da
Mabaruka ya zauna, sannan ya
dauki yan siraran hannayenta ya
rikesu a tausashe ya sa alamun
damuwa na karya a fuskarsa,
sannan sai ya matsa da bakinsa
kusa da kunnen ta ya ce.
"Mabaruka...me ke damunki ne,
na ga duk kamar ba kya cikin
walwala, ko har yanzu fushin ki
ke yi dani? Ba na nemi afuwar ki
yafe min ba?" Mabaruka ta
langabe kai duk da yake dai bata
yi masa murmushi ba, to amma
fuskarta ta nuna alamun jin
dadin tarairayar da ya yi mata.
"Anas, wallahi zuciyata ce ke cikin
fargaba." Anas ya dubeta cikin
mamaki, sannan ya matse
hannayenta a cikin nasa ya ce.
"Fargabar me kuma, Mabaruka?
Kina da kudi da duk wani jin
dadin duniya da ki kebukata, tun
da dai Allah ya hore miki dukiya,
haka nan kuma kina da ni, ga ni
kusa da ke, to mene ne kuma na
fargaba?" Mabaruka ta dago
kanta ta dubi Anas cikin mamaki
ta ce a sanyaye.
"Ina da kai fa ka ce?" Anas ya
gyada kai ya ce. "Kwarai kuwa
kina da ni, ni ba mijinki ba ne?"
Mabaruka ta dan lumshe idanu
sannan sai ta bude su ta dubi
Anas.
"Ka ga ni kuwa fargabar da nake
yi gani nake yi kamar kwace min
kai za a yi, rabuwarmu ta zo." A
wannan dan takin lokacin da
take kalamin sai Anas ya ji
tausayinta ya sake kama shi a
karo na biyu. Tabbas ya san
batunta gaskiya ne, domin tuni
ma in dai batun soyayya ne an
riga an raba su, abinda ya rage
tsakaninsa da ita a yanzu shi ne
auren kaddara.
"Ka da ki ce haka Mabaruka, bai
kamata ba irin wadannan
kalamai marasa dadi suna fitowa
daga bakin ki." Anas ya dauke kai
gefe guda fuskarsa cikin
damuwa. Da ace za ka ga
fusakarsa a lokacin, mutum sai ya
rantse da Allah cewa abin da
yake fada har zuciyarsa haka nan
yake.
Mabaruka ta yi wata kwakkwarar
ajiyar zuciya ta dubi Anas.
"Ba ni lemo na sha." Anas ya mike
cikin sauri ya tsiyayo mata
tacaccan lemo cikin kofin
alfarma sannan ya zauna kusa
da ita kana ya dan janyota jikinsa
ya kara mata kofin a bakinta
Cikin farin ciki mara misaltuwa
Mabaruka ta fara shan lemon
kadan-kadan har sai da ta
shanye gaba daya. Abin ya baiwa
Anas mamaki domin bai taba
ganin ta yi haka ba. Amma ga
Mabaruka hakan da ta yi akwai
dalili mai karfi dalilin kuwa shi ne
rabon da Anas ya yi mata irin
wannan tarairaya tun daren
amarcinsu na farko
"Lemon ya ishe ki ko na karo
miki?" Anas ya tambayi Mabaruka
a tausashe Mabaruka ta dubeshi
da murmushi a karo na farko ta
girgiza kai
"Ya ishe ni." Ta dan yi shiru
sannan sai ta ce
"Ina ma ace kullum haka muke
da na fi kowa farin ciki a duniya"
Anas ya sunkuyar da kai gami da
murmushin yake shi kansa
kunyar hada ido yake yi da ita
domin a zuciyarsa cewa yake yi
ina ma wannan tarairayar da
yake yiwa Mabaruka ace Ummi
ce
Abin da Mabaruka ba ta sani ba
shi ne duk wannan tarairaya da
Anas ke yi mata kokari yake yi ya
sami hanyar da zai bi ya sulle ya
ziyarci Ummi
"Daga yanzu zan manne ma
kamar cingam duk inda za ni
muna tare." Kalaman Mabaruka
suka fado zuciyarsa Anas ya ji
gumi ya fara tsiyaya ta bayansa
duk kuwa da cwa wayewar gari
kenan kuma koda ma babu
sanyin iskar safiya akwai na
na'urar sanyaya daki.
"Tunanin me ka ke yi Anas?"
Mabaruka ta tambayeshi babu
zato babu tsammani ashe duk
abin da yake yi tana lura da
fuskarsa
Adaida lokacin ne to
wata dankareriyar karya ta darsu
a zuciyar Anas ya riga ya san ita
ce damar sa ta karshe ta samun
damar zuwa gurin Ummi dan
haka sai ya dubi Mabaruka ya ce
a tausashe.
"Kin san ina da abokai a cikin
gari da yawa wadanda rabon da
mu gana dasu tun kafin na
aureki shi yasa ki ka ga na shiga
cikin damuwa saboda ina
fargabar kada su ga kamar dan
na sami canjin rayuwa ne shi
yasa na watsar da su." Mabaruka
ta dan yi shiru na lokaci tana
kallon kofin da ke gabanta.
Zuciyar Anas ta fara harbawa da
karfi, yana jiran ya ji abin da za ta
ce, ya san idan ta ki amincewa
bashi da damar ganin Ummi,
haka nan kuma idan tare zasu
fita nan ma bashi da damar zuwa
gurin Ummi kenan.
Tsawon lokaci, sannan Mabaruka
ta dubeshi a tausashe ta ce cikin
murmushi.
"Kuma ka ki ka sanar dani tun
dadewa ko tsorona ka ke ji?" Ta
dan fashe da dariya. Jin haka shi
ya sa Anas ya washe baki har
kunne, zuciyarsa kamar ta fasa
kirjinsa saboda doki. Anas ya
dada rungumo Mabaruka.
"Ya ya zan ji tsoron matata?"
Wannan abu da ya fada shi ya
kara narkar wa da Mabaruka
zuciya, cikin sauri ta dubi Anas.
"Yaushe za ka je ku gaggaisa da
abokan naka?" Anas ya yi sauri
har zai ce yau, sai wata zuciya ta
ce dashi bi a hankali Anas,
wannan nannadaddiyar matar ta
fi ka wayewa.
"Duk lokacin da ki ka ce
Mabaruka haka za a yi, in ma kina
ganin za ki iya jure shiga
gargada da kwari da tudu irin na
unguwanninmu na yan Allah
baku mu samu sai mu tafi tare ki
rakani, domin ba na son rabuwa
da ke." Mabaruka ta dage kai
cikin murmushi, sannan ta
girgiza kai ta ce.
"A'a ni ba zan iya shiga gargada
ba, kana ganin ma so nake yi mu
tafi london hutu, amma rashin
doguwar tafiya a jirgi ya hanani"
Ta dan yi shiru.
Zuciyar Anas sai harbawa take yi
yana jiran ya ji abin da za ta ce.
"Anas." Ta kira sunansa a
sanyaye.
"Na'am, Mabaruka." Anas ya amsa
cikin kwararren murmushinsa na
mayaudara. Mabaruka ta ce.
"Idan ka tafi kamar karfe hudu
na yamma sai yaushe za ka
dawo?" Anas ya dan yi jim
sannan sai ya dube ta, ya ce.
"In ba dan abokan nawa suna da
yawa ba da sai in ce dake karfe
takwas ma ina gida, to amma me
yiwuwa na kai har wajen tara."
Ya dubeta ido da ido.
"Babu damuwa?" Mabaruka ta
kama hannunsa cikin farin ciki ta
gyada kai ta ce.
"Na kara ma awa daya, amma
kada ka wuce karfe goma, domin
ko ruwa ba zan sha ba sai ka zo
ka ba ni." Ta dan yi shiru tana
duban Anas, suka yiwa juna
murmushi.
"Idan za ka fita sai ka dauki
motata shudiyar lexus din nan,
kada abokan ka su raina min
kai!"
***
Sidi mai jaka ya dubeni babu ko
saurarawa ya ce.
A can gidan su Ummi, Abdulmalik
ya tsinci kansa cikin damuwar da
bai taba shiga irinta ba, domin
kwanansa guda cur) babu dare
ba rana, yana ta faman rubutu
ne.
Na dubi Sidi mai jaka cikin
mamaki.
"Rubutun me kuma?" Sidi mai
jaka ya ce.
"Saurareni da kyau ka ji dalili."
Ka ga Nas, tun ranar da Ummi ta
halarci liyafar gidan Mabaruka,
inda ta baiwa Anas yar
rubutacciyar wasika, tana
komawa gida sai ta wuce kai
tsaye zuwa dakin dan uwanta
Abdulmalik.
"Yaya Abdulmalik." Ta kira
sunansa tun daga kofar dakin
cikin doki da farin ciki.
Abdulmalik ya dago kai cikin
damuwa ya dubi kyakkyawar
fusakarta domin ya san labarin
da ta zo dashi ba zai taba faranta
masa ba. Daman tun da yamma
kafin ta tafi sai da ta sameshi ta
ce.
"Yaya Abdulamalik...M abaruka
ta
gayyace ni liyafa a gidanta."
Abdulmalik ya boye kunar
zuciyarsa ya dubeta da
murmushin da bai kai zuci ba.
"Ki ce yau kin sami damar ganin
mutumin na ki." Ummi ta
sunkuyar da kai.
"Uhm, shi da ma yake da mata, ni
na san ma ai zai yi wuya in zai
kulani." Abdulmalik ya ji zuciyarsa
kamar za ta fashe.
"Namiji ai na mace hudu ne."
Ummi ta gyada kai ta ce.
"Yanzu yaya Abdulmalik idan
mun hadu da shi ya ya zan yi?"
Abdulmalik ya dube ta ya ce.
"Duk da yake dai nima ba sanin
irin al'amuran soyayyar nan na yi
sosai ba, to amma ina ganin
tunda dai ke mace ce, ba za ki
rasa dabarar da za ki bi ba wajen
nuna masa cewa kina kaunarsa.
Sai dai kuma ki bi a hankali kada
babbar kawarki ta kamaki kina
kokarin sace mata miji." Suka
fashe da dariya, A haka suka
rabu.
Wannan shi ya sa lokacin da ta
dawo sai ta shiga dakin cikin
farin ciki ta zayyanawa
Abdulmalik duk abin da ya
gudana tsakaninta da Anas
"Yaya Abdul kana jin zai zo gobe
din kuwa?" Abdulmalik ya ji
murmushinsa ya fara daukewa
"Me zai hana, tun da dai idan aka
yi la'akari da abin da ki ka ce
shima ashe ya dade yana kaunar
ki" Ummi ta yi tsalle a tsakar
dakin ta dire cikin farin ciki ta ce.
"Wallahi Yaya Abdul ba ka ga
yadda na ruda shi ba jikinsa har
rawa yake yi" Abdulmalik ya cije
baki sannan ya dage kai. Ummi ta
daina tsallen da take yi ta dube
shi cikin damuwa.
"Yaya Abdul...ba ka da lafiya ne na
ga kana cije baki?" Abdulmalik ya
dubeta.
"Kaina ne ke sara min da ciwo
tun da safe" Ummi ta dube shi cikin.TSOHON ALKAWARI-14
.
"Kaina ne ke sara min da ciwo
tun da safe" Ummi ta dube shi
cikin damuwa.
"Bari in dauko ma magani"
Abdulmalik ya yi sauri ya girgiza
kai. Sannan ya yi mika.
"Ina tsammanin gajiya ce ta yi
min yawa, na san idan na sami
isasshen barci zan warware
zuwa safe" Ummi ta kura masa
idanu cikin damuwa na tsawon
lokaci.
"Bari to na tafi na barka ka huta,
domin zuwa na yi mu yi
bankwana, na kuma fada ma
cewa gobe ne da daddare muka
yi dashi zai zo...in dai zai zo din"
Ta mike tsaye. Abdulmalik ya dubi
kyakkyawar fuskarta.
"Ina taya ki fatan alheri Allah ya
sa ya zo din" Ummi ta yi
murmushi ta ce.
"Ameen Yaya Abdul, Allah ya karbi
addu'arka, wallahi yau da kyar
zan yi barci"
"Ai ba ke kadai ba" Abdulmalik ya
ce cikin zuciyarsa.
"Sai da safe Yaya Abdulmalik."
Ummi ta ce da faffadan
murmushi. Sannan sai ta fice
daga dakin.
Tana fita sai Abdulmalik ya kifa
kai akan cinyarsa, ga mamakinsa
sai ya ji wani zazzafan hawaye ya
fara kwaranya akan fuskarsa.
Yana nan zaune har karfe biyun
dare ta gota barci bai samu ba,
domin Abdulmalik ya riga ya san
cewa idan ya yi lako-lako yana ji
yana gani kwado zai leko daga
tafki ya yi masa kafa ya koma.
Tabbas idan ya yi wasa yana ji
yana gani Ummi, abin da ya fi
kauna fiye da komai a duniya za
ta sulale ta tsakanin yan yatsun
ikonsa. A lokacin ne to dabarar ta
fado zuciyar Abdulmalik. A kullum
zuciyarsa kan fada masa cewa
hanya daya ce kawai zai bi ya
magance wannan bala'i dake
kokarin afka masa. Ita ce ya kira
Ummi ya yi mata bayanin cewa
ita fa ba yar uwarsa ba ce ta jini,
ya kuma yi mata bayanin irin
yadda ta shige zuciyarsa. To
amma kashedin mahaifinsa shi
ke taka masa birki. Wata zuciyar
ta kan ce dashi me zai hana ka
sanar da mahaifiyarka halin da
ake ciki. Kunya ba za ta bari ba.
Ita ce amsar da Abdulmalik ke
fadawa zuciyar tasa.
Yana cikin hakan ne to ya kasa
barci, kawai sai dabara ta fado
masa
Abdulmalik ya dauko littafin
rubutu, mai shafi dari da sittin, ya
dauki biro ya fara rubuta labarin
tun farkon haduwarsa da
marigayi Saifullahi mahaifin
Ummi.
Sidi mai jaka ya dubeni da
murmushi "Nas, wannan labari
da Abdulmalik ya rubuta shi ne
sanadiyyar duk wani labari da
nake baka a halin yanzu."
"Kamar ya ya kenan, ban fahimce
ka ba Baba Sidi?" Na ce dashi.
Sidi mai jaka ya ce.
"Za ka fahimce ni ne, amma sai
nan gaba, kai dai rabu dani na
karasa labarin nan, na ga
magriba ta karaso, bana son
labarin nan ya kaimu har bayan
isha." ya dauki tubani ya jefa a
baki sannan ya ci gaba.
Washe gari tun kafin magariba
Ummi ta shiga wanka, ba ita ta
fito ba sai karfe shida da rabi.
Bayan ta yi sallah sai ta shiga
kwalliya, sai da ta shafe sa'a
guda tana kwalliya. Bayan ta
gama shafe-shafe da feshe-
feshen turare, sai ta wuce kai
tsaye zuwa dakin Abdulmalik
domin tun da safe suka yi dashi
cewa shi ne zai rakata hirar,
domin Ummi ta ce dashi ba ta
son a san alakar a cikin gida har
sai Anas ya zo a kalla sau uku.
"Har kin shirya kenan?"
Abdulmalik ya dubeta cikin
karaya. Ummi ta yi murmushi ta
dubeshi ta ce.
"Dubanni da kyau Yaya
Abdul...dan Allah na yi kyau? Idan
ban yi ba fada min na yi sauri na
sake shiga kada ya zo ban gama
shiryawa ba." Abdulmalik ya
kurawa kyakkyawar halittar
idanu. Ba wai yana kallon Ummi
bane don ya ba ta amsar
tambayar da ta yi masa ba, yana
kallonta ne da idanun bege da
tsananin shaukin ina ma ace shi
ya mallake zuciyar ta baki daya.
Kai wannan Anas da sa'a yake a
duniya. Abin da ya fi damun
Abdulmalik da kuma bashi
mamaki shi ne, wai shin shi
wannan Anas din kamar ya ya
yake, wane irin kyawun siffa ce
dashi, ko kuma Ilimi, ko kuma
dadin baki, da har wannan
kyakkyawar ta mace da tsananin
kaunarsa.
"Ya ya ka ganni Abdulmalik, na yi
kyau?" Zazzakar muryar Ummi ta
sake ratsa kunnen Abdulmalik. Ya
yi ajiyar zuciya ya ce.
"Kin yi kyau wallahi sosai ma
kuwa." Ummi ta yi tsalle cikin
murna ta ce.
"Har na ji dadi wallahi, tashi to
mu tafi." Abdulmalik ya mike
tsaye da kyar kamar ya hadiyi
tabarya sannan ya ce.
"Idan momi ta tambaye kin inda
za mu ki ce da ita kanti zamu je
siyayya."
***
Karfe takwas saura kwata na
yamma Anas ya shigo titin a cikin
katuwar motar shudiya kirar
Lexus yana tafe yana bin wakar
kidan turawa abinsa cikin farin
ciki da wannan rana. Tun da ya
auri Mabaruka bai taba samun
yanci irin na wannan rana ba. Ga
shi dai daman tun ranar da ya
aureta ya yi tsalle ya fice daga
kurkukun talauci ga motocin
hawa sai wacce ya zaba ga
sutura
Kusan kullum sai ya sa sabon
kaya na yamma daban na
safe daban. Ga aljihunsa a cike
taf da mikakkun takardun kudi
na kashewa, amma duk a banza
bai jin dadinsu ba don kome ba
kuwa sai dan wannan nacacciyar
gurguwa kamar yadda ya kirata,
wacce ke manne da shi kullum
kamar cingam. Dan haka a yanzu
da ya shigo cikin titin sai ya dubi
kujerar motar dake hannun
damansa cikin farin ciki domin
yau Allah ya raba shi da cingam,
lokaci guda kuma sai ya dubi
takardar da ke hannunsa na
dama, yayin da hannunsa na
hagun kuma yake sarrafa
matukin motar. Tabbas titin ne.
Anas ya ce cikin zuciyarsa,
sannan sai ya dada kallon
takardar kwatancen da Ummi ta
bashi, kana ya sake dago kai
yana nazarin jerin gidajen dake
gurin yana kokarin hangen mai
lamba ashirin daga cikin su. A
daidai lokacin ne to hasken fitilar
motarsa ta hasko masa abin da
ya sa yar autar hantar cikinsa
kadawa. Sannan sai ya fara musu
da zuciyarsa, kai wannan ba ita
ba ce, ya ce da kansa, sa'ar da ya
hangi kyakkyawar hallitar tsaye a
jikin katangar wani sabon gida
da ba a gama ginin sa ba. Ita da
wani saurayi ne kyakkyawa dogo
fari mai dogon saje da dogon
hanci mai doro daga tsakiya sai
ka ce hancin Larabawa. Anas ya ji
wani bakin kishi ya turnuke
zuciyarsa sa'ar da ya tabbata
lallai Ummi ce ba wata ba.
Abin da ya fi bata masa rai shi ne
saurayin da ke tsaye da ita shima
kyakkyawa ne, duk da yake dai
Anas bai ga alamun saurayin ya
zo da mota ba, to amma a
yanayinsa babu alamar talauci ko
kankani a jikinsa.
Sannu a hankali ya ja birki ya
tsaya a daf da su kana sai ya rage
hasken fitilar motar kadan ya
dada nazarin fuskar Ummi. Abin
ya bashi mamaki, domin ya lura
da cewa sun juyo inda yake, sun
zubawa motar idanu.
Sidi mai jaka ya yi shiru, kana ya
sheka wata uwar hamma ya
dubeni a yatsine ya ce.
"wato Nas, tubani na da dadi,
amma tsiyata da shi saurin sa
mutum barci, ga shi da sa cikin
mutum ya yi nauyi wata sa'ar sai
in ji kamar na hadiyi duwatsu."
"Dan ma ka saba cin sa." Na ce
dashi a kagauce domin na matsu
na ji yadda za a yi.
Sidi mai jaka ya dafa cikinsa da
busassun yan yatsunsa gami da
dan runtse, idanu sannan sai ya
dubeni ya ce.
"Sannu a hankali Nas, Anas ya
tuko motar zuwa inda suke ya
tsaya, lokaci guda kuma ya sauke
gilasan motar.
Cikin sauri Ummi ta nufo gindin
tagar motar, Abdulmalik na biye
da ita a baya, a lokaci guda kuma
ya ji wani matsanancin bakin ciki
ya lullube shi
Na shiga uku ya ce a cikin zuciyar
sa, Ashe Anas din shima
kyakkyawa ne."
"Anas..." Mabaruka ta kira
sunansa a kunya ce. "Ummi..."
Shima ya kira sunanta, sai dai har
yanzu zuciyarsa na bugawa
domin bai fahimci matsayin
saurayin dake biye da ita a baya
ba.
Ummi ta lura tun da ta zo gurin
idanun Anas akan Abdulmalik
suke don haka sai ta yi sauri ta
dube shi ta ce.
"Anas...ga Yayana Abdulmalik ba
ku gaisa ba." Sannan sai ta juya
ta dubi Abdulmalik da faffadan
murmushi ta ce.
"Yaya Abdul...ga Anas dina da
nake baka labari yau dai Allah ya
hada ku."
Cikin sauri gami da ajiyar zuciyar
jin dadi abin da ta ce, Anas ya
bude kofar motar ya fito, sannan
ya mikawa Abdulmalik hann.
"Yaya barka da yamma." Samarin
biyu suka cafke hannun juna,
kana suka dubi juna ido da ido,
Abdulmalik ya riga ya san
matsayin Anas a gurin Ummi, to
sai dai shi Anas bai san matsayin
Abdulmalik ba a gurin Ummi, duk
da yake dai ta ce dashi wai
Yayanta ne, akwai wani abu a
yanayin fuskar Abdulmalik da ya
jefa shakka cikin zuciyar Anas,
tabbas abin ya jefa shi cikin
kaduwa, domin irin yanayin da
yake gani a fuskar Abdulmalik, ya
sha ganinsa a fuskokin gomomin
samarin da ya sha kwace musu
yan mata a baya, to amma da
yake a yanzu bashi da wata
kwakkwarar hujja abar dogaro,
sai ya dubi Abdulmalik ya kuma
cewa.
"Ya ya ayyuka...ko kuma ya ya
karatu zan ce..."
"To, karatun dai...ai har yanzu
yayan naka dalibi ne." Abdulmalik
ya ce a karo na farko.
Aka sake yin shiru na yan
mintuna, Ummi na kallon Anas,
shi kuma na kallon Abdulmalik,
Ummi ce ta fara bata shirun.
"Yaya...Abdulma lik yau dai Allah
ya hadaku da Anas din da nake
baka labari."
Ba na fatan na kara haduwa da
shi. Abdulmalik ya ce cikin
zuciyarsa, sannan sai ya ce a fili.
"Malam...Anas, ta sha bani
labarin ka...ga shi sai yau Allah ya
hadamu." Ya dan yi shiru yana
duban Ummi kana sai ya ce.
"Daman zuwa na yi mu gaisa da
wanda kanwata ke so...ni zan
koma, gara na barku ku dan
zanta." Yana gama fadin haka sai
ya fara juyawa da baya.
Ummi ta dubeshi cikin mamaki-
mamaki kaduwa-kaduwa, domin
ta fahimci lallai yana cikin
damuwa. Na shiga uku. Ummi ta
ce a ranta.Ummi ta dubeshi cikin mamaki-
mamaki kaduwa-kaduwa, domin
ta fahimci lallai yana cikin
damuwa. Na shiga uku. Ummi ta
ce a ranta. Yaya Abdulmalik
jininsa bai hadu da na Anas ba.
Ta kuma fadi cikin zuciyarta,
sannan sai ta ce a fili.
"Yaya Abdulmalik...ta fiya za ka yi
tun yanzu?"
"Eh mana, ai gara na ba ku waje
ku yi hirar ku...na sa kannena a
gaba?" Ya fadi gami da jeho wani
takurarren murmushi. To sai dai
kuma ba Anas ba wanda tuni
daman ya gama fahimtar
Abdulmalik, hatta Ummi ta gane
cewa murmushin yake ne tabbas
ta san yayanta yana cikin
damuwa.
"Sai an jimanku..." Abdulmalik ya
kuma fada sannan cikin sauri ya
juya ya nufi gidan su.
Suka zuba masa idanu har sai da
ya shige cikin gidan ba a samu
wanda ya ce kala ba. Ummi ta yi
ajiyar zuciya sannan ta sunkuyar
da fuskarta akan kirjinta cikin yar
damuwa.
"Ya ku ke da shi?" Anas ya
tambayi Ummi yana dubanta
cikin zargi, wani bakin kishi na
kokarin tsaga masa zuciya.
"Yayana ne." Ummi ta bashi amsa
kai tsaye lokaci guda kuma ta
kalleshi ido da ido.
Anas ya dubi fuskarta na tsawon
lokaci yana nazari a cikin duhun
daren, abin ya bashi mamaki
domin a yadda ya ga tana
kallonsa da karya take yi ba za ta
taba iya hada idanu da shi ba. To
amma me ya sa kyakkyawan
saurayin mai hancin larabawa
yake irin wannan dabi'a haka
kamar wanda yake tsakiyar
kogin begen Ummi? Tambayar
kenan da Anas ya kasa amsawa
kansa.
"Kina nufin yayanki na uwa daya
uba daya ko kuwa dai kawai
yaya ne na yan uwa."
A wannan karon Ummi ce ta
dube shi da wani tattausan
murmushi ta ce.
"Oh...Anas kenan, lallai na fahimci
kai ma kana da kishi kamata." Ta
dan yi shiru lokaci guda kuma ta
dafa kofar motar dake bude da
hannunta na hagun ta dubi Anas
ta ce.
"Ka da ka bari kishi ya hana
mana jin dadin hirarmu ta farko
da kai."
Cikin sauri Anas ya sassauta
fuskarsa duk kuwa da cewa har
yanzu zuciyarsa tafasa take yi.
"Ki gafarce ni Ummi, masifar
sonki ce ta yi min yawa a cikin
zuciya, irin yadda nake kaunar ki
ko kuda ya sauka a kanki sai na
yi kishi da shi...to ballantana
kuma wannan kyakkyawa da ki
ka ce wai yayanki ne."
Ummi ta fashe da wata zazzakar
dariya, wacce sautinta ya sa
wasu yan gajerun samar dake
can gefe guda suna jiran fitowar
tasu budurwar suka juyo cikin
sauri suka kalli bangaren da su
Ummi da Anas suke.
"Kai Rabe...ka ji wata cika tana
dariya kamar ana busa sarewa."
"Ummi kenan." Daya saurayin ya
ce da abokin sa "Duk unguwar
nan babu cikar da ta kai
haduwar ta, ba ka ganin
gashinta daga nan har sheki
yakeyi kamar madubi, to don ma
da daddare ne da rana ce in ka
kalli gashin kanta sai ya dauke
maka idanu." "Allah mutumi
na...to ko barin wannan kucakar
zamu yi mu koma can mu gwada
sa'ar mu." Daya saurayin ne yake
fadawa Rabe haka.
"Rufawa kanka asiri." Rabe ya ce
da saurayin.
"Ummi me shegen girman kai
kamar ibilishiya tun da nake ban
taba ganinta da wani saurayi ba
sai yau...kuma in ban da
rigimarka ma ina kai ina Ummi?
Zoben dake danyatsanta guda
daya fa sai ya yi ma dinkin sallah
karama da sallah babba har sau
uku, kuma ya bar ka da ya canjin
kashewa...samar i yan hutu ma
masu kafafu hudu da iya kwalisa
ba ta sauraresu ba sai kai mai
katon kai da fadi kamar faranti."
"Ka ga bana son iskancin
banza...kai din kyau ne da kai ko
dan ba ka kallon madubi."
Saurayin ya ce da Rabe a kufule.
A daidai lokacin da Rabe ya fara
kokarin mayar da martani ne to,
kofar wani gida ta bude sannan
wata yar gajeriyar budurwa fara
ta fito cikin sauri ta nufi inda su
Rabe suke, ko da ta zo giftawa ta
kusan inda su Ummi suke, sai ta
tsaya turus ta Kalli Anas sama da
kasa sannan ta dauke kai ta dubi
Ummi ta ce.
"Yaya Ummi ina wuni."
"Lafiya kalau Hasiya...ya ya ki ke?"
"Lafiya nake." Shiru Hasiya ta dan
yi sannan sai ta sake duban
Fuskar Anas ta ce.
"Lalatacce mayaudari nan kuma
ka dawo?" Anas ya ji gabansa ya
fadi sannan zuciyarsa ta harzuka
ya dubi budurwar a kidime yana
kokarin tuna inda ya san ta.
"Ai ba za ka iya tunani ba
mayaudari tun da muna da yawa
a gaban ka." Tana gama fadin
haka sai ta juyo ta dubi Ummi ta
ce.
"Ki bi a hankali Yaya Ummi kada
ki sake dashi domin ba zan so
ace kin fada tarkon sa ba." Tana
gama fadin haka sai ta juya gami
da cewa.
"Bari in je in fatattaki wadancan
yan iskan...duk sahunsu guda da
wannan da yake gabanki, kar ki
yarda da shi mai kyan dan maciji
ne."*****
0 comments:
Post a Comment