Wak`ar *broken angel* aka saka a lokacin shigowar Kerry, cike da k`asaita ta fito daga motar ita da saurayin ta Triple A, hannun su sak`ale da juna suna wani taku kamar basa son taka k`asa,
Ihu duka wurin aka d`auka take suka fara fiddo wayoyi suna snapping nasu, tafi kake ji sosai wurin da k`arfi, kai da kagan su kasan suna cike da farin ciki tsantsar shi, banda Feenat data ware kanta gefe cike da haushin zuwan ta wurin.
*karfe 6:30pm*
A lokacin ne za`a yanka cake, nan aka hau tafin yanda Triple A ya kama hannun Kerry ya d`ora akan cake d`in, hotuna sosai suke d`aukar su kuma a lokacin ne hotunan sukafi yin kyau saboda rana ta fad`i hasken flash lights yafi fita da kyau.
Sautin kiran sallar magrib ne yake fita kad`an kad`an daga wani masallaci nesa da dam d`in, da alamar dai can cikin garin Ajiwa yake. Feenat ce zaune tana tunanin yanda za`ayi tayi sallah, can wata dabara ta fad`o mata, a bakin wani famfo taje tayi alwala ta bud`e handbag d`inta ta zaro hijabin ta ta saka, can daga gefe inda ba`a jin kid`an ta koma tayi sallar ta sannan ta dawo cikin mutanen.
*k`arfe 7:30pm*
Cashewar su suke sosai kowanen su ya kama partner d`in shi, a hankali na fara jiyo wani sauti mai had`e da wani irin kuka_kuka kamar kukan shanuwa ko alade, sukam da yake sunyi nisa a casun su har yanzu basu fara jin shi ba, tun sautin yana fitowa kad`an kad`an har ya fara yawaita, sautin wak`a na fita daban sannan na wancan kuka kukan ma yana fita daban, sai kuma yanda kururuwar take k`ara tashi sosai.
Feenat ce keta bige hannun MD dake faman shafar gabanta har yana k`ok`arin kai hannu cikin rigar ta, kunnen ta ta kasa sosai dan yanda sautin abun yake fita har ya fara yin yawa, ido ta fara zarowa 😳 tana kasa kunnuwan ta cike da tsoro da fargaba, da k`arfi ta buge ma MD hannun shi wanda yasa shi dawowa hayyacin sa,
Da sauri ya koma wurin Reeshat dake rawa ita da MC, rungumo ta yayi ta baya ya fara shafar ta a hankali, nan sukaci gaba da romancing juna cike da jindad`i.
Itakam Feenat sosai hankalin ta ya tashi, nan ta fara tunanin to wannan kururuwar ta mecece? K`ok`arin magana take masu amma muryar ta bata fita saboda sautin wak`ar dake tashi.
"Na shiga uku ni Safeenat! Wannan k`arar ta mecece? Kar dai namun daji ne zasu cinye mu" ni kuwa Amrah nace in namun daji ne ma ai da abun yazo da sauk`i saboda akwai hanyoyi da yawa zaku iya guduwa.
Sosai wannan k`arar take k`ara yawaita, a hankali sautin speakers d`in ya fara canjawa yana komawa irin wancan sautin na kuka, Reesha ne yace "oh common! Dj wannan kukan daka kunna mana fa? Abeg ka canja shi mana, abu kamar kukan jaki", Sally dake rungume da Reesha tayi dariya tace "wuce jaki ma wannan".
Amrah and Rerbeeart sk novels,
Admins
ONLINE HAUSA READERS📚
[5:22pm, 20/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘:
💀 *A YINI 'DAYA* 💀
👹💀 💀👹
👺
*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*
Page8⃣
Sautin ne ya k`ara d`aguwa sosai, Dj`n ma hankalin shi ya soma tashi, shidai a iya sanin shi bashi da wannan sautin a duk wak`ok`in shi, k`ok`arin wucewa ya fara yi amma d`if! Wayar ta d`auke, dvd d`in ta mutu, ga hasken fitilar duka ya mutu, sai wannan sautin da yake ta k`ara yawaita.
Feenat jiki sai rawa yake, ta ambaci sunan Allah amma sam ta kasa, ga wani irin mugun duhu daya mamye wurin, Dj ma hankali ya k`ara tashi, Sally tace "mun shiga uku! Wa ya kashe mana hasken?",
Reesha yace "kila dai cikin samarin nan ne wani ya kashe ta, shegu maza! Iskanci yayi dad`i kenan",
Cike da tsoro da rawar murya Sally tace "wannan ba kashe shi akayi ba, kaji sautin da yake tashi fa, na shiga uku ni Saleemah" sai hawaye sharrrr a kumatun ta.
Wata irin k`ara da k`arfi speakers d`in sukayi wanda yasa lokaci daya kowa ya dawo hayyacin sa, tsoro duk ya kama su, wani irin iska mai had`e da guguwa ya fara tashi, Kerry uwar birthday tuni hawaye sun cka mata ido, wayar ta take ta nema amma ta rasa inda take, ita dai tasan akan table ta ajiye ta a lokacin da zasu yanka cake amma kuma yanxu ta duba nan babu ita, can daga nesa ta hango hasken ta alamar ana kira saboda wannan muguwar k`arar bazata bari k`arar waya ta fita ba, hannun ta ta zira zata d`auko amma sai taga wayar ta k`ara yin gaba kamar anja ta, k`ara zira hannu tayi amma wayar ta k`ara tafiya, binta taci gaba dayi ana jan wayar har saida tayi nisa sosai ta fara fita daga cikin mutane, har tabar baki d`aya area`n da suke party.
Ihu dukkanin su suke, daga mai kiran dady sai mai kiran momy amma babu mai kiran sunan Allah, sannu sannu kukan nan ya k`ara yawaita, da suna jin murya d`aya ne amma yanzu ya zama muryoyi da yawa babu adadi.
"Tashin hankali" na fad`a a raina, tuni biro na ya kufce ya fad`i tsananin tsoro da fargaba, ban san a ina yake ba dole sai Sis ta siyo min wani.
Muje zuwa, ba`a fara komai ba yanzu za'a fara inji Amrah.
Amrah and Rabeeart sk novels,
Admins
ONLINE HAUSA READERS📚
[8:16pm, 21/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: [8:02pm, 21/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘:
💀 *A YINI 'DAYA* 💀
👹💀 💀👹
👺
*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*
Page9⃣
*'Karfe 9:00pm*
*_AJIWA DAM_*
Iya rud'ewa da kid'ima yau *AREWA STARS* sunyi ta, kuka suke su duka 19 d'in banda Kerry da tabi wayar ta, hankali tashe Feenat ta ringa kiran "Ummah! Ummah!! Ummana kizo ki taimake ni, alhakin ki ne Ummana, kullun k'ok'arin ki ganin kin bani kyakkyawar tarbiyya amma bana d'auka, ina watsi da duk tarbiyyar da kike bani, yau gashi nan muna ganin abunda muke shukawa", sosai take kuka duk ta fita hayyacin ta.
A hankali guguwar nan ta fara isowa inda suke, k'ura ce mai had'e da wasu irin k'ananan halittu wanda bazasu iya misaltuwa ba, da yawan gaske suke ta zuwa wurin su, ga wannan kukan mai muryoyi da yawa shima yana ta k'ara yawaita, ga kuma duhu shima babu wanda ke iya ganin ko tafin hannun sa.
Wurin Eseeee k'warin suka nufa da mamaki naga sun k'adaddabe ta baki d'aya kamar yanda zuma kema mutun idan ta kama shi. Sosai take kuwwa tana ta k'ok'arin murje su daga jikin ta amma sai k'aruwa suke, da mamaki wannan halittun suka ringa shigewa a cikin fatar Esee suna yawo ciki kamar wani bororo, har cikin kanta suka shiga suna mata yawo akai, banda soshe soshe babu abunda take, take gashin kanta ya fara kakkaryewa yana fita har sai da baki d'ayan shi ya fita kanta ya koma swal, in banda yawon wannan halittun dake cikin kan.
Fatar jikin ta ta fara zagwanyewa tana barin tsokar ta baki d'aya kamar wadda ta k'one, kamar gari haka fatar ta ringa murmusa a k'asa, take Esee ta fad'i wurin bata a hayyacin ta.
Reesha da Sally kam har yanzu basu saki junan su ba, cike suke da tsoro da fargabar wannan al'amarin,
Can suka ji wannan halittun sun dawo kan su, yanda suka ma Esee suma haka suka masu kuma har a lokacin suna manne da juna basu rabu ba hannun Reesha a cikn rigar Sally kan k'irjin ta.
Fad'i sukayi a tare suma basa a hayyacin su.
Da wata irin dariya da k'arfi naji wata muryar da tunda babata ta haifeni ban tab'a jin ko makamanciyar ta ba,
Wannan k'warin ne suka hau dunk'ulewa guri d'aya, d'aya na cin d'aya har suka zama guda d'aya babbar halittar da babu halitta mai girman ta a duk doron k'asar mu ta Nigeria.
Nan ta hau jijjigar jikin ta saboda duk inda bai gama had'ewa ba ya had'e.
Idon ta ma jaa ne tamkar garwashi wanda hasken idon kawai ake iya gani a duk fad'in filin.
Afnan ce b'oye a bayan wani katako wanda jikin shi duk k'usoshi ne ta lafe jikin ta sai rawa yake, da k'arfi taji an buga ta jikin k'usoshin duk suka caccake ta, take jini ya fara ambaliya daga jikin ta, tun daga nan itama ta fita hankalin ta da alama suma tayi, bata kuma sanin abunda yake wakana ba.
Nan ma wata dariyar ta kuma yi da k'arfi wadda tafi waccan ma tsanani.
Ruky wadda tuni ta sume tsananin tsoro da tashin hankali da k'arfi halittar nan ta d'auki Ruky ta d'aga ta sama ta nanata k'asa, take kuwa Ruky ta farfad'o, sake d'aga ta sama tayi ta jefar sai kan wani dutse, take jini ya fara ambaliya daga kanta itama ta sake sumewa.
Dj da Mc kuwa had'a su tayi da karfi ta matse su sai ga hannun Dj ya b'ullo ta bayan Mc, hannun Mc kuma ya b'ullo ta cikin Dj, wulwula su taci gaba dayi sannan ta jefar dasu daidai kan dutsen da ta jefar da Ruky, take suma suka sume.
Dariya mai had'e da sautin kuka ta fasa lokaci d'aya, wanda yasa sauran da bata kashe ba suka k'ara tsorata da ita, dan cikin su har da wanda ya saki zawayi daga zaune akwai, a ransu kuwa banda dana sani babu abunda sukeyi, ni kuma Amrah nace maganin irin ku kenan, wata k'ila wasu idan suka ji labarin ku koda halin su ne zasu daina, basu san aron lokaci bane Allah ya basu amma sun kasa ganewa, yau gashi sun had'u da daidai dasu, muje zuwa dai inji ni Amrah.
Amrah and Rerbee'art sk novels,
Admins
ONLINE HAUSA READERS📚
[8:14pm, 21/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘:
💀 *A YINI 'DAYA* 💀
👹💀 💀👹
👺
*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*
Page1⃣0⃣
Bari mu koma b'angaren gidajen su.
*Karfe 10:30pm*
*~Gidan su Feenat.~*
Ummah ce zaune tayi tagumi baki d'ayan hankalin ta a tashe yake, ita dai tasan a duk inda Feenat take ya kamata by now ta dawo gida, "to ko dai jikin maman Afnan d'in ne ya rikice?" Ta fad'a a ranta,
"To inko hakane ai ya kamata Safeena ta kira ni a waya ta sanar dani in ma acan zata kwana, amma gashi har dare yayi babu ita babu kiranta kuma",
Wayar ta ciro nan ta hau neman lambar Feenat tana ta ringing amma bata d'aga ba, a hankali ta soma jiyo k'arar ta daga d'akin Feenat alamar can ta barta, "to kenan anan ta bar ta kome?",
D'an guntun tsaki tayi tare da komawa ta kishingid'a ko zataji zuwan Feenat dan har a lokacim bata rufe gida ba.
Jin shiru har sha d'aya ta kusa yasa tace "bari dai in tashi in tafi gidan su Afnan d'in sai a fad'a min asibitin da maman take, wata k'ila dai babu lafiya",
Hijabin ta ta zira a hargitse ta rufe gidan da makulli ta fita. Da sa'a kuwa tana zuwa bakin titi ta samu napep babu kowa, bata koyi ciniki ba ta hau ta kwatanta inda zai kaita.
*Karfe 10:49pm*
*~Gidan su Afnan.~*
Momy ce zaune ta rungume Affan dake ta bacci abin sa hankali kwance, ita kuwa tv kawai ta tsura ma ido tana kallon NTA wai a nufin ta ko za'a fad'i cewa wani jirgi yayi had'ari amma har yanzu babu, canjawa tayi ta kai AIT amma nan ma babu, tab'e bakin ta tayi tace "wata k'ila har an gwada ban gani ba, Allah dai yayi ma duk musulman cikin jirgin rasuwa, wanda suke raye kuma Allah ya basu lafiya, nayi zaune har Alhaji ya kwanta ya barni da wannan rigimammen",
D'aukar Affan tayi ta d'ora a kafad'ar ta sannan ta kashe kallon,
Daidai zata kashe wutar parlor'n ne yayi daidai da shigowar Umman Feenat.
Cikn mamaki Ummah ta gaishe da momy, momy ma amsawa tayi da mamaki dan sam bata wayi Ummah ba,
"Ina zuwa dan Allah" momy ta fad'a tare da nufar d'akin Affan ta kwantar dashi sannan ta dawo.
Zama tayi tace "baiwar Allah lafiya dai a cikin wannan daren?",
Ajiyar zuciya ummah ta sauke sannan tace "to ko dai ba inda nake son zuwan bane nazo? Ni inda zanje fa mai gidan bata da lafiya tana asibiti, kuma tun a waje mai gadi yace min wai me nan gidan lafiyar ta lau",
Momy tace "Allah sarki! Gaskiya ba nan bane sai dai ko makwaftan mu, ya sunan mai gidan da kike neman?",
"Ban san sunan su ba gaskiya, sai dai nasan sunan 'yar Afnan Abbas tana da k'ane kuma Affan, maman ta bata da lafiya ne 'yata ta tafi ganin ta, amma gashi har yanxu bata koma gida ba shine nake son jin ko lafiya?, amma babu komai nagode barin ci gaba da bincike ko Allah zaisa in dace", ta fad'i hakan ne tare da mik'ewa tsaye tana neman fita.
Cikin mamaki Momy ke kallon Ummah, baki a sake da 'kyar ta iya furta "b..b..b..baiwar Allah ai nan ne gidan su Afnan Abbas, kuma nice mahaifiyar Afnan, sai dai kuma ni lafiya ta k'alau babu abunda ya same ni",
Da sauri Ummah ta dawo ta zauna tana kallon momy, "kina nufin 'Yata Safeenah Al-hassan ba nan tazo ba kenan?",
"Gaskiya ba nan tazo ba, k'ila dai wani wurin zataje shine ta miki k'aryan zatazo gani na",
"Hajiya dan Allah ki kira min Afnan in tambaye ta ko tana da masaniyar inda Safeenah ta tafi" ummah ta fad'a tashin hankali k'arara a fuskar ta,
momy cike da tausayin Ummah tace "sai yanzu na gane ki ashe kece maman Feenat, kin san kolacin da muka had'u last speech and prizes given d'in su ban kalle ki sosai bane, wallahi Afnan bata nan taje gidan rasuwa ne",
Ummah tayi salati ta rufe idon ta tana matsar hawaye, "to ina Safeenah taje? yaushe Safeenah ta koyi wannan halin? Kenan k'arya tamin? Allah yasa dai ba maza tabi ba suka sace min ita" wasu zafafan hawaye sukaci gaba da bin ta.
Momy kuwa a ranta cewa take "kai! Allah ya shiryi yaran yanzu, k'ila ma yawon iskancin ta xata tafi shine ta ma uwarta k'aryar banda lafiya, kuma ta rasa wanda zata ce baida lafiya sai ni",
Dady'n Afnan ne ya fito yana fad'in "maman Afnan lafiya kuwa?", yana fad'in haka yana kallon Ummah cike da mamakin yanda tazo gidan su cikin wannan daren dan shi tsoro ma ta bashi.
Momy bata bashi amsa ba sakamakon sallamar da sukaji, maigadi ne ya shigo yana fad'in "yallab'ai wani bawan Allah ne yaxo, da ganin shi dai babban mutum ne yace wai sunan shi Alhaji Abdallah, wai baban Ihsan ne k'awar Afnan, wai yana son ganin ka",
Dady yace "Alhaji Abdallan da akace yayi hatsarin jirgi ya rasu!? Kace masa ya shigo".
Tir k'ashi! Kallon sis R. Nayi cike da k'aguwa da shigowar Alhaji Abdallah, muje zuwa dai sis R. Ta fad'a, sai kuma gobe zakuji posting d'in mu insha Allah.
Amrah and Rerbee'art sk novels,
Admins
ONLINE HAUSA READERS📚
[11:43pm, 23/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: [11:36pm, 23/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: 💀 *A YINI 'DAYA* 💀
👹💀 💀👹
👺
*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*
Page1⃣1⃣
Ba'a jima ba kuwa sai ga maigadi tafe Alhaji Abdallah a bayan shi,
A kid'ime Dady ya mik'a mashi hannu suka gaisa tare da cewa "bismillah ga wurin zama",
Alhaji Abdallah ya zauna sannan yace "nazo ne dama inji ko lafiya tun da yamma Ihsan ta baro gida tace nan zata zo wai Afnan bata da lafiya, kuma gashi har yanzu bata koma gida ba"
Ido bud'e momy ta kalle shi cike da mamaki tace "Alhaji ai muma nan tun yamma Afnan tabar gidan nan wai kayi accident da jirgin sama ka rasu",
Salati Alhaji Abdallah yayi a bayyane yana mamaki, a ranshi yace "kenan Ihsan bata zo nan ba?",
Momy tace "innalillahi wa inna ilaihi rajiun! k'arya Afnan tamin kenan dama ba can zataje ba?",
Ummah dai na tsaye cikin tashin hankali tana sauraren su, sun jima d'akin babu wanda ya kuma cewa wani abu kowa da abunda yake sak'awa a ransa, sai daga baya ummah tace "in kuwa hakane tou duk inda yaran nan suke suna tare, babu mamakin ko wani wurin sukaje shine suka tsara mana k'arairayi mu kuma muka yarda, Allah dai yasa lafiya suke".
Dady yace "wannan hakane baiwar Allah! Tou ina yaran nan sukaje ne?",
Alhaji Abdallah yace "nima tunanin da nake kenan, wai yara k'anana har sun san su had'a mana k'arya idan zasu tafi, kuma ni wallahi bana kullen Ihsan sosai, inda ma ace ina mata tsanani ne da sai ince banga laifin ta ba".
Dady cikin tashin hankali yace "barin tafi Office yanzu nasan Sajent Musa yau night gare shi, inspector Bala ma kamar night ne saboda sanda na baro office lokacin yaje, barin hanzarta in tafi",
Alhaji Abdallah yace "na manta ashe tare nake da DSP, ai da sauk'i ma kenan, sai mu tafi tare".
Wayar Dady ce ta d'auki k'ara, dubawar da zayyi yaga Inspector Ashir ne, d'aga kiran yayi tare da fad'in "akwai magama inspector, gani nan zuwa Station d'in yanzu",
"Yallab'ai nan ma dai akwai matsala, mutun biyu sukazo wai suna so a masu cigiyar yaran su sun fita tun yamma basu dawo ba, d'ayan ma wai twins ne yaran", inspector'n ya fad'a cike da girmamawa.
Dady ya kalli Alhaji Abdallah sannan yaci gaba da fad"in "same case da zai kawo ni station d'in, ka jira ni yanzu zan taho" yana kaiwa nan ya kashe wayar tare da d'aukar key'n mota ya fita, Alhaji abdallah ma ya mara masa baya.
Basu jima a hanya ba suka isa station d'in, cikin hanzari Dady ya nufi office d'in Inspector Ashir ya samu mutun biyu dattijai zauna sai raba ido suke kamar sunyi k'arya an turke su (lol..).
Bayan inspector Ashir ya saaraa ma Dady sannan yace "yallab'ai kamar yanda na fad'a maka to ga mutanen nan, amma dai kaji daga bakin su",
D'aya daga cikin su yace "sunana Alhaji Ma'aruf, yara na 'yan biyu Shareef da Shareefat ne suka bat'a",
Cikin mamaki Dady yace "b'ata? Garin ya hakan ta faru?"
Alhaji Ma'aruf yace "d'azu ne da yamma lokacin da bana nan Shareef yaje wurin Mamin su yace wai zasu je wata gaisuwar rasuwa baban classmate d'in su ya rasu, to da naji su shiru shine na gano inda sukace sunje d'in da k'yar da wahala ma na gane gidan, naje sun shaida min su babu wanda ya rasu a gidan su, suma 'Yar su ta fita tun yamma bata dawo ba, duk gidajen dangi da nake tunanin yaran nan zasuje naje amma ban same su ba, ga lambobin wayar su bata shiga, hankali na ya tashi sosai shine nazo nan ko da wani abu da za'a iya yi min".
nannauyan ajiyar zuciya Dady ya sauke, gaban shi ya k'ara fad'uwa yayin da bugun xuciyar shi yake tafiya da sauri sauri, ya jima a haka kafin yace "to kai fa bawan Allah me ya faru?"
D'ayan mutumin yace "nifa tawa 'yar gidan mahaifiya ta tace min zataje ta duba ta wai ta dad'e bata je ba, nikau har da dad'i naji ta kula min da uwa, jn ta shiru har dare yayi bata dawo ba yasa na kira ta amma tak'i shiga, na kira mahaifiya ta tace min ai Nuratu bataje inda take ba, hankali na ya tashi sosai, nayi iya bincike na amma ban same ta ba, shine na yanke hukuncin zuwa nan nasan insha Allahu zakuyi bakin k'ok'arin ku".
Alhaji Abdallah in banda kallon su babu abun da yake yi, to wai miye dalilin da yasa yara matasa suka b'ata a lokaci d'aya? Kuma same case ne kowa k'arya yayi kafin yabar gida? Tambayar da yakewa kansa kenan wadda yasan bata da amsa har sai lokacin da aka gano yaran.
Dady ya gyara murya yace "abunda ya kawo ku nima shine muhimmin abunda ya fito dani a wannan lokacin nida bawan Allah'n nan.." nan ya basu labarin duk abunda ya sani har Ummah dake gidan su akan b'atar 'yar ta itama.
Alhaji Ma'aruf yace "tabbas yaran nan aduk inda suke suna tare, baza'a tab'a kiran wannan da coincidence ba saboda abu ne wanda yake a bayyane, fatan mu dai Allah yasa a duk inda suke suna lafiya",
Alhaji Bashir (Baban Nuratu) yace "ai sai asan abunyi ba wai mu tsaya anan muna magana ba, ko gidajen radio ne sai mu fara xuwa kafin gari ya waye asan abunyi".
Da wannan maganar suka rantaya su duka hud'un a cikin motar Dady, basu zarce ko ina ba sai VISION FM, nan suka bada sanarwar b'atan yara matasa wanda dukan su babu wanda ya wuce shekaru 16-17 ba.
Amrah and Rerbee'art sk novels,
Admins
ONLINE HAUSA READERS📚
[11:43pm, 23/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: 💀 *A YINI 'DAYA* 💀
👹💀 💀👹
👺
*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*
DOWNLOAD MORE NOVELS FROM http://hausabooks.com.ng
Page1⃣2⃣
K'arfe 11:05pm
*~AJIWA DAM~*
Wani irin haske ne mai had'e da guguwa mai k'arfi ya haskaka wurin,
Feenat dake gefe makure har ta sik'e da kuka tana ganin hasken ta saki ajiyar zuciya dan wani sanyi sanyi taji a ranta, d'aga kanta da zatayi taga yanda akayi kaca kaca da *AREWA STARS* kamar wasu dabbobi,
Can kuma hasken ya canja launi izuwa red colour,
Md da Reeshat dake gefen ruwa suna kallon ikon Allah bayan hasken ya b'ullo sukaji alamar motsi ata inda suke, cike da tashin hankali Reeshat ta k'adaddabe Md gabanta sai dukan uku uku yake, bata ankara ba taji anja gashin ta dataima mayen gyara sama ana ta wulu wulu dashi, sosai take jin zafi dan dama a ranar tayi sabuwar relaxer, sai da tayi sama sosai da ita sannan ta jefar a bakin wani k'arfe da akebi ta jikin shi idan za'a shiga ruwa, take ta sume bayan ta sai zubar da jini yake.
Md ma ta up side down ta d'auke shi da k'arfi ta jefar a jikin Reeshat, shima sumewar yayi inda k'afar shi d'aya ta cire tun daga cinyar shi sai zubar jini take, cinyar daban ta fad'a a cikin ruwa sai sauran gangar jikin ne a jikin Reeshat.
Nuratu, Shamow da Sady sun dunk'ule junan su suna kallon yanda wannan halittar take wuji wuji da Md da Reeshat saboda har a lokacin wannan jan hasken bai mutu ba, hankalin su tashe dan sun san dole suma sai anzo kansu, babu mai iya yiwa d'an uwan sa magana a cikin su sai faman rawar lab'b'a suke, ga wata irin zufa na keto masu duk da sanyi sanyin ruwan Dam d'in dake akwai amma bai hana masu jin zafi ba.
A hankali wani irin ruwa ya ringa saukowa a daidai inda suke, ruwa ne bak'i k'irin tamkar ruwan kwata ga wari da yake yi,
Da mamaki a duk inda ya d'iga na jikin su sai yayi wani irin bororo kamar masu gyambo, haka yaita sauka a jikin su har saida yayi masu kaca kaca da jiki kamar wanda suka k'ok'k'one,
A had'e ta jefo masu wani d'an k'aramin dutse wanda baki d'ayan su ya had'a ya sumar dasu a lokaci d'aya basu kuma sanin kome yake wakana ba.
Dariya ta kuma fashewa da ita da k'arfin gaske har sai da itacen wurin suka ringa girgiza da kansu, k'yallayen da akayi decoration dasu kuwa da kansu suka ringa yayyagewa, speakers da generator kuwa rugurgujewa suka ringayi kamar yanda ake rugurguza dunk'ulallen gishiri ko maggi,
Ta dad'e tana dariyar kafin ta d'aure fuska wasu irin blue ruwa suka ringa kwaranya daga idanuwan ta wanda da alama ruwan hawaye ne,
Girgiza kanta tayi taci gaba da waigawa gabas da yamma bata ga kowa ba, ta diba kudu inda taci karo da Samir wanda ya gama kid'imewa amma shi a zaton shi ya tsira saboda a wani lungu ne ya lab'e inda matuk'ar baka san yana wurin ba to bazaka ganshi ba, amma da mamaki wannan halittar ta zira dogon hannun ta ta cafko shi a tafin hannun ta, bakn ta takai a cikn wandon shi sai ga kayan marmarin sa (lol..) a bakin ta had'e da jini sai zirara yake,
Tofar dashi tayi sannan ta jefar da Samir wanda a lokacin har ya sume tsabar azaba da tayi masa yawa.
K'arfe 11:30pm
*~kerry~*
tayi tafiya mai nisa har sai da ta sik'e da tafiyar ta nemi wuri ta zauna sai haki take, hankalin ta tashe sai nishin gajiya take,
A hankali ta fara jin hayaniya a kunnen ta wadda ta k'ara tsorata ta, k'ara kasa kunnenta tayi taji k'arar tana k'ara yawaita,
"Oh Dad help me!" Kawai take fad'a,
Da k'arfi halittar ta jawo ta da hannu ta rik'e ta da tafin hannun ta, wata shu'umar dariya tayi wadda ita kad'ai tasan ma'anar ta sannan ta busa ma Kerry iska da bakin ta adaidai kanta sannan ta jefar da ita, take Kerry ta sume itama.
bakin Dam d'in ta koma ta kalli Arewa nan taga Feenat takure sai rawar jiki take,
Hannun ta tasa ta jawo ta ta rik'e ta, a hankali Feenat ta fara furta *"AU'DHU BI KALIMATULLAHI TAAMMAAT MIN SHARRI MA KHALAKA, BISMILLAHILLADHI LA YADHURRU MA'ASMIHI SHAI'UN FIL ARDI WALA FISSAMA'I WAHUWAS SAMI'UL ALEEM"*
Amrah and Rerbee'art sk novels,
Admins
0 comments:
Post a Comment