🤐 WA ZAI FURTA??🤐
0⃣1⃣
*Gaba daya labarin tukuici ne ga Hajiya Rabi badawi ( maman Ibrahim ) Allah ya shirya Miki zuri'a ya Kara arziki Aunty Rabi tawa*
*KINA RAINA MAMAN WEEDAD MARUBUCIYAR ALJAZEERA DA DR. JUNAID.*
*FARKO*
*Federal University dutsinma*
Gudu-gudu, sauri-sauri take tafiya Babu abinda kirjinta keyi sai dukan tara-tara, dodazon mutanen dake chunkushe bakin gate wadanda security suka dakatar don bincike saboda Babu dalibin dake wucewa wurin sai ya gwada I D card, takaici da karuwar faduwar gaban suka Hana ta sukuni, sakamakon yaune ranar farko da zata Fara shiga aji a makarantar.
Tana cikiniyar wucewa taji an janyo hijabinta alamar an mayar da ita baya Shi Kuma ya wuce da sauri Yana faman daga ID card din nasa, ta bishi da kallo saurayi ne matashi dogo..... *Anwar! Anwar !!* Wani ya bi bayansa da gudu, dai dai ta nuna nata ID card din ta wuce Shi Kuma ya juyo don ganin Mai kiransa har lokacin bai tsaya daga saurin da yake faman yi ba.
Ta kalleshi sosai tare da samun tabbacin fuskar bazata taba guje mata ba, tayi guntun tsaki tabi wata hanya.
Da tambaya ta gano ajin, da Shi ta Fara tozali lokacin da ta kunno Kai, ta hade fuska gabas da yamma ya bita da kallo har ta zauna ....kallon ta yakeyi Yana karanta karancin shekarun ta yanda har ta shigo jami'a wannan yar ficiciyar diyar...... Ya Dan tabe baki, may be giyar kudi taja iyayenta mata jumping.....shigowar lecturer din yasa Shi watsar da zancen.
Sakamakon sune Yan alfarma list din karshe na admission yasa lectures duk sunyi nisa har wasu sun kusa karewa, da alama ajin ita kadaice musulma domin duk matan ajin arnaku ne babu Mai alamar ko gyale ko wace ka gani gashi hirtsi-hirtsi.
Yawancin su ko *zo in kashe ka* basa ji da hausa, a gurguje malamin ya raba script na test din da yayi, yace class rep. Ya raba ma kowa, layi-layi yake bi. Zuwa can malamin idon sa yakai gareta, ya tako zuwa inda take tare da Fara jefo mata tambayoyi.
Gaba daya hankalin Yan ajin ya dawo kanta ana jiran aji idan zata iya bada amsa da turancin kamar yanda yake magana wasu nata sumke dariya cikin su harda Anwar saboda kowa yasan yaran hausawa da kwabar turanci.
Ta Sha *mur* kawai yayi maganar duniya taki bashi amsa. Kowa mamaki yakeyi *Anwar* ya Kara binta da kallo duk miskilancin sa yau ga kakar sa ya samu. Hankalinta a kwance ko motsi takiyi haka malamin ya gaji ya kyaleta tare da Shan alwashin idan tasan wata ai Bata San wata ba. Dai dai lokacin da class rep ya gama raba takardun. Lecturer din ya ce Wanda baiga nashi ba ya fito, mutum biyu suka fita duk Mata sunfi mintuna shidda a tsaye kafin yace su kadai ne? Duk akayi shiru yayi ta maimaitawa Amma ba Wanda yayi magana, ya fiddo takardu uku yace *Hamza Yusuf* ya Kira sunan yafi sau goma Amma da alama baya ajin yace shine highest he scored 9/10 ya kalli biyun yace kune second highest kunci 8/10 ya Mika wa kowace takardar ta da one thousand naira, yace class rep ya turo mishi *Hamza yusuf* office domin ya amshi kyautar sa da Kuma script din nasa.
Har ya kai bakin kofa ya juyo what is your name? Kanta a kasa sai da ta kusa da ita ta zungurota sannan ta dago har lokacin fuskarta a murtuk, da kyar ta iya bude baki tace *Bilkisu Abdullahi gada* ya kada Kai *Discuss the macro objectives of ERGP In Nigeria* you'll present it next week in front of everybody as your make up of this test.....ya na gama fadar haka ya fi ce abunsa, ta sunkuyar da Kai kawai tana rubuta question din a bayan littafin ta .......kowa ajin ita yake kallo ganin ba wani alamun damuwa a gareta .....Anwar ya kalli abokin sa yace waccen yarinyar gadararriya ce yayi murmushi ta kaika?.
Ganin an Fara mikewa yasa tayi zumbur ta Mike Babu inda tayi ma tsinke sai sit din Anwar Yana ta kokarin tattara takardu zai Mike ta tsaya kansa, agidan ku ba'a koya maka tarbiyyar daratta mace ba? Ta fada Kai tsaye gaba daya shock ya Kama Yan ajin masu niyyar fita duk suka dakata, da sauri ya kalleta..... Ta jefe Shi da wani mugun kallo na wulakanci kafin ta ce kawai don ka dauki mutane banzaye Ina tafiya zaka Kama mun hijab ka mayar dani baya .......ke! Ya daka mata tsawa tare da mikewa tsaye .....itama ta daka mishi tsawa, zaka dakenine marar tarbiyya? Tare da zaro mishi ido idan hannunka ya Kara gigin taba mun hijab wallahi duk Wanda ya tsaya maka a school din nan sai na ganshi mtseww....ta buga tsoki sannan ta nuna Shi do yatsa, ka kiyaye ni banzo Nan don inyi wasa ba kasa hakan a ranka ta watsar da takardun kasa ta koma ta zauna, wani uban tsalle yayi wallahi sai ya daketa aka rike Shi yana ta faman ihu kamar mahaukaci , ko ajikin Bilkisu taci gaba da rubutun ta kawai da kyar aka fitar dashi ajin.
Mutane sunfi ashirin bisa kansa suna bashi hakuri hada Yan aji uku da hudu akan kada ya biye Mata yarinya ce. Da kyar aka shawo kansa.
Ya fakaici idon kowa ya tafi amsar script dinsa domin baya so a gane Yana da kokari cewarshi Shi baizo don nuna shidin wani ne ba, yayi wa malamin karyar baya aji ne kawai.
Yana komawa hostel ya Fara karatun presentation din Bilkisu domin yi mata tambayoyi, ita kuwa da yake wani gida take na haya dakuna shidda ne a gidan kowa ne daki sai mutum hudu ko biyar su Kama Amma ita nata Bata Kama da kowa ba iyayenta ita kadai suka Kama wa daki daya sakamakon dakunan suna da tsada ko wane da kitchen da toilet akan dubu dari da ashirin 120k. Notes din da aka wuce ta tabi wadannan Yan matan biyu dasuka ci gift ta karbi nasu tayi photo copy ganin sune masu kokarin ajin. Karfe biyu suka koma wata lecture din Bata yarda ta makara ba, taki sakar ma kowa fuska saboda tana son sanin halin kowa don tasan dawa zatayi abota.
Karatun hauka Anwar keyi saboda Bilkisu ya gama tsanar yarinyar kamar yanda itama Bata kaunarsa, kullum tunanin sa yanda zai rama wulakancin da tayi mishi yayin da ita Sam ta shafe babin sa ta manta da al'amarain shi daga masallaci sai daki tayi kwanciyar ta tana duba litattafai abinda ya shige mata Kuma sai tayi goggling.
Ranar presentation ta zagayo kasancewar ajin sunfi dari yasa malamin zuwa da microphone tana cikin tashin hankali da firgici Amma miskilancin Bilkisu yasa ba Wanda ke gane hakan. Abinda kawai ya kawo malamin shine don tayi presentation din kusan Shi da Anwar Abu daya suke sakawa a zuciya watan sai sun kunyatata.
Fuskar ta tamau ta Mike ta isa gaban Allon yayin da ya Miko mata abun maganar jikinta ya tsinke da kyarma anan ya fahimci hakan wurin amsar abin maganar yanda hannun ta ke kakkarwa. Idanun ta suka kawo ruwa tayi saurin cewa *innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Ta tsaye tare da sunkuyar da Kai kasa ta Fara magana a hankali cikin taushin murya wacce ke cike da tashin hankali.......
My name is Bilkisu Abdullahi gada and I'm here to present the macro Economic objectives of Economic recovery and growth.......yanayin fitar turancin nata yasa ajin natsuwa tare da Kara zura mata ido lecturer din ya Goya hannuwa biyu kawai Yana kallonta Shima .....
Bayani take karantowa cikin natsuwa tana Kara lankwasa turancin nata cikin kalmomin kwarewa da birgewa hakan ya Kara tarwatsa zukatan kowa ciki harda Anwar ta share kusan mintuna hamsin tana magana har sai da malamin ya dakatar da ita Shi kansa jikinsa yayi sanyi.
Ta saki ajiyar zuciya a hankali har lokacin kansa na sunkuye ....ya kalli Yan class din *Any question*? Duk akayi tsit! Amma wasu idanun su Yana ga Anwar kallonta kawai yakeyi ya rasa ma mezai fassara tunanin sa. Malamin ya watsa hannu tunda ba tambaya ni ina da ita, ya jefa mata daya.....tayi jimmmmm kamar bazata iya amsawa ba kafin ta Dan motsa kadan ta Fara zakulo bayani, gaban ta yazo ya tsaya Yana kallonta har ta Gama, sannan tayi shiru.
Yafi mintuna shidda baiyi magana ba kafin ya kalli Yan class yace please will you help me give her a roundplus? Duka ajin yadau tafi.......raf raf raf abun mamaki ciki hada Anwar.....ya fiddo five thousand ya Mika mata congratulations you score 10/10 wallahi......ajin ya dauki ihu da sowa.... Ta danyi murmushi kadan kafin ta karba ta wuce abinta har lokacin jikinta na karkarawa.
Duk ajin ya rikice da hayaniya kowa na fadin albarkacin bakinsa, haka malamin ya fita kamar jira Anwar keyi ya Mike ya Isa wurin ta, congratulations sai a bamu ladar ganin ido......Ibrahim da sauran Yan aji kowa ya zaro ido domin kowa yasan Anwar da gadara, rainin saying da Kuma girman Kai.
Kowa na jiran abinda zatayi sai kawai ta dago tana Yar dariya ( domin Bilkisu Bata da riko ko kadan da anyi mata zata rama Kuma ya wuce har abada wurinta).
Ta tura mishi kudin to gashi ai ba nisa sukayi ba ta fada tana Kara Yar dariya, tadanji kunya matuka domin neman fada yazo, ya danyi murmushi kya turan kudi? Kiban kaso na kawai ko rabawa zamuyi? Ta Dan kalleshi kadan.......gabansa ya Fadi kwarai a karo na farko. To mu raba Mana ta fada tana maida kanta bisa littafi.... Okay ya Mika hannu bani nawa toh, ta nuna kudin da baki gasu nan ka dauki naka kabar mun nawa..
Yayi Yar dariya kafin yasa hannu ya dauki 2500 yabar mata 2500.
Amma Kuma ya kasa tafiya sai juya kudin yake da hannu Yana murmushi. Ta dago Kai ta juya mishi ido alamar tsayuwar ta mecece tunda ta sallameshi? Sai kawai ya bushe da dariya yace okay thanks. Ya fice class din abikansa da wasu Yan ajin suka bi bayansa, ta kwashi Yan takardunta tayi daki domin sai 2 zasu dawo wata. Yana tsaye duk an rufeshi ana mishi surutai sai dariya kawai yakeyi tazo ta raba ta wuce ya ringa satar kallon ta har ta kule.....
*****************
*KADUNA RIGASA*
Amira kiyi hakuri wannan auren da zanyi ki daukeshi amatsayin kaddara wallahi wallahi bazan taba wulakanta ki ba don girman Allah kiyi hakuri ki daina wannan kukan......baban Ahmad Dan Allah ka fita ka bani wuri wallahi ko ganin ka bana sonyi na tsaneka da dukkan wannan rayuwar.....ya zukunna na tuba na rantse Miki da Allah ba zanyi auren nan don in wulakanta ki ba mu daukeshi matsayin kaddara Amira kiyi hakuri nasan ban kyauta Miki ba, ta Mike tsaye yaudarar maza wacece ban sani ba? Haka kuke cewa Amma wallahi ka zalunceni ka cuceni kaci amanar kauna.....kada kice haka na rantse da Allah har gobe Ina kaunar ki.....karya kakeyi baka kaunata da baka ga wata har ta birgeka kake kokarin kawo ta gidan nan ba. Shima mikewar yayi bacin Rai zaisa ki Fadi haka Amma Ni nasan wallahi ba haka bane Amira kiyi hakuri laifi ne na riga nayi na tuba Dan Allah kiyi hakuri.....mtsew ta wuce nabar maka dakin tunda Kai bazaka tafi ba. Tabar Shi Nan tsaye.
Ya dafe Kai kwalla suka zubo mishi Shi kansa yasan Yana kaunar Amira Kuma baida niyyar Kara aure, matsalar kanwar abokin sa ce yasan kaunar da yarinyar keyi mishi tun Yana saurayi da farko Yana ba yarinyar fuska ba tare da Yana tunanin zata iya like mishi haka ba, kowa yasan suna tare Yanzu idan yace bazai aure ta ba kamar yanda abokin nasa ya bukata lallai zasu Bata.
Ya zauna bisa gefen gado ya dafe Kai dole in lallaba Amira har ta sauko tabbas bazan yi auren Nan ba matukar Bata cikin kwanciyar hankali.
Ya kwashe kusan kwana biyar Yana faman lallashi kafin ya shawo kanta hakan yasa Shima ya Sami sukuni da kwanciyar hankali. Nan da Nan suka Fara hidimar aure shida ita . Ya dauketa suka tafi Kano hado lefe, ya zauna gefe yace to ki Fara zabar lesuka , tayi jimmmmm kamar zata ce dauko mun Yan dubu uku da dari biyar sai Kuma wata zuciyar ta kwabe ta da cewar kisa tsoron Allah ga wannan lamarin bazaki taba tozarta da wulakanta ba.
Ta Fara ma lesussukan kallo tana tambayar farashi har aka kawo na karshen masu kudin daga dari suka Fara, ta ce nawa za a Sanya ne? Yace yanda duk kike ganin ya Isa ni Dan kallo ne, ta dunga darzo manya manyan lesussuka tana warewa idan ta dauki red Shi sai ya dauki pink ko maroon, haka sukayi tayi har aka Gama da suturu aka koma kayan shafa da kalmomi.
Sun kashe kudi yafi miliyan uku sannan suka je gurun jakun Kuna da akwattai nan ma aka darje kusan set takwas ta daukar ma Amarya pink shi Kuma ya dauki sky blue.
Bata kawo komai cikin ranta ba, tana ta addu'o'i na Kara karfin guiywa kamar yanda mahaifiyarta ta Bata shawara.
Ita dashi aka Kai lefe, gidansu yayi wa Amarya sabon gini kusa da nata, sai dai yafi nata kyau nesa ba kusa ba saboda tsarin yabanbanta.
Sati daya saura bikin ta dawo gidansu da maraice ta tarar an fitar da kayanta duka anata fenti tayi tsaye turus, sai gashi ya fito daga gidan amaryar yace shigo kiga anyi wa Amarya jere Amira. Gabanta ya bada Ras! Da karfi ta daure tana yake tabi bayansa, na mutu.....kawai na mutu...abinda take nanatawa kenan cikin Rai ganin dukiyar da aka lafta gidan. Sai dai kwalla su cika idanunta tayi saurin mayarwa ganin yanda yake ta zakwadin nuna mata ko'ina. Jikinta yayi mugun sanyi ya kamota suka zauna babban falon Wanda suka Fara wucewa, Amira ya naga jikinki kamar yayi sanyi? Ta Dan kakaro murmushi ba komi tana faman sunkuyar da kai, yayi kasa da murya ki aminta Dani Amira tunda Kika kwantar da hankalinki tare da kwantar mun da nawa wallahi na Miki alkawarin bazan taba watsa Miki kasa a ido ba, yanda mutane suka zuba Ido suga wata baraka Basu gani ba Yanzu daga wurin ki ba wallahi bazan taba bari su gani ba.
*Wannan gidan naki ne bana amarya ba* ita gashi can ana mata fenti kayanki gasu can ana sakawa mota za a Kai wa su *Umma* ( mamar ta ).
Tayi saurin dago Kai Amma suna hada Ido sai ta rushe da kuka.....ya rungumota kiyi hakuri na Miki laifi I knew!
Ita kanta Bata San ya sunan kukan da takeyi ba Yanzu. Amma Tasha almwashin zata Kara daurewa taba maradda kunya har sai taga iya gudun ruwansa though har yau ta kasa aminta da kalaman sa tana ganin kamar yaudara ce irin da mazan yau.
Ya sungumeta zuwa dakin da Basu shiga ba Nan taga ikon Allah duk yafi dakunan kyau da girma yafi ko'ina Jin kayan alatu sannan taga akwatunan da ya saya jere sky blue yace kema ga lefenki can. Kece shaida Babu abinda na banbanta sai kala.
Ahmad da Almustapha ma nasu na tafe gobe anmun waya sun zama ready.
Ta kankame Shi ta saki wani irin kukan Dadi.....kayi hakuri abinda na maka wallahi bazan taba watsa maka kasa a ido ba.....ya Kara rike ta nasan haka Amira kiyi hakuri.
Tuni labari yakai gidan su Amarya Nan da nan maganganu suka tashi wasu na cewa ta Gama dashi wasu na cewa tsoronta yakeyi surutai kala kala har Amarya takai ga ta harzuka.........😄😄 Turkashi a tsumayi diyar Aunty Rabi (mamn ibrahim) kada a manta a ringa Sanya mun ita cikin addu'a Allah ya Kara mata yawancin kwana ya shirya Mata zuri'a da rufin asiri.
Har Yanzu babana ma Yana bukatar addu'a Allah ya bashi lafiya yaba maman mu ladar jinya.
💞 Ni din dai ce Zainab Dahiru wowo maman Abdullah 😄😄💞
🤐 WA ZAI FURTA??🤐
0⃣2⃣
*Tukuici ne ga Aunty Rabi ( maman Ibrahim) Allah ya shirya Miki zuri'a ya Kara arziki*
*KINA RAINA MAMAN WEEDAD KO DA YAUSHE*
*DOMIN KU AUREN FARI FANS ANA MUGUN TARE*
*Federal University dutsinma*
Semester tayi nisa komai yayi zafi har Yanzu Bilkisu bata Sami sakewa ba, karatun Yana mata mugun wahala, ahankali take bin su chinyere suna nuna mata abubuwa duk Wanda ta fahimci Yana da kokari zataje don Kara fahimtar abinda ya shige mata.
Su Anwar sune Yan baya ga komai, ya biye wa mashiririta yaki nuna ma kowa Shi din Mai kokari ne, masu karyar suna da kokari sai ya kwantar da kanshi Yana Jin yanda suke kwabar bayani musamman idan akazo gun lissafi.
Hankalin sa a kwance duk C.A din da akayi shine overall, Yana amsa sunan Anwar a zahiri ba Wanda yasan Shi da Hamza Yusuf a badini.
Fahimtar halin Bilkisu na rashin girman Kai yasa Shi suke gaisawa da ita sama-sama Yana son kulla mu'amula da ita Amma Yana ganin hakan a gareshi zai zubda mishi aji. Ita kuwa a gareta Sam bai ma gabanta ko kadan idan an hadu a gaisa idan ba a hadu ba Bata ko tunanin sa. Shine ma sau da yawa take Dan takura tunanin sa kadan kadan.
Ta Dan Fara sakewa da su chinyere saboda ta lura sune masu kokarin ajin, takan zauna tayi tunanin akwai department din da yakai Economics barin wuta duk makarantar? Sau da yawa tana tunanin Anya ba hausa ko Islamic zata koma ba?
Ta gama tsorata da makarantar musamman yanda taji ana bada carry over, probation da Kuma withdraw. Takan yi tunanin ai ita abun kunya ne gareta ta sami Koda carry over din ne ma hakan yasa ta Kara dagewa tana Kara naci cikin karatun ta musamman da jarabawa ta karato kullum tana library ko Kuma tare da su chinyere tana Kara koyon karatu.
Saura kwana hudu su Fara jarabawa misalin karfe hudu na marece tana zaune wani class tana faman karatu yazo wucewa kunnensa like da air piece har ya gitta said yaga kamar ita, yayi jimmm Yana tunanin ita ce ko gizo idanun sa keyi Masa kamar kullum?
Kamar kada ya dawo sai Kuma dai ya koma don tabbatarwa .....ita din daice tana ta faman Mimi da baki ya kyalkyace da dariya lokacin daya kunna Kai ajin hankalinta naga littafi har yazo ya zauna kusa da ita....tayi firgigi cike da tsoro ko da taga shine bata San lokacin da ta balla mishi harara ba.....yayi murmushi afuwan matsoraciya duk wadannan mutanen meye zai kamaki da rana gatse gatse haka? Ya karasa maganar Yana janyo littafin ta gaban sa, meye kike karantawa ayi mun bayani.
Haushi ya turnuketa domin karatun ya Fara shigar ta sosai gashi yazo zai rikita ta, Tasha mur tare da janyo littafin Dan Allah karatu nake zaka rikitani ka tashi ka bani wuri.....bazaki koya mun ba?
Nima Yanzu ai nake karantawa ta fada cikin fada fada, yayi murmushi it's alright go ahead and read ya sunkuyar dakai kawai bisa desk din. Ta ci gaba da karatun ta ba tare da ta Kara bi ta kansa ba.
Idan ta karanta sai that bude can karshen littafin ta rubuta haka haka Yana ta lura da ita duk ta dage bakin Rai bakin fama Nan da nan ya gane hadda ce takeyi. Yana so ya mata bayani Amma ya rasa ta inda zai Fara......
Tana son kamshin turaren sa ainun Anwar Dan gayu ne matuka Yana daukar wanka gashi kyakkyawa. Kamar ta karanci zuciyar say ta Dan karkato Dan Alalh wannan kalmar me take nufi? Ta sungo mishi littafin a gaban sa. Daman tun zaman sa kusa da ita ya kashe music din hakanan wayar ke jikin kunnen sa.........yayi kamar baiji me tace ba har sai da ta kalleshi sannan ya Dan zare wayar daga kunne Shi ala dole baiji me tace ba ya dan kalleta Shima kina magana ne?
Cewa nayi me wannan kalmar ke nufi? Ta nuna mishi da yatsa ....yabi hannun nata da kallo Yana kallon Zara zaran yatsun ta ya ce bari muji sentence din, Ya fada mata ma'anar kafin yace kin gane course din nan ne? Ta Dan bata rai to gashi dai Ina karantawa...... Ya Kara janyo littafin gaban sa ya budo shafin farko...... Kin San fa abun duk labari ne Kinga.......ya Fara mata bayani a hankali ahankali Nan da nan ta Fara fahimta sosai saboda bayanin nasa duk da hausa yake mata. Haka haka har ya gama mata littafin. Taji dadi sosai da sosai ta fadada fara'ar ta ohhhhh Ashe ka Gama covering komai ko???.......a'a fa nima kawai na gane darasin ne lokacin da yake bayani a class.....Amma wallahi ka iya bayani saboda har kafi malamin ma iyawa....ya danyi dariya tinda na Miki bayani da hausa ko? Ta kyalkyace da dariya yabi fuskar ta ta Yana Kara kallo ta bude jakar ta to Dan Allah ka gane wannan math din? Ta fiddo littafin. Dariya kawai yake cikin Rai Amma a zahiri yadan basar.......ya kalli littafin, gaskiya ban iya Shi ba Amma ki bari yau sanje dakin wani dan aji hudu ya koya mun gobe sai mu hadu in nuna Miki......da karfe nawa? Ta katse shi, Yayi murmushi duk lokacin da kike so goben....... 8:00am Zan jiraka anan.
Ya zaro ido 8? Gaskiya sai dai 4 saboda barci bazai barni na fito da wuri ba.
Kamar zatayi magana sai Kuma ta fasa ta ce Allah ya kaimu lafiya tare da janye littafin yabi Dan karamin bakin ta da kallo har ta sunkuya.
Ta Mike tana kokarin sagala jaka ta kalleshi tana murmushi Dan Allah ka koya da kyau Zan jiraka anan din goben in shaa Allah.
Yace ba damuwa.....see you then. Ta wuce.
Yabi ta da kallo kamar ya rufa mata baya amma Shi kansa yasan bazai iya hakan ba ( saboda gadara ).
Zuciyarta Fara fes! Ta isa daki taji dadin bayanin Anwar matuka.
Washe gari tana fitowa masallaci ta wuce class din kamar yanda sukayi alkawari, ta fiddo wani course theory ta Fara karantawa kafin ya iso. Ta nayi tana Dan kallon taga tare da duba agogon wayarta har kusan hudu da arba'in.
*Anwar* kuwa Yana can Yana shakar barci abinsa sammm ya manta da maganar su.
Allah ya taimaketa kawai sai ga su chinyere sun shigo karatu Suma Kuma cikin sa'a statistics din zasuyi solving sai kawai tayi joining suka Fara.
Tana yi tana tunanin watakila Anwar bai iya bane Yana Jin kunyar zuwa....ta tabe baki to meye na karyar zaije ya koya bayan yasan bashi da wani kokari....mtsew taja guntun tsoki.
Bai farka ba sai shidda saura ya tashi a hargitse ga takaicin lokacin sallah ya shige ga Kuma tunanin sabawa Bilkisu alkawari da yayi.
A gurguje ya watsa ruwa yayi sallah ya fito da sauri.
Ya shawo kwana ita Kuma ta fito ajin zata tafi. Tana hango Shi tayi sauri bi ta dayan side din tabayan azuzuwa tayi hanyar fita gate sauri sauri.....tana tunanin watakila Yana can Yana faman koyo don yazo ya birgeta..tayi tsoki to karya tame ne?
A hargitse ya shiga ajin sai wurge wurgen ido yakeyi girman Kai da nuna Isa sun Hana ya tambayi su chinyere ko sun ganta. Rai bace ya fita Nan ya Fara bin azuzuwa neman ta.
Helen ta tabe baki I don't like this Anwar honestly.... Mtsew don't mind idiot abeg inji chinyere Nan gulma ta tashi.
Ya cika girman Kai da nuna Shi wani ne, baya yi ma kowa magana sai abokansa uku. Surutai kala kala saboda Shi din Daman baida farin jini a class din tun zuwansu Wai ya cika fadin Rai da gadara.
Tunda ga ranar bai Kara Sanya Bilkisu a ido ba yayi neman har ya gaji gashi baida no. Ta bai Kuma San Wanda zai tambaya ya bashi ba haka Kuma baisan accommodation dinta ba hostel take ko off campus. Wasa wasa abun ya Dan dameshi.
Ranar da zasu Fara jarabawa da yake ta karfe uku ce tun biyu saura yake hall din Yana so ya ganta, ita kuwa tun 8 tana library sai biyu da Rabi ta fito bayan tayo sallah. Kansa sunkuye baiga shigowar taba har ta zauna bayansa.
Lallai Anwar ka kyauta shine ka shanya ni rannan ko? To kayi dai dai ta fada tana faman hararar sa .
Da sauri ya dago Kai zaiyi magana kenan invigilators suka shigo tare da fadin everybody out..ta rigashi fita, ko da aka Fara shiga ma tayi saurin fadawa don Zama gaba gaba.
Alhamdulillah jarabawar ta mata dadi ainun domin duk abinda ta karanta suka fito.
Ita ce ta biyar din bayarwa ( submitting ) bata jira kowa ba tayi masallaci don gabatar da la'asar saboda lokacin biyar da kusan ashirin.
G
Haka semester din ta kare ba tare da sun Kara haduwa da Anwar ba, ko kadan Bata yarda su hadu tasan karya zai shirga mata don kare kansa.
Shi Dan garin Kano ne ita Kuma Abuja mahaifinta ke aiki Amma asalin su Yan katsina ne.
Washegarin da suka Gama jarabawa tabar garin Anwar kuwa karfe biyar na ranar yabar dutsinma.
Hutun baida tsawo sati biyu akayi aka dawo. Sun dawo da sati daya aka saki result a *portal* Murna tsalle ga Bilkisu saboda ta cinye ko wane Bata da carry over ko daya ga point dinta 4.33
Hakan ba karamin dadi yayiwa Yan gidan su da iyayenta ba.
Anwar kuwa 5:00 dai dai ya samu saboda duka courses din da sukayi goma Sha daya ko wane *A* yaci. Yaja bakin sa ya tsuke.
A cikin ajin kowa nata fadin result din sa daga Mai 4 point sai masu 3 point da abubuwa. Duk Wanda ya tambayi Bilkisu sai ta ce lafiya Lau ne ni Daman carry over ke bani so to ban samu ba. Bata yarda ta fada ma kowa result dinta ba. Tana zaune an gama lecture din wani mugun malami ta kura ma dan rubutun da tayi ido tana nazarin ya zata ci jarabawa da Dan wannan rubutun? Suleiman ya mata sallama.
Suleiman matashi ne Shima a cikin ajin Mai natsuwa da son addini babancin say da Anwar yafi Anwar saukin Kai da yarinta. Ya zauna kusa da ita bayan ta amsa sallamar Dan Allah Hajiya Bilkisu na kasa bude portal dina ya akeyi ne?
Tayi murmushi Ina wayar taka in nuna maka?
Wallahi daki na barta ki nuna mun da taki.......hankalin Anwar na kansu haka kawai sai yaji ya tsani Suleiman karon farko a rayuwar sa.
Ta fiddo wayar tare da tambayar sa password da matric number.
Portal din na budewa ta Mika mishi wayar kaga inda zaka Danna..... Ya danyi dariya to bude Mana ai ba komai don kin gani. Ta kalleshi tana mamaki saboda tasan Portal sirrin dalibi ne ba kowa kake yarda ka nuna mawa ba. Ya Kara Yar dariya ki bude ba komi. Ki gane mun Ina da carry over?
Ta ce to a sanyaye tana mamakin irin warda da yayi mata farat daya zuciyar ta cike da Jin dadi tare da ganin kimar say da mutunci.
Kaiiii....ta fada tare da zaro ido ka Fadi accounting. Sai kawai yayi murmushi nasan za'a rina sai wane? Ka Fadi GST English Shikenan. Nawa ne point dina? Ta duba can kasa tana warware ido..... Okay gashi Nan 2.65. Ta kalleshi, amma Suleiman me yasa ka yarda dani haka?......Au kin San sunana kenan? Ya fada Yana kallonta cike da mamaki, tayi murmushi eh Mana nasan sunan ka Suleiman.
Ina fatan ke dai lafiya lau ko? Sai kawai ta budo mishi portal din ta tace kaga nawa.
Ya zaro ido kaiiiiiii...... Ta danyi murmushi Amma bana son Dan Allah ka fadawa kowa result dina.
Ya Jin jina Kai in shaa Allah Zaki sameni Mai rike sirrin ki, amma Bilkisu kinyi wuta da yawa fa!
Ta yi Yar dariya kawai.
Allah yasa albarka. Kiban no. Ki dan Allah ko da wani Abu Yana tasowa Kuma idan bazaki damu ba Zan ringa matsowa kina tasar Dani inda ban ganewa.
Ba matsala ga number rubuta........
A harzuke Anwar yabar class din tunda ga ranar sai kawai yayi baya da ita ko gaisuwa baya son suyi cikin kankanin lokaci ta Saba da Suleiman ta fahimci Yana da saukin Kai bashi da girman Kai sannan Yana da addini tare da daratta mutane.
Ko da ya gane Bilkisu nada kokari sai ya like mata ko C.A zasuyi Yana manne kusa da ita baya yarda tayi mishi nisa.
Ko kadan Bata da mugunta duk amsar da ta kakare mishi zata bashi ya kwashe tsaf!.
Akwai wani course Mai matukar wahala gashi three credit unit ne Kuma calculation Mai rikitarwa kowa Yana Jin course din. Anwar yayi burus da ita Yana Jin kowa na kokawa Amma ya ki nuna ya iya. Kwana takeyi karatu da salloli, Ranar jarabawar course din ana ta jera layi kawai malamin yace ta zauna can, hankalin ta ya tashi ganin ya cillata gaba don yau baya take son Zama saboda ta Sami taimakon wani.
Tana Zama sai taga Anwar ne a gaban ta, ita dai kawai sai addu'a takeyi tasan yau sai Allah da malaman gari. Tambayoyi bakwai be a amsa biyar tambaya ta farko dole ce gata da 'ya'ya har goma.
Saura kadan ta kurma ihu saboda duka tambayoyin guda daya ne kawai ta sani itama theory ne ba calculation ba.
Idanun ta suka kawo ruwa, taga tunda Anwar ya duke bai dago ba, hall din yayi tsit! Ta yi zugummm, zuwa can kawai ta Fara amsa wacce ta sani.
Mafi yawancin malaman dake tsaron nasu duk sun maida hankali wurin Yan baya. Haka ta dunga rubutu Dan Allah yasa ta Sami Koda *E* ne a course din ta wuce wurin.
Tana gamawa tayi zugummm kawai tana fargaba.
Yadan waigo kadan ganin malaman basa kusa yace kin iya question one naga tana da wahala fa.
Tayi kasa da murya wallahi question 4 kadai na iya cikin bakwai din nan ga Shi ta farkon naga 30marks ne.
Ya dan gyara zaman sa kadan tare da kango mata booklet din sa yace kiyi sauri ki kwasa.
Habaaaaa.....ga bilkiyda saurin rubutu gata very smart. Duba daya sai ta kwaso layi biyu. Cikin sauri ta gama shafin tace juya....Shi kansa yayi mamaki yace ke duba da kyaufa kada kiyi shirme. Wallahi na gama ka juya kawai.
Haka ya bata dukan sauran question hudun da bata iya ba.
Sai da ya tabbatar ta Gama tsaf sannan yaci gaba da amsa Shima question 4 din da tace tayi.
Ta Dan waiga ta hango Suleiman can baya an cillashi sai zare ido yakeyi.
Duk Wanda ka kallo zakaga ko Yana zufa ko Yana ta raba ido.
Kije kiyi submitting...ya fada kasa kasa ta ce toh.
Kowa sai kallonta yakeyi Yana mamakin yanda zata bayar da wuri haka, Wasu na tunanin kawai ta gaji ne da zama kamar yanda Suma suke zaune, tafi mintuna talatin kafin wasu tsirara suka Fara fitowa duk Wanda ya fito idanu jawur ana tsinar malamin kusan kowa ya sadakas da kawai faduwa zaiyi course din saboda rashin iya amsawa. Suleiman kawai take jira ya fito sai kuwa gashi Yana ganinta yace, Bilkisuuu..... Yau naji wuta wallahi Allah dai ya kyauta Amma question biyu kawai nake da tabbaci cikin sauran.
Tabbb....wallahi ni Allah ya taimakeni Anwar ya bani duka Wanda ban sani ba....hada question one?
Eh Mana.
Wai da gaske kike?
Wallahi kuwa.
To Ina Jin keda shine kawai kuka amsa ta don ko su chinyere gasu can suna cewa Basu gane ba.......Allah dai ya kyauta ta fada tare da cewa sai gobe ta ruga hango Anwar yayi hanyar *Gate* Yana ta faman sauri.
Anwar.. ta kwada mishi Kira, yasan za a rina Shi yasa yaso ma kada su hadu.
Ya Dan tsaya Yana murmushi , ya jarabawar Bilkisu ya fada Yana latsa waya.
Hmmm jarabawa yau Allah ya rufa man asiri bacin Kai ai Dana shiga uku. Na gode na gode Allah ya Kara ilimi......Daman ka iya course din sosai haka? Naga yanda ake ta kuka dashi Kai komai ka amsa.....hatta jamilu ma naga naka yake kwafa ( copying ).
Murmushi kawai yayi yace ba damuwa.
Ya wuce kawai. Ta bishi da ido. Anwar...ta Kara kwada mishi Kira.....ya juyo wallahi na gode kaji?
Sai kawai ya kyalkyace da dariya ya juya abinsa.
Taji dadi sosai da sosai a Ranar domin course din kadai kowa ke kuka dashi wannan semester din.
Hutun ya kasance dogo akalle ankwashe watanni biyu a gida kafin a dawo aji biyu.( Su Bilkisu an Fara manyanta ) wannan karon suna gida result ya fita inda take da 4.22 ta Dan sauko kadan saboda ansha wahala matuka Shi Kuma Suleiman Yana da 2.72 Amma ya Sami carry over daya.
Sun koma da makaranta da sati biyu akayi *convocation* tare da bayar da kyaututta ga first class da over all.
Bata halarci wurin ba. Saboda ba kowa ya maida hankali ga taron ba. Hakan yasa Anwar zuwa tare da karbar five pointer award da Kuma overall student na aji daya da suka gama.
Kamar munafuki ya karba sim sim sim yayi saurin barin hall din ganin babu alamun Yan ajin su ko wani Wanda ya sanshi. Ashe Suleiman yana wurin.
Ba karamin mamaki yayi ba watan Anwar shine *Hamza Yusuf* din da ake nema cikin class Amma wallahi sai ya fadawa Bilkisu.................
*************
*KADUNA RIGASA*
Yana ta mamakin yanda ummi ta mishi text tana son ganin sa alhalin bata taba hakan ba.
Yana zaune babban falon gidan nasu an cika gaban sa da kayan ciye ciye da lemuka kamar kullum ta shigo tana ta faman Bata rai .
Ya kalleta tana ta faman karairaye karairaye......Amarya bakya laifi ko kin kashe Ahmad ( Babban yaron sa ) ya fada cikin zolaya Yana Yar dariya hannun sa rike da samosa mutumen shi Yana ci.
Banga alama ba, ta fada tana taunar cingam.
Ya kalleta jin maganar ta fito gatsal....
Kamar Yaya?, Ya bukata.
Kamar yanda kaji.
Kamar yanda naji?
Ya maimaita cike da mamaki kafin ya ajiye guntun samosan bisa plate ya tattara hankalin sa duka wurin ta.....me ke faruwa ne ummi?
Tayi shiru!
Dake nake magana...me ya faru?
Ta gyara Zama, Ina ce apartment din da kayi sabo Ni ka gina mawa Amma labari yazo cewa Aunty Amira ta koma....... Ke ya daka mata tsawa.
Nan da nan ya harzuka, Ni na fada Miki Ina Miki gini?
Gabanta ya fadi tayi tsuru tsuru, kinji? Munyi dake Ina Miki gini?
Okay ita da Zaki aure Mata miji Bata kawo mun matsala ba sai kece Zaki fara kawo mun tsirfa? Saurara da kyau ya Mike tsaye Yana nuna ta yatsa wallahi matukar kina son Zama dani tare da Jin dadi sai kin daratta Amira kin mun biyayya kin Mata bazan dauki sakarci ko kadan ba.
Dukkan ku Ina sonku to dole kowace tabi ra'ayi na, idan Kika saki na gane kina da matsala to wallahi zakiji ba dadi.
Mtsew ya buga tsaki ya wuce.......ta yi zuruuuuu tana zare ido lallai ta gwada Bata ji dadi ba.
Kwallah suka zubo Mata. Ta buga ma babbar yayar su waya domin ita ce abokiyar shawarar ta .....salati ta kamayi ubanwa ya aike ki? Ai kinyi sauri bari zakiyi sai kinje gidan yasan dadin ki lokacin yazo hannu tukun Amma Yanzu ai lallaba matar sa yakeyi tunda ya Mata laifi.
Ki bari Zan baki ahawarwari idan na shigo gobe.
Tun daga ranar Bata Kara Sanya Shi a ido ba. Tuni a Mata hudubar kada ta saki ta dauki raini ga matar sa Kuma idan ta a gidan ta Sami damar juya Shi yanda zata amshe ragamar komai.
Babu yanda ba a yi dashi ba ko kamu ayi yace bai son bidi'a ba Dan komai ba kada ma akirkiri partyn Amira taji ba dadi.
Ranar walima akayi mashi Sha Tara ta arziki hada mota.
Yana falon sa zaune yaji marokiya na sanarwa. Shima ya Mike ya kirawo marokiyar ya bada makullin mota kirar *GLK* baka 2019 model ta kusan miliyan Tara yace yaba Amira ayi sanarwa.
Nan dangin Amarya kuwa suka Fara surutai............
Ko ajikin sa. Dangin ango dana Amirai kuwa suka Fara rangada guda suna tayata Murna.
Hakan ba karamin harzuka Amarya da danginta yayi ba. Nan suka Kara hure Mata kunnen wallahi sai ta tashi tsaye Dan kwato ma kanta yanci.
Kuka takeyi wuiwui.
Kafin karfe shida gida ba kowa duk an tafi.
Ana gama sallar isha'i ya ja Amarya zuwa sashen Amira don yi masu huduba.......
*Ayi hakuri da typing error please yanayin typing din ne saboda kawai ta WhatsApp nake yi Kuma gaskiya bana bi idan na Gama kawai nake turawa.
*Daga zainab wowo*💞💕💗😄✍🏼🤐 WA ZAI FURTA??🤐
0⃣2⃣
*Tukuici ne ga Aunty Rabi ( maman Ibrahim) Allah ya shirya Miki zuri'a ya Kara arziki*
*KINA RAINA MAMAN WEEDAD KO DA YAUSHE*
*DOMIN KU AUREN FARI FANS ANA MUGUN TARE*
*Federal University dutsinma*
Semester tayi nisa komai yayi zafi har Yanzu Bilkisu bata Sami sakewa ba, karatun Yana mata mugun wahala, ahankali take bin su chinyere suna nuna mata abubuwa duk Wanda ta fahimci Yana da kokari zataje don Kara fahimtar abinda ya shige mata.
Su Anwar sune Yan baya ga komai, ya biye wa mashiririta yaki nuna ma kowa Shi din Mai kokari ne, masu karyar suna da kokari sai ya kwantar da kanshi Yana Jin yanda suke kwabar bayani musamman idan akazo gun lissafi.
Hankalin sa a kwance duk C.A din da akayi shine overall, Yana amsa sunan Anwar a zahiri ba Wanda yasan Shi da Hamza Yusuf a badini.
Fahimtar halin Bilkisu na rashin girman Kai yasa Shi suke gaisawa da ita sama-sama Yana son kulla mu'amula da ita Amma Yana ganin hakan a gareshi zai zubda mishi aji. Ita kuwa a gareta Sam bai ma gabanta ko kadan idan an hadu a gaisa idan ba a hadu ba Bata ko tunanin sa. Shine ma sau da yawa take Dan takura tunanin sa kadan kadan.
Ta Dan Fara sakewa da su chinyere saboda ta lura sune masu kokarin ajin, takan zauna tayi tunanin akwai department din da yakai Economics barin wuta duk makarantar? Sau da yawa tana tunanin Anya ba hausa ko Islamic zata koma ba?
Ta gama tsorata da makarantar musamman yanda taji ana bada carry over, probation da Kuma withdraw. Takan yi tunanin ai ita abun kunya ne gareta ta sami Koda carry over din ne ma hakan yasa ta Kara dagewa tana Kara naci cikin karatun ta musamman da jarabawa ta karato kullum tana library ko Kuma tare da su chinyere tana Kara koyon karatu.
Saura kwana hudu su Fara jarabawa misalin karfe hudu na marece tana zaune wani class tana faman karatu yazo wucewa kunnensa like da air piece har ya gitta said yaga kamar ita, yayi jimmm Yana tunanin ita ce ko gizo idanun sa keyi Masa kamar kullum?
Kamar kada ya dawo sai Kuma dai ya koma don tabbatarwa .....ita din daice tana ta faman Mimi da baki ya kyalkyace da dariya lokacin daya kunna Kai ajin hankalinta naga littafi har yazo ya zauna kusa da ita....tayi firgigi cike da tsoro ko da taga shine bata San lokacin da ta balla mishi harara ba.....yayi murmushi afuwan matsoraciya duk wadannan mutanen meye zai kamaki da rana gatse gatse haka? Ya karasa maganar Yana janyo littafin ta gaban sa, meye kike karantawa ayi mun bayani.
Haushi ya turnuketa domin karatun ya Fara shigar ta sosai gashi yazo zai rikita ta, Tasha mur tare da janyo littafin Dan Allah karatu nake zaka rikitani ka tashi ka bani wuri.....bazaki koya mun ba?
Nima Yanzu ai nake karantawa ta fada cikin fada fada, yayi murmushi it's alright go ahead and read ya sunkuyar dakai kawai bisa desk din. Ta ci gaba da karatun ta ba tare da ta Kara bi ta kansa ba.
Idan ta karanta sai that bude can karshen littafin ta rubuta haka haka Yana ta lura da ita duk ta dage bakin Rai bakin fama Nan da nan ya gane hadda ce takeyi. Yana so ya mata bayani Amma ya rasa ta inda zai Fara......
Tana son kamshin turaren sa ainun Anwar Dan gayu ne matuka Yana daukar wanka gashi kyakkyawa. Kamar ta karanci zuciyar say ta Dan karkato Dan Alalh wannan kalmar me take nufi? Ta sungo mishi littafin a gaban sa. Daman tun zaman sa kusa da ita ya kashe music din hakanan wayar ke jikin kunnen sa.........yayi kamar baiji me tace ba har sai da ta kalleshi sannan ya Dan zare wayar daga kunne Shi ala dole baiji me tace ba ya dan kalleta Shima kina magana ne?
Cewa nayi me wannan kalmar ke nufi? Ta nuna mishi da yatsa ....yabi hannun nata da kallo Yana kallon Zara zaran yatsun ta ya ce bari muji sentence din, Ya fada mata ma'anar kafin yace kin gane course din nan ne? Ta Dan bata rai to gashi dai Ina karantawa...... Ya Kara janyo littafin gaban sa ya budo shafin farko...... Kin San fa abun duk labari ne Kinga.......ya Fara mata bayani a hankali ahankali Nan da nan ta Fara fahimta sosai saboda bayanin nasa duk da hausa yake mata. Haka haka har ya gama mata littafin. Taji dadi sosai da sosai ta fadada fara'ar ta ohhhhh Ashe ka Gama covering komai ko???.......a'a fa nima kawai na gane darasin ne lokacin da yake bayani a class.....Amma wallahi ka iya bayani saboda har kafi malamin ma iyawa....ya danyi dariya tinda na Miki bayani da hausa ko? Ta kyalkyace da dariya yabi fuskar ta ta Yana Kara kallo ta bude jakar ta to Dan Allah ka gane wannan math din? Ta fiddo littafin. Dariya kawai yake cikin Rai Amma a zahiri yadan basar.......ya kalli littafin, gaskiya ban iya Shi ba Amma ki bari yau sanje dakin wani dan aji hudu ya koya mun gobe sai mu hadu in nuna Miki......da karfe nawa? Ta katse shi, Yayi murmushi duk lokacin da kike so goben....... 8:00am Zan jiraka anan.
Ya zaro ido 8? Gaskiya sai dai 4 saboda barci bazai barni na fito da wuri ba.
Kamar zatayi magana sai Kuma ta fasa ta ce Allah ya kaimu lafiya tare da janye littafin yabi Dan karamin bakin ta da kallo har ta sunkuya.
Ta Mike tana kokarin sagala jaka ta kalleshi tana murmushi Dan Allah ka koya da kyau Zan jiraka anan din goben in shaa Allah.
Yace ba damuwa.....see you then. Ta wuce.
Yabi ta da kallo kamar ya rufa mata baya amma Shi kansa yasan bazai iya hakan ba ( saboda gadara ).
Zuciyarta Fara fes! Ta isa daki taji dadin bayanin Anwar matuka.
Washe gari tana fitowa masallaci ta wuce class din kamar yanda sukayi alkawari, ta fiddo wani course theory ta Fara karantawa kafin ya iso. Ta nayi tana Dan kallon taga tare da duba agogon wayarta har kusan hudu da arba'in.
*Anwar* kuwa Yana can Yana shakar barci abinsa sammm ya manta da maganar su.
Allah ya taimaketa kawai sai ga su chinyere sun shigo karatu Suma Kuma cikin sa'a statistics din zasuyi solving sai kawai tayi joining suka Fara.
Tana yi tana tunanin watakila Anwar bai iya bane Yana Jin kunyar zuwa....ta tabe baki to meye na karyar zaije ya koya bayan yasan bashi da wani kokari....mtsew taja guntun tsoki.
Bai farka ba sai shidda saura ya tashi a hargitse ga takaicin lokacin sallah ya shige ga Kuma tunanin sabawa Bilkisu alkawari da yayi.
A gurguje ya watsa ruwa yayi sallah ya fito da sauri.
Ya shawo kwana ita Kuma ta fito ajin zata tafi. Tana hango Shi tayi sauri bi ta dayan side din tabayan azuzuwa tayi hanyar fita gate sauri sauri.....tana tunanin watakila Yana can Yana faman koyo don yazo ya birgeta..tayi tsoki to karya tame ne?
A hargitse ya shiga ajin sai wurge wurgen ido yakeyi girman Kai da nuna Isa sun Hana ya tambayi su chinyere ko sun ganta. Rai bace ya fita Nan ya Fara bin azuzuwa neman ta.
Helen ta tabe baki I don't like this Anwar honestly.... Mtsew don't mind idiot abeg inji chinyere Nan gulma ta tashi.
Ya cika girman Kai da nuna Shi wani ne, baya yi ma kowa magana sai abokansa uku. Surutai kala kala saboda Shi din Daman baida farin jini a class din tun zuwansu Wai ya cika fadin Rai da gadara.
Tunda ga ranar bai Kara Sanya Bilkisu a ido ba yayi neman har ya gaji gashi baida no. Ta bai Kuma San Wanda zai tambaya ya bashi ba haka Kuma baisan accommodation dinta ba hostel take ko off campus. Wasa wasa abun ya Dan dameshi.
Ranar da zasu Fara jarabawa da yake ta karfe uku ce tun biyu saura yake hall din Yana so ya ganta, ita kuwa tun 8 tana library sai biyu da Rabi ta fito bayan tayo sallah. Kansa sunkuye baiga shigowar taba har ta zauna bayansa.
Lallai Anwar ka kyauta shine ka shanya ni rannan ko? To kayi dai dai ta fada tana faman hararar sa .
Da sauri ya dago Kai zaiyi magana kenan invigilators suka shigo tare da fadin everybody out..ta rigashi fita, ko da aka Fara shiga ma tayi saurin fadawa don Zama gaba gaba.
Alhamdulillah jarabawar ta mata dadi ainun domin duk abinda ta karanta suka fito.
Ita ce ta biyar din bayarwa ( submitting ) bata jira kowa ba tayi masallaci don gabatar da la'asar saboda lokacin biyar da kusan ashirin.
G
Haka semester din ta kare ba tare da sun Kara haduwa da Anwar ba, ko kadan Bata yarda su hadu tasan karya zai shirga mata don kare kansa.
Shi Dan garin Kano ne ita Kuma Abuja mahaifinta ke aiki Amma asalin su Yan katsina ne.
Washegarin da suka Gama jarabawa tabar garin Anwar kuwa karfe biyar na ranar yabar dutsinma.
Hutun baida tsawo sati biyu akayi aka dawo. Sun dawo da sati daya aka saki result a *portal* Murna tsalle ga Bilkisu saboda ta cinye ko wane Bata da carry over ko daya ga point dinta 4.33
Hakan ba karamin dadi yayiwa Yan gidan su da iyayenta ba.
Anwar kuwa 5:00 dai dai ya samu saboda duka courses din da sukayi goma Sha daya ko wane *A* yaci. Yaja bakin sa ya tsuke.
A cikin ajin kowa nata fadin result din sa daga Mai 4 point sai masu 3 point da abubuwa. Duk Wanda ya tambayi Bilkisu sai ta ce lafiya Lau ne ni Daman carry over ke bani so to ban samu ba. Bata yarda ta fada ma kowa result dinta ba. Tana zaune an gama lecture din wani mugun malami ta kura ma dan rubutun da tayi ido tana nazarin ya zata ci jarabawa da Dan wannan rubutun? Suleiman ya mata sallama.
Suleiman matashi ne Shima a cikin ajin Mai natsuwa da son addini babancin say da Anwar yafi Anwar saukin Kai da yarinta. Ya zauna kusa da ita bayan ta amsa sallamar Dan Allah Hajiya Bilkisu na kasa bude portal dina ya akeyi ne?
Tayi murmushi Ina wayar taka in nuna maka?
Wallahi daki na barta ki nuna mun da taki.......hankalin Anwar na kansu haka kawai sai yaji ya tsani Suleiman karon farko a rayuwar sa.
Ta fiddo wayar tare da tambayar sa password da matric number.
Portal din na budewa ta Mika mishi wayar kaga inda zaka Danna..... Ya danyi dariya to bude Mana ai ba komai don kin gani. Ta kalleshi tana mamaki saboda tasan Portal sirrin dalibi ne ba kowa kake yarda ka nuna mawa ba. Ya Kara Yar dariya ki bude ba komi. Ki gane mun Ina da carry over?
Ta ce to a sanyaye tana mamakin irin warda da yayi mata farat daya zuciyar ta cike da Jin dadi tare da ganin kimar say da mutunci.
Kaiiii....ta fada tare da zaro ido ka Fadi accounting. Sai kawai yayi murmushi nasan za'a rina sai wane? Ka Fadi GST English Shikenan. Nawa ne point dina? Ta duba can kasa tana warware ido..... Okay gashi Nan 2.65. Ta kalleshi, amma Suleiman me yasa ka yarda dani haka?......Au kin San sunana kenan? Ya fada Yana kallonta cike da mamaki, tayi murmushi eh Mana nasan sunan ka Suleiman.
Ina fatan ke dai lafiya lau ko? Sai kawai ta budo mishi portal din ta tace kaga nawa.
Ya zaro ido kaiiiiiii...... Ta danyi murmushi Amma bana son Dan Allah ka fadawa kowa result dina.
Ya Jin jina Kai in shaa Allah Zaki sameni Mai rike sirrin ki, amma Bilkisu kinyi wuta da yawa fa!
Ta yi Yar dariya kawai.
Allah yasa albarka. Kiban no. Ki dan Allah ko da wani Abu Yana tasowa Kuma idan bazaki damu ba Zan ringa matsowa kina tasar Dani inda ban ganewa.
Ba matsala ga number rubuta........
A harzuke Anwar yabar class din tunda ga ranar sai kawai yayi baya da ita ko gaisuwa baya son suyi cikin kankanin lokaci ta Saba da Suleiman ta fahimci Yana da saukin Kai bashi da girman Kai sannan Yana da addini tare da daratta mutane.
Ko da ya gane Bilkisu nada kokari sai ya like mata ko C.A zasuyi Yana manne kusa da ita baya yarda tayi mishi nisa.
Ko kadan Bata da mugunta duk amsar da ta kakare mishi zata bashi ya kwashe tsaf!.
Akwai wani course Mai matukar wahala gashi three credit unit ne Kuma calculation Mai rikitarwa kowa Yana Jin course din. Anwar yayi burus da ita Yana Jin kowa na kokawa Amma ya ki nuna ya iya. Kwana takeyi karatu da salloli, Ranar jarabawar course din ana ta jera layi kawai malamin yace ta zauna can, hankalin ta ya tashi ganin ya cillata gaba don yau baya take son Zama saboda ta Sami taimakon wani.
Tana Zama sai taga Anwar ne a gaban ta, ita dai kawai sai addu'a takeyi tasan yau sai Allah da malaman gari. Tambayoyi bakwai be a amsa biyar tambaya ta farko dole ce gata da 'ya'ya har goma.
Saura kadan ta kurma ihu saboda duka tambayoyin guda daya ne kawai ta sani itama theory ne ba calculation ba.
Idanun ta suka kawo ruwa, taga tunda Anwar ya duke bai dago ba, hall din yayi tsit! Ta yi zugummm, zuwa can kawai ta Fara amsa wacce ta sani.
Mafi yawancin malaman dake tsaron nasu duk sun maida hankali wurin Yan baya. Haka ta dunga rubutu Dan Allah yasa ta Sami Koda *E* ne a course din ta wuce wurin.
Tana gamawa tayi zugummm kawai tana fargaba.
Yadan waigo kadan ganin malaman basa kusa yace kin iya question one naga tana da wahala fa.
Tayi kasa da murya wallahi question 4 kadai na iya cikin bakwai din nan ga Shi ta farkon naga 30marks ne.
Ya dan gyara zaman sa kadan tare da kango mata booklet din sa yace kiyi sauri ki kwasa.
Habaaaaa.....ga bilkiyda saurin rubutu gata very smart. Duba daya sai ta kwaso layi biyu. Cikin sauri ta gama shafin tace juya....Shi kansa yayi mamaki yace ke duba da kyaufa kada kiyi shirme. Wallahi na gama ka juya kawai.
Haka ya bata dukan sauran question hudun da bata iya ba.
Sai da ya tabbatar ta Gama tsaf sannan yaci gaba da amsa Shima question 4 din da tace tayi.
Ta Dan waiga ta hango Suleiman can baya an cillashi sai zare ido yakeyi.
Duk Wanda ka kallo zakaga ko Yana zufa ko Yana ta raba ido.
Kije kiyi submitting...ya fada kasa kasa ta ce toh.
Kowa sai kallonta yakeyi Yana mamakin yanda zata bayar da wuri haka, Wasu na tunanin kawai ta gaji ne da zama kamar yanda Suma suke zaune, tafi mintuna talatin kafin wasu tsirara suka Fara fitowa duk Wanda ya fito idanu jawur ana tsinar malamin kusan kowa ya sadakas da kawai faduwa zaiyi course din saboda rashin iya amsawa. Suleiman kawai take jira ya fito sai kuwa gashi Yana ganinta yace, Bilkisuuu..... Yau naji wuta wallahi Allah dai ya kyauta Amma question biyu kawai nake da tabbaci cikin sauran.
Tabbb....wallahi ni Allah ya taimakeni Anwar ya bani duka Wanda ban sani ba....hada question one?
Eh Mana.
Wai da gaske kike?
Wallahi kuwa.
To Ina Jin keda shine kawai kuka amsa ta don ko su chinyere gasu can suna cewa Basu gane ba.......Allah dai ya kyauta ta fada tare da cewa sai gobe ta ruga hango Anwar yayi hanyar *Gate* Yana ta faman sauri.
Anwar.. ta kwada mishi Kira, yasan za a rina Shi yasa yaso ma kada su hadu.
Ya Dan tsaya Yana murmushi , ya jarabawar Bilkisu ya fada Yana latsa waya.
Hmmm jarabawa yau Allah ya rufa man asiri bacin Kai ai Dana shiga uku. Na gode na gode Allah ya Kara ilimi......Daman ka iya course din sosai haka? Naga yanda ake ta kuka dashi Kai komai ka amsa.....hatta jamilu ma naga naka yake kwafa ( copying ).
Murmushi kawai yayi yace ba damuwa.
Ya wuce kawai. Ta bishi da ido. Anwar...ta Kara kwada mishi Kira.....ya juyo wallahi na gode kaji?
Sai kawai ya kyalkyace da dariya ya juya abinsa.
Taji dadi sosai da sosai a Ranar domin course din kadai kowa ke kuka dashi wannan semester din.
Hutun ya kasance dogo akalle ankwashe watanni biyu a gida kafin a dawo aji biyu.( Su Bilkisu an Fara manyanta ) wannan karon suna gida result ya fita inda take da 4.22 ta Dan sauko kadan saboda ansha wahala matuka Shi Kuma Suleiman Yana da 2.72 Amma ya Sami carry over daya.
Sun koma da makaranta da sati biyu akayi *convocation* tare da bayar da kyaututta ga first class da over all.
Bata halarci wurin ba. Saboda ba kowa ya maida hankali ga taron ba. Hakan yasa Anwar zuwa tare da karbar five pointer award da Kuma overall student na aji daya da suka gama.
Kamar munafuki ya karba sim sim sim yayi saurin barin hall din ganin babu alamun Yan ajin su ko wani Wanda ya sanshi. Ashe Suleiman yana wurin.
Ba karamin mamaki yayi ba watan Anwar shine *Hamza Yusuf* din da ake nema cikin class Amma wallahi sai ya fadawa Bilkisu.................
*************
*KADUNA RIGASA*
Yana ta mamakin yanda ummi ta mishi text tana son ganin sa alhalin bata taba hakan ba.
Yana zaune babban falon gidan nasu an cika gaban sa da kayan ciye ciye da lemuka kamar kullum ta shigo tana ta faman Bata rai .
Ya kalleta tana ta faman karairaye karairaye......Amarya bakya laifi ko kin kashe Ahmad ( Babban yaron sa ) ya fada cikin zolaya Yana Yar dariya hannun sa rike da samosa mutumen shi Yana ci.
Banga alama ba, ta fada tana taunar cingam.
Ya kalleta jin maganar ta fito gatsal....
Kamar Yaya?, Ya bukata.
Kamar yanda kaji.
Kamar yanda naji?
Ya maimaita cike da mamaki kafin ya ajiye guntun samosan bisa plate ya tattara hankalin sa duka wurin ta.....me ke faruwa ne ummi?
Tayi shiru!
Dake nake magana...me ya faru?
Ta gyara Zama, Ina ce apartment din da kayi sabo Ni ka gina mawa Amma labari yazo cewa Aunty Amira ta koma....... Ke ya daka mata tsawa.
Nan da nan ya harzuka, Ni na fada Miki Ina Miki gini?
Gabanta ya fadi tayi tsuru tsuru, kinji? Munyi dake Ina Miki gini?
Okay ita da Zaki aure Mata miji Bata kawo mun matsala ba sai kece Zaki fara kawo mun tsirfa? Saurara da kyau ya Mike tsaye Yana nuna ta yatsa wallahi matukar kina son Zama dani tare da Jin dadi sai kin daratta Amira kin mun biyayya kin Mata bazan dauki sakarci ko kadan ba.
Dukkan ku Ina sonku to dole kowace tabi ra'ayi na, idan Kika saki na gane kina da matsala to wallahi zakiji ba dadi.
Mtsew ya buga tsaki ya wuce.......ta yi zuruuuuu tana zare ido lallai ta gwada Bata ji dadi ba.
Kwallah suka zubo Mata. Ta buga ma babbar yayar su waya domin ita ce abokiyar shawarar ta .....salati ta kamayi ubanwa ya aike ki? Ai kinyi sauri bari zakiyi sai kinje gidan yasan dadin ki lokacin yazo hannu tukun Amma Yanzu ai lallaba matar sa yakeyi tunda ya Mata laifi.
Ki bari Zan baki ahawarwari idan na shigo gobe.
Tun daga ranar Bata Kara Sanya Shi a ido ba. Tuni a Mata hudubar kada ta saki ta dauki raini ga matar sa Kuma idan ta a gidan ta Sami damar juya Shi yanda zata amshe ragamar komai.
Babu yanda ba a yi dashi ba ko kamu ayi yace bai son bidi'a ba Dan komai ba kada ma akirkiri partyn Amira taji ba dadi.
Ranar walima akayi mashi Sha Tara ta arziki hada mota.
Yana falon sa zaune yaji marokiya na sanarwa. Shima ya Mike ya kirawo marokiyar ya bada makullin mota kirar *GLK* baka 2019 model ta kusan miliyan Tara yace yaba Amira ayi sanarwa.
Nan dangin Amarya kuwa suka Fara surutai............
Ko ajikin sa. Dangin ango dana Amirai kuwa suka Fara rangada guda suna tayata Murna.
Hakan ba karamin harzuka Amarya da danginta yayi ba. Nan suka Kara hure Mata kunnen wallahi sai ta tashi tsaye Dan kwato ma kanta yanci.
Kuka takeyi wuiwui.
Kafin karfe shida gida ba kowa duk an tafi.
Ana gama sallar isha'i ya ja Amarya zuwa sashen Amira don yi masu huduba.......
*Ayi hakuri da typing error please yanayin typing din ne saboda kawai ta WhatsApp nake yi Kuma gaskiya bana bi idan na Gama kawai nake turawa.
*Daga zainab wowo*💞💕💗😄✍🏼
🤐 *WA ZAI FURTA?* 🤐
0⃣3⃣
*TUKUICI NE GA AUNTY RABI ALLAH YA KARA ARZIKI DA RUFIN ASIRI*
*KINA RAINA MAMAN WEEDAD*
*Domin ki.... blood sister khadija Dahiru wowo miji na gari I pray my besty*
*DAYA TAMKAR DUBU AL'AMEEN ZUBAIRU* TANNY ALLAH YA RAYA MIKI YARON NAN YA KARA MISHI KYAU DA KWARJINI💖
*Federal University dutsinma*
Tunda aka dawo bai yarda sun hadu da Bilkisu ba har suyi wata magana. Tana ta kokarin su hadu Amma yaki yarda.
Suna tsaye ita da su favour bakin ajin da zasuyi darasi ta hango Suleiman na taho wa, tun daga nesa suke ma juna dariya saboda Yanzu sun Zama tamkar *Wa da kanwa*, Anwar har yazo ya wuce ta gaban ta bata ganshi ba amma Shi Suleiman man din ya hango shi.
Yana karasowa malamin Shima ya iso haka suka rankaya zuwa aji.
Ko Zama Yanzu kusan tare sukeyi.
Har Yan class din sun Fara lura da shakuwar su.
Ya fakaici idon malamin ya Fara mata magana kasa kasa.
Wai Bilkisu kinsan Hamza Yusuf din say ake nema ajin nan Anwar ne?
Ta zaro ido *Anwar*?
Eh wallahi. Jiya gaba na ya amshi award din first class da Kuma overall award ina kallon sa yayi saurin boyewa ya bar hall din da sauri.
Ta rike baki. Innalillahi, wallahi sai na mishi magana naga wannan semester din ma tunda muka dawo sai wani shareni yakeyi.
Hmmm, ai da yake kece, Amma Anwar inba ke ba waye ke mishi shigar kawara duk makarantar Nan. Kinsan girman kansa, jiji da Kai da kuwa maida kowa banza yasa aka tsane Shi wallahi ya cika gadara....... Duk yaji dashi nikam daga yau wallahi ya shiga uku dani.
Ba abinda nake nema wurin sa inba karatun ba.....ta katse shi.
Hmmm Hana wallahi nayi mamakin *Business finance* din last semester, bana fada maka cikin mintuna da Basu wuce talatin ba ya gama kusan questions 4 kowa na kuka da question one amma Shi duka yayi. *B* fa gareni course din Kuma wallahi C A da 22 na shiga......ohh ni *Balky* ai wallahi ya shiga uku dani.
Suleiman man dai sai dariya yakeyi yace idan kin kwaso wurin sa Kya ringa koya mun....tabbbb tare zamu je kyaleshi ai wallahi sai na fitine Shi ga wannan semester din kurar ta tafi ta aji daya.
Daya ke Anwar din Yana ta gefenta sai kawai ta yi ta kallon sa.
Tun bai lura har ya fahimci tana kallon sa. Ya Dan juyo suka hada ido ta balla mishi harara Shi Kuma sai ya kawar da Kai Yana murmushi kawai. Haka sukayi tayi da sun hada ido sai yayi murmushi ita Kuma ta harareshi.
Yana ta sake sake cikin Rai *Kuma yau me nayi Ni Hamza* bana iyawa rigima da fitinar Yarinyar can. Ya kawar da Kai bai yarda sun Kara hada ido ba har aka gama.
Hankalin ta na kansa yana mikewa itama ta Mike.
Abinka ga namiji kafin ta sunkuya ta dauki jaka har yabar ajin. Da gudu tabi ta kofar baya kawai sai dai ya ganta gaban sa.
Gaban sa yayi mummunan faduwa Amma miskilancin Anwar bai yarda ta gane hakan ko a fuska ba hasali ma sai yayi Yar dariya *Hajia Bilkisu an tashi lafiy?*
Ta rike kugu To yau Allah ya Kama ka, Ashe Kai ne *Hamza Yusuf*........ Har ga Allah ya Dan razana. Amma a zahiri sai kawai yayi dariya duka kumatunsa suka lo6a ....inji wane makaryacin? Ya fada Yana dan waige waige kada sauran Yan aji masu fitowa suji,
Wallahi Kaine *Hamza Yusuf*.... Ta fada tana hararar sa. Tana matukar bashi dariya saboda ko gida bai taba samun Wanda ke mishi magana Kai tsaye Babu shakka ba irin Bilkisu.
Yadan Sha mur Yana Dan zare mata ido ke ni bani bane ya gitta zai wuce .....Tasha gaban sa da sauri tare da ware hannuwa ba inda zakaje sai ka fada mun wanene jiya aka bashi kyauta ya boye ya gudu?......tuni hankalin mutane ya dawo kansu an Fara fahimtar meke faruwa.
Ya zaro ido..... Ke ni bani bane..... Wallahi Kaine.
Naji nine yanzu meye kike so? Ya fada Yana Yan waige waige kamar marar gaskiya. Zaka ringa koya mun karatu wallahi don bazan kyaleka ba....shine damuwar? Ya fada cikin kosawa, shikenan duk lokacin da kika shirya Zan nuna Miki. Ya wuce da sauri ya barta tsaye.
Suleiman ya karaso kin dai gani ko?
Kyaleshi ai wallahi na daina wahala daga yau addabar sa zanyi.
Nan wuri ya rikice da surutai kowa na mamaki.
Tun daga lokacin kimar Anwar ta Kara karuwa duk masu Jin haushin sa suka daina. Matsala daya ce Babu Mai iya tunkarar sa da maganar koyo duk ana Jin tsoro da shakkar sa.
Tun daga lokacin Bilkisu ta dami Anwar ya rasa yanda zaiyi da ita ba abinda takeyi mishi sai terere kowa Yanzu yasan wanene Shi , ya rasa dalilin da baya son mata wulakanci kamar yanda yake ma kowa.
Ko lecture za ayi Mafi yawan lokuta sai ta zauna kusa da Shi sai dai yayi ta dariya.
Na kusa dashi mamaki kawai sukeyi yanda baya hantarar Bilkisu ko kadan don ko su din lallabashi sukeyi.
Satin da ya kasance daga Shi sai na yin first C.A sun fito lecture seven to nine ( 7-9 ), Yana tsaye ta fito da sauri don kada ya gudu sakamakon daya ce kawai garesu a Ranar.
Anwar muje ka koya mun *Math for Economic* din nan ban gane komai ba gashi jibi yace Shi zaiyi nashi test din.
Duk Wanda ke wurin sai da ya kalli Bilkisu cike da mamaki yanda take mishi magana Kai tsaye haka, Sam bashi ma take kallo ba ko lokacin da takeyin maganar hankalin ta naga jakarta tana saka littafin da suka gama, yayi Dan murmushi ba dai Yanzu ba ko? Saboda ko break banyi ba yunwa...... Ta dago Kai da sauri Nima banyi ba ai idan mun gama duk ma tafi muje muyi.
Ta nuna mishi hanya wuce muje wallahi yau ba inda zaka je......bai San lokacin da ya kwashe da dariya ba Yana ganin karfin halin yarinyar nan sosai, zai Kara magana ta rike kugu tare da tafa hannu kasan Allah ba inda zakaje...... Wuce kawai.
Naji muje yayi gaba ita Kuma tabi Shi a baya. Duk illahirin wurin binsa akayi da kallo ana wani irin mamaki.
Shi ya Fara Zama kafin ta zauna.
Yawwa ko Kai fa....ai ka gama shiga uku dani watan Kaine Mai kokarin aji shine ka mayar damu samnoni ko?
Dariya kawai yakeyi, tana surutai tana fiddo littafi da calculator. Ta Mika mishi biro da doguwar takarda ..ungo Fara daga farko.....
Dariya yakeyi sosai .....daga farko Kuma? Ki dai fadi abinda baki gane ba.
Ni ban gane komai ba.
Ban yarda ba Allah nasan kina son wahalar Dani ne kawai gashi yunwa nake ji walhi.
Ko me kakeji yau muna Nan sai ka koya mun kawai Fara.
Ya bude littafin to bari mu gani ko na iya.
Ta bishi da harara
Yayi murmushi yace seriously.
A hankali ya Fara mata solving dalla dalla. Dayake Bilkisu na da kokari da saurin fahimta hakan yasa bai wahala ba nan da Nan ya fahimci lallai tana da basira saboda da yawa idan Yana koya ma wasu sai su kusan awa hudu bisa example biyu. Akasarin Bilkisu da Mafi yawan formulas din ma ta haddace su idan yanayi da ka take kawo mishi su.
Ya kalleta hajiyar dai ashe guruwa ce ko? Ya ajiye biro gaskiya na gaji wallahi duk kin iya kina son bani wahala ne kawai ko Bilkisu?
Ta Dan sunkuyar da Kai haka kawai taji Yar kunya ....wallahi a'a ban iya ba.
Yabi fuskar ta da kallo Yana Kara kallon yarintar da ke cike da kyakkyawar fuskar tata.
Ke ni yunwa nake ji gaskiya ya fada Yana rufe littafi.
Dan Allah ka taimaka saura fa biyu da mun gama sai mu tafi Zan siya maka break idan mun fita waje.
Au Zaki biyani ne?
Ta zaro ido wallahi a'a naga hostel zaka koma gashi har Sha daya ta kusa, Kuma yaushe kaje ka nemi abinci?
Ke Kuma fa?
Ni indomie zanci dana koma daki.
To Nima ita zanci. Ya fada Yana ci gaba da rubutu,
Ba damuwa Zan siya maka wurin Abdul Mai shayi na Nan waje ai nasan mutumun ka ne.......da sauri ya kalleta waye ya fada Miki?
Tayi Yar dariya ai Ina wuce ku ta wurin Mafi yawan lokuta.
Ya Dan harareta ke kin samun ido ko?
Ta kyalkyace da dariya Wai ma.....
Eh Mana.
Rabi labari haka suka gama duk idanun sa sunyi ja....Nan da Nan ta fahimci lallai baya da jimirin yunwa yanda har ya Fara galabaita.
Tare suka jera suna tafiya, baka da jimirin yunwa ta fada tana Yar dariya.
Ya danyi murmushi yunwa nada sabo ne?
Eh Mana Amma ga jaruman maza.
Dariya yayi sosai kafin yace naji ni ba jarumi bane ba.
Eh, ta fada tana murmushi
Ke ni sai anjima ya fada tare da yafito Dan mashin.
Ta zaro ido Ina zakaje?
Hostel.....
Indomie din fa?
Na gode....
Wallahi baka Isa ba , Dan mashin din na zuwa tace malam tafi.....ta kalleshi Allah sai na siya maka break kafin ka tafi ko muyi rigima.
Yau ni naga ta kaina....ya fada cikin zuciya.
Ya kalleta, kiyi hakuri da wasa nakeyi na gode,
Ni ban gode ba kawai muje ta nuna mishi hanya.
Dariya ma ya kamayi.
Haka suka je indomie din akwai layi tace kaga kada mu jira zo muje.... Yace to.
Bin ta kawai yakeyi yana kallon ikon Allah sai sauri takeyi suka zagaya babban restaurant din wurin duk yafi ko Ina kyau da tsada, tayi mishi take-away na chips and eggs aka Sanya mishi salad da sos din hanta sannan ta siya mishi gasasshiyar kaza daya da maltina biyu da Madara. Yana tsaye bakin kofar Daman ita kadai ta shiga. Ta fito da sauri tana ta wurga ido kafin ta hango shi can jikin bango.......barkan ka wallahi na dauka tafiya kayi yau da kaga tsiya.
Kallonta kawai yakeyi Yana Yar dariya.
Muje ka hau mashin din zaka shigo anjima school da karfe 4? Ina son ka koya mun *Human resources* ya danyi jimmm..... To bani tunani Amma Ina ga Zan shigo.
Ta fiddo waya samun no. Ka in kiraka kada ka shanya ni kamar last time. Yayi murmushi duk jikin sa yayi sanyi ya ce okay rubuta..... Yana fada mata Yana kallon fuskarta.
Yana Gama fada yace Shi Suleiman bazai koya Miki ba?
Eh bazai koya ba idan ya iya zance Kaine?
Ta hayayyako mishi. Ya kyalkyace da dariya Allah ya bada hakuri. Daidai lokacin da ya tare Dan mashin. Sai da ya hau sannan ta Mika mishi ledojin sannan ta Mika wa Dan mashin din naira dari tace hostel zaka kaishi. Duk meye kika ciko mun anan?
Malam ku tafi kaji...ta kalleshi tana Yar dariya na gode kwarai Allah ya Kara basira sai mun hadu anjima.......kirjinshi ya halba da karfi Shima ya bita da murmushi kawai. Sai kawai ta daga mishi hannu. Hakan Shima ya mayar mata Yana Jin wani masoki na sukar sa...........shi kadai yasan yanda yakeji a zuciyar sa, tana tafiya tana tunani da surutai a zuciya, a gaskiya yau ta Kara tabbatar wa da kanta Anwar na ganin mutuncin ta da kima saboda cikin karfin hali tayi attacking din sa tayi tunanin zai ki yarda kamar yanda yake ma kowa wulakanci.
Shi kuwa Yana zuwa hostel ya baje abincin dakin a cike Yan zaman jiransa kowa ya bude baki Yana mamaki lokacin da yake fada musu Bilkisu ta siya mishi. Bashir ya ce Wai Kai oga anya tsoron yarinyar nan kakeyi ne naga ba Wanda ke maka shigar kawara irin ta kana mata biyayya, dariya yayi kafin yace *ya na iya da Bilkisu*? Wallahi bana iya wa rigimarta ko baku lura ita Sam Bata tsoro na ba?
To ka dai bi a hankali domin Dr Dan Musa da alama Yana ciki wallahi ya gane kana kusa da ita haka zaka. ......mtsew bai iya mun komai wallahi. Ina ga Suleiman ya kamata ku ja ma kunne ba nima ba domin Shi ke binta Ni Kuma tana Bina .....ya lunkuma nama baki ya kallesu ..hope Kun gane karatun..
( Shin Wai wanene Anwar wacece Bilkisu? )
*********************
*KADUNA RIGASA*
Yaran duk sunyi barci.
Tayi ma falon kallon ta natsu .....lallai akwai aiki haka ya hada mata aljannah duniya?
Ya kalli ko wace kafin ya tsaida ido ga Amira ya Fara magana a hankali.
Alhamdulillah dukkan godiya ta tabbata ga Allah Wanda ya kawo mu wannan lokaci, kasancewa dare ya Fara yi Zan muku bayani Kai tsaye abinda ya tara mu a Nan.
Amira kece babba dake Zan Fara ga Ummi, kiji tsoron Allah ga dukkan al'amuran ki akanta ki dauketa tamkar kanwarki Salma, ki sani cewa kema Ummi Amana ce a wurinki kamar yanda dukanku kuke Amana a gareni. Babu wacce tafi wata a wurina sai wacce ta fi mun biyayya da tsare dokokina, tabbas ko wacece cikin ku zata fi Power ban baku a boye ba, Zan yi kokarin adalci a gareku Ina rokon dukkan ku duk wacce taga za a tauye mata hakki ko nayi kuskure ko akasin haka na baku damar nuna mun hanya domin ko wane Dan Adam ajizi kuma wasu a wurin da sukeyin kokarin yin dai dai suke ba dai daiba.
Bana son gulma , bana son Jaye Jaye abokai da yawan fita yawo marar amfani.
Ke Kuma Ummi ga Amira Nan, ki bata girma kamar sailuba bana son raini, rashin kunya da tsageranci. Tabbas na zauna da Amira nasan halinta don haka ki bita a sannu ku zauna lafiya. Duk abinda ya shige Miki na gidan nan ita Zaki tambaya tunda ni ba mazauni bane.
Da ita Zaki zauna kiji dadi ba ni ba saboda tafiya Zan ringa yi ina barin ku.
Ina da Yara, ko da wasa kada ki zagesu domin ba a zagi a gidan nan, idan sun Miki laifi kiyi musu duk hukunci amma banda zagi.
Amira dai tunda ta sunkuyar da Kai bata dago ba tana ta karanta addu'o'i a zuciya, Ummi din ma ce ke ta Yan wurge wurge.
Sai maganar kwana, a musulunce zanyi kwanakin da aka halatta a dakin Ummi a matsayin ta na budurwa daga Nan ko wace Zan ringa kwana biyu biyu hakan ya muku ?
Duk sukayi shiru.......Amira ya muku?
Ta dago Kai umm hakan yayi ko Ummi?
Ta Dan yatsina fuska ..um.
Da kyau!
Maganar abinci Kuma duk Mai aiki ita zatayi abinci, Ummi tsarina a gidan Nan ko Ina Nan ko bana Nan karfe Sha biyun Rana ya zamanto kin Gama abinci saboda Yara da masu gadi da Kuma sauran mutanen gidan.
Bana son kwauron abinci a ringa dafawa a wadace, tun daga safe har dare.
Amira zata Miki bayanin quantity din idan Kun zauna.
Ba wacce zanbi dakin ta lokacin kwananta duk ranar aikinki Zaki sameni sashena ban yarda da raba kwana ba Koda munyi fadan soke soken wuka.....
Ya kalli Ummi wannan shine tsarina. Duk wacce nayi ma laifi kafin ta tsiri yin fushi dani ta Fara sanar Dani idan har nayi bisa kuskure Zan bata hakuri, idan Kuma akasin haka Zan Fadi dalilina.
Duk Mai bukatar abu ta tambayeni Kai tsaye domin nine mijinku, idan anzo muku da magana akaina ku Fara sanar dani da Kuma Wanda ya kawo maganar ku fadan wanene.
Idan cikin ku wata keson haddasa fitina ta kawo muku gulmar daya to ku tsaidata ku kirawo wacce ake maganar kusanya ta maimaita a gabanta zakuyi maganin munafukai.
Ina fatan duk kun gane?
Wacce keda magana tayi.....duk sukayi shiru.
Ya Mike Ummi jeki Ina zuwa......kamar jira takeyi ta Mike.
Ya Mika wa Amira leda uwargida ga taki kazar.......wayar say tayi Kara ya ganka a kunne hello........na'am hajiya.....Nan ta fahimci mahaifiyarsa ce. Ya yahuto ta da hannu alamar tazo ta rufe kofa zai fita Yana ci gaba da tafiya.
Yana fita ya Sha kwana ya latse wayar daman fakaitar idon ta yayi ya latso wakar saboda Shi baisan yanda zai mata bankwana ba. ( Namiji?.....)
Tana rufe kofar ta duke a wurin tafara kuka na ban tausayi....( Kishi kumallon mata.....)
Ina bada hakuri Dan Allah.......
*zainab wowo ku muku fatan alkhairi*......✍🏼💖😄
0 comments:
Post a Comment