Gudu sukeyi,basu tsayaba seda sukaje jikin wani dogon gini,sannan suka tsaya kalle kalle.
Can suka hango wata mata wacce da gani sunsan yar nigeria ce.
Da gudu suka nufeta,sunaso ta taimakesu tamaidasu gida.
"Ayya na tausaya muku,amman kuyi hakuri inkaiku kuyi ayki tukuna seku,samu kuɗin jirgin komawa gida".
Cike da faraa,suka amince suka bita.
Dayake matar ita a makkah take,dan haka mota suka hau,daga jiddah zuwa cikin garin makkah.
Koda suka isa gidan matar,sunsha mamaki,domin shima cike yake da yanmata,yara da manya,sannan ga kekunan guragu nan kala kala.
Abinci tabasu sukaci,sannan takira wata halima tace mata.
"anjima inzaku harami,kutafi da wainnan,kinga zaa kara samun kuɗin sadakar"
sude su suhaima basu san manufarta ba.
Suna zaune,halima tazo da bandeji,tasa su suka dora hannayensu a kafaɗarsu ta ɗaure guiwar hannun da bandejin,sannan takawo kalar jini ta shafa akasan.
bame cewa ba yanke musu hannun akayiba,sude se kallon abun mamaki suke.
Mamakinsu be ƙaruba seda aka kawo musu keken guragu akace,su hau.
ba musu suka haye,wasu suka turasu zuwa harami.
Suna cikin tafiya,duk wanda yagansu se yabasu sadaka,ayko suna zuwa daidai,wani hotel,me suna land premiar,suka haɗu da yankame.
Suhaima se gani tayi,sauran sun kwasa da gudu,dan haka itama,sauka tayi akan keken,ta ruga da gudu,itako sajida kamin ta gudu har sun kamata,ihu take tana tsillewa dan batasan inda zaa kaitaba.
Suhaima leƙowa tayi daga inda ta boye,taga ansaka sajida a mota,fitowa tayi da gudu dan itama akamata,amman ina kamin ta ƙaraso sunja motar suntafi.
tsugunawa tayi agurin tanata rusa kuka,daga karshe tamike ta cigaba da tafiya tana share hawaye.
Dayake lokacin aykin hajji ne garin na makkah cike yake da baki.
Suhaima cigaba tayi da tafiya,har ta iso wani guri dataga jamaa da yawa se shiga sukeyi,kyan gurin da tsarinshine yasa suhaima shaawar shiga ciki taga kome ake gani.
Tana zuwa zata shiga da takalminta,taji wani megadin ƙofar yana faɗin,"haram haram"nuni yaymata data cire takalmi ba musu tacire,ya miƙo mata wata farar leda,tasaka aciki,sannan ta rike a hannu ta shiga.
Dayake gangarane,haka suhaima ta dunga tafiya kanta akasa,kamar ance ta ɗago kanta.
ALLAHU AKBAR.
Arba tayi da ɗakin Allah yayiwa sama rumfa.mutsike idonta tashigayi nason tabbatarwa ba mafarki takeba.
ay tunda taga dagaske shine seta fashe da kuka,t juya tafice zuwa waje tasha wahala kamin tasamu bahaushiyar data nuna mata gurin alwala.
alwala tayi tadawo,gurin kaaba.
Dayake batasan ya akeyiba,ita gurin kaabar kawai tanufa,dan ko alwala tayine,sabida tanaso ya amshi rokonta da gaggawane.
da kyar tasamu ta isa jikin kaabar,tunda taji hannunta yataba ta,se kawai ta rushe da kuka tana faɗin.
"Allah na daɗe ina wahala arayuwata,ka kawomin agaji,ya Allah,nagaji,katausayamin haka,nima baiwar kace ya Allah"ta ƙarasa adduar tana kuka.
********
Suhaima seda ta kwashe tsawon sati guda acikin harami,tana maimaita wannan adduar,alwala da tsarki kawai ke fito da ita,abinci ko ana raba sabil na dabino da madara,su take ci.
Yau jummaa,rana ta buɗe sosai agarin na makkah,bayan an idar da sallar jummaa ne,suhaima tafito,wajen haramin sabida tanaso ta siyi riga da kuɗin sadakar da aka bata ranar da aka kama sajida.
Tana fitowa,taita tafiya,tarasa mezatace inta shiga shagon,dan ita batajin larabci.
Wasu gungun mata,ta hango,zaune,jikin ginin bindau,da sauri tanufesu,sallama taimusu,suko suka amsa amman azatonsu balarabiyace,dan haka se suka mata larabci.
ido taware atanta tace dama akwai baƙaƙen larabawa,tunda tagade fatarsu baƙace.
Dakyar tace musu ita bahaushiyace,don Allah tanason siyan rigane batasan mezatace.
Wata acikin matanne,ta juya tayiwa yar uwarta magana da larabci,seta juyo tacewa suhaima.
"amman ke bakuwace ko?"
kai suhaima ta ɗaga mata.
murmushi matar tayi sannan tace.
"karki damu ki bini ni kuma namiki alkawari insha Allahu,zan samar miki ayki,aguri me kyau,yadda zasu dunga biyanki duk wata,inkin amince kibini muje,amman ba anan garin nake zauneba,ni ina riyad ne"
Suhaima da sauri ta amince,ayko guri tasamu tazauna jiran matar,har tagama abinda zatayi,suka nufi tashar mota,suka hau,mota zuwa riyad.
muje zuwa.
Surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*KANO TO JIDDAH*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*KHALEESAT HYDAR FACEBOOK NOVELS GROUP,NAGODE DA SOYAYYARKU GARENI,ALLAH YATSAREKU CIKIN TSAREWARSA AMEEN,*
*ZAKU DUNGA YIN HAKURI DA ABINDA YA SAUWAKA,BA KODA YAUSHE ZAN DUNGA TYPING BA,NAGODE DA ADDUOINKU MASOYANA*.
*DEDICATED TO ZAHRA BUKAR*
*13-14*
Tafiyace me tsayi tsakanin makkah da riyad,dan haka sun jima kamin sukai.
Kamarde sauran,shima gidane me ɗauke da yawan mutane mazauna nigeria.
Tunda suhaima taje garin hankalinta akwance yake,sabida dankalin turawa kawai suke soyawa su fitar dashi,waje su siyar,hajiya murja sunan wacce takawo suhaima riyad,tana da kirki sosai kuma akwaita da tsoron Allah.
Sannu ahankali,suhaima har tasoma jin larabci,kamin wani lokaci taƙware dayin yaren,shiyasa take yawonta ko ina batare da ƴan kamen tikari sun kamata ba,sabida harshenta har ya karye,ko hausarta bata fita da kyau,sannan kamanninta babu mecewa ba balarabiya bace.
Watan suhaima biyar tare da hajiya murja,rannan da safe suna zaune sega,wata aminiyar,hajiya murja tashigo,me suna hajiya safiya.
fuskarta ɗauke da murna ta faɗo gidan,har tana tuntuɓe,amman bata damuba faɗi take.
"hajiya murja,fito,yai nasamo kabar me daɗi,fito fito"
da sauri hajiya murja ta tari aminiyar tata tana faɗin.
"akbirni kawata,meyafaru,kinsa nafara murna tun kamin naji"
guri suka samu suka zauna,sannan hajiya safiya tace.
"Dama gidan,sarki Abdulaziz Assa'udi ne,aka kama maaikatan gidan da laifin yunƙuri kashe ɗanshi,tahanyar bashi guba,to shine aka kori kowa,to yanzu sababbin maaikata suke ɗauka,kuma kinsan basa ɗaukar baƙar fata,shine nace ko zaki gwada kai suhaimanki ko zaa dace su ɗauketa,tunda aykine me kyau,"
"Gaskiya naji daɗin wannan labarin,sede,abu ɗaya,wlh banaso suhaima tayi nisa dani,sabida,tabani labarinta gaba ɗaya,tausayinta nakeji,ina gudun nakaita,makkah bayan nataho kuma sugano ba balarabiya bace,asamu matsala,"
Murmushi,safiya tayi sannan tace.
"inbanda abinki suhaima ay tasan hanya,insuka korota seta dawo,nan,nide namata shaawar aykin wlh,ki daure kawai mu kaita mu bita da addua"
Ayko da kyar hajiya murja ta amince.
Sati guda tsakani,suka shirya suhaima zuwa makkah,da kuka suhaima ta amince da aykin,dan itama batason yin nisa da hajiya murjan.
Koda suka isa masarutar,sun tadda mutane jibge ana musu screening,dan haka suhaima tahau layi,amatsayin me share share.
Koda akazo kanta ashe bata saniba se kana da takardar zama ɗan kasa,ido ta dunga warewa inda tace tamantoshi a gidansu dake riyad.
Kyan suhaima da kwarjinintane yasa mutumin yasa sunanta amatsayin me shara agidan batare da katin ba.
ganin sunanta yashigane yasa ta dawo gurin su hajiya murja sukayi sallama,sr kuka sukeyi,ahaka suka rabu,bayan hajiya murja taba suhaima ɗayar wayarta,sabida sudunga gaisawa.
Bayan angama tantancrwa ne aka shigar dasu suhaima cikin gidan,aka gabatar dasu ga alummar,gidan,daganan akaba kowa,ɓangarenshi,daze dunga kula dashi,cikin ikon Allah ɓangaren,babban ɗansarkin mesuna.
*SHUREIM ABDUL'AZEEZ AS-SA'UDI* ,ya faɗo acikin bangaren da suhaima zata dunga gyarawa,kuma dama duk inda,aykinka yake to anan ɗakinka yake,amatsayinka name kula da gurin.
Danhaka,ɓangaren aka kai suhaima,aka bata ɗakinta,mecike da kayan more rayuwa,kamar bame aykiba.
********
Hajiya duniyar sama sanda ta dawo tasamu labarin su suhaima sun gudu ba ƙaramin baƙinciki tayiba,ranta sosai ya ɓaci.
Hakanne yasa takira bokanta dake ƙasar indiya,tashaida mishi tanaso ya haukata suhaima da sajida,
alkawari yamata inda yashaida mata,yana da ayyuka sosai agabanshi,amman ta jira bayan wata shida ze kammala yashiga nata.
bata damuba,sabiɗa tasan boka guru maharaja da cika alƙawari
Anashi ɓangaren kuwa,boka guru maharaja,yaune waadin daya dibarwa,duniyar sama,dan haka tuni yashiga ɗakinshi na yin tsafin domin aywatar da nufinshi.
Wanda yay daidai da shigar suhaima masarautar makkah amatsayin hadima agidan.
Sajida kuwa bayan ankamata,sijin aka kaita,watanta biyu aciki,aka sakata,ajirgi,zuwa nigeria.
a kano aka sauketa,kuma bata da kuɗin mota hakanne yasa ta ɗauki drop din mota zuwa bauchi.
Sosai iyayenta sukayi murna da komawarta gida bayan sun cire ran sake ganinta,sukai taaantar hajiyar sama da tawagarta.
muje zuwa.
surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*KANO TO JIDDAH*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*Dedicated to zahra Bukar*
*17-18*
Yana zuwa ya samu mahifin nashi zaune yana cin tuffah,
Bayan ya gaisheshine yashaidamishi abinda ke faruwa.
Akiɗime sarki yake tambayarshi.
"taya haka tafaru,yanzu yarinyar tana ina?"
"Tana ɗakina tasamu bacci"
"muje in ganta"cewar sarki yana miƙewa.
Ɓangaren Shureim ɗin suka dawo tare,koda yaga suhaima sosai yatausaya mata,kallonshi yamayar gun shureim yace.
"bata da wayane,ay yana da kyau asanar da yan uwanta halin da take ciki"
Da sauri shureim yaje yaɗauko wayar suhaima yakawo masa.
Number hajiya murja suka kira bugu ɗaya ta ɗauka dan dama gaba ɗaya a firgice take na rashin jin suhaima kwana biyu
jin muryar namijine yasa hajiya gigicewa tana tambayar waye cikin harshen larabci
"Shureim sunana,dama anason ganinki da gaggawa a inda me wannan number take ayki,sabida kwana biyu kenan bata da lafiya"
salati hajiya take tana ƙarawa bakinta har rawa yake gurin bada amsar gatanan zuwa.
kamin hajiya tazo,sarki sawa yayi aka maida suhaima wani ɓangare na musamman aka kunna mata karatun qurani
cikin dare hajiya ta iso batare da tsoron komaiba sabida tana da igama.
Gurin kwana aka bata kamin gari ya waye.
hajiya ta kasa bacci burinta kawai tasan halin da suhaima take ciki.
Washe gari seda rana tafito sannan Sarki ya buƙaci agabato masa da hajiya murja.
Rusunawa tayi tagaisheshi,sannan tanemi guri ta takure.
"baiwar Allah meye haɗinki da yarinyar nan,gaskiya nakeso kisanar dani"
Hajiya murja batare da tsoron komaiba ta faɗamishi duk abinda tasani gameda suhaima,harda labarin suhaima nacan nigeria da suhaiman ta bata.
Sarki seda yashare kwallah na tausayin suhaima,daga haka sawa yayi aka nemo manyan malamai,suka shiga saukewa suhaima qurani me girma.
tsawon sati guda aka kwashe ana mata karatu,cikin ikon Allah aljanun suka fara magana,malaman basuyi kasa a guiwaba,gurin ci gaba da karatun,har suka samu aljanun suka fita.
kowa se hamdala yakeyi nasamun nasarar samun lafiyarta,
Sede tunda tasamu sauƙi kuma se bata magana sede nuni take da hannu.
Shureim inyasata agaba yana kallo har beso yadena,tunda yaji labarinta yaji takwant mishi arai,d mahaifinshi ze amince da ba abinda ze hana be nemi auranta ba,dan harga Allah suhaima tana cikin jerin irin matan dayakeso ya aura,wato mata wainda suke da rangwamen gata,domin yatallafi rayuwarsu.
Hajiya murjace tacigaba da kulawa da suhaima agidan sarki batare da tsangwama ko takurawaba.
tsawon watanni biyu takwashe tana kulawa da ita,sumul tawarke maganace kawaide har yanzu batayi amman babu inda yake mata ciwo.
Ganin hakane yasa hajiya murja tafiya ita kuma suhaima ta koma bakin aykinta,na kula da ɓangaren shureim.
tunda lokacin bata sakaci da addua kullum inde bata aykin komai to zaka samu karatun qurani take.
Sarki da kanshi ya bukaci suhaima tayiwa sojoji jagoranci zuwa jiddah domin kamo su hajiyar sama,dan dama dabida irinsu ake kamen tikari.
sunsha wuya kamin tagane gidan,cikin ikon Allah su hajiya karimatu da hajiya uwar mabuƙata duk suna gidan,ayko ba wanda aka bari acikinsu aka kwashesu zuwa kotu,inda yanmata aka musu bulalar zina aka sakosu a jirgi aka dawo dasu nigeria,hajiyar sama ko hukunci kisa aka yankemata ta hanyar jefewa sabida tana da aure ita dasu hajiya karimatu,da uwar mabuƙata,dan duk suna da aure.
Suhaima tayi mamaki da sarki ya barta taci gaba da ayki agidan batare daya sallametaba.
tamaida hankalinta kan aykinta,ba ruwanta da hayaniya,natsuwarta na ɗaya daga cikin abinda yake ƙara sawa shureim sonta da ƙaunarta.
muje zuwa
Surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*KANO TO JIDDAH*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*dedicated to zahra bukar*
*15-16*
Yau da wuri suhaima ta tashi,ta ɗauki injin shara da mopping ta nufi ɗakin yarima.
Da sallamarta ta,shiga sede bakowa adakin.
Ba abunda yafiba suhaima mamaki,kamar ganin ɗakim kamar bame hankali aciki,sabida mugun dattin dayayi,wadrope a buɗe,kayan daya cire gasunan zube aƙasa wasu akan gado.
Tattara kayan wankin tafara yi takaisu cikin worshing marchine,tazuba ruwa da omo,sannan ta kunna,ta dawo taci gaba da aykin ɗakin.
Ranar suhaima tasha wuya sosai,dan kwalema tayiwa ɗakin,harda canjawa gado gurin zama,sannan tasa sabon bed shit,kayanshi ko data wanke shanyawa tayi suka bushe ta zauna ta gogesu tas,sannan,ta kwaso na cikin wardrope ɗin gaba ɗaya tasake sabon shiryawa.
kamin wani lokaci ɗakin yafito fess kamar bashiba.
Koda tashiga toilet nanma ta tarar dasi boxsize dinshi da singlet,jibge aciki baa wankeba,a kunyace suhaima ta kwashesu takai,worshing marchine suma tawanke ta goge masa,ta feshesu da turare ta shirya masa.
Koda ta koma ɗakinta wanka tayi ta gasa jikinta sannan tayi sallah,ta nufi kitchen dan samawa cikinta abinda zata ci.
Sabida gidan komai a adalce sukeyi,kowanne ɗan ayki a ɓangarenshi akwai,kitchen da store daze dunga girka abinda yakeso yaci ba takurawa.
Koda suhaima taje kitchen dambun coucous tayi wanda yasha naman kaza da kayan lambu.tuni,ɓangaren nasu ya buɗe da ƙamshi.
tana gamawa,ta juye a kula,sannan tazuba wanda zataci ta fice daga kitchen,tanufi ɗakinta,tazauna taci tasha ruwa,tabi lafiyar gado.
***********
Shi ko Shureim tunda ɗakinshi yayi datti yadena kwana agidan ya tattara abinda yake buƙata,yakoma kwana a hotel,dan baze iya kwanan ɗakinba.
Yau yana tasowa daga office har ya shiga lifter zuw Ɗakinshi,sekuma kawai yaji yanason zuwa gidansu,dan haka fasa hawa saman yayi yadanna ta dawo dashi ƙasa.
yana sauka yashiga motarsa zuwa gidansu.
A aladar gidan basa zaman falo,dan haka be tarar dakowaba,ɗakin mahaifiyarshi yanufa.
me suna hajiya fatima,a kishingiɗe yasameta,me mata tausa tana matsa mata ƙafarta.
Nufarta yayi da sauri yarungumeta ya sumbaceta,ita kuma ta shafa gashin kanshi tana samasa albarka.
kan kujera yaje yazauna,suna hira,duk da cewa shureim miskiline na bugaw A jarida,wanda magana ke matuƙar tsada agurinshi,amman baya yiwa mahaifansa.
"Shureim ina kashige kwana biyu bana ganinka?"inji mahaifiyarshi cikin harshen larabci.
"Ummi wlh ɗakina yayi masifar dattine,ni kaina kunyar ɗakin nakeyi,shine kawai yasa natare a hotel acan nake kwana,tunda ankori yan aykin gidan"shima ya bata amsa da lataɓcin.
Murmushi ummin tayi sannan tace.
"Kaide akwai shiririta,to ay ankawo wasu maaikatan jiya,kuma kaima antura me kula da ɓangarenka,nasan angyara komai yanzu,kaje kaduba inbeyi maka ba base a canja kayan ɓangaren gaba ɗayaba"
Taɓe baki yayi sannan yayiwa ummin tashi sallama yanufi ɓangaren nashi.
Tunda yake betaɓa jin ƙamshin dayakeji aɓangaren nashiba yanzu,kamshin turare ganida ƙamshin girki,tuni cikinshi ya juya,alamun yanajin yunwa.
Kasa jurewa yayi yanufi kitchen ɗin,ba kowa se cooler buɗewa yayi wani tiririn ƙamshine ya daki hancinshi,da sauri,ya ɗauki plate ya juye abincin aciki,ya ɗauka yanufi ɗakinshi.
Abinda yagani ba ƙaramin mamaki yabashiba,inbanda ƙamshi ba abinda ɗakin yake komai naciki yadawo sabo,wardrop ɗinshi yanufa acan yasha makurar mamaki,ganin komai a wanke a goge se ƙanshi sukeyi.
toilet ɗinshi yanufa acanma yasha kallo,besan sanda murmushi ya kubce afuskarsa ba,a fili ys bayyana.
"ko waye yayi wannan aykin ba balarabe bane,sabida su basu saba da wahalaba,,musamman nacikin birni bankiba kona kauyem zasu iya kwatantawa, nasan koma waye to tabbas namiji ne,dan mace bazata iyaba"
da wannan bayanan nashi yaje yazauna yafara cin abincin,ji yake kamar kunnenshi ze fita,dan daɗi sam babu tafarnuwa aciki,shidama yatsani tafarnuwarnan,dande kawai yazamar musu tamkar aladarsu ce cinshi.
Shureim duk yawan abincin seda yakwasheshi tas yasha ruwa,yamiƙe ze fice ji yayi ya gaji dan hska lafiyar gadonshi daya gaji da haɗuwa yabi,yayi kwanciyarshi tuni bacci yayi awon gaba dashi.
*********
Tunda daga wannan lokacin,kullum suhaima seta girka abinci me rai da lafiya ta haɗa harda shureim sabida ta fahimci inta rage s kitchen yana zuwa ya cinye,dan kullum taje gyara ɗakinshi seta fito da plate.
tsawon wata guda kenan,tana ɗawainiya dashi,tuni yamurje,har wata kiba yayi,ga ɗakinshi kullum cikin gyara,gashi be taɓa ganin me aykin nashiba,kuma bedamu dason ganin me aykinba dan azatonshi namiji ne.
Yau tunda suhaima ta tashi kanta ke ciwo,dakyar ta cire kayanta,ta ɗaura towel tashiga wanka,adaddafe tagama wankan ta ɗauro towel ta fito,tana fitowa tayanke jiki ta faɗi aƙasa.
Tsawon kwanaki biyu kenan shureim,bega angyara mishi ɗakiba,kuma baa dafs mishi abincinba,wanda yasan da baa fashi.
hakanne yasa yashiga damuwa,nason sanin halin dame aykin nashi yake ciki.
Suhaima ko tunda ta faɗi bata tashiba seda ta kwans biyu ahaka,cikin dare ta tashi a haukace,tuni tayi fatali da towel ɗin dake ɗaure jikinta,se buga kanta take a bango tana zage zage.
Shureim cikin bacci yaji ana buge buge,a firgice ya tashi,silifas yasaka yafito,falo ananne yafahimci aɗakin me kula dashine abun yake faruwa.
Da gudu ya nufi ɗakin,yatura yashiga,ganinta tsirarane,yasa yayi saurin dakatawa gamida runtse idon shi yana fadin.
"Auzubillahiminashshaidanirrajeem"
itako suhaima se buga jikinta take da bango,har ta jiwa kanta ciwo,ganin zata illata kantane,yasa shureim daurewa ya ƙarasa inda take ya riƙeta,nanfa dambe ya kaure,ita ala dole seta kwace,inda shi kuma ya gwada mata ƙarfe,ta hanyar rungumeta gabaɗaya ajikinshi.
Se gurnani takeyi kamar tsohon zaki,ɗaukarta yayi gaba ɗayanta,yanufi ɗakinshi,da ita se son kwacewa takeyi,amman ya hanata.
koda yakaita ɗakin,ɗaureta yayi da ƙafar gado sannan yakoma ɗakinta,ya ɗauko doguwar riga da dogon wando,har ze fita ya hangi wayarta jone ajikin charge,cirota yayi yaga tana da missed call har guda goma.
Da sauri ya koma ɗakinshi,likacin saura kaɗan ta kwance daga daurin daya mata,da sauri yaƙarasa inda take,sunci uban dambe kamin yasamu yasaka mata kayan,
yana gama sakamata,yafara rera karatun qurani,cikin zazzakar muryarshi akunnenta,sannu a hankali tafara gurnani,da buge bugen,zuwa can kuma seta zube jikinshi sharab alamun tayi bacci.
kan gadonshi ya ɗorata,ya gyaramata kwanciya,sannan yanufi ɓangaren mahaifinshi,domin sanar dashi abinda ke faruwa.
muje zuwa.
surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*KANO TO JIDDAH*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATIONS
*Happy sallah to all muslims ummah over the univers*
*dedicated to zahra bukar*
*19-20*
Yau da wuri suhaima tashiga ɗakin shureim domin gyarawa,sede shigarta keda wuya,taci karo dashi kwance a ƙasa riƙe da mara yana ta kwara amai duk ya galabaita.
A gigice tayi kanshi,tana jijjigashi,amman ko kulata beyiba sema idonsa dake yin sama,
Da gudu tafice daga dakin tanufi cikin gidan,daidai lokacin sarki da tawagarsa zasu fita batasan sanda tabige sarkinba,hankalinta duk yatashi,bata cikin natsuwa.
Wani sojane ya kamota yana tambayarta ko haukartane ta motsa,dayake bata magana nuni kawai take da hannu tana hawaye kai kace mutuwa akamata.
fahimta sukai akwai abinda ke faruwa,a ɓangaren prince,hakanne yasa,suka ɗunguma har sarkin zuwa gurin.
Suhaimace agaba tana musu jagora.
koda suka ga halin da shureim yake ciki basu ɓata lokaciba suka nufi asibiti dashi.
hankalin sarki atashe yake,dan in akwai abinda yafiso arayuwarsa to shureim ne sam bayason ganin shi cikin damuwa,dan haka yakasa zama burinshi yaji abinda yake damun ɗannashi.
Likitocin sun jima kamin daga bisani suka fito babban cikinsu ne yafara yiwa sarki bayani cike da girmamawa kamar haka.
"Ranka ya daɗe wannan matsalarce de da take damunsa itace tasake tashi"
Cikin rashin fahimta sarki yace.
"wacce matsala kenanfa,dama shureim yanada wata lalurane wacce ni bansaniba?"
cikin daburcewa likitan yace.
"Ranka yadaɗe,kimanin shekara guda kenan ay,da matsalar tafara damunshi,kuma tun farkon zuwanshi nan na bashi shawara akan yasanar dakai,dan ayi maganinta da gaggawa"
cikin fargaba sarki yace.
"kaga likita kafito fili kasanar dani damuwar ɗana,ni bansan komai gameda ciwonshiba"
"to batu na gaskiya,yana fama da shaawa me ƙarfine,wacce inta motsa in be samu biyan buƙata ba se sperm ɗin ya daskare a marar sa,wanda hakan shike haddasa masa ciwon mara me tsanani,wanda dole se yazo nan mun narkar da sperm ɗin mun tsuƙe masa shi tukuna yake samun lafiya"likitan ya ƙarasa zancan cikiɓ girmamawa.
Ido sarki ya ware sannan yace.
"likita to yanzu meye maganin wannan lalurar?"
"maganinta shine agaggauta yimasa aure cikin ƴan kwanakin nan,to in yatara da matarsa kome zezo da sauƙi daga ƙarshema ze rabu da matsalar,dan yanzu yakai stage din da komai ze iya faruwa dashi dan haka a shawarce shine ayimasa aure"
Shuru sarki yayi yana nazarin zancan likitan,to sho yanzu ƴar waye zece Ze aurawa shureim,dan yasha kawo mishi ƴaƴan sarakuna na ƙasashen larabawa da ƴaƴan masu kuɗi yana cewa baya so,koda yatambayeshi yo wacce kalar mace yakeso, ya shaida mishi mara gata yakeso ba masu gata ba,to shi ina zeje ya samoma shureim irin irin macen dayakeso?
sabida koda zaa bashi mara gatan to yana da kyau abashi wacce take da natsuwa,da sanin abinda shureim yakeso da wanda bayaso,dan samun zaman lafiya a tsakaninsu.
*suhaima hadimarsa* shine sunan daya faɗo bakin sarki.
tabbas shureim zesota tunda itama bata da gata,sede ba balarabiya bace,amman kuma tana da tausayi duba da ganin yanayin data shiga da ganin shureim ɗin bashi da lafiya.
Duk wata shawara da sarki yakeyi da zuciyarsa ta gaza hango masa wata sama da suhaima,dan haka sallama yayiwa likitan yanufi gida,yabar wasu daga cikin masu kula dashi dazasu taho da shureim gida anjima,sabida likitan yashaida mishi bacci yakeyi yanzu da zaran yatashi baze sake jin ciwonba.
koda sarki ya isa gida.
gurin mahaifiyar shuriem yanufa,anan ya shaida mata duk abinda yafaru da kuma shawarar daya yanke,sosai ta tausawa ɗannata,dan dama ta jima da fahimtar yanada damuwa amman shegen miskilancinshi baze bari ya faɗiba.
Tayi naam ɗari bisa ɗari akan a aura masa suhaima,inda ta ƙara da cewa inyaso inbe sonta daga baya se ya ƙara da kafilat yarinyar sarkin masar datakw masifar sonsa shi kuma be ƙaunarta,sabida shi kafilat ta baro masar ta dawo saudiyya da zama.
Suhaima sarki yasa aka kira masa,tazo cikin natsuwa ta zauna tana sauraron dalilin kiran.
"suhaima shureim bashida lafiy,ance se in anyi masa auran gaggawa lalurar dake damunsa zata kau,shreim bashida tsayayyiyar budurwa bare muje mu nema masa auranta,dan haka amatsayina na mahaifinsa ina neman alfarmarki ki amince ki auri ɗana domin cetoshi daga cikin halin dayake ciki"
Suhaima jinta tayi tana shawagi asararin samaniya,wai itace sarkin makkah yake neman alfarma agurinta,alfarmar da itace zataje nema wai ita ake nema agurinta.
Hawayene kebin fuskarta Tana bin sarkin da kallo.
Tambayarta yasake yi da cewa
"kinyimin alfarmar?"
kai ta ɗaga da hanzari bayan ta ɗaga kan miƙewa tayi da gudu ta koma ɗakinta tana hawaye.
Dama ranar larabane,danhaka ranar alhamis hajiya murja da tawagarta suka iso,dan suhaima ta tura musu saƙo.
Nanfa aka shiga gyaran amarya,mahaifiyar shureim ma baa barta abayaba gurin gyara suhaima.
Kamin wani lokaci tuni ƙasar ta ɗauka dan sarki zeyi aure da hadimarsa.
shureim sanda labarin auranshi da suhaima ya iso kunnensa ba ƙaramin daɗi yajiba,amman be nuna hakan a zahiri ba sema wani shan ƙamshi daya shiga yi.
Ranar jumma ɗaukacin jamaar dake masallacin harami suka shaida ɗaurin auran shureim da suhaima,kowa se murna yake taya su
suhaima ranar tasha kuka kamar ba gobe,wai yau itace da ubanta araye amman se wanine yay mata walicci agurin auranta.
da ƙyar su hajiya murja suka rarrasheta tayi shuru,kwalliya aka shiga yimata sabida anjims zaaje walimar da sarki ya haɗa a fadarshi domin tayasu murna.
Mahaifiyar shureim ce ta shigo ɗakin da ake shirya suhaiman,tace mata taje ɗakin shureim,kayan da zatasa yana gurinshi so in angama mata kwalliyar taje tasa kayan acan.
amsawa suhaima tayi cike dajin kunya.
Bayan angama yimata kwalliyarne,tamiƙe,jiki asanyaye ta nufi ɗakin shureim domin amsar kayan da zata sak ɗin.
muje zuwa.
surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*KANO TO JIDDAH*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
Zahra Muhammad mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*mommyn zahra namiki mgn ta sms baki bani reply ba kinga kenan kece kika manta dani🤣🤣🤣🤣🤣*
*Dedicated to Zahra Bukar*
*21-22*
Tura ƙofar tayi bakinta ɗauke da sallama ta shiga ɗakin.
Ba kowa aciki,jin motsi tayi abayanta da sauri ta waiga dan ganin ko menene.
Shureim ne fitowarshi daga wanka kenanɗaure da towel a kugunshi,yayinda kanshi kuma wani towel dinne yana goge ruwan kanshi.
Duk da akwai naurar busar da gashi a toilet ɗin to shi beson zama a toilet yafiso yafito se yayi.
Da sauri suhaima ta ɗauke idonta akanshi dan gaba ɗaya kunya ce ta kamata.
Takowa yayi cikin takunshi na ƙasaita ya zo ind take tsaye ya tsaya abayanta,har jikinsu na goguwa,da sauri suhaima tai yunkurin barin gurin,sede yarigata,dan kamota yayi stee ta bayan ya haɗata da jikinshi sosai,yayin da hannunshi ke zagaye da mararta sabida karta gudu.
daga shi har ita wani sabon abune ke shiga jikinsu da zuciyarsu,hakanne yasa suhaima lumshe ido ta kwantar ɗa kanta akan ƙirjinshi.
Janta yayi a hankali suka nufi gaban mirror ahaka,kallon juna suke ta cikin mirror ɗin,kuma steel shureim be saketa ba,sema wani shinshinata da yakeyi shima yana lumshe idon.
Da kyar ya saketa dan yaji hankalinshi ya fara tashi,yana sakinta,tayi wuf zata gudu,damƙota yayi,ya ɗagata cak ya ɗora akan gado,se mutsu mutsu take nason guduwa.
sakinta yayi yaje ya kulle ƙofar sannan yadawo gaban mirror yazauna yana kallonta ta cikin mirror ɗin,kamar wanda akawa dole yace .
"zo nan"
ba musu ta miƙe a tsorace ta nufeshi,tana zuwa gabanshi ta durƙusa tana jiran umarnin shi,hakan datayi ba ƙaramin daɗi yayiwa shureim ba.
"Taso ki shiryani nima lokaci na tafiya"ya faɗi yana kallonta.
idon suhaima kamar kwaɗo,ta waresi tana kallonshi,bakinta har rawa yake gurin furta
"yallaɓai ay ni ban iya shirya manya ba,ni banma san yadda ake shirin irin naku ba"ta fadi harda gumi na keto mata
"Ay dama ba cewa akayi kin iya ba,koya zakiyi yau,dan haka karki ɓatamin lokaci kitashi kiyimin,kuma ni banason dogon magana"
Jikin suhaima kamar wacce aka jonawa shucking haka yake rawa.
Gaban mirror ɗin taje ta jawo mai,ta fara shafa mishi,harda ƴar kwallarta,shiko wata niimace ke ratsashi aduk sanda hannunta ya taɓa fatar jikinshi..
Haka taita shafeshi da mai,bayan ta gama ta busar mishi da gashi,tsayawa tayi kallon uban maya mayan dake kan mirror ɗin sotake ta gano wanne ne na gashi amman tagaza ganewa,hakanne yasa shureim sa hannu ya zaɓo su yashiga bata ɗaya ɓayan ɗaya tsna shafawa.
bayan ta gama,comb tasa ts gyara gashin.
Gefe ta koma ta zumɓuro baki sannan tace.
"ni na gama"
takowa yayi yazo inda take,har lokacin bata dena turo bakinba,yana ƙarasowa kanta ya riƙe,sannan ya manna bakinshi akan nata yashiga kissing ɗinta.
Cikin solo da ƙwarewa yakw shan bakin nata,su suhaima ba baka ba kunne se zuci da gangar jiki.
Shi kanshi shureim,bada niyyar jin daɗi yaje yin kiss ɗinba,yaje da niyyar yimata hukuncine agameda turo masa bakin datayi.amman sede daɗin dayaji baze misaltuba,
Hakanne yasa yaci gaba da kissing ɗinta very hot and romantic,jawota yayi jikinshi,suka faɗa kan gado.
Tun suhaima bata mayar mishi da martani har itama tazo tafara mayarwa,ay farawarta tace tasa shureim ƙara charge.
gaba ɗaya ya gama yimata rumfa da faffadan kirjinshi yana kissing ɗunta ahaka,daƙyar suhaima ta cire bakinta acikin nashi tace a shagwaɓe.
"nifa ummi ce tace nazo kabani kayan dazansa bacewa tayi kayimin haka ba"
Shureim wanda gaba ɗaya network ɗinshi rawa yake,a hankali ya furta.
"nasani ay,to amman ayke matatace,inason insamu natsuwa daga garekine,shiyasa namiki hakan"
Shuru suhaima tayi tana jinshi,ya miƙe ds ƙyar yaje,ya ɗauko kayan nashi da nata,yadawo ya sameta,kwance akan gadon takasa tashi,dan gaba ɗaya ya kashe mata jiki.
Hannu yasa ya ɗagota,ya zuge zip ɗin rigar jikinta dayake a tsaye suke,take rigar ta faɗi ƙasa,yarage daga fant se bra ne jikin suhaima.
kunyace ta kama suhaima musamman ganin irin mayen kallon da shureim yake mata,domin kawar da kallonne yasa tayi saurin shigewa jikinshi,tana mishi kukan shagwaɓa,harda bubbuga ƙafa takeyi aƙasa.
Shureim,rungumo yayi sosai yashiga rarrashinta,gami da cewa.
"ya isa haka faɗamin me kikeso?"
cikin siririyar muryarta tace.
"ni sanyi nakeji kasamin kayan don Allah mutafi"
"bade sanyiba,sede kice kunya,dan gashinan jikin ki da ɗumi,kice bakyason naga miki boobs ne shine kawai"
Suhaima jin maganar tayi tamkar saukar aradu sabida kunya.
seda suka ɓata lokaci sosai sannan suka shirya,cikin shigar,kayan da kuka gani a hotonsu😁
sosai sukayi kyau,janta yayi suka fice abun mamaki ba kowa agidan duk sun tafi walimar,harabar gidan suka fito anan suka tarar da comber na motocin da zasu rakasu ƙofar fadar,duk da ba nisa.
koda suka isa gurin taron,kabbara ce kawai ke tashi,ana ɗaukarsu hoto,koni sun burgeni har suka isa gurin zaman da aka tanadar dominsu.
Kafilat ƴa ga sarkin masar tana ɗaya daga cikin mahalarta taron,tazo taga abinda suhaima tafita dashi da har shureim ya zaɓeta akanta.
koda taga suhaima kukane ya kubce mata,dan nesa ba kusaba suhaima tafita diri me kyau da ɗaukar hankali,kyau kawai kafilat tafi Suhaima dashi kasancewarta balarabiya ta ƙasar masar.
Har aka gama taron kafilat bata dena kuka ba,amman fa tasha alwashin seta hanasu jin daɗin zamansu,sabida bazata jure ganin shureim da suhaima ba ita ba.
se washegari aka kai suhaima gidan mijinta dayagaji da haɗuwa,sede fatan Allah yabada zamal lfy.
Shureim dama ya ƙosa kowa ya watse yabar mishi matarshi.
shikaɗai ya shiga ɗakin sallamarshi.
Alwala yasa ta ɗauro sukayi sallah rakaa ɓiyu domin godewa Allah.
Bayan sun idar,Apple kawai sukaci sukayo brush,sukabi lafiyar gado.
Asuba ta gari
muje zuwa
Surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*KANO TO JIDDAH*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*Daga yanzu har na gama kano to jiddah na matan aurene,ban amincewa kowacce budurwa taci gaba da karantawa ba,akiyaye pls🙏🙏*
*Don Allah a ɗanyi haƙuri da gyaran da zanyi,🙏🙏🙏🙏typing biyu nayi yau,na farko shine wanda na turo muku yau,to se bayan na gamashi sena tuno ay suhaima nace bata magana,sena koma nayi wani page,wanda bata maganar,to mistake da na samu,gurin posting ne,memakon inturo wanda bata maganan sena turo wanda nasa tayi,so don Allah kumin afuwa,da naso inturo ɗayan senayi tunanin ze birkita littafin shiyasa banturoba,so labarin ze ɗora a suhaima bata magana,don haka amin uzuri,wlh saurine gurin posting ya janyo hakan*
*dedicated to zahra bukar*
*23-24*
Suhaima duk jinta take wani iri kwanciyar dasukayi da shureim kan gado ɗaya,sr juyi take ta kasa bacci.
Shima shureim ba baccin yakeba,jin motsin suhaima yayi yawane,yasa ya matso da ita jikinshi,yayi mata rumfa da ƙirjinshi ya matso da bakinshi dede nata suna gogar juna yace cikin tattausar murya.
"me ya hanaki bacci har yanzu?"
Lumshe ido tayi sannan ta buɗe su akansa,se ta girgiza kai.
Nufinta ba komai kenan.
Murmushi yayi ya ƙara mannata da ƙirjinshi,sannan yace.
"kinso inmiki abinda ze saki baccin?"
kai ta ɗaga,dan batasan me ze matan ba.
Hular kanta ya cire,sannan ya fara wasa da gashin kanta,yana hura mata iska a kunne,zuwacan,yafara gangarow ƙasa,zuwa wuyanta,yana shinshinata,yana shaƙar ƙamshin dake fita a wuyan nata(gareki kande!!! shafa turare a wuya da bayan kunne yanada muhimmanci da ƙasan boobs da tsakiyarsu,da hammata,se matse matsin cinya,da tsakanin mazaune ta baya,ita kuma haq asamata almiski,in baayi dan jin daɗiba pls ayi kodan kada garbati ya shinshino wari da tsami,🤣)
Dirar hannunshi kan boobs ɗinta seda dukansu suka ɗauke wuta na ƴan mintuna.
shafasu yakeyi,yana ɗan matsawa,dagashi har ita numfashi kawai suke ja,sannu a hankali yafara ɓalle botir ɗin gaban rigarta,yana sa fuskarshi a tsakanin boobs ɗin ta yana gogawa,sannu a hankali ya zame rigar,wanda kusan atare ya ciresu da rigar jikinshi,manna bakinshi yayi anata yashiga kissing ɗinta,itama tana biye mishi,ahaka har yacire bra ɗin dake jikinta,
A tsatstsaye suke suna kallonshi,sun cika sun tumbatsa,gasu farare dasu,hannu yasa yana wasa dasu,zuwacan ya kafa bakinshi akai yafara surcking ɗinsu,very hot and romantic,suhaima kukan daɗi shureim kukan daɗi,(gareka garbati,sucking ɗin,boobs ɗin matarka,koda kuwa haihuwarta goma yana da amfani matuƙa,riba biyu ne,nafarko de zakuji daɗi,na biyu kuma kariyace ga matarka,daga haɗarin kamuwa da ciwon cancer,so ko bazaki don jin daɗinba,kayi kodan kareta daga ciwon cancer,kodan kare mutunci da martabar aljihunka🙏🙏)
Gaba ɗaya basu cikin hayyacinsu daga shi har ita,hannu yasa domin cire mata pant,sede idon da suhaima take zarewa,ga rawar da jikinta yakeyi kamar mazari,shi ya tabbatar masa a tsorace take,shiko baze taɓa kusantarta tana cikin halin tsoron shiba,dan ze iya jimata ciwo,hakanne yasa ya fasa abinda yayi niyyar.
kamota yayi ya haɗa ƙirjinsu guri ɗaya,zuciyarsu na bugawa atare,hakan sosai yayiwa shureim daɗi sabida boobs ɗin suhaima dake tottokare da ƙirjinshi,se ƙara manna yakeyi da ƙirjin nashi.
kamin wani lokaci tuni suhaima tayi bacci akan ƙirjin nashi,se shafa bayanta yakeyi,seda baccin yayi nauyi sannan ya lallaɓa ya kwantar da ita,shikuma yashiga toilet.
ya jima aciki yana sakarwa kansa ruwan sanyi sannan yayi wankan tsarki,ya ɗauro alwala yafito ya shimfiɗa dardums,yatada kabbarar sallah.
kwana yayi yana nafilfilu da adduoi,kiran sallar asubane yasa yasallame,dayake akusa da gadon yake hannu yasa ta ƙasan bargon yana yiwa suhaima tafiyar ƙadagare a ƙafarta,miƙewa tayi zaune tana murje ido,
binshi tayi da kallon se taga ba ita yake kalloba,dubanta takai inda yake kallon.
Ƙara taɗan saki,ta maida jikinta cikin bargon,sabida kamashi da tayi yana kallemata na shanunta..
Murmushi kawai yayi yamiƙe yashiga toilet yayi tsarki ya ɗauro sabuwar alwala,ya fito,kamin yafito,tuni ta maida kayan baccinta,dan haka yana fitowa,ta shige toilet ɗin,wanka tayi sannan ta ɗauro alwala tazo yajasu sallah.
suna idarwa,miƙewa yayi,ya ɗauketa gaba ɗayanta bayan yacire mata hijabi yayi toilet da ita.
Se zullo takeyi nason guduwa amman ya hanata,ruwa ya haɗa yay mata wanka tas sannan ya naɗota kamar jinjira yakai kan gado.
sannan ya koma shima yayi yafito ɗaure da towel.
shida kanshi ya kimtsasu,sannan ya ɗauketa cak zuwa ɗakinshi,sabida dama nan ɗakinta ne,yana shiga da ita ya ɗorata kan gado,sannan shima ya hau,yaja bargo ya rufesu yajanyota jikinshi,suka koma bacci.
muje zuwa
Surbajo for life.
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*KANO TO JIDDAH*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*Dedicated to zahra bukar*
*25-26*
Suhaima uwar son jiki lafewa tayi a ƙirjinshi suka cigaba da baccinsu.
Bugun da akewa ƙofar falon gidan shi ya farkar dasu a firgice,cigaba akayi da buga ƙofar,Rai aɓace,shureim yasako takalmi ya kamo hannun suhaima suka fita zuwa falon.
Kafilat ce atsaye taci kwalliya cikin doguwar riga light blue,yayin da tayi rolling da jan gyale,kafarta sanye cikin jan takalmi yayinda hannunta riƙe da jar jaka,glass ne baƙi a fuskarta.
Tana ganinsu,da sauri taje ta rungume shureim,tana faɗin.
"Ango ykk"
Rungumeta shima yayi ya sumbaceta a goshi,badan komaiba sedan haka aladarsu take,sannan yace.
"lafiya lau,"
Daga haka sakinta yayi yanufi kan kujera ya zauna,Sannu da zuwa suhaima tamata daga inda take,ta hanyar ɗaga mata hannu da yin ƙasa da kai,amman kafilat tahowa tayi ta rungume suhaima tamata kiss a goshi,tana faɗin.
"Amarya ykk ya amarci?"
Murmushi kawai suhaima tayi tayi ƙasa da kanta.
Gurin shureim suka nufa,suma suka zauna,shureim ne yakai dubansa gurin kafilat yace.
"ke inbanda abunki wayace miki ana kawowa ango da amarya ziyara adaidai wannan lokacin?"
Maganar ta ɓata ranta,amman bata da yadda zatayi,se ta ƙirƙiro murmushi tace.
"Ayya kuyi haƙuri nasan ba daɗi irin hakan,dama wlh Abbana na tambaya akan zanzo nayi hutu agidanka,shine ya amince,yace nazo ɗin,amman naga kamar bakayi murna da zuwanaba,bari inshaida mishi awaya cewa amarci kuke ci yanzu"ta ƙarasa maganar tana murmushi.
Shuru shureim yayi yana ƙaremata kallo,tabbas yasan ƙarya takeyi,to amman kuma baze iya korar taba,badan komaiba sedan daraja baƙonka.
miƙewa yayi yana faɗin.
"lah,base kin faɗa masa ba,muna maraba da zuwanki hutu gidanmu,"daga haka shigewa ɗaki yayi.
Miƙewa suhaima tayi tabishi abaya,tana shiga ya rungumota jikinshi yana tsotsar bakinta.
Sunyi nisa cikin shanbakin junansu,kawai se ganin kafilat sukayi tsaye akansu,tana murmushi tana kewaya ɗakin tana faɗin.
"kai gaskiya gidanku yayi kyau wlh,ji wani haɗaɗɗen gado"ta faɗi sanda ta zube akan gadon.
Da sauri suka saki junansu,toilet,shureim yashige,yayinda suhaima duk ta daburce sabida jin kunya,se soshe soshe takeyi.
murmushi kafilat tayi sannan tace.
"muje ki nunamin ɗakina,nagaji sosai,sonake nayi wanka,na huta"
Jiki a sanyaye,suhaima tayi gaba itakuma tabita abaya,zuwa ɗakin,acikin ɗakunan dasuke ƙasa suhaima takaita,shiga ciki tayi,ta zauna,har suhaima ta juya zata fita se kafilat tace.
"Don Allah in bazaki damuba,kiɗan haɗamin ruwan wankan"
Ba musu suhaima ta juya zuwa toilet ɗin ta haɗa mata tafito zata fice,sake tsayar da ita tayi tace mata.
"Nagode,amman don Allah kiɗan jirani,inshiga wankan in fito wlh tsoro nakeji"
Guri suhaima tasamu ta zauna sannan kafilat ta shiga wankan,seda ta jima sannan ta fito.
koda tafito,hand drayer taba suhaima ta busar mata da gashi,shima ba musu tayi mata yadda ta buƙata.
Shiko shureim tunda yafito,yaga ba suhaima a ɗakin ranshi ne ya ɓaci,dan yafiso tazo yamata wanka ya shiryata kamin ya shirya,yajima a zaune amman ba ita ba alamunta.
Shiryawa yayi yafita falo,zamansa ba wuya yaji ƙarar bell alamun sunada baƙo,rai aɓace yanufi ƙofar ya buɗe,matane,sun kai su goma,ɗauke da kulolin abinci,basu hanya yayi suka shige,bayan sun gaisheshi.
Abincin suka ajiye agabanshi,sannan,sukace,mahaifinshine yaturosu amatsayin masu aykin gidan gaba ɗaya.
Ana haka sega,suhaima da kafilat,sunfito,bame ganin suhaima yace itace me gidan,duba da yadda kafilat ta haɗe cikin wasu riga da wando,masu bin jiki,farare,sunyi matuƙar yimata kyau se ƙamshi takeyi,itako,suhaima duk tayi wani iri,kamar yar aykinta,dan kafilat hanata fita tayi,seda tajira tagama shiryawa sannan suka fito.
Ran Shureim gaba ɗaya yagama ɓaci,da ganin suhaima ahaka,shida duk azatonshi taje ɗakinta ne ts shirya ashe ba haka bane.
Koda suka ƙaraso gurin shi kujerar dayake kai kan hannunta kafilat taje ta zauna,yayinda suhaima ta zauna aƙasa ɗan nesa dasu,ko ince kusa da masu aykin tazauna,wanda hakan ya janyo ta saje dasu.
Rai aɓace shureim yace.
"ga abinci nan ankawo,sannan wainnan ƴan aykine,aka kawo mana seki rabawa kowa aykinta"
Carab kafilat ta amshi zancan da cewa.
"waya cemaka mata baƙaƙen fata kamar mune,?musamman matan nigeria,ay basa son masu ayki,acewarsu kwace musu miji takeyi,hakanne yasa suka fison sudunga aykinsu kowanne irine,da kansu,kuma duk kuɗin mijinsu dakansu sukeyin komai,bakaji kwanaki ma shugaban ƙasarsu ya faɗa ba,yace aykin matarshi,ta dafa mushi abinci,ta gyara mishi other room,"ta ƙarasa maganar tana murmushi.
Dubansa yakai gurin suhaima,dake zaune tanajin su,sannan yace.
"kinji abinda kafilat tace,wai hakane bakwason masu ayki?"
Suhaima tanaso tayimasa ƙarin bayani,amman tasan ba ganewa zasuyiba tunda ba magana zata iyaba,hakanne yasa kawai ta ɗaga mishi kai.
Mamakine yakamashi,yakai dubansa gurinta yace.
"Nanfa ba nigeria bane,gidane ns sarauta,taya a matsayinki na matata,ace kece meyin komai da kanki,gaskiya ban aminceba,wannan ay se girmana ya zube".
kafilat tace da sauri.
"Aki kenan,to ay sucan baruwansu da muƙamin mijinsu,matar shugaban ƙasarsu ma dakanta take shiga kitchen ta dafa abinci inji mijinta,taya se kaine zakace zaka sauketa akan tsarin aladar ƙasarsu?"
Sake tambayar suhaima yayi dan beson yayi abinda bata so,ayko seta sake ɗaga kai akan batason masu ayki.
Dan haka kai tsaye shureim ya sallamesu kamar yadda ta buƙata.
Bayan tafitar ƴan aykinne,suhaima ta miƙe,zataje tayi wanka da sauri kafilat ta tsayar ds ita da cewa.
"ukti ya haka zaki tafi bski zubama mijinki abinciba?"
Da sauri suhaima ta dawo ta kwashi kulolin takaisu dinnig sannan ta zuba musu abinci,sun zauna sin faraci kenan,suhaima tasake yunƙurin tafiya yin wanka,da sauri kafilat tace.
"ukti anya ke kuwa ƴar nigeriace,naga su ko matsawa basayi akan mijinsu in yana cin abinci,zama suke suna ma mijinsu labari me daɗi yayinda yake cin abinci,to amman ke naga kamar gudunshi kikeyi"
Shide shureim abincin shi kawai yakeci,itako suhaima haka ta dawo ta zauna tana kallonsu har suka gama cin abincin,suna miƙewa itama tanufi hanyar ɗakinta,tsinkayo muryar kafilat tayi tana cewa shureim.
"gaskiya kasa amaka binciken kasar da matarka tafito,dan inde nigeria to wlh bs haka sukeba,sufa in aka gama cin abinci,basa barin gurin sesun gyara,kuma ko kitchen basa fitowa sesun wanke kayan da akaci abincin,in sukaga lokaci ma ze ƙure musu,basa fitowa sesun gama wani abincin,amman kalli yadda tabar dinning kacs kaca don Allah "
Da sauri suhaima ta dawo ta gyara gurin,sannan koda taje kitchen seda ta wanke komai,zata fita ta kalli agogo taga lokacin ɗora abincin rana yayi,hakane yasa ta fasa fitar ta koma ta shiga hidimar ɗora abincin.
Yayinda kafilat kecan falo ita da shureim suna kallo,ba mecewa ba itace amaryarba,duk da hirar tata labarine akan ƙoƙari da jajircewa da jure wahala irin na matan nigeria,uwa uba kuma,sun iya kwalliya gasu da tsabta,so uku suke wanka arana su sauya kaya,na huɗun da daddare sukeyi,inzasu turaka.
Sosai shureim kejin daɗin hirar badan komaiba sedan yasan shima ya more,tunda ya auri ƴar nigerian,zata yimishi duk abinda kafilat ta faɗa masa.
kiran sallar laasar ne ya tashesu a falon,kafilat na shiga ɗaki ta tuntsure da dariya,sannan tashiga dansewa,
"Suhaima kinyi ganganci,na shiga tsakanina da shuriem,ke hadimarsa ce,kuma nasha washin har abada ahaka zaki nasance agurinshi da gidanshi,dan matarsa ta aure nice"inji kafilat ta faɗi tana tuntsurewa da dariya.
0 comments:
Post a Comment