Yana kwance cikin tafkeken bahon wankan da ke cikin tsfkeken bayin, Sam bai yi kama da bayi ba, domin yana da girma kwarai. Bahon kato ne haka nan daga inda bahon kana iya kallon TV manne jikin bango can daga nesa kadan ga gurin da zaka zauna don yin bahaya (toilet) tsararre ne mai tsafta.
Kwance cikin baho Modibbo ne, daga in da yake cikin bahon da ya cika da ruwan dumi da kuma ruwan sabulu mai shegen kamshi yake canza tashar da yake kallo zuwa (CNN) daga inda yake yana jiyo karan kawankawasa kofar bayin. Shin wanene? Ya tambayi kanshi amma ci gaba yayi da kallonshi. Da ya tuna duk Wanda ya matsu ya jira shi kusan rabin sa'a sannan ya soma cuda jikinshi, ya cire abin da ya toshe rariyar da ruwan ya tsiyaye sannan ya kunna wani dake zubowa daga inda aka rataye su ya rufa a jikinshi sannan ya dauki karami yana goge sumar kanshi. Bayan yazura lallausan silifas a kafarshi zama yayi kan wata kujera duk dai nan cikin bayin ya shafe jikinshi da mai mai kamashi tare da turaruka ya gyara sumarshi tare da shafa mata nata kalolin.
[8:45AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 02 馃彽
Modibbo yana kashe ma kanshi kudi fiye da zaton mai tunani,mikewa yayi cikin tafiyarshi ta kasaita ya nufi dakin barcinshi don saka tufafi ya kalli kofar da zata kaishi falo sai ya tuna ana jiranshi, din taski yaja sannan ya rufe kofar (bedroom) din shi bayan ya shige tare da fadin ko ma waye zai tafi ne don yanzun lokacinan na kar2 ne. Shirayawa yayi cikin wandon {jeans blue} da rigarsahi mai dogon hannu ya isa kan durowa ya kwashi takardu tare da wayoyinshi ya zuba su cikin aljihu, takalmanshi sawu ciki ne ya saka sannan ya fita.
Vicky ce zaune a falon tana jiranshi,ji yayi tamkar bai ganta ba duk da tsananin son da yake yi mata. Ya nufi hanyar fita, ta taso da sauri tana kiran shi.
Darling prince D P
Ci gaba yayi da tafiya, ta soma gudun sassarfa ta cinma shi ta dafa kafadarshi tana cewa cikin turanci.
Duban ta yayi tamkar ba zai magana ba sannan yace amma kin yi saurin hucowa. Ya taba baki" ina zaton kin manta ni wanene shi yasa kike yi min fushi, bani da lokacin lallashin ya mace duk da son da nake musu. Ki gane bani Yarima Modibbo ke bin mata ba, ni suke bi. Je ki ci gaba da fushi dan kin ganni da wata. " yaci gaba da tafiya yana sake fadin Yanzu lokacin kar2 ne ba na surutu ba.
Ta tsaya ranta a bace,hawaye ya soma zubo mata tana tunanin yaushe ne zata daina kuka saboda prince? Yaron da take matukar so, yaron da mata suke rububinshi, yaron da yake ma mata jan-aji, yaro mai kyau da kwarjini, ta zube ta soma kuka.
Kafin ke dubin ki sun yi Vicky .
Yarima Al-amin kenan. Kenan dan sarki Ismail jikan Abdullahi mai mulkin yankin Bauchi. Matashin yaro dan shekara ashirin da biyu Wanda aka fi sani da YARIMA MODIBBO A malesiya gurin kar2 ake CE mi shi prince
A ZARIA FA?
Katon gida ne ginin kasa mai dauke da sassa kusan goma sha biyu, gida ne ginin kasa tun na da wato ginin gargajiya. Kafatanin 'yan gidan dangin juna ne in ka dauke Fatima'yar mutanen Bauchi da aure ya kawo ta gidan. Yanzun da haka fatimar ce zaune tana tuka tuwon dawa, Bilkisu ta yi sallama ta shigo jikinta sanye da atamfa java, ta rataya jaka kana ganinta kasan daga makaranta take. Bilkisu kyakkyawa ce ta bugawa a Mujalla, domin idan har za'a zuba gasar kyau ta shiga ciki babu abin da zai hana ta lashe gasar 'yar kimanin shekara ashirin da biyu CE. Ta isa gurin mahaifyarta Fatima tana fadin.
Mamarmu sannu da gida Ta dube tace da kulawa duk da kasancewarta'yar fari ta ce "yauwa sannu maigado. { shi ne sunan da ake kiranta da shi } ma'ana mai gadon zinar. Kirarin maisuna Bilkisu.
Yau kin dawo da wuri. Ta ce " Eh, Mamarmu wata kawar mu muka je dubawa da tuni na dawo. Ta ce Allah sarki, bata da lafiya ne?
Zazzabin cizon sauro ne, nan sabon gari suke.
Allah ya bata lafiya. In ji mamar. Amin . Bilkisu ta amsa. Sannan ta nufi dakin mamansu duk da gajiyar dake tattare da ita sai da ta share dakin fes tare da gyara shi. Sannan ta fito ta share tsakar gidan duk da cewa ba'a siminte yake ba, yakan ba da sha'awa in an share .
Asma'u Auta ta shigo da sallama, ta dawo daga Islamiyya tace, Sannu Mamarmu, sannu Aunty Maigado. Bilkisu ta harare ta da sauri ta gano laifinta ta ce, Na manta ne, yi hakuri. Tana yar dariya . Bilkisu ta ce ban son Aunty ki ce min Bilkisu kawai don bana son maigado . Ranar da ki ka kara fada sai na fasa miki baki. Mama ma ta ce. To ai sai a hankali zata saba, mu dai ai ba yanda za ai damu.
[8:45AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 03馃彽
Ta dubi Asma'u.
Auta amso min kwanukan mutanan gidannan in kwashe tuwon nan. Dakuna uku duk da na su hudu sashen Babansu malam mamman kenan matanshi hudu ya'aya ashirin da takwas, don haka kwanukan da Asma'u ta baje gaban Maman mu sai ke ce za'a kaima gidajan layin gaba daya ne, yawancin kwanukan duk sunyi tsatsa da kuma lamba, haka Mamanmu ta ci gaba da kwashe tuwon nan tana zuba ma kowane. Bilkisu ta fito daga daki tana cewa, Mamanmu bari in debo ruwa in kin gama sai na dora ina son na yi wanka.
Tace, ai fa ke kam ko kwado ya San da zamanki gurin wanks. Dariya tayi sannan ta dauki bokiti zuwa gurin rijiya. Kananan yara sun kai hudu suna wasa da kasa a bakin rijiyar, maza uku mace daya macen mai suna Safiya tana zaune tsakiyar tabon da suka kwaba, rigarta duk koko haka nan fuskarta, kanta rabi a tsefe rabi da kitso. Tsaki Bilkisu taja sannan ta ce da su. Kai Ku ta shi a nan kazaman yara kawai." Bala dan babba a cikin su ya kalle ta.
To ina ruwanki dama za ki ce mu ta shi?
Ta samu kanshi ta dan buga dai dai da shigowar mahaifinsu Malam Mamman. Yace ke ke ke kar ki sake ki duke shi, ki shafa mishi bakin jininki
Ta dakata. Me yayi miki? Ko zalinci da mugun Abu za ki nakasa min da namiji gashi ke uwarki bata iya haihuwar ya'ya maza ba. Ya ja tsaki kai Bala. { hahahah wai bala dama bala sunane?} Idi, kuzo muje ciki domin zata iya jefa Ku cikin rijiyar nan yan ubanci ba karya ba ne. Allah ya kyau ta.
Bilkisu hawaye suka zubo mata, ita dai tana matukar mamakin irin tasanar da dukkan dangin mahaifinta 'yan dai-dai-ku suke yi mata ta dibo ruwan ta dawo, yanda taga fuskar Mamanmu tasan cewa ta ji duk me baba yace mata, don haka ta ce kiyi hakuri Mai gado wata rana sai labari .
Da daddare kwance take kan gadonta, gefenta Asma'u ce tana ta shara barcinta, ita kam ta zurfafa cikin tunanin cukurdaddan al'amarinta, kullum tana tambayar kanta shin me ke faruwa da ita ne? Tana da kyau na gani afada, tana da hankali ta sani domin mutane suna fada, tana da ilimi duka biyu wato islama da na boko. Natsuwa da kamun kai kuwa ba a magana, amma me ya hana ta burge maza? Me yasa ba ta da saurayi?me ya hana wani yace yana son ta? Kuka ya kufce mata Wanda ya zama dan kullum. A fili tace. Meke faruwa ne da nine? Wa zai bani amasar tambayata? Shin ko Ubangiji bai kaddaro ni cikin wadanda zasu yi aure ba ne? Allah kai kadai ne mafi sani......... Ta daga hannuwanta Ya Allah Ya Ubangiji halitta kai ne majibancin al'amurana, kafi ni sanin halin da nake ciki, Allah ka zaba min mafi alkairi. Ta maida kai ta kwanta ta soma tuno ita wacece?
Uhm sai an jima.
GIDAN MARINA, shi ne sunan da ake kiran gidanmu a unguwarmu, wato Ojo saboda 'yan gidanmu ita ce sana'an da suka gada daga kakanninsu, kuma ita ce har yau yayanmu suke yinta wato rini. Gidanmu katon gida ne mai dauke da sassa sama da goma. Asalin maigidan shi ne Malam salisu, shi ne mahaifin su Babanmu. Yana da mata hudu 'ya'yanshi talatin da bakwai maza guda goma sha biyar sauran duk mata ne, mahaifinmu yana cikin ya'yan Goggo Amarya shi ne da na uku a gurin ta yana bin mata biyu, kakanmu malam salisu mai rini mutumin kirki da sanin ya kamata, ya rasu tuntuni lokacin ma ba'a haife ni ba, uwargida ma lantana Allah ya yi mata rasuwa, yanzu saura mata uku. Tun rasuwar malam salisu gidan ya lalace rigingimu tare da matsaloli sukayi ma gidan yawa. Gidanmu ba'a cika auran bare ba sai dai dan wannan daki ya auri 'yar wancan daki, suma su ja na su sasan ko kuma cikin dangi na wani gu ya auro kuma dangi na wata unguwar ya auri yar gun, haka suka ke yi har zuwa kan mahaifinmu, wanda suka yi bikin wani abokinsu aka kawo Amarya daga Bauchi, cikin kawayan Amarya idon shi ya kyallo Fatima yar mutanan Bauchi daya daga cikin kawayan Amarya, nan ya birkice kun san bazazzagi da mace. Nan fa ya shiga zarya tsakinin Bauchi da zariya, Fati ta yarda itama tana son Muhammadu, wanda yan gidan basu goyi baya ba, saboda tuni yasan da hatun ladiyo yar kanin mahaifinshi baba isa dake jushi, hakan yasa duk yan gidan kin amin cewa da batun har da mahaifiyarshi goggo Amarya .
Goggonsa ce kurum ta ce ai hakuri ba a san rabo ba, tasa'ya'yanta su shige mishi gaba gurin neman auran, bayan kai-kawo aka biya sadaki sai bikin, ya gina sanshi kamar sauran'yan gidan ginin kasa ciki da falo, aka kawo Fatima dakinta, zaman nasu ba laifi sai dai bata jin dadi'yan gidan sai Goggon sa kurum.
[8:45AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 04馃彽
Bayan'yan watanni sai rayuwa ta canza tun da gara ta kare shi kenan mataloli suka kunno kai cikin zaman nasu, farko ya sakar mata sayan su sabulu, man shafawa, daga baya suturar a shekara dama yake mata itama ya daina, daga baya ma sai ya zama abinci in ya kawo masara ko dawa ko kuma doya to batun cefane can ta gane, cikin haka dangi suka soma tsegumin shekara biyu babu haihuwa gaskiya sai dai ya sake aure, haka ce ta faru. Ladiyo tana jiranshi nan ko aka soma shirin biki Fatima ta zuba ido domin sabon shafi ne na wulakanci ya bude tsakaninta da dangin mijin da kuma shi kanshi maigidan saukin ta daya goggon sasa tana yin kuli to sai tana bata mirji da suya tana biyanta a haka Goggo ladiyo ta shigo cike da gadara da jin kai har zama yayi zama kafin wata biyu ladiyo ciki ya bayyana.
Nan dangin miji suka sakota gaba ko yaransu suka hana ta aika, sukan ce ta abr musu'ya'yansu in taga dama ta haifi nata, ya zama sai dai in tana son aike sai taje, ko kuma ta fita makota ta aika yaransu. Duk wannan ba shi ne tashin hankalinta ba irin yanda Ladiyo ta tsiro tsirfar bata son warin tuyar kuli kuma in taga tunkuzar kuli tana sakata yin amai, kenan'yar sana'ar tata ta barta a halin da ita ne take samu tana rufa ma kanta asiri.
Tabbbas nufin Ladiyo ta samu ta raba ta da sana'arta, maigidan kam ya ce baya son ya kuma ganin kuli ko tunkuza, ta ce amma kasan cewar da wannan sana'ar na dogara ko? Nan take ya fusato, kenan ke kike ci da kanki? Ta ce menene marabar dambe da fada? In ka kawo min hatsi ko doya shi kenan, ba kudin cefane ba na nika ko na ice, sabulu, man shafawa duk a jikina suke fita, ya ce to koma menene dai a daina min kuli, tace gaskiya ba zata yiwu ba, ni kenan kullum sai dai dangi su taimaka min? Ya ce kanki aka soma? ai ba kanki mata suka fara cefane ba, don haka ki canza sana'a, ta ce amma ai ita Ladiyo kana bata ba dan baka dashi ba ne kake hana ni, saboda haka yanzun na soma yin kuli in ba'a so in yi sai a tsare min komai, " ya fita tare da fadin To bismilla, kiyi ki gani, haka ko washegari ta amso aikinta ta shiga yi, Ladiyo ta fito shi ne kike kulin dan ki ga bana son warin so kike cikina ya zube ne tun da ke ba ki iya samun cikin ko? Bata tanka ba ta ci gaba da aikinta, makira mijin na shigowa da gudu ta shige daki ta hau gado tana ta burgima tare da kakarin amai. Yana ko karasowa ya shiga masifa har da zaginta, a karshe ma dukanta yaso yayi ta shige daki. Washe gari kam ta ce ta gaji gida zata tun da tana da gatanta hakuri kuma ba hauka ba ne. Wannan tsiya, yau miji ya maka gobe mutan gida, uwarmiji sai ta shigo har sasansu ta zage ta tas tana cikin wannan tunanin tana hada kaya, taji muryar Goggo Amarya.
Ina kike 'yar mulki da iko da an ce ki daina aikin kuli saboda mai cikin haihuwa ke naki cikin ban da kashi ba ya iya daukar komai shi ne za ki bar gidan, itama mai baki aikin ai munafunci ne ga mata da yawa kowane sashe ta mika aiki ai yi zasu yi amma dan gulma ta fi son ta ba ki shi yasa bata ciniki to mai farar kafa ta taba ba dole yayi kwantai ba?
Fatima kam shiru ta yi tamkar bata nan, Goggo ta gama masifarta ta fita,itama ta dauko kayanta da saka su cikin garin yayi zafi ta fita a waje yayyan maigidan ne su biyu sani da Rabi'u suka ce ina za ki? Ta ce zan yi tafiya ne, suka ce in dai yaji ne kiyi hakuri, ta ce kai ita ta gaji gara taje garin su.
Daf da magriba ta iso Bauchi, sanda ta shiga gidan su mahaifiyarta tana alwala ta ce lafiya kuwa? Murmushi taye tare da fadin lafiya kalau bayan sun yi sallah sun ci abinci nan ta shiga zayyano ma Umma abin da ya faru tare da halin da take ciki. Umma ta ce bari Malam ya shigo.
Iyayanta suna da mutunci tare da sanin ya kamata, suna son Fatima sosai, saboda ita kadai ce ya mace a cikin 'ya'yansu maza guda biyu. Aminu da Abubakar wadanda suke kasuwancinsu a nan babbar kasuwar Bauchi, kuma suna da iyalansu suna matukar kula da iyayansu da kuma Fatima.
Sun hada mahaifinsu da yayyanta sun yanke shawarar in yazo biko za'a ja mishi kunne sannan ta koma, ta ce ita in so samu ne a raba Auren amma sai mahaifinta ya ce ba zai yiwu su kashe mata aure ba, ta je ta ci gaba da hakuri. Satin ta daya sannan 'yan uwanshi suka zo shima sakamakon yanda 'yan uwanshi suka matsa mishi da magana har da makota sannan ya yarda yazo bikon tare da'yan uwan nashi.
An ja mishi kunne 'yan uwanta sun hada mata jari tare da dunkuna sun ce taje ta sayi fridge ko ruwan sanyi ne tana saidawa, ta dawo dakinta ta ci gaba da hakuri tare da yan sana'o'inta haka nan ta sai fridge din tana kuma samun alhairi haka Ladiyo ta haihu suka yi ta rawar Kansu har aka yi suna hankalinta kawance, tunda tana sana'arta. Cikin watan ya sake ta da wani dakin yana gamawa ya rigimo Auren karima bazawara ce daga unguwan kaura aka sha biki itama tabi sahun yin cefane da kanta, wankau ta ke yi, shekarara danta sunusi daya ta kuma samun ciki sai fa suka soma gasar haihuwa ita da karima Fatima ta da dai zuba ido ya'yansu maza suke Haifa.
[8:45AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 05馃彽
Kamar wasa ya kuma tada daki ashe zai cika ne wannan karon 'yar yarinya ya dauko musu daga kauyan Turunku Mara kunya nan suka hada kai su uku suna mata habaici wai juya su kam sai zazzaga haihuwa suke, cikin ikon Allah sai ga Fatima itama ta wayi gari da ciki. Kwanci tashi har haihuwa tazo, komai na gama da ciki don kayan yara duk ita ta siya, domin da ta tambaye shi cewa yayi shi dama bai taba sayan kayan jarirai ba kuma kanta ba zai fara ba. Suko sauran kishiyoyin nata sai zundenta suke wai ba saban ba su wance anyi ciki.
Bisa ga yardar Ubangiji ta haifi'yarta ita daya kuma cikin dare, maigidan dama dakin Amarya yake, ita ce ta yanke cibi da kanta dama tana da sabuwar rezarta, sannan in ta zaga sasan Goggo sasa takan tambaye ta yanda zata yanke cibi saboda ko zata haihu cikin dare, ba zata samu mai kira mata Goggo ba. Ta nade' yarta cikin zani da ta huta ta tashi ta kwashe jinin. Da Asubahi Allah ya kara mata karfin jiki ta fito ta dora ruwan wanka, ta wanke 'yarta mai matukar kyau sunusi babban yaron maigidan nasa dan gidan Ladiyo ya leko wai in ji Goggo salame ( amaryarsu kenan) ta ce ki bata kwanon koko, ta ce babanka fa? Ya ce ta yana dakinta ta ce kaje ga kwanonin ka kai sannan ka ce babanku yazo na haihu, da murna yaron ya tafi kun San yara da dokin haihuwa, sai ko gashi ya shigo ba yabo babu fallasa fuskarshi ya dauki yarinyar ya gani ba ko addu'a ya aje ta kilama bai iya addu'ar ba ta ce don Allah ka siyo min dan kayanta mana? Ya dube ta ke Fatima dube ni ba kanki na soma haihuwa ba, bare ki min tsurfa in za ki sha kunu kisha duk sauran kunu ake dama musu.
Ta ce to yanzu wa zai je ya fado ma'yan Bauchi? Ya ce wannan kuma ya rage naki, ni dai bani da kudi haihuwar nan ma ki samu ko masarar fate in Samar miki kada ki sa rai zan yi wata karya dan bani da hali. Ta dube shi cikin takaici tare da da na sanin auranshi. Ta ce duk matan ka ka fifita su kai na, domin ganin idona kana sai musu kayan (shayi) sannan ka musu ragon suna har ma da dan dinkin suna, ban sani ba ko sun fini yi maka biyayya ne? Tsaki yayi sannan yayi waje, tayi ta tashi wani dan saurayi jikan Goggon sasa ta mishi kwatance ya tafi Bauchi don shaida ma iyayanta.
Washe gari kanwar Umma ta biyo dan aike suka dawo ta ci gaba da kula da ita a zaman Inna hausi ta tabbatar Fatima tana matukar hakuri domin komai da kanta take saye don abincin gidan nasu baya ciyo ga Inna hausi sai daiu su yi yar miyarsu haka ake har suna tun ana gobe yan Bauchi suka zo, masara kurum ya miko ko gishiri bai bada ba ita ce ta yi komai, dangi sun hada mata shatara ta arziki, ya kuwa ta ce suna Bilkisu mai gadon zinari. Tubarkalla Masha Allah haka kowa ya ke cewa in ya ga Bilkisu shi ko ubanta ko kaza bai yanka mata ba bare rago amma ta zuba ido kuma ta bar ma Allah.
Haka Bilkisu ta taso cikin sha'awa da kuma birgewa amma gurin uwarta domin mahaifinta bai taba mata ko da wasa ba daga nesa bare ya dauke ta, a haka ta kuma samun cikin Sakina sannan Maryam sunnan Umma ne don haka suke kiran ta momy, sai Ku Asma'u lokacin tana goyon Asma'u abubuwa sun mata yawa ga yara maigidan baya biya musu bukatun 'ya'yansu cima ba dadi, in kana son ci da dan galmi sai ka bude bakin jakarka yara babu karatu su sun usima da suke maiya ya dai saka su amma ya bar iyayan da siyan takarda da biyan dan kudin jarabawa, don haka suka hana yaran zuwa makaranta kowacce ta kama Sana'a tana dora ma ya'yanta suke nan da yake son su bare Fatima wadda ita da ban za duk daya, gidan Hajara ta shiga wato aminiyarta, suka shawarta tace hajara shawara na kawo miki, ta ce ina jin ki Fatima, tace kina dai kallon rayuwar da muke yi a gidanmu. Ba cin kirki sai gasar haihuwa, to ba zan iya ba so nake don Allah ki ma Malam maigidan ki magana ya taimaka min da wani dan taimako haihuwar nan ta tsaya in samu in ji da tarbiyar wadannan ma balle ni mai'ya'ya mata ta ce kin yi tunani zan ko gaya mishi haka ko aka yi rubutu yayi mata haihuwar ta tsaya ta samu ta saka Bilkisu firamare..
[8:45AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 06 馃彽
Sana'o'i ta ringa yi sbulu, omo, manja,mangyada, lallai ana shan wahala da rayuwa,haka nan tayi ta kula da yaranta har suka soma tasawa. wata karamar sallah tazo nan ta shirya ita da yaranta, don zuwa bauchi, Bilkisu yarinya mai kyau da shiga zuci, lokacin shekarunta biyar, kawunta Aminu ya tafi da ita kallon hawan sallah, tana sha'awar kallon hawa ko a zariya tana son zuwa amma Mamanmu bata bari haka suke ce ma fatima, ba wanda ya burge Bilkisu gurin kallon hawan nan kamar wani dan yaron sarki ba zai fi shekara biyar ba tsaran ta kenan, an mishi nadi shima cikin wata alkyabba bayan shi runduna ce guda, yaron yana ta daga ma mutane hannu, itama sai daga hannu take tana mishi bye-bye, ai ko kullum bata da labari sai na Yarima. haka kawunta ya ce mata sunanshi har suka bar bauchi suka dawo zariya lbrin yarima take yi haka nan kuma sai ta shiga yin mafarkin yarima. kullum ta kwanta sai tace tayi mafarki sun wasa da yarima har abin ya ishi mamanmu tace kada in kuma jin zance yariman nan,
don haka ko tayi sai tayi shiru. kowane sassa zundenta suke wai ta ki dora ma yara talla gata da ya'ya mata, in ta tashi aurar da su saga ni me zata kai ma ya'ya daki? sam wannan bai damu mamanmu ba ita dai burinta shine taga 'ya'yanta sun samu tarbiya tare da kulawa. Bilkisu yarinya ce mai tsananin hakuri da zurfin ciki, tana da kwazon karatu da son karatu, sabanin Sakina mai fada da kin raini don haka duk kishiyoyin mamanmu ta tsane su matuka, Maryam ko sai dai fushi da miskilanci. Asma'u auta itama akwai tsiwa tun tana karamarta, yanda yayyinu suk dukan Bilkisu sai dai ta yi kuka. Asma'u kam bata raga ma abokan goyonta shi yasa rigima kullum. Salame ta shiga dakin karima tana fadin ke 'yar gari king uwar mata? Me tayi? In ji karima bayan ta bada dukkan hnkalinta, Yau kuma takalma silifas sababbi ta sai musu. kan ta yi magana sai ga Ladiyo, kunga uwar mata? A gindinsu zata kare an siyo musu silifa. Karima taja tsaki ai ta haifar ma kanta wahala mata kai ta musu bauta ko gidan Miji suka je ba ka huta ba, mu ko masu mazan da farko in sun kawo karfi sai dai mu kwanta su mana su ma kannansu matan. salame ta ce ai Allah ya taimake mu da muka fara da maza. Ladiyo ta ce ni duk ba wannan ya dame ni ba, irin in ma kalli Bilkisun nan yarinya kyau tamkar aljana? salame ta ce kuma tafi sonta ba, tsorona daya kada wani mai halin ya aure t. Ladiyo tace kada nima ina wannan tunanin amma ga shawara ta rada musu wata magana a kunnuwansu, suka saki dariya tare da fadin kin kawo shawara. Bilkisu da kannanta cikin kayan islamiya suka nufi islamiyya, sai da ta raka kannanta kofar ajinsu Sakina da mami, sannan ta tafi ajinsu, duk malaman makarantar sun son Bilkisu saboda kokarinta tare da hazaka ga ladabi ga kuma tsafta duk da cewa kayan makarantar tasu sun tsufa amma tsaf suke a wanke. ta shiga suka soma karatu, basu dade ba wani malami ya shiga da wata yarinya sabuwar zuwa ce, duk ba zata fi Bilkisu ba, ta shigo tana yan kalle-kalle alamun bakunta Bilkisu ta kalle ta cike da murmushi,
[8:45AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 07 馃彽
don haka sai ta je ta zauna kusa da bilkisu. Bayan sun tashi sun fita bilkisu tace yaya sununki? Ta ce Mansura Sadik, ke fa? Ta ce ni sunana B M S, da fatan zamu zama kawaye? Mansura cikin murna ta ce. Insha Allahu. Ta debo kannanta itama da kaninta Abba ta dakko shi daga ajin da aka kaishi suka jero suna hira. Gidan su Mansura ba shi da nisa da islamiya, don haka Mansura ta roki Bilkisu ta shigo ta gaida Ummanta, jikin Bilkisu yayi sanyi da ganin daular da su Mansura suke ciki, lallai Mansura ba abokiyar yinta bace, domin an ce kwarya ta bi kwary. hajiya mero mahaifyar mansura nurse ce mahaifinta kuwa ma'aikaci ne a {G T Bank} da ke kaduna.
makarantar bokonsu ta kudi ce mai tsada, haka ne yasa Bilkisu dan Jan jiki da Mansura, amma Mansura sai ta kara shige ma Bilkisu ta ki sai wata rana bata da lafiya don haka bata samu zuwa islamiyya ba hankalin Mansura ya tashi don haka kuwa ana tashi ta bi su Sakina don ta dubo Bilkisu. Sam Mansura bata damu da yanda taga gidan su Bilkisu ba, har ma da ta samu Mamanmu ta gama tuwo sai da taci, hakan ya sanyaya zuciyar Bilkisu don tana son Mansura musamman ma da ya ke Mansura iyayanta sun kasance yan gombe, tana ganin gombe da Bauchi kamar daya ne gunta tana son yan Bauchi dangin uwa masu sonta, tana ganin kamar bata da masu sonta sai yan Bauchi shi yasa duk inda ta ga yan Bauchi tana girmamamasu, Mansura tana da son tuwo don haka sai ta samu gurin zuwa.
Ko Bilkisu bata nan Mansura tana zuwa gurin Mamanmu jin ta take tamkar mahifiyarta waton Ummanta suka niyan gidan sai suka tsiri sakin habaici, Bilkisu ma nan ta saki jiki da Umma Umma da Mamanmu suka zama kawaye, haka ya sosa ran su Ladiyo musamman da suka ga tana basu kayan sawa zuwa dan abin marmari.
Bilkisu tana zaune ciki wani ciyayi mai kama da cafet guri sanyi da iska yanda yake Kore fatau ya bata sha'awa ga fararan tattabaru suna tashi wasu suna sauka. Can daga nesa sosai take hango dan matashin yaron tasaranta bisa kan doki yana isowa gurinta ya tsaya cike jin kai. Yace ke wa ya kawo ki gonata?
Ta dube shi nan ne gonarka? Kafin ya bata amsa sai ga wasu mutane su biyu suka kama mishi linzamin doki ya sauka, sannan ya isa wata kujera dake can gefe irin ta sarakannan ya zauna sai ga wasu mutane cikin jaja yan kaya sun tsaya a bayanshi, can kuma sai yace na sallame Ku. Suna tafiya ya dawo gurin Bilkisu ya zauna kusa da ita ke yar sakin wane lardi ne? Ta dube shi ba ni da alaka da sarauta. Ta bashi amsa, yace kin sanni? Ta dube shi cike da mamaki kai ba ka da gane mutane so nawa muna wasa da kai? Firgigita ta farka daga bacci yau mafarkinta ba irin na sauran ranaku ba ne, domin sauran ranakun tafi mafarkin suna wasan kwallon kafa, ko na raga koma na tebur, suna hira sosai, amma ya kan nuna bai ma Santa ba ne, tayi murmushi, tun tana yar shekara shidda take mafarkin Yarima gashi yanzun tana shekarar karshe a primary shekarar haihuwa kuwa sha daya su Bilkisu an soma zama yammata, kyanta kullum karuwa yake yi.
Hankalin mamanmu ya tashi domin ba ta da kudin da zata yi ma Bilkisu hidima dan zuwa secondary, duk da cewa ta ci domin makarantun gwamantin ma wannan zamanin sai kana da hali. Da kanta taje makarantar da Bilkisun ta ci sun mata lissafin tun daga rijista zuwa uniform da takardu dubu takwas har da dori. Hankalinta ya tashi bata da inda zata samo kudin nan, gidan hajara kawarta ta shiga don yin shawara, hajara ta bata shawarar me zai hana Bilkisu ta yi aikin gida ko na wata uku ne, in yaso sai ta shiga a zango na biyu tun da an amso form. Mamanmu jarumar uwa ce wacce samun kamarta sai an tona, tsamaranta cewa zata zamar wa ya'yanta uwa kuma uba, don haka ta ce ma hajara ni zan yi aikin da kaina wa ki ke ganin zan samu ya nemo min aiki? Hajara ta ce kada ki damu akwai mata masu hali da suke zuwa gurin malam zan dinga musu magana har a dace, shin maigidan naku zai barki?
[8:46AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 08 馃彽
Ta ce tunda ba bani zai yi ba ai batun hanawa ma bata taso ba, shi fa yanda na kula koma menene kije kiyi amma kada ki tambaye shi, sukansu kishiyoyin nawa da yake sonsu baya musu komai, amma don rashin tunani suna nan suna ta zabga gasar haihuwa,yaran bacin kirki bare sutura, karatu kuwa sai dai na zagi ashar kam, kwando-kwando za ki ga dan karamin yaro yana saukewa, gaskiya 'yan gidanmu su ne suke bata ma zage zagi suna, shin haka kowane gida suke yi? Hajara tace a'a akwai dai masu yin amma ba duka ba.. Cike da farin ciki tabar gidan hajara, ta samu Bilkisu da yan kannanta a cikin daki, tana koya musu darasin lissafi, nan ta zayyane ma Bilkisu komai, Bilki ta ce mamanmu ki bari ni nayi aikin in an samu, ta ce a'a nafi soe ni in yi bana son kije ki bata ma masu gidan har su sallame ki, bukatarmu ya zama bata biya ba. tace mamanmu amma kinsan bana fada ko? tace na sani maigado, amma ki bari sai dai an samu din kisan ke yarinya ce ba kowane abu ne zaki iya yin shi ba. Sallamar Mansura ta katse su, suka amsa ta shigo kusa da mamanmu ta zauna sannan tce mamanmu ina kwana? Suja gaisa ta dubi Bilkisu tace "Bily ya dai, yaushe zaki fara shiga school ni dai on monday zan fara zuwa. Bilki tace ni kam ba rana Mansu, kila ma sai second term. Mansura tace akan me? Tace kudi, mamanmu tace kin san ko mai yanzu sai da kudi ana cewa ne dai makarantar gwamnati amma suma duk shegiyar darin ce ga kudin motan zuwa makaranta kullum mansura tace bari Abbanmu yazo week end zan gaya masa. Bilki har suna hada baki da mamanmu, a'a kar ki yi masa magana shima yana ji da nasa iyalin. Mansura tayi shiru, amma a ranta ta raya sai ta fada mashi... Haka kuwa yana dawowa ta gaya mishi, ya tambaye ta ko njawa suke nema? Ta ce ya basu kowanne ita dai bata sani ba, kuma ta san ko ta tambaye su ba zasu fada ba. Dubu goma ya bata yace, gashi ki basu." sai da ta kai kudin mamanmu da yaranta suka je suyi godiya,Bilki kuwa sai da tayi kukan murna, sannan tana ta mamakin dama da gaske ne akwai iyaye masu yiwa 'ya'yansu hidima? Ba sabanin iyayansu mata da wahala? Cikin nasara ta shiga j.s.1 mansura kullum in za su je makaranta sai ta saka direbansu ya biyo sun dauki Bily, sunan da ta ke kiran bilkisu kenan, ita kuma Bilki tace Mansu, wani abin da yake kara ba Bilkisu mamaki shi ne, yanda mafarkin Yarima ke kara yawaita a gare ta, ko gyangyadi take sai ta yi bare barcin dare. saboda sabon da suka yi har ta saka mishi Yarima aboki, shi ko yana kiranta Beauty, tana son sanar da mamanmu amma tasan mamanmu zata ce shirme ne, shi yasa take bar ma cikinta don ko mansu bata taba ba wa lbri ba. cikin haka hajara tazo ta ce, an samu aiki. Mamanmu tace ai ko zan yi,
[8:46AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 09 馃彽
Suka je gidan hajara inda hajiyar da za a yiwa aikin take jiransu.Bayan sun gaisa tadubi mamanmu tayaba da tsaftarta don haka tace girki nake so zaki iya? Mamanmu tace me zai hana.Nan suka sasanta ita da hajiya kilishi, gidanta na nan tudun wada, sun sasanta kan dubu uku, kuma za'a dinga zuwa ana daukarta haka nan za'a dawo da ita ko da ta samu maigidan nasu da batun sai yace,shi ina ruwan shi,ta dai sani dole ran girkinta tazo shima ta mishi,dama tasan haka zai ce,tunda shi dama baya son ma mace tace ko da bani kudin kamu,wani lokaci takan zauna tana tunani, anya maigidansu yana son lahirarshi ta mishi kyau?In'yan abinshi suja motsa haka zai je ya nado tsiranshi yazo ya zauna gaban'ya'yanshi yana ci ba zai sammusu ba in ma yaga suna kallonshi sai yace kai daina kallona ka da ka saka ni in kware.Ko ya fita bakin titi da yamma ya sayi doyarshi da kwai ya zauna yana ci in an ce yara suzo suce yaba da kudin cefane sai yace kai zauna nan kayi wasan ka shareta,kuma fa in yaron nan ya zauna haka zai cinye ya hana yaron, halin wannan mutum sai shi hakika baici sunnanshi ba. Cikin sa'a Mamanmu ta soma aiki tana tafiya da safe in yaranta sun tafi makaranta da sha biyu suke maidota gida, in ta gama musu abincin rana domin tana son ta zo ta sallam yaranta. hajiya kilishi kan ce Dibar musu ki kai musu. Sannan karfe hudu zata koma tayi na dare, in ranar girkinta ne kuma sai shida take tafiya don ta samu ta gama na gida. Su kam su ladiyo, nan suka soma nuna hassada tare da canza mata suna daga uwar mata zuwa boyi. Su yi ta mata habaici tare da maganganu marasa dadi, kafin wani lokaci mamanmu da 'ya'yanta sun canza,sunyi kyau, saboda cima ta canza in ta kawo abincin takan dibar musu ta mika ma ladiyo tace su ba wa yara, suna zaginta suna komai haka zaki ga suna kason su sai kace daukin nama su da ya'yan suna ci tandar harshe. Hajiya kilishi tana da yara mata kusan sa'annin su Bilkisu don haka suna samun kaya. Rayuwa dai ta canza yanzu har da sabulu mai kamshi suke wanka. Cikin haka suka shiga J.S 2 lokacin alamun girma ya soma shigar ma Bilkisu, kyanta ya soma bayyana, duk layin kowa sai zancenta yake yi, sun kuma kara shakuwa da mansura duk in da kaga zara za ka ga wata.Bilkisu tana da kulafucin karatu don haka bata da lokacin komai sai na karatu. Azumi ya matso gashi, lokacin ana fama da rashin kudi a gari, 'yar doyar da maigidan ya kawo buhu daya ce, nan ya kasata gida hudu yace kowa ya kwasa sannan kada wacce tai mishi zancan geron kunu domin ba shi dashi, cikin haka Azumi ya kama. Saboda rashin hankalin su ladiyo sai suka ce ma maigidan su fa kowa tayi girkinta kenan suna kyashin taimakon juna, maigida yace wannan lalurarsu. Mamanmu ta ji dadin hakan domin ya'yanta hudu ne,kuma dama aiki yana mata yawa,ranar girkinta yanzu kam hajiya kilishi tace ki dinga hada girkin tare da yaranki,dama ga alale da kunun tsamiya na sadaka da ake yi ana bai wa al'ummar Annabi sai kurum ta huta da yin girki biyu,in ma dakinta yake sai ta dibi nashi cikin kwano samira da kunu a kofi. Bilkisu taje ta amso, wataran ta roki direban ya kawo nan zaka ga malam maman an baza tabarma tsakar gida ana kwasar gara, cefanan wani kai ka kasa, haka matan ke ce mishi,in sunga yana rawar kan cin abinci ran girkin mamanmu,haka nan mijinta da yayi rabon kayan azumi shinkafa, masara,gero,da kuma suga sai daya ba mamanmu kowanne buhu,jikin kishiyoyinta ya dauki bari bakin cikinsu ya kasa boyuwa ita kam kowa sai da ta dibar mishi har 'yan sauran sassan da su rukarta su goggon sasa tare da matan yayyin maigidan nasu da na kannai. Wato mamanmu mace ce mai rama alkairi ga duk wanda ya mata sharri, tana da matukar hakuri tare da sanin ya kamata, in ban da haka yanda kishiyoyin nan nata suke mata kai har shi kanshi maigidan yafi mata wulakanci akan sauran kishiyoyin nata, amma hakan bai sa tayi tunanin cin zarafinshi ko kishiyoyin ta ba sai ma kyautata musun da take yi, shi yasa kullum cikin ci gaba take. Hatta abincin sadaka ko nata in tayi sai ta basu..
[8:46AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 10馃彽
Bilkisu tana tafe amma duk wanda yasan ta in ya ganta yanzu zai fahimci tana cikin damuwa,duk da cewa dama ita ba mai son hayaniya ba ce, ko yawan dariya akan hanya,ta tsaya kofar gidan su mansura tace Sakina shiga kice ma Mansu in ta shirya tazo mu tafi,mun yi latti. Sakina na saka kai Mansura na fitowa,tace "ashe kun iso?Nima naga shiru nace bari naje gidan na gani shin lafiya?Bilkisu ta dan yi tsaki sannan tace, to lafiya,suka soma lafiya mansu tana korin cewa. Gaskiya bily ban yarda lafiya ba,idanunki kamar kin yi kuka.Tace kawai bana jin dadi ne.Ko a islamiya bilkisu babu kwanciyar hankali duk malamin da ya shigo sai ya gane,saboda zazzakar muryarta mai kayata karatun nasu in suna yi yau adusashe take,haka nan kyakkyawar Fuskarta yau kam a daure take tam.Mansu ma duk ta damu suna tashi bata shiga gida ba sai kannanta tace ma ku shiga gida ku ce ma umma zan gaida mamanmu in dawo, Bilkisu ta dubeta mamanmu tana gidan aiki,mansura ta kada kai na sani ina so ne muyi wata magana,suka nufo gidansu bily.
Sai da suka zauna sannan mansura tace wai me yake damunki ne bily? Bilki tace ba komai Mansura. Ta daga mata hannu alamar tayi shiru, ina baza ki fada min ba to in tafi gidanmu kawai bana son dogon labari. Bilkisu tace to ni ban san ta ina zan soma ba, abinne kamar tatsuniya kin gane! Tun ina karama ne muka taba zuwa sallah bauchi,shi kenan kawuna yaje dani kallon hawan sallah, naga dan sarki, shima yayi hawan, dan yaro ne tamkar ni a wancan lokacin shi ne fa tun daga nan kullum ina cikin mafarkinshi har yanzun. Mansura tace ban gane ba? Bilki tace ai ba zaki gane din ba.donni ma da bani ce ke yi ba zan karyata ne. Mansura tace wane irin mafarki ne haka kullum kina mafarkinshi ya kara girma ko yana nan kamar da? Sannan shi ne sanadin bacin ranki yau? Bilki tace, yana girma nasan zaki sha mamaki in na gaya miki tun daga randa na ganshi, nake mafarkinshi har yau din nan ko gyangyadi ne ya dan sace ni sai nayi mafarkin shi,sunan shi Yarima modibbo, yana da kyau kuma dan kwalisa ne komai nashi da ka'idarshi Komai da lokacinshi, misali baya cin abinci a lokacin karatu,kin gane irin abun yana ce min wasan da yake zuwa muna yi lokacin wasan kenan, awa daya da rabi muke yi sai ya tafi, wai baya son shiga lokacin wani abin, kuma shi ma'abocin son girma ne, baya son raini ni fa da shi har fada muke yace ya girme ni, ni kuma in ce karya ne yanzun nan zaki ga yayi fushi ya tafi nesa dani kafin lokacin tafiyar shi yaya. Mansura taja tsaki, ni don Allah ki gaya min damuwar yau. Bilki tace kin cika garaje baza ki gane ba ne hn ban miki dalla-dalla ba. Haka muka taso tare dashi cikin mafarkina shima yanzun js3 zai je, kin gane ai jiya kuma ita ce ranar da nayi mafarki mafi muni kin aji, wai sai na isa gurin da muka saba wasa, yau ma na riga shi zuwa kamar sauran lokutan, sai dai har lokaci yayi nisa bai iso ba, na soma damuwa ga hadari har an soma yayyafi, dan tsumman riga da siket din da ke jikina suka jike dama sun sha jiki sai suka matse min a jiki iska ta shiga kada min shi, ni kadai a filin Allah,
Kamar daga sama sai naji an dafa ni ta baya ina juyowa sai nagaYarima tsaye,yana sanye ne da riga da wando na farin shara-sharan yadin shi ma din duk ya jike,nace zan tafi dubi duk na jike,ya dubi kirjina,don kirgan dangin daya soma nuna yake kallo,nace zan fa tafi fa,in gaya miski mansu sai jina nayi a jikinshi,na soma kai mishi duk ina cewa,bani son iskanci an ce maka ni yar iska ce?Yace ke wawuya ce beauty wani wasa Zan koya miki In dai takaita miki wai sai gani ni da shi muna...Mansura ta rufe mata baki ita kuma ta fashe da kuka,mansu tace shi ne to na damuwa ba a cikin mafarki ba ne?Nace bara fa kiji tashi nayi na ganni cikin jini...Jini? In ji mansura,bilkisu tace eh shiyasa narasa yanda zan yi,kuma na kasa yaya ma mamanmu tsorona daya kada ace ina da ciki mansura tace gaskiya ne kin sani yanzun muje mu samu.Ummarmu tunda ita tana aikin asibiti ne zata sani,da sauri bilki ta mike.Sun same ta tana sallah suma suka yo alwala har zasu tada salla,mansura tace kin mata malam yace,inda jini jikin mutum bazaiyi salla ba Bilkisu tace ai yace jinin haila ni ko wannan ba haila bace bana ma yin wannan, wannan fa kin ji yanda aka yi jinin fa yazo, basu ji shigowar umma ba sai suka ji tana cewa wane irin jini ne? Tsuru-tsuru suka ji tace da ku nake fa, kuka bilki ta soma yayin da mansura ta soma magana cikin in-ina, gaya mata dai. In ji mansura, cikin kuka bilkisu ta shiga bai wa umma labarinta da Yarima har zuwa jiya, a karshen lbrin ta dora da cewa ni tsorona kada ace ina da ciki. Tamkar umma ta kwashe da dariya, amma sai ta boye tace kin san haila ko? Bilkisu tace malamin fikihunmu yana mana bayani amma ban santa ba, umma tace to haila ce ta same ki, batun mafarki kuwa sai dai na kiya ya dan tsoratani, yanda ki kace tun kina karama, Allah yasa ba aljanu bane suka fake da Yariman da ki ka gani? Kin san suma shu'umai ne, amma zan yi batun da mamanku.
Sannan ta dube su tace, yanzu abin da zan ce muku shi ne dake da ki ka balaga da ita din da bata soma ba na sani tana kan hanya, ku kula. ta dai ja musu kunne.ta fita sai gata da part ta nuna mata yanda zata yi amfani da shi, umma ta samu mamanmu sun zanta kan batun mafarkin Bilkisu, mama tace bana zaton maigado tana da aijanu, kinsan in ka kallafa abu a rai dole ne kayi mafarkinshi, tun tana karama da taga dan sarkin garinmu shi kenan bata da zance sai nashi. Umma tace to bilkisu tana da nutsuwa sai dai ki kara ja mata kunne ko in ce nasiha, tunda yanzun ta girma sai da saka ido, dan yau sai Allah. Mamanmu tace Insha Allah komai zai zo da sauki,Allah dai ya shirya mana daukacin ya'yan musulmi.Umma tace.Amin,yau din ce tayi wuya,sai ki ga yarinya ta tashi da hankali da nutsuwa,ki daga ki yi mata tarbiyar kwarai daga baya sai kiga samari ko wasu kawaye sun rusa komai. Mamanmu tace kwarai dole ne mu sanya ido kan ya'yanmu, wadannan irin kawaye ne suke tare dasu,haka nan kar mu yarda da samarin banza.
[8:46AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 11馃彽
Da wannan hirar suka yi bankwana.Tun daga wannan lokacin take tsoran maza sam bata son wata hulda ta shiga tsakaninta da kowane namiji,balle da mamanmu ta kara nuna mata cewa kar ta yarda da 'yan kananan samarin nana masu bata yara suna kai su suna barowa.Mamanmu tace ki lura don shi da namiji duk abin da yayi ado ne, ke kam mace ce duk in ki ka yarda aka bar miki abin kunya shi kenan rayuwarki ta lalace,koda ba ai miki ciki ba da an kau miki da budurcinki shi kenan,duk mijin da kika aura baki da wata daraja ko mutunci a gunshi in me kawaici ne zai daure ya barki da Allah,in ko mai zafin kishi ko in ce wanda ba zai iya hakurin bane kisha magana gori har yaranki suta so yana miki don haka ki kula. Bilkisu yarinya ce amma akwai zurfin tunani, domin tun daga nan tasa ma kanta da nazari kan maza ana ta ganin maza sun cika son kansu musamman in tayh duba ga mazan gidansu tun daga kan yayun da kannai na mahaifinta tare da shi kanshi mahaifin nata mazan gidansu daidai gwargwado suna samun kudi da irin sana'ar da sukeyi. Amma sam ba sa biyama iyalansu bukatu, ya'yansu babu boko babu islamiyya, sai yawon talla, kusan duk matan gidan su ke ci da kansu da kuma ya'yansu,ba sutura, amma abin da yake bata mamaki yanda su kuma matan ke faman gasar haihuwa tare da fada da kishi mai tsananin a junansu, saboda mijin da bai san darajarsu ba, ita kam ta gode Allah da yasa mama ta kasance uwa agare su don ta tsaya musu da tarbiya da ganin sunyi karatu sun zama yaran kwarai, kuma insha Allah baza su bata kunya ba, sannan su zama rahama gare ta ba kamar yanda yan gida da suke cewa wahala bashi yasa ko cikin mafarkinta yanzun bata sakar ma Yarima fuska sannan ta dage da addu'a kan Allah ya yaye mata mafarkin Yariman nan. Haka nan hasashen umma na cewa, ko Bilkisu tana da aljani ne ya saka mamanmu cikin tunani don haka ta samu mijin Aminiyarta Hajara tai ma malam mudi bayani, shima da ya yi Istihara ya gano bata da aljanin kowa, don haka yace da mamanmu rudin ne kurum irin na mafarki kada ta damu don haka sai ta kwantar da hankalinta.
tare da ci gaba da neman na rufin asirinta gurin Allah
Yau da gobe asarar mai rai in ji yan' magana gashi Bilkisu har an shiga ss1 lokacin tana da shekaru sha shidda, daukacin unguwar Oja da kewayenta labarin kyawun ta ake ita har mamaki take yi idan taga mutane sun shagala da kallonta, farinta irin farin nanne fes jikinta na dauke da lafiyayyar fata me laushi sumul- sumul suma kwance jikin fatar sai ka zata cikin AC take kwana doguwa ce amma ba can ba, dirin jikinta irin mai wahalar samu din nanne danko ta keru, farin da jikin duk na mahaifiyarta ne,
Ko mace'yar uwarta kan shagala gurin kallonta, gefen kumatunta ya kan lotsa ko da magana zata yi shi yasa duk sanda ta fita sai taga jama'a na kallon ta sai dai abin mamaki bata taba samun ko da wasa wani da namiji Yazo yace yana sonta ba, hakan bai dame taba nata ganin rashin sakin fuskar da take yi ne in zata fita da kuma tsoron da ta kema mazan, dama bata bukatarsu tunda ana ta ganin sun cika zalunci tare da dan nema mata hakkinsu shi yasa basu ne a gabanta ba, amma ga mamanmu tana son taga cewa Bilkisu tana da tsayayye kafin ta kare secondary in yaso taci gaba a dakinta, sai ga shi mansura samari sun mata Caa! Haka Sakina da Maryam kannan Bilkisu wadanda ke j.s 2 yanzun haka, sannan'ya'yan su ladiyo duk ba Sufi sha biyu sha uku ba amma duk suna da samari yan cikin gidan yayaran yayin mahaifinsu.
Malam mamman ya shiga dakin mama tana zaune kan dardumar da ta idar da sallar isha'i, ta amsa sallamar da yayi tare da fadin sannu da zuwa, yace yauwa. Ya zauna " Dama nazo ne kan batun Bilkisu , don na kula yarinyar bata da mutunci shi ne ma dalilin da yasa ban taba ganin saurayi yayi kiranta ba, sai dai kannanta, kila tana nufin sai me mota ne ko? To ba zan yarda da zamanta ba, ba ruwana da wata bokon baza can, ke da ki ke daure mata to ki gaya mata na ce aure zan mata, mama ta sanyaya murya sannan tace to kayi hakuri amma ma yarinya take da za ka daga hankalinka?
Yace ke Fatima ban San zancan wofi su suwaiba ba kannanta ba ne? Tani da Amina duk sun sasanta dasu Jibrin, don haka ba ruwana da wani lokaci , su ladiyo sun Fiki tunani, tunda suka sa 'ya'yansu suka fito da miji sai kece oho na fahimci gaskiyar su ladiyo ne da suka ce kin ce ke'yarki sai mai kudi ko?
Zaku ga kudin in nayi sada ka da ita kuma almajiri zan ba sadaka, ya fita yana mai ci gaba da fada har zuwa gurin mahaifiyar shi wato goggo amarya nan ya shaida mata nufinshi na sadakar da Bilkisu ta ce jeka ba da ta in ma mahaukaci zaka ba shi, uwarsu ta ci dogon buri akan su bari ka ji in shaida maka in har ka sakar ma wannan matar taka fuska to zaka yi da ka sani , tunda ta daure ma ya'yan ta mata suna wannan bokon na san cewa tana da mugun kuduri nufinta ta tarasa suyi mana gandan- gandan a cikin gidanka, ya zama kai ba da kayi bata karba saboda ka jibge balagaggu cikin gidanka, tashi kaje duk nufinta ni na sani burinta kenan sai mai kudi....
Yan rigingimu sun faru cikin yan kwanaki in da su ladiyo tare da sauran dangin na maigidan suka yi ta zuga shi yana zuba wa mama da ya'yanta wulakanc. Bilkisu tana zune ta ma kasa cin abinci,saboda hankalinta yana tashe ne, yan kwanakin mansura tana zaune gefenta tana lallashinta, can cikin daki kuma mamanmu ta tasa su Sakina tana musu nasiha kan cewa ba su isa kula samari ba, shekarunsu ko sha biyar basu kai ba sakina tana sha hudu maryam sha uku maigidan ya shigo da fada yana cewa ina Bilkin ne? Da sauri ta mike tana matukar jin tsoro shi, yace fita maza ga bakon ki can waje shi ne mijinki shi na baki, saboda bakin jininmu,na idar da sallar la'asar na tashi ina cewa ina da 'ya duk mai bukata na bashi amma na rasa mai so sai da na toho hanya sannanna ci karo da wannan dan garuwan shima sai da na roke shi arziki da kyar ya yarda sauran ki mishi wulakanci, cikin kuka ta fita yana tsaye jikin gidansu riga daban wando ma haka, kuma duk na shadda, kodaddu sun jike, ta isa gurinshi tace sannu da zuwa.
Baki ya saki yana kallonta,cikin in-ina yace ke ce kece babanki ya bani?Ta daga kai yace,tab gaskiya kin fi karfina,wannan rike ki ai sai gwamnatin tarayayya,karamar hukuma ma kam ba zata iya ba.Ya tafi yana waiwayanta yana cewa kaga mutum zai cuce ni? gida ta koma cikin jin dadi tana gaya masu mansura da su mamanmu abin da ke faruwa.Muryar babansu taji ya kwala mata kira, da sauri ta fita.Ya dube ta kun gama magana ko?Tace ya dai tafi ne.Yace kina nufin baku daidaita ba?Ta daga kai alamar eh.Yace ki dai ce kin koreshi,yau ko kyaci ubank.Ya ciro igiyar guga ya shiga dukanta,mama sarkin hakuri tana jiyo su kuma zuciyarta na zafi amma haka ta daure bata fito ba,sauran matan sai dariya suke ba wadda tace ai hakuri,jina-jina yayi mata ya fita yana zage-zage,ru mansura suka kamata suna kuka suka shige daki.Tun daga nan kullum cikin turo mata maza yake,amma kamar hadin baki duk wanda yazo sai yace tafi karfinshi hakan nan shima bai fasa dukanta ba,har bikin su suwaiba yazo aka yi biki aka watse Sannan Bilki ta dan sama sauki sai dai sun sha habaici ranar bikin, wannan bai dame su Bilkisu ba. Maryam zo ki jawo min ruwan wanke wanke. Cewar Bilkisu, tace Allah sarki Anty Bilkisu dazun fa nice na ja miki na wanki ga Sakina can Allah bata komai. Sakina ta fito tana cewa, sannu da cewa bana komai wa ke gyaran daki? Bilki tace maryam ja min ruwa sakina je ki karasa gyaran dakin, ladiyo ta dubi karima tace. Allah mun huta su tani ana can dakin kai, salame ta cafe ai yafi musu ni in bar 'yata gwansame duk wanda ya shigo ya kasa gane waye uwa wacece yar. Karima ta kalli Bilkisu, sannan ta kalli su Salame, Ya'yan namu sun da farin jini ne, amma wasu zaki ga ga dai kyau sai a rasa ma shinshini. Ladiyo tace kin kaita da nisa, kin manta da wadda uwar ke fita yawo boyi gidan masu dashi, ya'yan na gantalin boko, amma babu mashinshini. Karima tace babu ya babbar kullum sai uban ya kima, su kasa dariya,daidai sanda Sakina tazo tana ce ma Bilkisu.Anti Bilki ina abin kwashe shararmu
0 comments:
Post a Comment