Yarima yayi murmushi dama so yake ya kunna Magaji,kuma yayi nasara.Ya dubi Bily sannan ya wuce tare da cewa,wa ma sunanki? Biyo ni tace,Hum sannan tabisa ranta fal kunci gurin Umma suka soma shiga ta zauna gaban Umma kanta akasa tana gaida Umman,ita ko Umma Allah ya dora mata son Bily,don haka ta jawota jikinta tana cewa matso nan 鈥榶ata,yaya jikin?Cike da kunya Bily tace da sauki.Yarima ko cewa yayi da Allah malama taso in kaiki ni sauri nakeyi,Umma ta daure fuska ta dubesa,bai sake magana ba,Umma tace babu inda ke miki ciwo ko?Tace a鈥榓 to kina bukatar wani abu?Nan ma tace a鈥榓,har ta mike zasu fita Umma tace,amm Bily babana dai baya miki wani abu ko?Da sauri ta dubesa ya ko banko mata harara ta kautar da kai sannan tace ba komai Umma,tace ki gaya min in dai da matsala,ba komai Umma cewar Bily,tace to zanba jakadiya sako ta kawo miki,tace to suka fita duk tausayin Bily ya cika ta don taga hararar da Yarima ya mata da alama tsoransa takeji.Sun zaga ko鈥榠na sannan Yarima yayi hanyar fita ta bishi ta zata nan ma wani sassan ne,ya dako mata tsawa ke!Dabba ina zaki bini?Ta ja ta tsaya,sannan ta juya azuciyarta ko fadi take,ina da aiki.Daki ta koma ta hau gado tana karanta addu鈥榓r yaye kuncin zuciya,nan take taji zuciyarta ta wanke tayi fes,kuma tun daga ranar kullum sai taje ta gaida su Umma,Umma tana nuna mata kauna sosai.Yarima zaune agaban mai martaba yana cewa ranka ya dade,gobe ne ya kamata in koma makaranta, domin tun wancan satin muka soma karatu.Mai martaba ya gyara zama sannan yace to madallah,sai ka sanar da iyalin naka ta shirya ko?Ko ka shaida matan?Yarima ya danne damuwarsa na zaci nan zata zauna?Saboda karatuna yana bukatar nutsuwa.Mai martaba yayi dan murmushi,sannan yace yaro,yaro ne yanzu kai dama baka fahimci don ka nutsun bane nace lallai ina bukatar kayi aure?Ya dafa dan nasa kada ka damu Modibbo, yanzun ne ma zaka samu nutsuwa yanda ya kamata kuma kayi karatunka cikin nasara,tashi kaje Allah yayi muku albarka maza ka sama mata biza kaji ko?Yace to na gode ranka ya dade,ya fita zuciyarsa fal kunci
[4:28AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 52馃彽
Haka ya shigo pallon umman shi rai bace Bily yana ta fadin shi gaskiya an takura mashi tare da nuna billy wai umma da wannan abun zan tafi ai kau umman ta hau shi da fada sosai ita ko billy kanta na kallon kasa tana ta sharar da hawaye, Yarima ya mike ya fita Bily ta daure ta dubi Umma tace Umma nima nafi son abarni anan.Umma tace a鈥榓 Bily banaso kice komai kinji ko,ke dai kiyi ta hakuri sannan kici gaba da addu鈥榓,share hawayenki kinji ko?Nan take tace to Umma,Yarima ya rasa yanda zaiyi dole shi suka je shi da Magaji suka kammala mata komai,yana ta zafin rai,ai ko suna dawowa har daki ya same ta yayi mata tatas,yace in har kika bini dama kisan kin nemi maganin hawan jini dana ciwon zuciya,don kam kaken dana miki yanzun ne zaki gane dalili,sannan in har kika sake, kika tafi da wata kuyanga bana ji ana wani cewa ai musu biza ba tun cikin jirgin zan turo ki in huta,kinsan zan iya banza wawuya 鈥榶ar matsiyata ya fita,kukan da Bily tasha ranar babu iyaka daga karshe dai ta hakura ta kira Mansu ta gaya mata komai,Mansu ma hakuri dai ta bata,Bily cikin kuka tace,Mansu yaushe zanji dadi ne irin na kowa?Wai ni MEKE FARUWA dani ne?Haka zan dawwama Mansu,wallahi dana so aure saboda kuncin rayuwar gidanmu amma yanzu ga aure ga daula amma gara zamana na gidanmu gara ina gaban Mama su Gwoggo Ladiyo suyi ta min gorin yafi min yanzun.Mansu ma ta soma kuka tana cewa kiyi hakuri wata rana sai labari,haka suka yi sallama zukata abace.Sai da tayi kokari ta natsu sannan ta sake kiran Mansu tace mata ki kula min da Mamanmu.Mansu tace,kinsan wannan dole nane,ko baki ce ba,ni dai fatana ki kwantar da hankalinki duk me ya miki ki daure ki sama ranki cewa kina ibada ne,kinsan kuma bautar Allah sai da hakuri na sani kin sani no condition is permanent. Allah ma ya fada cikin Alkur鈥榓ni kowane tsanani yana tare da sauki,lokaci yana zuwa da zakiyi dariya aminiyata cike da jin dadi Bily tace na gode Mansu,naji dadi insha Allah maganganunki zasu zamar min abin tunanina, duk lokacin dana shiga kunci,sukayi sallama katan guda biyu cike da begen juna. Yanda taga rana haka taga dare, tunani ne ya cika zuciyarta MEKE FARUWA da ita?Me yasa bata da sa鈥榓 ne ita arayuwarta?Duk yanda Mamanta tasha wahala kanta ta kyautata rayuwarta taso kwarai ta samu mijin da zai kula da ita da mahaifiyarta,amma sai gashi wani can wanda bai san kimarta ba marar tausayi mara imani wanda in aka tsare sa koda bindiga ba zai nuna mahaifiyarta ba ya aureta ya kuma sameta abudurwa bai ko kula da hakan ba,wanda ada ita taci buri sosai akan budurcinta,domin tasan abin alfahari ne sai gashi amma shi ya keta ta ba tare da yako juya ba.Shin wane zama zasuyi a Malesia?Tasan sai tayi hakuri tasan zai bi mata,tasan sai dare zai dinga dawowa,tasan yana zuwa club,kila ma wata rana yazo mata a buge, tunani dai barkatai,lallai ta bakin nasa ta nemi maganin ciwon xuciya. Tun shigowarta gidan yau ce rana ta farko da taga ainahin gidan,mutane tankam an fitar musu da kaya,Umma dai tana ta nanata mata cewa,lallai in taji yaya ne ta kirata ta shaida mata,shi kuma taja masa kunne cewa ya kula da ita don ita din amana ce agaresa,kuma ta yabesa da cewa dama kai mai alheri ne,don haka ka lura da ita ka wadatata nan ya tuno da batun Modibbo jiya da yaje masa sallama,yace takwarana don Allah ka lura da matarka sosai,ka sani yanzu ka shiga wata rayuwa ce mai daraja kuma kaima ka zama cikakken mutum,yanzun ka kula da karatunka banda shirme.Yarima yace,insha Allah na kuma gode,an raka su zuwa filin jirgin sama inda Bily ta kara yarda Yarima dan gata ne,saboda 鈥榶an rakiyazuwa jami鈥榓n tsaro ne,suka shiga jirgi zuciyarta cike da addu鈥榓r hawa abin hawa,inda Yarima ya zauna kusa da wani tana ta hangen inda zata zauna kusa da mace 鈥榶ar uwarta tunda shi bai damu su zauna tare ba,don haka sai ta zauna ita daya akujerarta,wani kuwa yana shigowa ya zauna kusa da ita tare da gaishe ta,ta amsa tana satar kallon Yarima,don suna gabansa ne shi kam ko kallo bata isheshi ba,haka nan da jirgi ya tashi mutumin nan ya dameta da surutu har dai ta gaji ta soma baccin karya.
[4:31AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 53馃彽
Kai jama鈥榓!Anya mutane ana cewa babu kudi babu kudi,shin gaske ne?Gidansu take kallo tana fadin haka cikin zuciyarta tana tsaye tsakiyar falon gidan Yarima tana kallon tsarin falon irin dai gidajan da take gani cikin fina-finan turawa ko mujallarsu. Yarima ya nuna mata dakinta yana kusa dana sa ne,ta shiga gado ne madaidaici sai durowoyi wordrop da dai dan sauran abubuwa,ta kintsa daki duk da dai bashi da datti,ta shiga bayin karami ne ta tsaftacesa sannan tayi wanka da alwala wata tsohuwar baturiya ta shigo tana dauke da tire,tarkace ne ita jus din kawai tasha sam bata san wannan tarkacen ba,har wayewar gari bata fito ba,tunda tana da bayi kuma tazo da dambun nama dana kifi wanda Umma tasa akayi musu don haka bata da matsala,dama bata yi zaton Yarima zai nemeta ba,kuma hakance ta faru.Da safe ta lalubi kitchen taje shima ya tsaru,madam Dora tana ta 鈥榶an aikace-aikacenta suka gaisa,Bily ta soma hakilon neman abin karyawa,tea ta hada ta soya kwai babu ko bread taci kayanta ta koshi anan kitchen din take suna hira da madam Dora inda madam din take shaida mata cewa tana da kyau,shin ita 鈥榶ar wace kasa ce?Tace mata 鈥榶ar Nigeria ce,sai tace oh,ta manta dama Prince ya gaya mata cewa ita kanwarsa ce.Bily batayi mamaki ba tace,eh hakane.Madam Dora tace dan uwanki yana da kirki sosai,tun farkon zuwansa nan kasar nake masa aiki ni da sauran ma鈥榓ikatan yasan darajarmu yana mana adalci.Bily ta danyi yake tace ai hakane halinsa yake,tace koya sunanki? Bilkisu inji Bilyn ta shaida mata madam ta kasa sai dai Bikis haka ko taci gaba da kiranta.Da dare tana zaune afalo tana kallon wani fim,zuciyarta ko tana tunanin cewa tunda suka zo bata ko saka Yarima cikin idanunta ba,sai gashi ya shigo kamar ta share shi,sai dai ta daure tace masa sannu da zuwa tamkar baiji ba kuma tasan yaji don haka ta share shi kusan awa daya ya fito cikin 鈥榶ar T-shart fara da 3 kwatan wando ya nufi kitchen mai hade da dinning room.Can dai tana zaune sai taji wani abu yana kara,ashe intercom ne sai taga madam Dora tazo ta bude.Wata mace ce ta shigo tana sanye da siket da iyakar cinya,sai 鈥榶ar bes kana ganinta kaga chanis,suka gaisa da madam sannan ta nufo ciki tana tambayar madam ko prince na nan?Madam tace yana dining room can ta nufa,madam tazo tayi ma Bily sallama da cewa zata gidanta don basu da nisa,Bily tace to mu kwana lafia sai dai tanayi zancen ne kawai amma zuciyarta na gurin su Yarima,shin wacece wannan?Jim kadan suka jero ita da Yarima suna 鈥榶an hirarrakinsu,suka zube nan falon.Tamkar a fim ko cikin mafarki sai ganin Yarima tayi yana wasanni da wannan macen,sam tamkar basu san da mutum agurin ba.Kasa jurewa tayi ta mike ta shige dakinta kan gado ta fada,har yanzun bakin Yarima take gani cikin na wannan matar, tasan bata son Yarima amma dole ne tayi kishin mijinta.Kai ko ba mijinta ba ba zata so taga wani musulmi yana kusanta kansa da zina ba,bare har ya aikata.Tasha kuka daga baya tayo alwala ta soma nafila tana kaima Allah kukanta.Washegari ko da safe misalin goma tayi yo kwalliyarta cikin super riga da zani tayi kyau,tana zaune kan dining tana karyawa ya shigo cikin shirin makaranta.Madam dora ta mika masa dan kofi da plate coffee ne aciki yana sha,suna gaisawa tana masa korafin sister shi tafi son tayi girki da kanta,yace eh ko gida ma haka take.Madam tayi 鈥榶ar dariya sannan tace kuma Bikis tana da kyau,sai ya fita daga kitchen din yana cewa,chelen tana jiransa bari yaje.Can hanyar fita ya nufa,sannan ya aje kofin da plate din ya tafi abin tsoro mata gidan Yarima wasu suna shigowa wasu suna fita,kuma karka ga yanda yake wani shassha musu kamshi,abinda kullum ke bata mamaki har yau da take satinta daya agidan bai taba mata koda magana ba kuma koda ta gaishe shi baya amsawa, haka nan baya damuwa ko agabanta ne yayi yanda yake so da 鈥榶anmatansa hakan nan in sun nemi sanin ko ita wacece agabanta zaice kanwarsa ce.
[4:35AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 54馃彽
Hankalin Bily bai gama tashi ba,sai daran ranar data cika kwana goma a kasar.Ta fito zata kitchen saboda tana son tashi da azumin alhamis,me zata gani?Yarima ne da mata guda biyu tamkar zasu cinyesa,kowace tana son nuna masa karshen soyayyarta,kuma tana son burgesa har ya juyo gurinta,cikin tsananin tsoro tace, A'uzubillahi minash shaidani rajim.Suka dubeta su biyun banda Yarima wanda ya rungumo su duk da ya ganta juyawa daki tayi ko ganin hanya batayi don tashin hankali cikin sanyin jiki ta zauna tama rasa wane tunanin zatayi ne?Kodai don bata kai kanta garesa ne yake kawo su gida don ya bata mata rai?Inko haka ne ai gara ta kai kanta gurin nasa koda zai riga mata fyaden ne in dai zai daina kawo wadannan matan masu kama da bebyn roba ta sani ba sun fita kyau bane ta sani ba wai tana son Yarima bane sai dai tasan in don rashin zuwa gurin Yarima ne yake zuwa ya kawo mata,to tabbas tana da kamashon zunubi,kila ma nata yafi nasa.Tabbas Yarima baiyi kuskure ba daya ce ta nemi maganin ciwon zuciya dana hawan jin,har gari ya waye tana tufkawa tana warwarewa.
Yaya batun su Mamanmu? Duk wanda ya auri boka da 鈥榶an tsibbu lallai yana cikin dimuwa ba kuma zai gane ba,har sai ranar da karya ta kare,ga dai su Ladiyo nan anata fama yanzun ma da suke zaune gaba dayansu acikin dakin Karima suna tattaunawa ne akan duk malaman da suka je gurinsu,Salame tace abin kamar hadin baki malaman nan sunce mana inma an daura auren kwata-kwata ta dade tayi sati daya agidan mijin zai koro ta amma gashi yau mun shiga sati na uku.Ladiyo ta gyara zama ga kuma tsohon ciki tace yanzun ko bacci bana iyawa tunda akayi auren nan kullum ina raba idanu ne inga ta shigo gidan nan wutsiya zage,bani da buri sai na ganin bayan Bily.Karima tace kedai bari Ladiyo wallahi baki kaini ba,Ladiyo tace um um daina cewa ban kaiki ba,ni nan da kika ganni ko wannan cikin na jikina bana tunanin ranar haihuwarsa kamar yanda nake tunanin auren nan na Bily gashi kuma shiru. Salame tace mu koma mu sanar dasu aiki baiyi ba.Ni damuwata ma daya yanda mai adashen nan ke ta min sintiri naci na kasa zubi kudin da sune na bada muka kai gun malaman nan yaya tazo tana neman abin dauka, nace indai bani zaki dauka ba,ko yara ga sunan kwancar bani da wani abu dazan iya baki gaki dai ga dakin,in kinga abin dauka to dauki.Duk suka sa dariya,Ladiyo tace nima gado ne kurum yanzu ya rage min,Karima tace wa ma zai sayi wannan gadon naki,ko鈥榠na kudin cizo yayi kashi.Ladiyo tace eh,in zan saida ai dama wanke sa zanyi. Salame tace ai ko yaci klin din dari biyu dukkansu suka sa dariya,tace mu bar dariya mu fuskanci matsalarmu fa?Haka ko sukayi,washegarin ranar suka shiga mota suka nausa.kusan duk bokayan sunce musu kada su damu,aikin zaici ahankali. Shiko asalin bokan nasu cewa yayi yana zaton ma fa anyi sakin kila uwar yarinyar taki yarda su sani ne,sannan takai yarinyar gurin 鈥榶an uwanta.Ya kara musu da cewa haba ku sai kace ba mata ba?Ku kanku ma fa sharri ne mai zaman kansa cikin irin siyasarku ta mata da kissa ai kwaji koda gurin mijinku ne.Kai ita kanta yanayin amsar da zata baku zaku iya ganewa, suka ce hakane.Ladiyo tace malam sai dai fa maigidanmu da kake cewa zamuji gurinsa wallahi yanzun ya juya mana baya tunda yarinyar ta samu dan sarauta shikenan duk ya birkice mana.Malam yace a鈥榓 kuce akwai sabon aiki kenan,to kuna da kudi ko?Suka ce zamu nemo, amma don Allah ai mana aiki mai kyau,yace musu don wannan kada ku damu,an gama kuzo dai da dubu takwas,sannan da kaji biyu.Suka ce to sun gode,sannan suka muke suka dauki hanyar gida.Allah kasa mufi karfin zuciyarmu, amin. Suna shigowa gidan sun samu Mamanmu zaune tana yiwa auta tsifar kai,nan suka kyafta ma juna ido alamar su bigi cikinta,don haka sai suka hada baki gurin yin sallama.Mama ta dubesu ta amsa,sannunku da dawowa suka ce yauwa. Karima tace munje barka ne matar wan Salame,cike da fara鈥榓 Mama tace,Allah sarki to Allah ya raya,ai da kun gaya min da munje. Salame tace umh ni ai gani nayi na gaya musu bikin Bily sunki zuwa, shiyasa nace bazan gaya miki ba tunda abinba tsoro bane,su basa son zuwa
[4:36AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 55馃彽
Amma suna son aje musu.Mama tace,kai sai kace bin bashi?Ai lada ne in naje din,to Allah ya raya suka ce amin.Ladiyo tace,auta anata shan tsifa ne?Mama tace eh wallahi kin ganta nan kitson tunna bikin maigado taki tsefe sa,taje tasa anmata kitso yangu-yangu kuma sai da nace kar tayo kanana,amma da yake tana da kunnan kashi sai da tasa aka mata shi.Ladiyo tace ai duk haka suke,itama uwata gashi nan dama ita ba gashi ba yana nan kan duk yayi dugu-dugu ni dai ai bani da lokacin tsifa.Mama tace nifa tunda taki tsefewa ai tasan tawa tsifar sai na fece kai tas ta mun kuka in nade ta.Salame tace da kina can gidan amarya ai da kin huta.Asma鈥榰 tace ba Mama ce tace adawo dani ba.Karima tace,ina ruwan amare,ana can dai.Duk suka kalli Mama suga yaya fuskartata zata nuna?Mama tace,um suna can,sun ma tafi ni wacce kasa ce inda mijin ke karatun likita.Gaba dayansu suka ce me?Cikin Ladiyo ya shiga juyawa,Mama ta kallesu saboda yanda taji sun hada baki,Karima ta wayance tace,a lallai Allah ya bada zaman lafiya. Asma鈥榰 tace Mamanmu sunan kasar wai Malesia inji anty Mansu.Ai tuni suka sulale kowacce ta shige dakinta zuciyarta tana zogi tare da son tuno MEKE FARUWA ne?Abubuwan suke zo musu ahaka?
Sumayya taja tsaki sannan ta kashe wayarta,anty Salma ta dubeta ke kuma dawa kike tsaki? Sumayya tace,wannan Magajin Malam din mana ya dame ni wai ni yake so,ni ko gaskiya be min ba.Anty Salma ta harareta,sannan tace to menene aibun Magaji?Momy 鈥榶ar gidan anty Salma itace ta uku tana da kannai da kuma yayye guda biyu maza,tace Mama ita fa Sumayya wai uncle Yarima take so,lokacin bikinsa duk inda mukaje sai tayi kuka.Anty Salma tace ai da kina sonsa kika yi shiru?Sumayya tace, wallahi Ummanmu ce ta hanani magana.anty Salma tace,to ba gara ke ba,da wannan 鈥榶ar matsiyatan. Momy tace,ni ko ina sonta Mama tana da kyau.Anty Salma tace, ja can sakarya tayi ta kyannata mana,sannan ta dubi Sumayya tace,karki damu bari ya gama karatu ya dawo sai mun hadaku. Ai dama itama wannan ba wani sonta yakeyi ba hadinsu mai martaba ne da Modibbo. Murna Sumayya ta hauyi yayinda Momy ta shiga turo baki itama tsarar Sumayya ce Momyn.Tace to baga Magaji yana sonta ba,Sumayya tace to ni bana sonsa Momy ta taba baki sannan ta tashi ta basu guri.Umma ta kira lambobin gidan nasu Yarima na can Malesia ta hanyar land line har sau uku ana ukunne madam dora ce tazo tana buga ma Bily kofa domin Yarima ya fita,Bily taso taki daukar wayar don ita tun fitowar da tayi daren jiya datayi mugun gani koda ta daga wayar jin muryar Umman Yarima yasa tajin wani sanyi,tace sannu Umma ina yini? Suka gaisa tace ina baban nawa?Bily tace ya tafi makaranta,Umma tace ina fata dai kuna nan lafiya babu wata matsala ko?Ba komai Umma cewar Bily,to kiyi ta hakuri dai kinji ko?Tace to Umma. Umma tace yauwa 鈥榶ata ki kwantar da hankalinki, wata rana sai labari,nasan Yarima sarai ki ta hakuri tace to Umma,to na gaisheku in yazo kice masa na kira ina gaidasa, tace to mun gode,zan gaya masa.Ta lura yana shigowa ne karfe hudu, don haka kafin hudu ta shiga kitchen tayi 鈥榶an girke-girkensu na hausawa,sannan tayi wanka,kwalliya tayi sosai irin wadda ake mata, sannan ta saka wani leshi mara nauyi kalar sararin samaniya,riga ne da siket tayi kyau ta saka gwala-gwalai kunne da wuya,da kuma yatsunta,tayi kyau sosai.Yau sai biyar ya shigo shida wani abokinsa dan Africa ne mai suna Saddik,tunda tazo sai yau ta gansa da musulmi,ta fito tace masa sannu da zuwa.Ya kalleta wani takaici ya cikasa aransa yace,har abada wannan ba zata waye ba,yace ai ke yafi dacewa ayi miki sannu, ko don wadannan kayan da kika lafta wa jikinki.Taji zafin maganar, amma sai ta daure tace Umma tana gaisheka, daxun tayi waya hanyar dakinsa yake tafiya amma sai ya dan tsaya ba tare da ya juyo ba yace me tace? Bily tace,ta gaishe mune kawai.Ya shige daki, ta dubi bakon sannu da zuwa ta masa cikin harshen turanci,sai taji ya amsa da hausa duk da hausar tasa batayi gargar ba,suka gaisa ta nufi daki.Bako Saddik ya bita da kallo,sanda tare da shiga daki gaban madubi ta tsaya bata ga aibun kwalliyarta ba,amma har yana wani cewa ta lafta ma jikinta kaya
[4:39AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 56馃彽
Taja tsaki ai dama ita ba wai tana son sai ta burgesa bane kawai tana son ceto shine daga halakar daya shiga,amma akasan zuciyarta sai tana jin kamar ta canza shiga, amma sai wata zuciyar ta kwabe ta da cewa kinma damu sai kin burgesa kenan,don haka sai ta fasa ta fita zuwa kitchen dai dai lokacin ne taji bakon yana cewa,gaske kanwarka ce?Yarima yace,um hum! Bakon yace don Allah ina sonta she is very beautiful.Yarima ya mika masa littafin hannunsa tare da cewa amsa Saddik,kula min da littafina kasan ba鈥榓 samunsa anan nima sai a England aka samo min duk da cewa muna dasu a library amma ba鈥榓 son a fito dashi.Saddik yace, kada ka damu,yanzu muyi maganar sister dinka,I love her.Ga mamakin Bily, sai taji yace jeka gaya mata mana ni kazo ka dame ni kana sonta. Bily Sai data kusan faduwa don mamaki,shi wanan wato ko kishinta ma bayayi? Koda baya sonta ai ya dace yayi kishinta amatsayinsa na mijinta. Shin me hakan yake nufi? Guri ta samu acikin kitchen din ta zauna ta zabga tagumi,mijinta ne ke turo mata wani daya ce yana sonta,shin ko dai gaske ne Yarima bai san addini ba?Haka ta mike ta nufi daki bata ko ganin hanya sosai,dolenta ne tayi duk yanda zata ceto Yarima,amma duk da haka wata zuciyar tana ce mata Yarima ya wuce da tunaninta,amma sai tana karfafa ma kanta gwiwa da cewa,ai mata yake so kuma su yake nema,haka nan itama mace ce duk abinda wadancan matan suke dashi itama tana dashi,shin me zai hana itama ta bishi yanda sauran ke binsa?Ai itace ma ya dace ta bishi tunda mijinta ne,zata gwada irin nata salon,Allah yasa adace. Ta sani duk inda Yarima zaije baya wuce sha biyu.Wata rana ma baya kaiwa zaka ga ya shigo ko shi kadai ko shida 鈥榶anmatansa,ko sai in yazo sannan su biyo shi,yayi ta ja musu aji.Don haka kafin ya shigo tayi wanka ta gyara jikinta da turaruka,don turare yana motsa sha鈥榓wa musamman irin masu sanyin kamshin nan,rigar bacci tasa kalar pink mai yala-yala,wato mai bin jiki tana da gidan nono kuma shi les ne mai shara-shara, ta gyara gashinta ta daure da ribon pink,ta kalli kanta a madubi tayi kyau ta zauna jiran Yarima Sha biyu saura ya shigo anci sa鈥榓 shi kadai ne ya shigo,sai daya jima da shiga dakinsa sannan ta nufi dakin tana turawa kofar ta bude,ta shiga da sallama baya dakin amma da alamar yana wanka ne, ta kalli ko ina a dakin,lallai Yarima bashi da matsalar komai arayuwarsa,shiyasa yake yin yanda yaso.Zama tayi kan durowar gefen gadon tana cike da fargabar yanda zasu kwashe,kusan mintina goma sannan ya shigo dakin,waton ya fito daga bayin.Ya kalleta fuskarsa da alamar tambaya.Bily dai tana kallonsa bata ce kala ba,shima yaci gaba da harkokinsa.Shafa wannan matso wannan sa a hanci,sa a hammata, mamaki ma yake bata sai kace karuwan namiji,rigar bacci mai wando ya saka,sannan ya nufi wani dan fridge kwalbar jus ya ciro ya dauki kofi asaman fridge ya zauna gefen gado yana tsiyaya,ta gane nufinsa waton kala bazai ce mata ba,tasan zai iya abinda yafi haka ma,don haka sai tace,ina yini?Sai daya kurbi jus din sannan yace menene dalilin shigo min daki ba tare da izinina ba?Ta mike ta nufo shi yanda take tafiyar duk komai na jikinta girgiza yakeyi,kusa dashi ta duka,nazo ne in sauke nauyin da Allah ya dora min a matsayina na matarka.Ya dubi fuskarta idanunsa ya sauke akan lebunanta 鈥榶an yala-yala masu laushi jajaye tamkar ta saka janbaki,sannan ya kauda kai wane irin nauyi?Tayi jim don nauyin kalmar da zata fada.Hakkinka dake kaina.Ya sake kallon saitin kirjinta,sannan ya kauda kai yace, bana bukata,in kina nufin bani kanki ne,wancan lokacin ma nayi ne domin in banbance miki tsakanin yaro da babba,wato aikin da namiji zai iya da kuma wanda mace ba zata iya ba koda 鈥榶ar shekara sittin ce shi kuma dan talatin duk da kince kashina baiyi kwari ba,nasan zaki shaida cewa ni ba raggo bane,don haka yanzun kama kanki bana bukatarki ko da zan ganki tsirara. Kash! Mu hadu a littafi na uku (3) don jin yadda zata kasance,shin yanayin hakurin ko ko,ita tana yin zuciya koko batayi.
[4:42AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽 MEKE FARUWA 57馃彽
Jikinta yayi sanyi, zuciyarta ta
baci,duk da shakkarsa da takeji gami kuma da
yanda yake cika mata idanu,sai data ce kai ma
kasan baya ga aure mai hada namiji da mace
baka isa in zo ince maka gani ba,ka sani nima
bada son raina bane,don kawai na fita daga
hakkinka ne,kuma Allah ya sani na fita.Ta mike
tayi waje rai bace,da kallo ya bita tun daga sama
har kasa yake kallonta,har ta fita.Ya runtse
idanunsa yana kallon yanda jikinta yake
motsi,wata sha鈥榓warta ce ta mugun tsirga
masa,ta baya ya fada kan gadon hannu ya kai ya
jawo filo ya saka akirjinsa ya matse gam,bakinsa
yana kwadayin lebunanta yana son jin kalar miyanta,nan zuciyarsa ta shiga tuno masa ni鈥榠marta duk da ya kusance ta ne cikin garari ba tare da wasu wasanni ba,amma abin ya tsaya masa a rai .Ya kuma shakar kamshin data tafi ta bar masa a dakin,ya sani bawai yana sonta bane
amma sha鈥榓warta tun ranar daya soma ganinta
ta tsirga masa,ba kamar yau da yaga siffofinta
a fili,yace kai she is a beauty.Yayi tsaki tare da
cewa,ni gaskiya banyi ba,ta kawo kanta amma na tsaya, yayi shiru yana son ya tuno wai ma me ta
masa ne?Yasan dai ta shiga rayuwarsa tunda
tasa an masa aure da wuri,sai ya kasa manta
zagin data masa na cewa jahili.Wata zuciyar tace
kada ka manta kaima ka zageta,yayi birgima
akan gado ya koma rufda ciki,sha鈥榓warta na bin
duk jininsa sai kurum yaji an kwanta a bayansa,ga
zatonsa itace,don haka ya juyo da sauri tare da
rungume ta tsam a kirjinsa,sai yaji muryar chelen tana cewa,oh my prince.Nan ya sassauta mata rikon tare da bude idanu yayi ajiyar zuciya kuma duk sai yaji ransa ya baci,tana kokarin neman
bakinsa ya tsaida ita tare da nuna mata hanyar
waje.tasan wanene prince in ba yayi yana bukatar
a kyalesa,don haka sai kawai ta mike ta fita,haka
ya kwana ranar juyi kawai yakeyi. Bily tana komawa daki kofa ta kulle ta hau gado tana aikin kukan bakin ciki,ta danne xuciyarta ta zubar da ajinta na mace ta kai masa kanta shi kuma ya nuna banza wofi ma ta fita,to daga yau duk abinda zaiyi yaje yayi tayi,ganinta ma bazai kara ba, hakance kuwa ta kasance,domin tun daga ranar Bily ta shiga kulli kurciya tsakaninta da Yarima in yana gidan bata fitowa har sai ya fita,dama tasan shi dan ka鈥榠da ne,lokutan fitarsa dana dawowa ahaka suka kwashe sati uku bai sata a idanunsa ba,tun baya damuwa har ranar ya zauna ya yini,amma bata fito ba,ya tambayi madam dora tace tana fitowa sometimes ita ko duk ta mika lamuranta ga Allah,daga nafilfili sai addu鈥榦鈥榠 sai karatun kur鈥榓ni,sai kuma kuka don tunani wani sa鈥榠n gashi yaushe rabon wayarta da kudi bare ma ta kira wani sai dai Mansu tana kiranta.Malam Mamman ya shigo dauke da buhun doya kofar Mamanmu,ya sauke sannan yace Fatima tana daga ciki tace na鈥榓m.Ta fito tana cewa gani Malam,yace ga doya nan ki kasa.Tayi shiru domin duk tsawon xamanta agidannan malam bai taba kawo mata abu wai ta kasa ba,sai dai su Ladiyo su kasa,kuma bata kwasa sai wanda suka kawo mata,wata rana ma tana kallo za鈥榓 kasa din a hanata.yace kinyi shiru Fatima,tace malam kabasu kawai su kasa kaga sune masu yara,yace nine dai maigidan ko?Tace kai ne malam.Yace to nace ki raba muku, Fatima ni tsakanina da Allah yanzun na gane kuskurena,kadaki zata zanci gaba da muzguna miki ne,nidai afuwarki nake nema.Mama tayi dan murmushi,sannan tace dama ni ban rike kaba malam,na sani duk abinda bawa keyi mara kyau dole lokacin nadama zaizo,ko yayi nadamar mara amfani ko kuma yayi ta lokaci bai kure masa ba.Yace nasan dana ke mai hakuri ce Fatima na gode don haka ki kasa kurum nina fita.Tace to sai ka dawo malam,haka ta kasa doyan su masu yara tasa musu kashi bibbiyu ita ko ta dauki daya,har kofar dakin Ladiyo taje tace Ladiyo kuzo ku kwashi doya gata da malam ya kawo ai fa nan suka fito cike da masifa baki nayi duwawu nayi,su za鈥榓yi ma salo da iyayi?Da itace mai rabawa? Tace malam ne nima yace in raba.Nan sukayi wata shewa,鈥淗e!!! Lallai samun sarari tusar asuba,wannan kinibibin na malam ya isa haka don bamu taba nuna masa bacin ranmu akan sauyin halin daya yi mana ba,Karima tace ai kwadayi ne ba wani abu ba,don 鈥榶arta ta auri dan sarki.Salame ta amshe da cewa,aikin banza da wannan auren ba gara babu ba,daga malam din har ita uwar 鈥榶ar ai ba abasu wata daraja ba,don ko da an basu da yanzun mu gani akasa.Ladiyo tayi shewa,sannan tace fadi ki kara inda za鈥榓 tsare angon da bindiga bazai ce ga surukansa ba.Daidai nan malam ya shigo,yana tsaye suka cigaba da fadin don haka mu yanzu babu wani salon da za鈥榓yi mana,munsan komai. Karima tace,tallarta fa akayi,matar cushe ko bata kwarjini.Malam yace ai tallar hoton ma hanya ce,haka nan in an tallata wani an siya wani ko kyauta aka bada babu mai amsa,in ma kuna masifa kan doya ne,nine nan nace ta kasa,in bakwa ci ku barta yanzu na dawo cikin hankalina,in ma da kun min asiri ne to ya karye,鈥榶an bakin ciki,da hassada,ahaka zaku gama rayuwarku a tsiyace,ita ko kuna mata bakin ciki tana kara gaba.Mama ta dubi malam tace yi hakuri malam,jeka abinka.Nan ko ya juya itama ta nufi daki,su ko sun kasa magana don mamaki. Ladiyo tace yau mun shiga uku da makirci,(ta kwaikwayi muryar Mama)tace har da cewa wai yi hakuri malam,kuji makirci.Salame tace eh tana kuma cewa ya tafi ya ko juya.Ladiyo tace yanda na tsani matar nan da in na kashe ta babu hukunci da tuni na daba ma shegiya wuka,amma duk da haka sai nasa an sabautata.Haka dai suka yi ta surutansu ta inda suke shiga bata nan suke fita ba har suka gaji suka bari. Bily tana zaune tana karyawa akitchen,sai taji anata doko sallama, mamaki taji domin ta manta rabonda taji anyi sallama.Da sauri ta fito don tasan ba Yarima bane,ga mamakinta sai taga Magaji.Murna sosai tayi da ganinsa,sannu da hanya kai kadai ne?Yace wallahi ni kadai ne na kawo ziyarar bazata,ina maigidan?Tace yana makaranta,zauna bari na kawo maka abin kari karfe biyu saura,lallai ku 鈥榶an gayu ne ni dai na karya acikin jirgi sai dai abani na rana mai gishiri.
[4:45AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 58 馃彽
Suka yi dariya taja jakarsa ta kai dakin Yarima sannan tazo ta soma dafa masa taliya,shi kuma ya mike don yin sallah.Suna gun cin abinci ne yake tambayarta shin ko abokina ya canza?Bily bazata iya boyewa Magaji ba,don tasan shi mai gyarawa ne a kowane lokaci,don haka sai tace ya dai canza kila nan gaba,tacigaba Magaji bazan baka aboye ba,ina nadamar zamana da Yarima,munanan halayensa sunyi yawa.Yarima mazinaci ne kuma mashayi.Magaji ya mike tsaye tare da dafa kirjinsa yace,innalillahi wa鈥榠nna ilaihir raji鈥榰n!Me Yarima yake sha?Tace giya.Zufa ta soma tsattsafowa Magaji,yace a ina yake sha? Tace kana duba kowane fridge na gidannan zaka gani.Ya soma dana kitchen,duk jus ya gani sannan ya koma na daki nan ma bai gani ba ya dawo yace,ban gani ba.ta mike ta ciro masa kwalba daya na jus,tace wannan ba ita bace?Magaji yayi ajiyar zuciya sannan yayi murmushi ya mika mata,gashi ki karanta. Zama tayi ta karanta rubutun dake jikin kwalbar tare da ganin nau鈥榠n 鈥榶ayan itatuwan da aka hada jus din dasu,sannan sun rubuta cewa babu giya aciki.Kunya taji kuma ba boye-boye tace,niban san irin wadannan jus din ba,kuma ban karanta ba,amma ai ahaka za鈥榓ce giya ce ko?Magaji yace ga wanda bai sani ba?Ni nasan Yarima baya shan komai na maye,sai dai batun mata yana dan tabawa,kuma zuwa yanzun da kika zo ya dace ace matsayinki na mace kinyi duk yanda zakiyi kin rabasa dasu,tayi murmushi tace Magaji kenan kana yi kamar baka san Yarima ba.Yaushe ya bani darajar yin haka?Ba sai ya maida ni mutum ba sannan zai kula ni,har ma na hana sa abinda yayi niyya?Ni tsoronsa ma nake ji, kai atakaice ma ni nafi karfin wata uku ban gansa da idanuna ba.Yace ba gidan yake kwana ba?Tace anan yake kwana mana, kuma duk 鈥榶anmatansa nan gidan suke zuwa wai da rashin tsoron Allah irin na Yarima har da mata biyu yake kwana?Shine dalilina na kaura ce ma ganin wannan bakin cikin.Ta soma hawaye,Magaji ka taimake ni Yarima ya sakeni,yanzu haka rabona dana gaisa da mahaifiyata na dade banda kati banda kudi kullum tana raina ni ina nan cikin bakin ciki bazan iya ba.Magaji yace kiyi hakuri wata rana sai labari,gidansu Yarima ba鈥榓 saki inba kin aikata wani mummunan laifi bane kamar zina,Allah ya kiyaye shine za鈥榓yi saki,yanzun yana sakinki abinda kowa zai dauka kin aikata kenan.Sai dai kiyi hakuri sauki yana nan zuwa bada jimawa ba,wata rana sai kince ma Yarima ya fita sannan zai fita.Magaji ya fada cike da tsokana tace tabdijam,Yarima ne mace zata juyashi?Lallai kuwa kace wata rana jaki zaiyi kaho.Magaji yayi 鈥榶ar dariya sannan yace,ai gara kema da tawa matsalar. Ta dubesa me ya sameka?Yace ai kin san Sumayya ko?Kanwar su Faruk mijin kawarki? Tace na santa,yace ita nake so tamkar in mutu, ita kuma bata sona wani daban take so,ta gaya min na kasa hakuri.Bily ta tuno hirar dataji Sumayya suna yi lokacin da Mansu ta haihu,sai tayi murmushi tace,nasan Sumayya Yarima take so.Magaji yace yaya akayi kika sani?Tace sun taba hirar a gabana ita da 鈥榶an uwanta.Magaji yace,to yanzu na rasa inda zansa kaina,kwanaki ta zo Bauchi gidan anty Salma ta sauka in naje bata fitowa,sai dai Momy 鈥榶ar gidan Salman ce ke fitowa tana bani hakuri.Bily tace, ni dai nawa ganin kayi ta addu鈥榓,amma ka barta zaifi inko kaci gaba da naci zaka yi ta shan wulakanci,don ko na lura tayi zurfi a son Yarima. Shiru Magaji yayi yana auna yanda za鈥榓yi ya rabu da ita,shin wane hali zai shiga?Yace to zan kwatanta, kuma a nata gefen ma bazata samu abinda take so ba,don Yarima bashi da ra鈥榓yin aje mace biyu.Bily tace ko ma ta nace ta auresa me zata tsinta gidan Yarima in banda bakin ciki?Magaji yace ai kuma baki sani ba,ita tunda tana sonsa zatayi duk yanda zata samo kansa,kinsan namiji shi tamkar yarone wani sa鈥榠n ballantana Yarima mai son matan tsiya, shi yasa nace kema inda zaki rike masa wuta tsaf zaki samo sa.Bily tace ba irinsu Yarima bane,shifa wani irin hali garesa duk da ba dogon zama nayi dashi ba na lura da halayyarsa,sannan ko 鈥榶anmatansa kar kaga yanda yake gara su. Magaji yace Yarima kenan,ni dai hakuri kurum zan baki wata rana komai zai canza,tace to Allah ya kawo mana sauyi na alkairi,yace amin Yarima ya shigo gidan kusan biyar na yamma kamar cikin mafarki yaga Magaji,cikin dariya yace,waton ni har yau ba za鈥榓 daina min zuwan bazata ba ko?Magaji yace sai ranar da ka soma hankali,Yarima yace na gode.Ya shiga dakinsa bayan sunyi sallar isha鈥榠 ne kusan karfe takwas saura Yarima da Magaji suna zaune a wani gurin shakatawa hasken fitilu tamkar rana kowa yana abinda yake so mata kuwa suna ta shawagi ko Yarima zai taya amma yaki ko da kallonsu.Magaji ya dubi Yarima yace,abin na bani mamaki,na me fa?Inji Yarima,yana magana yana danna waya.Yanda mata ko ina ka shiga suke sonka kamar kafi sauran maza.Yarima yayi murmushi to kai me ka gani?Shine ai nake son jin dalili,Yarima yace dalilin kenan, nima ina sonsu. Magaji yace to ai ban gani a goshinka an rubuta Yarima mai son mata ba,sannan in kun hadu bakai ne ke kallonsu ba,sune ke kallonka. Yarima dariya ce sosai ta rike shi yace wannan daga Allah ne,Magaji shima ya dara,sannan yace muyi zancan daya kawo ni garin nan.Yarima ya gyara zama,ina jinka magaji yaci gaba da cewa,Umma ta damu nata ganin ba kwa zaman lafiya da matarka, dalilinta shine duk sanda ta bugo waya ka dauka sai kace kana makaranta in kuma Bily ta kira sai tace ka fita in ko da daddare ne sai kace tayi bacci,shine tace inzo in duba,shi ko mai martaba da bai san abinda ke faruwa ba,yace ne in har tana da matsala to ka kawo ta gida a kula da ita,kadai gane matsalar ko?In baka gane ba yana nufin ciki.Yarima yayi dariya sannan yace,old man kenan,shi yanzun har yana sa ran zan haihu nan kusa?Ya taba baki gami da girgiza kai dubeni fa Magaji am still young,just 24yrs,sannan ace ina da yaro haba mana,Magaji yace to batun Umma fa tana son sanin kalar zaman da kuke yi,yace ka samu matar gidan mana ba kuna shiri ba,nasan zata gaya maka.Magaji yace,tsoronka ya hanata fitowa,sannan abubuwan da kakeyi sun saba ma shari鈥榓 har cikin gida kake shiga da matan banza?Yarima yace ok ta gaya maka kenan? Eh.Inji Magaji, gaskiya ka canza tsari,Yarima yace nidai kace ma Umma muna zaman lafiya shikenan.
[4:46AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 59 馃彽
Magaji yace ai baka isa inyi karya ba,alhalin kai ba akan gaskiya kake ba,ce mata zanyi ka hanata fitowa,mata kake kawowa ka dai san zan iya ko? Dama ita bata san iskancin da kakeyi anan ba,to inna koma zaka sani.Yarima yace to me zan mata?Ita ke kulle kanta zan ta binta ne?Magaji yace,ni dai leken asiri aka kawoni,duk abinda idanuna suka gani kaji na rantse maka shi zan fada,shiru Yarima yayi yasan tsaf Magaji zaya aikata hakan.Don haka suna shigowa gida ya shiga toilet,bayan yayi wanka sannan yayi ma duka 鈥榶anmatansa waya cewa kada wacce tazo gidansa har sai shi da kansa ya nemeta,yana fitowa ya samu Magaji kwance share-share a gadonsa,ya kalli Magaji zamu tuna da kenan, na me?Inji Magajin,na kwana gado daya,sai kace baka da mata?Ko kuma ka kwana a falo ince falo kake kwana,wallahi har ma da sharri inba sai na hada maka ba kace shege nake,in kana son tsira da mutunci to har in tafi in ta ganin zaman lafiya.Yarima yace amma dai kasan ba鈥榓 tursasa ni ko?Magaji yace, nima ai bance dole ba, inna so in maka mugunta ai zance nazo dubaku ne kawai,inga abinda na gani inje in fada.Yarima bai kara magana ba,ya saka kayan bacci ya fita.Ya kai kusan daya saura afalo sannan ya tashi ahankali ya nufi dakin Bily,bai zaci yana tura kofar zata bude ba,amma ga mamakinsa yana turawa ta bude,ya shiga.Kamshi ne ya soma yi masa sallama,ya maida kofar ya kulle,idanunsa masu girman nan ya zuba mata,tana sanye da fara kal din rigar bacci mai yala-yala ta kwanta rigingine.Rigar ta dan zame daga kirjinta,haka nan cinyarta duk tana waje wato rigar taja sama.Ya kafa ma santala-santalan cinyoyinta ido,ya dubi lebunanta ya dan rumtse ido ya bude, numfashinsa yana fita da sauri ya kasa daurewa ya isa gaban gadon ya duka daf da fuskarta,sai wata zuciyar tace masa inta farka fa?Nan take ya mike ya fita kai kawo yakeyi acikin falon 鈥榶an mazan taka ta motsa,ita kurum yake gani ya kasa ya kuma komawa ya kalleta shigarsa ta uku lokacin kusan karfe uku da rabi ya samu ta farka kenan,nan take ta firgita da ganinsa ya dake ya shiga yamutsa fuska sai kace yaga kashi. Yace na lura Magaji an turosa leken asirin irin zaman da mukeyi ne,don haka zan daure inci gaba da kwana nan har ya tafi. Bily tace ba damuwa,ni zan koma falo ko toilet,ya dubeta cikin mamaki amma sai ya boye mamakin nasa yace,ai sai dai ki koma toilet din domin kwananki afalo ba zai yiwu ba,tasan zai iya cewa haka don ba kaunarta yake na,ta mike zata nufi toilet yace ke dawo,ta dawo koma gadonki ni na zauna anan ya nufi can gefe ta dauko bargo da filo ta mika masa yace no barsu ma haka ma is ok,duk su biyun babu wanda yayi bacci ita sai juyi shi kuma yana aikin kallonta,dan baccin daya dauke shine ya samu nasarar yin mafarkin yana saduwa da ita,don haka dole da asubahi sai da yayi wanka sannan yayi sallah.Duk satin Magaji na kula da Yarima,ya zama lazy shi kansa Yarima baisan me yasa sa kasala ba,amma zuciyarsa tana gaya masa matsananciyar sha鈥榓war Bily ce ke damunsa, kullum dakin yake kwana azaune.Magaji yaso tayi amfani da wannan damar ta shawo kan Yarima amma sai ta shiga nesanta kanta dashi,ta hanyar kwana da kayan jikinta yanda baya shiga harkarta ko ya shigo dakin itama bata kulasa,sai dai yakan kira 鈥榶anmatansa awaya cikin dare suyi ta hirar banza.Satin Magaji daya ya soma shirin tafiya,randa ya cika kwana tara ya tafi bayan ya kara yiwa Bily nasiha,tare da jama Yarima kunne.Sun koma 鈥榶ar gidan jiya na wasan boyo,sai dai dan canjin da aka samu, Yarima ya daina shigo da mata gidan sai dai suje Hotel.Sati biyu da tafiyar Magaji,kusan sha daya na safe Bily ta fito tasan kamar yanzun Yarima ya tafi school ta fito tana sanye da rigar bacci light blue,鈥榶ar daidai jikinta ce rigar don haka tabi jikinta ta lafe ta fito tana hamma nan tsakiyar falo tayi mika tsayawa tayi tana kallon wani fim da akeyi cikin talabijin,jefi-jefi kuma tana mika saboda duk jikinta ciwo yake mata.Yarima wanda yayi mantuwar littafinsa ya dawo don ya dauka,tsaf ya tsaya yana ta kallonta yanda take mika shine ya burgesa,ya kwadaitar dashi har ma yasha alwashin yau zai ajiye wannan zafin kan nasa ya sauke ma kansa wannan damuwar ya huta. Bily hankalinta ya tafi ga kallo bata san yazo dafda ita ba,kai bata ma san ya shigo gidanba,tayi dan tsaki aranta ta raya yinwa take ji bari ta dauko abinci tazo ta zauna tayi kallon, wucewar da zatayi kawai sai taji an rike mata hannu cikin tsananin tsoro ta waigo tareda cewa, innalillahi wa鈥榠nna ilaihir raji鈥榰n,Yarima ta gani ya zuba mata manyan idanunsa ta bata rai shi kuma ya daure fuska,taja hannunta alamar kwacewa, ya janyota zuwa jikinsa ta fado kan kirjinsa,matse ta yayi gam har sai data yi 鈥榶ar kara, yace likitoci suna cewa in mace bata da yinwa ko bacci kaga tana mika bata bukatar komai sai namiji,y yaci gaba da cewa,bani da yanda zanyi tunda an daura min ke dole ne duk sanda na ganki cikin wannan feeling in biya miki bukatarki,amma ba wai don sona ba.Bily tace wannan kuma kai ta shafa, nidai nan daka ganni bana bukatar komai daga gareka,yasa hannu ya dago fuskarta yatsunsa yasa ya matse mata baki har taji tamkar ta saki fitsari,yace kina nufin karya na miki?Yasa bakinsa ya tsotsi lebenta na kasa,sannan ya saki mata baki tasa bayan hannu ta share bakinta sannan tace,duk ma likitan daya ce maka in mace na mika namiji take bukata ta gefena bai karanta daidaiba, ka hada bakinka dana kowace banza sannan kazo kasa min?Yace ni duk me zanyi danke zanyi kada kiyi ta shiga damuwa amma kema kinsan baki kai kwatan matan da nake hulda dasu ba,tace wannan fa ni ba damuwata bace,nidai sake ni na wuce.Ya saketa,daki ta nufa maimakon kitchen da niyar dauko zani ta daura,sai dai tana shiga ta nufi gurin daukar zani tana daukowa ta juyo don daurawa sai kawai ganinsa tayi tsaye.Kallonsa kawai ta tsaya tana yi don tama rasa me zatace,ya nuna mata rigarsa da yatsansa,tunda ke zan taimakamawa zoki balle min botiran rigar nan tace cikin fargaba ni dai don Allah ka tafi wallahi bana bukatar komai,ya wani daure fuska zakiyi yanda nace koko sai na miki irin wancan karon,jikinta ne ya dauki bari kayi hakuri don Allah ka barni ya dora yatsansa a leben shi yace shsh!Ya tako zuwa gabanta yayi mata nuni da hannu,ma鈥榓na tayi yanda yace. Ta duba taga ba halin guduwa balle ta gudu
[4:47AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 61馃彽
Duk suna zaune gaban asalin bokansu,Ladiyo ta gyara zama tace,gaskiya boka duk yanda kace muyi haka mukayi amma duk ba wanda yaci,yanzun da haka suna kasashen turawa ita da mijin. Salame tace sannan shima na maigidan munyi kuma yaci amma tamkar ma mun kara masa masifa ne, Karima tace ga 鈥榶ayanmu nan dake gidajan mazajansu suma mun amsar musu duk abinda ya soma tasiri sai kuma ya tsaya.Boka ya dubesu daya bayan-daya sannan yace,ance muku kullum ake kwana agado?Amma dai kun san ba yau muke tare daku ba ko?Sau nawa ina muku aikin yana ci?Duk sukayi shiru,Ladiyo tace to yanzun yaya za鈥榓yi? Yace yanda za鈥榓yi kenan kuje kuyi hakuri danni nan da kuka ganni da zaran mutum yayi min korafin aiki baici ba to aljanu sun daina masa aiki don haka yanzun ku tashi tun kafin su iso keme cikin nan su cire dan su saka miki kwado.ai da gudu suka tattara yanasu-yanasu suka tashi,suna tafe suna jimami har gidan wani malamin, a takaice ranar yini sukayi garari gidan malamai da bokaye.A hanyarsu ta dawowa suna cikin mota ciwon haihuwa ya kamo Ladiyo suka rasa yanda zasuyi,mai mota yayi parking gefen titi yayi ta masifa yana cewa ku karata can nidai ku saukar min daga motata,in banda bala鈥榠n yawo mace kina da ciki wata tara in banda asibiti ina zaki? Amma ke kin fito shegen gantali ai gara ki haihu a titin kila zai zama darasi ga mata masu shegen yawo irinki,su Karima suna cewa,malam don Allah ka barta taji da damuwarta, shi dai ya sauke su yana cewa ku karata dai. Gyaluluwansu suka cire tare da taimakon wata Bayerabiya suka tare ta har ta haihu,saidai ga maza masu saide-saide a gefen titin ga kuma yara sun taru ta haihu da kyar uwar ta biya,sannan suka rufe jinin da kasa suka nado 鈥榶ar agyalan uwar suka nemi shatar mota duk da babu mai sisi cikinsu sai bayan magariba suka zo gida,lokacin malam mamman yana tsaye kofar gida ransa bace yana son yaga ta ina matannan zasu bullo ne? Karima ce da girki tun safe suka ce zasuje gaisuwar mutuwa har yanzun ga yaran duk yinwa ta ishesu,suna ta kuka,Mamanmu ce ma data gama girki ta zuba ma kananan ta soma sa musu su duka to amma bata yi da yawa ba,don bata san sun fita ba sai da bata ji duriyarsu ba,ta idar da sallar magariba kenan tana tasbihi sai kawai ta jiyo muryar maigidan yana ta zazzaga masifa,yana fadin dukku nemi hanyar gidajanku,badai gidana ba tun safe kuna ina?Yau gari ya waye?Da sauri Mama ta fito ko hijabin bata cire ba,sai taji ashe ma akofar gidane ake diramar,don haka sai tayi waje.Karima da Salame sunyi tsuru-tsuru,malam Mamman nata zabga bala鈥榠,Ladiyo ko tana cikin mota bai ma san ta haihun ba don suna tsayawa yaga sun fito yako hau ruwan bala鈥榠. Mama ta matso tana cewa,lafiya malam duk makota suna jin muryarka? Yace ba dole aji muryata ba,inna yi fada ace na cika masifa,Allah ya hadani da matsiyatan mata,ace macen arziki ta fita gida tun safe tana gantali ita ba ma鈥榓ikaciya ba,ba 鈥榶ar kasuwa ba,yawo kawai shiga nan fita nan?To duk suyi gida dama nina gaji da halinku. Mama tace a鈥榓 malam ka bari kaji uzurinsu mana. Yace basu da wani uzuri, Salame tace malam wallahi muna da uzuri,dai dai nan mai motan ya karaso gurinsu yana cewa,ku bani kudina ina sauri ne,Karima tace malam kaba mai motar nan dari hudu,wallahi Ladiyo ce ta haihu ahanya dalilin dadewarmu kenan,Allah ya tsareni ai ko kudi zasu kasheni bazan baku ba,ai yanzun don wulakanci a titi ta kware gaba ta haihu? Amma Allah ya isa tsakanina daku.Yayi ciki,Mama tace ina Ladiyon?Suka ce gata nan cikin mota,mai mota yace ku bani kudina sannan ku dauke ta na taimaka muku kuna ta bata min lokaci,gashi motata sai karnin jini Allah dana sani da ban taimaka muku ba.Mama tace to ku sallamesa a fito da ita mana.Salame tace,um babu mai ko taro cikinmu, gida Mamanmu ta koma ta dauko dari biyar taba mai motan,sannan aka fito da Ladiyo,suka taimaka mata zuwa cikin gida.Malam yace shifa su fita don yayi musu saki dai-dai,Mama tace haba malam,menene haka? Yace ba ruwanki,ki koma daki kada ki kuma min magana,su fitar min daga gida kawai.Mama ta wuce daki,Salame kuwa ta nufi sashen Gwoggo da kuka.Ta shaida mata cewa malam ya sakesu, gwoggo ta saki butar dake hannunta ta zabga salati saboda me?Inji Gwaggo amarya,saboda munje gaisuwa Ladiyo ta haihu can.Gwaggo tace muje gidan an kada an raya da malam yace dole ne su bar gidan nan yau,haka nan sai yayyansa suka ce to su dai je gidan asan yanda za鈥榓yi,Gwaggo tace ta sani ba haka kawai bane anje ne an kau mata da hankalin da daga kan matansa.Ita ko Mamanmu daya shigo dakinta magana ta shiga yi masa akan cewa ya dawo da matansa don ita bazata iya kula da yara kusan ashirin ba,yace sun cika masa ciki ne amma zai dawo dasu wasa-wasa sunfi sati sannan ya yarda suka dawo,maimakon ya zamar musu darasi,a鈥榓 sai suka shiga tunanin yanda zasu dauki fansa acewarsu Mama ce tayi musu asirin da aka sakesu,don haka itama sai an mata sakin babu ma kamar Ladiyo tace ai gara ku nida na tara uban bashi ina lissafin inna haihu zan dan rage gashi yanzun babu batun suna tunda yace ba wani taron da za鈥榓 masa yasa ma jaririnsa suna dole ne na hakura tunda yanzu an dusashe mana haskenmu daga idanunsa,Salame tace ai ko kun hakura ni sai naga bayan shegiyar matar nan da 鈥榶ayanta.
***************************
Umma ta dubi anty Salma tace,ke Yariman ne yace miki yana son Sumayya?Anty Salma tace,a鈥榓 Umma Sumayya din ce wai ashe tana sonsa ta kasa fada ashe ma akansa ne taki sauraron samari.Umma tace,to yanzun ai sai ta sauraresu don kinsan Yarima da yaya ma aka samu yayi wannan auren?Don haka tama nemi mijinta inma da yana sonta baya sonta ba, ai daya yi magana, saboda haka kibar ma wannan zancan,ni na mafi son ya nemo matarsa can wani gurin kamar yanda yayi nan itama sai ta nemi mijinta bana son hadin nan su zo su bata mana zumunci,don Yarima bawai yana da dama bane.Anty Salma tace Umma bada wannan da ba asan asalinta ba ni wallahi matar nan ta Yarima bata min ba. Umma tace, karta miki ai badon ke aka aureta ba,don bata miki ba wata tsiyar ce? Bana ma son ta miki.
[4:48AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 60 馃彽
Ta rumtse idanu sannan ta soma balle masa botiran, shi ko fuskarta ya tsurama idanu,xuciyarsa tana fadin,she is beautiful kwadayin lebunanta ya kamashi ya kasa daurewa,hannu yasa ya kamo fuskarta cikin tsananin zumudi ya manna bakinsa cikin nata.Daga nan komai ya cigaba da wakana,Bily dai tamkar gunki ta zamar masa yayinda shi kuma yake duk yanda yaga dama da ita.Bily wanka takeyi tana kuka,ba wai tasha wuya bane kamar wancan karon,duk da dai taji jiki wannan din ma kukan bakin ciki ne ko na menene ita dai bata sani ba,amma wata zuciyar tana gaya mata cewa kukan rashin mai so ne,ita da dai tana son ta san me yasa maza basa sonta?Ta sani Yarima ba don yana sonta suke zaune ba, yama gaya mata kuma lokaci ya kure mata da jin wannan kalmar ta so daga bakin wani tunda tana da miji yanzun kila ita haka Allah yake son ya ganta ma鈥榓na bai kaddaro ta cikin wadanda zasu samu maza masoya ba.Yarima koda yake kwance cikin bahon wankansa, idanunsa lumshe yana tuno irin halin daya shiga ne lokacin da yake tare da Bily,me yasa yakan fita daga hayyacinsa harma yayi ta surutai,in yana tare da ita?Wanda ko chelen da suke shaye-shaye don nishadinsu shida ita baya samun kansa cikin wannan yanayin,kuma fa wai ma don bada son ran Bilyn bane,in da da son ranta ne zata masa duk abinda su chelen keyi masa yaya zai ji kenan?Tsigar jikinsa ta tashi yarr!A fili yace,kila sai na suma don haka yasa a ransa zaya yi kokari ya gwada yanda zai samu hakan.Ya jima yana tunani kafin daga baya yayi wanka ya fita,yayi mamakin ganin yanda lokaci ya tafi har haka daga yin mantuwa ya dawo dauka shine har kusan awa uku,yayi tsaki kowane lokaci ya bata lokacin sane kan yarinyar nan ce,bai san mutum ya zauna yana tunanin banza ba sai kanta,tun farkon haduwarsu har yau ita kadai ce din dai ke saka sa tunani me yasa?
[4:49AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 64馃彽
Yana gaya mata cewa kada ma ta kama cewar yana da aure karta gayama kowa ma azata gaske ne. Chelen tace to yaya kake da ita? Yace kanwata ce bata son ta ganni da 鈥榶anmata don kinsan addininmu bai yarda ba,tace ai ta yarda ba matarsa bace,tunda ta jima tana zuwa gidan inda matarsa ce tasan da tuntuni zata dauki mataki,yace kin gane ashe.Shi Yarima sam baya so chelen ta kai labarin yana da aure cikin school dinsu,shiyasa yayi haka sam baiyi don ya bata ma Bily rai ba,danne zuciyarsa yayi kawai,ita ko Bily bakin ciki ma ai ba鈥榓 tonawa,ace mijinka ya nuna karuwa ta fika,ko baku son juna ai aure ya wuce wasa,da abin ya isheta da tukuki arai sai ta dauko maganin ciwon zuciya da hawan jini,kai da dukkan wata cuta ma,ta shiga karantawa,wato Alkur鈥榓ni mai girma.Yanzun ta daina zaman dogon tunani,in ranta ya baci Alkur鈥榓ni take dauka sai kaga nan take ta manta da duk wata damuwarta, don Allah kema ki gwada 鈥榶ar uwa,da zaran kin shiga damuwa ki dauko Alkur鈥榓ni ko falaki da nasi kike ta karantawa,sai kinji sanyi aranki in baki manta ba dama shi waraka ne. Yarima ko bayan tafiyar chelen,ya shiga don ya dan watsa ruwa,lokacin sallah ya kusa hankalinsa yana tashe ne,can kasan zuciyarsa tana ta mintsininsa, me yasa zaima beauty haka?Jin damuwa tana son sasa dogon tunani yasashi yin maza ya watsa ruwan, sannan yayi alwala ya fito yana cewa bazai dinga zaman tunani ba,saboda ita amma me yasa kasan zuciyarsa yake mintsininsa? Me yasa zuciyarsa kullum burinta ta ringa kwadaita masa yarinyar?
Ladiyo ta dubi gefen da Mama take zaune,sannan ta kalli su Karima ta soma magana dubi matar can,sunan 鈥榶arta na gidan sarauta amma kullum fate da rana.Salame tace ke da kike wannan zancan an san da zamansu ne?Har shi malam din da yayi hanyar auren,itama yarinyar tunda akayi auren shiru ko irin tazo din nan.Ladiyo tace ta samu dadi yaushe zata tuna da uwarta? Ai dai ba鈥榓yi dacen haihuwa ba wallahi. Duk Mama tana jin su,yi tayi tamkar bataji ba,aranta tace,oh yaushe rabon ta da faten ma,yau ma malam ne yace ta masa amma da sheri harda cewa kullum fate.
Tana mamakinsu gasu da abin zagi rututu amma sun danne suna zagin wani su da girkin ranar ma sai su debe shekara basuyi ba,ita bata da matsalar abinci,dan ko yaushe ne ma ko sati ba鈥榓yi ba da Mansu tazo ta kawo mata buhun shinkafa,katon din taliya,harda galan man gyada gashi su Sakina da Maryam suna mata aike daidai gwargwado,kuma zancan maigado su daba sa kasar kwana biyu ma basuyi waya ba,ko lafiya?Malam ya katse mata tunani da cewa,hakimi ne ya aiko inzo Fatima,bari inje in dawo.Tace lafiya dai ko?Yace nima ban sani ba,sai dai na dawo. Tace to,ya fita ba tare da musu magana ba,suka soma kwasa dariya suna cewa kila ma 鈥榶ar ce aka sako ta.Ladiyo tace,Allah yasa hakane,da sai na zuba ruwa akasa nasha don dadi.Karima tace,haba dani nan bari dai mu jira dawowarsa. Suka shiga 鈥榶an wake-wake su adole burinsu ya cika.Shiko malam yana isa gurin hakimi ya samu 鈥榶an aike daga Bauchi, mota ce guda shake da kayan abinci zuwa na masarufi,inji mai martaba sirikinsa,鈥榶arsa aka kawo ma mahaifin sirikarsa lokacin da ya iso gida murna dai ta kasa boyuwa,tun daga bakin kofa yake fadin ina Fatima,ga sako daga 鈥榶arki.Nan aka soma shigo da kaya ana kimewa, Mama tace ikon Allah haihuwar 鈥榶a mace mai dadi,yau ga uwar mata tana murna ni Fatima na gode Allah.Ai su Ladiyo sai aka shiga sirarewa ana shiga daki,zuciya fal bakin ciki,hassada ga mai rabo taki ce,haka abin yake. Mama ko cewa malam tayi,wannan kaya shi aka ba,don haka sai ya raba yaba kowace hakkinta, yace a鈥榓 san musu za鈥榓yi,tace ai ba zai yiwu ba,a karshe dole ya amince ya raba musu,sai dai duk da haka sai daya kara mata,sannan ya ware mata wanda zata ba mutane,tayi rabo kam duk sauran sassan ta basu,haka kawayenta Umman Mansu ma takai mata da yawa su Ladiyo ko kunya aka amshe shinkafa har ki ga ana salo gurin dafawa ana ci ana zagin Mama da 鈥榶arta, mutum kenan ba鈥榓 iya masa.Umma tana ta zaton cewa Bily tana da ciki ne,don haka duk sanda sukayi waya da Bilyn sai ta rika ce mata don Allah kada ki biye ma babana da cin zakin nan da shan sanyin nan nasa kinji ko?Bily bata gane ba sai tace,to Umma shima Yarima sai ta riga cewa babana amma gida zata dawo nan gaba ko?Shima bai gane nufinta ba,sai yace dama fa kune kuka matsa sai nazo da ita,duk Umma ta damu har takai ga sanar da mai martaba damuwarta,tace ranka ya dade ina zaton matar Modibbo cikine da ita kuma daga shi har ita babu mai hankali cikinsu kada yaje yayi ta tura mata sanyi azo a haifi dan da sanyi ayi ta fama,mai martaba yace to yanda za鈥榓yi tunda ga azumi yana zuwa,in salla ta kusa sai mu tafi Ummara tare dasu daga can sai mu wuto da ita.Nan Umma taji dadin haka.Abinda yayi mugun bata ran Bily, harma da azumin nan Yarima bai daina kwana da mace ba,al鈥榓marin yayi mugun daga mata hankali, tasan cewa duk wani shaidani yakan aje shedancinsa a cikin wata mai alfarma,wata mai daraja,watan tuba,watan yafiya,watan da Allah yake 鈥榶anta bayinsa,watan lada.Don haka tayi niyar zata yiwa Yarima nasiha koda zai dake tane, shiyasa ma yau tayi nufin zama a falo don yin buda baki.Ya fito dakinsa yana sanye da jallabiya fara tas,yaxo ya nufi dinning bayan ta gama mikewa taji zuciyarta tana karfafa mata gwiwa kan cewa taje ta masa magana,don haka ta isa gurin kallo daya yayi mata ya kauda kai tare da cigaba da buda bakinsa,ta zauna tana fuskantarsa.Nazo ne ina son yin magana da kai,ya dubeta sannan yace 鈥渦mhum. Taci gaba da cewa nazo ne in maka tuni kan wani abu dana san ka sani kila ka manta ne,matsayinka na musulmi bai dace ace cikin watan Ramadan kana aikata alfasha ba,kana zina ka sani duk wani musul.....ke!Ya katse ta da tsawa tare da buga teburin cin abinci har kofin glass ya fado kasa ya fashe,abincin gabansa ya tarwatse,ki shiga taitayinki dani,ni sa鈥榓nki ne? Nace ni abokin wasanki ne?Itama tayi karfin hali ta mike tsaye danna gaya maka gaskiya?Yace bana son ji, ki fita daga idanuna,inba haka ba zan nuna miki waye ne Al鈥榓min.
[4:53AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 65馃彽
Ya daga kyallen tebur din ya watsa mata a jiki ya fita daga gidanma.Tsaye Bily tayi tana tunanin dama Yarima ya iya ihu haka?Allah ya kyauta.Shi kuma tun daga ranar ya bude mata sabon daure fuska,wani bari na zuciyarsa yana zugasa kamar sa Yarima dan sarki wannan zatayi ma wa鈥榓zi? Lallai ta samu sake,duk da cewa kasan zuciyar nan tasa tana masa zogi,tare da hura masa wutar sha鈥榓warta, cikin wannan halin azumi ya kai ashirin mai martaba yace,lallai su zama cikin shiri,Magaji yana nan zuwa su wuce saudi tare,su gobe zasu wuce,don haka su samesu can.Bashi da amsar data wuce to duk da suna karatu,yasan tafiyar bazata shafi karatunsa ba,matsalarsa daya itace mata,zaije ibada ne.Ya tsaya neman mata? Sannan ma zuwan Magaji yau din nan zai sa dole ya hakura da kawo mata,shima gaskiya ba sansa bane kawo matan nan da yakeyi cikin wannan watan,amma da zarar yasha ruwa sai yaji su kurum yake bukata, daren ranar yayi niyyar hakura har sai sun dawo amma bazai iya ba,shida kansa yayi ma chelen waya tazo.Suna tare ne a falo sai ga vicky suna jin haushin juna amma ba sa gwadawa a gaban Yarima,domin sun san sa suna soma 鈥榶an harare-harare zai sallamesu,kila kuma ya zama shine karshen alakarsu,kuma in har kikayi fushi kika tafi,to in zaki shekara nawa sai dai fa ke ki dawo.Shiyasa kullum yake ma kansa kirari baya bin mata sai dai su bi sa.Vicky ta zauna adayan gefen tare da dan tsikarinsa ya dubeta da guntun murmushi,sannan ya duketa a kirji,irin dai wasa na gogaggun matasa.Sun sashi a tsakiya kowace burinta taja ra鈥榓yinsa kanta,suna tayi masa wasanninsu na jan hankali,musamman da yake sun sansa yafi son wasannin fiya da ya kwanta da su don haka sai suka kuke dayi.Sha biyu da rabi Bily ta farka daidai lokacin da take tashi kenan,tunda aka shiga goman karshe tsayiwar dare takeyi har asubahi,in tayi sahur sai ta kwanta bayan tayi sallar asubahi kenan.Don haka inta tashi takan ajiye komanta na sahur ne akusa,kitchen ta fito don nufin dauko ruwan zafi tana fitowa falon sai me zata gani? Yarima ne da matan nan duk basa a hayyacinsu,batasan sanda tace,A鈥榰zu billahi minash shaidanir rajim.Sannan tace haba don Allah haba Yarima,kaji tsoron Allah kana tuna mutuwa kuwa?Kana tuna kabari?Kana tuna ranar da zamu tsaya agaban Ubangijinmu?Watan Ramadan cikin goman karshe kuma karshen goman ma da duk wani musulmi yake rage bacci,don kwadayin daran nan na (Lailatul kadari)kuka ne yaci karfinta ta juyo da gudu ta koma ta fada kan gado,sai kuka a dhekarun baya ko watannin baya,tayi kuka tayi addu鈥榓 tayi tsayuwar dare duk roko take Allah ya bata mijin aure.Yau ga miji yaro sharaf mai kyau ga ilmi da ake tunkaho dashi a yau ga kudi ga mulki gata cikin daula taci wanda take so tasha kuma wanda take so, amma hakan bai mata rana ba,hakan baisa ta farin ciki ba,zamanta ada gaban iyayanta yafi mata alkairi,zamanta cikin kunci da kiyayyar mahaifinta yafi mata auren Yarima shin dama haka matan da mazansu ke bin mata suke ji?Lallai ta jinjina musu don suna cikin ukuba,jin zuciyarta take tamkar ta fashe don bakin ciki.Shiko Yarima jikinsa ne yayi sanyi,nan take kwadayinsa ya kwanta sannan ya dubi su chelen yace,su tafi cikin daurewar kai suke tambayarsa dalili, tsawa yayi musu tare da cewa su fita mana?Vicky ta mike ta fita abinta, chelen ce ta tsaya son jin me kanwarsa ta gaya masa? Yace ta fita kafin ransa ya baci da ita,haka itama ta figi rigarta ta fita tana gungunai,shiru Yarima yayi azaune tunani ne fal zuciyarsa yasan tuni ta masa amma anasa girman kai yana nufin ita bata isa ta gaya masa ba,nasa ganin ba girmansa bane tayi masa wannan abin ba.Ya mike ya nufi dakinta har lokacin kuka takeyi,kausasa murya yayi yace,ke!Da sauri ta dago tana dubansa,fuskarsa adaure yace,ban hanaki shiga harkata ba?Bance bana son sa ido ba?Ke kin isa ne ki sani nayi abinda banyi niyya ba?To bari kiji karki kuma shiga harkata, nima kaddara ce Allah ya dora min,bata san lokacin da tace daina gaya min kaddara,Allah baya dorama wata rai abinda ba zata iya dauka ba, wannan wani abune daka dorama kanka.
A yau in kaga dama.... saukar marin data ji ne yasa ta dafe kunne,yace ni kike ma ihu?Ni kike gayama magana?Tace bazan gaya maka ba? Kullum ina dana sanin aurenka bazan gushe ba, gara min auren talaka lis wanda sai ya fita yasha wahala ya nemo sannan muci,matsawar ya tsare kansa daga zina nan ya kuma gabza mata wani sabon marin wanda yasa sai da network dinta ya dauke na wucin gadi.Ya nunata in har kina neman zaman lafiyarki to ki cire idanunki daga kaina iyayena ma basu takura min ba balle ke banza wofi kuma yanda kike dana sanin aurena haka nima nake dana sanin ganinki tun farkon ganina dake,kece mutum ta farko data ke min katsalandan arayuwa,bansan tunani ba bansan mugunta ba duk kece sanadi,ban taba marin wani ba ko zagi ke duk kin sani na iya,don haka in kina neman zaman lafiya dani to ki cire idanunki akaina.Kin taba zagina jahili yau kuma kina cemin mazinaci,kece mutum ta farko da kika taba zagina,ko mahaifina lallabani sukeyi,don haka ina gargadinki da babban murya ki fita harakata,in kin manta wanene ni Yarima Al鈥榓min nake,ni daya ne tamkar da dubu agidanmu, dan haka maida hankalinki ya fita.Kai ta kifa taci gaba da kuka wato yanzu duniya babu gaskiya don kawai ta sanar dashi abinda zai amfane sa, shine harda dukanta?Ranar dai kwana tayi tana kuka ko sahur batayi ba.Wayewar ranar ne Magaji yazo shi kansa yayi mamakin ganin yanda fuskar Bily ta kumbura,idanun suma sunyi luhu-luhu ya nemi jin ba鈥榓si tace,ba komai aranar suka gama abubuwansu na tafiya.Ana jibi sallah suka tafi,ko cikin jirgi 鈥榶ar shariya akayi.Magaji da suka zauna guri daya da Yarima yake cewa,kai dama bakaje ba,Yarima yace wai saboda kurewar lokaci? Magaji yace,a鈥榓 bama don haka ba,na gane kana gaba da iyalinka kuma zaka gari mai tsarki.Yarima yace ka barni da yarinyar can 鈥榶ar rainin hankali ce ita,tsaki Magaji yayi tare da cewa Allah dai ya shiryi halinka. Sun hadu dasu Umma da mai martaba gidan da mai martaba ya kama musu nan suka same su.
[4:54AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 66馃彽
Bily ta yarda da zancan Yarima,da yace shi da daya ne tamkar da dubu,domin yanda taga iyayan suka nuna karara son dan nasu suke,haka nan manyan mutane abokan nasa da wasu da suka samu zuwa daga cikin danginsu sai ina ka saka ake dashi.Umma ko sororo tayi lokacin da suka hada idanu da Bily, tasa rai ta ganta tana daga kafa da kyar sai gata tangaran to ko dai karami ne ko kuma yabi jiki?Duk wannan tunanin Umma ne amma tasha alwashin zata tambaye su taji kar dai suna shan kwayoyi ne?Yin wannan tunanin sai da gaban Umma ya fadi tace,inko haka ne sun cucemu.Bayan shan ruwa sunci sun sha ana zaune ana hira kafin lokacin zuwa masallaci,Umma ta dubi Yarima tace,ubana na zaci zanga matar taka da tsohon ciki?Yarima yace,haba dai Umma tun yanzu?Tace kaji shashanci da sai yaushe mu da kullum addu鈥榓rmu muga 鈥榶ayanka,yace dazun ma mai martaba fa cemin yayi wai to kai Modibbo in zamu tafi da matarka zamu wuce inta haihu sai ta dawo,abin ya daure min kai nace ranka ya dade tana da ciki ne?Sai cemin yayi kuji zancan banza, ni zaka tambaya?Suka kwashe da dariya, Umma da Magaji.Yarima murmushi yayi don shi baya kyalkyala dariya.Bily kam sai tayi kasa da kai, Magaji ya mike tare da cewa zo muje masallaci. Yarima yace kwarai muda bamu zo da wuri ba.Suna fita Umma ta dubi Bily wai da gaske ne 鈥榶ar nan baki da komai?Kunya ta rufe Bily,kanta na cikin cinyarta tace,wallahi Umma ba komai,tace ko dai kwaya kike sha ne?Tace Allah bana shan komai,tace ko shine dai ke baki,yace kada ki fada?Don fa karki yarda ki dinga shan kwaya nan gaba ta miki illa,kinga shi namiji ne da zarar yaso 鈥榶aya zai iya karo aure,ke kuma an cuceki. Bily tace,wallahi Umma bama shan komai,to kun taba ganin likita?Cewar Umma,a鈥榓 inji Bily,bamu taba gani ba,tace to wannan ai shirme ne,kafin mubar garinnan sai munje kunga likita. Gurin kwanciya, Bily ta shige gurin Umma dama su Yarima suna can masallaci suma zuwa sha biyu suka nufi masallacin, haka sukayi ta ibada har ranar sallah.
Bily kam ranar data ganta gata ga Ka鈥榓ba,ai addu鈥榓 sai wadda ta manta. Murna kuwa harda hawaye, domin arayuwarta bata taba tunanin yau rana zata zo da zata ganta agaban Ka鈥榓ba ba.A cikin addu鈥榦鈥榠n da Bily tayi ta roki Allah game da aurenta da Yarima,kan cewa in mai shiryiwa ne Allah ya shirya shi sannan ya daidaita tsakaninsu in kuma babu daidaitawa,to Allah ya watsa abin ya kawo mata karshen wahalarta,sannan ta roki Allah ya sassauta ma mahaifiyarta,game da abokan zamanta ya kuma sa mahaifinta ya dawo kan hanya.Ranar sallah mai martaba ya nufo gida,Umma dai ta tsaya sai sunga likita.Daran ranar Yarima ya kasa hakuri da jarabarsa ta motsa,dakin Umma ya shigo Ummar tana toilet sai Bily dake zaune,tana neman layin Mamanmu sun gaisa da kowa amma ta kasa samun Mamanmu ya dubeta ransa ya sake biyawa,amma girman kai ya hanasa yayi mata magana.Har zuwa sanda Umma ta fito,tace yaya ne babana?Ya danyi murmushi sannan ya dubi inda Bily take zaune yace ba komai dama nazo ne nace miki sai da safe. Abinka da manya,nan Umma ta gano nufin dan nata,don haka tace,Bily tashi kije gurin mijinki mana, ni sai naga ma kamar gudunsa kike tunda muka zo banga kina bashi wata kulawa ba.Tana wannan maganar ne bayan fitar Yarima,taci gaba da cewa kin san fa su maza 鈥榶an lallashi ne,suna san kulawa bare irinsu Yarima.Bily tace Umma ba kirana yakeyi ba,Umma tace kaji sokuwa, yanzun yaushe ake jiran kiran miji?Har dai Yarima dan jin kai?To maza tashi ki bishi dama zaman da kukeyi kenan sai yace zo? Tashi-tashi maza-maza kar in sake jin haka.Bily ta mike ranta bace zata tafi,Umma tace,haka zaki je ba ko dan saka turare?Bily kam ta cika ne da mamaki,da bata zata haka Umma take ba,kuma sai tana ganin kamar ko san kai ne Umma take nunawa,don dai Yarima danta ne,duk da ta sani Umma tana sonta.Hoda ta murza sannan tasa turare ta saka kayan bacci sannan tasa hijabi ta fita,yana zaune bakin gado ya rasa me ke masa dadi,kamar ya zama kuda ya dauko Bily yake ji. Ta shigo da sallama fuskarta daure, tamkar an jefa shi cikin gidan aljanna haka yaji,harda yin wata ajiyar zuciya,amma don jan aji irin na Yarima sai ya wani daure fuska tare da cewa, lafiya ?Bata yi magana ba,ta zauna can gefe kan kafet,kin shigo min daki kina ta wani daure-dauren fuska bayan ban kira ki ba.Shiru dai ta masa,yace ok,in baki da magana tashi ki kama gabanki.Ga mamamkinsa sai yaga ta mike zata fita,yasha gabanta, ai bazaki fita ba har sai naji dalilin zuwanki. Bily ta dubesa, Umma tace inzo,oh shine dan kin raina Ummar zaki koma can ko?Tan ki koma din,ya koma gefen gadonsa ya zauna sannan ya dauko laptop dinsa ya soma kunnawa tana dai tsaye.Ta dawo ta zauna inda ta tashi yaci gaba da tura wani assigment ya jima yana turawa har ya gama,lokacin ta soma gyangyadi yace,ke ta farka idanunta fal bacci yace zo ki kwanta ba don halinki ba,tace nan ma ya isa, yace ke komai sai kin min gaddama,harda kice nan ya isa ance miki ina kalanki ne?Kema gulma ta kawo ki ko da Umma tace ki zo nasan kina son zuwan ko don a sosa miki abinda ke miki kaikayi, bani da yanda zanyi tunda an makala min ke.Mikewa kawai tayi taje ta kwanta, sai daya gama mata wulakanci kala-kala sannan ya shiga yin abinda ransa ke so da ita,jikinsa har bari yakeyi duk da dai yau ma kamar kullum,gim ta masa kamar kullum,haka ma da safe gari yayi haske amma ya fake da cewa kada ta kuma dawo masa yau bari ya sallameta gaba daya,bashi ya barta ba sai da Umma ta kwankwasa musu ita dai ta sani arashin 鈥榶anmatansa ne ya kula ta shiyasa bata jin itama zata sakar masa kanta yanda ta kula yafi bukata, ta aje aranta yanda ta rasa wanda zaice Bily ina sonki,haka ta hakura da jin wannan dadin don a duk lokacin da Yarima yake kusantar ta zuciyarta tana gaya mata cewa makiynki ne ke son hutawa da ni鈥榠marki,don haka sai taji duk mugayan maganganun da yake gaya mata suna dawo mata,kuma sai taji tana kyamarsa saboda matan da yake hulda dasu, sannan burinsa na taji dashi dadi ba zata ji dashi ba har abada,sai dai yanda suka saba.
[6:28AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 67馃彽
Suna zaune gaban likita sun masa dukkan bayanin daya dace,sannan ya shiga dubasu.likitan ya tabbatar da cewa lafiayarsu lau,sannan ya basu wadansu kwayoyi wai su sha bayan sun dawo gida Umma tace,to su zo suje suyi tsaraba don ita gobe jirginsu zai tashi zuwa Nigeria su kuma sai gobe sannan zasu wuce Malesia tace wallahi Umma naso in biku gida nayi missing din Mamana.Umma tace,me zaki je Nigeria kiyi mijinki yana wata duniyar?Ke dai kiyi hakuri ba shekara mai zuwa bace zai gama ko ta sama ce? Kamar yau ne gurin Allah Mamanki ba kuna waya ba?Tace mu kanyi saboda yawanci sai sanda Mansu taje gidan sannan ta kira ni,Umma tace a鈥榓 bata da waya ne?Tana da shi,inji Bily to ni yaushe rabona da wayata taga kati sai zuwanmu nan da Magaji yasa min,Umma ta kalli Yarima, me kenan babana?Yace to Umma yaya zan mata,ita fa tunda taje tafi karfin tace min tana son kaza,ko na ci ko a na sha bare kati, Umma tace to ke kuma ai wannan hauka ne, keda mijinki?Kusan shekara kin kasa sakin jiki dashi to dawa zaki saki jiki?Ki daina haka kinji ko, gaki kamar kanki a waye?Duk abinda kike so ki masa magana tace,to Umma yace kuma da kanta take abinci amma bazata ce tana son abu kaza ba,madam dora ce ma take gaya min cewa, tana cin taliya shine in sun zo shi cefane sai nace ya siyo mata,Umma tace ta daina haka Bily tace to insha Allahu bazata kara ba, azuciyarta sai mamaki takeyi shin Yarima da gaske ne da zata tambayesa abu zai mata?Tasan kila bazai ba don dai yaga mahaifiyarsa ne kurum.Sun shiga siyayya shagunan larabawa,nan taga mamaki Umma cewa tayi duk me take so ta diba na tsaraba nasu Mamanta ma ta dauka sai ta wuce dasu ta bada akai musu,amma ta kasa daukar komai sai Umma ce ke cewa, dau wannan dau wancan daga karshe ta daukar ma Asma鈥榰 auta dankunne da sarka na gold ita da yarinyar Mansu,sannan ta yiwa Dady tasa haka suka yi ta shiga shaguna suna kashe kudi,Yarima dai ya jidi kananan kaya harda 鈥榶anmatansa yayi ma tsaraba,da Umma tace na Bily ne kai tsaye yace a鈥榓 ya sayawa abokan karatunsa ne,kuma ga mamakin Bily Umma ba tace komai ba.
[6:30AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 68馃彽
Komai me lokaci yana da iyaka,su Yarima anyi jarabawa cikin nasara an gamata a sa鈥榓,ya zama cikakken likitan mata gwani,Doctor.Ana gobe za鈥榓 tabbatar musu da zamansu likitoci,su Magaji suka iso tare da mai martaba,da kuma wasu daga cikin yayyansa,tunda Umma ta sanarda Bily zuwan bakin nasu,suka je kasuwa don shirin tarbar bakin,sun kammala komai,sannan bakin suka iso.Su anty Fulera sai 鈥榶an harare-harare akeyi,Bily dai ta kula da take-takensu amma ta share ita farin cikinta daya, kammala karatun Yarima zata gida taga Mamanta da 鈥榶an uwanta,ranar rantsar da likitocin rana ce mai mahimmanci gurin Yarima da mahaifinsa guri yayi guri,manyan mutane daga nahiyoyi sun halarta. Yarima shine dalibi mafi kwazo cikin daliban da suka hattama karatun,don haka hukumar ilmi ta kasar ta bashi lamba ta farko data yabo sannan ta bashi dama ya zabi duk kasar da yake so cikin jerin kasashe goma don yin wani course na daban har na tsawon shekara daya ko biyu,wannan nasara da Yarima ya samu tasa shi farin ciki shida masoyansa,sun shirya 鈥榶ar kwarya-kwaryar party shi da abokansa. Can gida kuma suma suna tasu walimar.Mai martaba dai yana can masaukinsa,tun ranar suka so,a nade kaya farin ciki gurin Bily ba鈥榓 magana, a daren ana gobe zasu dawo gida Yarima an samu nutsuwa,tunanin shi daya inya koma gida babu mata kenan, Allah sarki,Ashly yarinyar da suka hadu babu dadewa tana masifar ji dashi, shiyasa ma yake matukar sonta don shi yana son akula dashi,ko bai sallama da kowa ba dole ne yayi sallama da ita,suna hira ne da 鈥榶an uwansa amma ya mike can gefe ya kirata ya kuma sanar da ita cewa su hadu guri kaza. Ashly irin black american din nan ce,tana da tsawo da kiba,amma kibar ta a mazaunai ne da kuma kirjinta,tana son Yarima musamman data fahimci shi mai sha鈥榓wa ne,tana matsa shi sosai kuma ba tsararsa bace,zata girmesa,kafin yaje gurin ta rigasa,sun lalace son ransu sannan ya tile mata kudi sukayi sallama,kuma ya mata alkawarin indai ya ga da sarari zai mata kwatance tazo Nigeria itama harda kuka,nan Yarima ya kara susucewa danshi yana so yaga mace ta mutu kansa. Sanda ya dawo suna ta hira da Bily,yana shigowa ta kallesa ta kauda kai tasan me yaje yay,haka nan Magaji.Washegari suka hau jirgi sai gida. Abuja suka sauka,Bily tana shakar iskar kasarta sai taji tamkar an sakata cikin gidan aljanna,nan suka hau wani jirgin zuwa Kaduna,Bily taji tamkar ta sauka zaria lokacin da suka dauki hanyar Bauchi. Lifaya sosai aka shirya musu,sunci sun sha ana ta hira ita dai Umma damuwarta rashin ganin Bily da tsini agaba,haka sauran kishiyoyin Umma sai da sukace amare har yau anata amarcin tukunna?Anty Fatima tace,mu bama son wani amarci,鈥榶aya muke bukata,mun gaji da sai dai aci ayi kashi.Umma tace kadaku matsa mata, haihuwa aita Allah ce,ni damuwata ma ko kiba banga ta kara ba 鈥榶ar tawa. Anty Saliha tace, amma Umma aita murje,dibi yanda fatarta ke sheki,sai kace tarwada?Bily dai tana jinsu,ita dai matsalarta daya tana son ganin Mamanta,zata gwada tambayar Yarima ta gani ko zai barta?Da safe ta shiga gurinsa ta samesa zaune yana kallon(BBC)ta zauna dan kusa dashi tace ina kwana?Ya dubeta dama kin iya gaisuwa?Tace to inna gaishe kane baka amsawa,ya dan taba baki tare da cewa,kina bukatar wani taimako ne?Tace,em dama ina wannan ne ya dubeta kiyi magana bana son kwana-kwana,tace ina son naje naga mahaifiyata ne,yace yaushe?Tace duk sanda kace,yace shikenan kije sai sanda nace din,tace to yaushe? Yace bana son naci ki jirani tukunna,tace shikenan ta mike ta fita.Satin duk bata da sukuni ba ta zuwa sasan shi shima baya nemanta duk da yana bukatarta,jin shiru ne yasa ta sake nemansa taje da dare baya nan da safe zata shiga kenan tazo falonsa na kasa sai gashi ya sauko tayi sauri tace,ina kwana?Ya amsa da lafiya, zai wuce tace gurinka fa nazo,ya tsaya sannan ya juyo yana kallon lebunanta da matsala ne?Maganar zuwa gida kaga tunda nazo ban taba zuwa ba ka dubi tsawon lokacin?Ya soma tafiya da cewa duk sanda kikaga ya dace sai ki sanar dani,tasha gabansa da sauri yau ko gobe,yace fine ya fita ta tsaya shiru ko dai gatse yake mata?Kai takan rasa gane hali irinna Yrm,shi kullum ana tarasa nan yana botsewa data shiga gurin Umma suka gaisa ta sanar da Umma cewa tana son zataje gida don taga mahaifiyarta,kuma ta sanarda Yrm yace ko yau ko gobe,Umma tace sai dai goben don sai an sanarda mai martaba,tace to data shiga dakinta murna harda tsalle,sai kace karamar yarinya.Ta kira Mansu ta shaida mata cewa gobe tana zuwa,ta kira su Maryam da Sakina duk ta sanar dasu,ta kira Mama tace gobe tana hanya,Mama tafi kowa murnar zuwan Bily,saboda gorin da kishiyoyinta suke mata cewa sukeyi tir da wannan 鈥榶ar ta samu daula ta mant da uwarta,gori harda surukarsu Gwoggo amarya,tace inda kwadayi to da wulakanci,an tura yarinya gidan miji gidan sarauta don kwadayi gashi nan kila ma tana can tana wahala,inba haka ba shekara nawa bata zo ba,kamar an saida ita.haka nan 鈥榶an unguwar akayi ta surutu,wasu ma sai sun hadu a sha鈥榓ni sai kaji sun ce ina amare?Ana can dai,Mama kance um tana can da an dameni batayi aure ba batayi aure ba,yanzun kuma tayi an koma kan bata zuwa indai tana zaune lafiya acikin dakinta ai alhamdulillah, sai kaji mutane ana cewa hakane fa,Mama tana sa tare da cewa insha Allah maigado tazo garin nan sai nace ta shiga duk makotan nan ta gaidasu. Malam ya shigo tace, Malam gobe fa maigado tace tana hanyar zuwa,murmushi ne ya subuce masa cike da fara鈥榓 yace ikon Allah,nidai dama kullum yarinyarnan tana raina,lallai muna da babbar bakuwa,Allah yasa ta iso lafiya,Mama tace amin.Bily daren ranar batayi baccin kirki ba, saboda tsabar murna,tunda duku-duku ta shiga gurin Umma, umman lazimi takeyi don haka gefe ta samu ta zauna bayanta gama suka gaisa,Umma tana murmushi tace,Bily kin kosa kije gida ko? Tayi dariya tare kuma da sunkuyar da kai,Umma tace to kinyi tsaraba ko?Bily tace,sai dai wadda muka yo daga malesia, tace a鈥榓 wannan tayi kadan tunda kila wasu kika gayyade kika sai musu wannan ko ganin gida zaki je,gashi baki taba zuwa ba,sannan gashi kina gidan sarauta,ina Yariman?Tace am yana daki,ta dai fadane don ita yanzun dai bazata ce ga inda yake ba,Umma tace ya dace ma ace tare kuka je dashi,donsu gansa,tunda bai taba zuwa ba
[6:31AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 69馃彽
Bily tace to sai dai inya shigo ki masa magana kiji,Jakadiya ta shigo da sallama,sannan ta zauna ta gaida Umma suka gaisa da Bily,Umma tace Jakadiya a duba cikin store din nan afito min da bandiran zannuwa da kuma shaddodi,tace to ranki ya dade,zamu sha sababbin dinkuna kenan?Umma tace a鈥榓 ba naku bane,Bily ce zata ziyarci mahaifanta. Jakadiya tace, a lallai gimbiya yau sai murna,Umma tace da Yariman ya shigo ai da kunje kuyi ma mai martaba sallama,kafin ta rufe baki sai ga dan halak din nan shikenan ma kuje ta yiwa mai martaba sallama kaima kuma ya dace ace kaje ka gaida surukan naka. Yarima ya dan ya mutsa fuska sannan yace gaskiya sai wani lokaci Umma,don yanzu ina Busy na shirye shiryen Zan je wani course wanda muke matsalarsa anan Nigeria ma鈥榓na in samu wani horo game da wata cuta wadda babu likitocinta sosai anan gida,Umma tace um Allah ya taimaka,amma ka sallame ta da tsara ba ko?Yace to ai batace min zatayi tsaraba ba,Umma tace to ni nace maka, yanzun ku shiga gurin mai martaba ta masa sallama. Mai martaba yaji dadin wannan ziyarar da zataje, sannan yace ki sanarda mahaifanki duk su biyun zasuje aikin hajji bana,ta shiga godiya,Yarima yana tayata mai martaba yace, babu komai wannan kyautar ya kamata ace tuntuni akayita, kasancewar basa kasar sai abin ya kwanta masa da murnarta take sanarda Umma tana godiya tayi tare da ce ma Yarima babana kadai ji kunya kaine ya dace ace kayi wa surukanka wannan kyautar,Yarima ya mike tare da cewa Umma bari nayi wani aiki cikin computer.Ya fita Umma tace kace dai bari ka gudu baka son fadan gaskiya. Bily tayi shiri sosai ga tsaraba Yarima ko kudi ya zube mata sababbi dal 鈥榶an dari bibbiyu,鈥榶an naira dari,鈥榶an dari biyar zuwa dubu daya,kasa magana tayi ta tsaya kallonsa,yace nace ne ki dauki yanda zai isheki tace ni nafi son ka bani da kanka,yace ni kuma nafi son ki dauka don kina sa Umma tana daukana marowaci,baki tambayeni abu ba yaya zanyi in san kina da bukata?Tace to naga karatu kakeyi shiyasa banason matsa maka, yace wannan ba hujja bace,tunda baki taba ganin don ina dan makaranta yau nace wayyo yaya zanyi bani da kudi ba. Don haka dauka in kika dauka duka ma ba matsala,ya juya zai fita tace,to bari na dauka sai ka wuce dashi cikin kowane dauri ta dauki daya,sannan tayi godiya yace a鈥榓 ki gode ma Allah ya dauki jakarsa ya fita. misalin karfe sha daya su Bily sun dauko hanya ga tsaraba mota guda,farin ciki gurin Bily karki tona yau za鈥榓 ga Mamanmu.Ita ko Mamanmu ba zato sai ga Maryam daga kaduna zuwa jimawa kuma ba sai ga Sakina ba,suna cikin gaggaisawa ne sai ga malam da kaji guda shidda yankakku,yace Fatima gashi ku tashi kuyi azama ku gyarama bakin nan me da me za鈥榓 siyo na cefane?Su Sakina suka fito suna gaidasa tare da cewa,ai ko bari muzo mu kama aikin,cikin fara鈥榓 yake cewa duk yanzu kuke tafe?Yaci gaba sannunku da zuwa,Allah ya shi muku albarka,cikin mamaki suka ce amin,yace kun samu labarin zuwan 鈥榶ar uwar taku ne ko? Suka ce ta kiramu ne ta shaida mana yace to to madalla tunda gaku sai kuyi azama ku shirya musu abinci ko?Ya miko dubu biyu gashi sai kuyi cefane,ya zamana dai an shirya musu girkin mai kyau kan lokaci,suka ce to baba.Mamanmu dai ranta kar,yana tafiya sukace oh abin mamaki yanzu baba kara sonmu yakeyi dibi yanda yake ta rawar jiki,Mamanmu tace to ku addu鈥榓 banza ce 鈥榶ayan nan?Kuna fa gani babu dare babu rana ko yaushe cikin du鈥榓鈥榠 nake.Sakina tace,kuma muma munayi bamu zauna ba,nan suka hau aiki,auta ma ta dawo daga aike itama nan ta hau aikin.Su Ladiyo ko sun ga shigowar malam da kaji don haka suka kafa dandali suka soma tsegumin nasu,karima tace tunda nake gidan nan ban taba ganin malam yazo da ko kaza guda yace a soya ba,sai yau. kodan su Sakina ne ya siyo?Ladiyo tace kince kaza ko kwai ya taba kawowa?Don haka kan kajin nan sai anyi tsiya,inma dansu Sakina ya sawo mu fa da 鈥榶ayanmu suke zuwa me ya taba kawowa suka dafa?Salame tace,bana zaton donsu Sakina ya kawo nafi tunanin wani sabon wulakancin za鈥榓 fara mana don ko ni ashirye nake dan ko daidai za鈥榓 raba kajin nan,nan dai suka kasa suka tsare kowacce tana cika tana batsewa.
[6:32AM, 12/28/2016] 鈥�+234 814 912 1821鈥�: 馃彽MEKE FARUWA 70馃彽
Su ko su Sakina suna ta aikinsu girka wancan dafa wannan soya wannan har suka gama suka share gidan suka gyare dakin auta wato dakin Bily na da suka cire gadon suka shimfida babbar tabarma,suka jera abincin ciki.misalin karfe uku sai gasu Bily sun shigo birnin zazzau,jinta take tamkar anyo mata wahayi cewa an mata gafara.Sai da suka bita masarautar zazzau sannan suka wuto,ita daya ce sai kuyangi biyu Atika da Asabe,dayar motar kuwa dogarawa ne sai tsaraba,tunda suka shigo cikin unguwarsu take ta kalle-kalle,unguwar tana nan yanda ta santa,wasu gidajen sun kara lalacewa, wasu gidajan kuma sun samu gyara,daidai kofar gidansu motoci ne suka tsaya gidansu shima ya kara lalacewa sai dai duk da haka an share kofar gidan tas, yayinda mahaifinta da kannansa da kuma shi kansa mahaifinnata duk suna kofar gida suna ta alwala,nan suka tari su Bily da dogarawa aka bude ma Bily mota ta fito,subhanallahi,ganinta sukayi tamkar ba mutum ba don kyau,ta kara fari fatarta shar,duk da bata kara kiba ba daka ganta kaga hutu,durkusawa tayi tana gaida iyayanta suma kuyanginta haka sukayi, Asabe tana rike da jakarta suka shiga cikin gida, matan gidan suna nan gurin da suke suna sakawa suna kwancewa game da girkin da suka ga anyi an turasa cikin dakin auta,yanzun sun karkata tunaninsu kan cewa kila mazansu ne zasu zo shine akayi wannan girki,Karima na cewa wallahi bari zamuyi sai mazajan sunzo suna cikin cin abincin muje gurin Fatimar mu tada masifa muce sai an bamu hakkinmu, kunga mun kunyata ta gaban surukai.Ladiyo tace don surukai ba sufi surukai ba,namu surukan ko fiya wata ya taba sai musu?Sallamar Bily da kuyanginta ne ta tsaidasu daga hirar da sukeyi,cike da doki ta shigo tana cewa,sannunku Gwaggo,mamaki hade da firgici suka hanasu magana,bata kula ba ita dai burinta tayi arba da Mamanmu,tun kafin ta isa dakin ta soma kiran Mamanmu!Mamanmu!!Su Sakina ne su uku suka fito da gudu suka rungumeta suna oyoyo anty Bilki.Nan take hawayen farin ciki suka soma zubo mata. Mama tana zaune abakin gado cike da fara鈥榓,Bily taje ta zube jikinta Mamanmu tace menene haka?Nan suka zauna aka shiga gaggaisawa,su Asabe ma suka gaishe su daga nan sai dakin auta,nan suka zube suna cin abinci.Dogarawa kuwa sun wuce sallah ne tare da su malam ,suna dawowa yasa suka shiga dakin Sani,nan kofar gida ya shiga ciki ya amso musu nasu girkin.Nan kuma jikinsu Ladiyo yayi sanyi,sunma rasa me zasu tattauna ne akan wadannan mutanan. Mama ta kira auta tazo tace amso kwanukansu Ladiyo azuba musu mana,su Sakina ne da gaddama tun dazun ina cewa su zuba musu suna cewa baza鈥榓 basu ba,auta ta samesu jugun-jugun tace,Mamanmu tace ku bada kwanuka asa muku abinci.Salame ce kurum tayi karfin halin nuna mata kwandon kwanukan ta dauka taje ta kawo musu ta aje su dai suna nan yadda suke.Bily ko bayan sunci sun sha sunyi sallah, sannan tace Mamanmu bari naje gidan Umman Mansu.tace to ki shiga sauran sasan gidannan ku gaisa,duk da nasan sunji kinzo,amma Gwaggon sasa ce kawai ta shigo wajan nan, sannan duk makotan nan ki shiga ku gaisa,tace kash!Gashi kuma ban tambaya ba,amma zan masa waya ko gobe ne sai na shisshiga tare da su Sakina da kuma kuyanginta suka nufi sasan,Asabe na rike da jakarta yayinda Atika take rike da wayoyinta kafinsu wuce sai data shiga dakunan su Gwaggo ladiyo suka gaisa, dukkansu jiki babu laka yaransu kuwa sai kallonta sukeyi nan tace,Asabe ban jakar nan ta ciri bandir din 鈥榶an dari bibbiyu ta mika ma auta,gashi ki raba ma yarannan sunsha alawa.Nan ko suka yance ta suna Asma鈥榰 ni baki bani ba,iyayan suna lekowa suka gani nan kowa ta soma raya abinda zatayi da na 鈥榶ayanta in sun kawo.Ta babban sasa suka fara inda gayyar gidan take,suna ko tsakar gida suna ta labarin zuwanna Bily yaran gidan suna ta bada labarin zuwanta suna cewa taci gayu ga wasu hadaddun motoci masu burgewa,kai kunga masu tsaronta sun rike wasu manyan bulalai, sallamarsu ce ta katse Mairo lokacin da take cewa,uwarsu yau sai ji da kai.Bily ta shigo tare da gayyarta,daki-daki tabi kowa suka gaisa yayinda Asma鈥榰 ta shiga rabawa yaran dari bibbiyun.
Mansu ta kira wayarta, Atika ta miko mata wayar tare da cewa,ranki ya dade an kiraki.Ta amsa ta duba sunan Mansu data gani ne duk ta rude tana cewa mutuniyata kin iso ne?Tace mun kusa na jira dady ne ya taso daga islamiya, tace a鈥榓 aminiyata kina son tafiyar dare,sai kin iso tawan,ki wuce gidan Umma don can zan nufa,tace to sai na karaso,amma fa gidana zaki kwana,ban tambayo ba.Cikin dariya Mansu tace yayi kyau,inna iso aida kawai waya akira itama cikin dariya tace,sai kin iso din,ta kashe ta mikawa Atika,sannan suka cigaba da gaisawa,sai kallonta sukeyi ganinsu salo take musu da iyayi gami kuma da yanga,don haka tana fita suka hau kwatanta yanda take magana.Gurin Gwaggo sasa suka shiga,sun gaisa cikin barkwanci take cewa ina angon namu,shi ba zaizo ba?Bily tace,zaizo yanzun aiki ne yayi masa yawa,daga nan sai gurin kakarsu,wadda tayi wani kici-kici da rai suka shiga suka gaisa,sannan ta soma cewa ke kuma sai yanzu kika ga damar zuwa garin,ance miki aure hauka ne,don kinyi aure shikenan sai ki manta da batun iyaye?Ba鈥榓 tamu kakanni,to da mijin naki kuka zo ko?Tace a鈥榓 mu kadai muka zo shi yana aiki ne,Gwaggo ta turo baki tare da cewa,um ba wani aiki shi dai yace bazai iya zuwa gidan talakawa ba,kila ma ke kanki ba鈥榓 bakin komai kike agurinsa ba,banda haka ace aure shekara nawa amma iyaye ace in mijinki ya gansu bazai sheda su ba?Bily ta mike zata fita,to kin fita mana tunda na dauko batun gaskiya,Bily tace ba haka bane,kwata-kwata yaushe ne ma muka dawo kasar, ai zaizo ne.Gwaggo tace kada ma Allah yasa yazo,wannan ruwansa ne.Sakina ta mike zo muje kinji anty,tunda dai kina zamanki lafia da mijinki kada ma yazo din,Gwaggo tace to shugaban marasa kunya, naci ubanki yanzun ni sa鈥榓rki ce da zaki gaya min magana?Nan dai suka fice suka barta. Bayan sun shiga ko鈥榠na sai kuma suka koma gida inda malam ya samesu dakin Mama sai sannan suka gaisa yace yaya me gidan naki?Yaya iyayan nasa duk dai kuna lafia ko?Tace lafia lau,to yaya gurin Umma fa?Wato kakarta Umman Mamanmu, tace suna nan lafia
0 comments:
Post a Comment