D'akin da Abdulmajid yake ta koma, tana shiga ta taradda Mairo dake tsaye tana jikin kofa da alama nemanta take.
Yanda ta ganta yasa tasan ba a hayyacinta take ba, Mairo ta ja hannunta ta shiga da ita ciki sannan ta zubo ruwa a kofi ta mika mata, tace " naga kina bukatar kad'aicewa ni bari na wuce."
Khadija bata tanka mata ba haka kuma bata sha ruwan ba sai daj yana rike a hannunta.
Tashi tai taje kusa da Abdulmajid tana kallansa, hawayene kawai yake zubo mata, ganin kukan na neman kamata tai ban d'aki da gudu.
Tana gama kukanta ta fara wanke fuskarta, taje zata bud'e kofa ta fito taji muryar Hisham na cewa Khadija? Da alama shigowa yai nemanta, bayan kofar bandakin ta labe da sauri, shi kuma jin shiru yasa ya d'an bud'e ban daki, da yake a rikice yake bai yi tunanin zata iya b'oyewa ba, kawai sai yai tunanin bata ciki.
Juyowa yai zai fita, Magajiya ce ta shigo, ko ta kanta baiyi ba ya fara kokarin wucewa, ba abinda ta tsana irin a ganta ai kamar ba'a ganta ba, a xuciye tace " Waziri meye hakan?baka ganni bane?"
Yace "na ganki, sai dai abinda ke gabana yasa idanuna suka rufe."
Ganin yana neman fita a xuciye tace " Yaya Tsaya!"
Tsayawa yai sannan ya kalleta yace " bakiji nace idanuna sun rufe ba? Alama ce ta ba lafiya ai."
Tace " wannan ba damuwa ta bace, damuwar ka ce, sai dai inaso in sanar ma inma ka nuna baka ganni bane saboda abinda na fadama na cewa ka tabbatar kace kaine sanadin komai, kake neman yadda ni to kada ma ka soma, ka fi kowa sanin nice yar uwarka kadai a duniya nice sirrinka kuma nice reshenka."
Ran Hisham yakai makura yace " reshen da bai dade ni da komai ba sai wahala? Sanar dani me wannan reshen yamin a rayuwa?"
Magajiya tace "mene? Ni kake fadama haka yaya? Ni kake tambaya me na maka? Duk daula da jin dadin da kake zaune a ciki waye sanadi? Kana tunanin karfinka da matsayinka ne yasa?"
Cikin takaici yace " daular banza daular wofi, daular data sa 'ya'yana suka tarwatse? Daular da ta ke rinjayata nake aikata abinda bashi bane? Daular da tasani kisan kai?"
Jikin Khadija ne ya kaure da rawa, batasan sanda ta tsugunna a bandaki ba, kisan kai?
Abdulmajid kam gaba d'aya jiyai gab'obin jikinsa sun daina aiki.
Magajiya ce ta sa dariya tace " ashe kasan da wannan, na d'auka ka manta da mumuman abinda ka aikata."
Hisham fuskarsa ta canza sosai yace " kina tunanin duk abinda nake miki kyaleki nake ko dan ina tsoranki? Dama ina jurewa ne saboda d'ana, yanzu kuwa abinda nake jurewa dominsa na kwance ba lafiya, kina tunanin akwai abinda zai tsayar dani?"
Kallansa tai tace " me zaka iya yi in baka jure ba? Sanar da abinda muka aikata? In haka ne kaine a ruwa dan kai kasan ni da kaina ban taba kaahe mutum ba haka kuma bantaba sawa da bakina a kashe wani ba."
Hisham kallan tsananin mamaki kawai yake mata, yace " mene?"
Tace " ni na saka kaje kashe Turab sanda aka haifeshi?ko nice na saka ka sama gidansu wuta ka kashe yayan mahaifiyarsa da matarsa?"
Abdulmajid ji yai kansa na wani irin juyawa, yanasan yai kara yace musu khadija na bandaki sai dai inaa, wani irin juyawa kansa yakeyi wanda gaba d'aya bakinsa ma ya kasa bud'uwa.
Hisham ya sa hannayensa biyu ya shake ma Magajiya wuya, kallansa tai tace "wani kisan kake san yi? A gaban d'an ka?"
Kallan Abdulmajid yai sannan ya saketa, nuna ta yai da yatsa sai dai baice komai ba sai idanunsa da fuskarsa da suka canza sosai.
Magajiya ta kalleshi shekeke tace " yaya baka isa ka gudu daga tarkona ba."
Kallan Abdulmajid tai sannan ta juya dan tambayar Likita halin da yake ciki.
Abdulmajid mutsu mutsu kawai yake akan gado.
Mairo kuwa harta hau kan mashin ta tuna tabar ledar kayan da zata canza in zata gidan bikin daga gun Umma.
Saukowa tai ta nufi ciki.
Tana shiga ta taradda Abdulmajid na kokarin faduwa, da sauri ta shiga ciki ta rikeshi tace " Abdulmajid!"
Jin muryar Mairo yasa ya bud'e idanunsa wanda suka canza kala sosai, hijab dinta ya riko bakinsa ya shiga rawa yana san magana.
Mairo duk ta gama rikicewa, kallansa take tana cewa " menene?"
Ganin ya kasa magana ta gyara mai kwanciya sannan ta zare d'ankwalinta ta shiga fifitashi, dan gumi yake kamar ba fanka a d'akin.
Wani irin ajiyar zuciya yai wanda duk wanda yake kusa sai ya juyo, Mairo ta kalleshi tace " Abdulmajid!"
Yace " Toilet, Mairo Toilet."
Toilet? Ta maimaita tare da yin hanyar, A kwance taga khadija shame shame a cikin bandaki, duk ta gama rikicewa nan ta shiga kokarin fito da ita, da kyar da jawota duk yanda ta jijigata ta kasa tashi, ga kayanta duk ya soma jikewa, a rikice ta shiga kokarin cire mata kaya, ta d'auko nata wanda ta manta, ta zare zanin ta sa mata siket dinta.
Ganin rigar bata jike sosai ba yasa fito da sauri dan neman nurse.
Wani ta gani da farar riga irin ta likita, tace " Dr wata ta fadi."
Likitan ya kalleta yace "a ina ne?"
Nuna mai d'akintai suka shiga.
Khadija na kwance, ya shiga da sauri inda take ya gyara ta zuwa rigingine.
Ya dade a kanta kafin ta farfado, kallan sa kawai takeyi, tana kuma bin d'akin da kallo.
Mairo na zaune ta baza tagumi Magajiya ta shigo.
Kallanta tai tace " ke kuma fa?"
Mairo tace " Khadija......."
Fita!
Abinda kawai tace mata kenan tare da nuna mata hanyar kofa.
Mairo ta kalli Abdulmajid wanda ke kwance idanunsa a rufe, kawai tai waje duk tsiwar mutum kwarjinin Magajiya daban ne.
Gidan Sarki kawai ta wuce, ga yamma tayi.
***********
'yan kawo Amarya kam sun sha hidima, dan ba shakka an musu tarba sosai, sai yamma suma sukai ma Bilkisu sallama suka kama hanyarsu.
Mairo ta iso sai dai bata samu ko ganin Turab ba dan yana cikin mutane, umma kuma tana ta fama da mutane, balle dama batama san me zatacema Basira ba.
Turab kam bai samu ya shigo ba sai bayan isha'i, shima tare yake da 'yan rakiya, yasha kwalliya sosai.
Bangaren Umma kawai lekowa yai ya mika kaya ya wuce, Mairo tana sallar isha'i ya shigo, tana idarwa ta tambaya akace ai ya tafi bangarensa.
Haka tai sallama da Umma ta fito dan tasan in aka rakashi shida fitowa sai gobe.
Gimbiya na zaune a d'aki, tasha had'adiyar alkyabbarta kayan jikinta masu tayi kyau sosai da sosai, sai dai an saka hular alkyabbar sannan an kawo mayafi an rufe fuskarta.
Jeren da aka mata kuwa, ko ban fadaba kowa yasan an kashe kudi dan ma dai lokacin ba kamar yanzu bane da kudinmu bashida daraja.
Da masu kula da ita wanda daga can kano aka raho mata dasu guda biyu saboda rashin sabo da batai da na nan ba.
Su Sabi'u manyan yan tsokana, haka sukai ta tsokanar shi kafin daga baya su bada kudin siyan baki, wanda rashin kawaye yasa sai ajiyewa sukai anan, da yake haka ta taso ba kawa sannan cikin maza ta taso bare tai abokantaka da yayunta, haka suka fita suka bar Ango da Amaryar sa.
Turab ne ya zauna kusa da ita sannan ya yaye mata mayafin dake yafe a fuskarta sannan ya kalleta yace " Gimbiya Bilkisu barkanki da shigowa gidan auranki, barkanki da sauka cikin wannan gida."
D'agowa tai ta kalleshi sannan ta maida kanta kasa, rabonshi da ita ya dade, haka itama, ba shakka yayi mamakin tsananin kyan da ta kara, itama a ranta taga yayi kyau sai dai kallo d'aya datamai ta ga ya fada.
A hankali tace "Barkanka dai Yarima Turab."
Murmushi yai yace "kinyi sallar isha'i?"
Tace " a'a."
Yace " ki tashi kiyi alwala sai muyi tare."
Kanta ta sunkuyar tana wasa da hannunta wanda yasha lale.
Jikinsa ne ya bashi da alama bata salla, sai yace " bari nai sallah ni tukunna, ga abinci nan ki fara ci."
Ya fada tare da shiga ban d'aki, sai dayai sallah yai shafa'i da wuturi sannan ya dawo inda take.
Ledar na gabanta sai dai ko bud'ewa batai ba.
Zama yai yace " Tunanin gida?"
Kallansa tai tace " kawai inajin abin ne kamar wasa."
Ledar ya bud'e tare da ciro ledar naman ya sauka kasa kan karamib carpet din tsakar d'akin ya zauna, sannan ya ciro ledar juice masu sanyi ya ajiye.
Alama ya mata da hannu akan ta sauko ta zauna, ya fada yana nuna mata kusa dashi kadan.
Murmushi tai sannan ta sauko ya tura mata gabanta sannan ya mike ya d'auko cup ya tsiyaya mata juice d'in yace " Bismillah."
Kallansa tai tace "banajin yunwa, ni kai naga ma kamar kaine bakaci abinci ba."
Fuskarsa ya taba yace " na rame ko?bayan amare aka sani da rama."
Tace " ka rame mana, badai matsalar bace har yanzu bata warware ba?"
Iska ya furzar yace " Abin ai ba karami bane."
Tace " Da alama an tsorataka?"
Dariya yai wanda harsaida hakwaransa suka fito yace " Tsoro? kuma fa kin fadi gaskiya an tsoratani."
Tace " an ba da ni."
Yace " ahh ya zakiyi yanzu? Gashi na riga na kwaceki bare a kasa ni?"
Kanta ta sunkuyar tace " Ni dai nace an badani, banaji ni akwai abinda zai tsorata ni."
Yace " hmm a hakan? Ke har zaki iya wani abun ma? Ni da na d'auka zan taddake irin ba wasan nan sai naganki mai saukin kai."
Wayau yake mata yaga inyana sata magana tana kara sakar jikinta dan gashi yanzu har naman ta fara dan ci.
Kallansa tai tace " a haka ne ka ganni mai sauki, amma in na rikid'e? Hmm ba wasa."
Ohhhh kice akwai wadi side ban sani ba, ko za'a gwadamin?
Murmushi tai tare da yin kasa da kai tace " Ka fadamin wanene yake baka matsala kaga abinda zan iya yi."
Yace " kice sai dai in koma baya in kallo?"
Tace " Magajiya ce?"
Kallan mamaki ya mata yace " me kika gani?"
Murmushi tai tace " Ka manta a inda na taso ne? Na kuma san d'anta taso ta had'a dani, sannan d'anta takesan tasa a kan mulki."
Turab yace " hmm lalai, na sha mamaki."
Kallansa tai sannan ta sunkuyar da kai tare da zare hannunta daga ledar, ya tabbata gida ta tuno, matsowa yai ya jawo ta jikinsa ya rungume ta tsam.
Yana shafa bayanta a hankali alamar lalashi, yace " i will try my best not to make u lonely, sannan ban manta da alkawarina dana miki ba, bazan nemi wani abu ba a tsakaninmu harsai na kammala abinda ke gabana, a lokacin ne zan nemi yardar na zamantakewa, a lokacin ne zaki yanke hukunci in zaki iya zama dani."
Luf tai a jikinsa, sun dade a haka kafin ya d'agota a hankali sannan ya shiga bata naman da kansa.
Da kunya ta ke amsa sai dai wata shakuwa na kara shiga tsakaninsu a hankali.
Yanajinta kamar kawarsa dan abinda zai gaya mata bayaji akwai wanda yake iya fadawa kai tsaye, bai san me yasa yakejin yardarta har zuciyarsa ba........
***********
*TURAB*
************
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*76*
Washegari.
Da asuba ya farka a kan kasan carpet din daya kwanta, salati yai sannan ya mike tare da kallan kan gadon da Gimbiya ke kwance, karasawa yai inda take ya gyara mata bargon data luluba dashi, sannan ya juya zai fita.
Jiyai ta kamo hannunsa, juyowa yai ya kalleta yace " idanki biyu?"
A hankali ta bud'e idanunta tace " yanzu dai na farka? Masallaci?"
Yace " eh, sai na dawo."
Sakeshi tai sannan tace " adawo lafiya."
Murmushi yai sannan ya juya yai gaba.
Alwala yai sannan ya fita, sun idar da sallah ya fito, jiyai ance " Yarima Turab!"
Yanda aka kirashi cikin rad'a yasa ya juya ba tare da ya amsa ba dan ganin me kiran.
Daga lungu ya hangoshi a tsaye jikin bango.
Turab ya karasa sannan ya kalleshi cikin mamaki yace " Waziri lafiya?"
Hisham ya kalleshi duk ya canza yace " Kaga Khadija?"
Turab yace " bangane naga khadija ba? Wannan wace irin tambaya ce?"
Hisham a rikice yace " Turab?"
Ya fada tare da riko hannayensa yace " ka taimakeni dan Allah bansan inda Khadija tai ba, tun jiya nake nemanta wlh ko barcin arziki ban samu ba."
Turab kallan mamaku yake masa yace " Ni fa nakasa fahimtarka, b'ata tai ko me?"
Hisham yace " da kanta ta tafi, sai dai bansan inda tai ba."
Turab ya kwace hannunsa yace " da kanta ta tafi? Kuma ko kunya kazo kana tambaya ta?"
Hisham yace " Turab na rasa inda zansa kaina, in ta fada hannun mutanen banza fa?"
"wannan damuwarka ce ba tawa ba, kaine ka lalata mata rayuwa ko menene ya sameta, sannan karkaga kaine ka haifesu kayi tunanin duk wani abu da ka aikata musu ba laifi bane, haifarsu kai ba hallitarsu kai ba."
Ya juya yai gaba.
Hisham idanunsa suka ciciko dan shikam yana cikin garari.
Turab tafiya kawai yake sai dai abin zirya yake tamai a zuciyarsa, ina taje? Menene kuma dalilin tafiyarta?"
Har yaje zai shiga bangarensu sai kuma ya juya, Garzali ya kira suka wuce asibiti.
Abdulmajid na kwance yana bacci, sai wata baiwa da Magajiya ta sata zama a gunsa, d'ayan gadon ya kalla wanda da ba kowa, amma yanzu yaga Khadija kwance.
Mamaki ya kamashi yaje kusa da ita, sannan ya dawo inda Abdulmajid yake yad'an tabashi.
Sannan yace " d'an tashi."
Abdulmajid bai bud'e ido ba sai dai yana jinsa.
Turab ya kalli wannan mai kula da su din da aka bari yace " bamu guri ko?"
Tace " to ranka ya dade." tai waje
Turab ya kalli Abdulmajid yace " magana zamuyi."
Abdulmajid a hankali ya bud'e idanunsa ya kalli Turab.
Turab ya zauna kusa dashi yace " ya jikin naka?"
Baice komai ba sai dai ya kawar dakansa.
Turab cikin wata irin murya yace " Nagode Abdulmajid."
Cikin tsananin mamaki Abdulmajid ya kalleshi, sannan yace " karkamin godiya dan ba saboda kai nai ba."
Turab yai murmushi yace " saboda ba saboda ni kai ba shi yasa nake ma godiya."
Abdulmajid yace " mene?"
Turab ya ce " Mu bar wannan maganar, me ya samu Khadija?"
"kana tunanin zan fadama?"
Turab yace " sosai, dan duk duniya yanzu ni kadai ne zaka iya fadama wannan sirin naka."
Wata dariya yai yace " bakai tunanin na gwammace na had'iye matsala ta ba?"
Turab yace " wannan tsarinka ne, zaka iya yadda zakuma ka iya kin yadda, sai dai in har kanaso ka ceto rayuwar mutanen dake kewaye dakai dolene mu had'a kai."
Abdulmajid ya kalleshi sai dai baice komai ba, Turab ya cigaba " haka zakabar matar da ta rikeka ta cigaba da tafka laifufuka? Haka zaka bar mahaifin daya haifeka ya cigaba da aiwatar da laifufuka? Ko kuwa rayuwar kanwarka dake neman tarwatsewa?"
Abdulmajid ya juya kai idanunsa suka ciciko, Turab yace " tunda ka zabi yin shiru, ni zan aiwatar da abinda naga shine daidai."
Ya mike zai fita, Abdulmajid a hankali yace " inajin kunyar hada idanu dakai, bansan abinda iyaye na suka aikata maka ba kenan, duk abinda sukai how can i face u?"
Turab ya juyo ya dawo kusa dashi ya zauna sannan ya kalleshi yace " bazance kaima bakada laifi ba dan kaima kayi abubuwa marasa kyau a baya, sai dai yanzu kana biyan laifin daka aitaka." ya fada tare da kallan kafarsa wacce ba hope din zata mike.
Turab ya cigaba " dole ne ka cire tsoron Magajiya in har kanasan ka taimaketa, kaine kadai wanda inka juya mata baya zataji gaba d'aya duniyar ta mata zafi domin dakai ta dogara sannan saboda kaine take ganin komai zatai ba zai zamar mata wani abu ba."
Abdulmajid ya share kwallarsa yace " haka ne, sai dai banaji ko ni Umma zata saurarawa, sannan Waziri ba tun yanzu yake kisa a kaina ba, na kula duk abinda ke faruwa saboda ni ne...."
Ya kasa karasawa saboda wani kuka daya taho mai.
Turab wani tausayinsa ne ya kamashi, daurewa yai yace " yanzu ba lokacin kuka bane, inhar ka yadda kana da hakki akan laifufukan da suke aikata wa to dolene ka nuna musu kuskurensu gun aikata abinda auka aikata."
Abdulmajid yace " hakane, yanzu me zanyi?"
Turab ya kalli Khadija sannan yace " da farko kasa Waziri ya maida yarinyar nan kano."
Abdulmajid yace " Khadija?"
Turab yace "eh, zuciyarta mai rauni ce duk da tasan mahaifinta da kanwarsa sun tafka kuskure intaga ana wahalar dasu zuciyarta bazata d'auka ba."
Abdulmajid yace " haka ne, zansa gobe amaida ita."
Turab yace " sannan ka nuna ma kowa ka farfado."
Yace " sai me?"
Turab ya matso daf da kunnensa ya rad'a masa wani abu wanda duk yanda nakai kunnena gun banji me yace mai ba, sai da ya gama sannan na kalli Abdulmajid naga yana kallan Turab.
Turab yace " me? Bazaka iya ba?"
Kai ya girgiza yace " ko d'aya kawai dai ina mamaki ne wanda yanzu na fahimci komai, a da ina kishin ko mai na rayuwarka, daga yanda Abba ke sanka zuwa yanda kuke hira da Mahaifiyarka cikin kulawa, zuwa yanda Kanwata da Wacce nakeso ke sanka bani ba, sannan zuwa yanda mutanen fada ke girmamaka, saj dai yanzu na fahimci dalili."
Turab yace " menene dalilin?"
Abdulmajid yai murmushin yake sannan yace " zuciyarka itace dalili."
Turab ya kalleshi ya murmusa, Abdulmajid yace " yanzu me yasa ka yarda dani? Baka tunanin zanci amanarka tunda abu ne na mahaifana?"
Turab yace " ko kadan, saboda yanzu idanunka sun canza, a da ambition da kuma kishi nake gani karara a idanunka sai dai yanzu ina ganin tsantsan guilty da kuma dana sani a idanunka."
Abdulmajid yai kasa dakai.
Turab yace " u have to do it right, karka bari kwarjini da tsoron magajiya yasa ka kasa."
Abdulmajid ya d'aga kai yace " nagode Turab."
Turab ya kalleshi ya dafa shi sannan ya juya.
Kallan Khadija yai ya juya ya fita.
Abdulmajid ya bishi da kallo idanunsa na zubda kwalla.
*********
Magajiya yau cikin baccinta ta tashi yakai sau uku, kalaman Hisham ne ke mata yawo, da kuma Turab, yau kam ta tabbatar Turab yasan Abdulmajid ba d'anta bane.
Ana sallar asuba kuwa ta aika a kira mata Jakadiya.
Tun 6 take zaune tana jiranta sai dai ba labari, har wajen karfe 8 abin ya gama damunta ta mike a zuciye ta fito.
Karfe 7:30 kuwa Turab ya iso gidan, yana sauka a mota Jakadiya ta taho da sauri.
Kallanta yai yace " Jakadiya lafiya?"
Jakadiya a rikice tace " Yarima tun dazu nake jiranka, Magajita ce ta aiko naje."
Turab yai murmushi yace " ai na d'auka tun jiya ta kiraki, ashe zata iya bari sai yau?"
Jakadiya ta mai kallan mamaki tace " Bam gane ba?"
Turab ya kalleta yace " kije in ta kiraki sannan ki sanar da ita abinda kika sani."
Jakadiya tace " abinda na sani? Ban gane ba?"
Turab yace " ba kiranki nai nace zan hukuntaki ba? Ki sanar ita duk abinda ya faru."
Kallansa tai tace " amma baka ganin zata iya lahantani?"
Turab yace " in ta lahantaki ma tsakaninku ne, ai kema kinyi laifi bawai wannan ne kawai abinda kika aikata ba, banaji inada damuwa akan abinda zai faru tsakaninku."
Hankalin Jakadiya ya tashi da sauri ta tsungunna a gabansa tace " Ranka ya dade kasan Magajiya."
Turab yai murmushi yace " na sani, saninta da kuma saninki ne yasa na fadi haka, ki kwaci kanki tunda kema da wayanki kuma ba ta yau bace."
Ya juya yai gaba yana murmushi.
Bangarensa ya nufa, yana shiga ya wuce d'akinsu, sallama yai yaji shiru hakan ne yasa yai tunanin ko bata ciki ko bacci taje har a lokacin.
Kofar ya tura tare da shiga da sallama, yana shiga ita kuma tana fitowa daga band'aki d'aure da towel, wani kamshin dadi ne ke fitowa daga ban d'akin wanda hakan yasa nasan lalai anyi wanka da kayayaki masu kamshi.
Da sauri ta juya baya, baisan sanda idanunsa suka shiga kallanta ba tundaga kafarta har zuwa kanta ba, abinda da zuciya ga Bilkisu mace ce mai tsananin kyau da kira.
Juyowa tai ta kalleshi da sauri ta sake juyawa tace " Ba ka fita ba?"
Turab yai murmushi sannan ya tako a hankali har zuwa inda take daf da ita yazo zuciyarsa na rayamai abubuwa, ita kuwa gabanta ne ke faduwa dan ma tasan ba sallah take ba.
Harta runtse idanunta tana tunanin zatajishi kusa da ita ko wani abu.
Toilet ya shiga sannan yace " A shirya lafiya."
Ya karasa maganar tare da tura kofar.
Kallan kofar tai sannan ta saki wani ajiyar zuciya kafin tai wata yar siririyar dariya.
Turab shima yana rufe kofar ya saki wani ajiyar zuciya, yana mamakin me ke damunsa? Bayan bai tabajin haka ba,yaji wai zuciyarsa na kwadaitamasa taba mace?
*********
*TURAB*
**********
.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*77*
Tana shiga kilisarta Magajiya dake zaune ta mike tsaye sannan tace " biyoni.
Sai da suka shiga cikin d'akinta Magajiya ta zauna akan kujerarta sannan tama Jakadiya alama da hannu akan ta matso inda take.
Jakadiya ta karasa gun ta zauna sannan tace " Barkanki da Safiya...."
Magajiya ta kalleta tace " Me kuka kulla ke da Turab?"
Gabanta ne ya fad'i tace " ban fahimt......"
Kinaso in sake maimaitawa?
Jakadiya tace "Ai ban fahimceki bane Magajiya."
Magajiya tace " ba sai kin fahimceni ba, sannan nayi kuskure ma dana tambayeki, abinda ya dace shine ki jira kiga yanda wanda ya ci amanata yake kasancewa, dan wlh sai na baki mamaki."
Jakadiya tai kasa dakai tare da fashewa da wani irin kuka tace " Magajiya ni na isa naci amanarki?bansan komai a abinda kike fadaba, ni dama wata magana nazo sanar dake banyi tunanin neman da kikemin da biyo kike min ba."
Magajiya ta kalleta tace " magana?"
Jakadiya ta juya ta kalli kofa sannan tace " naji wani abu wanda ya tsoratani."
Magajiya ta kalli kwayar idanunta.
Jakadiya ta dan had'iyi yawo tace " Jinai Abu Turab yana magana wacce ta tsoratani tsantsa, ta yaya akai kika bari yaran nan yasan sirrin nan namu?"
Magajiya ta kalleta tace " me kike nufi?"
Jakadiya ta matso tace " Jinai yana cema Basira wai Abdulmajid d'an Waziri ne, wannan labarin ya tadamin hankali tsantsa, ta ina yaji? Garin kuma yaya?sirrin da mukai alkawarin rikeshi har bayan ranmu?"
Magajiya jitai hannunta na rawa, ta daure ta kalli Jakadiya tace " bani guri."
Nan Jakadiya tai wuf tai waje kai kace dama jira take ace ta fita.
Tana fita Magajiya ta dafa kanta, tabbas yasan sirrin nan, garin yaya? Dolene ta b'olo da hanyar da zatasa ya kasa fadan komai, amma Basira ta sani ai, tabbas sai tayi dogon nazari.
**********
Sai daya cire kaya ya gama wankan sannan ya tuna ba towel a cikin toilet din.
Tsayawa yai, yai shiru yana tunanin mafita.
Ita kuwa Bilkisu ta shirya tsaf cikin wani had'ad'en leshi mai kyau, peach colour tayi kyau sosai, tana kokarin kame kanta da ribbon ne taji alamar kwankwasa kofa, kallan band'akin
tai tana mamaki, sannan ta mike tazo kusa da toilet din tace " Daga nan ne?"
Turab yai gyaran murya, tace " wani abu kake so?"
Iska ya furzar sannan a ransa yace sai ince bani towel?
Itace ta katseshi da cewa " Yarima?"
Turab yace " towel zaki d'an bani."
Idanu ta zaro sannan tace " to."
BJuyawa tai ta d'auko sabon towel ta kwamkwasa a hankali ya d'an bud'e kofar tare da zuro hannu, ita kuma ta juya kanta tana ta mikamai, yana kokarin kamo towel ya kamo hannunta, shiru ne ya biyu baya batare da ya sake ta ba, a hankali ya shafa zuwa kasan hannunta ya ja towel din.
Itakam gaba d'aya jikinta yayi sanyi tanaji ya turo kofar band'akin ya rufe.
Juyowa tai ta kalli toilet din sannan ta murmusa.
Turab kam shima a ciki yana rufewa yai murmushi sannan ya sa towel din, tana jin alamun zai fito ta fita falo.
Sai da ya shirya tsaf sannan ya fito falon, tana zaune kan kujera, kasan carpet din an jera musu kayan abinci kala kala, kamshin turarensa ne yasa tasan ya fito.
A hankali ta lumshe idanunta.
Kallanta yai yace " Amarya kin tashi lafiya?"
Murmushi tai tace " ina kwana? Kaga ka sa ban gaisheka ba sai daka fara tambaya ta ya na tashi?"
Yace " daga masallaci na biya wani guri ne."
Tace " ayya! Kaci abincin sai muje gaisuwa."
Gaisuwa?
Tace " eh, zaka kaini in gaida matan Sarki."
Yace " ohh lalai, to sauka muci abincin."
Tace "nasha madarar shanu ni sai anjima zanci."
Bai ce komai ba ya zauna a kasan carpet din, yana kokarin bud'e kula ta sauko tare da d'aukan plate ta zuba mai.
Kallanta yai fuskarsa d'auke da murmushi yace " masu aiki nawa kikeso a turo nan bangaren?"
Tace " amin uzuri da masu aikin nan, tun ina karama komai sai dai amin banasan a gidan mijina ya zamana komai sai dai amin, ni ba abinci na iya ba ba shara na iya ba balle wanke wanke, banaso akawo mutanen da zasusa ya zamana kula da kaina da mijina sai dai amin."
Kallanta yai cikin jin dadi yace " Kina tunanin zaki iya?"
Tace "ummm"
Yace " shikenan zan sanar ma Umma."
Ya gama cin abinci sannan suka nufi bangaren Matar sarki ta biyu, sai da suka gaisa sannan sukaje gun ta uku, duk inda sukaje sai kowa yai mamakin tsananin kyau irin na Gimbiya, sannan suka nufi bangaren Magajiya.
Tasa an had'a abincin sha da kayan marmari an jera a falon ta dan dama tasan da zuwansu, taci kwalliya na gani na fada kai kace wani had'ad'en taro zata hallarta.
Sai da suka zauna sannan ta fito cikin isa da izzarta.
Gimbiya tayi zama irin na 'ya'yan mulki a gaban iyayensu Kanta na kasa ta shigo.
Magajiya ta zauna tare da kallansu, Turab yace "Umma Magajiya Barka da Safiya."
Tace " Ango na d'auka zaka bari sai zuwa jibi, irin wannan wahalar da amarya haka?"
Ta fada tana kallan Bilkisu.
A hankali ta d'ago ta kalli Magajiya, idanunsu ne suka had'u, Bilkisu ta sakar mata wani sansanyan murmushi tace " Barka da Safiya."
Magajiya idanunta na kanta tace " Amarya barka da shigowa masarautar Zazzau, dafatan zaki samu kwanciyar hankali kamar yanda kike samu a can."
Tace " Karki damu indai farin ciki ne Umma dan na tabbata d'anki zai kula da ni sosai."
Ta rasa meyasa taji zafin kalamanta, bayan ba wani abun ta fada ba, amma me yasa takeji kamar magana ta fada mata?
Daurewa tai tace " Haka akeso, ai Turab yaro ne na gari."
Bilkisu tace "Godiya muke, dan yabonki yana nuna hakan take a gun al'uma."
Magajiya ta kara kallanta, me yasa yanzuma taji maganar ta bata mata rai?
Turab kam murmushi yai yace " na d'auka kina gun Abdulmajid."
Tace " dama ku nake jira mu gaisa sai in fita."
Yace " ohh amma da sai naji kamar kince da mun bari sai nan da kwana uku."
Ta kalli Bilkisu tace " hmm ai da dai ka barta ta huta d'in."
Bilkisu tace "godiya nake da kulawa, amma Umma duk wani hakkina ina ganin gwara nayishi lokacin daya dace."
Tace "haka ne."
Turab kallan Magajiya yake yana mamakin yanda take amsawa Bilkisu duk da dai yasan da bakunta amma yasan dukda haka wannan ba style dinta bane.
Basu wani dade ba suka fito, har ya kai falo tace " Turab."
Dawowa yai ya shigo d'akin, kallansa tai tace "Magana nakesan muyi."
Yace " banaji akwai wata magana data rage a tsakaninmu a wannan lokacin, sannan asibiti nakeso na tafi dan kuwa naji labarin Abdulmajid ya farfado inada bukatar jin wanene a kuma garin ya ya aka aikata mai hakan."
Magajiya zatai magana yai gaba.
Yana fita ta mike tare da matse hannayenta, Abdulmajid?
Yana fita itama ta mike ta sanar da masu kula da ita akan zuwa asibiti.
********
Hisham ya gama galabaita gaba d'aya ya wuce asibiti dan ganin Abdulmajid da jikinsa, yana zuwa ya tadda khadija a zaune ta had'a gwiwarta da kanta a kan sallaya.
Yana shiga ya tafi da sauri inda take ya rike hannayenta ya d'agota yace " Khadija!"
D'agowa tai sannan ta kura mai idanunta da suka kumbura, wanda har fuskarta itama ta kumbura.
Muryar Abdulmajid yaji yace " Khadija zaki iya komawa gida da kanki?"
Kallansa tai batace komai ba, yace " kije gida ki jira Waziri, ko kuma kije waje ki jirashi yazo kuje gida, magana zamuyi."
Mikewa tai kamar wacce ba tada laka a jiki tai waje ko kara kallan Mahaifinta batai ba.
Tana fita Hisham ya matso yace " Abdulmajid yaushe ta dawo....?"
"Ba wannan bane abinda yasa nace zamuyi magana, tambayarka nakesanyi."
Hisham ya kalleshi gabansa na faduwa.
Abdulmajid yace " menene tsakanina dakai?"
Hisham ya had'iyi yawo yace " naam?"
Abdulmajid yace " ni d'anka ne?"
Hisham kallansa kawai yake dan bashida amsar da zai bashi.
Abdulmajid yace " inaso daga rana irinta yau ka cire batun nan a ranka dan bazanci amanar Umma ba, ban damu da wanene ya haifeni ba wacce ta raineni itace Uwa a gareni, akan Umma zan iya juya ma baya zan kuma iya tozartaka, kaine ka d'aukeni ka bata dan haka babu damuwata akan duk wani abu da zai shafeka."
Hisham bai taba tunanin abinda zaiji daga gareshi ba kenan, yace " Abdulmajid kanaso kace ni dana haifeka banida matsayi a gunka?"
Yace " matsayi? Kai kasan wannan, sannan ka gaggauta maida Khadija kano inhar kanasan rayuwarta ta daidaita, sannan in har kanaso in d'inga ganin kimarka da darajarka a matsayin wanda ya haifeni ti ka tabbatar ka fita hanyar Umma ta, sannan ko da wasa naji labarin ka aikata abu irin kwatankwacin abinda ka min banaji zan iya yafe maka."
Hisham da sauri ya d'ago ya kalleshi yace " naji bazan aikata ba ko kadan amma laifin dana aikata a baya fa?"
Abdulmajid ya ce " au akwai abinda ka aikata irin wannan a baya? To a wannan d'akin inaso ku warware a lakar dake tsakaninmu."
Hisham ya matso da sauri yace " Abdulmajid kayi hakuri wlh....."
Idanu ya runtse sannan yace " naji amma kada ka kuskura abinda ka aikata ya fito fili dan bazan iya kallan mutane ba in har abinda ka aikata ya fito fili, ciki kuwa harda abinda kamin."
Hisham da sauri yace " naji, naji."
Abdulmajid yace "kaje gun Khadija, ba dadi take ji ba."
Nan yai waje.
Yana fita ya kalli kofa sannan yai ajiyar zuciya, yace " anya Turab wannan hanyar zata bule?"
Tunowa yai da kadan daga cikin kalaman Turab dayace " ka tabbatar ka nunama Waziri kai a bayan Magajiya kake sannan ka nuna masa in har ya amsa laifinsa to lalai kai dashi har abada........"
Tunowa da ragowar kalaman yai a ransa sannan yace a fili " Turab kenan, wato in Waziri ya ki amincewa da laifinsa sannan ya fahimci ni a bayan Magajiya nake lokacin ne kishi zai afko a tsakani, ita zataji haushin kin amsa laifinsa wanda za'ai ta bincike gun gano gaskiya, sannan shi kuma zaiji takaicin bijerewata zuwa gun magajiya, idan ya raba tsakaninsu sai ya sani nasa Umma ta fadi laifukanta da kanta cikin ruwan sanyi ba tare da tasan abinda takeyi ba, saboda yardarta gareni ganin na ki mahaifina saboda mulki............"
Murmushi yake yai ganin ya fara hada kan puzzle din da Turab ya bashi, a fili yace " daidai nake aikatawa??????"
Nikam da sauri nace " Kwarai😄😂"
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*78*
Hankalin Hisham yayi tsananin tashi yana fita jiyai jiri na neman d'aukansa sai daya dafa bango.
Daga nesa ya hango Khadija a zaune a jikin bango tana bin mutane da kallo, tsananin tausayinta ne ya kara ratsashi, shi dai bai ga ranar da wannan buri nasa ya masa ba, ina amfani gaba d'aya ya tarwatsa rayuwar 'ya'yansa?
Kusa da ita yaje yace "Khadija "
Kallansa tai sai dai ba magana, yace " tashi muje."
Mikewa tajeyi da yake batada karfi tai kamar zata fadi, da sauri yasa hannu ya rikota yace "yi a hankali."
Hannunta ta fizge sannan tai gaba.
Kallabta yai jiki a sanyaye suka shiga mota, ya ja sukai gida.
Har suka isa ba wanda yai magana a cikin motar, tana shiga gida ta wuce d'aki ta sauko da akwatinta ta shiga had'a kayanta.
Umma ce ta shigo cikin kulawa tace "Khadija ya jikin Yari......"
Ganin tana had'a kaya yasa maganarta ta tsaya, kallanta tai tace " Khadija me kenan?"
D'agowa tai ta kalleta sai dai bazata iya cewa komai ba dan ta tabbata tana magana kuka ne zai zo mata, kurama Umma ido tai a ranta tace " me yasa kikai haka Umma? Me yasa baki hana Abba aikata munanan aiyukan nan ba?"
Kallanta Umma tai tace " Khadija lafiya?"
Khadija ta maida kanta kan kayan ta cigaba da shiryawa, ganin batada niyyar magana yasa ta fito.
Hisham ta tarar a d'aki ya baza uban tagumi, ko sallamar da tai bai amsa ba, tace " Baban Khadija me ke faruwa?"
Kallanta yai shima sororo, tace " ba shiru zakai ba me ke faruwa naga Khadija duk ta canza sannan tana ta faman hada kaya? Sannan ni bakacemin komai game da ciwon Yarima ba kadai cemib kawai bayajin dadi ne......"
Ya isheni haka nan, ki barni da abinda ke damuna dan Allah, haba! Kinsan ya nakeji a zuciyata a wannan lokacin? Komai na neman rugujewa a rayuwata, d'an da nake tunkaho zai ramamin rashin mutunci da cin zarafin da Magajiya tamib yanzu ya rikide yace shi ba wani abu tsakanina dashi, itace uwarsa, sannan Khadija ko kallona basan yi take ba ke kuma zakizo ki sani a gaba kamar wanda ya amshi bashinki?"
Umma tace " ban gane me kake nuf......"
"ba sai kin gane ba, dama ina kanki zai yi aiki? Kwakwalwace dama kamar ta kifi?"
Umma ta juya jiki a sanyaye tai waje, dakin Khadija ta koma ta tsaya kawai tana kallan ikon Allah.
Khadija kam dama tun jiya idanunta biyu taji sanda Turab yace ta koma kano, sannan dama itama bataji zata iya cigaba da zama a wannan garin, Umma ta kalla tanasan mata magana sai dai ta kasa.
Umma idanunta duk sun ciko dan itakam kalaman Hisham sun kona mata rai, inda sabi yaci ace ta saba amma duk sanda ya mata sai ta dingajin ba dadi.
Hanyar band'aki ta nufa bayan ta dau zanin wanka, ta daure tace " kano zan koma."
Ta shige ban d'akin, kallan kofar Umma tai jiki a sanyaye sannan ta mike hartaje zata shiga d'akinsu kuma ta fasa saboda takaici, juyawa tai ta koma d'akin khadija ta zauna.
**********
A bangaren Basira kuwa su Gimbiya anata kunyar suruka, Umma sosai ta yaba da hankalinta, nan tasa aka kawo mata abincin safe jin Turab yace bataci abinci ba, duk da bataso ci ba sai da Umma tasata taci, sun dade kafin Garzali ya turo a sanar da Turab akan zata fita.
Abinda kawai aka ce kenan shiyasa Basira bata fahimcesu ba, Gimbiya kuwa kallansa tai sai dai bata tambayeshi ba, ya kalleta yace " in barki anan ko in maidake can kafin in dawo?"
Tace " ina nan."
Yace " ok, ba dadewa zanyi ba."
Umma ta kallesu tai murmushin jin dadi.
Turab ya juya ya fita, Garzali ya tarar a waje yace " ta fito?"
Yace " yanzun nan."
Turab yace " muje, ka tura a sanar mai?"
Garzali yace " eh Ranka ya dade."
Mota suka shiga suka tafi asibitin, suna kallan motarta daga gaba su kuma suna baya, har suka isa.
Magajiya ta fito ta nufi d'akin da aka kwantar da Abdulmajid.
Turab yana kallanta ta shiga shikuma ya tsaya a bakin kofa.
Tana shiga aka ajiye kayayyakin data kawo, kallan danta tai cikin jin dadi ta matso tace " Abdulmajid? Idanunka biyu?"
Kallanta yai sai dai baice komai ba.
Magajiya ta zauna kusa dashi cikin jin dadi tace " na sani ai, nasan d'ana ta ina magajin sarki zai kwanta kamar bara numfashi?"
Abdulmajid ya murmusa yace " Umma kiyi hakuri na saki damuwa."
Kanta ta girgiza tace " wa ke wannan zancen? Ai farfad'owarka shine komai nawa."
Kallanta yai sannan yace " Umma kinsan Kawu yanada hannu akan abinda aka min?"
Idanu ta zaro sannan tasa hannu a kirji tace " mene?kanaso kace shiya ja maka wannan abun?"
Turab ya murmusa yace " GOOD JOB ABDUL"
Abdulmajid yai kasa dakai cikin rashin jin dadi, Magajiya tace " karka damu ba yayana ba ko Sarki ne ya kuskura ya tab'amin kai bazan taba yafemai ba."
Abdulmajid ya kalleta yace " na sani dama........"
Turo kofar da akai ne yasa shi yin shiru, Turab ne ya shigo tare da sallama.
Bata juyaba amma tanajin sallamarsa sai da gabanta ya fadi, me ya kawoshi?
Turab ya matso yana cewa "Umma ashe kin garzayo."
Juyowa tai ta kalleshi tace " Au Turab kaine?"
Yace "ni ne, kinsan dolene nazo duba Abdulmajid tunda ni aka je halakawa tsautsayi.........."
Katsesh tai da sauri cikin tsoro tace " ina amaryar? Badai barinta kai ba?"
Yace " ya zanyi? Dolece ta sani zuwa ai, naje gunki akan zamu gun Mai Martaba dan yin wata magana ashe ke kina nan?"
Idanunta ne suka fito, duk yanda taso b'oye tsoronta sai da ya nuna tace " ban gane ba?"
Turab ya matso yace " magana ce wacce ya dace ayi gani gaki ga Abdulmajid sannan ga Waziri."
A rikice ta d'ago ta kalleshi sannan ta kalli Abdulmajid tace "Turab wai kwanan nan meke damunka ne? Wuce muje gida mayi maganar a can."
Murmushi yai sannan yace " Bakyaso muyi a nan?"
Hararsa tai tace " muje ko?"
Ta na kokarin mikewa Zagi ya sanar da isowar Mai Martaba.
Kallan Turab tai dan tabbas tasan yasan da zuwansa, murmushi ya mata sannan ya d'an d'aga gira kadan ya juya kai.
Sarki ne ya fara shigowa bayansa kuma Waziri ne ya shigo.
Abdulmajid ya kalli Turab dan baisan me yake shirin aikatawa Ba.
Sarki ya nemi fadawa daau fita dan zai duba d'ansa.
Nan kowa yai waje, kallan Abdulmajid yai cikin tausayawa yace " Ya jikin naka?"
Abdulmajid ya dan sunkuyar dakai yace"Barka da war haka Takawa."
Kallansa sarki yai sannan ya kalli Turab wanda ya rusuna tare da gaidashi, Magajiya ma tace " Barkanka da war haka."
Sarki ya kalli Turab bayan ya zauna yace " me kakeyi anan kabar yar mutane ita kadai, ba kayi dubiyar ba?"
Yace " yanzu nake kokarin tafiya dama inasan zuwa gunka ne nida Umma."
Magajiya ta kalleshi sai dai kafin tai magana yace " Dama wani abu nake san......"
Katseshi magajiya tai da sauri tace "Ya kamata ka koma gida ko? Ba dadi ango daga aure ace yana waje."
Turab ya kalleta sannan ya kalli Hisham wanda yai tsuru tsuru yace " Magana ce akan Abdulmajid."
Yanda gaban Magajiya ya ke faduwa zata iya cewa wannan shine rana ta farko da takejin faduwar gaba haka ba kakkautawa dan tabbas tasan so yake ya sanar da tsakaninta da Abdulmajid......
Meye mafita?
Kafin kwakwalwarta tai aiki muryar Turab taji yace "Umma maganar da mukace zamuyi da Abba akan abinda ya samu Abdulmajid, ina ganin dolene ga Waziri anan wanda nake tunanin yafi kowa sanin abinda ke faruwa."
Wata irin ajiyar zuciya ta saki wanda sai da kowa ya kalleta.
Kallan Hisham tai sannan ta kalli Turab a ranta tace " tanan ka b'ulo?"
Hisham kam gaba d'aya ya rasa abinda ke mai dadi, ga Abdulmajid yace karya kuskura ya aminta akan shine sila.
Magajiya ta kalli Turab sannan ta kalli Sarki tace " haka ne Turab sai dai ina ganin abari yaji sauki tukunna kafin ai wannan maganar."
Turab ya kalleta yace " haka ne amma bakya tunanin kafin nan wanda ya aikata laifi ya kamata shima ya fuskanci, ba dai saboda zargin da akema yayanki bane yasa kike......"
Wani mugun murmushi tai tace " Kana tunanin in har Waziri nada hannu a ciki zan nemi birne laifinsa?"
Turab zaiyi magana sarki yace " ya isa haka, ina kuma tunanin tunda naji maganar na kuma sam mai ya faru yanzu dolene ayi bincike a fada, gunda alkalai suke."
Hisham! Kaine ka aikata?"
Hisham ya kalli Abdulmajid sannan ya kalli Magajiya tunowa yai da Khadija wacce ta fito da akwatinta a gida tana jira ta tafi aka aiko yazo shine yace ta jira ya dawo.
Ina zai sa kansa?
Magajiya tsoro take kar magana ta shiga fada dan tabbas in ta shiga daga bincike sai ance meye dalilinsa na aikata hakan, daga nan kuma tana tsoron kalaman da zasu fito daga bakin Hisham in yaji ana tsananta bincike a kansa.
***********
Turab ne ya kalli Magajiya wacce fuskarta yau ta bayyana da shakka karara, murmushi taga ya sakar mata a ransa yace " are u scared?"
"In kika tsorata tun yanzu the game will not be fun."
Idanun Turab kawai take kallo..........
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*79*
Mikewa tai tace " Turab me yasa kuke san bud'e abu cikin bainar jama'a? Me zai hana........"ganin irin kallan da Turab, Sarki da Abdulmajid suke mata ne yasa ta fahimci tana neman kauce hanya, daurewa tai sannan tai wani murmushi tare da komawa ta zauna tace " Yaya! Abu d'aya zan tambayeka kafin in cigaba da magana, da gaske kaine ka nemi halaka Abdulmajid?"
Hisham ya kalleta cikin mamaki dan shi gaba d'aya ya rasa ma mai zaice, Abdulmajid ya kalla wanda shima kallanaa yakeyi.
Turab ya kallesu sannan yace " Abba da alama ya kamata kaba Umma lawyer cikin gida."
Kallansa tai tace " mene?"
Turab yai dan dariya yace " menene na tada hankali Umma? Naga kamar kina neman d'aurama Waziri laifin da ba lalai shine ya aikata ba."
Bakinta ta dan motsa sannan tace " me kakeso kace a takaice?"
Sarki ya kalleshi sannan ya kalli Hisham yace " Waziri!"
Hisham ya rusuna da sauri, takawa yana kallansa yace " me zaka iya cewa game da abinda ke faruwa a d'akin nan?"
Hisham yai kasa dakai cikin tashin hankali, Sarki yace " jeka jirani a fada in har bakada abin cewa anan, to lalai zaka samu abin cewa a can, saboda dolene ka sanar damu dalilin dayasa ake zarginka."
Hisham yace "Tuba nake ranka ya dade amma ni kaina bansan dalilin dayasa akemin wannan zargin ba."
Turab yace " gaskiya ne, nima kaina ban fahimci me yasa ake ma wannan zargin ba, me ka aikata takamaima? Shi yasa nake ganin gwara aje fada yanda za'a tabbatar da zargin da akema ba gaskiya bane."
Abdulmajid yace " Haka ne, nima ina tunanin hakan yafi Umma."
Magajiya ta kalleshi gabanta na faduwa sai dai jin wata dabara ta fad'o mata yasa ta murmusa tace " hakan yayi, sai yaushe yanzu za'ai zaman?"
Turab ya kalleta, kamar wanda ya shiga ranta sai jitai yace " Abba gani nake yanzu in har ba abinda zakai gwara ai shari'ar nan yanzu, in ba haka ba shi kansa Waziri banaji zai samu kwanciyar hankali."
Takawa yai gyaran murya sannan yace " hakan yayi, ina neman Waziri da Turab a fada nan da minti talatin."
Abdulmajid yace "Abba nima ina neman alfarma dan hallarta."
Sarki ya kalleshi yace " karka damu, kai dai ka kula da kanka."
Abdulmajid kasa yai da kai dan shi kam yafisan yasan kome ke faruwa a idanunsa.
Turab ya fahimci haka sai yace " Abba zaman asibiti ba dadi mai zai hana mu nemi sallama, in yaso saboda kafarsa sai a dinga turashi a kujera?"
Sarki yace " a'a ku barshi anan dan samun lafiyarsa."
Magajiya kam kamar wanda aka nausa a ciki haka taji ta, tsananin tashin hankalin data shiga, dolene a cikin minti talatin d'in nan tai tunanin abinda zata tsarama Hisham dan fad'a a fada dan in batai da gaske ba lalai asirinta zai tuno, ita tsoronta ma wannan munafikin yaran dazai kasance a gun.
Sarki ne ya mike sannan yai waje.
Yana fita Turab ya mike shima yai waje dan ya tabbatar Magajiya tana bukatar kadaicewa da yayanta.
Abdulmajid ta kalla sannan tace " Abdulmajid bari in raka Yaya tunda fada zai wuce."
Kai kawai ya d'aga.
Suna fita ta mai alama daya biyota, sai da sukai tafiya sosai gun da ba mutane sosai, yau ko tafiyar kasaitar ma batai ba, suna shiga gun daba mutane ta juyo tace "Yaya ya zamuyi?"
Hisham yace "game da me kenan?"
Tace " ina tsoron kar muje akwai wata shaida da wannan yaran yake dashi na kana da hannu akai, dan yanda yake magana na tabbata akwai wani abu a kasa."
Hisham ya kalleta yace "ni ba wannan ne a gabana ba Khadija na gida tana jirana."
Kallansa tai tace " Waziri!"
Kallanta yai dan yanda ta kira sunan alamace ta ranta ya baci, Magajiya ta had'e rai tace " me kake san kace? Ba damuwarka bane ko me ya faru?"
Ya kalleta yace " ba haka nake nu......"
Tace " ko ma menene ba damuwa ta bace, abu d'aya na sani idan har ka kuskura ka bari sunana ko alamun sunana ya fito daga cikin wannan abu to ba shakka zan iya yada kai, kafi kowa sanin wacece ni, akan kaina ba abinda bazan iya aikatawa ba."
Ta juya ta fara tafiya, idanu ya runtse dan yama rasa ya zaiyi, da girmansa da komai amma yana cikin halin tsoro na jin kunyar duniya, juyowa tai ta kalleshi tace " ahhhh na manta ka kiyayi bakinka tun kafin 'ya'yanka susan kisan kan daka aikata."
Ta juya tai gaba.
Hannayensa yasa ya shafi fuskarsa sannan ya kalli sama, a hankali ya juya yai waje.
Gida ya nufa.
Khadija na kwance akan gado kalaman da taji tsakanin Magajiya da Hisham ne suke mata yawo a kwakwalwar, kalaman da bata taba jin mugayen kalamai irinsu ba, filo tasaka ta rufe kanta wasu zafaffan hawayene suka shiga zubo mata.
Mahaifiyarta ce ta shigo ta kalleta, jikinta ne yai mugun sanyi ta karasa gunta tare da d'aga filon, Khadija ta gani tana hawaye hannunta ta rike tare da cewa tashi khadija.
Khadija ta mike a hankali ta zauna, hannu tasa kan goshinta saboda taji zafi sosai sanda ta rike hannunta.
Jin yanda kanta ya d'au zafi yasa ta kalleta tace " Khadija meke damunki? Meke damunki da kike san tafiya ki bar mahaifanki?"
Khadija a hankali ta kwantar da kanta kan cinyar mahaifiyarta wasu zafaffan hawayene suka zubo mata a hankali tace " Umma mecece rayuwar nan? Me cece a ciki da har mutane ke jefa kansu akan san zuciya wacce ba komai bane a ciki sai tsantsar buri da halaka dake cikinta?"
Umma ta kalleta tace " Haka rayuwar ta maidamu Khadija, ni kaina ina dana sanin abinda zuciya ta sani na aikata, a koda yaushe ina takaicin abinda na aikata."
Khadija ta d'ago ta kalleta tace " Umma!"
Kallanta mahaifiyar ta tai tare da maida hankalinta kanta.
Khadija tace " me yasa kike yadda akan duk abinda Abba yace? Mai kyau ko mara kyau? Haram ko halal?"
Umma idanunta ne suka canza kala tana kallan Khadija, tace " ban taba yimai musu ba haka kuma ban taba bijerima abinda yake so ba, shine ginshikin yan uwana, da abin hannunsa suka zama abinda suka zama yanzu."
Khadija tace " saboda abin duniya? Saboda 'yan uwanki suji dadi kike yarda da duk hukuncinsa? Ba kya tunanin kema kinada kamasho na laifufukan da ya aikata?"
Umma ta mike tare da kokarin maida kwallarta tace " Khadija! Kada ki kuskura kiyi rayuwa irin tawa, kada kisa 'yan uwa da iyayenki gaba da maganar Allah, wannan shine babban kuskuren da muke tafkawa idan Mahaifanmu,mijinmu ko 'yan uwanmu suka samu abu, bama tunanin dacewarsa ko kaucewarsa a addininmu sai muyi kokarin aikatashi dan musu biyayya da faranta musu."
Ta kalli Khadija wacce ke hawaye tace " khadija me kika sani? Me kika ji wanda ya tada hankalinki haka, kin canza, kin rame tunda kikazo ko abinci baki ci ba sannan neman barin gari kike yi, menene kikaji da yasa ko kallan iyayenki bakyasan yi?"
Khadija ta runtse ido wasu hawaue suka fito tace " menene ribarku akan kai Ya Abdulmajid gun Umma Magajiya?"
Gaban Umma ne ya fadi ta kalleta a tsorace, Waziri da tun dazu yake tsaye yana jinsu duk gab'obin jikinsa sunyi sanyi, jin wannan magana ta khadija yasa ya kalli kofar d'akin da sauri, cikin tsananin tsoro.
Khadija tace " kuna tunanin wannan sirri bazai taba fitowa ba? Idan Abba yayi hakan dan samun karfin mulki da juyowar mulki daga zuri'ar jinin sarauta zuwa nashi, kefa?"
Umma kallan Khadija kawai take batasan hawaye na zubo mata ba.
Hisham juyawa yai jiki a sanyaye yai waje zuwa masarauta, dan bazai iya jin naganganunsu haka ba.
Umma ta tsugunna a inda take tare da dafa kanta, Khadija kuka take dan bazata iya fadar dayan abinda taji ba dan ta tabbata Umma batasani ba, sai yanzu ta fahimci tsantsar dalilin dayasa Turab ya canza mata, ba shakka ba yanda za'ai sanda yake mata yai tasiri in har yasan sirri nan, bayan ita din jinin Hisham ce bawai rikonta akai a gidan ba.....
************
A cikin fada kuwa Sarki na zaune akan kujerarsa ta mulki cikin nad'i na sarauta, Galadima da Barde su kadai aka kira sai alkalin cikin gida.
Sai dogarawa dake tsaye a gefe, Turab ne ya shigo ya zauna a inda ya kamata, shiru sukai suna jiran Hisham dan isowarsa.
Galadima ne ya kalli agogo yace "Ranka ya dade minti 15 ya wuce daga lokacin daka bashi."
Sarki yace " a kara mai minti biyar."
Minti biyar ce tai, Barde yace " minti biyar tayi ranka ya dade."
Sarki ya kalli Alkali yace " wannan alama ce ta ya aikata abinda ake tunanin ya aikata ko?"
Turab kam addu'a kawai yake akan Allah yasa ya zo.
Alkalin zaiyi magana aka sanar da isowar Waziri.
Wani irin dogon numfashi Turab yaja na jin dadi.
Wannam shine shafin farko na d'aukan mataki akan abinda Magajiya ta aikata musu, shi, mahaifiyarsa, Sarki, Abdulmajid da Khadija.
Bazai so wani abu ya jawo rashin zuwan Hisham ba.
**********
Mairo kam duk ta rasa me ke damunta, ba shakka tunanin halin da Abdulmajid yake ciki shine ya dameta, yaci abinci? Ya sha ruwa? Karfa tun abincin data bashi har yanzu bai sa komai a cikin sa ba?
Mikewa tai zaune daga tsintar wanken da bata san ma me takeyi ba.
Tace a fili, zanje in dubashi ne bawai dan na damu da halin da yake ciki ba, sai dan zuciyar muslunci da tausayi.
Kai ta d'aga tace " ai duba mara lafiya ma babban aikin samun lada ne, dan haka dubiya zanje bawai dubiya zani saboda Abdulmajid ba....."
😄😄😄😂Nace anya kuwa Maryama????
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*80*
Kowa da ke cikin gurin ne ya zuboma Hisham ido, jiki a mace ya shigo ya zauna.
Galadima ya kalleshi sheke ke ya tuno abinda dansa ya sanar dashi, ba shakka ko waye ya ji dolene yasan da hannun Hisham a wannan lamarin inba haka ba ta yaya ya san inda aka kai Abdulmajid?
Gyaran murya da sarki yai ne yasa kowa ya nutsu, Takawa ya kalli Hisham sannan ya kalli Alkalin yace " a fara."
Nan alkalin ya ciro takardar ya fara karantawa kamar haka.
" A jiya ranar lahadi ne aka kawo karar Hisham wanda akace ya nemi da a kama Abdulmajid wanda hakan ya jawo masa karaya a kafarsa da kuna manyan ciwuka a gab'obin jikinsa."
Kallan Hisham yai yace " Hisham kana da abin cewa a game da laifin da akace ka aikata?"
Kalaman Abdulmajid ne suka fad'omai ya kalleshi yace " ta yaya zan so wani abu ya samu d'an kanwata? Ni fa na kasa fahimtar takamaimai me na aikata"
Galadima yace " ina muka san manufarka?"
Turab ne ya d'ago sannan ya kalli Hisham ya juya ya kalli Alkali yace " Gaskiya ni kaina na kasa gane takamaimai me ka aikata, zuwa gun d'aurin aurena dakai ka tambayeni a inda na taho? Ko kuwa jin Abdulmajid ya taho a motar daya kamata in taho da kaji hankalinka ya tashi? Ko kuma ganin da Sabi'u yama ka je ka d'auko Abdulmajid? Ni kaina Mai Martaba na Kasa gane mai Waziri ya aikata."
Hisham yace " dan na tambayeka in da ka taho gani nake ai ba laifi bane."
Turab ya jinjina kai yace " haka ne, sai Dai ya akai kasan inda Abdulmajid yake farat d'aya? Ba tare da bincike ba?"
Hisham ya d'ago ya kalli Sarki.
Sarki ya kalleshi yace " amsarka nake san ji."
Hisham ya daure yace " nima ba sani nai ba bincike nai har Allah ya kaini gun."
Galadima yace " gaskiya kam, ai hakan zata iya faruwa, amma ni a sanina Sabi'u baiga alamar bincike a tattare da kai ba."
Hisham ya kalli Galadima cikin takaici sai dai bai amsa ba.
Turab ya mike ya dawo gefen da Hisham ke zaune ya kalli sarki yace "Ranka ya dade menene dalilin daya sa Abdulmajid ya shiga motar da ta kasance mota ce wanda Ango zai shiga?"
Kallan Hisham yai yace " Waziri mai kake tunani?"
Hisham ya kalleshi dan bai fahimcu me yake nufi ba.
Turab yace "baka tunanin yaji wani abu game da abinda zai faru?"
Idanu Hisham ya zaro yace " kanaso kacemin Abdulmajid yasan abinda zai faru a ranar?"
Turab yace " ranar? Wace rana kenan?"
Hisham kallansa yai sannan yace " bansan me kake so kace ba."
Turab yace " zata iya yiwuwa, sai dai da alama bakwa tunanin abinda Abdulmajid yakeji a wannan lokacin, ace yayan mahaifiyarsa shine ya nemi halaka mai rayuwa, ko meye ribarka........"
Cikin zafi Hisham yace " kai yaro, ya isheka haka, har yaushe aka haifeka da zaka zo ka dinga d'aure magana? Hauka nakeyi da zan nemi halaka Abdulmajid? Tsautsayi ne dai ya afka ya shiga motar da bai kamata ya shiga ba, amma ni ban yarda ya ji ba, ni ina tunanin kai ne ka sashi ya shiga motar ma."
Kallan Turab sukai, Shikam bai san sanda ya sa dariya ba, yana dariya ya sunkuyar dakai yace " tuba nake ranka ya dade, bansan sanda dariya ta kwacemin ba, ni? Meye ribata in nayi hakan?"
Hisham yace " ka hau mulki ba tare da matsala ba mana."
Turab yace " kana so kace in har d'aya ya kauda d'an uwansa a tsakaninmu d'ayan zai hau mulki ba tare da matsala ba kenan?"
Hisham yace " Sai ka tambaya?"
Turab yace "ahhh na gane, amma in na kusa damu ne suka neman taimaka mana gun rage mana iri fa?"
Hisham yace " ban fahimceka ba."
Turab ya kalli Alkali yace " ina so a duba maganar Hisham kamar haka, na farko yace Tsautsayi ne dai ya afka ma Abdulmajid ya shiga motar, na biyu zuciyarsa tana tunanin halaka junanmu shine hanyar da ya fi cancanta d'ayan mu ya hau mulki, sannan bai musa ba akan shi da wani sun aikata wani abun tunda sanda na cemai Abdulmajid yaji bai musa ba akan bai san me yaji ba sai cewa dayai wai bai yarda yaji ba."
Ji sukai " Abu Turab kuka so ya shiga motar?"
rq
Gaba d'aya kallan mai martaba sukai wanda idanunsa ke kan Hisham, ya cigaba " motata dana bada ta ango ce, menene dalilin dayasa ba'a tare ko wace mota ba sai ta Ango?"
Turab Murmushi yai dan dama shi bai isa yai tambayar nan ba, fatansa d'aya mahaifinsa yai.
Hisham ya rikice ga tsananjn kwarjini na idob Sarki, kalaman Khadija ne kawai suke mai yawo, meye ribarsu?meye ribarsu? Duniyar ma nawa take?
Sarki a zafafe yace " Dakai nake magana Hisham."
Hisham ya kalli Sarki a tsorace sannan ya kallu Alkali.
Turab ya kalleshi, Hisham duk ya rikice.
Turab ganin ya gama rikicewa yai sauri yace " Waziri nine bakasan gani a duniyar? Me na tare ma?"
Kallan Turab yai yana huci yace " tambaya kake? Zuwanka duniya shine abu na farko da mukai dana saninsa."
Sarki yace " mene?"
Hisham ne ya kalli Sarki a tsorace sannan yai saurin sukunyawa duk jikinsa rawa yake, ina zai sa kansa?me zaice wanda bazai taba rayuwar Abdulmajid ba.
Turab jiki a sanyaye yace " kai da wa kukai dana sanin zuwana duniya?"
Hisham ya kallu Turab sannan ya kalli Alkali dasu Galadima da Barde wansa suka saki baki dab tsananin mamaki.
Hisham ya gama sadaukarwa yau kam tashi ta kare.
Idanu ya runtse yace " nine na aikata, ni ne nasa a kamaka, tsautsayi ya fada kan Abdulmajid."
Dolene ya fadi haka ba wai dan Magajiya ta sashi ba sai dan yasan yau kam tashi ta kare, ko ma menene dolene ya kare rayuwar Abdulmajid.
Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.....
Abinda kowa ya shiga fada kenan a fadar.
Turab yace " kana so kacemin kai kadai ne ka shirya wannan abin?"
Hisham yace " ni kadai ne, da dani dawa nake yanke shawara ta?"
Turab yace " ni na kasa fahimtar menene ribarka a ciki in Abdulmajid ya hau mulki, dan yana d'an kanwarka? Ko kuwa da wani abun?"
Gaban Hisham ne ya fadi ya kalli Turab, tsananin tsoro ne karara a idanunsa.
Sarki a kufule yace " kai da wa kuka aikata? Magajiya?"
Kasa yau da kansa da sauri yace " ko d'aya bata ma san da wannan zancen ba, ni kadai na aikata bawai kuma saboda mulki na aikata ba sai dan ina bakincikin yanda Khadija ke san yarima Turab shi kuma yana murnar auransa."
Turab ya kalleshi a ransa yace taban ka biyo? wato so kake har karshw kar ka nuna dana sani ko? Zuciyarka ta gama kekashewa wanda ko kayi dana sanin bazaka taba sanarwa mutane da ka yi ba? Kunyar duniya ce bakasan kaji?
Ran Sarki ya baci yace " Alkali inaso a kewa Hisham daga wannan lokacin sannan ayi bincike sosai akan kaf laifufukan daya aikata inaso a sanar dani nan zuwa kwana uku."
***********
Magajiya kam ta rasa ina zata sa ranta, a zaune dai take kusa da Abdulmajid amma sam hankalinta baya gun, tashi hankalinta bai wuce sanda ta tuna abinda Abu Turab ya mata ba bayan sun rabu da Hisham.
Tana kokarin shiga d'akin taji muryarsa a bayanta yace " kin gama tsaramai?"
Juyowa tai ta kalleshi batace komai ba, sai wani kallo da take mai wanda ni kaina bansan manufarta ba.
Turab yace "shawara nazo baki, kiyi gaggawar zuwa ki sanar da laifufukan da kika aikata, dan wannan karan bazan taba bari kici galaba akaina ba."
Murmushi tamai tace "bari? Kana nufin kai kake bari nake yin nasara akan al'amurana? Sai dai ya zakayi Turab? Har karshen rayuwarka baka isa kai nasara akai na ba, ka sa wannan a ranka."
Ta shige d'akin, idanunta ta runtse sannan ta mike da sauri, bataga ta zama ba.
Kallan Abdulmajid tai wanda shi kansa a kwance kawai yake tace " zan je gida."
Bata jira amsarsa ba tai gaba.
Da kallo ya bita.
Baga dade da fita ba yaji an turo kofar, idanunsa ya maida ya rufe dan ya d'auka itace, sam baiji sallamara datai ba.
Kusa da gadon taje a hankali tace " Malam kaci abinci?"
Idanunsa ya bud'e da sauri sannan ya kalleta, ji yai wani sanyin dadi ya ratsashi sai dai yana tunanin ko ita taji sirrinsa kila kallonsa ma bazata sake ba.
Had'e rai tai tare da cewa " karma kai tunanin damuwa nai dakai nazo dubaka, asibitin nazo shine na karaso inga Khadija."
Murmushi ya sakar mata yace " ko ma menene dalili naji dadin ganinki."
Baki tad'an tabe tace " ya jikin Khadija?"
Yace " ta koma gida."
Tace " yayi, kai fa? Ka daina pretending d'in baka farfado ba?"
Murmushi yai yace " me? Kin damu ne akan rashin cin abincin da nake? Kullum ina kwance?"
Kai ta kawar da sauri tace " inji wa kenan? Tab!"
Dariya ya d'anyi ganin yanda tai saurin bashi amsa...........
**************
A can bangaren Turab kuwa, Gimbiya na zaune a kan gado ita kadai a cikin d'aki, ba shakka ya dade bai dawo ba, dan ita ma bata dade da dawowa daga bangaren Umma ba.
Jitai an kwankwasa kofar tare da yin sallama.
Amsawa tai sannan ta mike jin muryar Turab.
Kallan kofar tai a hankali taga ya shigo.
Tana ganin yanayinsa tai saurin karasowa inda yake tace " lafiya?"
Jitai ya jawota jikinsa ya rungume ta tsam.
Mamaki ne ya kamata, sai dai bata nuna ba, a hankali takai hannunta bayansa.
Ajiyar zuciya yai a hankali......
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*81*
Ya dade a jikinta kafin ya d'ago ya kalleta yace " i'm sry."
Abinda ya fada kenan yai fara takawa zaiyi waje.
Takunsa biyu yaji ta riko rigarsa, tsayawa yai ba tare da ya juya ba, a hankali ta tako zuwa inda yake itama ta sake rigarsa sannan ta kwantar da kanta a bayansa.
Yayi mamakin jin ta a bayansa dan shi har yanzu gani yake auren had'i ne tsakaninsu shi kuma bazai taba shiga hakkinta ba.
Cikin wata murya mai sanyin gaske tace " Thanks alot for showing me ur weaknesses."
Jiyai wani abu ya tsirgamai, murmushi tai mai sanyi sannan tace " ban san me ke zuciyarka ba game dani, sai dai at least nasan abu d'aya wanda inaji shikadai ya isheni zama dakai cikin farin ciki."
" menene shi?"
Kanta ta d'aga daga bayansa tana murmushi tace " nasan u are comfortable in kana tare dani."
Murmushi yai sannan ya juyo ya kalleta yace "Hmm abinda kika ce......"
Kallansa tai cikin mamakin dan yanda yai maganar alama ce ta zai musa abinda take tunani, da sauri ta juya bayanta tace " ba sai ka fad..
.."
Kansa ya sako ta bayanta saitin kunnenta yace " abinda kikace hakan yake."
Sam ta manta da kanta na gefen kunnenta ta juyo da sauri jin amsarsa.
Numfashinsu ne ya sarke dan fuskarsu tayi daf da juna, a hankali ya saukar da idanuwansa ya kalli bakinta wanda yake dan karami mai kyau, gashi tasa jan baki jaa amma bai turo ba.
Wani abu ne yaji yana tsirgamai, dif sukai kamar an d'auke wutar nefa sai shi da yake dan kokarin kara karkatar da kansa wanda ita kuma tai kasa da idanunta saboda kunya.
(mai kake shirin yi Turab? Me zuciyarka take neman saka? Ina alkawarin?)
Jisukai an kwankwasa kofa, juyasa yai da sauri ya nufi kofar ya bud'e.
D'aya daga cikin masu kula da Gimbiya ne, ta gaisheshi sannan tace "Yarima an turo Mai Martaba na banana. "
To kawai, yace yai waje.
Yana fita ya furzar da wata iska sannan ya d'anyi fifita da hannunsa yace " why am i feeling hot?"
Itama yana fita ta fada kan gado ta kwanta tare da saukar da ajiyar zuciya itama.
Bangaren Mai Martaba ya nufa, a waje yana jiran kafin a sanar ma Mai Martaba zuwansa ya kalli wani yace " Jakadiya fa?" yace " ai yau da safe tace wai yarta ba lafiya, shine aka dawo da wannan nan, ita kuma ta tafi." ya karasa maganar yana nuna mai wata.
Murmushi yai dan ya tabbatar guduwa tai, nan ya shiga bangaren Sarki.
Yana zaune ga abincin nan a gabansa da alama yanzun nan ya gama ci.
Sai da ya kara gaisheshi sannan ya zauna tare da lankwashe kafafunsa yace " gani."
Sarki ya kalleshi yace " me kake tunani game da Waziri?"
Turab yace " ban fahimceka ba..."
" na rasa me yasa nake ganin kamar akwai abubuwa da dama da kake b'oyemin."
Turab yace " me yasa kake tunanin haka? Ni kam ba abinda nake b'oyema."
Takawa ya kalleshi sannan yace " Turab? Kana tunanin zaka iya kama Magajiya da kanka?"
Turab ya d'ago ya kalli Sarki sannan yace " Abba me yasa ka ke kokonto a kaina?"
Sarki ya girgiza kai yace " Abu Turab!"
Kallansa Turab yai jiki a sanyaye, yace " Hajiya ta farfado, sannan naji abinda ya ke faruwa."
Idanunsa ne suka canza yana kallan Mahaifinsa saboda tausayawa.
Sarki yai murmushi yace " alokacin da naji abinda ya faru lokacin ne na tabbatar da Magajiya tafi karfina sannan babu ko dan d'igon imani a zuciyarta, a da nayi tunanin rashin nuna mata kulawa ne yasa ta rikid'e ta koma haka, sai dai abinda naji sam ya hanani bacci, hankalina ya tashi. Ban taba tunanin a duniya akwai wanda rashin imani zai sa ya aikata hakan ba, sannan bayan abinda ta aikatamin har ta nemi halakamin mahaifiya, a wannan rana nayu dana sani sosai na zamantowata Sarki dan da ace ni ba Sarki bane banaji duk wad'an nan abubuwan zasu faru dani."
Turab yace " Kaddarar ka kenan Abba, sai dai fatan Allah yasa kaci jarabawar da ya maka."
Sarki ya kalleshi yace " wato ita daga d'anta bata san in sake haihuwa kenan?"
A ran Turab yace " Abba shima ba naka bane."
Sarki ne ya cigaba, Turab kai Kainuwa ne dashen Allah, shi yasa duk wani makirci da kiyayya bata hanaka takawa duniya ba, bata kuma haka bud'e ido ba a duniya, wannan itama Baiwa ce da Allah ya bani wanda nake gode masa."
Turab ya d'ago ya kalli Mahaifinsa yanajin wani tsananin tausayinsa na ratsashi, cikin takaici yace "Abba wai kana sarki ke zai hana ka hukuntata daidai da laifukanta, barinta fa da akeyi shi yasa ma take abubuwan dataga dama."
Sarki ya dade kafin ya murmusa yace " Turab kenan, bakasan me nene nauyin dake d'aure akan kujerar nan ba, sannan abu ko ya shafeni dole sai na fitar da shaida sannan nai hukunci cikin jama'ar fada, sai dai matsalar itace Magajiya bata barin abinda zaisa a gane tayi abu, sannan duk wani wanda yake da hannu akan abun to fa sai ta san yanda tai ta kawar dashi."
"Hajiya fa?"
Sarki yace " wa zai yadda da shaidar tsohuwa? Sannan suruka?"
Turab yace " haka ne na tabbatar zata iya juya laifin kanta."
Sun dade suna tattaunawa kafin su rabu.
Turab na fitowa ya bi d'akin mahaifin nasa da kallon tausayi, tabbas dolene ya hanzarta sanin abinda ya kamata yai da Magajiya.
Magajiya kam tana dawowa taji labarin killace Hisham da akai, wannan abu ya tabata sosai ya kuma kara tada mata hankali domin ta tabbata Turab sai tayi da gaske akansa, wannan shine karo ma farko da aka kada ita da dan uwanta akoda yaushe sukecin riba bawai su a ci riba akansu ba.
Bayan La'asar ta aika a kira mata Basira.
Basira kam ta gama had'a kayanta kenan da Turab yace ta koma can ko sati d'aya zuwa biyu ne tayi, sannan Sarki yace za'a maida Hajiyarsa can gidan.
Jin wannan sakon yasa tai shiru kafin ta fito, dan a ka'idar mulki Magajiya ce Sarauniya wacce duk matan sarki ke karkashinta dolene ta amsa kiran data mata.
Magajiya na zaune kan kilisarta kai kace ba wani abu dake damunta sai dai zuciyarta fal take da tsoro da shakkar abinda ke faruwa.
Basira ta gaisheta sannan ta zauna.
Magajiya ta kalleta cikin izzarta tace " Basira kin san ko ni wacece ko?"
Basira ta kalleta cikin mamaki da rashin fahimtar abinda take nufi, Magajiya ta murmusa sannan tace " ba wai wani abun nace ba, tuna miki dai kawai nakeyi, ni d'in macece wacce banida yafiya akan duk wanda ya nemi tozartani, inaso kisa hakan a ranki sannan ki sanarma na kusa dake abinda na fada, daga ke har abinda kika haifa banaji kunyi kaurin wuyan da zai sani na tsugunna muku, tunani yakeyi shine yake cin galaba akaina shiyasa na kiraki ke wacce kika haifeshi in sanar dake hakan."
Basira ta kalleta sannan tace " Magajiya ni na kasa fahimtarki, Turab ne ya tozartaki kike sanar dani in gargad'eshi ko me?"
Ran Magajiya ya b'aci sai ta saki dariya tace " me? Tozartawa?au har an hallici d'an dazai tozartani a duniyar nan?"
Basira ta murmusa sannan tace "nima abinda na gani kenan, shi yasa nake mamaki danaga kin kirani kika neman sanarmin in jaa ma Turab kunne, bayan yaran nan naki ne."
Magajiya ta kalleta a ranta tace " wato kema kin rika ko?"
Basira tace " zan koma in ba wani abun."
Bakin ciki baisa Magajiya ta kara tanka mata ba.
Tana fita Magajiya tasa kafa ta ture tiren inibin dake gabanta cikin b'acin rai, sannan tai wani dan karamin kara ma takaici, me yasa yanzu sam bata iya shanye bakin ciki? Mikewa tai cikin takaici tace " ke aika a kiramin Waziri."
Baiwar ta sunkuyo tace "Ranki ya dade kin manta an........."
Matsowa tai ta kifama yarinyar mari sannan tai ciki ranta na soyuwa.
Tafiya ta kamayi a d'akin cikin b'acin rai, yanzu ba Hisham wanda sai dai tana daga zaune tasashi aiwatar mata da duk abinda take so, sannan ba Abdulmajid wanda take tunkaho dashi Yana can a kwance.
Kanta ta dafe sannan ta d'ago idanunta cikin tsananin bacin rai, tace "Abu Turab!!! Ka jirani, zan shayar dakai abinda har karshen rayuwarka bazaka manta dani ba, wannan shine zai zama fad'anmu na karshe dakai, in har nai kuskuren halaka rayuwarka to tabbas nasan tawa rayuwar zatai rawa."
Kurama kasa ido tai cikin tsananin takaici, rabon datasamu bacci mai dadi ta manta, kullum sai tai mafarkin Turab na neman illatata, tabbas dolene suyi fito na fito yakin karshe a tsakaninsu.....
(😂😂😂😂nace Allah yaba mai rabo sa'a)
Khadija kam ta gaji da jiran Mahaifinta tana zaune a waje akwatinta na gefenta, ganin yamma tayi yasa ta mike ta fito waje.
Tsayawa tai ta kira mai kula da kofar su, ta tambayeshi " ina Abba wai yaje?"
Yace "wlh ban sani ba na dai san ya fita."
Juyawa tai ta koma ciki kawai, Umma na kwance a d'aki tunda sukai maganar nan da Khadija ta shiga d'aki bata fito ba, tanaji kannan Khadija da yayyinta na shigowa su fita amma ta kasa tashi, saboda tsananin dana sani dake damunta.
Wannan kenan..........
*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*82*
Bayan tayi sallar magrib ta yafa mayafinta katon gaske, lulubi tai sosai da sosai, wanda inba kaga fuskarta ba bazaka taba cewa Magajiya bace, ta fito, tara bayinta tai ta sanar dasu zata fita sai dai batasan kowa yasan ta fita sannan ko anzo nemanta a tabbatar ance tana bacci.
Ita kadai ta fito ta nufi inda aka killace Hisham.
Tana zuwa ta sauke mayafinta sannan ta kalli masu tsaron gun tace "yana ciki?"
Kallanta sukai bayan sun gaisheta sukace " Ranki ya dade Sarki ya umarcemu akan kar kowa......."
Wani kallo data buga musu shine ya hana su karasa maganar, tace " nice kowa?"
Da sauri sukace " ba haka bane......"
"ya isheni, bud'e."
Jikinsa na rawa ya bud'e kofar ta shiga."
Hisham na zaune ya had'a kai da gwiwa saboda abin duniya da duk ya taru yamai yawa, ba shakka yana cikin tsaka mai wuya.
Ta window ta tsaya tace "Yaya!"
D'agowa yai ya kalleta, ba shakka wannan itace wacce ta ruguzamai rayuwa, dan itace ta kawo shawarar d'aura d'ansa akan mulki wanda hakan ne yasa ya bata d'an ba tare da yin wani dogon nazari ba, sannan wannan shine dalilin daya sa sam idanunsa suka gama rufewa yakejin koma meye zai iya zuciyarsa ta zarme indai akan hawan d'ansa mulki ne to tabbas zai iya koma menene.
Kallansa tai cikin zafi tace " magana nake."
Mikewa yai ya iso inda take, kallanta yai yace "ya akai?"
Tace " baka tambayeni jikin d'anka ba?sai kacemin ya akai?"
Kallanta yai yace " d'ana? Bayan kece kika hana wannan maganar?"
Tace " yaya ai duk hanawar danai jini ai jini ne, sannan karka damu da gida, zan kula dasu kamar yanda zan kula da kaina, kai dai ka kara hakuri."
Kallanta ya sake yi yace " me ya kawoki? Dan na tabbata bazaki taso nan ba bayan kinsan abinda ke faruwa kizo nan ba tare da kwakwaran dalili ba."
Tace " Yaya ka san kome nakeyi a yanzu saboda Abdulmajid nakeyi ko?"
Kallanta yai dan yama kasa magana, tace "yaya karka damu da duk abinda ke faruwa, koda wani abun ya sameka ni ina nan, sannan in har ina duniya tofa kamar kai kana cikinta ne, d'an mu da 'yayanka ni na d'au alkawarin rikesu amana......."
Katseta yai da cewa " me kikazo fad'amin."
Juyowa tai ta kalli waje, can ta hangoni rakube jikin window rike da takardata da birona, kallo d'aya ta sakarmin na fita a guje kamar wacce aka biyo da wuka, dan tabbas na tsorata, wannan dalilin yasa sam Bansan me tace masa ba.
Sai dai tana gama maganarta na kalli Hisham, kallan da Hisham yake mata kadai zaka kalla ka tabbatar da lalai shi kansa yasha mamakin kalamanta.
Kallansa tai tace " Yaya bansaka dogon tunani ko dogon nazari ba dan abinda na sanar maka shi za'a aikata indai kana san kanka da lafiya, ni kabarni da waccen yaran, kai dai kayi abinda ya dace."
Yama kasa magana sai kallanta da yakeyi, tace "ni na wuce, ina kuma jiran ganin abinda nace."
Ta juya ba tare da taji asarsa ba.
Tsananin mamaki kawai yake, sai binta da kallo kawai da yai.
Tana fitowa ta ciro abu a jikinta ta mikama masu kula da kofar tace "waye ya ziyarci Waziri?"
Da sauri sukace " ba kowa ranka ya dade."
Juyawatai tai gaba abinta.
Tana shiga bangarenta cikin d'aki ta yaye mayafin ta shiga zirya a d'aki, Hisham zaibi abinda tace? A fili tace dole ne ai.
Ya zatai in bai bi ba?? Kai take girgizawa da sauri in zuciyarta ta nemi kawo mata wannan tunanin, sai tace innaaaa....."
*******
Basira kuwa da yama ta wuce gidan dan Turab dashi da Garzali ne sukazi suka rakata, hmm Umma anga Lantana.
Nan suka shiga hirar yaushe gamo bayan ta dan zauna gun hajiya ta dubata da jiki.
Turab ya zauna gun Hajiya wanda jikin nata dai to, sai a hankali duba da yanayin tsufan datai, sannan dama in girma ya kama dama ciwo kad'an ke zaunawa a jikin mutum, ita kadaice wacce take da wannan shekaru a cikin masu mukami dake gidan, dayake duk kishiyoyinta basa gidan sai ita wasu matan nasa sun mutu wasu kuwa sun bar gidan.
Turab ya kalleta duk ta rame ta kara motsewa, tace " Ina cikin farincikin ganinka, a koda yaushe tambayata d'ayace kana ina? Kana lafiya? Dan gaba d'aya hankalina yana kanka tunda na riga nasan abinda ke faruwa."
Yace " me kika sani hajiya?"
Tace " kasan komai ko? Wannan shine yasa nake tsoro saboda wannan matar batada imani ko kad'an, na tabbata bazata taba kyaleka ba."
Yace " Hajiya karki damu, ba ta isa tamun abinda Allah bai mun ba, in har wani abu kuma ha sameni to tabbas kaddara tace bawai wani abun ba, karkisa wannan a ranki."
Tace " Turab kana tunanin taimakawa yarinyar nan da kake hakan shine daidai? Karfa ka manta itace ta dinga zubamin magani
"
Yace " na sani hajiya hakan ne ma ya sa naji taimakon take bukata, Da ace mun farga ko munsan halin da take ciki mun taimaka mata da wuri banaji Magajiya ta isa ta sa ta wannan abin, sai dai ganin tana cikin hali na bukata yasa takejin zata iya yin komai.....
Hajiya kallansa kawai take cikin jin dadi.
********
Yau ma a kasa ya saukar da filonsa ya kwanta, tana kan gado a zaune ta kalleshi tace " ka dawo nan, ni sai in sauka kasa."
Kallanta yai yace " so kikeyi gobe in ziyarci asibiti?"
Tace " saboda me kenan?"
Yace " kin taba kwana a kasa?"
Tace " zan fara yau."
Murmushi yai yace " ke dai ki kwanta a inda kike kafin ki tada mana hankali da ciwon baya da gab'obi."
Kallansa tai tace "kai ma ciwon bayan kakeyi?"
Gani tai ya kwanta sannan ya ce wash Allah na, cikin irin muryarnan ta marasa lafiya.
Hankalinta ne ya tashi, da sauri ta sauko inda yake ta zo ta sa hanny tad'an d'agoshi tace " Lafiya? Menene?" duk ta rikice."
Idanunsa ya bud'e sannan ya mike ya zauna yace " yanzu in ni ina namiji daga kwanana a kasa na fara ciwon baya ai na zama rago."
Harararsa tai tace " yanzu nan d'in kenan zolayata akai?"
Dariya ya guntse yace " a'a"
Hannunta data ririkeshi ta nemi zarewa tare da had'e rai, hannu yasa ya rike hannun yanda ba yanda za'ai ta zare, kallanta yai ita kuma tai saurin juya kanta gefe.
Yace " ta ya za'ai ina namiji na barki ki kwana a kasa?"
Kallansa tai tace " ni ma tayaya za'ai in dinga barinka kana kwana a kasa?"
Murmushi yai yace " ke bakisan wahala ba......"
Kallansa tai saurin yi tace " kai sani kai?"
Murmushi yai yace " Bilkisu ni a kauyen kayau na taso."
Kallansa tai da sauri tace " kauyen ina?"
Murmushi yai sannan ya kwanta a kan filo din sannan ya jata itama fa kwanta a kan filon ta gefensa, duk suna kwance a rigingine.
yace " kinsan nayi makanta ko?"
Kai ta d'aga tace " eh"
Yace " da ita aka haifeni."
Shiru tai dan jin tausayinsa ya kamata, a hankali ya shiga sanar fa ita rayuwar da yai a kauyen nan.
Har zuwa dawowarsu garinan, hawaye ne ya gangaro ta gefen idanunta wanda ita kanta bata farga da zuwanshi ba.
Ya karasa zancen tare da juyowa yace " kinga kuwa ni a kasa ma wanda ba carpet zan iya kwana."
Kallanta yai yaga hawaye ya zubo mata, komawa yai ya kwanta sannan ya sa hannu ya riko hannunta.
Kallansa tai tare da sunkuyar dakai, yace " Kiyi hakuri na barinki kina yini ke kadai."
Murmushi tai batace komai ba, shiru ne yad'an ratsa kafin can tace " Umma......"
Sai kuma tai shiru, juyowa yai kalleta ta saitin inda take, yace " me ne?"
Tace " Na jinjina mata ne a raina."
Yace " jinjinar me?"
Tace " duk yanda ta shiga cikin wannan halin bai hanata kula da baka tarbiyya ba."
Murmushi yai sannan a ransa yace " shiyasa bazan taba yafema wad'anda suka ruguza mata rayuwa ba." ji yai tace " basu cancanci yafiya ba, sannan duk da bansan me suka mata ba na san d'anta zai hukuntasu daidaj laifikansu."
Murmushi yake yana kallanta,
Sund'an dade suna hira kaffin bacci ya d'auketa, shiru yai yana tunani shikam, a wani hali Khadija take jin abinda ya sami mahaifinta? Dan ya tabbatar bata tafiba tunda ya tambaya.
Bilkisu ya kalla sannan ya mike ya d'auketa ya d'aurata a kan gado ya rufeta da bargo dannan ta mike ya zai sauka, jiyai ta riko hannun rigarsa.
Idanunta a rufe tace " baka tunanin kaine ya dace ka kwanta akan gadon?bayan kasha wuya kana karami?"
Yace " ba bacci kike ba dama?"
Bata bud'e idon ba sai kara kasa datai dakai, yace " zan kwanta ta can bayanki, zan kuma sa filo a tsakaninmu, shikenan?"
Kai ta d'aga cikin jin dadi.
Mikewa yai har ta d'aukama yayi gaba, sai jin muryarsa tai saitin fuskarta yace " in mutum ya hauro inda nake garin bacci, duk abinda ya biyo baya ba ruwana...."
Ya juya yai gaba yana murmushi.Filo ta janyo ta rufe fukarta tana murmushin kunya.
*********
Khadija kam ana sallar asuba ta fito waje, tana ganin gari ya waye ta taho gidan sarki cikin tashin hankali.
B'angaren Magajiya ta nufa.
Tana kwance tana bacci taji ana kwankwasawa.
Cikin mamaki ta mike a d'an zabure, jitai gefen cikinta yad'an amsa, tai tsaki sannan ta mike ta zo ta bud'e.
Khadija ta gani, tace" Khadija?"
Masu kula da ita ne suka shiga bada hakuri, tace " kuje."
Khadija ta shigo sannan ta kalli Magajiya tace " Umma ina Abba?"
Magajiya tace " Yaya? Ina yaje?"
Khadiya ta kalleta tace " ke zan tambaya ai, banaji akwai wani dayasan inda yake bayan ke."
Magajiya ta kalleta tace " khadija! Ni kike tsarewa da magana?"
Khadija ta kalleta tace " wanda ake kasa magana a gabansa wanda yasan girma da darajarsa kenan bawai wanda ya halaka rayuwarsa, ta 'yayansa da kuma ta 'ya'yan yayan nasa ba sannan ya ruguza rayuwar duk wani wanda bai mai ba."
Magajiya tace " mene?"
Khadija wacce hanayenta da kafafunta duk sun sunyi shakaf sabida tsoro tace " kina tunanin kullum cikin samun nasara kike?"
Ba abinda Magajiya ta tsana irin a dinga nuna mata abinda ta ke tunani ba daidai ba.
Wani kallo ta mata tace " karki bari raina ya baci, ina raga miki ne saboda san da nake miki da kuma darajar sunan naki."
Khadija bata damu ba tace " Ya Turab bazai taba barinki kice nasara ba, domin kuwa Allah na tare dashi sannan gaskiya tana da adalci na yawo a jikinsa, in kinga Abba, ko inya dawo daga aikin sharrin da kika sashi ki sanar dashi ni na wuce."
Ta juya ta fita da sauri saboda karkaraa da jikinta keyi..........
*Turab*
*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*83*
Kanta ta dafe a waje tana tunanin abinyi, bazatace bata damu da inda mahaifinta yake ba, sai dai ganin mahaifiyarta yau da asuba ta yabbatar bata samu bacci ba jiya.
Ya Turab? Abinda yazo mata kenan, sai dataje bangarensa ta kalla, ganin kofar ba mai kula da ita yasa ta tuna da ashe fa yanzu ya tashi daga nan, tunda yanzu yayi aure.
Haka ta juya jiki a mace ta koma gida.
Magajiya tai shiru tana tunani, tafi awa d'aya a zaune shiru kafin ta mike sannan ta shiga wanka.
Sai data cancad'a kwalliyarta kamar yanda ta saba sannan ta saka alkyaba mai tsananin kyau, wanda ya kara fito da kyanta.
B'angaren Sarki ta nufa.
Yayi mamakin jin ance itace ke nemansa, kuma wai a kilisarsa bawai a bangarensa ba.
Tana zaune, irin zaman data saba na isa da mulki.
Mai Martaba ne ya shigo sai daya zauna sannan ta gaisheshi.
Abinda ya bashi mamaki, yana zama sai ga Alkali ya nemi izinin shigowa, nan ta bada izini ya shigo.
Ko zama baiyi ba sai ga Abu Turab, Sabi'u sun shigo, shikam Turab ya d'auka ma Sarki ke nemansa.
Yayi mamakin ganin Gimbiya a zaune, shikansa Sarki kawai kallan kowa yake cikin mamaki, Turab na ganinta yasan akwai abinda ta shirya.
Sai da suka gaida Sarki da Magajiya sannan suka zauna.
Magajiya ta kalli Sarki tace " Ranka ya dade muna bukatar Hisham a gun nan."
Kallanta yai sannan yace " Ba yanzu ba, sanar dani me ke tafe dake sannan inyi tunanin kiransa."
Ta numfasa sannan tace " jiya naji duk abinda ke faruwa, dan ni bansan abinda ke faruwa ba, duk yanda na tambayi Abdulmajid bai sanar dani ba."
Sarki yace " meke tafe dake yanzu?"
Murmushi tai sannan ta kalli Sabi'u t ace " Abinda na kasa fahimta shine na d'auka Sabi'u shikadai ne shaidar abinda ke faruwa?"
Turab kallanta kawai yakeyi, haka kawai zuciyarsa take raya masa abinda take shirin yi.
Alkali yace " eh shikadai ne."
Magaijiya tai murmushi sannan ta kalli Sarki tace " Sabi'u kowa yasan aminin Abu Turab ne, me yasa mutane suka yarda da maganarsa ba tare da bincike ba? Me yasa ba wanda ya kawo Turab shine ya sa a kama Abdulmajid shikuma Sabi'u ya tafi inda aka killaceshi, wanda bai sani ba ashe Waziri ya bishi a baya?"
Turab ya kalleta baisan sanda wani murmushi na takaici yazo mai ba, lalai matar nan bala'i ce.
Sarki kallan mamaki shikansa yake mata, ita kuwa ta kalli Alkali tace " Turab d'ana ne sai dai ko d'ana ne naga zaiyi abinda bai dace ba dole ne na maidashi kan hanya."
Alkali yace 'm" haka ne, kuma sai da kikai magana naga ya kamata kam a sake bincike."
Kallan Sarki tai tace " Takawa tuba nake in na b'ata ma rai, sai dai Abdulmajid yaji magana a lokacin da yake kwance agun, kuma tabbas sunan yarima suka kira, banaji kuma akwai wani yarima wanda yake masarautar nan bayan Abdulmajid to Abu Tutab ne."
Sarki ya kalli Turab wanda kallan Magajiya kawai yakeyi.
Sarki yace " Turab!"
Abu Turab ya kalli Magajiya bai d'auke idansa daga kanta ba yace " haka ne, ba shakka Umma kinyi gaskiya, Sabi'u abokinane sannan ni da Abdulmajid bama shiri."
Magajiya tace " Banso nai maganar nan ba sai dai ina ganin dolene a sake bincike saboda ina tsoron kar wani kazamin sirri ya fito daga bakina."
Turab ya kalleta yace " me kike nufi?"
Kallan Sarki tai sannan tace " Banasan ragewa wacce ta haifeka daraja a idon duniya wanda nake ganin shine dalilin.......
Sarki ne ya katseta " me kike shirin cewa??"
Ta kalleshi tace " ba wai dan Hisham yaya na bane sai dai dan bazan baro a hukunta mara laifi ba."
Kallanta Turab yake zuciyarsa na wani irin kuna, ji yake kamar ya tona asirin Abdulmajid a gun nan, sai dai abu biyu ne ke hanashi, na farko yana tsoron yanda Sarki zaiyi inyaji wannan maganar duba da yanayin girmansa, sannan yana tausayawa rayuwar da Abdulmajid zaiyi nan gaba."
Alkali ne yace " me zai hana a kira Abdulmajid da Hisham aji abinda ke faruwa daga garesu?"
Magajiya tace " Abdulmajid na asibiti amma za'a iya tambayar Hisham."
Sabi'u wanda ransa ya gama b'aci yace " wallahi da idona naga Waziri yaje gun, sannan nine na bishi ba shine ya bini ba."
Tace " wanene zai yadda da hakan? Bayan ba kada shaidar da zata nuna hakan?"
Turab ya sa hannu ya dafa cinyarsa yamai alama dayai shiru.
Sarki tsananin mamakin ta ma yasa ya kasa magana.
Daurewa yai yace " gobe za'a sake zama saboda wannan maganar, zakuma a sake yin shari'a akan wannan al'amari."
Magajiya tai kasa dakai tace " Godiya muke ranka ya dade."
Nan ta mike cikin isa tai gaba.
Tana fita alkali yai sallama ya fita, Turab ya kalli Sabi'u yace " dan bamu guri."
Nan Sabi'u yai waje.
Turab ya kalli Sarki wanda gaba d'aya fuskarsa ta canza, tsananin bacin rai ne bayyane a fuskarsa.
Kallan Turab yai.
Turab ya kakaro murmushi yace "Abba ba wani abu "
Sarki yace " Turab ina matsayin mahaifinka? Nasan duk abinda ke faruwa amma banida ikon bin bayanka? Banida ikon kareka? Ina zaune za'a maka sharrin da baka sani ba?"
Turab yace "karka damu Abba, muna wani stage ne na wanda ko ni ko ita, wani mataki muke wanda in har bata nakasa rayuwata ba ni zan nakasa tata, dolene dukanmu mu fito da b'oyayen ajiyar da mukama junan mu dan gogawa, karka damu Allah na tare da mai gaskiya."
Sarki ya kalleshi cikin kulawa yace "kada ka kuskura kai mulki irin nawa wanda zaka sakarwa matarka komai, ka kuma bari ta dinga cin galaba akanka."
Turab ya jinjina kai kafin ya mike ya fito.
Yana fita yai waje mai makon ya koma cikin gida.
******
Magajiya kuwa tana shiga bangarenta ta saki wani murmushin jin dadi tace " Takawa ya kaji a zuciyarka? D'an da kake masifar so na cikin halaka?"
Turab kam gidan da Umma take ya nufa.
Suna zaune a waje suna yar firarsu da Lantana.
Ya shiga, sai da suka gaisa sannan ya kallu Lantana yace "ina yarinyar nan?"
Tace "wa kenan?"
Yace " mai kula da Hajiya."
Tace " au Marakisiya? Tana gun Hajiya."
Shiga yai ciki kai tsaye tana shara, Hajiya ya kalla wacce ke kwance tana bacci, yace " zo."
Tace "to."
Falo suka dawo ya zauna kan kujera ita kuma ta nemi kasa ta zauna, kallanta yai yace " baki manta abinda kika cemin ba ko?game da ko a gaban waye zaki fadi gaskiya akan Magajiya?"
Tace " eh."
Yace " kinsan waye ya saki ba hajiya magani?"
Tace " eh wacce tafi zama kusa da Magajiya ce."
Yace " Yauwa."
Mikewa yai ya fito.
Bai ko zauna gunsu Umma ba ya fita.
Bayan ya shiga mota ya dade a zaune a bayan mota shiru yana tunani, kafin yacema Garzali su tafi Asibiti.
**********
A gida kuwa Mairo ta gama cin abincin safe kenan tai wanka, ta hau kan gado, tunowa tai da abinda Abdulmajid yace mata da zata tafi.
Yaushe zaki dawo?
Tsaki tai a fili tace " harda wani tambayar yaushe zan dawo ko kunya, ko mai zan koma in mai?"
Can kuma tace " ni biki ma zamu tafi gobe zuwa cikin garin kaduna, kaga wacce zata zo."
Kara gyara kwanciyarta tai.
Abinda yaban dariya shine batafi binti biyu da kwanciya ba naga ta sauko daga kan gadon tace " hmm bari dai inje neman lada kafin mu tafi kaduna."
Hijab d'inta ta janyo ta fito.
Abdulmajid na kwance akan gado, yana tunanu, wanda kwanan nan aikinsa kenan, gaba d'aya tunani sun kasa barin zuciyarsa, gani yake duk yanda rayuwa zata juyamai bayaji zai taba samun jin dadi wannan rayuwar, bata ubansa ba ba kuma ta uwar data rike shi ba.
Sallamarta ce tasa ya kalli kofar.
Shigowa tai fuskarnan a had'e tare da kallan d'akin tace " hmm da alama yauma Khadijan bata nan"
Abdulmajid kallanta kawai yake yana murmushin jin dadi. Tace "Sannu da jiki, ni na tafi in ta dawo ma had'u."
Juyawa tai kamar mai shirin fita.
Da sauri yace " Maryam!"
Tsayawa tai cak sai dai bata juya ba, yace " Maryam!"
Yanda ya kira sunan ta ne yasa taji ta wani iri.
Abdulmajid yace " Maryam dan Allah karaso nan."
Juyowa tai a hankali ta kalleshi sannan ta karasa inda yake.
A jikin gadon ta tsaya tace " gani, menene?"
Yana kallanta yace " bazan tambayeki komai ba, ko magana in bakyasan na miki bazan yi ba, so nake kawai na kalleki ko na minti biyu ne, please."
A hankali ta d'ago idanunta ta kalleshi, sannan cikin sanyin murya tace " meke damunka kwanan nan?"
Yace " ba komai, ko ince ko me ke damuna inaji in har ina ganin fuskarki kullum ko na minti biyar ne zan iya jurewa."
Maida idanunta kasa tai batace komai ba.
Zaiyi magana Turab ya kwankwasa kofar Tare da sallama.
Da sauri ta matsa daga jikin gado tare da kallansa.
Yana kallan kofar yace mata "tsoro kike kar yai tunanin ko akwai wani abu tsakanin mu?"
Harararsa tai batace komai ba.
Turab na shigowa ya kallesu, Mairo ta kalleshi sannan ta d'an matso da sauri ta gaisheshi tace " Ya Turab na shigo asibitin ne shine na leko neman Khadija."
Turab ya kalleta yace " au ba dubiya kika zo ba?"
Kallan Abdulmajid tai wanda ya juya kai, kasa magana tai.
Turab ya kalli Abdulmajid wanda ya kula shima yad'anji ba dadi yace " Mairo kenan, da alama kunyar yayan nan naki kikeyi, me zaisa in miki fada dan kinzo duba shi?"
Kallan Turab tai sannan ta sunkuya kai tai gefe da sauri tai waje.....
Murmushi Turab yai, duk da dai yana tunani akan wannan lamarin nasu sai dai yana musu addu'a dukansu.
*TURAB*
.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*Gaisuwa Gareki Maman Abrar wannan shafin naki ne, Allah yabar zumunci Ameen.......*
*84*
Ajiyar zuciya yai sannan ya kalli Mairo, kanta ta sadda kasa sannan tai hanyar fita.
Abdulmajid ne ya bita da kallo, sai dataje jikin kofar zata fita sannan ta juyo idanunsa na kanta dan Ji yake kamar kartaje ko ina.
Murmushi tamai sannan taja kofa tai waje Tare da rufo musu.
Tana fita ya maida kallansa gun Turab yace " Waziri fa? Ya aka kare?" dan tun jiya abin nan ke damunshi.
Turab yace " yana gida sai dai Sarki yasa an killaceshi kafin a gama shari'a."
Mairo taje zata gangara ta hango Magajiya na nufo gun.
Gefe ta matsa tare da juya baya har ta wuce, har taje zata sauka ta tafi sai kuma ta fasa.
Turab ya kalleshi yace " Magajiya ta bu'lo da wani sabon al'amari."
Abdulmajid yace " na me kenan?"
Turab zaiyi magana yaji Garzali na sanar da isowarta.
Tura kofar tai ba tare da sallama ba, dama tunda taga Garzali tasan Turab na nan.
Tana shiga ta kalleshi sannan ta kall Abdulmajid.
Murmushi Tai sannan ta karasa ciki.
Kallan Turab tai tace " kana nan ashe?"
Turab ya kalleta sai dai baiyi magana ba.
Girarta ta ja sama sannan ta kallu Abdulmajid tace " zuwa nai in maida kai gida, a kula dakai acan."
Kallanta yai yace " gida?"
Tace " eh, sannan dama inasan inma wata tambaya agaban kanin nan naka, nikam Abdulmajid tsakanin Waziri da Abu Turab wanene ya nemi halaka maka rayuwa?"
Kallan mamaki ya mata yace " ban gane me kike nufi ba?"
Tace " tsakanin Turab da yayana wanene yasa aka kamaka?"
Yace " ni ai ba........"
Katseshi tai da sauri tace "bakaji tambaya ta bace? Tsakanin Turab da Yayana wanene yasa akama ka?"
Turab ya kalla wanda daidai lokacin shima ya kalleshi.
Turab a hankali yamai wani murmushi.
Magajiya tace " kai nake jira."
Yace " Turab ne."
Wata dariya ta saki tace" kaji ko? Ina fatan kasan yanzu amsar da za'a bada a zaman da za'ai, sannan banasan wanda ya nemi kashe min d'a yazo kuma yana neman shiga jikinsa, dan haka karna kara ganinka da Abdulmajid."
Turab ya kalleta idanunsa na kanta ya taku har inda take yana tafa mata, sai dayazo daf da ita yace " Bravo! Kai gaskiya Umma u are indeed a very dangerous woman."
Da yake lokacinta ba makaranta tai ba, sai dai tsabar basira datake dashi ta tabbatar magana ce ya fada mata, tunda lokacin karatun mata ba'a wani daukeshi da wani abu ba.
Kai ta jinjina mai tace " in fadama wani sirri?"
Kallanta yai, tace " abinda kake dashi akaina ba abinda zasumun, kasan dalili? Ta matso daf dashi saitin kunnenaa tace "Saboda kai jinin mahaifinka ne, bazaka taba sanar dashi d'an dayake tunanin nashi ne ba nashi bane."
Sannan ta kalleshi tace " kasan dalili?saboda kana tsoron halin da zai shiga."
Turab kam jiyake zuciyarsa kamae zata fashe saboda takaici, daurewa yai ya kalleta yace " haka kike tunani?to in har haka kike tunani kin bada ni, domin in har irin wannan d'an karamin abun zai firgitashi to ba shakka bai dace da mulki ba."
Ya juya yai waje.
Dunkule hannunta tai ta matse a jikin zaninta, ji take kamar ta jawo yaran can ta shake shi.
Shikansa yana fita ya saku wata ajiyar zuciya sannan ya dan cije labbansa, yai gaba.
Kallan Abdulmajid tai wanda ganin yanda suke magana yasa ya runtse idanunsa saboda takaici, waje tai a zuciye Ta tambayi inda likitansa yake.
A hankali ya bud'e idanunsa, hawaye ne suka zubo mai dan ba shakka shikam yasan duk abinda ke faruwa duk saboda shi ne.
Tura kofar tai a hankali ta shigo, taba kallan sanda Turab ya fita, Sannan taga yanda Magajiya ta fito rai a bace.
A hankalu ta tako inda yake, hannunsa ya rike yana karza babban d'an yatsansa a kan bayan hannunsa sam bai kula ba gun yar ya d'an fashe.
Har ta karaso gun baimasan tazo ba, hannunta tasaka akan hannun da yake karzawa, idanunsa ya d'ago ya kalleta, kura mata ido yai, daurewa tai tace " me kakeyi hakan?"
Kasa magana yai sai kallanta kawau da yakeyi, tace " ko me ke damunka addu'a zakai bawai karza hannu ba."
Ta zare hannunta tace " zan wuce."
Ganin yanda fuskarta take a had'e yasa yai saurin riko hijab d'inta.
Tsayawa tai ba tare data juyo ba, yace " kiyi hakuri."
Kallansa ta juyo tai cikin zafi tace " me yasa kake cutar da kanka? Me yasa in abu baima ba bazaka fadi abinda ke ranka ba? Mahaifiyarka tafi wanda ya halliceka ne? Akan me bazaka dinga nuna mata abinda take aikatama ba daidai bane? Ko zuciyarka ba irinta Turab bace at least kai namiji ne ya kamata in har tai abinda bai dace ba ka nuna mata."
Ko mai ta tuna, sai kuma tai shiru taja hijab dinta tai waje.
Magajiya na dawowa ta sa aka sashi a keken guragu aka kaishi mota, sykai gida.
***********
Juyi tai ta ganshi akan sallaya, agoggo ta kalla taga karfe d'aya saura minti goma.
Farkawa ta kara yi , Abu Turab ta gani a zaune a kan kujerar dake d'akin, ya had'e hannayensa alamar dogon tunani, dayake ba haske sosai a d'akin, sai wata yar karamar fitila dake gefen gado ta d'aya bangaren ne a kunne.
A hankali ta kalli agoggon d'akin karfe biyu da kwata, mikewa tai ta zauna sannan ta kalleshi.
Kallanta yai dan yaji motsi, ganinta a zaune yasa ya mike ya taso yazo inda take.
Kusa da ita ya zauna sannan yace " farkawa kikai?"
Kallansa tai tace " eh, kai fa? Kasa bacci kai?"
Kai ya girgiza, tace " tunanin gobe kake?"
Juyowa yai saitin da take kallansa yace " Bilkisu."
"Uhmm mm"
Shiru yai sai kallanta da yake, tace " inajinka."
Hannayenta ya kamo duka biyun ya rike yace "bansan ya zata kaya mana ba gobe, shiyasa nake tunanin wani abu."
Kallansa tai tare da tattara hankalinta zuwa kansa.
Yace " idan har Magajiya taci galaba akaina, wani abu ya sameni inaso ki koma gida, ba tare da waiwaye ba, kiyi rayuwarki kamar baki san niba, zan aiko da takardarki......."
Hannunta ta zare daga cikin nasa sannan ta sa kalleshi tace " me kake sam cewa?"
Yace " nama mahaifinki alkawari bazan......."
Katseshi tai tace " kana nufin in had'a kayana kenan kafin gobe ko me?"
Baice komai ba sai kallanta da yake, mikewa tai ta kunna fitilar d'akin sannan ta bud'e wardrobe dinta cikin kunar rai ta shiga zubo da kayanta kasa.
Ganin yanda take zubo da kayan ne yasa ya mike ya karasa inda take, hannu yasa ya riko hannun da take zubo da kayan, yace " Bilkisu!"
Juyowa tai ta kalleshi idanunta sun ciciko da kwala tace " na d'auka kai kace in shirya kaya na?"
Yace " Na fada amma."
Tace " kanaso ka nunamin ni da kau ba d'aya bane? Kanaso ka nunamin matsalarka ba tawa bace?"
Bata taba nuna bacin ranta ba a iya zamansu tun kan suyi aure sai yau, hannunta ta shiga kokarin kwacewa.
Rungume ta yai a jikinsa, sai da yaji tayi sanyi da kokarin kwace kanta sannan yace " ba haka nake nufi ba, banaso insanyaki cikin damuwar da ni kaina bansan sanda zata kare ba."
Idanunta ta lumshe tace " menene tsakanin miji da mata? Na d'auka duk runtsi duk wahala su shanyesu tare, su birne matsalarsu sannan su taimaki junansu? Da wannan buri nai aure, taya zaka cemin inka shiga matsala in tafi gida? Bakasan gwara kace mu rabu saboda baka sona ko saboda akwai wani abu nawa da baka so ba?"
Kara rungumeta yai yace " ko d'aya, in fact a kullum nai sallah ina gode ma Allah daya bani ke a matsayin matata, wacce ban taba zato ba, sannan maganar bamu zama d'aya ba ko kad'an ba haka bane."
D'agowa tai ta kalleshi tace " me yasa kake tunanin fad'uwa? Baka tunanin kaine zaka kada ta?"
Murmushi yai yasa hannunsa d'aya a kan kafadar ta, tace " mai gaskiya baya faduwa, sannan Allah na tare dakai, muma muna ma addu'an samun nassara, inaji a jikina matsalar ka ta kusa warware wa, sannan da yardar Allah ba wanda zai cutar dakai."
Murmushi kawai yakeyi yana binta da kallo, tace " me? Baka yarda dani........."
Batai zato ba taji bakinsa cikin nata, shikansa bai san sanda zuciyarsa ta sashi hakan ba.
Sun dade suna aikama juna sakwan ni, abinka da wanda bai taba yi ba, jinsa ya dinga yi kamar ana angizashi.
Sam ya manta da alkawarin da ya d'aukarma kansa.
Jin kafafunta suna neman kasa d'aukarta ne yasashi sa hannu ya zareta zuwa kan gado, a hankali ya zare bakinsa daga nata, ya kai fuskarsa zuwa wuyanta tare da sa hannu yana kokarin rabata da kayanta.
Cak ya tsaya, tare da saurin mikewa idanunsa sunyi jaa sosai.
Kallansa tai ita kanta duk da tana tsoron wannan rana sai dai abinda takeji a yanzu dadi ne muraran.
Idanunsu ne suka hadu da juna, dawowa yai ya zauna tare da rungumeta tsam yace " what should i do?"
A hankali tace " akan me?"
Yace " the promise......"
Kanta ta sunkuyar tana murmushi, dan ya bata dariya.
A hankali yace " ya zanyi?"
Murmushi kawai takeyi, d'agota yai ya kalleta, idanunta a lumshe a hankali ya maida bakinsa cikin nata...........
Nace su Turab dai to😂
*************
Washegari da sassafe bawan da Magajiya ta aika ya iso, rabansa da gidan sarki yau sati d'aya kenan.
Tanajin shine ta ce ya shigo.
Yana gaisheta yace " Magajiya na samoshi."
Tace "yana ina?"
Yace " yana wajen gidan."
Tace yauwa na gode........
*THE LAST BATTLE 😄*
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*Gaisuwa, jinjina gareku Aminan Arziki 'yan Sauyi, Dizzy, Rabes, Faty Shafi'u, Yar Gaya, Salamah, Kozali, Sharubutu, J.B, Rambi, da sauran Yan Sauyi......
*85*
A hankali ya bud'e idanunsa, sannan ya kalleta, bacci takeyi akan hannunsa na hagu, haka kawai ya samu kansa da yin murmushi, sannan ya tuno abinda ya faru jiya.
Ya akai jiya idanunsa suka rufe? Sam ya kasa controlling din kansa? Har sai da ya maidata mace? Lalai jiya yaci sa'a Bilkisu tayi wankan tsarki, da tabbas yanda yaji jiya in har bata sallah baisan yanda zaiyi ba, abu yaji wanda tunda aka haifeshi bai taba ji ba.
Lalai wannan rana ta zamar mai ranar da bazai mantata ba, murmushi yai sannan ya tuno da, a da ko zaiyi tunanin aure sam zuciyarsa bata raya mai farin ciki.
Khadija zuciyarsa take kauna kuma ya tabbata in ba dai wani ikon Allah ba bayanda za'ai ya aureta, shikuma bayaji zan iya rayuwa da wata ba ita ba, sai dai a yanzu ya tabbatar abin ba haka bane.
In har ka samu mace wacce ta sanka, sani ba wai na suna ba, sannan wacce ta ke sanka, take kokarin farantama rai, zuciyarta da kuma suffarta masu kyau ne, mai addini, to lallai shikam yana gani a hankali zuciyar mutum zata koya ma san wannan yarinyar.
Zuciyarsa haryanzu tana so da kaunar Khadija sai dai baxai taba auranta ba, saboda har abada ya tabbata bazai taba manta abinda jininta suka aikata mai ba, sannan inya hukunta iyayenta me zaice da 'ya'yan da suka haifa nan gaba in har sun tambayeshi kakaninsu na bangarenta? Kuma abu ne na sarauta wanda zai bar tarihi, ko da ya b'oye musu ya tabbatar labari zai isa har kunnensu, mai zai ce dasu a lokacin? Iyayenta sune suka...........
Motsin da Bilkisu tai da kanta shine ya katsemai wannan tunanin, kiran Sallah ake tayi a massalaci, idanunta ta bud'e cikin bacci ta kalleshi.
Ganin idanunsa a bud'e shima ita yake kallo yasa tai saurin maida idanunta ta rufe, sunkuyowa yai ya sumbaci goshinta sannan yace " zanyi alwala."
Kai ta daga mai alamar to, yace " zan dan fita daga nan kina ganin ba matsala? Naga........"
Da sauri tace " zan iya." dan batasan maganar kunya takeji.
Kanta ta zame daga hannunsa a hankali, murmushi yai bayan ya mike.
Bandaki ya shiga yai alwala sannan yai waje.
Idanunta ta bud'e a hankali bayan taji alamar fitarsa, sannan ta mike zaune, yaye bargon tai, sannan ta mike a hankali.
Dama tasa an sanar da ita duk abinda ya dace tai, yanzu zamani yazi ilimin addini ya kara wadata balle a mata tonon silili.
Bedsheet din ta yaye tai toilet, a roba ta sashi ta zuba ruwa sannan tai wankan tsarki bayan ta gasa jikinta da ruwan dumi wanda sai data dafa a heater.
Kallo d'aya zakama yanayin tafiyarta ka fahimci ba daidai take tafiya ba, bayan tayi sallah ta dade tana ma mijinta addu'a kafin ta mike.
Turab kuwa a massalaci, bayan ya gama addu'oinsa ya fito shida Garzali bayan gari yayi haske suka fito wajen gari.
**********
Magajiya kam jin an taho dashi yasa taji wani nishad'i ya kamata, gari yana haske tasa aka kira kata matan sarki.
Bayan sun zauna ne ta kallesu tace " yau munada zama na shari'a da za'ai, hakan ne yasa nakiraku dan inji ta bakinku, da Abdulmajid da Abu Turab wa kuke ganin zai gaji Sarki?"
Kallanta sukai fuskarsu da murmushi sukace "Abdulmajid mana."
Tace " ba sai na tsaya bata lokaci na ba tunda kunsan abinda ya kamata, ina fatan zaku bi bayana anjima."
Kallan juna sukai kafin su amsa da to, suka taso suka fita, suna fita d'aya tace " matar nan tana neman maidamu yaranta, da izinin Allah d'an datake takama dashi bazai zama sarkin ba."
D'ayar tace "Ameen."
************
Gimbiya tayi kwalliya tana zaune a falo wata yarinya ta nemi izinin shigowa.
Bayan ta shigo ne ta mika kata wani dan karamin kwali na agoggo tace " daga fadar mai martaba nake, aikoni yai da agoggo wai aba Yarima Turab, sannan yana mai fatan alkairi."
Kallanta Bilkisu tai sannan ta amshi agoggon, tana shiga d'aki ta d'aurashi akan madubi dan ita kam bata ji hankalinta ya kwanta da agoggon ba
Sai daya gama shiryawa yazo kan madubi yana sa turare yaga kwalin agoggo, yace " wannan fa?"
Ta sanar dashi abinda yarinyar tace data kawo sannan tace " ni amma......."
Kwankwasa kofar da akai ne ya katse maganar, kofar ya nufa tare da zura agoggon yana tambayar waye.
Mai kula da Gimbiya tace itace sannan tace wai lokaci yayi, yce to.
Sannan ya kalli Bilkisu yace " Muje?"
Tace " ina?"
Yace " gun mana."
Cikin mamaki tace " harda ni?"
Murmushi yai sannan yazo inda take ya tsaya yace " bakyasan kije?"
Tace " inaso inje amma......."
Kasa tai da kanta alamar kunya.
Murmushi yai har hakwaransa suka fito yace " kunya kike?"
Ta mike tace " bafa haka bane, tafiya......"
Sai kuma tai shiru.
Yace " menene a ciki? Indai bazaki bane, bazan takura miki ba."
Ya juya, takunsa uku ana hudu tace " zanje."
Murmushi yai kafin ya juyo sannan yace " muje."
Komawa tai ta d'auko babban mayafinta.
********
Karfe 11 na safe an gyara babban d'akin da za'ai shari'a.
Basira itada Lantana sun iso gidan, dan Sarki yace duk a kira na cikin gida tunda shari'ar ta cikin gida ce, sai a kara shaidu.
A d'akin taro kuwa, Hisham na gefe a zaune daga gefe, dogarawa biyu na tsaye kansa.
Galadima da Barde da mai Shari'a su suka fara zuwa.
Sai Matan sarki ne suka fara isowa a mata, sannan Basira.
Magajiya ce ta iso cikin shigarta ta isa da jin kai da sanin akwai kudi da matsayi, gefenta Abdulmajid ne aka turoshi a kekensa.
Kallo d'aya tama Hisham ta d'auke ido sannan taje gaba ta bangaren Mata ta zauna, bangaren maza kuma akasa Abdulmajid wanda ya zamana yana saitin ta.
Ranta ya baci ganib ta riga Abu Turab zuwa.
Sanar da isowansu akai, shigowa sukai shida Gimbiya a tare, tayi iya kokarinta na ganin ta saita kafafunta kar a gane, shikansa Turab saboda ita yake tafiya a hankali.
Suna shigowa aka zubo musu ido, Abdulmajid sai a wannan lokacin shima ya ganta.
Ba shakka ta hadu sosai, Magajiya ce ta dago ta kallesu, takaicinta daya yanda ita kanta sai da kayan jikin Bilkisu suka birgeta, Turab ya samu gu ya zauna kusa da Abdulmajid wanda hakan yasa ta zauna kusa da Magajiya dan Basira ce ta nuna mata gun zama.
Bilkisu sai data gaida Basira ta gaida matan sarki sannan ta kalli Magajiya tace " Umma Barka da warhaka."
Magajiya ta kalleta, bata amsa ba.
Basira tai murmushi tace " Bilkisu da alama bakisan tsarin mu na masarautar zazzauba, a ka'ida sai kin fara gaida Magajiya.
Bilkisu wacce dama tasan da hakan, tai murmushi sannan ta kalli Magajiya tace "Umma nayi laifi kenan?"
Magajiya tace " karki damu ai bakisan tsarin bane."
Bilkisu tace " godiya nake." sannan ta d'auke kanta.
Shigowar Sarki ne yasa aka tsaya da gaishe gaishe, mai martaba ya samu guri ya zauna.
Sannan akai addu'a aka tunatar da abinda akazo yi.
Turab yace "Takawa ina neman izinin shigowar wata bakuwa wacce take da dangantaka akan shari'ar nan."
Sarki yace " to bismillansu."
Shigowar Matar Hisham ne yasa Magajiya ta kalli Turab, murmushi yai sannan ya d'auke kai daga kanta, kallan juya sukai da sauri shida Abdulmajid ganin wacce ke tafe a bayanta, Khadija? Me ya kawo ta.
Khadija kuwa wacce d'an aiken ita ya sanar mawa tace ma Mahaifiyarta ai tare aka ce suzo, ta kalli Turab sannan ta kalli Abdulmajid.
D'auke kai tai har suka zauna.
Mai shari'a ya kalli Magajiya yace " Magajiya ta kawo nata sharhin a game da shari'ar da akai kwanaki, in akai duba da kalamanta tabbas suma suna da nasu ma'anar, hakan ne yasa aka daga shari'ar zuwa yau."
Sarki ya kalli Abdulmajid yace " Abdulmajid sanar dani da bakinka a kuma cikin mutanen nan, wanene yasa a kama ka? Mahaifiyarka tace Turab ne, shi kuka Turab yace Hisham ne ya nemi halakashi kai kuma ka sadaukar da kanka, wanene yake fada mana gaskiya?"
Abdulmajid ya kalli Magajiya wacce itama kallanshi kawai take yi, Khadija ya kalla wacce itama shi take kallo.
Juyowa yai ya kalli Turab, wanda yake kallan Kasa.
Sarki yace " Abdulmajid!"
Abdulmajid yana kallan Magajiya yace " ni kaina bansan wanene ya sa aka kamani ba."
Magajiya ta kalleshi tace " mene?"
Turab kam ko gizau baiyi ba.
Magajiya ta kalli Sarki tace " ta yaya Turab bazai nemi halaka Abdulmajid ba? Bayan yasan in akaji sirrin mahaifiyarsa shida sarauta sai dai a lahira? Amma in ya halaka Abdulmajid ko ma menene shi kadai ne jinin sarki dole ne a yafe mai."
Galadima ya kalleta yace " sirri? Mai kike nufi kenan?"
Kallan Sarki tai wanda idanunsa suka fara canzawa, sannan ta kallu Turab wanda ta tabbatar maganin ta yafara aiki dan yanata lumshe ido kamar mai bacci sannan ta kalli Basira tace " Basira? Me zakice?"
Umma kam jikinta duk ya fara rawa, Magajiya tace " ina neman izinin shigowar mai bada shaida."
Sarki ba yanda ya iya dole yace " ya bada"
Shigowar mutum ne yasa gaba d'aya jikin Basira ya hau rawa, Bilkisi dake kusa da ita tasa hannu ta rike hannunta tana kallanta, kallan Turab tai wanda gaba daya ta rasa meke damunshi dan kamar baya baya cikin hayyacinsa.
Basira kam duk ta gama rikicewa. Ganin haka yasa hankalin Sarki ya tashi.
Magajiya tai murshi sannan tace " Basira kin gane wannan? Badai zaki mance da wanda ya amshi budircinki ba?"
Cikin tashin hankali kowa yaji maganar, nan fa aka fara kananan gulma, Sarki ya runtse ido saboda tsananin takaici.
Turab wanda ke kokarin maido da hankalinsa ne ya kalli wanda ake magana, cikin layi.
Kallo d'aya zakamai kaga alamar shaye shaye da talauci a jikinsa, tsugunne yake yana dan cicila ido.
Kallan Basira yai wacce gaba d'aya jikinta rawa yakeyi.
Bilkisu ganin ba wanda yai magana yasa ta kalli Turab da sauri, gani tau kamar baya hayyacinsa.
Khadija itama kallan Turab tai dan kowa ya san zaiyi magana, yanda taga yanayi da kansa ne yasata kuramai ido tana san gano meke faruwa.
A zuciyar sarki kuwa addu'a kawai yake akan Turab yai magana.
Bilkisu ce ta kalli Magajiya wacce ta saki wani murmushin mugunta tare da kallan agoggon hannunsa ta gefe, a tsorace Bilkisu ta kara kallan agoggon tabbas bata karasa sanar dashi ba dazu aka kwankwasa kofa.
Matsowa tai gun Basira da sauri ta rada mata abu a kunne.
Basira ta kalleta sannan ta kalli Turab wanda idanunsa ke juyewa.
Mikewa tai ta zo inda Turab yake, tunda wannan mutumin ya hangota ya taso da sauri ya biyota yana neman rikota yana cewa " kece ko? Kamar kece? Kai na tabbatar ma kece."
Da sauri Dogarawa suka rikeshi, nan aka shiga tambayar wanene wannam din? Kowa fuskarsa dauke take da tambaya.
Basira ta daure ta karasa inda Turab yake, kowa yana jira yaga mai zatai, da karfinta ta dage ta wanka mai wani wawan mari wanda yasa kowa kallan Turab.
Bilkisu da sauri ta mike ta isa inda yake, Turab kallanta yai.
Basira tace " bakada hankali ne? Ta ina zaka bari magani ya rinjayi jikinka? Bayan ni ina cikin tashin hankali? Ta ina......."
Kuka ne ya nemi kamata, da sauri Bilkisu tasa hannu ta balle agoggon ta zareshi daga hannunsa, sannan ta kalli Turab wanda ya ke kallan Mahaifiyarsa gaba daya idanunsa sun canza.
0 comments:
Post a Comment