Bata zame ko ina ba sai gidan malamin ta haka ta kwashe komai ta fada masa,,kulli magani ya bata sannan yace mata ta tabbar fatima ta tsallake wannan maganin idan har ta tsallake shi cikin zai zube kuma itada kara haihuwa har abada,,,cikin murna ta ciro kudi ta bashi,,,
haka ta kara kamo hanya buguzum buguzum tana tafiya tana sake saken mugunta cikin ranta,,koda ta isa ta tarar da fatima zaune bakin dakin,,yaranta kuma kowa ya tafi yawon shi,,ko kallon inda fatima take bata yiba ta shige dakinta,,,ita dai fatima baiwar allah tunda ta mata sannu da zuwa taji bata amsa mata ba taja bakinta tayi shiru,,daga karshe ma dakinta ta shige tayi kwanciyar ta
asabe na daki amma sake sake take yi a ranta na yadda zata zuba wannan maganin a kofar dakin fatima,,,lekawa tayi taga tsakar gidan ba kowa komawa daki tayi ta dakko maganin sannan ta fito ta fara tafiya a hankali har takai kofar dakin fatima da take can daki tana barci bata san wainar da ake toyawa ba,,,,bude kullin maganin tayi sannan ta barbada shi a duk kofar dakin sannan ta juya ta koma tana murmushin nasara...
kiran sallar la'asar ne ya farkar da ita daga barcin da takeyi buta ta dauka domin zagawa bandaki kafin tayi alwala,,bata ko kalli kofar dakin ba ta tsallake tayi wuce,,,tana wucewa taji kamar an tsikare a mararta bata kawo komai ba a ranta ta shige bayi,,,,ta tsugunna da niyyar yin fitsari a maimakon ya fito sai jini taga yana fita kamar anbude famfo,,,cikin tashin hankali ta mike da sauri amma kuma sai taga jinin nabin cinyoyinta ga wani murdawa da mararta keyi,,dakyar ta lallaba ta fito ta koma daki duk inda tabi sai jinin ya zuba...
i
asabe na daga kofar window din dakinta tana ganin komai farin ciki ne ya kamata ganin aikin ta yaci,,,murmushin mugunta tayi tana fadin ni asabe wazai ja dani ya kwana lafiya ballantana wata karamar alhaki wai fatima kinta gani kenan keda haihuwa har abada sai dai kiga mata nayi...(nidae nace ta allah bata kiba asabe🤨🤨)
muhammadu kamar yasan abinda ke faruwa yau yaji yana son dawowa da wuri haka ya kamo a er kekensa ya taho gida,,,dakin asabe ya fara shiga,,kallon da yaga tana mai ne yasa shi kara kallonta,,ganin zai dagota ne yasa ta fara magana,,sannu da zuwa ai yanzu na dawo daga wajen kawu yace yana gaesheka,,,toh kawai yace ya fita ya nufi dakin fatima,,,asabe bata so ya dawo yanzux tasone jinin ta yayi ta zuba har azo a samu gawarta,,,,(MUGUWA😡)
jinin da ya gani kofar dakin ne ya sashi karasa wa da sauri cikin dakin inda anan ne yaga tashin hankali,,,kwance take cikin jini shame shame sai numfashin ta dake fita kadan kadan,,,cikin tashin hankali ya karasa inda take tare da tallafo yanayin daya ganta ne yasa shi fashewa da kuka,,,,da yaga haka bazata mai ba sai ya sabeta a kafada yayi waje da sauri,,haka ya rinka ratsawa har ya isa da ita karamin asibitin dake garin,,,da sauri aka amshe ja aka shigar da ita ciki,,,shi kuma ya koma gefe yana zirga zirga tare da tinanin me ya jawo mata hakan shidai yasan lafiya lau ya barta kafin ya fita,,,,
sai dai aka share awa biyu a kanta da kyar likitan ya samu ya tsayar da jinin dake zuba sannan aka mata allurar barci,,,likitan na fitowa muhammadu ya taso da sauri yabi bayan shi sai da ya shiga office din likitan kafin ya fara tambayar shi halin da fatimar ke ciki,,,,bayani ya fara cikin nutsuwa,,,,gaskiya duk iya dubarwa da mukayi bamuga wata matsala ba da har yasa wannan jinin zuba ba,,,sannan kuma har yanzu cikin nanan bai fita ba sai dai zaka bari zuwa gobe sai a sallameku,,,farin cikin da muhammadu yaji a lokacin bai misaltuwa,,,gidan su fatima yaje ya fadawa mamanta abinda ke faruwa tare suka tawo asibitin sannan shi kuma ya koma gida dakko kayan da zasuyi amfani dashi,,,
sai da fatima tayi kwana2 a asibiti jiki kam alhamdulillah taji sauki sosai,,ba wanda baije gaisheta ba amma banda asabe,,,,dan tunda taji ance fatima ta samu sauki take cikin takaici da bakin ciki
haka sanda fatima ta dawo duk makota na shigowa yi mata ya jiki asabe naji tana zaune a dakin tana fama da bakin cikin da ya cika mata zuciya,,,
haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin fatima na girma amma daga ita sai muhammadu suka sae tanada ciki kowa yana tinanin cikin ya zube ciki kuwa harda asabe,,,wadda keta murna shiyyasa yanzu kota kanta bata bi
ita a tinanin ta ai tariga ta gama da ita
🤣🤣🤣Asabe sai dai kiji kukan baby aradu
Pls kuyi hakuri da wannan
Ur's princes deejerh💝
[16/01, 18:48] khadija ahmad dija Marubuciya Barauniya ce Frien Din Hassn: ✨✨BA DON SHIBA✨✨
By Princess Deejerh
New Writer
Ina kuke 6ters na kwarai wannan shafin sadaukar wa gareku ina yinki irin totally dinnan
Aisha mohammed sani(Zayeeshart)
My Nusaiba mu'hd auwal(Nusy bea)
Ruqayyerh tertherr risqua(er kanwata)
Umma muhammad(Ummu aiman)
Pharteemah Ahmad(teemah sulfat)
Phertymah harun(mommy kd)
Ga masu son shiga group dina BA DON SHIBA FANS CLUB ko kuma PRINCES DEEJERH NOVEL sai ku tuntubeni ta wannan numbers
08104609894
09061274993
08060972795
07033851935
Page6⃣6⃣to7⃣0⃣
Haka fatima da muhammadu suka cigaba da rainon cikin da ba wanda yasan dashi domin kuwa kullum da hijab take kuma dama cikin nata bamai girma bane
Ranar wata talata da safe fatima ta fara nakuda bata sha wata wahala da kanta ta santalo lafiyayyar ya'rta mai kama da larabawa dan kuwa fara ce jajir babu ta inda ta bambamta da uwartt,,,farin ciki kuwa gurin muhammadu bai irguwa da kanshi yaje har gidan su ya taho da kanwar innarta ita tayi mata komai ta yanke ma jinjirar cibi ta wanke ta tass sannan aka nadeta a wani farin towel,,sannan ta hada ma fatima ruwan itama da kanta tayi mata wankan,,kafin ta dumama mata tuwaon dawa ta kawo mata,,,idan kaga fatima ba zaka ce itace ta haihu ba dan kuwa lafiyarta kalau ita da jaririyarta,,,muhammadu ne ya shigo dakin hannun sa rike kayan tea da siyo mata gurin ya nufa tare da daukan jinjirar fuskar nan fal farin ciki da annushuwa,,sai da yayi ma yarinyar addu'a kafin yayi mata huduba da suna HAUWA'U JIDDAH,,,fatima tayi matukar farin ciki da yasa mata sunan innar ta,,,sai a lokacin mutane suka fara shigowa gidan suna yi mata barka suna santin kyan yarinya,,,ita dai saidai kawae tayi murshi idan mutane na tambayar ta wai dama ciki gareta,,,ko en uwanta da suka zo mamaki suka rinka yi tare da godema allah,,,
shigowarta kenan gidan taga mutane wasu na fitowa daga dakin fatima wasu na shiga ga kuma en uwanta zazzaune a kofar dakin,,,mamaki takeyi tow meye akayi haka da har dangin mayyar can suka zo suka wani cika musu gida da hayaniya inama mutuwa shegiyar can tayi ai wlh da sai ta kira masu kidan kwarya sun buga mata ta cashe,,,sallamar muhammadu ce ta katshe mata tunanin da takeyi ko amsar sallamar bata yiba ta tsaya kallon shi ganin sai wani washe hakora yake,,,katse yayi tare da fadin amm... asabe munfa samu karuwa yau a gidan nan,,,,be tsaya jin me zata ceba ya cigaba da fadin dazu fatima ta haihu mun samu ya' mace jiddah,,,tana zaunau a kan kujera ertsugunne amma sai data wuntsila tare da bajewa a dakin tayi zaman yan bori,,,cikin zaro ido tace wata fatiman,,,hanyar waje yayi yana fadin fatima nawa garemu a gidan tareda ficewa,,,yana fita ta zube a kasa burgima ta fara a tsakar dakin ta rasa inda zata tsoma ranta kawai saita fashe da kuka da wannan ranar ai gara mutuwar ta malam ya cuceni ya yaudareni,,kuka takeyi kamar karjmar yarinya,,,fatima ce wai ta haihu ta kara maimaitawa wallahi sai naga bayanta ita da shegiyar ya'r tata,,,
Haka akayi suna cikin kwanciyar hankali rago biyu manya manya muhammadu ya yanka mata bayan kaya da ya dinka mata itama jiddah ya saya mata kaya sosae ga kuma wanda dangin fatima suka mata komae dae alhamdulillah,,,tun mutane na tambayar fatima ina kishiyar ta take har suka bari,,dan asabe bakin cikin ta take nunawa kiri kiri ba abinda ta taba ko taci wanda ya danganci haihuwar fatima kuma bata fasa bin malaman ta daka ganta kasan bata da kwanciyar hankali...
taron suna ya watse kowa na sam barka fatima ta cigaba da renon yarta itada muhammadu,,,asabe saidai ido dan ita kadai tasan tsiyar data shuka kuma tasadm tabbas wannan sai tayi nasara domin wannan ba irin wancan bane...
Wata ranar sati muhammadu ba zai taba manta ta ba da kuma iyayen fatima da en uwanta,,,a safiyar da aka nemi fatima sama ko kasa aka rasa ba inda baa je nemanta ba a kauyen kiyawa har makotan su amma ko sawunta ba'a gani ba,,muhammdu suma yayi sai da ya kusan awa biyu kafin ya farfado ,,,yana farfadowa ya tashi tare da nufar kofar gida mutane suka rike shi amma ina turjewa yakeyi yana fadin abar shi yaje ya nemo fatimar sa,,,basu kara shiga tashin hankali ba sai da jiddah ta fara kukan yunwa aka rasa yanda zaayi innar fatima ce ta amshi yarinyar tana jijjigata amma ko alamun yin shiru batayi,,,fashewa da kuka kowa yayi ganin muhammadu na kuka wiwi kamar mace,,a yau asabe tayi rawa tayi juyi tayi hawayen farin ciki burinta ya cika,,dama sabon malaminta yace kurciya zaa mata itada dawowa garin kiyawa har abada,,,
Tsawon sati biyu kenan ba fatima ba labarinta jiddah kuwa tana gurin innar fatima itake renonta a yanzu kudi muhammadu ya bada isassu aka siyo madarar jarirai kuma da akayi saa tanasha sosae,,,muhammadu a yanzu rayuwa kawae yake domin kuwa asabe saida ta mallake shi tsab komai sai idan ita tace yayi tsoronta yake matuka yanzu,,kudi take amsa a gunsa koda yaushe tana wadakarta ita da yaranta shiko ya zama konko yanzu
BAYAN SHEKARA DAYA
a yanzu kam muhanadu baida komai asabe ita da ya'ya'nta sun gama cinye kudin shi tsab yanzu shagon da yake zuwa ma ankwace saboda rashin biyan kudin haya,,,
jidda kan yanzu shekarar ta daya tana gudun ta koina har anyaye ta,,yarinya me kyau me shiga rai ga gashinta dogo baki sidik daka ganta kasan jikar fulani ce,,,
A wannan lokacin ne kuma muhammadu ya samu aiki a garin kaduna na gadi saboda haka duka zasu tafi harda asabe da yaran yaso yabar jiddah amma asabe ta rura wuta sai da ya amsota,,,
haka suka tattara suka koma garin kaduna da zama a gidan suke zaune a BQ a lokacin ne jiddah ta fara shiga matsalar rayuwa duk da kuwa kankantar ta amma haka asabe ke mata mugunta kalakala,,ana cikin haka ne malam muhammadu ya sayi wani dan karamin gida da kudin da yake ajiyewa suka koma can,,,sun koma ba dadewa malam muhammadu ya fara ciwon ajali kwana2 yayi yace ga garin ku nan,,,asabe tayi kukan mutuwar shi nadan lokaci ta share ta cigaba da rayuwas itada yaranta,,,
mutuwarsa tasa jidda kara shiga matsalar rayuwa asabe sai taga damar bata abinci yawo take kamar almajira a cikin unw a lokacin shekarta 12 su rabi kam a lokacin anza entayi galan ana kawowa inna asabe kudi tana amshewa tana murna
ana cikin irin wannan rayuwar ne ALLAH ya jefo ammar cikin rayuwar jiddah ganin farko daya mata yaji ta shiga ranshi ga kuma tausayinta da yakeji saida ya tuntubi makota suka bashi labarinta tofa tunda ga wannan rana ammar ya fara kula da jidda da kansa ya sata a makaranta ya dinka mata uniform,,shike bata duk wata kulawa,,,inna asabe zata mai rashin mutunci ya nuna mata nashi rashin mutuncin yafi nata haka nan ta hakura badan ranta na so,,,,,
CIGABAN LABARI ku biyo a next page
Ur's princes deejerh💝
[16/01, 18:48] khadija ahmad dija Marubuciya Barauniya ce Frien Din Hassn: ✨✨BA DON SHIBA✨✨
By Princes Deejerh
New Writer
AMEENTA WRITERS ASSOCIATION🤝
Page 7⃣1⃣to 7⃣5⃣
CIGABAN LABARI
Tun dawowar inna asabe daga wurin bokan ta ta kasa zaune ta kasa tsaye.domin kuwa a yaune take son ta gama duk wani mugun kullin ta a kan jiddah ta rasa yadda zatayi ta shiga dakin dabara ce ta fado mata dakin ta shiga ta dauko kudi sannan ta nufi dakin jiddah.kwance ta tarar da ita amma ba bacci take ba tana ganin shigowar inna asabe ta mike tare da fadin sannu inna ashe kin dawo,eh tace‘’sannan ta fara fadin yauwa jiddah dama so nake na aikeki gidan mutuniyar ki maman salaha ki amso min kayan na 100.
to tace sannan ta dauki hijab ta zira takalmi sannan ta fita.
fitar ta keda wuya inna asabe ta bankade er yagalalliyar katifar dubawa tayi taga ba wani rame a wajen kuma idan tasa a haka zaa gane wuka ta dauko ta samu bakin katifar ta bula sai da taga yayi zurfi sannan ta barshi ta ciro layar dake daure a habar zanin ta ta tura ciki kara komawa dakin ta tayi ta dauko zare da allura ta dinke bakin wajen sai da ta kalla dakyau ta ga ba wani alamun da za'a gani sannan tayi murmushin mugunta tace‘’jiddah na gama dake kodah wannan na barki na rama bakin cikin dana kunsa na uwarki da naki,mikewa tayi ta fice daga dakin.
AMMAR ne zaune a daki shi kadai yana hutawa yau bashi da lecture ya kara kyau ya kara fari fatar nan sai glowing take saboda hutu da amfani mayuka da alamu dai kasar india ta amshe shi,wani dan karamin passport ne a hannun shi tun dazu ya kura masa ido yana duk sanda ya kalli ta jikin hoton sai gaban shi ya fadi,wayar sa dauko domin kiran ta kamar dai ko yaushe yauma a kashe take,
wurgi yayi da wayar cike da takaici yana fadin why jiddah zaki kashe waya bayan kinsan zan nemeki.
Abbas ne ya shigo dakin tare da fadin kaga na jiddah ba da kanka asare idan aka ga bacin ranka to jiddah aka tabo.
kallon shi ammar yayi kafin ya kaude kai yana fadin saura 2 years na gama karatuna gaskiya yayi min nisa inaso insan halin da jiddah ke ciki nifa ina ji a jikina wani abu na faruwa.
abbas ne ya katse shi tare da fadin "to yanzu me kake nufi kenan?uhm idan kayi hakuri kamar fa gobene yanzu 3years kenan da zuwan ka 2years zai maka wahalan karasa,ka daina sa tunani a ranka jiddah tana nan lafiya.
kallon shi ammar yayi tare da fadin ALLAH yasa hakan.
Ba wani dadewa tayi ba ta dawo hannun rike da kayan miya dakin inna asabe ta nufa ta bata,har zata juya sai kuma ta dawo tana fadin"kawo in gyara,A'a kibar shi kawae jeki cigaba da baccin ki..
dakin ta ta koma ta cire hijabin har zata kwanta ta tuna gobe suna da test,jawo jakar ta tayi sannan ta fara duba littafan ta sai da ta kwashe kusan 1hr sannan ta ajiye ta kwanta kafin la'asar tayi.
Kiran sallah la'asar ne ya farkar da ita tana son tashi tayi sallah amma ta kasa gaba daya jitayi gabobin jikinta na saki.
komawa tayi ta kwanta tana fadin anjima nayi,
haka ya faru a lokacin sallar magrib.
inna asabe ce zaune da su rabi duk cikin su bamai kayan arziki HALADU kuma na gefe yana cin abinci.
inna asabe tace"Rabi dake da asiya ku zabar ma jiddah kaya a cikin naku amma fa duk kananu kamar dai na jikin ku din nan,to suka ce tare da mikewa dan sun riga da sun san manufar hakan..
kallan kayan take daya bayan daya sanda inna asabe takai mata kuma tana fadin wai nata ne su rabi suka bata.
amsa tayi kawai amma har cikin ranta kayan basu mata ba amm kuma ta kasa musawa....
Ur 's princes deejerh💝
*✨✨BA DON SHIBA*✨✨
*By Princes Deejerh*
*New Writer*
*AMEENTA WRITERS ASSOCIATION*🤝
*Page* 7⃣6⃣ *to* 8⃣0⃣
Inna asabe tana ganin *jiddah* ta amshi kayan ta koma daki tana murna ita da 'ya'yan ta.
rabi ta fara magana cikin gatsali tare da fadin."inna anya kina ganin wannan aikin yayi kuwa"
kallon ta inna asabe tayi sannan tace" ke yarinya ce amma nina yadda da aikin sa saboda yadda mutane ke tururuwar zuwa gurin sa"
kin san da aikin sa bayayi ai ba za'a rinka masa wannan layin ba.
kuma ai na fara ganin canji nifa naji a raina tabbas wannan karon wahala ta tazo karshe.
ba abinda zai hana *jiddah* wulakanta a idon duniya.
nayi alkawrin haka ko zanyi yawo tsirara kuwa.
rabi ce amshe tana cewa"ai innah idan har wannan aikin baiyi ba to ki hakura kawai ki barmu da ita tunda yanzu wancan mahaukacin *ammar* din baya nan"
ke dallah rufe mana baki ke mai zaki iya yi mata duk abinda zaki mata sai dai taji rauni a zuciyar ta.
amma idan har abinda nake so ya tabbata tofah ba ita ba duk wani maisonta sai ya shiga bakin cik....maganar ta ce ta katse tare da kallon bakin kofar.
mikewa sukayi gaba daya tare tare da zare ido.
duk cikin su ba wanda ya iya furta kalma ko guda daya.
kallo nakai ga kofar domin inga me ya kada su inna asabe haka.
nima kaina idon na zaro ganin *jiddah* sanye da daya daga cikin kayan da rabi ta bata.
wando ne dogo pencil amma sa crazy ya kamata sosa.
sai rigar pink colour da kadan ta wuce cibiyar ta itama ta kama ta tsam kirjin nan kamar zai fashe saboda cika.
karasowa tayi cikin dakin tana murmushi.
rufe baki inna asabe tayi tare da kallon gefen da rabi take.
a tare suka maida kallon su kan jiddah,
kusa da rabi tazo ta tana fadin"inna baki ga yadda kayan suka mun kyau bane naga baki yaba ba".
washe baki tayi sannan tace"ai ni bakin magana ma na rasa saboda kyan da kika yi bazai fadu ba"
dama cewa nayi barin ingwada kayan ko zasu min kyau bari inje in cire.
da sauri inna asabe tace"A'a ke ko daga saka kaya sai ki cire ki bari mana sai anjima.
kinga kuwa dama rabi zataje kome suke cewa abin ma batdee ko?ta juyo tana kallon rabi.
dariya duka suka kwashe da ita ganin inna asabe bata iya fada ba
sai da suka gama dariyar su kafin rabi tace"inna birthday ake cewa fa"
yauwa to naji zaki raka rabi can kinji ko jiddah.
amsawa tayi saboda hakanan taji tana son zuwa wajen birthday din.
karfe 8 daidai rabi ta gama shiraya wa cikin wasu kaya da marabar su da tsirara kadan ne.
wasu kayan ta kara ba *jiddah* ba irin na dazun ba wannan ma dai wandone pencil black shima duk an masa crazy.
sai riga me hannun vest itama ta matse ta sosae sai er karama wadda zata daura a sama.
dama kanta a tsefe yake gashin nan ya zubo har gadon bayan ta tayi kyau har ta gaji.
suna gama shiryawa suka yima inna asabe sallama wadda ke farin cikin ta ya kasa boyuwa.
wata tsaleliyar mota ce a kofar gidan da alamu dama su ake jira.
rabi ce a gaba saboda haka ita ta fara nufar inda motar take.
tana zuwa aka bude mata bayan mota ta shiga kafin jiddah ta zauna a kusa da ita.
sai a lokacin wa inda ke cikin motar suka lura ba rabi bace kadai.
su hudun e uku maza mace daya.
dukan su kallon jiddah suke cike da maita dan sunga er yarinya gata kuma komai yaji.
wani ne a cikin su yace ma rabi wannan bea din fa.
bata kalle shi ba tace"kanwata ce"
gaskiya kanwar nan taki ta tafi dani ya fada yana lashe baki kamar tsohon maye.
kada ka damu kawai kawai rabi tace"
har suka isa gurin bai daina kallon ta ba.
ita kuma gaba daya jinta take a takure ganin irin kallon da yake mata.
fita gaba daya sukayi a motar har *jiddah* gurin tsiit da alamu dae har anfara.
mu shiga kawai mansu inaga fa har an fara.
wanda a ka kira da mansu din ne ya karasa kusa da tare da kamo hannun ta.
kallon shi tayi da sauri tare da kokarin janye hannun ta.
rabi ta kalle ta girgiza mata kai hakan ne yasa ta kyale shi.
shi kuwa wani farin ciki ne ya mamaye zuciyar shi.
0 comments:
Post a Comment