Rayuwa ta sauya mana dani da ɗan mijina, nida tun ran da ya mayar dani matar sa ban kuma ganin shi yayi ƙiyamul layli ko azimin na shi ba a zuciyata nakan ce daman ba don Allah ake yi ba, sosai na matsa wa aliyu akan muje china ya ƙara ganin dr. ɗin nasa, daga ƙarshe ya yarda in da yai mana visa tare muka luluƙa birnin sin,
Mun sauka Beijing daka birnin china inda muka sauka ana suburda sanyi, don haka kullum muma manne da aliyu na😘 love one tin tin, yaje ya ga dr. ɗin nasa inda ya shaida masa ba wani matsala amma ya dinga gujewa da abinda zai dinga ɓata mata rai, kasancewar da turanciyayi bayanin nasa ya sa na ɗan fahimci wani abin, amma ba duka kasancewar accent ɗin chinese ya fita daga cikin maganar sa don haka ganewa sai ka nutsu sosai
sai yanzu na fahimci dalilin da zakuga sanyi na wucewa sai kiga mata suna laulayi, ashe su maza kasuwar su ce take buɗewa in ana sanyi, ko ya ka ɗan taba namiji sai kaji ka a ƙasan sa, ba damar kana cikin murna kace zaka rungume mijinka abi na gaba da zaka fuskanta shine fuskar ka tana kallon ceiling 😂😂 wayyo gani sabon shiga amma hakan bai sa aliyu tausaya min ba
watan mu biyu a china kasancewar nan ma wani wurin aiki wa mijina kuma ayadda naji anan ya fara samun arziƙin sa, nakan bishi deport ɗin in har jirgin shi daya ɗauko kaya ya iso, ina mamakin ganin irin maka makan jiragen ruwan da mijina ya mallaka at his age, aiki ne sosai ba ƙarami baya faɗa
sai da muka shafe wata biyu sannan muka kama hanya inda muka sauka ƙasa mai tsarki, nai murna nai kuka wai yau nice a ƙasa mai tsarki, mun yi ziyarar mu sosai a madina, ba inda bamu je na tahiri, inda da muka je dutsen uhud na siya dabinon ajwa don gashi nan baja baja kamar basa so, akwai ɗanye akwai busash she ni dai busashen na siya don tsaraba zanyi
satin mu biyu a madina mukai makka sai da muka tsaya a zul hulayfa inda ake ɗaukar niyyar ummara in ka taho daga madina masallaci ne babba sosai da banɗaku na saboda wankan ɗaukar niyya umma,
mu ka ɗau niyyar umara, mukai wanka muka sa haramin tare da yin sallah raka'a biyu kamar yadda yake a sunnan sannan muka shiga mota muka kama hanyar makka
tafiyace miƙaƙƙiya daga madina zuwa makka inda nai ta mamakin wai wannan doguwar tafiyar ma'aiki (saw) da sayyidina abubakar suka yi daga makka zuwa madina don tabbatar da addinin islama, wanda mu muka zo muka same shi a cikin ruwan sanyi gaskiya dole ne ajinjina musu
sai ƙarfe biyun dare sannan muka ƙarasa makka , wai nice yau a garin makka abin kamar a mafarki, direct hotel muka nufa wanda yake a unguwar bin laden, bashi da nisa sosai da haramin,
sai gab da asuba sannan muka je haramin don yin umara, tafkeken masallaci na ci karo da shi, nai godiya ga ubangijin talikai, nayi addu'ar shiga masallaci na shiga, muka shiga har can ciki inda haramin yake, ɗawafi muka kama yi sannan bayan mun gama aliyu ya jani har jikin ka'aba don in sunbace ta tare da yi adda'a nayi kuwa sosai da sosai har mahaifiyata da bata duniyar nan sai da tasan na zo ɗaki mai tsarki yau sannan daga ƙarshe na haɗa da dukkan ƴen uwa musulmai duk na addu'e mu da fatan mai duka zai karɓa.
V
Mm
ko da muka gama ummara, mu ka koma masaukin mu don hutawa, kwanan mu takwas a makka sannan muka wuce jidda inda daga nan muka wuce dubai don aliyu yana da aikin da zai yi anan, kwanan mu huɗu a dubai ya gama abinda ya kawo shi daga nan sai ya tsiri cewar muyi yawo don ganin gari, ni kuma a lkcn ba abinda nake so da wuce bacci, da na ɗan zauna sai gyangyaɗi sai bacci, na ɗauka ko na gajiya ne har aliyu yana tsokana ta wai bazan iya yaƙi ba tunda daga yin ummara na tsiri bacci ba ji ba gani
ganin baccin nawa kamar harda rashin lfy yasa aliyu matsa min muka je asibiti, ko da muka je asibiti bayan dogon bincike ya nuna cewar ina da shigar ciki har na sati takwas da kwana biyar, inda alamu suka nuna a china na samu wannan cikin
farin ciki waken aliyu kamar ya zuba a ƙasa ya sha yai farin ciki sosai har kyauta yayi wa dr ɗin daya dubani mai tsoka, a hanyar mu ta zuwa gida ne ya dameni
"wai nine nayi cikin nan, da gaske, don Allah ya akayi nayi cikin nan, kamar mafarki fa haka nake gani wai nima daga ƙarshe dai zan ga wanda zan ki ra nawa na kaina" ya dinga sunbatun sa shi kaɗai ni daya ishe ni ma kwanciyata nayi nayi kamar ina bacci har na gasken ya zo yayi awon gaba dani
sama kawai naji anyi dani ashe har mun zo hotel ɗin namu bansani ba, da muka shiga ya dire ni akan gado
"wannan cikin naki calls 4 celebration, dole ne muyi celebrating samun ciki ya faɗa cire rigar sa dana ga yana yi yasani na fahimci irin celebration ɗin da zamuyi kai namiji dai sai dai abarshi na faɗa araina
haka aliyu yai ta nan nan da ni akan cikin nan dana samu har tambaya yake yi wai ina ji motsi don Allah kunji wani zance, ko da muka koma nigeria ma haka kulawar tashi bata ragi ba nan ina samun kulawa sosai daga gare shi ko yana office ne yai ta doka min kira mu wuni muna abu ɗaya yana tambayata ya nake ji ko ya fara motsi ni sai dai in bishi da a a har yanzu, da abinya ishe ahi wai babyn be fara motsi ba ya kwashe ni sai asibiti inda yai musu compain na cewar babyn bai fara motsi ba
an duba ni inda aka tabbatar da lafiyar babyn sannan aka ce mana motsi sai nan da wata uku a lkcn yana da wata biyar kenan sannan hankalin aliyu ya kwanta muka dawo gida, bana laulayi ko kaɗan kuma duk abin da na samu ina ci ina ci ƙamshin turare ne kawai bana so don haka dole aliyu ya hakura da sawa
yau tj ya kawo mana ziyara, ya shigo har part ɗina don mu gaisa, inda naji ƙamshin turaren sa yai min daɗi har wani lumshe ido nake don daɗin sa da nake ji, suka ƙaraci hirar su ba abinda na fahimta tunda yawancin maganar tasun akan harkokin su ne don haka ne ma yasa ban samu baki ba ni dai kawai shaƙar ƙamshin turaren nake yi ina lumshe ido na kamar mai jin bacci
ko da tj ya tashi tafiya sai na ɗan bata raina,
"lfy kuwa madam" Inji tj
"ƙamshin turaren ka yayi min" na amsa, aliyu ne ya doka masa harara
"sai ka cire rigar taka ka ajiye mata kusa da ita muje in baka wasu kayan daga nan ka raka ni nima in siyo irin shi, ba dole ta so turaren ba ka sako turaren mata sai kace wani ɗan daudu"
sai da suka je part ɗin sa ya bashi kaya ya saka sannan suka kawo min wadanda ya cire har wani kai fuskata nake yi kusa da rigar in shaƙa ina jin daɗi
ko da suka daso daga siyan turaren aliyu ya baje jikin sa da turaren ko daya zauna kusa da ni har wani ƙara shishi shige masa nake yi ina shaƙa wannan ne ya bashi damar sauke min nauyin da ke marar sa a sauƙaƙe ba tare da nayi complain ɗin banaso
mijina ya samu dama ta don haka cin karensa yake yi babu babbaka akaina ba dare ba rana da ya bushi iska abinsa sai yaje ya bazo turaren sa ya matso kusa dani yasan cewar ina jin ƙamshin nan zan dinga shishi shige shi kuwa dama abinda yake so kenan sai yaci karen sa babu babbaka
to kunsan abin me ciki ba tabbas don haka Allah ya taimake ni na daina son ƙamshin turare nan, ranar kuwa ya bazo shi ya tinkari gadon da nake kwance zai kwanta da amai ya taso min da gudu nayi banɗaki sai da na amayar da duk wani abinda yake cikina sannan naji daɗi ko da ya tambaye ni ma ya samin amai sai nace masa warin turaren sa ne bana so aikuwa wanka ya je yayi sosai ya fito amma duk da haka bai daina ƙamshin bahi daman sawars mugunta yayi shiyasa Allah ya kama, don haka dole yau angulu ta koma gidan ta tsamiya don kuwa shinfiɗa yayi a ƙasa ya kwanta don bana son warin tj yau ya sha zagi yau sosai wai bai gaya mai ba cewar abin nawa ba permanent bane shi duk ya sakankance, ina jinshi bance komai ba sai ma dai bacci daya dauke ni me daɗin gaske
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :22🌹
sai da na wahalar da aliyu sosai sannan na haƙura na cemasa ya daina warin turaren ba ƙaramar kewata yayi ba na gane hakan ne ta yadda ya dinga rawar jiki a kaina hmmm
Cikina ya fara fitowa, nan rawar kan aliyu ya kuma ƙaruwa sai ya zauna yai ta hira da cikin, siyayya kuwa yi yake yi ba kama hannun yaro hatta kayan funitures sai da ya canza min ni kuma na aikawa khadija nawa
Gyaran gidan ya shiga yi da yaga lkcn haihuwa ya kara matsowa, ko kaɗan baya jin kuɗin sa in dai aka zo maganar cikin jikina ne kuɗi kawai yake fitar wa kamar baisan zafin su ba, ko na yi masa magana sai yace bazaki gane bane, yanzu zanga wanda kullum zan dinga tunawa cewar nima yanzu ga jinina a kusa da ni, yakan ƙulle min kai da maganganun sa tare da soki burutsu don haka nake ɗaukar zancen nasa
Lahadi da daddare muka shirya domin zuwa asibiti awo, na ci kwalliyata sosai kamar ba me ciki ba , muka ɗau hanya, ko da muka je asibitin da nake awo sai aka ce likitan bata nan don haka sai dai muga wani, shi kuwa aliyu ba abinda ya tsana da ya wuce ace namiji ne zai ganni don haka tun farko ya nemi likita mace ta zam dr ɗina,
ko da na faɗawa aliyu ceqar bata nan si dai namiji, sai yace shi bai yadda ba bari kawai ya kirata, ko da aka kira ta sai tace mu same ta general hospital
nan muka je don ta duba mu, labour room ta sa na je don tayi min awon a can, ko da naje da mutane don hka sai tace inɗan jira kaɗan, tana cikin duba aka zo aka kira ta emergency don haka sai ta fita, sai ta sa wata dr ɗin ta ci gaba da duba mu,
ko da zo sai ta kalle mu tace
"duk naƙuda kuke yi" dukaan su suka ansa banda ni, ta kalle ni tayi murmushi
"daga gani har yanzu bata matse ki sosai ba shiyas kika ci wannan kwalliyar"
sai da ta gama duba su tsab snnan tace min in zo, kamar zan mata musu sai dai na tafi, ta sani na kwanta ta duba ni
"kina 2cm,nan da 4hrs zaki iya haihuwa, kije kiyi ta zaga yawa" saukowa nayijikina yai sanyi wai zan haihu
ko da na fito na tarar da aliyu yana jira na
"me suka ce"
"nan da 4hrs zan haihu"
"wattttt kina nufin nan da awa 4 ƙwarara ina nan da baby na a hannu" ya tambaye ni gyaɗa mas kai nayi
nan ya rikiɗe sai sunbatu yake duk ya bi ya ɗaga hankalinsa wai ance haihuwa da wuya, shi bai shirya ba kawai mu tafi gida ma dawo nan gaba idan ya shirya, ya kalle ni
"zainab bana son ki wahala wajen fito da babyn nan mu gudu gida kawai kinga dole haihuwar ta haƙura har sai lkcn da muka shirya ko" ya faɗa yana ja min hannu alamar mu bar wurin
ni da nake shirin fito da babyn hankalina ya fi nashi kwanciya
"hubbi, ba komai am alright, we can do together, baby yace yau yake son yazo ku haɗu pls lets grant our babys first wish" na faɗa masa ina mai tallafar fudkarshi don mu haɗa ido, wannan abinda nai masa ba karamin kwantar masa da hankali yayi ba har ya fara rakani takawar
sai ƙarfe 1:30 na dare sannan na shiga cikin labour room din lkcn wahalar haihuwa ta fara damƙata, na sha wahala sosai bini bini naga call ɗin aliyi kon haihu sai ince masa da saura
ba ni na haihu ba sai da asuba, byan ma anshiga masallaci sallah asuba sannan Allah ya suke ni lfy na haifi ɗana namiji kyakkyawa fari tas da shi
ya na idar da sllah y kirani na faɗa masa na sauka, kashe wayar kawai naji yayi, inda daga baya ya kirani yai ta min godiya tare da addua, aka shirya baby nima akai min duk abinda ya dace ai min da karfe 6:00 aliyu ya kira ni
"ga abinci nan na sa an miki za a shigo miki da shi ki ci, naji ance me jego ta dinha cin abinci sosai ko ruwan nono ya zo ko" to kawai nace
na ɗauka abinci ne irin baifi food flask biyu ba, ba sai naga sai shigo da abinci ake yi, dariya abin ya bani ohh aliyu komai naka daban ne na faɗa arai na, bismillah naƴi wa nurses ɗin da kowa da kowa har ƴen uwana masu naƙuda da waɗanda suka haihu sai da suka sa albarka atakaice da ɗan karamar liyafa akai da safen nan
Sai ƙarfe takwasa sannan aka sallame ko da aliyu ya ga babyn har ƴar ƙwalla yayi tare da kissing ɗin babyn, San nan muka kama hanyar gida,muna komawa gida naga duk ma'aikatan gidan sun fito domin tarar mu, naji daɗin hakan da suka yi mana
ɗakina na wuce direct aliyu ɗauke da babyn ko da muka je zama nayi don bansan abin da zanyi ba, kallona yayi yace
"madam lfy ko" ya tambaye ni yana kashe min ido
"ba komai, kawai dai ban iya wankan baby bane"
"oh na ɗauka ma ko har kin fara missing ɗine ne, kar ki damu akwai wacce zata zo"
murmushi nayi masa nayi masa godiya nasan cikin *dangin sa* zai sa wata ta zo min, wataya ta na ɗauka na fara kira ina faɗawa mutane ga mamaki su khadija ma sun sani wai baba ne ya faɗa mu, na kira number mama ban samu ba nasan zata ce zata zo suna mama kenan na faɗa
aliyu ne ya ƙara shigowa ɗakin ɗauke da babyn kasancewar dama ya fita da shi don masu aiki su ganshi
"madam kin ga yaron nan kowa sai cewa yake yi kamar mu ɗaya" ya faɗa ya kallon babyn
"hmmm kawai suna faɗa ne amma ba abinda ya ɗauko naka,sai haske" saboda babyn fari ne sosai
"kina dai baƙin ciki, kin ga yaro jinin larabawa"
"yauwa hubbi, pls ka koya wa babyn nan namu larabci kaji"
"ce miki akayi na iya"
"ba balarabe bane kai"
"mahaifiyata ce balarabiyar saudiya, mahaifina baƙi ne kamar ki" ya faɗa yana lakuta min hanci
"baka girma da ita bane" na kuma jeho masa tambaya, don a gaskiya babu wanda na sani a *dangin sa* tunda muka yi aure sai tj kawai
Kissing lips ɗina yayi sannan yace
"ga lips ɗin nan naki da kyau gashi da tambaya, bari inje inga me akeyi a wajen nan" ya juya ya fice, aliyu ya iya waskewa idan baya son ansa tambaya
ban damu ba saboda yanzu nasan na haihu dole ƴen uwansa su zo suna, na faɗa a raina, daga dukkan alamu baya son magana akan *dangin sa* har ya kai ƙofar fita ya juyo
"wai yaushe zaki gama wannan abin naki ne"
"wane abu" na tambaye shi da mamaki
"ina nufin yaushe zaki warke, don insan kwana nawa zanyi ban same ki ba" ya faɗa yana kashe min ido
oh Allah ni abu yau Allah ya haɗa ni da miji ɗan world nafaɗa araina
"ko da yake ai akwai ƴen dabaru da zamu dinga yi ko,akwai darussa sosai da ya kamata ace kinyi degree akan su a harkar nan, amma ba komai tunda har lkcn yazo zamu fara darasin mu daga yau ba ɗaga kafa" fahinta yayi cewar duk kunya ce ta rufe ni yasa shi fita yana dariyar mugunta tare da cewa
"ki shirya darasin na yau na musammam ne"
Mama ce ta shigo tare da amina ƴar autar mu, mamaki ne ya kamani ganin ta kwatsam a gida na
"mama" na faɗa ina zare ido
"na'am me jego, kinyi mamakin ganin mu ko, ai mijinki yana kira da asuba yace kin haihu baban ku yace min in shirya, shine mijinki ya sa aka samu a jirgi"
murna ce ta kamani na kamo amina da naga tana noƙewa kamar bata saki jikin ta ba, na zaunar da ita kusa dani tare da ɗora mata babyn akan cinyar ta
"ga ɗanki" na faɗa
"au abin ma ɗan wariya ne" mama ta faɗa tana dariya
"mama bari ta ganshi sai ta baki, kin san abin jini" na mayar mata nima da raha
"to ai shike nan"
"bari insa a haɗa muku breakfast" Na faɗa ina fita don bada umarnin na a haɗa musu breakfast
naji daɗi zuwan mama sosai don gaskiya bata da son jiki ko kaɗan duk da dai ina da masu aiki baja baja amma hakan bai sa mamabata zama ko kaɗan, kwanana uku da haihuwa su khadija suka zo da maryam harda ƴaƴan mama wato su iyami da ƴen uwanta da yaran su, na fa gidan ya kuma cika, da daddare sai ga tj ne nan da matar sa ashe baya gari ne shiyasa bai zo ba ni kuwa nayi mamakon rashin ganin sa
ana jibi suna mama ta faɗwa wa aliyu cewar tana son kwatancen gidan don akwai masu tahowa saboda suna, sai yace duk su haɗu a gidan mu gobe da safe zai sa aɗauko su, ai kuwa haka akayi har gida ya sa aka kawo su
da daddare *dangin sa* suka ƙaraso na ɗauka zanga farar fata ko ɗaya ne amma ga mamakina duk baƙaƙe ne yen uwana, a zuciyata nace ko dangin uban sa ne
Sauka ta musammam akai musu inda aka basu ɗaki biyu don su sakata su wala, sai shirye shiryen suna akeyi ba kama hannun yaro, ƴen uwana da abokan arziƙi sin min kara sosai har mutan gezawa sai da na aika musu da kuɗin mota suka zo har ƴen uwan mahaifiyata sai da suka zo kasancewar duk ƴen gezawa ne, gida ya cika danƙam ba masaka tsinke sai shirye shiryen suna akeyi idan na kalli waɗannan ayawan mutanen na gano ceqar duk don ni suka zo sai inji wani daɗi ya lulluɓe ni nakan godewa Allah da ya bani ƴen uwa masu ƙaunata
kashegari muka tashi da sunan aliyu aliyu sani sunan mahaifin shi jariri yaci inda zamu dinga ce masa haidar, ansha hidima, ga ciye ciye ba kama hannun yaro munyi hotuna sosai don tarihi sai dai muce Allah ya raya mana haidar aliyu
kashegarin suna aka fara watsewa inda duk wacce zata tafi da tsarabar sunan ta a leda sannan a biki da kuɗin mota wanda aliyu ne wanda yanzu ya koma abu haidar ya ba mama cewa adinga sallamar baƙi da kuɗin mota kuma za a baka wanda zai kaika gida har da ɗan wanda zai rage
ranar labara mutan kano suka shirya tafiya wato *dangin sa* basu shirya da wuri ba don haka lkcn suka shigo ina banɗaki ina jin khadija tana ce musu ina banɗaki to bari miuj inda aka sauke mu mu jira ta
suna fita na fito daga wankan, zan shirya mama tace min insa hijabi na inje in sallame su ba daɗi jira, na ɗauko zunbululen hijabi na na saka sannan na kama hanyar ɗakin su don muyi sallama, ina shirin tura ƙofar ɗakin naji suna magana tare da kama sunan mijina don haka sai na dakata don in ɗan ji
"ke dai bari hauwa wallahi ko kaɗan baya kyautawa, dubi yadda ya bar *dangin sa* cikin ƙunci da talauci kamar ba abinda ya haɗa su, sai ma kinga ƙannen mahaifinsa da ke unguwar mu su da ƴaƴan su yadda kika san almajirai, wallahi babu wani abinda yake musu" ɗaya ta faɗa, wata ka ta kama
"rannan da naje jakarar gidan mu na shiga dan gaisawa da inna kakar tasa wallahi zanin jikin ta bazakiyi tsimma da shi ba saboda tsabar lalacewar da yayi, tsayawa kawai nayi ina kallon ikon Allah, nace a zuciyata wai jikan matar nan ne yake da maƙudan kuɗin da baisan iya adadin su ba amma jibi kayan da ke jikin ta don Allah"
"ke dai bari zulai nima abinshi yana bani mamaki kome sukayi maka ba sai ka haƙura ba, tunda ko ba komai yanzu ka fisu, Allah kinsan hauwa ko banɗaki basu da shi a gidan nan nasu, langa langa ce aka sa arufe wai shine bayi"
suka ci gaba da tattaunawa akan talaucin da ke tattare da *dangin sa* wanda sukw mamakin rashin kula sun da bayayi, jikina ne yayi sanyi na shiga ɗakin a sukwane, duk sai suka sha jinin jikin su
tsugunnawa nayi muka gaisa
"lfy naga me jego jiki ba ƙwari sai kace bakya shiga ruwan zafi" Inji ɗaya daga cikinsu kasancewar ba sanin su nayi ba yasa na kasa tantance waɗanda sukayi maganar da naji
"da zazzaɓi na tashi yau" na amsa ahankali don duk maganar da sukayi ta gama kashe min duk wani kuzari na jikina
"ayya dahuwar ƙashi ce, Allah ya sauwaƙe" amin na kuma ansawa a sanyaye duk sukai min Allah ya sauwaƙe sannan mukai sallama da su na tafi zuciyata cike da tunanin ta me kenan ya ke faruwa tsakanin mijina da *DANGIN SA*
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :23🌹
Ko da na koma ɗakina kasa shiryawa nayi duk zancen su sai nake jin sa kamar yanzu akayi shi sai dawo min yake yi yana min yawo a ƙwaƙwalwata, ga shi bana son faɗawa kowa saboda wannan kamar sirri ne day kamata in ɓoye tunda ya shafi mijina kuma ba abin alkhairi bane, khadija ce ta shigo ta ganni zaune ba tare da nasa kaya ba
"tooo me jego a zaune yai ba kaya a jikin ta" ta faɗa tana kama bakin ta
"kodai jikin ne" girgiza mata kai nayi
"ai kuwa ya kamata ki sa kaya a jikin ki don kar sanyi ya kama ki, muje in taya ki zaɓar kayan don yau naga gaba ɗayan ki bakya jin daɗi" closet ɗin muka tashi muka nufa, nidai tafiya kawai nake yi amma jikina gabaɗaya a mace yake na rasa abinda yake min daɗi
Wata jar shadda ta ɗauko min ɗinkin bubu sabuwa dal
"karɓi saka wannan" ta faɗa tana miƙo min,
"khadija ina mama" na tambaye ta
"tana can wajen rabon kayan suna kinsan duk yau za a watse, itama wannan ƴar iskar tana can, sun tasa kaya a gaba suna ta rabo, sukan duk waɗanda take mutunci da su da basu samu daman zuwa ba ta ɗiban musu, har da maƙotan ta, kinji ƴar iska" murmushi nayi maryam ai yadda kasan mama ce ta haifa ta wajen shishshigi da rawar kai haka take
"wani abu naji daga bakon ƴen uwan aliyu da suka zo ya tsaya min a rai" dawowa tayi kusa dani ta zauna tare da zare min ido menene
tas na kwashe abin da naji na faɗa mata ba tare da na ɓoye komai ba,
"haba biri yayi kama da mutum, nan mama take cewa ita fa bata ga wani abinda ya nuna alamar cewa waɗannan da suka zo suna sun haɗa wani abun da mijinki ba, shi fari tas kana ganin shi ka ga balarabe su kuwa ko ni nan na fi su haske" ta faɗa tana kallon hannun ta
"mahaifin shi baƙi ne kamar ki, na ɗauka dangin mahaifinsa ne tunda yace mmn shi basaudiyace"
"to ina iyayensa suke" shiru nayi don tunda nake ban taɓa tanbayar sa ba hasalima daga gani baya son a dinga yi masa zancen *dangin sa*
"ina tunanin sun rasu koo don tunda nake da shi bai taɓa cewa ga inda suke ba, to kinga ƙila sun rasun" na faɗa ina kallon ta
"ba shakka ƙila sun, sannan shi kuma ya tashi a wurin *dangin sa* inda suka yi masa ƙila ruƙon sakaynar kashi ina jin shi yasa shima daya girma ya watsar da su" khadija ta faɗa tana mai jinjina kanta alamar gaskata abinda ta faɗa
haka muka zauna muna ta tattaunawa akan abinda yasa aliyu ya daina kula da *dangin sa* amma har muka ƙare zancen namu bamu samu wani ƙwaƙƙwaran dalili ba
"kinga ance waƙa a bakin me ita tafi daɗi, ki bari idan aka watse si tambaye shi hankali akwance ƙila yai miki bayani ya fi wannan shaci faɗin da muke tayi" khadija ta faɗa tana me ƙoƙarin kauda mana da zargin da muke, don kar muje mu zargi bayin Allah waɗanda basuji ba basu gani ba,
"hakan zanyi ya na iya, amma ya zama dole in san me yasaijina ya ke wulaƙanta *dangin sa* baya taimaka musu ya barsu suke rayuwa kamar almajirai"
"hmmm Allah dai ya kyauta kar kiyi saurin yanke hukunci baki san me ya faru ba"
"haka ne Allah dai ya kyauta" na faɗa ina miƙe wa
ko da muka je sallama da su kawai kallon su nakeyi gashi ina son tambayar su dalilin daya sa suke wannan maganar amma ba dama tambayar su don sai suce nayi musu laɓe ina kallon su haka suka kama hanya suka tafi ciki na cike da tambaya amma ba daman yi
su khadija sai da suka ƙara kwana biyar sannan suma sukayi haramar tafiya, bayan na cika su da goma ta arziki kai ɗan uwa da daɗi yake, haka suka tafi ina kewar su ya rage daga ni sai mama, don ita tace sai anyi arba'in haka sukayi da baban mu wato ita mama babu ruwanta da yiwa kanta baƙin ciki inda wata ce cewa zatayi bazata zauna ba saboda ƴar kishiya ce amma mama ko a jikin ta zaman ta tayi
na so mu keɓe da mijina watoa abu haidar don in samu in amayar masa da tambayoyin da ke ciki na amma hakan ya gagara don kuwa aiki yake yi tuƙuru ba kama hannun yaro, idan ya shigo wurin mu kusan a tsats tsaye yake ganin mu ya ƙara gaba, ga kuma mama bana son inyi masa tambayar tana nan
sai da mukayi arba'in da kwana biyu sannan mama ta fara haɗa ya nata ya nata don tafiya ita ma, abu haidar ya kaita siyayya hmmm naga hidima wurin mama ta kwaso kaya kamar ba gobe haka ta dawo dasu niƙi niƙi, sai shi wa mijina albarka take yi, ni dai kawai riƙe baki nayi ina kallon iyayen kayan da mama ta kwaso Allah ya kyauta na ce a raina
ranar da mama ta kama hanyar lagos ranar shima abu haidar ya kama hanyar china wurin wani project da suke yi shi da wani ɗan china, bayan ya yarde min inje kano yawon arba'in, har airport na raka shi sannan na dawo da zummar kashegari zan tafi kano wayyo daɗi yaushe rabona da birnin dabo Allah ne kaɗai ya sani na faɗa a raina
kashegari da wuri na kama hanyar kano a mota kasancewar ina son ganin gari sosai, tafiyace miƙaƙƙiya daga abuja zuwa kano, a gajiye liƙis na sauka don na manta rabona da irin wannan tafiyar, directly gidan tj na nufa don nan zan sauka, ɗakine guda aka haɗamin da ban ɗaki a cikin sa, watsa ruwa nayi kawai na kwanta don na gaji sosai, bacci kawai nake so don jiya kawana nayi ido na biyu
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :24🌹
Bani na fito daga ɗakin ba sai da safe sannan na fito saboda gajiyar da nayi ko abincin dare banci ba, ina jin salma ta shigo ɗakin ko motsawa kasa yi nayi
Sai da nayi wanka nayi wa haidar na shirya sannan na fito falon gidan sanye cikin shadda ta brown ɗinkin bubu kasancewar ni akwai son buba sannan na ɗauko hijabi na ɗora tunda gida ba naka bane
Tj na tarar a falon da salmar suna karya wa, ina fitowa salma ta karɓi haidar inda tj ya karɓe shi daga hannun ta"yaron nan kullum kamar shi baban sa ƙara fitowa takeyi" ya faɗa yana kallon haidar
"da baban sa ko dai mamansa, ai wannan kamar su ɗaya da zainab kudai kun fiya son kai ne, haka da haifi Islam kace kamar ku ɗaya"
"ai ku bakusan kama bane shi yasa, me ya haɗa wannan da mamansa ai wannan kamar ɗan uwa yayi kaki haka yake bari kiga ya ƙara girma.............."
"a lkcn ma zaka ga kamar tasa da uwarsa ta ƙara fitowa" salma ta ƙarashe masa zancen nasa, sakin baki yayi yana kallan ta
"to ai shike nan zamu gani" ina dai ban tanka musu ina dai zaune ina jiran su gama musun su mu gaisa
"sannu wannan baƙuwa Allah ya zuba miki bacci, tun da kika zo gidan nan kike bacci sai kace wata kasa" tj ya faɗa yana dariya, murmushi nayi tare da cewa
"ina kwanan mu" duk nayi musu jam'i
"lfy kin iso ƙalau tun jiya nake sa idon ganin ki salma tace kina bacci, bayan kafin kizo ba irin jan kunnen da ba ayi min ba akan in kula da ke da haidar sosai" ya faɗa a zolaye, murmushi nayi kaɗan daga aikin abu haidar ne zai aikata na faɗa araina
"bari a kawo miki abinci" inji salma
"no bazan sha shayi ba indai da cheery noodles ita nake son ci, bari ma kiga in shiga kitchen ɗin in dafa" tashi nayi tsam na shige kitchen ɗin don gabaɗaya ban sake ba
Biyo ni tayi
"ya baƙuwa da girki, ko kina son aliyu yace bamu riƙe masa amanar da aka bamu bane"
"ko kaɗan akwai yadda nake son dafa noodles ɗina ne, karki damu" na mayar mata da martani tare da murmushi
"to bari in taya ki"
"ba komai kije ki sallami mijinki tukunna"
"yace ya ɗau hutu daga wajen aiki har sai kin tafi don zai dinga kaiki unguwa" shiru nayi ina sauraren ta sai banji daɗi ba
"laaa dama kince ya ci gaba da aiki ai da driver na zo saboda yawon"
"wannan kuma ki gaya mai da kanki ƴar amanar mu" ta faɗa tare da dafa min bayana, murmushi na cigaba da yi ita kuma ta fice
ko da nagama dafa abata na juyo ta plate da niyyar in wuce ɗaki amma salma sai ta hanani tace sai dai in zauna a falo inci tj ya fita, ba yadda na iya haka na zauna a falon nan ba dan na so ba, sai dana kammala sannan ya shigo ɗauke da haidar ga islam a hannusa, tana gani na ta taho a guje ashe bata manta dani ba
"lallai islam ashe bakya manta mutane" na faɗa
"ai wannan kusan kullum sai tayi hirar abj" salma ta ansa min, tj ne ya zauna sannan ya ce
"yayat yaushe za a fara zaga dangin ne, kuma ina zaki fara zuwa" shiru nayi don ni ban san kowa ba acikin *dangin sa* ba tunda muka yi aure ba wanda na sani, gashi waɗanda nake tunanin sune *dangin sa* ɗin sunce ya kasa kulawa da *dangin sa*
"jakara, jakara zan fara zuwa" na faɗa tabbas jakara naji sunce a nan kakarsa take,
nayi mamaki sosai dana ga alamar tsoro ko ince mamaki a fuskar tj
"jakara zaki je"
"eeeh nan nake son in fara zuwa ko akwai wani abinne"
"no no no no ba komai" ya faɗa yana girgiza kansa kamar ba a cikin hayyacin sa yake magana ba
"sai muje anji ma in kin shirya"
"ba abinda zanyi ni a shirye nake" na faɗ ina gya hijabin da ke jikina
"ok bari in watsa ruwa sai in fito, tashi yayi ya shige ni kuma na koma ɗaki ɗauke da haidar a hannuna, ban kawo komai a raina ba illa murnar da nakeyi yau ɗana zai ga *dangin sa* na ɓangaren uban sa, nasan ƴen gayu ne ƙila ma farare ne kamar abu haidar ɗin
ƙara duba kaina nayi a mudubi na tabbatar ko shugaban ƙasa zan iya gani a haka sannan hankalina ya kwanta bana son inje gidan ƴen gayu a raina ni, na zauna ina tunani na na yadda ƴen uwan abu haidar zasu karɓe ni ko da fara'a ko a wulaƙance ni dai sai saƙe saƙe na nake tayi, salma ce ta shigo ta ce min yana jirana, ɗan ƙara kimtsawa nayi tare da sa mayafin da zai shiga da kayan, sannan na ɗauko haidar na fito
A mota na same shi ya buɗe min sit ɗin baya na shiga ni da ɗana, na zauna sannan muka fara tafiya, kasancewar bansan garin kano ba yasa bansan ina muke daso ba, bayan mu ɗan yi ƴar doguwar tafiya muka zo wata unguwa wacce layikanta suke a tsuke sai da dabara ma sannan muke iya wucewa,
ƴar tafiya muka yi kaɗan sannan tj yayi parking, muka fito ya karɓi haidar ya fara tafiya, mun yi tafiya da ɗan dama kafin mu zo wani ɗan durƙusash shen gida wanda yake ginin ƙasa ne, duk gefen soron wajen gidan ɗan pilastar da akayi masa ya zazzage ana gani jar ƙasa muraran,
Soro biyu muka shige waɗanda duk sun dafe kamar ana girki a cikin su, sannan muka shiga, tsakar gidan na ƙasa ne ko arziƙin siminti bai samu ba, yara ne a baje a tsakar gidan suna ta wasansu a cikin ƙasa ba tare da iyayen sun damu ba, sallamr mu ce ta katsewa iyayen hirar su da suka yi dandazo sunayi ba tare da sun kula da halin da ƴaƴan su suke ciki ba, gabaɗayan su suka juyo tare da ansa mana
"wa 'alaikumus salam, a a awata sabon gani tijjani ne yau agidan namu, lallai yau za ayi ruwa da ƙanƙara" inji wata wacce daga ganin ta zata haifi tj ɗin,
"mmn habu wallahi uzuri ne yayi min yawa kiyi haƙuri"
"kayya ba komai ku ƙaraso ai iyar tana ciki"
ƙarasa shiga ciki muka yi inda kwata tayi wa gidan kwalliya, sai da muka tsallaka wata yar ƙaramar kwata sannan muka shiga wani ɗaki wanda saka durƙusa sannan zaka shiga,
babu abinda ke ɗakin sai wata ƴar tsuhuwar kujera guda ɗaya a gefen ɗakin wanda cushion ɗin kujerar duk sun patattake kana ganin soson cikin kujerar wanda shima yayibaƙi ya yayyage, ƙasan ɗakin an simince shi amma duk ya fargashe ramuka ne aoaai a ɗakin kamar ba mutun ne a ciki ba, bangon ɗakon yai baƙiƙƙirin da shi kamar ana girki da murhu a ɗakin, sai iayayen calandu na mutane duk an zagaye ɗakin da shi
Wata ƴar tsohuwace ta fito daga cikin uwar ɗakan ɗakin,
" wa nake ji kamar ahmadu, lallai yau nayi gamo da alheri" ta faɗa tana fitowa tare da ƙoƙarin gyaran ɗan kwalinta tsohuwa ce amma daga gani harda rashi ya sa ta ƙara lalacewar tata
tabarma ta ɗauko ta shinfiɗa mana muka zauna, bayan mu gaisa ne take cewa
"wannan dai ba sirikar tawa bace ba koo, ko kuma idon nawa ne"
" iya idonki ras yake ba ita bace matar ali ce, ta haihu shine tazo gaishe ku" tsayawa tayi tana kallo na
"ali dai ali alin hjyr" ta faɗa, murmushi yaya tare da gyaɗa kansa
"shi kuwa" hannun ta na rawa ta matso ta ɗauki haidar da ke hannun tj, sai ga hawaye a idon ta, ni dai ina zaune ina kallon ikon Allah don har yanzu bansan inda muka zo ba, amma koma ina ne daga gani talauci ya zuba ƴaƴa har da jikokin sa a gidan nan, don babu wacce zaka gani kace bata fama da babu har ita tsohuwar da ke gaban mu tana fama da babu, zanin jikin ta kawai zaka kalla kasan cewar talauci yai mata damƙar kuku
tashi tayi ta fita sai gata da mutanen gidan sai shigowa suke yi ana gaisawa da ni suna ɗaukar haidar, da yake ɗakin ba wani girma gare shi don haka sai wasu sun fita sannan wasu suke shigowa ko da aka gama gaisuwar sai gashi an kawo mana ruwa a wani kwanon silba, ni bin kwanon nayi kawai da kallo amma gaskiya bazan iya shan ruwa cikin sa ba, ganin cewar kamar bazamu sha ruwan bane yasa iyan tace wa wata yarinya da bazata wuce shekara shida ba
"humaira zo kije gidan ummi kice nace ta bani pure water guda huɗu nayi baƙi" a guje yarinyar ta tafi can zuwa jimawa sai gata ta dawo duk tayi duƙun duƙun da ita
"iya kinga ina cikin gudu na faɗa kwata"
"ina aiken da na miki" iyar ta tambaye ta
"au tace wai shekaran jiya da kikayi baƙi kika karɓi na 15 baki aiko mata da kuɗin ba" yarinyar ta faɗa batare da damuwa ba
fuskar iyar ta nuna damuwa sosai tj ne ya ce
"iya karki samu damuwa bama jin ƙishi ma" ya zaro 1000 ya ba yarinyar gashi nan jeki ce ta ɗauki kuɗin ta, yarinyar ce ta kuma kallon iya inusa me shago ɗazu yayi min maganar bashin sabulun wankan da kika karɓa"
"kije shima ya ɗauka aciki" inji tj wallahi matar duk sai ta bani tausayi don ƙiri ƙiri kana gani kasan cewar tana buƙatar taimako, tj ne ya katse shirun da mukayi tare da tambayar iyar ragowar ƴaƴan nata inda ita kuma take bashi ansa dai dai sanin ta
Wata mata ce ta shigo ɗaki kamar an jeho ta
"lfy bilki sai tace wacce aka koro"
"wallahi iya yara ne suka je gidana suka ce matar ali tazo shine wanki ma nakeyi na ajiye na fito don inganta"
"ina kwana sirika ta" ta juyo gare ni muka gaisa
Suka gaisa da tj har tana mai ƙorafin ya yada daita shi kuma ya dinga kawo mata uzirin sa na baya zama ne
hannun ta da ke jike ta goge tare da miƙowa iyar hannu kawo jikan nawa inganshi, ta karɓi haidar tare yi masa addua, sannan ta juyo gareni
"ashe a abuja kika tare" gyaɗa mata kai nayi
nan ta zauna suka dinga hira da tj itama iyar takan ɗan tanka musu ni dai ina zaune idan anyi abin dariya in dara, mun ɗan jima ni dai buri na in fita daga gidan don haƙurin zama kawai nakeyi, tare muka miƙe da bilkin muka fito har soro mutan gidan suka rako mu inda bilkin ta karɓi number wayata wai don mu dinga gaisawa da kuma wai inta haihu zata kira ni ta faɗa min kasancewar ciki ne da ita ya fito sosai, tj yai ta musu rabon kuɗi hatta yara ƴen ƙanana sai da suka samu suna ta shi masa albarka muka fito har muka ƙule daga lokon gidan suna kallon mu wata ajiyar zuciya na saki dana ga mun bar layin nan kai Allah mun gode ma amma talauci baiyi ba ko kaɗan
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: L🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Paga :25🌹
Har muka ƙaraso inda mukai parking ina tananin bayin Allah nan Allah ya gani ina tausaya musu, kamar suna rayuwa a ƙauye kamar ba civilization, jikina duk yai sanyi na rasa yadda zan kwatanta bayin Allah nan, muryar tj ce ta katse
"madam daga nan sai ina"
"tj nace ma gurin kakar aliyu zanje in gaishe ta" na faɗa jiki na duk yai sanyi har yanzu ina tunanin bayin Allah nan, na ɗauka wani abin yake yi amma ga mamakina in ɗagowa sai naga ya kallona,
"kima nufin baki san gurin wacce kika je ba yanzu" girgiza masa kai nayi
"itace kakar aliyu, iyar da muka ke ɗakinta muka zauna ta ɗauki haidar itace ta haifi mahaifin aliyu" rasa bakin magana nayi
"kana nufin iyar da muka fito daga gidan nan yanzu ita ta haifi baban mijina"
"ƙwarai kuwa, duk waɗannan da kike gani daga matan ƙanin baban sa sai ƙannan baban sa a gidan babu bare, itama wannan bilkin da kika ga ta shigo daga ƙarshe itacw autar iyar, uwarsu ɗaya uban su ɗaya d bbn ɗan uwa"
shiru nayi jikina duk yayi sanyi mekenan yake shirin faruwa aliyu ne *dangin sa* suke rayuwa kamar almajirai, kamar akansu aka yanke wa talauci cibiya abin ma wallahi da ɗaure kai
"tj kana nufin waɗan nan sune dangin aliyu, waɗanda zai kalla yace sune *dangin sa*
gyaɗa kamsa kawai yayi tare da ƙoƙarin buɗe ƙofar don in shiga, shiga nayi amma gabaɗaya hankalima yana tashe, ya za ayi ace wai waɗannan su ne *dangin sa* mutumin da ya mallaki dukiyoyi bila adadin ko jirgin ruwa ɗaya gare aliyu zai iya ciyar da kusan rabin kano amma mutumin daya mallaki jiragen ruwa wai shine *dangin sa* suke cikin wannan baƙin talaucin
"tj kana ganin abu haidar ya san halin da ƴen uwan sa suke ciki" na tambaye shi a ƙage
"gwanda dai ki tambaye shi kinsan ance waƙa a bakin me ita tafi daɗi" ba yadda ban yiba don inji wani abin a bakin tj amma ƙiri ƙiri duk abinda na tambaye shi sai yace in dai tambayi mijina, haka na haƙura nai shiru
"akwai inda kike son zuwa ne kuma"ya kuma jeho min tambaya, bazan iya zuwa ko ina ba don gabaɗaya jikina yayi sanyi ganin irin yanayin da na samu ƴen uwan mijina
"tj kai ni gida kawai gobe nayi yawon amma gaskiya yau ina buƙatar inyi nazari sosai akan halin da bayin Allah nan suke ciki" shiru yayi bai tanka min ba
ko da ya ajiye ni bai shiga gidan ba wai yana sauri, na shiga ni kaɗai salma tai mamakin gani na, na dawo da wuri, nan na rattabo mata abinda na gani a gidan dana je ko zanji wani bayani daga gare ta amma ga mamakina sai ta nuna min bata san komai ba, ba irin tambayar da ban mata ba amma ƙiri ƙiri tace min wallahi bata san komai ba amma dai tasan akwai wata mai tsami sosai tsakanin miji na da *dangin sa*
"to waɗanda suka zo suna fa ba *dangin sa* bane"
"ƙannan baban islam ne"
"meye dangatakar mijinki da nawa" na tambayeta a ƙagare, dafa ni tayi
"in kina son ansar da zata gamsar da ke ki tambayi mijiki" tana faɗar haka ta juya tayi shigewar ta ɗaki ta barni da baki a buɗe
kasancewar hausa ba wani isa ta tayi ba sosai ya sa na tsaya ina nazarin abinda salmar tace amma har na gama bincika dictionary ɗin ƙwaƙwalwata ban ga ne me take nufi ba, haka na shige ɗaki na kwanta don ina buƙatar kaɗaicewa ko nayi ɗan nazari
me ya haɗa mijina da *dangin sa*haka da har yayi tsami har ya iya kallon su cikin halin da suke ya ƙyale su ba tare da ko ɗan kula su ba, me yayi zafi, ko dai sun wahalar da shine lkcn da iyayen sa suka rasu, haka naita saƙa ina warwarewa babu me kama min ni kaɗai nake ta saƙe saƙe na babu me gyara min ko kuma me faɗa min abinda ya faru sai dai injira dawowar shi wanda abin ya faru da shi, ƙila shi ya faɗa min abinda ya faru kai doe ne ma ya faɗa min tunda yanzu ai mun zama ɗaya na faɗa ina mai juyi akan gado don inji daɗin kwanciyata
sai bayan sallah magariba sannan abu haidar ya kira ni, muka gaisa da wasa da dariya,
"mutan kano ya kanon an fara yawon, Allah yasa dai ba a wahalar min da ɗana" ya faɗa a zolaye
"ni ko ka tambayeni ta ɗan ka kake ko" na faɗa tare da zunɓuro baki kamar yana wajen
"yi haƙuri habibti ya kike"
"lfy" na ansa a taƙaice
"an fara yawon ne" ya tambaya
"eewh yau munje jakarah" shiruuuuuu naji yayi har na ɗauka ko wayar ce ta katse sai da nace hello sannan naji yace min
"wa ya saki kije"
"ai naga ƴen uwankane"
"shut up, dont provoke me now young lady, da izinin wa kika je,na ce miki ki je can ne" ina iya jiyo nunfashin da yake fitar wa saboda tsabar fushi da yake ciki
"ki shirya kayan ki yanzu ki bar kano kin gama yawon"
"ban je ko ina baa" ɗitttttttttttt naji ya kashe wayar, me kenan hakan yake nufi na faɗa, raina ya baci sosai da sosai komawa nayi na kwanta abin abu haidar ya fara sha min kai yanzu
*************
sun fito kenan daga meeting zasu cin abinci a wani sea food da ke kusa da deport ɗin da suke yace bari ya kira wannan me yawon yaji ta fara yawon nata amma abin mamaki yana kiran ta sai yaji wani zance da ya fi muni gareshi wai taje wurin waɗan da a aduniyar nan bashida maƙiya kamar su me zai kaita jakarah, ya maimaita tj ka cuceni don me zaka ɗauki mamata da ɗana ka kai wa mutanen da tun ina cikin uwata suke kirana da shege, don me zaka kai min iyalaina wurin mutanen da tunda nake basu taɓa so na ba don me zaka kaimin iyalaina wurin mutanen da basa so na ko kaɗan
lallai yau dole ne ta bar garin nan, don naga almar tj baya son ta zauna agidan sa ne, ɗaukar wayar sa yayi ya kira tj ɗin, ringing biyu tj ɗin ya ɗauka
"ɗan uwa ya birnin sin ɗin" tj ya tambaya ba tare da kawo komai a ransa ba
"tj na gode da abinda kayi min kuma na gano ka baka son matata ta zauna a gidan ka ne shiyasa har ka kaita gidan da kasan na fi tsana, don haka ka tattara min ita ka kai min ita airport ta kama hanyar gidan ta"
shiru tj ɗin yayi yasan cewar aliyun ya faɗi abinda ya faɗa ne cikin ɓacin rai,
"ko baka jine ka mayar min da matata" ya daka masa tsawa
"sai da safe don yanzu dare yayi"
"ban damu ba ni dai kawai matata ta bar min gidan ka yanzu"
"kamar yadda nace sai da safe kawai ka haƙura sai da safe"
"idan bazaka sa ta a jirgin ba zan aiko a ɗauke ta da kaina"
"ince dai tana cikin gidana zanga wanda zai shigo min gida wai da nufin ɗaukar ta ayau, in kuma ka isa ka baro inda kake ka zo ka ɗauke ta" yana gama faɗin haka ya kashe wayar don yasan idan ya ci gaba da biye masa sai suyi ɓatacciya don ya san halin aliyu sarai in dai ta kan *dangin sa* ne sai ya rufe idonsa ya ci maka mutunci
to inba aliyu ba waya faɗa wa zainab maganar jakara, salma salma ce zata faɗa mata ya faɗa aransa amma zata gane kurenta duk jan kunnen da yayi mata akan duk abinda zainab ɗin zata tambaya tace mata bata sani ba amma sai da ta saki baki tayi magana, gaskiya salma baki kyauta min ba ya faɗa tare da shiga motar sa domin zuwa gida dole ne ya nuna wa salmar kuren ta
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :26🌹
Tunda muka gama waya da aliyu na kashe wayar gaba ki ɗaya don kar ya dame ni don me bangama yawona ba zaice wai in koma don kawai na je gidan su mtsss na ja dogon tsaki wasu mazan ma sai su, kwanciya nayi ina shirin bacci na ji tj yana ƙwalawa matar sa kira tun daga ƙofar falo, tooo Allah dai yasa ƙalau na faɗa tare da jan bargo na ina mai yin addua ta yin bacci
Tun daga bakin ƙogar falo yake ƙwala mata kira
"salma salma salma" gaskiya yau salma ta ƙular da ni don me zata faɗa wa zainab cewar dangin mijinta suna jakara, har cikin ɗakin nata ya shiga ya tarar tana salla dole ya samu wuri ya zauna don gaskiya baiji daɗi ba
ko da ta idar sai da ya jira ta shafa sannan ya fara mata magana
"yanzu salma don Allah ba nace miki babu ruwanki da sha'anin zainab da aliyu ba ba nace miki duk abinda ta tambaya kice mata baki sani amma shine sai da kika guntsa mata cewar kakarsa tana jakara, me yasa baki bata labarin abinda ya haɗa su da *dangin sa* gabaɗaya ba,"
bata tanka masa ba sai da tabari ya gama ban bamin sa sannan tace
"baban islam ita zainab ɗin ce ta cemaka ni na faɗa mata akan kakar tasa" ta faɗa da fsukar tausayi, kasanceqar tj yana da sanyi sosai ya shi ganin yanayin ta ya ɗan sauko
"to in ba ke kika gaya mata ba waya faɗa mata"
"wallahi ban sani baamma kaje ka tambayeta mana" tashi yayi ya fice dole ya kamata ya san ta ina zainab taji labarin nan
ina kwance bacci ya fara kwasa ta naji knocking,
"yayata nine pls ɗan buɗe muyi wata magana" Tashi nayi na ɗauko hijabi na na saka snnan na buɗe, yana tsaye a bakin ƙofar yana gani na ya koma falo, nima sai na bi bayan sa, wuri na samu na zauna kamar yadda na ganshi a zaune
"yayata don Allah salma ce ta gaya miki akan dangin mijin ki suna jakara ko" Salma? Girgiza kaina nayi
"to inba ita ta faɗa miki ba wa zai faɗa miki ni naga babu wani wanda zaku zauna kuyi hira da shi sai ita" Allah sarki baiwar Allah shiyas yazo yana ƙwala mata kira ɗazu ya ɗauka ita ta faɗa min
"wallahi ba ita bace ta faɗamin ba hasalima ni ba muyi hirar wasu da ita ba" Murmushi yayi na takaici don bai yadda, da naga dai ba zai bar zargin baiwar Allah ba sai na kwashe duk yadda naji ƴen uwansa sun hira na faɗa masa to ya zanyi da ya zargi wacce ba ruwanta ba gwanda ya ji gaskiya ba
mamaki ne ƙarara ya bayyana a fuskar sa, don be taɓa tsammanin abinda zan faɗa nas ba kenan, shiru yayi na wasu ƴen sakanni sannan daga baya yace
"shikenan Allah ya kyauta, mijinki yace in saki a jirgi gobe ki koma don haka ki kwanta da wuri da safe si in kaiki airport" to kawai na iya cewa sannan na juya na wuce ɗaki na kwanta
Da safe da wurwuri na shirya takwas muna airport ina jin lkcn da aliyun ya kira shi shi kuma tj ya faɗa masa gamu a airport ba yadda na iya haka na hau jirgi na koma abj ba tare da nayi yawon ba tunda ya matsa kai namiji sai dai a barshi na faɗa a raina, ina sauka na tarar har ya turo driver na hau na kama hanyar gida
Aliyu bai dawo ba si da na yi sati biyu da komawa sannan ya dawo, babu sanarwa kawai sai ganin shi nayi kamar wanda aka jeho daga sama, duk da dai bai faɗa min ba hakan bai hanani yi mai sauka ta musaman ba, sai da na tabbatar da ya nutsu sannan na gabatar masa da abincin lafiyayye wanda na shiga kitchen da kaina na dafa saboda shiya zauna ya ci sosai tare da godewa Allah sannan na kwashe kayan
Ko da na gama kwashe kayan sai shi kuma ya ɗauki haidar suka tafi garden,ni ma ina gama kwashe kayan na bisu na samu wuri kusa da shi na zauna tare da jingina da jikin sa sannan nace
"abu haidar me ya haɗa ka da dangin ka ne" shiru naji yayi sai na ɗauka ko be ji bane don haka sai na juyo don inga ko me yakeni
ni yake kallo fuskar nan tashi kamar anyi masa da albishir da mutuwa,
"kina son mu zauna lfy da ke, kina son mu zauna ba tare da kowa ya ji kan mu ba, too ina son ki ɗauke kanki daga abinda babu ruwanki a ciki"
"to amma gani nayi dangin ka ne ƴen uwan ka ne" hankaɗe ni yayi daga jikinsa ya tashi tare da ɗaukar haidar
"sai kiyi abinda kike ganin shi ne dai dai agareki" ya faɗa yana kama hanyar ɗakin sa ko da na bishi ya rufe ɗakin da mukulli haka na gama bugawa ta na kama hanyar part ɗina in ɗan yayi kuka ya kawo shi da shi na faɗa a raina
wasa wasa sai gashi mun fara faɗa da mijina a kan *dangin sa* da naga cewar abinda nake so bazan taba samu ba indai har na bari muka ci gaba da faɗan nan ba wani riba da zan samu don haka sai na kwantar da hankalina in dai zan shawo mijina akan *dangin sa* sai dai in canza tsari amma wannan ba zai yiwu ba na faɗa araina, da yamma na tashi nayi masa ɗan wake da farfesun catfish, sai lemun jinja sannan bayan na gama na kwashi kayan abincin na kai masa part ɗin sa na jera a dining table ɗinsa
komawa nayi part ɗina nayi wanka na shirya cikin body hug top ɗita blue colour wacce a gaban ta aka rubuta *YOU AND I* da golden colour, sai leg jeans ɗina wanda iyakacin sa gwiwa ta, nayi parking ɗin kaina a tsakiya sannan na ɗau ki ɗana nayi part ɗinsa don in jira dawowarsa
ko da na koma part ɗin nasa sai da na sake gyarawa duk da yake a gyare yake ban wani daɗe ba sai gashi ya shigo, da gudu na naje wajen sa na rungume shi sai naga yana ƙoƙarin ƙwace kansa ƙara ruƙunƙume shi nayi tare da manna masa kiss a lips ɗin sa hakan ya sa shi yin ɗan sanyi, sai da na tabbatar da ya ɗan sakko sannan na sake shi na ja shi zuwa toiƙet din ya ɗan watsa ruwa, na taimaka masa yayi wanka sannan bayan ya shirya nayi masa jagora zuwa dining table ɗin
sosai ya ji daɗin ganin abincin dana dafa masa amma sai ya dake, na fara zuba masa farfesun tas ya shanye, ya kuma ci ɗan waken sosai sannan ya sha drink ɗin kas ɓoye murnar sa yayi sai ya ce
"kin iya ɓata wa mutum rai amma idan kin so kin iya daɗaɗa wa mutum" ya faɗa yana goge bakin sa da tabƙe napkin ɗin da ke gaban sa
"ai na dena, ba za a ƙara ba"
"gwanda dai" ya ansa a taƙaice
mun koma mun ɗinke sosai nida mijina kamar ba abinda ya faru tsakanin mu, sosai yake ji da ni da ɗana sosai, bilki ƙanwar baban aliyu ta kira ni kuma naji daɗi mun gaisa sosai da ita har na kuma tuna mata idan ta haihu ta kira ni duk da dai ba zuwa zanyi ba amma zan aika mata da ɗan abin hannu na na faɗa araina
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :27🌹
Yau na tashi duk na gaji da zaman gidan don haka ko da na haɗawa abu haidar breakfast sai na zauna ina yi mai ƴar hira kafin in kawo masa buƙatata
"kinga ni bana fahintar abinda kike ceqa yadda kika ganni nan sauri nake yi zan shiga meeting nan da 2hrs da wasu turawa kuma ko haɗa documents ɗin nawa da zanyi presenting banyi ba don haka ki faɗa kawai" na faɗa ina in'ina
"dama ina son fita ne"
"kije ina wa kika sani a garin nan"
"ni ko ina ne ma nidai kawai in fita" shiru yayi na ɗan wsu sakanni yana tunani, ni kuma Allah Allah nake yi kar yace a a don nasan halin sa
" sai kije sabon shopping mall ɗin dana buɗe a wuse zone 4 dama baki je, kiyi shopping ko ya kika gani" tsalle na daka
"yayi yayi yayi na gode sosai" na faɗa tare zuwa kusa da shi na rungume ni na manna masa kiss
"wow wow wow wow young lady yanzu fa na ce miki ina da meeting amma kina son ki hana ni fita" ya faɗa yana ƙoƙari janye jikin sa, sarai na fahimci abinda yake nufi don haka sai na ɗan sake shi, ya gama cin abincin shi ya fice tare da cewa in ina buƙatar wani abin in kira shi kafin 9:00, har ya shiga mota na bishi
"baka bani kuɗi ba haka zanje shopping ɗin ba kuɗi" na faɗa a shagwaɓe
"sweety nace miki shopping mal ɗinki fa zaki, ai ba sai kin biya ba"
"to in attendant ɗin yace bai gane ni ba fa ko kuma ma ai bai sanni ba ni kuma gaskiya bazan iya tsayawa yi masa bayani ba" atm card ɗinsa ya ɗauko ya bani
"ayi shopping lfy" ya faɗa yana me rufe ƙofar, driver ya ja suka wuce ina ɗaga musu hannu
sai ƙarfe 12:20 sannan na fita nasan zanje in tarar da mall ɗin a cike, i was so excited, nima at last zan fita, nayi shirya tare da shirya ɗana driver ya jamu sai shopping mall ɗin don yin shopping, nasan zan shiga in tarar da mutane sosai din wurin sabo ne gashi kuma a area yake
nayi mamaki sosai da na shiga na ga wurin kamar anyi shara ba kowa sai ma'aikata, sun wani jeru sai miƙo min gaisuwa suke, to me take faruwa ne, dama basa samun customer's ne na tambayi kaina
duk cikin uniform ɗin su blue and maroon colour, dey look really good haka zalika uniform ɗin yai kyau da tanbarin *ajaban* a gaban kowane uniform, manager ne ya matso da kansa don kwasar gaisuwa inda ni kuma na kasa hakuri na tambaye shi ya naga mall ɗin kamar anyi shara ba sa samun customers ne
"no yallaɓai ne yayi waya yace ayi evacuating mall ɗin wai zaki zo shopping shi yasa muka sallami kowa kuma muka hana kowa shigowa har sai kin gama" ya faɗa da fara'ar sa,
raina ne ya ɓaci don me zai ce a kori kowa taya ma za ai in yi shopping ni kaɗai ai it will very boring, wayata na dauko na kira shi
"hello habibti ya shopping ɗin naki"
"wane shopping bayan its boring, me yasa kace a kori kowa amall ɗin"
" so sorry habibti wai don ki sake ki zaɓi abinda ranki yake, kar ki samu damuwa bari insa a gyara"
"tayaya zanji daɗin shopping bayan babu wanda zan gani in tambaye shi
ya kyan product yake"
"am really sorry habibti, bari in gyara kin san nace miki ina meeting yanzu ma ɗan fitowa nayi zan ɗauki abu a office ɗina naga wayar ki"
"ok" na faɗa ina kashe wayar
ɗaukar shopping basket ɗin nayi na fara bi ina ɗaukar abinda nake so, abin mamaki sai ga masu aikin wurin suma kowa ya ɗauki basket sun fara zagaw suna ɗaukar abubuwa, mtsss lallai ma wato ya mayar dani wata yarinya ke nan
na cigaba da abina nayi kamar bansan ma suna yi, wajen cream na nufa don in duba hand cream, wani hand cream na gani na ɗauko, sai naji muryar wata a baya na
"mam wannan cream ɗin akwai pig's fat a cikin sa" juyowa nayi naga wata mace daga gani itama staff ce
"tanks wanne kike ganin ba pigs fat ɗin"
ta nuna min muka ci gaba da shopping ɗin da ita don naga alamar ta san aikin ta sosai har na gama sannan ta rakani counter, na biya aka biyo ni da kayana har mota na kama hanyar gida nidai kawai na fita ne amm ko kaɗan banji daɗin fitar ba mtsss
kashegari da daddare una dinner tare da abu haidar si wayata tai ringing, ina dubaw naga aunty bilki gaba na ne ya faɗi don abu haidar be sn muna waya da auntyn sa ba, a sanyaye na ɗauka
"salamu alaikum kin sauka ne" na tambaya ba tare da na kama suna ba
"wallahi tun la'asar na kasa samunki ne si yanzu, an samu baby girl"
" maa shaa Allah, Allah ya raya ta"
"amin amin ina alin" ta tambaya
"gashi nan"na faɗa ina shafawa haidar kai a matsayin kamar shi ake tambaya
to a gaishe min da shi da jikana"
"zai ji in shaa Allah, Allah ya rya ya baki lfy sai na kira" na faɗa ina katsa wayar don kar ta tambayi abinda bazan iya ansawa ba
"ƙawata ce a lagos ta haihu" na faɗa don kar ya kawo wani abin a ransa duk sai na tsargu kun san ance mara gaskiya ko a ruwa gumi yake
"Allah ya raya" ya faɗa atakaice
har muka gama cin abinci ina soki burutsu na ni gani nakeyi kamar ya gane basarwa kawai yayi amma a zahirin gaskiya bai gane ba, sai da muka gama dinner ya wuce part ɗinsa sannan na ƙule a ɗaki na kira ta mun sha hira sosai har nake tambayar ta iya tace tana nan ƙalau daga ƙarshe dai na buƙaci ta turo min da account number ta don in turo mata ɗan abinda za a asiya wa baby kayan suna, tai murna sosai inda daga ƙarshe tace zata turo min da acc number maƙociyar ta, kamar yadda tace kuwa sai gashi ta turo min
bayan kwana biyu na fita na je kai haidar allura daga asibitin na biya ta bank na tura mata 100k, na kira ta nace ta ɗau 50k ta bawa iya 50k, na sha godiya harda kukan ta, har iya sai da tayi min godiya ni duk kunya sai ta kama ni irin dukiyar da jikan ta ya mallaka ita mai iya kyautar dubu 100 ce amma wai yau anbata 50 shine take irin wannan godiyar, ko da yake dole ne tayin akayi la'akkari da irin yanayin da ta ke ciki Allah ya kyauta gaskiya akwai matsala sosai tsakanin da aliyu da *dangin sa*wanda zanso ace nasan masomin abin da ya haɗa su, wanda nake fatan in kawo ƙarshen sa
watan haidar bakwai da haihuwa na fara period ɗina ban kawo komai ba amma to my surprise tunda nayi sau ɗaya ban kuma bakuma yi ba gashi yanzu kusan wata biyu kenan wannan ya tabbatar min ina ɗauke da wani cikin, ba haka na so ba na so sai ɗana yayi wayo sosai sannan zan kuma haihuwa
amma ko dana faɗawa aliyu shi a ɓangaren shi abin ba haka yake ba yai murna sosai da sosai har wani special tattali nake samu, kasancewar wannan cikin ya zo da laulayin na rashin son cin abinci sai abu haidar ya ɗauko min nutritionist wacce zata dinga kula da zan dinga ci har ma da haidar ɗin kasancewar muna shirin yaye shi, macece me tsauri ba koamai take yarda inci ba har tafi linda tsauri, komai a tsare yake ban isa inci komai ba sai tace for the sake of the baby, da ta ishe ni ba shiri na sa aliyu ya sallame ta na ce masa na warke don bazan iya wannan iyayin nata ba me ciki da aka sani da kwaɗayi amma ni ba daman ince ina sha'awar wani abun sai a ce min for the ske of the baby Allah ya kyauta
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page:28🌹
Gaskiya cikin nan yana gwara nk ba kaɗan ba ba abinda nake da ya wuce kwanciya,
ganin haka ne yasani signing a face book na farayi don ya ɗebe min kewa, tunda haidar yanzu kusan a wajen nanny ɗinsa yake wuni,
duk da dai ban yaye shi ba saboda likita yace sai ya shekara sannan za a yaye shi amma yakan wuni wurin nanny ɗinsa don in samu hutu sosai,
ni cikin jikina sam baya gaba na in da hali da tuni na cire shi don ni naso ɗana yayi wayo sosai amma ya zanyi da abinda ya fi ƙarfina
yau na hau face book wani saƙo ne ya ɗauke min hankali inda naga an rubuta *children are d greatest gift from Allah pls cherish them*
saƙon ya taɓa min zuciya sosai na tsaya na karanta shi ya fi a ƙirga, wanda don tsabar shiga zuciyata da saƙon yayi har ban san lkcn dana tsinci kaina ina shafa ɗan cikin da ke jikina ba
Saving saƙon nayi don yayi min daɗi sannan nayi liking ɗin shi na kuma yi comment *jzk u just save a soul* sannan na fita,
haka na wuni ina juya kalmar nan a raina maganar haka take dubu nawane suke neman haihuwar basu samu ba amma ni na samu ba abinda na rasa amma wai ina kawo wani uzuri nawa mara tushe, Allah dai yasa mu gane
ko da na hau da daddare sai naga baiwar Allahn nan tai min reply da *am happy to be able to help u* naji daɗi saƙon ta na tura mata da ɗan murmushi ☺😊,
tun daga ranar kullum sai matar nan ta turo saƙo akan yadda ƴaƴa suke wata ni'ima ce a rayuwa, babu abinda ya fi su in mun gyara su,
har abada mu zamuci moriyar mu, mu more su muna raye sannan idan mun mutu su zame mana sadaƙatul jariya
ban taɓa hawa face book ba ba tare da na duba profile ɗin baiwar Allahn nan ba wacce sunan ta yake *salma abdul jalal* matar tayi gaskiya sosai,
kusan kullum sai munyi chatting da ita, ga shawarori da take rubutowa akan aure da tarbiyya yara, na zama da miji, *dangin sa* da dai sauran su,
tana bada shawara sosai akan kar mace ta sake ta auri namijin da *dangin sa* basa ƙaunar ta barin ma uwar sa
don kuwa muna ganin kamar idan mace ta auri namji shikenan to ba shikenan ba duk wacce ta auri namiji ba shi kaɗai ta aura ba gaba ki ɗaya da shi da *dangin sa* ta aura,
na kan yi mamaki to ni dai gani nayi aure amma mijina ya nuna min shi kaɗai na aura har baya son mu yi mu'amala da *dangin sa* ya sa katanga ya katange tsakanina da *dangin sa* ya nuna min shi kadai ne babu wani kuma
ganin face book bashi da sirri yasa na tura mata don Allah ina son ta bani contact address ɗinta mu dinga chatting ta whatsapp don ya fi sirri,
ikon Allah ta aiko min, amma to my suprise number nata na turai ne, ko dana koma profile ɗinta sai naga ashe balarabiyar saudia ce take zama a london, sannan likitar yara ce
nayi saving number nata muka fara chatting ta whatsapp da ita, a hirar tamu ne na gano ashe babba ce tama haife ni,
na ce mata nima mijina mamansa ƴar saudiyya ce amma ta rasu, sosai tayi mamaki wai ƙaddara ce ta haɗa mu, nima na yadda da cewar kaddarar ce ta haɗa mu, itama ta bani labarin cewar ta taɓa zuwa nigeria ta haihu amma ɗan ya rasu, na tausaya mata sosai
"kina da wasu ƴaƴan" na tambaye ta
"no babu, tun daga kanshi ban kuma ba , saboda na samu matsala wajen haihuwa, amma ina ruƙon ƴaƴan mijina yanzu" wayyo kuka ne kawai banyi mata ba amma na tausaya mata sosai
muka sha hirar mu sosai ranar mafi yawancin hirar tamu akan yara ne ina bata labarin haidar she was very intrested in hirar ɗan nawa, har na faɗa mata ina da ciki da bana so sai da naci karo da text ɗinta a face book sannan na soma son abinda ke ciki na,
tai min faɗa sosai tare da nasiha mai kashe jiki, naji daɗin hirar mu sosai na kuma gode mata, daga nan ta bani tips akan yadda zan dinga kula da mijina da yadda zan dinga tsara tafiyar da lamarin gidana naji daɗi sosai tunda nake babu wanda ya taɓa zaunar dani ya bani wannan shawarar sai wannan baiwar Allah da na sa mata suna mimma
ita ma taji daɗin sunan har tana cewa ta samu ƴa a nigeria, rayuwar gidana ta sauya sosai domin shi kan shi abu haidar ɗin ya ga changi sosai a tattare dani kuma duk godiyace ga mimma,
irin tattalin sa da nakeyi da irin yadda nake tsara komai ba kamar da ba wani lkcn har cewa yake yi kamar ba zainab ɗin daya aura ba don yanzu duk wata hidima tashi na ɗauke ni nake yi ba kamar da ba da rabi nayi rabi masu aiki suyi,
kullum na hau akwai sabuwar dabarar da mimma zata bani na harkar sha'anin gida da kuma aure kuma idan na gwada kamar yankan wuƙa haka zanga yaci
don haka yanzu mijina ya kuma sakankancewa dani, baya iya aikata komai sai dani ko shawarata wata shaƙuwace sosai ta shiga tsakanin mu da shi wanda har office idan abu ya faru yakan kira ni ya faɗa min inbashi shawara ko tafiya yanzu abu haidar ya daina yi sai dani
dai dai da kayan da zai sa sai ya kirani na nuna masa ko kuma in ɗauko masa in kuwa ba haka ba bazai sa ba har sai na gama abinda nake yi na ɗauko masa, duk wannan shaƙuwar tamu duk ta dalilin mimma ne babu abinda zance mata sai dai godiya
Ga son haidar da takeyi kusan kullum sai ta tambayeshi, ko tace me ya saka yau turo min hoton shi nakan tura mata wanna ne yasa pics ɗin haidar a wayarta sau fi nawa,
page guda gare shi a profile ɗinta na face book, hatta da profile pic ɗinta na face book da whatsapp pic ɗin haidar ne tana son shi ba kaɗan bahar video taping ɗinsa take sani yi mata in tura mata tai ta kallo, wannan ne yasa nima na ƙara son baiwar Allah nan na kuma ƙara sakin jikina da ita kun san ance me ɗa wawa
cikina yana ƙara bunƙasa ina ƙara samun kulawa daga wajen mijina tare da samun shawarwari daga mimma, harya isa haihuwa addu'o'i sosai mimma ta bani na mata masu ciki wanda na kasance ina yin su ba dare ba rana
ranar wata alkhamis da safe na tashi da naƙuda wanda Allah ya taimake ni abu haidar yana gida bai kai ga fita ba yana sunku tata bai tsaya ko ina ba sai asibiti inda bamu wani daɗe da zuwa ba na sauka lafiya tare da samun ɗana namiji
nai murna sosai tare da gode wa Allah ubangiji (swt) da ya bani haihuwa lfy tare da adduar Allah ya raya mana su bisa sunna ma'aiki (saw)
duk murnan nan da nayi ban kai abu haidar don shi har kuka yayi sai dana ɗan tattaushe shi sannan yayi shiru bansan dalilin kukan nasa ba amma nasan cewar wani abun ya tuno shi yasa shi yin kukan ko ma dai menene Allah ya magance mana, na faɗa a raina
bamu wani daɗe da haihuwa ba aka bani sallama gani ni lfy nake haka zalika ɗan ma directly gida muka koma don mu gyara jikin mu, wata mata me suna baba ita ce a gidan yanzu mama ce ta kawo min ita tun cikina yana da wata takwas wai saboda haihuwa ita bata son ƙedaran su dinga taɓa jarirai ba bisimillah suka iya ba
itace ta wanke min ɗana tas ta shirya shi nima ta samin ruwan wanka na yi naji daɗi sai bacci daga ni har ɗan jaririn
abu haidar ne ya faffaɗi haihiwar tawa don ni ko ta kan waya ma ban bi ba ina ta kaina, da daddare daya dawo directly ɗakina ya shigo ya ganmu kwance reras ni da ƴaƴa na sai ga hawaye again a idon sa
tooo wannan kukan sa na biyu kenan a yau lfy na faɗa ina jawo shi zuwa jikina tareda shafa masa baya alamar lallashi
" idan na ganki da ƴaƴan nan nawa sai in godewa Allah wai yau ni aliyun dana rayu cikin ƙyama da kyara daga dangi na wai yau nine da ƴaƴa har biyu sai inji zuciyata ta karye"
kara shafa masa baya nayi tare da cewa
"duk abinda ka gani ya samu bawa muqaddari ne daga Allah haka Allah ya ƙaddaro masa don haka duk abinda ya same mu bama cewar ba zamu yafe ba sai dai mu yafe hakan zai kara kusan tamu da ubangiji" gyaɗa kai yayi
"zainab kenan wasu abubuwan sun wuce mutum ya yafe sai dai kawai ya ɗauke kansa daga wurin gaba ɗaya"
"kamar me fa"
"kar ki damu bari inje in watsa ruwa a jikina yau duk zan feɗe miki daga biri har wutsiyar sa na abinda ya haɗa ni da dangi na har na watsar da su"
to kawai nace ya manna min kiss tare da faɗin i love u with all my heart sannan ya wuce toilet don wanka, komawa nayi na kwanta ina tunanin yau me zanji ya haɗa aliyu da *dangin sa* Allah dai yasa matsalar da zan iya warware wace da sauki na faɗa a raina
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :29🌹
*Asalin labarin*
jakara ta kasance unguwace tsohowa zaka gane hakan ne idan kayi la'akkari da irin gine gine da ke cikin unguwar wanda yawancin su ginin ƙasa ne, inda a ɗaya daga cikin gine ginen ƙasa ya kasance na mlm musa me icce ne,
sana'ar icce yake ko an san shi sosai kasancewar iccen shi akwai sauƙi sosai, yana da mata ɗaya tare da yara 10 maza 5 mata ma 5,
acikin ƴaƴan sa sani shine na biyar, yaro ne zuciya tun yana ƙarami, yake neman nasa na kansa, mlm musa yana da mata ɗaya wadda ƴaƴan ta suke kiran ta iya,
markaɗe shine sana'ar, inda in ta kunna injinmarkaɗen ta tun safe sai ya kai 1:00 na rana a kashe ba saboda tsabar markaɗe
mlm musa beyi ilimin boko ba don haka be sa ƴaƴan sa, ya kan de jasu zuwa wajen sana'ar sai da itacen sa su taimaka mishi, sani shi kaɗai ne yake makarantar boko a gidan shima da kanshi ya sa kanshi kuma yake ɗaukar nauyin kansa don daga malam ɗin har iyar babu wanda ya damu da boko
abokin sani wanda gidan su yake jikin su sanin shine kaɗai yake ƙarfafa wa sanin akan karatun boko wanda tare da shi suke yi, kuma da taimakon Allah Allah bai hana sani wani abin na biya wa kai buƙatar mkrt
sai ya wuni yana taimakawa iya markaɗe inda in ta bashi ladan aikin sa sai ya adana yayi hidimar mkrt da shi a haka yake karatun nashi, ana ta gurgurawa da daɗi ba daɗi haka suka dinga karatun su inda duk lkcn da abu ya kakare wa sani abokin nan nasa me suna buhari shine dai me taimaka masa don bai isa ya tinkari iyayen sa ba sai suce ai ba su suka aike shi ba
ko da suka gama secondary school, sai suka fara fafutukar neman jami'a, inda Allah ya taimake su suka samu abu zaria, inda suke karantar ɓangaren lab science duk da dai sani likota ya so zama amma hakan bai samu ba
suna cikin shekarar su ta biyu a jami'a gwammatin kano ta raba scholarship, da taimakon malamin secondary ɗin su wanda ya shige musu gaba suka samu scholarship ɗin inda zasu india karatu
murna a wajen waɗannan bayin Allahn ba a cewa komai ba, ba su ba har iyayen su, gwanda mahaifiyar buhari wadda ake cewa hjy da gumin ta ɗan ta yake karatu,
amma mlm musa da iya waɗanda basu san ta yadda ɗan nasun ya samu ilimin ba ma suna ba a barsu a bayan wajen murnar ɗan su zashi india karatu, duk wani wanda yake mu'amala da iya ko mlm musa ya san da wannan zancen
a kazo aka fara shirye shiryen tafiya duk wannan ɗokin da iyayen da sani suke ko da aka zo batun kuɗi duk sai suka noƙe, sani shi yayi fafutukar shi shi kaɗai ba tareda taimakon kowa ba har Allah yasa suka ɗaga zuwa kasar india lfy don karatu
sun sauka india lfy sun fara karatun su lfy lau ba kama hannun yaro duk inda kaga ɗaya sai kaga ɗayan haka suke, sun maida hankalin su sosai akan abinda ya kawo, a haka har suka ƙare shekarar su ta farko lfy ba matsala, ba su dawo gida ba acan suka zauna sukayi hutun to in sun dawo ma wa zai basu kuɗin jigin komawa
a shekarar su ta biyu a mkrt ne Allah ya haɗa sani da matashiya ƴar saudiyya, me suna salma, da farko ƙawance ne ya ɗa su, amma daga baya sai ƙawance su ya koma soyayya
Tun suna yi a rufe har suka fito da shi kowa ya sani, salma riga sani shiga mkrt don ita a 3rd year ɗin ta take, ina take karantar medicine,
Soyayya su ce ta kaisu ga ɗaura aure don gudun gujewa ruɗun shaiɗan, buhari ya so ya hana sani yin auren nan, amma sani ƙiri ƙiri ya ƙi ya biyewa salma suka ɗaura aure, inda suke tare a sabon gidan su
soyayya suka dinga zubawa sannan ga karatun suna yi hankalin su kwance duk wanda ya gansu saisun bashi sha'awa ganin yadda suke son juna tare da tattalin junan su
Suna cikin shekara ta biyu da aure Allah ya sa salma ta samu ciki, murna sosai sani da matar sa salma suka dinga yi, suka shiga tattalin cikin,
tun buhari na kau da kai daga lamarin su har ya koma shima yayi tsamo tsamo cikin hidimar cikin siyayya sukayi sosai har Allah ya kaisu lkcn haihuwa
lami lafiya ta haihu amma ƴar ta zo ba lfy, inda bayan kwana biyu tace ga garinku nan baƙin ciki a wajen salma da sani kamar ba gobe har kuka sai da suka yi, sannan daga baya suka dangana
pls kuyi haƙuri da wannan yau uziri yai min yawa salam 🙏🏻
[7:44PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :30🌹
Sai da ta ɗan huta na shekara ɗaya sannan suka kuma trying, kuma Allah ya basu sa a ta sami cikin, wannan karon ba karamin kula sosai suka ba wa salmar ba, sannan suna karatun su lfy, inda ahalin yanzu salmar tayi graduating shi kawai take jira ya gama su koma gida
Sun gama yanke shawarar cewa baza su zauna a nigeria ba sannan bazasu zauna a saudiyya ba zasu samu wani garin su zauna ne, ganin haka yasa suka yanke hukuncin zuwa nigeria salmar ta haihu daga nan sai su wuce saudiyya don dangin salmar suga babyn kafin nan sun gama shawarar inda zasu zauna
Duk wani siyayya na haihuwa sun gama, lkcn da sani ya gama course ɗin sa a lkcn cikin salma yana wata tara haihuwa ko yau ko gobe don haka sai suka shirya tafiya nigeria inda suka bar buhari zai yi musu lodin kayan su ta cargo kafin ya biyo bayan su
Sun sauka lfy a nigeria inda suka wuce jakara directly sani yaga yadda unguwar ta ƙara lalacewa, wato a nigeria in ba unguwannin masu kuɗi ba to vaza ka taɓa ganin cigaba ko, ya faɗa a ransa
A farkon layin su taxi ɗin da suka ɗauko ta faka, suka tako a ƙafa, salma tana ta mamakin irin wannan rayuwar amma bata kushe masa ba ganin shi take so kuma ba anan zasu yi rayuwa ba,
har suka cikin gidan yana mata bayanin yadda halin rayuwa yake a nan nigeria mu ita kuma tana gyaɗa kai cike da tausayawa, a tsakar gida suka ci karo da iya inda da sairi sani ya je ya rungume ta
waigowa iya tayi cike da tsoro waye wannan, ganin ɗan ta da ta daɗe bata gani ba yasa yin saurin ƙara ruƙunƙume shi, tare da sakin kuka, sai daya rarrashe tayi shiru, sannan ya nuna mata salma wacce tun shigowar su tana tsaye tana kallon su
"iya ga matata dana aura a india, amma ƴar saudiyyace" ya faɗa yama miƙa salma hannu wanda ita kuma ta ƙaraso tare da riƙe hannun nasa
wani shegen kallo iyar ta bita da shi daga sama har ƙasa, ganin salmar da tsohon ciki ya sa iyar ƙara murtuke fuskar ta
"abinda kaje ka koyo kenan a indiar, kazo da mace da tsohon ciki kace matar kace, uban waye ya ɗaura maka aure da ita, ko an gaya maka saboda bamu da ilimi yasa kake tunani cewar bamusan sai da aure ake kiran ɗa ɗan halak ba" ta faɗa tana miƙa wa salmar harara, wanda hakan ne yasa salmar sunkuyar da kanta tare da ƙara shigewa jikin mijin nata
wannan abun da salmar tayi ƙara tunzurawa iyar rai yayi"au karuwancin da kuke yi zaku zo ku ƙara nuna min a gaba na, ai ba sai kun kwatan ta ba cikin da ke jikin ki ya isa ya nuna sheƙe ayar da kike yi da wasu mazan"
"iya ba fa haka bane wallahi matata ce, sai da na aure ta fa sannan, wannan ma ba shine na farko ba ta farkon ta rasu"
"kawai cewa zakayi ta gama zuzzubar da cikin mutane shine wannan ta ƙi zubar da shi ta maƙala maka, ta wai ma waye shaidar cewa ka aure tan"
"iya buhari mana shima yana nan tahowa cikin satin nan"
"ni zaka rufe a bai bai, to wallahi ban yadda cikkn nan ba naka bane shege ne, kuma bazan yadda ka zauna da karuwa ba sai dai ka ƙyale ta ta koma can gari su taje taci gaba da watsewar ta, haka kurum bazan haɗa zuri'a da kuruwai ba"
"iya don Allah kidaina faɗin hakan wallahi matata ce"
"wai baka ji me nace bane ban yadda ba, me kake in cewa mutane sani ya je turai ya dawomin da karuwa a matsayin matar sa harda cikin shege, wallahi ƙarya kake ban tonawa kaina asiri ba babu ɗan da ya isa ya tona min" ta faɗa tana gyara kallabin wanda sauran ƙiris ya faɗi saboda tsabar masifa
babu yadda sani baiyi ba don ya fahimtar da iya amma ta rufe idon ta tai ta tafka bala'in tun suna yi su kaɗai har ƴaƴanta suka fara shigowa suna taruwa
duk wanda ya shigo yaga sani ya dawo sai ya fara murna amma da yaji faɗan da iya take yi sai su koma bayan ta suna goyan bayan ta na bai isa ya haɗa su da shege ba, a cikin faɗan nasu ne ma yaji rasuwar mahaifinsu shekara uku da suka wuce abu goma da ashirin suka haɗu suka haɗar masa ya rasa acikin ƴen uwan nasa wanda zai ɗan fahimce ahi koda so ɗaya ne su dai burin su kawai ya kori salma da cikin da ke jikin ta, su tsaya ma suji abinda zai ce su ƙi kawai haniya suke yi tsakanin su tare da rantsuwar baza su zauna da karuwa ba
kasancewar gidan su buhari katangar su ɗaya da su sani yasa hjyr su buharin jin hayaniyar tasu, tasan tsakanin iya ne da ƴaƴanta kamar karta shiga sai kuma wata zuciyar tace ki shiga haƙƙin maƙotaka ce tasa, hijabin ta dake jikin ƙyaure ta ɗauko ta saka tayi gidan iya
ko da shiga taga sani tayi mamaki amma sai ta danne don sulhu ta zo yi daga baya taji lbrn ɗan natan, tambayar abinda ya faru tayi inda wata matar wan sanin tayi wa hjy bayanin abinda ya faru, to ita hjy bata ga abin tada jijiyoyin wuya ba menene don yaro ya auro farar mace ta faɗa
har wajen iyar tajee tayi mata nasiha akan tabi abin a sannu don a samu a shawo kan maganar amma iyar ko sauraran ta batayi ba inda daga ƙarshe ta ƙare wa hjyr tanadi tas har da cewa ita taga ɗan ta ita ma ta jira taga da wace tsararbar ɗan natan zai zo mata dashi
ba haka hjy ta so ba ta so iyar ta kwantar da hankalin ta har a samu bakin zaren amma daga dukkan alamu iyar ta riga tayi nisa kuma harda laifin ƴaƴanta don kuwa su suke ƙara zugata, can ta hango sanin idon shi ya kaɗa yayi jajir sai lallaɓa matar da yazo da ita yake yi wacce ita kuma take a tsugunne tana kuka, su kuma ƴen uwan nasa suna gurin iyar suna ta zigata
har kusa da shi hjyr ta ƙarasa tayi masa nasiha sosai akan darajar uwa sannan ta kama hanyar gida don bata ga alamar iyar tana da niyyar sauraren wani a wannan lkcn ba
haka aka wuni ana abu ɗaya babu sassau a cikin lamarin ta tubure sosai sai salmar ta bar gida, inda maƙarraban ta ke zigata
sani hankalin shi ya kasu biyu ga faɗan da iya take tayi ta ƙi shiru duk tabi ta tara mutanen unguwa ta sheganta masa ɗa tun kafin ya zo duniya, ga ita kuma salmar ta tada hankalinta baza iya zama ba tafiya zata yi, ga wani azababben ciwon kai da yake damun sa wanda ya sashi yaka ganin dishi dishi, matsawa yayi kusa da salmar wadda har yanzu take kuka domin ya lallashe ta amma ga mamakin sa jikin ta zafi rau da shi
"subhanallahi salma zazzaɓi kike yi ne" ya faɗa yana ƙara taɓa jikin ta tabbaa zazzaɓi ne, tausayin ta ne ƙara rufe
"isbiri la tabki habibti" ya faɗa tare da share mata hawayen da suke gangariwa daga idon ta
"saufa ashtari lakkid dawa" gyaɗa kanta kawai tayi, tare da gyara zaman ta
tashi yayi ya miƙe don ya je ya samo mata magani, dole ne ya bar salma ta tafi saudiyya, dole ne ya haƙura salma har sai Allah ya daidaita su da mahaifiyar sa dole ne salma ta tafi in ya so idan ya fahimtar da iyar cewar salmar halak malak ɗin sa ce in yaso daga baya sai su kuma tsara yadda zasu ci gaba da rayuwar su, amma bazai iya rayuwa ba salma ba taya ma zai iya rayuwa babu salma a cikin ta dole yasan yadda zai yi salma ta riga ta zama komai na shi na rayuwar zai san yadda yayi ya shawo hankalin iyar bayan ya mayar da salmar yasa ganin salmar anan ne yasa iyar tayar da hankalin ta amma da zarar salmar bata anan idan hankalin iyar ya kwanta in shaa Allah zai san yadda zai shawo kanta ta yadda da auren nasu da salma hakan zaiyi ya faɗa yana gyaɗa kansa
gabaki ɗaya tafiya yake yi amma sam bai san inda yake jefa ƙafarsa ba don yayi zurfi a cikin tunani, baya iya ganin komai kawai tafiya yake yi ƙugin mota kawai yaji tare da sunkuce shi da motar tayi ta maka shi da ƙasa wani azababben zafine yaji ya ziyarci kansa wanda bai taɓa ji ba, ƙoƙari yayi don ya motsa amma sai ya kasa, idon shi a buɗe suke amma baya gani komai sai duhu haniyar mutane yaji suna ƙarasowa inda yake
"kar ku taɓa shi kanshi ne ya fashe yake zubar da jini" tun yana iya fahintar abinda suke cewa har ya koma ya daina
inna lillahi wa inna ilaihir raji'un ai ya mutu inji wani daga gefe
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling*
0 comments:
Post a Comment