Page :31🌹
Salma tana zaune ainda ya tafi ya barta, gaskiya dole ne in bar musu gidan su, ta faɗa a ranta, yau ɗinnan kuwa gwanda ko hotel ne ya kama min, kuma da na samu jirgin saudiyya in gudu ta faɗa tana ƙara gyara zaman ta a saman ƴar tabarmar da take zaune
duk ta gaji hankali gabaɗaya a tashe yake sai kace sun ga wani kashi yadda sukai treating ɗin ta kamar ba musulmai, gaban ta ne ya yanke ya faɗi,
"subhanallah" ta faɗa tare da dafe ƙirjin ta, cigaba yayi da faɗuwa inda ita kuma ta ci gaba da kwararo addu'o'i tana mai neman tsari da duk wani sharri da zai zo gareta
Gafara gafara gafara kawai taji ana cewa duk da dai bata san abinda yake faruwa ba amma ta ɗago kanta don taga menene
Mutum taga an shigo da shi an shige da shi ɗakin iya, tsayawa tayi tana tunanin lfy, kukan iya taji tare da kururuwa tana ƙwalawa sani kira, bata san lkcn da ta zabura tayi ɗakin iyar ba, bangaje mutane tayi ta yi har sai da taje kan sa,
"innalillahi wa inna ilaihi raji'un" shine kawai abinda bakin ta yake faɗi
Durƙusawa tayi kjsa da shi ta fara kuka cikkn nutsuwa, iya da ke kansa tana kururuwa ta ɗago don jin mutum a kusa da ita, tana ganin salma tayi kanta da duka da zagi
"mayya daga zuwan ɗana kin lashe masa kurwa" ta dinga dukan ta tana zagin ta
ko kaɗan salma batai yunƙurin hana ta ba don ita raɗaɗin da yake damunta a zuciyar ta ya fi ƙarfin dukan da iyar take mata, kuka kawai take yi tare da yin istigfari ga Allah ubangiji (swt)
hjy tana gidan ta ta kuma jiyo hananiya da kururuwa tare da ƴen koke koke, hijabin ta kawai ta kuma ɗauko wa tayo waje, tana zuwa gidan ta tarar da mutuwar sani da kuma irin jibgar da iyar take yi salmar wanda babu wanda yai yunƙurin hana iyar
da sauri taje ta janye salmar,
"idan kika kashe fa" inji hjy
"na kashe banza na kashe wofi ai nima kashe min ɗana tayi Allah ya isa tsakanina da ke shegiya" ta dinga bin salmar da zagi, ragiwar ƴaƴan iyar suma suka yooo chaaa wai sai sun dake ta ikon Allah
ba shiri hjyr ta janye salmar zuwa gidan ta don taga alamar zasu iya yiwa salmar lahani in aka bar musu ita, gida ta wuce da ita direct, ta ɗauko panadol da ruwa ta ba don taji jikin nata zafi rau da shi oohhh Allah haka yake ikon sa
ko da tasha sai tayi mata shimfiɗa don ta ɗan kwanta don a gaskiya tana buƙatar hutu don sai ta iya shiga wani hali ga halin da take ciki,
har akayi wa sani sutura aka fita da shi salma tana kwance ita ba bacci take yi ba komai ba, hjy ta so ƴen uwan sanin su bar salmar tayi masa kallo na ƙarshe amma ƙiri ƙiri suka ce idan ta zo sai sun lahanta ta me yayi zafi inji hjy
Salma ranar taga baƙin ciki ido da ido ta rasa abinda yake mata daɗi burin ta kawai gari ya waye ta kama hanyar garin su, ko da dai tana tunanin me zata cewa iyayen ta idan sun ganta da ciki amma hakan ita a ganin ta sai ya fi mata kwanciyar akan irin wulaƙan cin da take fuskanta a nan
cikin dare nakuɗa ta kama salma, ta sha wahala sosai, hankalin hjy ba ƙaramin tashi yayi yadda taga salmar tana nunfashi sama sama gashi ta kasa nishin, ita hjy ba turanci balle larabci ita salma ba hausa ba, don haka sai communication yai wuya sosai a tsakanin su ga naƙuda ta zo da matsala sosai, ga dare babu abin hawa, addua kawai hjyr ta dinga tofawa tana ba salmar tana sha wuya sosai kafin daga bisani Allah ya sauke ta lfy gab da asuba, ta samu ɗanta namiji
Shi kanshi ɗan a wahale ya zo don sai da aka watsa masa ruwa sannan yai kuka, hamdala hjy ta dinga yi, inda salma ba abinda take yi sai kuka,
hjy ta haɗa mata ruwan wanka don ta ɗauraye jikin ta, hjy ta kama ta ta kai ta har banɗaki ta ɗauraye mata jikin ta sannan ta haɗa mata ruwan lipton me zafi tace mata ta sha,
ta kuma haɗa ruwa ta wnke ɗan tsaf da shi ta ɗauko sabon zanin goyo ta naɗe shi a ciki ba abinda salmar take yi har yanzu illa shash sheƙar kuka barin ma idan ta kalli yaron, hjy sai ta ɗauka ko tausayin sa take ji
shimfiɗa ta ƙara gyarawa salmar sannan tai mata umar nin ta kwanta, ita kuma ta ci gaba da kimtsa komai, salma kwanciya tayi ta tasa ɗan ta a gaban ta tana kallon sa wasu zafafa hawaye ne suke ta sintiri a idon ta, tausayin sa ne taf zuciyarta,
ko ya rayuwar sa zata kasance ta tuna irin tattalin da sani yake yiwa cikin tun kafin ya zo amma wai yau ga shi ya zo amma kuma ba sani, ya za ayi ta iya tafiya da ɗan da babu uban sa, inda ma ace sanin yana da rai ne da ta tafi da shi, amma yanzu taje tace wa iyayen ta ɗan waye, waye zai yadda cewar ba shege bane
zargin ta za a dinga yi, kuma yaron ya tashi a dinga yi masa kallon shege tunda babu wanda ya san uban sa, kuka ta kuma fashe w da shi, ta rasa mafita, ita baza ta iya zama a nan ba don ƙiri ƙiri mmn sani ta nuna mata ƙiyayya wanda har hakan yai sanadiyyar mutuwar mijinta, idan na tafi da kai bazan taɓa mantawa da wannan baƙin ciki ba, idan na tafi da kai shari'ar garin mu bazavta bari in rayu da kai ba, idan na tafi da kai har abada da tabo zaka tashi, rayuwarkar anan itace rufin asirin mu ni da kai, idan da rabon mu ƙara haɗuwa Alƙah ya sada mu da alkhairinsa ta faɗa idon ta taf da hawaye
ta gama yanke shawarar abinda zatayi, ta kalli yaron ta kallo na ƙarshe ta sinbace shi a kai tare da yi masa addua, sannan ta tashi saɗaf saɗaf tayi waje ba tare da hjy taji ba
ko da hjy ta tashi da asuba kasancewar ta ɗan kwanta bayan ta gama kafin asuba tayi, tai mamaki ganin ɗan jariri shi kaɗai sai ta ɗauka ko salmar ta shiga banɗaki ne, tai jiran har ta gaji don haka sai ta wuce ta duba ta, ba inda bata duba ba ba ita babu alamar ta
har gari ya waye ana neman salma bata ba dalilin ta a haka suka sadauƙar da ta gudu, haka mutan gidan hjy suka haƙura da neman nata suka zubawa sarautar Allah ido
hjy ce ta ɗauki ɗan jariri domin sada shi da *dangin sa* gidan iya ta shiga da ɗan jariri, iya tana zaune a falon ta ana ta cin naman salmar tana sha zagi wai dama shege ne ahi yasa ta gudu ta bar shi, shigowar hjy bai sa sunyi shiru, suka gaisa amma da ƙyar iyar take ansawa
hjy ta ɗauki ɗan ta ɗora shi a cinyar iya, "ga abinda aka samu nan" wani wulli da iyar tayi da jaririn daba dan hjyr tayi sauri ta sa hannun ta ba da tuni jaririn ya sha ƙasa,
"ya zaki ɗauki kazantar nan ta najasa ki ɗaura min kan tsabta taccen hannuna" ta faɗa tana goge hannun ta a ƙasa kamar ta taɓa kashi
"haba iya me yayi miki idan iyayen shi kina ganin sun ɓata miki shi me yayi miki, ko ba komai kya tausaya masa mana ta yadda ya rasa iyayen sa lkc guda"
Wata ƙanwar iyar ce tayi carab tace
"ai mummunar ƙaddara gare shi duk wanda ya ɗauki yaron nan yai ta gamo da mummunar ƙaddara kenan tunda shi haka aka hallice shi da ita tun randa zaizo duniya ƙaddarar tasa ta fara nunawa" nan suka ɗauka haka ne kam babu shakka
hjy tsayawa tayi tana kallon jahilci tsabarsa, tqna mamaki dama hannun ka yana ruɓewa ka yanke ka yar, shiru tayi sannan tace
"to nidai ayi haƙuri atunda ita mahaifiyar shi ta gudu kinga ruƙon yaron nan ya dawo hannun ki a matsayinki na kakarsa"
"uwar shi ma ta gudu saboda ƙaddarar da ke tattare da shi sai ki ɗauko shi ki ce uwar mu ce zata riƙe shi ke me yasa baki riƙe shi ba" inji wata ƴar iyar
"rabu da ita bata san cewar haushin ta neke jiba, don sai yanzu na fahimta cewar babu munafiki sai buhari, don ba gashi ya turo marigayi da wannan karuwar ba, shi ya zauna ya lafe so yake yi idan ƙura ta lafa ya lallaɓo ya dawo ya tunkuɗa ɗana ga halaka ya haɗa shi da ajalin sa, Allah ya isa tsakanina da shi munafiki kawai annamimi, maci amana kawai" ta faɗa tana kuka
abin nan da iyar tayi ba ƙaramin ɓata wa hjyr rai yayi ba tshi tayi tare da sauke ɗan a gefe tayi hanyar waje,
"zo ki ɗauke dawo ki ɗauke don babu wanda zai ɗauki wannan mummunar ƙaddarar a cikin zuri'a ta" tana jin ban bamin iyar da muƙarraban ta na ta dawo ta ɗauki ɗan amma tayi burus da su
bayan ta koma gida ta shige ɗakin ta tafara hidimar ta ,can zuwa anjima ta fara jin kukan jaririn tausayin sa ne ya kama ta ya fara jin yunwa kenan ta faɗa a ranta, ta ɗauka abin wasa ne amma ga mamakin ta sai taji har yaro ya doshi kusan minti talatin yana kuka normal kukan jarirai har yazo yana kuka kamar ana cutar da shi ne
ba shiri hjy ta yayimo hijabin ta ta fice abin mamaki da takaici a tsakar rana a dandamar ƙasa ta ga karirin sabuwar haihuwa, guje taje ta ɗauko shi tana kuka wannan wane irin rashin imani ne dama zafin rana yake kuka, rungume shi tayi ta kara sakin wani sabon kukan tausaya wa yaron, ta juyo ta kalle su kowacce tana sha'anin ta
"in Allah ya yarda sai yaron nan da kuka wulaƙanta ya zame muku inuwa" ta faɗa tana ficewa
baƙaƙen maganganu ne suka raka hjy tana jin su tayi tafiyar ta sune basusan Allah ba amma ita tana da imani kuma tasan Allah koda ace yaron nan shege ne ai bai cancanci ayi masa haka ba amma dubi yadda mutanen nan suka wulaƙanta ta ɗan jaririn da bai ji ba bai gani ba, ta duba fuskar ɗan jaririn da tayi ja jajir saboda tsabar dukan da rana tayi masa
"Allah ya raya min kai ka zama inuwa ga waɗanda suka wulaƙanta ka randa aka haife ka" ta faɗa tana goge ƴar ƙwallar da take fito mata saboda tausayin sa
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
page :32🌹
haka hjy ta ci gaba kula da ɗan jaririn wanda ranar suna ta sama masa sunan ɗan autan ta daya rasu wato Aliyu, har gidan iya taje ta kaimata shi tare da faɗa mata sunan da ta sa masa, amma iyar sai ta bita da baƙaƙen maganganu, haka ta taso ta bar gidan zuciyarta duk ba daɗi
satin aliyu uku da haihuwa buhari ya dawo, yai takaici tare da baƙin cikin abinya samu abokin sa, yai kuka kamar ba gobe, sannan ya tausaya wa aliyun ganin irin halin daya shiga tun randa zai zo duniya
har gidan iyar ya shiga don yayi mata bayanin yadda abin yake amma iyar ta toshe kunne ta, ta rufe idon ta ta wanke shi soso da sabulu tai masa tas, ba shiri ya bar gidan ,ko da hjy taga yanayin da ya dawo tasan cewar bai samu yadda yake so ba don haka sai tayi shiru
ko da kayan su sani su ka zo buhari sai daya kwashe duk wani kayan da ba na sanin bane sannan ya kaiwa iyar, amma iyar si ta zo tace wai sai dai abata kayan da buhari ya zo da su gabaɗaya, duk hjy ta nuna mata waɗanda suka ɗauka, kayan jarirai ne kawai, sai hotunan sanin da salmar waɗan da suka ɗauka tare don a ajiye wa yaron ko da nan gaba zai tashi sai ya ga iyayen sa
Ganin irin kayan jariran da suke wajen ba ƙanana bane ga uban yawa ya sa iyar nan fa ta hau bala'i ai ɗan ta ne ya siya kuma basu da gadon don haka sai an bata, buhari ne ya rufe ido yai mata tas hjy bata tanka masa ba don ita ma iyar ta kaita bango
me zatayi da kayan jarirai ba mamaki so take yi ta karɓa ta siyar, hatta kayan salmar an ba iyar amma wai kayan da za a sawa ɗan jaririn shine tazo tana tada jijiyoyin wuya sai an bata, ran hjy ya ɓaci sosai, sai ta ƙyale buhari yai maganin ta, da iyar taga baza ta samu ba sai ta haƙura ta fice tana Allah ya isa wai sun ci haram
haka hjy ta ci gaba da kula da ɗan marayan ɗan ta wanda buhari yai rawar gani sosai wajen tallafawa yaron har ragon sun sai da ya siyo aka yanka masa, duk da dai ragowar ƴaƴan hjyr musammam ma matan basu so hjyr ta ɗauki aliyu ba amma babu yadda suka iya tun da hjyr ta dage
aliyu ya taso da kuzarin sa idan ka ganshi, sai ka rantse nonon uwarsa yake sha yai shar da shi ga kyau kullum ƙara fitowa yake kamar su ɗaya da mahaifiyar sa, kamar tayi kaki ta tofar, wannan abun ne yake ƙara tunzura iyar take cewa yaron ya gado maitar uwar sa
aliyu yana shekara ɗaya da rabi, baba wato buhari kenan yai aure ya auro mama halima daga bauchi, Allah ya haɗa shi da mace ta gari, tana taimakawa hjy kula da aliyu sosai, ta so ɗan sosai da sosai, bata daɗe ba ta samu ciki, ko da lkcn haihuwa tayi Allah ya sauke ta lfy ta haifi ɗan ta namiji wanda yaci sunan bbn buhari wato ahmad amma ance masa tijjani
Rayuwa me daɗi suke ciki da buhari da iyalen sa babu abinda yake rabawa tsakanin aliyu da tijjanin komai ɗaya yake mu babu bambanci wannan abun yana farantawa hjy rai sosai don duk wanda ya kula da ɗan wani Allah zai kular masa da nasa
lkcn da tijjani ya isa yaye sai hjy ta haɗa su da aliyu ta riƙe ita kuma haleema a lkcn tana laulayin cikin ta na biyu don haka sai kawai ta ji da kanta, ko da lkcn haihuwa yayi sai halima ta roƙi alfarma awajen baba buhari na taje bauchi ta haihu be musa ba amma yace mata bazata tafi da su aliyu ba, ba haka ta so ba amma ba yadda ta iya
ranar wata jumma'a suka kama hanyar bauchi tare da buharin don ya kaita, tafiyar da badu kuma dawowa ba, don kuwa a hanya suka haɗu da haɗarin da yayi sakamakon rasa rayuwar su
sai da suka kwana biyar sannan hjy ta samu lbr ba shiri ta kama hanyar bauchin hankali a tashe, ta je ta tarar da wannan tashin hankalin, tun ran da suka rasu aka so faɗa mata amma kasancewar ba ɗan aike ya sa bata ji da wuri ba
haka hjy ta ci gaba da kula da ƴen marayun ƴaƴan ta har guda biyu, gwanda tj shi yakan samu taimako daga ɓangaren mmn sa ko ƴen uwan uban sa, shi kuwa aliyu sai abinda hjy ta samu tayi masa
rayuwa taci gaba da tafiya, Hjy tana kula da ƴen marayin ƴaƴan ta, don ta samu rufun asirin ta sai ta fara sai da alala da manja don kawai ta smu ɗan abun da zasu dinga kau da matsalolin yau da kullum
tj da aliyu suka taso tare tun suna ƙanana suke kiran junan su da ɗan uwa, da wuya kaji sun ambaci sunayen su, shaƙuwa ce aosai tsakanin su, baka taɓa jin tsakanin su ko hjy haka take ganin su ta bar su
aliyu ya taso mara son magana, in kaga hirar sa da dariya to ka tabbatar da hjyr sa ce ko kuma ɗan uwan sa, wannan dalilin ne yasa baya shiga mutane sosai babu yadda hjy batai ba na ya dinga zuwa yana gaida iya amma da kyar yake zuwa tabbas tasan iyar ce take zagin amma kuma ya zata yi jikan ta ne ta zama dolen sa
ganin hakan ne yasa idan hjy zatayi alala aliyu ne me kai markaɗe gidan iya, kuma kullum yaje da zagin da zai sha wajen iyar kafin tayi masa markaɗe
takan zage masa uwa tas, wai ta yada shi ta tafi yawon karuwanci, yakanyi mamaki wacece wannan uwar tasa kuma meye ya haɗa ta da iyar haka da har ta tsane ta kuma tsanar ta shafe haka
kamar kullum yau ma hjy ta aiki aliyu ya kai markaɗe yana fitowa daga gidan sai yaci karo da wani ɗan maƙocinsu bala da ƙanin sa
"alin hjy ina zaka" bala ya tambaya
"zan shiga gidan iya in kai markaɗe ne"
"iya bala'i zaka ce, kai baka gajiya kullum ka shiga gidan matar na sai ta zage ka, kuma ka kasa faɗawa hjy ta dai na aiken ka"
murmushi aliyun yayi be ce komai ba
"kawo ina habu ƙanina ya kai yau ka huta da zagi" kamar aliyu ya ƙi amma sai ya ba habun ganin cewar ai markaɗe ne kawai
"zo muje ka raka ni wani wuri" inji bala ya faɗa yana jan hannun aliyu
"zan taya hjy aikin alalan ta"
"ai ba daɗewa zamuyi ba zan koya wa wani yaro hankali ne" ya faɗa yana jan hannu aliyu wanda shi kuma ya bishi zingwi zingwi ba tare da ya sake yi masa musu ba
sun ɗan yi tafiya sai ya ga balan ya tsaya ya laɓe a ƙofar wani gida shima sai ya biye masa, wani yaro ne ya fito daga wani gida dake ƙasan layin, ko da yaron ya matso kusa da su sai bala ya ɗauko wani dutse ya jefi yaron da shi sannan ya ruga a guje, shi kuma aliyu sai ya tsaya yana kallon ikon Allah
ko da ya ga jini a goshi yaron ga kuma mutane sun fara taruwa sai shima ya ruga a gujen, yana jin wani yana cewa alin hjy ne ya jefe shi gashi can yana gudu
shidai tun daya samu ya tsere kawai sai yayi filin ƙwallo don yasan dole za a je gidan su neman shi, to idan suka je basu ganshi ba ai dole su haƙura ya faɗa, sai bayan la'asar sannan ya kama hanyar gida yasan yanzu ƙurar ta lafa ya faɗa aranshi yasan yau sai hjy tayi masa faɗan zuwa yawo ya faɗa yana kama hanya
yana shawo kwanar gidan nasu yaga ƙofar gidan cike daƙam da mata da yara sai zage zage suke yi, ko da ya lura sosai sai yaga ƴaƴan hjy ne sai mutan gidan iya da ita kanta iyar to me ya faru ya faɗa
ko da idon su ya kai kanshi da gudu aka je aka kamo shi kamar wanda yayi sata kowa yana masa tofin Allah tsine, babbar ƴar hjy wato hauwa itace taiyi masa mari a dukkan kumatun sa guda huɗu ƙwarara
nan suka hau dukan sa wai duk abinda uwarsu tayi masa sakayyar da zai mata kenan, gaba ki ɗaya duk cikon taron wurin nan daga me dukan shi sai me zagin sa, shi ko kaɗan be ma san abin da yayi ba
zagin sa da suka dingayi na tsintacciyar mage itace ta fi ƙona masa rai, duk cikin gurin nan babu me ƙaunar sa, to me yayi musu tabbas tun taso war sa yasan shi ba irin su don shi kana ganin sa kaga balaraben asali fari ne kyakkyawan gaske ga gashi irin na larabawa, ga baƙi ga kyau da sheƙi don ma baya samun kulawar da ta dace shi
tun tasowar sa yake fuskantar kyara da tsangwama su kansu ƴaƴan hjyr a gaban idon ta ne suke nuna suna sonsa amma da babu ita a wuri shike nan shi tashi ta kaɗe, ya rasa me yayi musu me mahaifiyar shi tayi musu me yasa suka tsane shi haka, shi bama sanin mahaifiyar tashin yayi ba amma kullum sai ya sha zagi da tsinuwa sabida ita wai me mahaifiyar shi tayi ne haka da muni da har abin yanzu ya dawo kansa
duk wannan dukan da suke yi masa da zagin nan idon ƙamas yake ba hawaye, sai dai zuciyar sa da ke bugawa tana wani karta masa kamar ana soka masa allura acikin ta, ƙirjin sa kawai ya kama tare da tsugunnawa ƙasa ganin halin da yake ciki be sa sun fasa zagin sa ba sai ci gaba da yi masa gorin hjyr su tayi masa shi kuma da yake tsintacciyar mage ne bata mage sai ya saka mata da wannan
Iya ce ta ɗauka kun manta yadda uwar sa ta kashe min ɗan ran da ya dawo, haka ne iya uwar sa ta lashe kurwar sani don kince ba ki yadda da auren su ba, nan suka fara caccakar mahaifiyata tare da bin ta da munanan addua
kun san ai munmunar ƙaddara ce take bibiyar sa tun haihuwar sa me zai hana duk wanda yake tare da ta shafe shi, inji iya
to wallahi ƙaryar ka mummunar ƙaddara ka baza ta faɗa akan uwar mu shekara goma sha uku hjyr mu tana ta ɗawainiya da kai uwar da ta haifeka ma tun da ta yar da kai ta gudu bata kuma waiwayar ka ba saboda ƙaddarar ka to wallahi tun wuri ka kama gabanka kasan inda dare yi ma don babu abinda ya haɗa mu da kai taimako ne sai ka jefa mana uwa cikin bala'i
to wai wacece mahaifiyata me ya haɗa ta iya da har ta kashe mata ɗa ina kuma hjy tayi me yasame ta ya faɗa a ransa gaskiya doƙe ya bar gidan nan ya bar mutanen tun da sun fito ƙiri ƙiri sun nuna masa basa ƙaunar sa kuma yana gudun kar munmunar ƙaddarar sa ta shafi hjyrsa macen da tafi kowa son sa da tausaya masa hjy ina kika shige nedon yasan inda tana nan basu isa suyi masa wannan cin kashin ba
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
*wannan page ɗin naku readers ɗin DANGIN SA na sadaukar da shi kacokam ɗinsa gare ku* 😁😁😁😁
page :33🌹
Gajiya sukayi da zazzaga masa bala'in sannan suka kama hanya ko ina zasu oh, na dai ji hauwa tana cewa ku zo muje muga uwar tamu mu ƙyale wannan tsintacciyar magen,
Kafin kace me duk an watse an barni a durƙushe riƙe da ƙirjina wanda zuciyata take bugawa kamar zata tsaga ƙashin ribs ɗina ta fito
tashi nayi don dole ne inje inji me ya samu hjyr, yana shiga gidan a tsakar gida ya tarar da tj yana ta sharɓar kukan sada sauri ya ƙaras kusa da ɗan uwan nasa
"ɗan uwa me ya same ka" ya tambaya yana dafa shi, jin muryar aliyu yasa tj ɗago da kansa tare da kallon aliyun
"ɗan uwa me su aunty hauwa suka yi maka" ya tambaye ni
"babu abinda suka yi min, ina hjyr take"
"ƴen sanda sunzo sun tafi da ita wai ka fasa wa wani kai"
aliyu be sain lkcn da yayi baya yai zaman daɓaro ba, oho sai yanzu ya fahimci dalilin daya sa su aunty hauwa yi masa haka, wai an kama hjy, to ai shi yayi ba
ya kalli tj wanda har yanzu yake shash sheƙar kukan sa
"wane police station aka kai ta"
"nima ban sani ba, amma tace idan ka dawo ka jira ta kar ka fita" gyaɗa kai kawai nayi
wato koda da tana cikin wannan halin amma ta damu da shi wayyo hjy wallahi bani nayi ba, kuka nake son yi sosai amma na kasa don idona a soye yake, sai zuciyata da ke ta bugawa da ƙarfi da kuma sauri kamar nayi gudu
haka muka zauna zaman jiran gawon shanu, hjy sai da akayi magariba sannan sai gata da ƴaƴan ta, tana ganina ta yo kaina tare da tambayar "kaci abinci kuwa" gyaɗa mata kai kawai nayi duk da dai banci komai ba amma ko kaɗan bana ji yunwa
"ya naji jikin ka zafi baka da lfy ne" ta kuma tambaya
"wallahi hjy bani na jefe shi bala ne"
"haba alina ko ba wanda zai shede ka ni zan shaide ka nasan ba kai kayi, ka kwantar da hankalin ka ba abinda akai min asibiti kawai na kai yaron" ta faɗa tana ƙara jawo ni jikin ta, wanda ni kƴma na lefe nayi luf da ni, gaskiya ina ƙaunar matar nan har cikin rai na
ƙiri ƙiri ƴaƴan ta suka nuna ya kamata tayi min faɗa nan ta hau su da faɗan babu ruwan su, ba yadda suka iya haka suka haƙura sai dai saƙon harara da suka dinga aiko min da shi
Sai da na kwanta jinya har na kwana uku kasancewar ƙirjin nawa ya saukar min da zazzaɓi me zafi, tare da ciwon kai hjy ta ɗauka zazzaɓin ne kawai don haka sai tayi ta dura min maganin malaria
aikuwa cikin ikon Allah na ɗan samu sauƙi don ita ma zuciyar ta ɗan rage dukan da take min, ko da naga na ɗan warwaresai na shirya barin gidan, don gwanda in bar gidan nan kar mummunar ƙaddara ta ta shafi hjy da tj mutanen da suke ƙaunata
da safe bayan na gama komai nayi sallama da hjy akan na tafi in gaida iya, hjy tai murna har tana samin albarka, ina kallon hjy ina jin zuciya ba daɗi idan na tune cewar baza ta kuma ganina ba
naira hamsin ce kawai a aljihuna, tun da na fita nake gararan ba na in shiga nan in fita nan har dare yayi min sannan na samu mkrt almajirai na lafe a cikin su nai bacci na
duk da ba wani baccin kirki nayi ba ni da saba bacci a lafiyayyar katifa amma wai yau nine kwance a dandamaryar ƙasa, hana kaina kuka nayi gwanda inyi wannan rayuwar da inyi rayuwar jin daɗi bayan hjy kullum zata dinga fuskantar ƙalu bale saboda ƙaddara ta haka har bacci ya kwashe ni ina tunanina
kashegari da sassafe na tashi na kama gabana tun kafin su fahinci cewar ni ba a cikin su nake ba, haka na dinga yawo kwararo kwararo inna gaji in samu inuwa in lafe inna huta in ci gaba da tafiya inna ji yunwa in tsaya inyi bara har sai na ƙoshi sannan in ci gaba
haka na ci gaba da rayuwa ta har na kwashe wata shida ni ba almajiri ba ni ba ɗa ba in kin ganni a lkcn baza kice nine alin hjy ba don na canza sosai, acikin yawace yawacen nawa ne na haɗu da wani almajiri me suna shapiu, ɗan katsina ne bbn shi ya kawo shi almajiranci amma da malam ya ishe shi da duka sai shima ya tsere, shine muke gararan bar tare
shapiu ya girme ni sosai don haka ya fini wayo nine me barar shi kuma yana zaune sai dai in samo in kawo mana sannan muci tare
rannan yawon mu ya kaimu ƴen kaba kasuwar kayan miya, ana ta loda kayan miya cikin motoci suna fita da shi zuwa garuruwa, abin yabi sha'awa nan nan nima na shiga loda kaya cikin mota, ko da muka gama sai aka bani naira 100
wannan kuɗin da aka bani ba ƙaramin daɗin su naji ba, sai na fara loda kaya a duk motar da tazo domin lodi ina samun kuɗi shi kuma shapiu ba abinda yake daga yaje wacce inuwar ya zauna sai ya je ya nemi wannan majalisar ya zauna ayi hira da shi nine me neman kuɗin
in kaga ya nemi ni to yaki yunwa haka zaizo yana min ƴar murya ni kuma bana iya hana shi ganin kamar shi kaɗai ne ya sanni don haka ina yi masa kallon ɗan uwana, idan kuwa na bashi bana kuma ganin shi sai ya ƙara jin wata yunwar
watan mu uku a kasuwar ƴen kaba shapiu ya kawo shawarar mu tafi lagos wai anfi samun kuɗi a can banyi wata wata ba muka kama hanyar lagos a cikin wata motar kayan miya, tafiyar da ta canza min rayuwata tafiyar da ta maidani abinda nake yanzu.
ayi hakuri da wannan yau na tashi ɗan jariri na walid ba lfy don Allah ku sa a addua 🙏🏻
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
*ga gode sosai da adduar ku gare ɗana ya ku masoyan dangin sa Allah ya barmu tare ya samu sauki Allah ya saka*
Page:34🌹
Hjy ce zaune a fali ta zuba uban tagumi tana tunanin rayuwa, yanzu aliyu a doshi shekara da ɓata ba shi babu lbrn sa, ta tuna lkcn da ya ɓata da taga har dare be dawo ba kuma tasan be saba yawo ta shiga neman sa
Babu inda basu ba shi ba ita da tj, inda tj ɗin ba abinda yake yi in banda kukan ɗan uwansa itama hjyr daurewa kawai take yi
daga ƙarshe suka biya gidan iyacigiyar sa duk da hjyr tasan bazai taɓa zama a gidan ba amma dai ance in kana neman raƙumin ka ko cikin tandu sai ka duba
nan iya ta kwashe lbrn abinda ƴƴan hjyr sukayi wa aliyun randa aka kulle ta police station tas ta faɗa wa hjyr, wai hjyr tana riƙe da shege bayan ƴaƴan da ta haifa basa son sa
Hjy rasa bakin magana tayi haka ta dawo gida jikin ta a sanyaye, a daren har kuka tayi tai sallah sosai ta roƙo Allah ya kare mata shi duk inda yake, kashegari ta kira ƴaƴan nata bayan sun zo ta wankesu tas da soso da sabulu sannan tai musu albishirin aliyun ya gudu don haka sai kawaccen su hankalin ta ya kwanta
haƙuri suka fara bawa hjyr nasiha tai musu sannan tace su kuma san da cewar duk wani abinda ya samu yaronnan mara kyau su san da cewar da kamashon su a ciki
kowacce sai jikinta yai sanyi bayan hjyr ta gama yi musu kuma ta patattake su, haka ta zauna ta dinga bin aliyu da addua kullum bata fasawa kuma bata mantawa,
****************
mun sauka lfy a garin *yanki* inji mazauna can, directly kasuwar idi yaraba muka wuce acan muka sauka na fara harkar dako, to rayuwar a lagos ba kamar kano bane, komai da sauƙi, don haka ni da shapiu kowa tasa ta fish she shi mukeyi
Wasu ƴen area boys yake bi babu yadda banyi da shi akan mu nemi abinda ya kawo mu wato bugun abuja amma ƙiri ƙiri sai ya nuna min shi ba sune a gaban sa ba babu yadda na iya shi haka na ƙyale shi, tun yana ɗan zuwa harbya koma ma sai in shafe qata bangan shi ba, a haka tarayyar mu da shapiu ta watse
Aikin da nakeyi na ɗaukar kaya sai kai kaya wurare ba ƙaramin samun kuɗi nake yiba kuma bayan abinci ba abinda nake siya tarawa kawai nakeyi don inyi wa hjyta siyayya
yau kusan watana bakwai a lagos kuma ba laifi na waye sosai na san gari kuma na san harka kama kuɗi nake yi dai dai aikina, akwai wani wai shi umar tare muke aikin mu da shi shima ɗan kano ne amma ɗan kurna da iyalen sa akano
ina son zama da umar sosai ko ba komai idan yana hirar iyalin sa sai inji kamar ina gida, rannan katsaham sai gashi wai gida zashi yayi kewar iyalinsa, kawai nima sai naji hjy ta faɗo min rai, gaskiya ban kyauta yau kusan shekara ɗaya kenan da wani abin da guduwata amma ban taɓa leƙa ta ba kuma nasan tabbas hankalinta ba a kwance yake ba
duk dani ma kullum suna raina ita da tj wanda wani lkcn tsabar tunanin su take sawa inji zuciyata na buga min tare da min wani azababben ciwo gaskiya dole ne inje inga hjyta na faɗa araina
Umar na samu na faɗa masa nima ina da ra'ayin zuwa kanon yai murna tare da min nasihar in dinga kula da iyayena barin idan basu da hali sosai
kuɗin da hannuna na haɗa muka tafi kasuwa nida umar, siyayya sosai mukayi, buhun taliyar nan irin ta damage na campany guda biyu, sai jan wake na san hjy ta na son sa, akwai wata madara da ake siyar wa daɗi gare ta, da bourntiva ɗinta a haɗe kawai sugar zaka sa sai ka haɗa shayi,botikin penti biyu na siyo sannan na samu gwangwani manya manya na madara na juye su a ciki, su hjy su sha shayi mu more,
sai kayan gwanjo masu kyau da sai wa tj, ita kuma hjy na sai masa lesis masu kyau guda uku marasa nauyi
muka kamo hanyar kano, a hanya ne na dinga ba umar lbrin abinda na sani game da rayuwata da dalilin guduwata, ya tausaya min sosai daga nan bai kuma cewa komai ba
mun tsaya a hanya muka sai doya da manja, tj kawai na hango don masoyin doya ne, a kura muka tsaya muka sai shinkafa ƴar hausa me kyau, ta dafawa da ta tuwo sai gero, sannan muka ƙaraso cikin garin kano
munyi siyayya kamar ba gobe barin ma niduk abinda na gani sai na siya, don haka muna sauka kano muka ɗau akori kura sai kurna gidan umar muka sauka don nace masa bazan je gidan hjy ba sai dai in masa kwatance
kasancewar da safe muka sauka sai da muka huta sannan da yamma muka kama hanyar gidan hjy don so nakeyi a ranar in koma lagos ɗin
taxi muka ɗauka aka loda mana kayan nawa har layin da za a shiga gidan hjy sannan muka sauka muka samu almajirai suka ɗau kayan, nai masa kwatancen gidan sosai sannan nabi bayan shi don in laɓe don ina son ganin hjyta sosai
dubu biyar na bashi tare da wasiƙar kwantar mata da hankali tare da nuna mata inanan lfy wacce na rubutata tun a lagos, sai hotunana guda biya, a ƙofar gidan ya tsaya ya doka sallama
hjyr ce da kanta ta fito sanye da hijabin ta tana nan yadda na barta Allah sarki hjyta na faɗa araina, sun daɗe suna magana tare da hjyr inda daga baya ya miƙa mata envelope ɗin da wasiƙar tawa da pics ɗin wa suke ciki
Hjy tana karantawa tana hawaye ni kaina sai ta bani tausayii amma dole ne inyi haka in tashi don in gina kaina don kuwa bani da gata bani da me yi min don haka dole in san in da dare yayi min, sukayi sallama bayan ya sa an kwashe mata kayan an shigar mata da su ciki
koda muka haɗu sai dinga min faɗan in koma hjy tayi kewa ta sosai tooo kawai nace masa mukayi sallama sanna na kama hanyar tashar sabon gari don komawa neman kuɗina
na koma lagos na ci gaba da neman na kaina, duk wani burina yanzu akan hjy yake da tj, duk wani abu idan na samu sai in tura kano umar sai ya tura ƙaninsa ya kai musu, bama waya amma muna musayar wasiƙu musamman ma tj, duk abinda yake so in dai ya faɗa min sai na siya na aika masa ita kuma hjy babu komai a wasiƙar ta sai nasiha da adduar kullum in zama me gaskiya tare da neman halal kawai
***************
hjy tana zaune tana girki taliya take dafa wa wacce taji kayan miya tare da nama, zuƙu zuƙu tana tunanin rayuwa yanzu komai sun fi ƙarfin sa in dai ta ɓangaren sutura ne da abinci to sai dai ta bawa wani, sallamar da aka doka ce ta katse mata tunanin ta, tashi tayi ta ɗan leƙa sai ta ci karo da nasiru ƙanin umar, ga kayan abincin nan buhu buhu a kusa da shi
bayan sun gaisa ya bata kayan ya kama hanyar sa har kuɗi ta bashi amma ƙiri ƙiri ya ƙi karɓa, haka ta sa aka shigo mata da kayan nan ko waɗan da ya aiko musu da shi wancen watan bai ƙare ba ko rabi basu ci ba amma wai yau gashi yanzu ya kuma aiko musu da wani kamar bai san ciwon kuɗin sa ba
shawara ce ta faɗo mata sai ta raba kayan biyu tasa yara suka ɗaukar mata rabi sai gidan iyababu abinda ba ta ɗibarwa iyar ba harda kuɗi dubu uku
iya ganin ana ta shigo da kaya ɗakin ta yasa ta sakin bakin tana mamakin waye, ganin hjy ya sata ƙara mamaki har da ƴar fara'ar ta rabon da hjy taga fara'ar iya har ta manta
bayan sun gaisa hjy tai wa iyar bayanin irin hidimar da aliyun yake musu sannan tace mata gashinan na raba kayan biyu na kawo miki rabi kema kici arziƙin jikan ki duk da dai kince ba jininki jininki bane amma kowa ya san jinin ki, don haka gashi kema kici arziƙin jikan ki
hjy ta ɗauka iyar zatai bala'in ta da ta saba amma ga mamakin ta sai taji iyar tana bin aliyun da adduar Allah ya kare shi duk inda yake , hjyr sai ta ɓoye mamakin ta tare da ansawa iyar da amin sukayi sallama a mutunce hjyr ta kama hanyar gida cike da mamakin canzawar da iyar tayi
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺U☺☺☺☺☺☺☺
page:36🌹
Haka na ci gaba da neman kuɗi tare da turawa hjy duk wani kuɗin daya zo hannuna, ban damu ba idan na zauna banni da ko sisi in dai na tabbatar da cewar gidan hjy akwai abinci to bazan damu ba
Shekara ta biyu a idi yaraba sannan Allah ya haɗa ni da wani bayarabe wai shi balogun, yakan zo kasuwar mu, a haka shaƙuwa ta shiga tsakanin mu, ko da muka shaku sosai sai ya yi min tayin wai in zo in fara aiki da shi a deport, ban wani dogon tunanin ba na bishi a lkcn umar yana kano don haka babu wanda inda na koma
Aiki a deport yana wuya amma kuma samun kuɗin da ake yi a can bama za a haɗa da idi yaraba ba, don haka kan a ce wannan na tara kuɗi ba kaɗan ba
Watana uku a deport na tara kuɗin da ni kaina ban san cewar zan same su ba, kuma har yanzu ban kuma neman umar ba, ranar wata talata ana saura sati biyu a fara azimi na shirya zuwa ganin umar don in aikawa da hjy kayan azimi, don in shaa Allah azimin bana hjy sai ta shana
bayan mun gama aikin mu na shirya sai idi yaraba, umar yai murna sosai da ganina tare da faɗa min yadda hankalin hjy ya tashi da taji lbrin ya bar idi yaraban, nan ya faɗawa umar sana'ar da ya koma yi a deport, ɗin
Umar ya jinjina wa aliyun yaro ne ɗan ƙarami amma Allah ya bashi zuciyar nema, komai wahala yanzu me ya kai aikin deport wahala, akwai samun kuɗi amma akwai wahala kuma, da kaya sun zo daga waje ko cikin dare ne dole ku fito ku kwashe tare da loda su a cikin motacin da zasu kai garuruwa, haka in kaya suka tashi a fitar da su daga nan, nan masai sun kwashe sun loda
sai ayi kusan sati a kan jirgi ɗaya ana kwashe odar daya yo, ya danganta da irin girman jirgin amma wai ita wannan sana'ar ɗan ƙaramin yaron nan yake yi gaskiya Allah ya bashi zuciya
Kasuwa ya rakani ni kaina bansan irin ɓarnar kuɗin da nayiwa hjyta ba amma gaskiya kaya na siya mata kamar za a buɗe wani ƙaramin kanti, shi kanshi umar ɗin sai dana yi masa siyayyan kayan abinci sannan na haɗa don turawa kano
amma sai umar yace in barshi kawai zai kai mana dama shima yana son idan ya samu kuɗi yai siyayyar kayan abinci zai je gida yayi azimi acan amma yanzu tunda na taimake shi gwanda kawai ya gudu
naji daɗi sosai ganin umar zaije kano da kanshi, na bashi kuɗi wanda zai ƙrasawa hjy siyayyar ta acan, irin su ƙwai, dankalin turawa gero, da dai sauran abinda baza siya anan ba
mukai sallamr da niyyar bayan sallah idan ya dawo zan shigo, shi kuma umar ya samu mota guda ya loda kayan na sai kano, direct gidan hjy ya fara zuwa ya sauke mata kayan da ya zo mata su, hjy kasa shiru tayi don duk ta tsorata da irin iyayen kayan da umar ya jibge mata tare da bata kuɗi har dubu ɗari
"umar ni kuwa yaron nan yanzu sana'ar me yake yi"ta tambaya, umar yai mata bayani irin aikin da aliyun yake yi da kuma wahalar da ke tattare da aikin
dukda dai hjy ta tausaya wa aliyun amma hakan bai hana ta tambayar umar ɗin ba
"yanzu kana tunani zai iya samun wannan dukiyar"
"kai hjy abinda yafi haka a sai ya samu"
ya bata ansa sai da umar ya kwantar w da hjy hankali akan aliyu sannan shima ya kama hanyar gidan shi cike da siyayyar da aliyun yayi masa wanda zai ishe shi da iyalen sa har a gama azimi
hjy kamar yadda ta saba wannan karon si ta raba shi kashi uku don gaskiya kayan abincin ka kaɗan bane shi kanshi buhun shinkafa sai da ya aiko mata da buhu takwas banda kwalayen taliya, buhu biyu ta aikawa da iya tare da ragowar kayan abincin da aliyu ya aiko mata
sannan ta aika wa da ƴaƴanta kashi ɗayar ita kuma ta ajiye kashi ɗaya, da daddare iya da kanta ta shigo don yin godiya inda hjyr tace mata ai nima arziƙinki nake ci, ta faɗa tun da dai duk abuna jikan ki, iya sai washe baki tare da faɗin haka ne
iya takanas ta gayyato ƴaƴanta wai suzo su ga abinda jikanta ya aiko mata, kowa ya tamayi wane jikan idan iyar tace aliyu sai kaji anacewa iya dama kina da jika aliyu ne, sai kaga iya tana zazzare ido ba damar ansawa
ita kanta hjyr sai da ta gorantawa ƴaƴan ta da suka zo mata godiyar kayan da ta aika musu, tace to me mummunar ƙaddara ce ya aiko min sai jikin kowacce yayi sanyi, sai yanzu suke danasanin abinda sukai yi wa bawan Allahn nan da sun san haka Allah zai buɗa masa cikin ɗan kanƙanin, duk sai kunya ta kama su lallai basu kyauta ba
**************
haka aliyu ya cigaba da neman sa , ba dare ba rana kusan duk dwport ɗinnan an san shi saboda kwazon sa da kuma aiki tsakani da Allah don haka kafin kace me, har ya taka matsayin da bai taɓa tunani zuwa nan kusa ba
***************
*bayan shekara biyar*
yanzu aliyu ya zama babba kuma me faɗa aji a deport ɗinnan ya tara kuɗi ba kaɗan duk wannan abinda ya keyi bai sa shi mantawa da hjyr sa ba yanzu shi ba yaro bane, yara gare shi kusan duk wani jirgi da zai shigo nigeria aliyu ya san da zuwan sa sannan yaran sa ne masƴ aikin sauke kaya, duk da ƙanƙantar shekarun sa hakan baisa waɗanda ke ƙasan sun raina shi ba, don duk girman ba zai ɗauki raini daga gare ka don kawai ka girme shi, sannan shi mutum ne da baya son son jiki aiki kawai, ko kayi ko kuma ka nemi wani ubangidan hakan ne yasa yaran sa sukai fice, aikin sa yake da biyan buƙata ba tare da ɓata lkc ba
wannan dalilin ne ya sa aliyun yai fice kuma ya zaman yana ɗaya daga cikin abokanan harkar tasu ya kasance shine babba, duk da ƙanƙantar shekarun sa
akwai wani alh tahir bala ɗan siyasa ne kuma ya kasance yana da jiragen ruwan kuma companyn aliyu ne suke kwashe masa kaya indai jiragen sa sun ƙaraso
ko da lkcn zaɓe ya zo sai ya nemi aliyun da ya bashi aron kuɗi domin yin canfen amma sai aliyun yai using wannan oppurtunity ɗin sai yace wa alh tahir bala ɗin ya sai da masa da jirgin sa guda ɗaya,
alh tahir ɗin yai ta faɗa tare da banbami sannan yai gaba, ko da yaje ta ƙure masa haka ya dawo dolen sa ya siyarwa da aliyun jurginsa guda ɗaya don kawaibya rabar da kuɗin ga mutane don ya samu kujera
wannan jirgin da aliyu shine yai asalin silar arziƙin aliyun inda da wannan jirgin ya mallaki jirage masu yawa da girman gaske, don kuwa ahalin yanzu ba inda jiragen sa basa zuwa ba don ɗauko kaya ko kuma kai kaya wannan dalilin ne yasa shi fara fantamawa, ba ma shi kaɗai ba hatta hjy yanzu sai dai tayi kyauta ba ita kaɗai dai dai da ƴaƴanta yanzu sun zama wasu har iya itama ba a barta abaya ba, har bawa mutane labari take yi wai jikan ta ne wanda hjy ta riƙe saboda ɗan saɓanin da suka samu da mahaifiyarsadon Allah kunji faa🤔🤔
aliyu ya kai hjy hajj da umma ba sau ɗaya ba inda yanzu umar ya bar lagos ya koma kano yana kula da dukiyar aliyu da ke kano don yanzu sun zama ƴen uwa duk abinda ya faru a gidan umar hjy tana zuwa har ƴa gare umar me sunan hjy saboda tsabar jin daɗin zaman tare, tj ma yanzu sai fantamar sa yake yi ya zama ɗan gaye karatun sa kawai yake yi babu kama hannun yaro
aliyu ne ya siyawa hjy gida dan karere a unguwar sharada sannan ya sa suka tashi suak tare acan inda aka sha shagali babu kama hannun yaro
sai da hjy ta koma sharaɗa sannan aliyu ya zo ta ganshi da farko bata gane ba amma kuma daga baya sai ta gano shi don yanzu ya zama aliyu ɗan balarabiya fari tas da shi ga kyau ga cikar zati
an sha ƴen koke z kafin daga bisani aka fara hirar yaushe gamo aliyu ya bata lbrn irin gwagwarmayar daya sha da irin wahalar daya sha amma da yake ɗan halak ne sam bai ambato mata irin cin fuskar da ƴaƴanta sukai masa ba hjy har kunyar sa take ji amma ta kasa cewa komai don yanzu babu abinda bai yi ƴaƴanta ba babu wacce be kai hajji ba
hjy ce ta tashi taje ta ɗauko masa wata ƴar jaka ta bashi buɗewa yayi ya ga wasu hotuna ne, nan hajiya ta zayyano masa tarihin rayuwar sa da alaƙar da ta haɗa da iya da yadda mahaifiyar sa ta tafi ranar da
ji yayi duniyar gabaki ɗayan ta tayi masa zafi ya rasa abinda yake masa daɗi ya ji ya tsani iyar da duk wani wanda ya shefeta har da ita mahaifiyar tashin da ta tafi ta barshi acikin tsumma bayan tasan wace irin rayuwa zaiyi ba
zuciyar shi ce tavfara wannan bugawar da take yi na rashin saiti ba abinda take masa sai, ba abinda yake ji sai jiri da ganin dishi dishi yanajin hjy tana bashi bakin wai ya haƙura ya rungumi *dangin sa* ba bu abinda yake yi daya wuce gyaɗa kai kamar yana fahimta
tashi yayi yace hjy bari inje sai anjima, to kawai tace yai hanyar waje tj ne ya bishi hjy ta kira shi tace mai ya ƙyale aliyun har sai ya sauko, mota kawai ya shiga ya sa driver ɗinshi ya kaishi hotel ɗin daya sauka don yana buƙatar zama shi kaɗai ko ya samu yayi tunani
kwanan shi uku a rufe a ɗakin daya sauka babu abinda yakeyi banda kuka me yayi wa mahaifiyar shi da zata wurgar da ɗan data haifa ta gudu in iya ta ƙishi ita sai ta kishi kuma tun randa ta tafi bata kuma waiwayar sa ba, ya za ayi ya iya yafewa mutanen nan daga mahaifiyar tasa har iyar bayan a dalilin su ne yasa shi yin ƙuruciyar sa cikin,ƙunci, tsangwana da gori shi bai taɓa more wani abuwai kuruciya ba a wajen hjy da tj ne kawai yake samun sassauci babu ni babu su, ya faɗa da ƙarfi
bugawar da zuciyar sa ke yi ga wani azababben ciwo da takeyi ne ya fara wuce ka'ida don yanzu numfashin sa ma da ƙyar ya ke iya fitar da shi ga zazzabi ya rufe shi ruf da ƙyar ya lalubi wayar sa ya kira pa ɗinsa akan ya zo ya kai shi asibiti yai masa kwatancen hotel ɗin da yake
yana gama wa yaji kamar an caka masa wani abu a zuciyar sa tuni ya fara neman nunfashinsa wanda yake ji kamar ana jamasa numfashin kafin yace zai ɗauki intercom ɗin dakin ya kira reception ya sume
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
*oppps hello danginsa fans nayi mistake last page 35 ne na manta nasa 36, so da fatan ba,za ku nemi 35 ba*
*masoya dangin sa wannan shafin naku ne kacokam ɗin sa na gode da soyayya ku*
*mun yi baƙi a grp ɗin danginsa duk ina yi muku barka da zuwa da fatan duk zamu ƙaru da juna, don Allah a dinga haƙuri da juna Allah yasa mu dace*
Farkawa nayi na ganni a asibiti hannuna da ƙarin ruwa sai ƙirji na da yake ta faman min azaba, duka zuciyata take ta faman yi kamar zata fasa ƙirjina
riƙe ƙirjin nawa nayi tare da anbaton sunan Allah, pA ɗina ne ya matso kusa dani "yallaɓai ka tashi bari in kira dr. ɗin" ya faɗa ban kula shi ba ya fita
Can zuwa anjima sai gasu shi da dr. ɗin
"sannu ya jikin, ina ne yake maka ciwo" inji likitan
Ban iya magana ba iya kacin ƙirji na dana nuna masa
"sanna" ya faɗa ataƙaice sannan ya ci gaba da rubutu a file ɗin da ke hannun sa
"aliyu kana fama da ciwon zuciya ne wanda ya kai stage ɗin da dole sai anyi mak aiki a zuciyar taka, don haka ya kamata ka fara shirye shirye zuwa aikin da gaggawa"
Ban iya magana ba sai pA ɗina ne ya masa magana inda likitan ya bada shawarar muje china, babu musu pA ɗina ya yadda ya fara yi mana shirye shiryen tafiya
PA ɗina ya so in faɗa wa dangi na akan operation ɗin da zai min tun wannan ana magana ne tsakani life and death amma ƙiri ƙiri na hana shi ba yadda ya iya haka ya haɗa mana visa muka kama hanyar china
mun sauka lfy directly muka kama hanyar asibitin kasancewar an san da zuwan mu yasa bamu wani sha wahala ba, sai kawai aka karɓe ni aka fara bani treatment kafin operation ɗin
Alhamdulillah anyi operation lfy kuma ma shaa Allah ina samun sauƙi ba laifi, ko da jikin nawa ya ɗan fara warwarewa sai na turo pA ɗin nawa ya dawo nigeria don ya ci gaba da kular min da harkokina ni kuma ina jinya ta
******************
hjy ta tare a sabon gidan ta cike da sa a, a da tana jakara takan taimakawa iya idan aliyu ya aiko amma tunda ta tashi shi kenan iya rayuwa ta juya mata, ya kasance wata ran ma abincin da zata ci sai ya nemi gagararta,
Nadama ce sosai ta saukar wa da iya tai nadamar abinda tayi wa salma mmn aliyu tai nadamara abinda tayi wa shi kan shi aliyun gashi yanzu ba ta san inda zata ganshi ba balle ta nemi shawarar sa, haka ta koma abar tausayi don duk ragowar ƴaƴan natan babu me tausaya mata in ma zata samu ta basu su so zasu yi haka rayuwa ta juya wa iya, ga hjy bata kusa balle ta faɗa mata halin da take ciki
nayi jinyata na watstsake dr. ɗina dr juan ya kafa min sharuɗa akan in kula da zuciyata sosai in dena sa abinda zai dame don in samu in zauna ƙalau wannan dalilin ne yasani haɗa dangina da mahaifiyata na sa su kwandon shara na fitar da su daga cikin lissafina saboda duk lkcn dana tuna su sai naji zuciyata tana min ciwo, wannan dalilin ne yasa ni mantawa da lamarin su, wannan shine dalilin daya sa na shafe zancen dangina a zuciyata don ta zauna lfy
*back to labarin*
rungume mijina nayi ina jin tsantssar tausayinsa a raina, lallai ka ga rayuwa sosai
"amma abu haidar baka ganin yafe musun shine dalilin da zai sa zuciyar ka ta zauna lfy" Ƙara jawoni jikin sa tare da kissing ɗina
"habibti bana son ki shiga wannan maganar na riga na kulle zuciyata pls kar ki samin wani sabon ciwon" ya faɗa
"to ina mahaifiyar ka take, baka ganin ya kamata ka neme ta"
"in neme ta ince mata me, ni da ta wurgar da ni tun ina tsumma kina ganin akwai abinda zata min yanzu"
"amma abu haidar baka ganin ...................."
"shhhhhhh habibti bamu haɗu anan ba saboda musu ban baki labari na saboda kiyi min musu, na faɗa miki ne kawai don ki guje wa mutanen na so pls kar ki min haka kar ki ƙara kawo min zancen dangina bani da ban taɓa samun su haka navtashi ni kaɗai kuma ina son rayuwata daga ni sai ƴaƴa na don haka inkina son zaman lfy da ni karki ƙara kawo min zancen su"
"amma baka ganin......." bai ma bari na gama zancen nawa bawa ba ya tashi ya miƙe tare da ɗauko doguwar rigar sa
" naga alamar bakya san in kwana aɗakin nan don haka sai da safe idan kinyi tunanin abinda na faɗa miki da safe ma haɗu" ya fita tare da ja min ƙofa
zama na tashi nayi gaskiya dole ne in gyara tsakanin mijina da *dangin sa* abinda ya fi bani mamaki ma shine wai mahaifiyarsa akwai chances na cewa ƙila tana a raye, amma tunda yake be taɓa tunanin neman ta ba
wace irin zuciya gare mijin dana aura innalillahi wa inna ilaihi rajiun kawai nake faɗa gaskiya dole ne in san yadda zan yi in kawo ƙarshen matsalar nan dangi ai sune mutum, duk da dai yanzu zamani ya zo da mutane suke ɗaukar ƴen uwan su ba abakin komai ba musammam idan ƴen uwa basu da shi amma a ko da yaushe ai mutum rahama ne,
haka na kwanta ina tunanin yadda zan ɓullo da lamarin gyara tsakanin mijina da *dangin sa* haka na kwnta tare da yin bacci na me daɗi kasancewar shawara ta zo min na san ta yadda zan fara mission ɗina
kashegari da wuri na tashi bba tayi wa yaran wanka ni kuma na haɗawa me gidan breakfast tare da kai masa, fuskar sa a sake ba alamar fushi ko wani abun don haka nima sai na saki raina, jikin shi na je na zauna, shi kuma sai ya ƙara jawoni jikin sa tare da sinsina ni
"me jego kina ɗaukar ƙamshi" ya faɗa tare ƙara cusa kan sa cikin jikina
ƙyale shi nayi yadda yake so da jikina ko ba komai ya yi missinga ɗina
"hubbi ka sauko kayi break fast"
"ur wish mi lady" ya faɗa
sai da na tabbatar da ya ci ya ƙoshi sannan na raka shi ya ga yaran wɗanda suka sha kwalliya sannan ya kama hanyar office ni kuma na koma gida don fara misaion ɗina
waya na ɗauko na kira aunty bilki ƙanwar bbn abu haidar na faɗa mata haihuwar tai murna sosai tare da min addua inda nai mata tayin ko zasu zo sai tayi ɗan jim kana daga bisani tace too shike nan in shaa Allah zasu zo
aika mata nayi da kuɗin mota ta account ɗin maƙociyata sannan na kira ta na faɗa mata ga kuɗin mota nan na turo masu kuma don Allah su zo da iya, tai murna sosai tare da cewar zasu zo, komawa nayi na kwanta ina fatan Allah yasa abinda nayi ya kawo ƙarshen wannan matsalar su
Ku yi haƙuri da wannan muna biki ne 😁
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
*Na kuma kwafsawa last page ba number don haka bari mu barshi a page 35 ɗin*😁😁
Page :37🌹
Kwanana huɗu da haihuwa mutan lagos suka ƙaraso har da maryam ita da take fama da tsohon ciki, sun aunty bilkisai ana gobe suna suka zo har da iyar kuwa
nayi murnar ganin su sosai matar tj salma ma tazo da ɗan babyn ta da ta haifa, wanda ban samu damar zuwa suna ba, nai mamakin da banga ƴen uwan tj ba ko dna tambayi salma si tace tj ne ya ƙi faɗa musu, na san dalilin daya sa ya ƙi faɗa musu sai nayi shiru kawai
Gida ya cika daƙam ya tubatsa yai albarka ko ina baka gani komai sai mutane,
ranar suna nasa akai mana decorating bayan gidan filine babba guda ba komai a gurin nan na sa aka sama kujeru tare da yi masa decoration me ƙayatar wa
anan aka zauna akayi shaglin suna lfy lau inda ɗa ci sunan kakan sa na wjen uba wato sani wanda zamu kira da muhammad, da yamma ana cikin hidimar sunan nan aliyu ya kira ni
rannan na shi a ɓace ba alamar fara'a
"lfy me ya faru ne" na tambaye shi, ranshi a ɓace, ya riƙe min kafaɗa ta tare da haɗa ni da bango
"me na ce miki akan waɗannan mutanen, ba nace miki ba ruwan ki da su ba, me yasa ba kya jin magana"
sai yanzu na fahimci da waɗanda yake magana
"amma abu haidar baka ganin..........."
"shut d hell up, ki kore su yanzu su barmin gidana in ba haka ba ki fuskanci fushi" ya faɗa yana saki na tare da juya wa da barin wurin
sai da na nutsu sannan na koma wajen taro na, ina iya hango su yadda kowacce a cikin su ta saki jiki tana ta hidima tare da dariya ya za ayi ince musu su tafiya ai ban isa ba na faɗa araina sai dai kayi duk abinda zakayi na faɗa araina
aliyu be zo ɗakina ba a daren ranar suna ba kamar yadda yake yi kullum nasan har yanzu fushi yake yi, don haka nima sai na ƙyale shi,
kashegarin suna aka fara haramar tafiya amma banda su iya koma sunce zasu tafi bazan barsu ba don kuwa ni burina shine in gyara tsakanin su kafin su koma, haka muka wuni ana shan hira tsakanin juna na gagga text ɗin aliyu nace war in kore su kafin ya dawo ni kuma sai na yi kamar ban gani ba
Ko da ya dawo da daddare har ɗakina ya shigo tare da min kashedin cewar idan na kuma bari suka kuma kwana a gidan sa to har dani zai kora, hankali na ya ɗan tashi don banga alamar wasa atattare da shi ba
suma anasu ɓangaren wai burin su in haɗa su da shi su gaisa tare da yi masa barka basu san wainar da muke toyawa ba akan su, don hka sai kawai na bisu da cewar baya gari don haka sai suka ƙara sakin jikin zama a gidan
kashegari ma haka gari ya waye rana ta take amma banga alamar su iya suna da niyyar tafiya ba har su khadija da ƴen uwana na lagos suka kama hanya amma su iya ba labari kuma ni fisabillahi bazan iya cewa su tafi ba
sai bayan la'asar sannan naga call ɗin aliyu na ɗauka amma hankalina gabaɗaya ba a jikina yake ba ko me zai ce min
"na ce ki kori waɗannan mutanen ki ƙi ko to ki tabbatar ban dawo na tarar da ke ba" yana gama faɗin haka ya kashe wayar
to faa yau ake yin ta in tafi inje ina na faɗa arai na, har dare jikina a sanyayae yake duk sai naji babu wani kuzari a tattare da ni ni da nayi haka da niyyar gyara amma sai gyara yake shirin taɓa min lfyr aure, wai aliyu wane iri ne na tambayi kaina, kasa bacci nayi don haka sai na zauna don kiran ya dawo in bashi haƙuri amma har kusan ƙarfe sha biyu ba shi ba labarin sa bansan nidai lkcn da bacci ya kwashe ni ba
kashegari da safe sai na aiki me aikina nace mata taje taga idan aliyu ya fito in zai fita ta faɗa min don ina son ganinsa
bata wani daɗe ba sai gata wai ya fito yana waje gurin parking motoci, iya tana ɗakin ta faɗi haka don haka sai ta miƙe
"bari inzo muje mu gaisa" na so in hana ta amma kafin in ce wani abun har tayi waje don haka sai nayi shiru na bita kawai
yana tsaye ya ci kwalliya cikin shadda milk colour ya ɗauko hular sa zanna bukar ya sa kansa yai mutuƙar kyau da kwajini, na ƙarasa kusa da shi tare rage sautin muryata sosai
"ka tashi ƙalau" na faɗa, bai juyo ba balle ya ansa kawai ya cigaba da abinda yake yi
iya ce ta ƙaraso kusa da mu da ƴar fara'ar ta
"ali ina kwana, an samu ƙaruwa Allah ya raya, ai mun ɗan jima a garin nan me ɗakin ka tace baka nan , ashe ka dawo"
kallon iskar da ta kwaso ta ma baiyi ba sai yayi gaba, ni kuma ina tsaye a wurin raina yai mugun ɓaci akan abinda yayi mata ko ba komai ai ta girme shi ita ce fa haifi ubansa duk abinda tayi masa ba kanta tayi wa ba
ashe bai gama rashin mutuncin nasa ba, ƙarasawa yayi kusa da me gadi sannan yace masa da ƙarfi yadda zamu ji
"idan na dawo na tarar da waɗancan a gidana ba a kore su ba abakin aikin ka" ya faɗa yana sa kai ya fice
wannan abun da yayi ya mutuƙar ƙona min rai sai naji kamar ƙasa ta tsage in shiga ji yadda ya disga baiwar Allahn nan a gaban ma'aikatan sa bayan ita ta kasance uwa ce ga mahaifin sa, haƙuri na fara bata inda ita kuma tace
"babu komai abu bari muje mu haɗa kayan mu munma gode da irin karrama mun da kikayi"
jikina a sanyaye na bi bayanta muka koma cikin gida inda naji tana faɗawa ƴaƴanta su haɗa kayan su su kama hanyar kano
"iya har zamu ko sati bamuyi ba" naji ɗaya daga cikin ƴaƴanta na faɗin haka
"to me muka zo yi ba suna ba, naga anyi sunan kowa ya watse to muma zaman me zamuyi, shi me gidan ma baya gari da yana gari ne da sai muce zamu zauna domin sa" ta faɗa
jikina ne duk yayi sanyi nasan tabfaɗi haka ne don ta rufa masa asirin abinda yayi mata amma gaskiya aliyu be kyauta ba,ai ance baƙon ka annabin ka
haka suka haɗa kayan su ina ji ina gani suka kama hanyar gida na bisu da kuɗin motar da nasan zai kaisu kano har da chanji
raina ne yayi mutuƙar baci lallai ma aliyun nan yau in ya dawo yau sai yasan cewar ni ya taba na faɗa araina har yamma haka na wuni ina tunanin irin rashin mutunci da zanyi wa aliyu idan ya dawo don gaskiya ya kaini bango
don yana kuɗi shine zai dinga ganin kamar ya fi kowa zai iya taka kowa ya kwana lafya ba abinda na tsana da ya wuce wulaƙanci ɗan adam yana da daraja, duk lalacewar ɗan adam ne kuma ubangiji yana ƙaunar kayan sa to akan me zamu wulaƙanta su don kawai kai Allah ya fifita akan su
kuma daɗin daɗawa wai mijina ne yake wannan wulaƙan ci gaskiya da sake wai an bawa me kaza kai bazan ɗauki wannan abin ba
[7:45PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page:38🌹
Aliyu be dawo gida ba aranar, don da safe dana tambaya sai aka ce min dawo, inda daga ƙarshe na samu lbrn ya tafi china, raina ne ya ɓaci wato ban ma kai matsayin da zai gaya min ba kenan ko, mmm zai dawo ne dani yake zancen
wasa wasa sai da aliyu ya kwashe wata har uku ba shi babu labarin sa shi be kirani ni ma kuma ban kira shi duk da dai ya aiko da wani yaro ya kawo min numbers sa ta can wai ko idan ina neman shi, wato ban isa ya kira ni ba sai dai ya turo min da number ko wai in kira shi to yaje yayi ta zama acen zai ga mara zuciyar da zata kira shi na faɗa a raina
*************
Aliyu yana zaune ranshi ne a ɓace wai ace zainab yauzu watan shi uku amma bata taɓa neman sa ba, kuma har tura mata da number da zata same shi tayi amma sai ta ƙi kiran sa
Tun bayan haihuwar mohd Allah ya bashi sa ar mallakar wani tafkeken jirgin ruwa wanda mutane daya wa suka so mallaka amma cikin ikon Allah me jirgin ya siyar masa,
wannan ne dalilim daya sa bayan sunan mohd ya kamo hanyar china ba shi don ya zo ayi wa jirgin gyaran daya kamata, kasancewar jirgin a bakin teku yake yasa dole nan ya koma tare da ɗaukar ƙwararrun ma'aikata don gyaran sa
jirgin tsohon jirgi ne, don haka dole yana buƙatar gyara sosai, inda yake sam babu service don kuwa can wajen garine sosai anan akaa ajiye jirgin, sai dai local telephone wadda baka iya kira ba sai dai a kira ka
wannan dalilin ne yasa ya aikawa da zainab number don ta neme shi amma cikin ikon Allah so ɗaya bata taɓa kiran sa ba, bata taɓa tunanin haƙin daya ke ciki ba amatsayin sa na mijinta balle tace zata kira shi
ya kai duban sa ga makeken jirgin ruwan da ake ta faman aiki a kai, in shaa Allah nan da wata guda za a gama aikin sa kamar yadda ma'aikatan suka ce, ya tuno irin gwagwarmayar daya sha kafin ya mallaki jirgi amma sai ya ji duk wani harkar jirgin ya fita kanshi idan ya tuno yadda matar sa tai watsi da lamarin sa
akwana a tashi Allah ya basu aliyu damar gama haɗa jirgin sa lfy, jirgin ba ƙananan kuɗi ya ci ba don gyaran jirgin ma ya fi kuɗin jirgin tsaɗa komai sai da aka canza sabo, komai sai da akayi modernizing ɗin sa shi kanshi yana mamakin irin kashe kuɗin da yayi akan jirgin amma idan ya tuna cewa cikin watannni ma zai iya mayar da kuɗin jirgin dana gyaran sa sai ya ji ɗan sanyi
ko yanzu ya saka jirgin a kasuwa zai samu riba sosai amma kasancewar harka da jirage na jigilar kaya shine sana'ar sa yasa shi doe ya bar jirgin sa don ya mori abin sa ba shi kaɗai ba harma da ƴaƴan sa
bayan an gama haɗa jirgin akai launching ɗinsa ya fara aiki, ko da aliyu yaga jirgin ya hau teku ya fara aikin sa sai shima ya fara haɗa ya nashi ya nashi don ya kamo hanyar gida, yana murnar zai zo yaga iyalin sa amma can cikin ranshi yana jin haushin yadda zainab duk wannan daɗewar da yayi bata taɓa kiran sa ba
jirgi ya sauke passangers ɗin sa daya ɗauko daga china lfy a abuja a cikin su kuwa harda aliyu ajaban, sanye yake cikin Texido ɗinsa blue daga gani dollar tayi kuka wajen siyen texido ɗin nan, ya yi shar dashi kamar wanda ya dawo daga honey moon
driver ne yake jiran shi don haka yana zuwa ya shiga mota ya kama hanyar gida, ya riga ya gama shirya rashin mutuncin da zai yi wa zainab har yanzu bata san shi ba tana ganin da ta haifi ƴaƴa biyu bazai iya rabuwa da ita ba, to shima da mahaifiyar sa ya girma kuma gashi nan dam ba abinda ya same shi rayuwar sa yake kamar kowa
ko da aka shige get ɗin gidan ya ganshi fes kamar yadda ya sa ran samun shi da kewar iyalen shi ya dawo amma sai ya dake ya kama hanyar part ɗin sa, ba tare da ya kalli part ɗin natan ba don shi a tsarin shi mace bata isa ya bita ba, don shine gaba da ita
a gaskiya yai tsammanin ganinta amma ga mamakin sa sai taƙi zuwa har dare yayi babu ita balle yaga ƴaƴan sa me kenan zainab take nufi
ita ma dai zainab a nata ɓangaren tana jiran shi ya shigo don taga dawowar sa harda ɗan shirinta don tasan yadda ya kwashe kwanakin nan bai gansu ta san zai shigo ya biɗa haƙƙin sa amma abin mamaki shiru bashi ba labarin sa har bacci ya kwashe ta
duk kowannen su ya kwana tare da bacin ran ɗan uwan sa, abinda bai taka kara ya karya ba ya kai ga masoyan nan cikin tashin hankali kowannen su yana ji haushin ɗan uwansa yana gani ɗan uwan bai ɗauke shi da daraja ba
haka suka tashi kowannen su yana cike da ɗan uwan sa gaba ce sosai ta shiga taakanin su inda a kowane ɓangaren suke cutuwa kuma suna begen juna tare da fatan faɗan nan zai zo ƙarshe amma da yake sun bar shaiɗan ya na yi musu huɗuba sai kowanne ya ɗau fishi tare da ɗorawa ɗan uwan sa laifi
har aliyu sai kwashe wata da wani abun gabar nan tasu babu sauƙi, ya gaji don haka sai ya nufe ta don ya na son sanin me take taƙama da shi da har zata dinga yi masa wannan abun kamar ba mijinta, wannan karon ba zai juri rashin mutunci ta ba inda tayi taga taci riba wannan karon bata isa ba ya faɗa tare da dosar part din natan
itama zainab a nata ɓangaren abin yana damun ta mutumin nan me yake nufi kenan bata wata daraja kenan ya tafi kusan wata huɗu be taɓa neman su ba yanzu kuma ya dawo ko ta kansu be bi ba hidimar sa kawai yake yi, wasu hawaye na takaici suka zubo mata bata bi ta kan hawayen ba sai ta ƙyale su suna zuba da kansu ko taji sanyi zuciyarta
banko ƙofar ɗakin natan taji anyi kamar ana yaƙi da sauri ta goge hawayen da ke zuba tare da juyowa taga waye, gogan ne ranshi a bace yana tsaye tare da riƙe ƙofar da hannun sa fuskar nan tasa kamar me don ya bala'in haɗe rai
"ke wai me kike taƙama da shi ne ki faɗa min, ko an gaya miki bazan iya rayuwa bake bane ko kuma don kin haifa min ƴaƴa guda biyu shine kike tunanin zakiyi min rashin mutuncin da ranki yake so, bazan zauna da matar da bata da mutunci ba wacce bata san mitinci mijinta ba kina ƙarƙashina amma baki san komai na kula da miji ba so kike yi kullum ya kasance ni zan dinga binki, ki kalle ni kyau banyi kama da namiji me bin mace ba ita kuma tana yin rashin mutuncin ta ni ban ɗauki mace a bakin komai ba face abara ajiye wa agida
ko kina tunanin ni da ƴaƴa na bazamu iya rayuwa ba sai da ke ki kalle ni nan tun uwata ta haifeni ta gudu ta barni kuma gani nan daram har nafi wasu mada suka rayu da iyayen su don haka bazan juri wannan rashin mutuncin naki ba tare rashin tarbiyya
ki shirya kayan ki ki koma gidan ku idan kinje kin koyo yadda ake kula da miji kya dawo don bazan iya zama da macen da bata san darajar mijinta ba, har ya fita ya dawo
kuma da fatan bazaki tafin min da ƴaƴa ba ko ɗaya har mohd ɗin ma ki ajiye min abina don bazan bari suje su koyo rashin tarbiyyar da kike taƙama da ita ba
ya fita daga ɗakin tare da banko ƙofar kamar zai balla ta kuka kawai na saki tare da tausayawa kaina, rashin mutunci aliyu ya isheni haka duk abinda yayi min be ishe shi sai daya biyo ni har ɗaki yai in rashi mutunci gaskiya dole ne in bar masa gidan sa na faɗa ina fara haɗa kayana
[7:46PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page:39🌹
Haɗa kayana na fara yi tare da sa na mohd ni ba mahaukaciya bace idan shi bashi da tausayi to ni ina da shi haidar de zan bar masa amma bazan bar masa ɗana me shan nono ba na faɗa araina
Bayan na gama haɗa kayana na fito da su tare da kiran masu aiki su taimaka min su fitar min da akwati na har bakin get naje da mohd a goye a baya na ga akwati na ina ja, amma sai me gadin ya hanani,
"hjy yallaɓai yace kar in barki ki tafi da yaro ko ɗaya" kaina ne ya ɗaure au har faɗawa ma'aikatan sa yayi cewar kar in tafi da yaro ko me
Na kai duba ga mohd wanda yanzu na sauko shi sai baccin sa yake tayi, hawaye naji sun cika min ido ya za ayi in tafi ba tare da wannan yaron ba me yayi, in ni yana ganin nayiasa laifi ɗana fa me yayi yaron da babu abinda yake ci daga nono sai ɗan ruwa in yaga dama
Komawa nayi cikin gidan indai kuwa bazai bari in tafi da ɗana ba to kuwa babu inda zani na faɗa, bai dawo ba sai dare, ya shigowa part ɗina ya nufa fuskar shi amurtuke
"ke da yake bai da mutunci nace ki tafi shine kika ƙi tafiya ko"
"ce maka akai gidan ka aljannah ne da zaka ce na ƙi tafiya, na so tafiya me gadinka ya hanani"
" au da kina nufin da ƴaƴa na zaki tafi"
"ai kai da yake baka da imani shine zaka raba ni da wannan ɗan jaririn" na faɗa ido na taf da hawaye
"rashin imani kike son gani, yau zaki san kin zo ƙarshe"
Ƙwace mohd yayi daga hannun na, bazan iya cewar zan hana shi ba don in muka ce zamuyi kokawa akan yaron shi yaron ne zai cutu,
nanny ɗin sa ya kira me suna hannatu don yanzu na sallami kafiran nan nannies ɗin yara duk musulmai ne, yace ta karɓi mohd ina kallo aka fitar min da yaro na kuka kawai nake yi ban taɓa ganin wulaƙanci irin wannan ba a raba ka da ɗan ka
dawowa yayi kaina yana jana har sai daya kaini waje sannan ya sani a mota tare da driver ɗin yasa lock a motar sai ga kayana an biyo ni da shi har da yar jakar hannun na
window ɗin ya buɗe tare da wullo min purse ɗin a fuskata "duk randa kika san darajar miji kya dawo" kuka na saki me sauti in Allah ya yadda ni aliyu har abada bazan kuma zama da mutumin da be san darajar ɗan adam ba na faɗa
driver ya ja muka fara tafiya sai lagos ina jin shi yana ja wa driver ɗin kunne ya tabbatar da ya ajiye ni a ƙofar gidan mu, sai kace wata yarinya, ranar naci kuka irin wanda ba taɓa yi ba
wai dama haka mutum yake ji idan wanda yake so ya ƙona masa rai don Allah ya za ayi in iya yafewa aliyu irin wannan cin kashin da yayi min, sai asuba sannan muka ƙarasa lagos aikuwa har ƙofar gidan namu ya kaini lkcn gari ya waye ma sosai kasancewar go slow ɗin da muka tarar a hanya
adaidai ƙofar gidan mu yayi parking tare da fita ya ƙwanƙwasa gidan ina zaune cikin motar ina jiran shi don gabaɗaya motar a kulle take har yanzu be buɗe ba
wata yarinya ce tazo ta buɗe, sai shi kuma ya juyo ya zo ya ɗaukar min akwatina tare da miƙawa yarinyar sannan ya buɗe min ƙofar na fita
tooo faaaa yau ake yin ta me zancewa baba kenan, na faɗa araina, ohhh ko ya ɗana mohd ya kwana shi kaɗai ya faɗo min araina naji wasu hawaye, goge hawayen nawa nayi sannan na saka kai na cikin gidan namu yau dai sai yadda akayi da ni
nayi mamakin dana ga falon gidan babu kowa sai yarinyar nan da ta buɗe min daka gani ƴar takwa ce ( ```irin yaran nan da ake ɗauko su daga niger suna yin aikatau```)
"ina maman" na tambaya ina neman wajen zama
"ta tafi shagamu da asuba ita da baba"
"me akeyi a shagamun"
"ɗan ƙanwarta ne ya rasu jiya da daddare shine sukayi sammako don su samu jana'iza" ta faɗa
Allah yayi mama da ƙanne sosai a shagamu don haka sai ban damu da sanin ko wacce bace na dai bishi da addu'ar Allah ya jikan rai
"to ina su amina da su bashir" na kuma tambayar ta ƙannena, wato ƴaƴan mama
"duk tare suka tafi"
"ke kaɗai ce a gidan" gyaɗa min kai tayi, daga gani ta ɗan jima a gidan amma da bata daɗe ba mama bazabta taɓa barin ta ita kaɗai ba
miƙewa nayi aikuwa banga ta zama ba da su mama na nan ne da sai in zauna amma tunda ba wanda ya san na zo gwanda in ƙara gaba don yanzu da sun dawo ni zasu ba rashin gaskiya tare da mai dani wurin wancan mara mutuncin da be san darajar ɗan adam.ba na faɗa tare yin waje da ɗan akwati na
"aunty zaki tafi ne in ta dawo wa za ace mata tazo" shiru nayi ina tunanin wa zance ni yanzu duk na manta ƙawayen maman ma balle in anbaci sunan ɗaya koma zan iya anbata ƙila yarinyar ta san su sai nace mata
"kice mata ƙanwarta ce ta zo su tafi shagamun tare, ko da yake barshi ba sai kin gaya mata ba idan muka haɗu acan zan cemata na biyo ta nan" to kawai tace min nai mata sallama na kama hanyar waje
purse ɗin da ke hannuna na duba naga tabbas kuɗin ciki zasu kai ni kano daga nan tashar mota dake agege na nufa domin kama hanyar kano
*************
duk da dai yasan badace ba abinda yayi mata amma hakan a ganin shi shine dai dai ƙila idan taje ayi mata faɗa, gaskiya yana son zainab sosai amma wani lkc dole ya rufe ido ya taka mata burki idan tanas wani abun nata
madara yaje ya siyo wa mohd, kan a dinga bashi shima sai yanzu yaga kuskuren shi ƙwace yaron da ya bar mata shi ƙiri ƙiri yaro ya ƙi shan madara tunda be saba da feeder ba, don haka sai ya ƙi karɓa yana ta kuka
haidar ganin ɗan uwansa na kuka ya sa shi fara kuka tare da kiran ```ammi na```kuka kawai suka dinga yi daga shi har mohd ɗin, nannies ɗin nasu rasa yadda zasuyi sai suka kira aliyu don ya san a halin da ake ciki
yana zaune a office aiki ne gare shi sosai a gaban sa, amma kusan rabin hankalin sa ya kan wayar sa yasan iyayen zasu iya kiran any moment shi ma so yake yi ta dawo ko don ƴaƴan sa ya faɗa,
"taurin kai gare ki baki iya bada haƙuri ba duk da kin san ke me laifi instead sai ki ka so yi min rashin kunya"
gabaɗaya ya rasa abinda yake masa daɗi, yana cikin wannan tashin hankalin ne ya samu waya daga gida inda aka gaya masa halin da yaran suke ciki
wannan shine tashin hankali akan tashin tashin, haɗe kayan sa yayi ya kama hanyar gida, yana zuwa gida ya ga halin da yaran suke ciki duk sai yaji ya ƙara shiga ruɗani, ya rasa abinda yake masa daɗi, wai me yasa iyayen zainab har yanzu basu kira shi bane ko kuma ƙarya taje tayi masa, ya tambayi kansa
ɗaukar yaran yayi ya sasu a mota ya fita dasu ƙila in sun ga waje sayi shiru, ga haidar wannan abin ya ɗanyi yi masa aiki amma mohd ko a jikin sa yunwa kawai yaron yake ji don haka kuka kawai yake yi babu ƙaƙƙautawa
hankalin shi fa ya tashi sosai da sosai, asibiti ya nufa direct don kar yaron ya kamu da wani ciwon saboda kukan da yake yi, babu abinda aka ba mohd face da aka cewa aliyu yunwa kawai yake ji a bashi abinci, ya roƙi dr. cewar mmn shi ba lfy ta tafi jinya kuma ya ƙi cin abinci
sai da dr. ɗin ta gama yi masa faɗan ta sannan ta sa ya kawo mata abincin babyn ta haɗa masa da ɗan dumi ta bashi da yake yaron yaji yunwa sosai sai kawai ya karɓa ya fara sha, aliyu har wani ajiyar zuciya yayi da gode wa Allah daya ga mohd ɗin ya karɓa, sai daya sha ya ƙoshi dr. ta lallashe yayi bacci sannan ta ba aliyu shi tare da ce masa akai shi wajen mahaifiyar sa
shidai be tanka mata ba don shi a ganin shi babu abinda zai sa ya nemi zainab bayan ita bata ne me shi ba, kai inta neme shi ma sai ya wana ta sosai ya ja mata aji don tasan cewar shi ba kanwar lasa bane (``` ni dai mmn walid nace zamu ga me jan ajin kai da kake fama da ƴaƴa da ita da take ita kaɗai```)
be koma gida ba sai daya biya ta wani pediatric hospital ya sa suka yo masa hayar nanny wacce tasan kan yara sosai, sannan ya haɗa da ita da yaran ya kai gida shi a tunanin sa ya gama da wannan
[7:46PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
Page :40🌹
Bamu muka iso kano ba sai ƙarfe takwas na safe kasancewar sai yamma muka taso, ina sauka na kama hanyar jakara gidan su aliyu, ko da naje na ga sauka kyakkyawa kuma yanzu iyar ba laifi don gaskiya ina turo mata ɗan abin inna samu
Tea ta haɗa min da egg ɗina har da bread, sai da naci na ƙoshi har na manta rabon da inci abinci, sannan nai mata bayanin zuwa na, tai mamaki sosai sai tace min ina ƴaƴan na faɗa mata duk yadda mukai da shi,
Ita kanta sai da naga jikinta yayi sanyi ƙila ta tuno da rayuwar aliyun ne
"haƙuri zakiyi abuu ki koma ɗakin ki ki riƙe ƴaƴan ki"
"iya ƙyale shi jikan nan naki be san darajar ɗan adam ba ya ɗauka kuɗi sune komai, idan yaji a jikin sa ya fahinci daraja ta na koma, amma yanzu nan nika zama" na faɗa tare da gyara zama na
"to shi sanin fa kin yaye shi ne"
"ina fa ya kwace shi, amma ai ina matse nonon idan ya ciko don haka zan cigaba da matse wa kar yayi tsamin har Allah yasa ya dawo da shi"
"ohhh ni saude wannan hali naku na yaran zamani"
"iya wallahi ba laifina bane" Iya de bata yadda ba babu yadda bata yi da ni ba akna in koma naƙi, haka ta haƙura ta zubawa sarautar Allah ido don ba yadda zatayi dani
da daddre da ƴaƴan ta suka dawo sai ta gabatar musu dani amatsayin na zo zan ɗan zauna ne amma bata faɗa musu daliin zuwan nawa ba, nima kuma sai naji daɗin hakan
kashegai iya ta kaini na zazzaga cikin gidan daga waje gidan yake ƙarami amma idan ka shiga ashe da girma sa waje waje ne kamar gidan ƙauye sai dai kowa ya ɗan gyara nasa dai dai ƙarfin sa
daga can ƙarshen gidan ne wani part shi kuma amma ya rushe ina jin ko rashin samun gyara, har gurin rusashen ginin muka je
"kinga nan nan ne gadon mijin ki"
"iya da gaske na faɗa fuskata da fara'a"
"sosai ai marigayi sani yana da gadon baban su, don haka kinga ai doe a ba mijinki gadon uban sa kuwa ko"
tsayawa nayi ina kallon gurin a taƙaice zai iya yin ɗaki biyu da ɗan banɗaki da kitchen harda ɗan tsakar gida, sai na juyo ga iya
"za a samu masu gini a unguwar nan"
" me ze hana ai ɗana lawan ma magini ne me zakiyi"
"ginawa zanyi in zauna a cikin sa"
mamaki ne taf fuskar iya
"kinsan kuwa gini da cin kuɗi" ta faɗa
"ba komai ai nima na zo da su"
"shi ke nan zanyi wa lawan ɗin magana sai a fara"
"yauwa iya" na faɗa
ko da ɗan iyar ya dawo oyar ta faɗa masa ra'ayin zainab ɗin na son gina part ɗin ijina sai yaji daɗi ko ba komai ɗan ɗan uwan su zai dawo gare su, tayi masa baya non ɗakin biyu take so da ɗan banɗaki inda hali da kitchen da tsakar gida
dariya yayi yace "kina rena wurin nan idan nace miki zeyi ɗaki uku da banɗakin babba da tsakar gidan kuma fa, ai shi fili kina ganin shi haka idan an gina shi kuma abinda za afitar a ginin yana da yawa"
nai masa godiya tare da cewa yayi min ɗaki biyu kowanne da banɗakin sa da kitchen da tsakar gida
muka rabu da shi akan zai je ya ga nawa ginin zai ci kuma nawa zan fara bayar wadon a samu a fara a sa, nai masa godiya sosai, bayan kwana biyu kuwa sai gashi ya kawo min list,
aunty bilki na kwasa muka je banki nayi using atm card ɗin da aliyu ya bani tun ina gidan nayi withdrawing kuɗin da zasu ishe ni sannan daga nan nayo iya cefa ne, ko da na kawo masa kuɗin a ranar yasa yaran sa suka fara ƙarasa ruguza ragowar ginin da bai zube ba tare fara haƙa
**************
aliyu dai rayuwa ta juya masa abaibai, don kuwa yaran gabaɗaya basa jin daɗin canjin da suka samu, ya rasa abinda yake masa
mohd baya cikakken kwana biyu da lfy bini bini ya kama gudawa ko amai, kuma indai ya kama yin su baya denawa har sai in an sa masa ruwa don gudawar tsululu haka yake yin ta
shima kanshi haidar zazzaɓin dare yake ta fama da shi ga yawan kiran ```ammi naa```kullum dare haka ake fama da shi, anke asibitin amma ina har nanny ya sha canza musu ko nannies ɗin ne amma ina
shi kanshi ba daɗin yake ji ba yana fama da zuciyarsa wanda ayanzu takan tayar masa akai akai ya sha zuwa asibiti sai likita yace masa ya daina damun zuciyarsa da bakin ciki ya dinga barinta tana huta wa saboda he has a weak heart very weak one,zata iya bugawa at any moment idan ya cika damun ta kuma zai iya rasa rayuwar sa saboda hakan, tayaya zai iya wai controling ɗin ta bayan zainab ta tafi kuma wai ƴen gidan su sun ƙi neman sa don sulhu
abubuwa ne suka haɗu suka chakuɗe masa, rasa yadda zaiyi yayi ga yaran kusan kullum basu da lfy barina mohd har yanzu ya kasa sabawa da madarar da yake sha, ba irin madarar da ba ai masa trying ba amma duk a banza be dena gudawar nan ba duk ya lalace da shi
shi kanshi haidar kusan kullum da zazzaɓi yake kwana tare da kiran sunan zainab ɗin, wayar sa ya ɗauko ya kira tj yai masa bayanin duk halin da yake ciki, don bashi da wanda zai gaya wa da ya wuce shi
faɗa sosai tj ɗin yayi masa kamar wani ɗan yaro sannan yace zai zo abujar suje lagos don dawo da ita, ba abinda aliyu yake yi sai godiya sai kace qanda tj ɗin yayi masa kyauta
tj ma be ji daɗi ba ko kaɗan ɗauko wayar sa yayi ya kira zainab ɗin amma wayar ta a kashe take don haka sai ya ajiye, ya fara haɗa kayan sa domin zuwa abujan, aliyu yana da matsala menene na korar da mace har da kwace mata ƴaƴa, daga gani zanab ɗin ba ƙaramin haƙuri take yi da ɗan uwan nasa ba
sarai ya san halin aliyu ba haƙuri gare shi sosai, ko ma dai menene idan Allah ya kaimu muka je maa jo ko menene, su ma iyayen zainab ɗin basu hankali ba ya fɗa a ransa, ai da sai su kira shi suji me ya haɗa su ko basuyi don komai ba sayi hakan dan ƴaƴan zainab ɗin
kashegari da safe tj ya bi jirgin safe daga kano zuwa abuja daga nan suka bi private plane ɗin aliyu zuwa lagos ƙarfe 11:00 dai dai na safe sun sauka agarin lagos daga nan suka kama hanyar gidan su, fisabillahi aliyu farin ciki ne taf zuciyar sa ganin yau zai ganta amma a fiskar sa sai ya wani haɗe rai kar ace ya kasa
amma abin mamaki da takaici sai mutan gidan su zainab suka ce ai bata zo ba, aliyu yai musu bayanin cewar shi da kanshi yasa ta amota drivern sa ya kawo ta lagos amma inaa suka dage bata zo ba
a bayanin da yake musu ne mama ta gano ai ranar da zainab ɗin ta gano cewar ranar da zainab ɗin tazo suna shagamu, don hka sai ta kira me aikin ta tare da tambayar ta ko tayi bakuwa ranar da ta tafi shagamu,
me aikin ta tabbatar mata da ƙanwar ta tazo a kwatancen da me aikin tayi na baƙuwar anan suka gano cewar zainab ɗin ce, to amma ina ta tafi daga nan shine babu wanda ya sani, nan aka shiga neman ta amma inaa duk inda ake tunanin za ta je amma abin mamaki bata nan
ko da su aliyu suka ga babu wani nasara sai suka kama hanyar abuja tare da yaran don yace ba zai iya barin yaran nan lagos ɗin ba duk da dai mama ta o ya barsu, amma ƙiri ƙiri ya ƙi haka suka koma jiki duk babu ƙwari
[7:46PM, 12/7/2017] +234 806 803 7117: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀
By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)
🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺
0 comments:
Post a Comment